Showing 258001 words to 261000 words out of 328222 words

Chapter 87 - Murfin Jallo Dan Uwa By ZAINAB IDRIS MAKAWA

ba nazone akan wani zance shiya kawoni to
yazid ai da dai mun dan shiga daga ciki akan ita matar Jafarne daine ko ?
Yaran nan basu jin shawara ai shi jafar tunda yazo min da zancen auren yarinyar
nan banso ba naso hanashi amma ya nuna min yayi niyar hakan na barshi yayi abinsa
ko uwarku bai kaunan ta sani.
Dakata kawu ba wanan zance ya kawoni ba ninazo zancen kudinane da mama tace min
suna hannun ka ina bukatan kudin a yanzu don ina son na kara jari ga sana,an dana
soma.
Kudi kuma yazid ita uwar taku tasan da zakazo tambayan kudin ka don ba kudinka
bane ta ban balle yanzu kazo tambayana haka kai tsaye ?
Ok hakane to zata zo din da kanta har in kudina yana hannunka ka tabbatar da ka
bata kafin mu sake haduwa irin haka don ina bukatan kudina a yanzu don Allah.
Yana fadan hakan ya juya a fusace ya bar kawu din da mamankishi tsaye yana bin
bayanshi da kallon can Allah ya bashi ikon budan baki yake fadin.
Waiko yazid kan ka daya kuwa koka fara shan wani abune haka jin hakan yasa Yazid
din juyowa a cikin mamaki yake fadin.
Yana nuna kanshi yana fadin ni kawu a hayaci nake don ko goro bana ci balle
wani maye nayima kama da wanda ke shan wani abu makamancin hakan yanzu ko ?
Sai yayi murmushi kafin kawun ya bashi amsa ya juya ya tafi har lokacin kawu din
yana tsaye a inda ya barshi har ya tafi.
Nisawa yayi ya juya yana wasi wasin a zuciyarshi don yasan bai jima da wanan
maganan da dubu ba akan zancen kudin yayi mata maganan da yake ganin hankalinta zai
kwanta yadda ya saba .
Yanzu kuma kwatsam saiga Yazid yazo da wanan zancen kudin yadda yaga yaron yazo
mashi tsatsaye a yau shine abinda ya daga mashi hankali.
Yasan inda zai kamo shirinsa ai da uwarsa zaiyi amfani itace logon diyan da ita
kawai zai hadashi ya daina wanan zancen.
Shiko yazid yana tafe yana faman shirya yadda zai fitowa kawu din tunda ya hango
rashin gaskiya tsantsa a idon kawu din zaiko gwada mashi bai isa ba wanan karon.
Tafiyan maman tudu yasa hankalin yaya Jafar komawa gareni ko yaushe zai zauna
zugun yana tunane ta inda zai bullowa zancen tafiyan nawa gida.
Don ya kulla da mama sam bata son wanan maganan haka shima habu yayi shiru da
alama yayi fushi akan rashin dawowana gidan tare dasu lokacin.
A lokacin mama ta shigo dakin ta sameshi hakana a cikin halin tunane ta soma
fadin Jafaru na horeka da zama haka kana faman tunane ?
Kasan jikinka ba lafiya gareka bafa ka daina tunanen yaran nan dukkansu yan
banzane don jinyar kane duk suka gujeka da kuma fitinan su ya koresu idan wani abu
ya sake samunka a yanzu ba hasaransu bane.
Haba mama ki daina zagin yaya mutane haka ita Nusaiba ai kowa yasan abinda ya
