Showing 48001 words to 51000 words out of 328222 words
Chapter 17 - Murfin Jallo Dan Uwa By ZAINAB IDRIS MAKAWA
basu rabuwa da gyara kullum.
Mamace ta mike take fadin bari ta duba ko ta falka ta bata maganin ta shiga nan
nake fadawa Salima takaddaman da mukeyi da ummah din wai kada a zageta yarta na
asibiti kwance ace tana batun kitso ita.
Lah ummah kizo gida ki wanke idan ba zaki zo ba kuma sai a kaiki sallon a wanke
maki a can tunda shi kitso dole sai anyishi.
Murmushi tayi tana fadin boni jam saloon kuma yar nan meya kaini zuwa saloon a
wanan shekarun nawa kuma yanzu ai garama inje gidan baku aimin a can din.
Itama salima din tayi dariya tana fadin kukan filani Allah yayiku da kunya ummah
meye a cikon kunyan haka kuma tunda ba tsufa kikayi ba ai nifa har yanzu zuciyata
ta kasa yarda cewa kece kika haifi su Ramaah wallahi.
Don kinfi kama da ace kece yayarsu dai ba mahaifiya ba ummah don sam baki tsufan
haihuwansu ba haka tayi murmushi tana dukar da kai.
Wai meyasa mutane da dama suke fadan hakane garemu bakece kika fara fada ba kowa
haka yake fadi a kanmu idan ya ganmu da ummah din.
Mama ta fito da kayan abincin da anty Yanda taci hakan yasa na tashi da sauri na
karbo a hannunta tana fadin tagode kayan da zamu dawo gida dasu ta fara tattara
muna waje daya harda wa yanda zan wanke masu.
Karfe shidda a gida yai muna ban kuma zauna ba saida na wankewa ummah mu kayan
nata dana anty yanda da ake kawowa gida in wanke ko yaushe.
Abinda ke ban mamaki yadda na kula da matan gidan basu damu da zama yar uwata
asibiti ba irin yadda na sani idan dan uwanka yana kwance ka dan rika lekasa din
sam basa sunayin hakan gareta ba su ?
Hakan yasa na kara nisantar lamarinsu iyakata dasu gaisuwame tun bayan da naje
neman magani in hade saboda ciwon kan daya kamani ta dalilinsu suka hana min magani
saida mijinsu ya sawo min har yanzu kuma ina amfani da sauransu wajena.
Iya taje asibitin ta zauna da matan kawu dauda a ranan don su karbawa su mama
zaman su dan dawo gida su dan sarara hakan yasa na samu daman banyewa ummah kai
nayi mata kitso irin wanda na saba yi mata a gida.
Sai wanan ranan yan gidan suka san dana iya kitso sosai har salima na fadin zan
mata idan ta banye kanta.
Port,harcourt rivers state ya J ne ya gama shirinsa na tafiya ma,aikatar da
zaiyi singnig don kayansu su samu shigowa arewa a cikin wanan watan.
Don sun gama duk wani proces din da akeyi dashi da maigidansa yana shiga wajen
yana kiyasta irin dukiyan dake kasan nan ta Nageria da Allah ya bamu.
Amma dan arewa yana zaune a cikin kunci yake rayuwansa zai iya rantsewa a wajan
nan ba wani bahaushe saishi kadai duk da suna bat da kama da irin shigar mutanen
wajen a yanzu.
Don shine ba zai rantse da hakan ba a lokacin a madakatar da zai sadaka da wajen
da za a sakama hannu din ya samu mutane birjit dake jiran su gana da babban mutumin
.
Wanda kowa da laluran daya kawoshi wajen bai dade da zama ba wani ya fito daga
office din yana kiran sunan company nasu hakan yasa ya mike don ba wanan ne zuwansa
na farko ba.
Mutumin dake zaune a barin hangunsane ya bishi da kallon mamaki don a iya
saninsa baisan mr Okah da wanan mutumin daya canjesa ba a baya.