hadani da ita gidan nan harta fita haka kuma ita Rahama saboda matsinki da saratu
akantane ai yasa ta tafi.
Amma ba don jinyana ba ko za a fadi hakan kuma banda Rahama yarinyar da tayi
tsaye a kaina har Allah yaban lafiya.
Yanzu kuma ace don kada tayi jinyana ko ta gaji da jinyata yasa tabar gidan
nan kawai dai irin maganan da kuke fadi a kantane yasata fushin zuciya ta tafi amma
ba,,,,
Wai Jafar kanka daya kuwa yau kake fadin wanan maganan haka kamar wanda wani abu
ya sama shima jafar din katseta yayi da fadin a,a mama maganan Allah udan yazo a
yishi don kina gani a gabanki saratu da Nusaiba suka matsawa yarinyar nan amma ba a
tsawata masu ba .
Lalai anyi gaskiya da akace macen bafulatana hatsarice ga mutum don basu shiga
gida ba su hada kan kowa a gidan ba idan basu sami hakan ba kuma sai suyi yadda
zasuyi suga sun halaka duk wani wanda ke gidan ,,,,,,
Wayanta dai daya dauki kara shiyanata karasa zancen datakeyi din ta tsaya daukan
wayan a cikin mamakin dan nata datakewa kallon tababe a ranan kan bafulatanan
matarshi din data tafi yasashi gigicewa hakan.
Ganin layi kawu daya matsa kiranta yasa ta dakatar da zancen ta dauki wayan da
sallama tana karawa a kunnenta ya amsa.
Gaisuwa ta fara mai ya amsa a gagauce ya soma fadin Dubu kina da masaniyar
zuwan yaron nan gidana kuwa ?
Ta mayar mai da tambaya itama da wani yaro ke nan kuma ya amsa da yaron nan
Yazid mana wai yazo tambayana kudinsa da akace suna hammunsa.
Kudinshi kuma shi yazid din yazo tambayanka kudi yaya ya amsa da kwarai yazo
shekaran jiya nace bari dai in kiraki in tambayeki ko kina da masaniya ga hakan ?
Wallahi summa tallahi yaya banda masaniya ga zuwanshi wajeka shi yazid din yaje
gidan ka yaya yana tambayan kudi kuma bayan na fada mai kada yayi wanan maganan a
wajenka .
Kwarai kuwa yazo min nan a fitsare wai yazo karban kudinshi a wajena nace yaje
sai munyi magana dake Dubu dama abinda nakewa gudu kenan gashi ko ya faru tun yanzu
?
Har yaushe aka bada kudin nan don Allah dubu da za a dinga matsawa da a bayar
dasu bayan an juya kudin zuwa kaddara yanzu.
Yaya kayi hakkuri dan Allah zan mashi magana sai faman fada yakeyi Jafar yana
zaune gefe yana kallon ikon Allah a tsakaninsu.
Saida ta gama wayan ta dago tana fadin kaji min kuma wai yazid ya samu kawunku
yana mashi zancen kudinshi .
Ok kawune kuke waya dashi yanzu ta juyo a cikin damuwa tana fadin yanzu haka
kawai yaron nan muna zaune lafiya da dan uwana yana son hada tsakanin mu.
A,a mama ku natsu ku bincika kuji meye dalilishi nayin hakan dole yana da
dalilin dayasa yayi hakan ai ba zai tashi haka yaje wajen kawu kai tsaye zancen
kudi ba.
Jin abinda Jafar ya fada yasa uwar kallonsa tana fadin barshi ya dawo ai zai
sameni bai yarda dani ba ke nan danace kudin suna hannun yaya yaje da kanshi ya
bincikeshi ?