Wanda a yanzu shima yazo ganawa da wanan mutumin ne ta yadda zai samu ya dan
jona ya fara business din don abubuwa da suke kokarin tsaya masa a yanzu din tun
bayan barinsa wajen mr Okah da abayansa yake yana ci yanasha yana duk wani biyan
bukatansa cikin mutunci har duniya ta sanda shi a lokacin.
Saidaga baya da ya yaudareshi ta hanyar cuta mr Okah din ya watsar dashi na har
abada da a yanzu bai aikin komai kuma sai dan buga buga don ya kare mutuncin kansa.
Lalai babu tamtama wanan yaron mr Okah ya aza a matsayinsa na baya amma wanan
yarone sosai anya kuwa tunanensa ya zo a gaskiya yasan halin mr Okah da kyau kamar
yunwar cikinsa fa ?
Mr Okah mutum ne da zai sakar maka dukiya kayi komai a kai kamar bai damu dasu
ba sai ranan daya bukaci sanin kan dukiyan zai waiwayeka akansu.
Wanan karon ma haka yaiwa Jafar din da kanwarsa tillo daya ta gabatar mai dashi
kuma ya yaba sosai da hankalin yaron da baiwansa bai taba tsamanin zai samu yaro
karami haka da zai rike wanan amanan da zuciya daya ba don yaron akwai basira da
hazaka ga zafin nema.
Haka hasken taurarinsu yazo daya kusan ma yace na yaron yana gab da taushe nasa
yadda masana suka fada mai akan yaron.
A bangaren jafar din kuma dashi da kaninsa Abubakar suke tsaye sai yan uwasa
biyu daya yaba da halaiyansu sune suke gudanar da wanan sana,an dayanzu darajan
gidansu ya soma farfafowa.
Irin jajircewan Jafar din da taka tsantsan akan dukiyan mutane yasa idonsa yana
kan komai yasan shige da ficen da yan uwan nasa sukeyi da dukiyan bai yarda ya
shagala a kan dukiyam mutane ba yana hasaso masu jin dadinsu gaba.
Har kawu dauda ya dora a wanan harkallan a yanzu a wasu jahohin dake kusa da
kaduna din shima sai tubarkallah a yanzu.
Nace ashe da zamu samu irin jafar goma a arewa ba za a barmu a baya ba indai dan
uwa zai samu ya tunane saura azo aci tare a tsira tare da mun rage raddin talauci
a nahiyar nan ta arewa.
Saidai mutane a yanzu kansu suka sani sai iyalinsu mutum bai tunane zai iya
mutuwa ako yaushe yabar baya da Kura ga magadansa.
Har jafar din ya fito wanan kafirin yana zaune yana jijiga kansa a wajen ya
fice abinsa ba zaka taba daukan wani abu maimuhinmanci yayi ba a lokacin.
Jafar mutum ne daya bude ido da neman kudi tun yana karami suna bin mahaifinsu
kasuwa suna ganin yadda ake harkan kasuwanci da har yazp kuma kawu dauda ya kara
dorashi kan wata sana,an .
Hakan baisa yayi sake da karatunshi ba don har masters yayi saboda daman da yake
dashi na magani a ganan yaron don ga tushen ilimin a cikin garinsu.
Hankalinsa yana kan tukin da yakeyi duk da a yan kwanakin hankalinsa gaba daya
ya koma gida saboda azumi dake karatowa yaso a satin nan yashiga arewa saidai hakan
ba zai samu a wajensa ba don kayan su dabasu daga daga kudun ba har lokacin.
Wanan yasa bai samu shiga gida ba sai dole an fara azumi badashi ba ke nan hakan
yasa ya jawo wayanshi ya soma kiran layin mahaifiyarsu dan yaji ya za ayi ke nan ?
Tana dauka yaji muryanta da alaman ba lafiya ko barci kuma ta tashi a lokacin
hakan yasa hankali tashe yake fadin lafiya dai mama ?
Dan murmushin dole mama din ta kakaro a fuskanta kamar yana gabanta take fadin
ba komai jafar yau dai na kwana da dan ciwon kaine kawai amma da sauki.
Kina asibitin ne tace a,a gamu gida iya da matar kawunkune can da ita yau mun
dawo gida mu dan huta muryoyin mu yaji a lokacin yace taba saratu waya take fadin
bata kusa tana can wajenka.
Salimace da Rahaam suke magana yace ta bashi salima din nan ta karbi wayan tana
gaidashi ya amsa yake tambayanta idan ciwon mama din sosai ne don yasan ba zata
fada mashi gaskiya ba ita.
Gaskiya tun jiya take kwance da muka sameta asibiti amma dai kuma yau da sauki
tunda tasha magani fada ya fara yana fadin shine baku kirani kun fada min ba salima
?
Me saratu takeyi can bayan mama na nan kwance bata masan halin da take ciki ba
yanzu zan turo Lawal yazo ya gani idan zai kaita asibitine ?
Hakan yasa ya fasa fadan zancen da yake sonyi da mama din a lokacin ba a dauki
lokaci ba mukaji sallaman lawal din yazo duba mama din da jiki .
Abokinsa ne nasanshi sosai yana yawan zuwa gidan idan yana gari wajensa haka
kuma sukanyi tafiya tare indai yana arewa.
Shiya shigo ya dubata har sukai dan hira da mama din duk da ina kitchen ina hada
girkin sara lokacin amma ina jiyo hiransu daga kitchen din.
Ya fita bai jima ba ya dawo tare da wani ma,aikacin jinya ya dubata ya bata
maganunuwan da zata sha a raina nace gata ke nan mai karami shike da babba akace.
Anty yanda muke sa rai a cikin mu yanzu ta nunawa mama damu wanan gatan sai dai
karfin mijinta bai kai ba amma duk da hakan Alhamdullahi gaskiya.
Abinda yasa nace hakan dole indai da nagarine kai kaga yadda iyalan mama suke
gudanar da rayuwansu dole abin ya baka sha,awa.
Don ko ya Habu saida ya kira yana fadin zai taso ta hanashi tace ya zauna yayi
abinda ke gabanshi ita lafiyanta kalau Jafar daine ya tayar da hankalinsa.
Shima ya Salis ya kira cikin damuwa donshi yanzu yana ghana yana karatune daga
can kuma ya kira yana gaida ita da jiki me zai hana bakaji sha,awan hakan ba yadda
diya keba uwarsu kula.
Bansan ya akayi ba saiga matan yaya din har saare sun shigo suna fadin mama ashe
bakiji dadi ba yau yanzu sweet j yakira yake fada muna.
Aina fada mai ni zaune nabar mama tana banyewa maman su Raamah kai da za aiwa
kitso fadan hakan yasa na kalleta don nasan mahaifiyar mu zataji nauyin hakan data
fada.
Sun dai dan jima kafin su fice daga part din lokacin har na hada komai da za
akai asibitin na shiga wanka don nice zanje nakai masu abincin .
ZAINAB IDRIS MAKAWA
[5/19, 21:37] Buhainat: Follow this link to join my WhatsApp group:
https://chat.whatsapp.com/K44JhTApwmM4gU33AbpqHC
MURFIN JALLO DAN UWAN TAFIYA,,,,,,,,,,,,
ZAINAB IDRIS MAKAWA
BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM,,,,,,,,1️
1️⃣8️⃣
GA MAI SON BANI HAKKINA ZAI IYA TURA KUDI NAIRA DUBU DAYA KACAL A WANAN LAMBAN
2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO A KIRA WANAN LAYIN WAYAN 08036959257
NAGODE ALLAH YA BADA IKON BIYA MUN GODE NAKU HAR KULLUN YAR MAKAWA, , , , , ,
YAR UWA KADA KI RAINA NAUYIN HAKKIN WANI A WURIN ALLAH DOMIN AMANACE HAKKI,WANI A
WAJENKA , , , , , ,
HAKKIN MALLAKAN JUYAWA AUDIOVISUAL S ZARIA TV KEDA WANAN HAKKIN KADA WANI KO WATA
YAYI GANGANCIN JUYASHI ZUWA AUDIO PLEASE,,,,,,,,,,,,,
Bayan kwana hudu ya sauka garin da tarin alheri mai yawa dan tab motar dayazo dashi
take da tsaraba.