Fada sosai mama din keyi ga yazid din ya fita tun safe bai shigo ba har mama
dubu ta fito zuwa part din don diba jikin jikannata nan ta samu mama din tana fada
saidai tana ganin iya taja bakinta tayi shiru.
Don da jafar da yazid suna dasawa sosai da tsohuwar habune kadai suke yawan fada
dashi lokaci lokaci wanan yasa ko yanzuma da yazid ya dawo da iyalinsa suke kadaici
itace mai zama dasu tana debe masu kewa.
Sai bayan la,asar ya dawo gidan part dinsa ya nufa inda ya dan zauna da
iyalinsa yaci abinci kafin ya fito don tun safe bai leka dan uwansa ba.
Ya shigo da yaronshi a hannusa cikin fara,a yana fadin yaya ka ganni sai yanzu
na tafi duban masu aikine can nake tun safe don kada su sake maimaita shirmen da
sukayi a baya.
Ya dan rankwafa yana fadin ya karfin jikin naka brother badai matsalan komai ko
yake tambayan dan uwan ?
Ya juyo wajen mahaifiyar tasu a sake yana fadin mama barka da gida yaya gidan
kuma da iyali ?
Suna lafiya Yazid yaushe kaje gidan kawun ku tambayansa kudi don dazun ya bugo
min waya yana tambayana ko ina da masaniyar zuwanka wajenshi ?
Ya samu bugo maki kenan naje ina son kudina dake hannunsa akwai abinda zanyi
dasu a yanzu don ba zan tsaya ace sai kawu ya juya min kudina ba mama ?
Yazid ni kake fadawa hakan kai tsaye ko kana son nuna min cewa mu bamu isa
rikema abinka ba ke nan ko ?
A take ya daure fuska yana fadin da karfina mama zan tsaya kawu yana juya min
dukiya aban abinna yadda akabawa kowa nasa in rika don ina da abinda zanyi dasu
yanzu .
Yazid kafita min a ido akan kudi kada ka tsaya kana min rashin kunya a gabana
yanzu da sauri yazid din ya katseta yana fadin .
Mama kudina fa nake zance ba wani abu ba ya ban ina da bukatansu tunda hakkinane
anbawa kowa nasa nima ina bukatan nawa a yanzu.
Kudi a yanzu kaddara aka mayar dasu don haka banson jin zancen kudin nan a yanzu
ka bari sai ranan da ya sayar da kaddarorin daya saya ya baku kudin ku.
Ba zai yuyu ba mama kudin nan fa kudinane bance aban na wani nayi amfani dashi
ba don haka a ban abinna don Allah ki fada mashi.
Yana fadan hakan ya juya a fusace ya bar dakin da danshi a hannunsa yana shiga
part dinsa ya zauna yana fada yana fadawa iya abinda ke faruwa .
Karshema ya dauki waya ya dannawa kawu waya yana fadin kawu zancen kudina nake
maka ina bukatansu nan da kwana biyu in Allah ya kaimu yana fadan hakan ya kashe
wayar tashi rai bace.
Shima a bangaren kawu bin wayar shi yayi da kallo yana mamaki yadda dan nasa ya
kirashi babu ko sallama yana mashi zancen kudinshi.
Yasan akwai matsala ke nan akan hakan don dole yakai kanshi gidan su zauna a
gaban mahsifiyarsu ta takawa yaron burki don yasan ita kadaice zata iya takawa
yaran a yanzu.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
[5/17, 08:44] Buhainat: MURFIN JALLO DAN UWAN TAFIYA,,,,,,,,,,,,