Mu mukai ta jidan kayan zuwa cikin gida dasu part dinshi muna tarawa a tsakar
falo koda muka gama kwanciya nayi lokacin.
Saida asuba da muka tashi yin sahurne nake jin yar wajensu anty Saare na fadin
dama tasan zai dawo da alheri haka mai yawa.
Don tana zaune yake tambayan su dame dame zai sayo a lagos don a rage kayan
sallah suka lissafa mashi yace saura sai idan yazo nan zai saya.
Anan na gane kayan da mukai ta jida zuwa cikin gida shi take nufi nikan ko kusz
ban kawo da rabona a cikin kayan ba don haka ban tsoma masu baki ba nasan dai shima
yaya Habu idan ya tashi saya zai sayo dani donshi ba zaice ya manta dani ba .
Tunda sanadinsa nake zaune a gidan wanda kiri kiri matan dan uwansa suka nuna
suna kyashin zaman mu a gidan mu kuma da muka fisu iya miskilanci muka nuna bamu
san sunayi ba ma.
Ruwan shayi kadai nake sahur dashi in kwanta ko ranan inga gama sha na shige
daki na kwanta da yake azumi na kai bakwai ban fito yin shara ba saida gari ya kara
haskawa na fito nayi shara da wanke wanke na koma na kwanta.
Yanzu mama tana gida kamar yadda yayanta sukace ta dawo gida da azumi sai ummah
mu da yar uwata ke asibitin gashi ita Yanda sai an hada mata abinci don ba halin
tayi azumi din a lokacin.
Abincinta na dora wanda a yanzu sau daya akeyi da ankai abin karyawa sai kuma
na dare donshi nakeyin wanda ba zai lalace da wuri ba akai mata.
Ina gamawa na koma daki na kwanta ban fito ba sai da azahar daidai lokacin kuma
muke fara shirin abin buda baki a kullum.
Saman gado naga kaya saidai ban tsaya ba na shige ban daki dana fitone na kula
laces ne saman gadon ajiye a cikin leda ban kuma tsaya budewa ba na tayar da sallah
ina gamawa na dauko dogon rigan da anty Salima ta ban nasaka dogon rigar atamface
dinkin pitted ya dan matse min jikina kadan don zan fita kurman jiki.
Falon na fito na samu mama tana gyaran kullum masa da za ayi ranan nayi mamaki
ganin hakan gaida ita nayi ta amsa tana fadin Rahama kin tashi ashe yanzu nake
zancen zuci a kanki ai.
Natashi mama na kara fada masa zamuyiwa yayan ku yau tun da safe nake aikinsa na
barkine ki huta tunda kin samu barci yanzu don Allah fitar min da kayan miyan can
daga waje mu dora murhu zaifi sauki ba zan iya yin wanan aikin a saman gas ba .
Na juya na dauki kayan miyan mai yawa a wani baho nauyin sa ya ban mamaki ina
fita nake jin mama na kwalawa yan matan ta kira da su fito su sameta waje.
Icen na hada da komao yadda ya dace a wajen gidan wajen wani dan innuwa kujera
na dora mata sai na nufi wajen famfon waje da kayan miyan .
Alokacin naga ashe naman kaine na saniya guda aka sare yasa roban nauyi sai kayan
miya da aka zuba sama ya rufe wanan din.
Mama ta fito tana fadin kinsan Jafar da hauka yace masa yake so ayi mai yau yasha
ruwa da abokansa na lissafa mai tare da sako tun safe a hada mun wan kullum yanzu
buhari ya kawo minshi daga can gidan da aka niko min.