ZAINAB IDRIS MAKAWA

BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM,,,,,,,,,

8️⃣1️⃣

GA MAI SON BANI HAKKINA ZAI IYA TURA KUDI NAIRA DUBU DAYA KACAL A WANAN LAMBAN
2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZENETH BANK KO A KIRA WANAN LAYIN WAYAN 08036959257
NAGODE ALLAH YA BADA IKON BIYA MUN GODE NAKU HAR KULLUN YAR MAKAWA, , , , , ,

YAR UWA KADA KI RAINA NAUYIN HAKKIN WANI A WURIN ALLAH DOMIN AMANACE HAKKI,WANI A
WAJENKA , , , , , ,


HAKKIN MALLAKAN JUYAWA AUDIOVISUAL S ZARIA TV KEDA WANAN HAKKIN KADA WANI KO WATA
YAYI GANGANCIN JUYASHI ZUWA AUDIO PLEASE,,,,,,,,,,,,,


Nayi sati hudu a gidan mijin ummah banda dan damuwa da sabo da zama a dakin aure
banda wani matsala a gidan kamar yadda na fada a baya.
Ganin hakan yasa na kirkiro tafiya Abuja na samu ummah da zancen take fadin anya
daddy ku zai yarda da hakan kuwa ?
Ace kina nan mun barki zuwa kuma abuja amma zan fada mai naji ko zai yarda da
hakan idan ya shigo yanzu ya tafi rigasa wajen abokinshi.
Ina kwance dakinta da yamma sai gashi har dakin ya shigo ya sameni tare da
ummah yana saye da coffe colour din jallabiya mai dogon hannu a jikinshi.
Saida yakai zaune saman kujera ya soma fadin diyata maman ke fada min kina son
ki karasa Abuja ?
Nace ko anyi maki wani abune a nan din da sauri na dago kai na dubi ummah kafin
na girgiza kai ina fadin ba komai daddy .
Kawai dai ina son inje can din ne kawai nagansu sai ya gyara mike kafanshi yana
fadin ayi haka kuma Rahama ?
Bayan mijinki da yan uwansa sunsan ki wajen mu yanzu kuma suji cewa kin koma
Abuja yaya kike son su dauki zancen a zuciyarsu ?
Sai na sake kasa da kaina na dukar yacigaba da fadin kinga hakan ba zai masu
dadi ba don hakan na nufin cewa mu nan mun gaza dake hakan ke nufin da sauri na
kara dago kai na dubeshi yayi murmushi yana fadin yes idan mun barki zuwa abuja
hakane zancen.
Ba zani ba daddy na fasa yace good girl Allah yayi maki albarka kinji kiyi
hakkuri har ki koma dakinki saiki tafi da bakin mijinki daga can na amsa mashi da
toh kawai.
Ya dan min nasiha nayi hakkuri don Allah na saki jiki kuma tunda nasan a yanzu
bani kadai banr a jikina yasan kuma bada jimawa ba mijina zaizo mu koma.
Ya dan jima nayi mai godiya ya mike ya fita daga dakin ummah tabi bayanshi suka
fice a hankali na sauke ajiyan zuciya na koma na kwanta ina tunane.
Sammako kawu ya bugo masu a gidan duk dai akan ya samu yazid din a gida a gaban
mama don kada ya fita suyi sabani donshi yafi bukatan ayi komai a gaban mama din
don ya hango rashin mutunci a idon yaron .
Kamar kullum saida mama tasa yan matanta sukai mashi abin karyawa yanayi yana
tambayan kada Yazid ya fita fa dubu gara a aika a fada mai ana nemashi.
Kada yazo ya fice daga gidan ba tare da sun sani ba kuma yazo daga baya ya bishi
gida yayi mai cin mutumci har wasu suci.
Da mama dubu taga ya matsa yasa ta tayar da salima akan taje part dinsa ta kira
matashi suna nemanshi ita da kawunsu.
Salima taje ta samu har lokacjn basu bude part dinsu ba don yana ciki hakan yasa
ta dawo ta fadawa mahaifiyar nasu cewa basu tashi daga barcin ba.
Karfe nawa yanzu kije ki kwankwasa masu kofa ya bude muna son ganinsa a nan hakan
yasa ta koma ta kwankwasa kofan .
Suna zaune suna karyawa a falon nasu sukaji nocking matarshi ta mike ta bude
kofan kamar kullum fuskanta yana a daure kamar yadda suke kiranta da mai dauraren
fuska haka suka gaisa a tsatsaye da ita .
Gashi kuma tana tsaye ta tare kofa alaman bata son ta shigo daga ciki fuska a
daure donshi suke kiranta mai dauraren fuska bata da saki ko kadan.
Dan uwanta ta tambaya take fadin yana ciki hakan yasa tayi kokarin kutsawa taja