Nagane me take nufi yasa naci gaba da mamaki miyan muka fara hadawa tunda miyan
naman kaine bamu tsaya sai markaden ya soyo ba irin miyan shinkafa.
Wanda a lokacin mukai mashi hadin gaba daya bayan mun soya mai daban muka lema a
saman markaden dake tafasa a wuta kayan kamshi da komai aka zuba muka shiga gyara
wuta idan ya jaye.
Saida mukai sallah la,asar ta fara suya da kanta a zatonta ban iya ba tunda ni
bafulatanan dajice ai don a daji suka dauko mu.
Sukan manta da kaddaran mutuwa ya mayar damu dajin da suka ganmu a ciki din amma
komai na rayuwan bahaushe shine akidar mu.
Saboda iya na koma ciki don tace ita sai an dafa mata shimkafa da miyan da
zataci da ganyen salad kai azumi bakaci ganye ba aiba yi bane.
Har nagama miya na dora shimkafa na fito anty Saare na samu saman tanda tana
tuyar waina nace ta kawo in gwada wutan na gyara na bajeshi da kyau kafin na fara
zuba man suyar cikin yan mintuna na tara waina karshe dai nice na karasa suyan mama
tana ta masu kwakwazon hakan .
Tace komai yar nan ta iya duk abinda kasa kanka a duniya zaka iya amma shiririta
ya hana ku tsaya ku koyi girki da zakuyiwa mazajen ku nan gaba.
Su wa yancan mashiririta kuna dai gani mijinsu yana son abincin gargajiya amma
basu iya ba sai shirme daga taliya sai indomi wanan girkin macen arzikine ?
Sai gashi kuma ya shigo da kayan shan ruwa niki niki aka jibgesu a nan inda
muken yana fadin ke Saratu don shi da sunanta na yanka yake kiranta dashi.
Ki gyara muna kiyi fruit salad a jefa kankara ta kalleshi tana bata fuska alaman
itafa ta gaji lokacin mama din tace wai kai don me ba zaka kaiwa matanka wanan
wahalan daka jajibowa mutane ba ?
Ya dan marairaice yace mama ai sai naji kunya wa yan nan me suka iya don Allah
banda shirme aida su fito su kama a samu a hada da wuri kada a makara.
No please mama son Allah barsu a can suna zuwa wajen nan aikin zai tsaya ko su
tafkawa mutane shirme yanzu dai a kara da ferfesun kifi irin na ranan da kika bani
da safe.
Ga wace ta hada can ai tana nuna mashi ni ta kara da fadin indai kaci abincin
arziki a gidan nan itace ta hadashi ko yar uwarta .
Mama wanda nace dake kamar hadin restaurants din nan fa itace na fada maka ko
masa yanzu data karba tayi bakaga yadda ya fita gwanin ban sha,awa ba shine ma nasa
su zuba maka.
Ya juyo ya dan kalloni yana fadin don Allah ki taimaka kiyi min irinsa ga kifi
nan a leda an wanke anyi komai sai ayi yadda ya dace ya miko kudi yana fadin gashi
idan za a sai wani abune akara a ciki ?
Da sauri anty Saare ta karbe kudin daga hannunsa uwar tace nan kikaci rani har
damina ya sameki wajen son kudi tandan masan na sauke na shiga ciki dauko kayan
hadin .
Dan attah kadan da albasa sai kayan yajin mu na hausa da citta yafi yawa da
tafarnuwa da species kadan na dauka daka na fito sharp sharp don lokacin daya
karato na shan ruwa har na gama hadawa ina jiran ya tafasa.
Naga suna shirme na karba uwar tagumi tayi ta zuba min ido tana kallon ikon
Allah tsab na hada fruit salad din da yaji madara da kankanran da zai sakashi
sanyi sai flavour don yayi kamshi.
Tabarama manya guda biyu anty salima ta shimfida masu saman barandan part
dinshi data share sai aka shiga jera kayan abincin harda shimkafan da miyan da
mukayi da kunun tsamiya duk aka fita masu dashi wajen shan ruwan da