gefe ta bata hanya tashiga gaisawa sukayi take fada mai mahaufiyarsu da kawu ke
nemanshi .
Yake fadin yazo ke nan kice ina zuwa daga haka ta juya ta fice duk da kayan dadin
dake zube a gabanshi yana ci da ace marainintane datace wanan fa yaya ?
Shikuma jafar zaice zoki zauna kice kodama batayi magana ba idan ta shigo hakan
zaice da ita bissimillah salima zauna mu karya.
Haka ta juya tana kunduma masu zagi tana fadin yaya J duk yafisu mutunci yan
iska masu tsoron matayensu kawai ?
Ta koma ta shedawa mama cewa yana tafe tashige dakin kwanansu ta bar falon a
lokacin iya na can tare da Jafar a part din da suke jinyarsa don maman tudu tayi
tafiyanta gida tabarta dashi.
Saida Yazid ya gama karyawa ya shigo part din dauke da dansa a hannunsa ya gaisa
dasu ya samu waje ya zauna yana fadin fuskatan mahaifiyarsu yace.
Salima tace kina nemana mama kafin ya kaiga rufe baki uwar tace ehh ga kawun ku
nan yazo akan zancen kudin daka sameshi gidansa.
Ok kudin ya kawo ke nan yazid din ya fada yana gyarawa dansa dake gefenshi zama
ya kyalla ido a gefensu ko zaiga kudin sai dai baiga komai ba yasa ya fuskanci uwar
dake magana.
Kaida kaje gunsa da zancen kudi kaika bashi kudin da zaka sameshi kai tsaye don
rashin kunya ?
Amma ai mama kudinane ko hakkina don naje na sameshi ai ba zai zama laifi ba ko
gyara zama kawu yayi yana kallon yazid din cikin mamaki.
Eeh lallai yazid ni kake fadawa kudinkane ko yanzu da sauri yace haba mama
kudinane fa hakkinane na tambaya ba wani abu ba idan yazo da kudinne sai aban su
mana shike nan don Allah ?
To baizo dasu ba mara kunya ko kuma radhin kunya zaka kawo muna yanzu tunda
hakkinkane ta yaya an mayar da abu kaddara zakazo da rana tsaka kace kana bukatansu
a yanzu.
Mama ko kaddaranne a nuna min insan yarda na juyasu zuwa kudi don ina da bukatan
kudi a yanzu ni banja ba bance aban na kowa ba nawa nake maganan abina a yanzu.
Kai Yazid kagane ko kudin tun lokacin data bansu nayi dabaran sakasu a kaddara
na sai filaye da gidajen kango sai a sayar a kara sayen wasu a jingine haka nayi da
kudin.
Ok to a kaini filin sai na saka nawa a kasuwa don kudi nake da bukata akwai
kayan danayo oda zasu shigo min zuwa wasu sati insha Allah.
Kai habu na fadama ka shiga hankalinka ba zancen kudin nan a yanzu sai ranan da
kawu ya sayar ya kawo maka kudinka idan lokacin hakan yayi.
Mama kudin nan kudinane hakkina da Allah ya wajabta a gareni ba don haka ina
bukatan abina a yanzu ko hannun wa suke kuwa ?
Kawu ina son kudina nan da sati daya kacal kudi ko kaddara a ban abina don ina
da bukata akansu yanzu.
Yazid ni kake mussu dani mama ta fada ya mike tsaye yana fadin Allah ya kara
lafiya da nisan kwana mama ni na isa inyi mussu dake kudina nake bukata kuma shina
fada nan da sati nake da bukatansu.
In kuma har aka wuce sati gaskiya za,a samu matsala a tsakani gaskiya don kudina
ba zasu wuce wanan rana ba in sha Allah.
Yasa kai ya fice daga part din kallon juna sukayi tsakaninsu kawu ke fadin
kingani ba Dubu aina fada maki kamar yasha wani abu daya zo min gashi kuma ya
maimaita agabanki kuma.
Ai kuwa bai isa ba yaya don na kula bayin kanshi bane don na fahinci an zugo
yaron nan ne mai zaiyi da kudi a yanzu hannunshi ?
Tunda kaf komai na dan uwansu yanzu hannunsu yake suke juya mai komai tunda ya
kwanta din nan dole akwai wanda ke zugashi yayi wanan abin haka .
Mama fa saare data dade tsaye kofan daki ta saurarensu tun shigowan Yazid takara
fada hakan yasa uwar ta juyo a hasale tana fadin meye ke kuma ko kema zancen
kudinne zaki tayar min da hankali kuma ?
Mama in tayar maki da hankali kuma kawai dai nima zance idan za a sayar da
kaddarorin a hada nawa don


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login