Showing 72001 words to 75000 words out of 328222 words
Chapter 25 - Murfin Jallo Dan Uwa By ZAINAB IDRIS MAKAWA
haihuwa ba kar kiyi
jahilci mana damuwan ku zai iya hanata samun lada .
Da zaran kun nuna baku yarda ba zaku sare mata gwiwa da hakan taji auren ya fita
ranta take fadin wanan matar da suke asibiti tare itace ta yaba da hankalin uwarku
ta nemawa dan uwanta aurenta.
Wai matarshi ta rasu shekara ukku ke nan yanzu ya kasa samun matar da zai aura ko
wace aka kawo mai yace batayi ba amma yana ganin umnan ku ya yarda.
Kinga ai hakan alherine ko har yazo suna asibiti ya ganeta a nan kaduna yake da
zama dan jahanan ne shi kinga ai ta dawo kusa daku ke nan idan Allah yayi abin.
Jinta kawai nakeyi ina tuna mahaifin mu daya rasu ta yaya ummah zatayi auren
wani kuma yanzu ?
ZAINAB IDRIS MAKAWA
[5/19, 21:37] Buhainat: MURFIN JALLO DAN UWAN TAFIYA,,,,,,,,,,,,
ZAINAB IDRIS MAKAWA
BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM,,,,,,,,
2️⃣5️⃣
GA MAI SON BANI HAKKINA ZAI IYA TURA KUDI NAIRA DUBU DAYA KACAL A WANAN LAMBAN
2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO A KIRA WANAN LAYIN WAYAN 08036959257
NAGODE ALLAH YA BADA IKON BIYA MUN GODE NAKU HAR KULLUN YAR MAKAWA, , , , , ,
YAR UWA KADA KI RAINA NAUYIN HAKKIN WANI A WURIN ALLAH DOMIN AMANACE HAKKI,WANI A
WAJENKA , , , , , ,
HAKKIN MALLAKAN JUYAWA AUDIOVISUAL S ZARIA TV KEDA WANAN HAKKIN KADA WANI KO WATA
YAYI GANGANCIN JUYASHI ZUWA AUDIO PLEASE,,,,,,,,,,,,,
Anyi tsegumi sosai ga irin hidiman da Ya J yayiwa matar dan uwansa tsegumin kuma
tsakanin can babban gida da wajen matan yaya sin yafi karfi.
Ita mama kan dadin hakan taji a zuciyar ta harma da fili wanan kuma shawaran Kawu
daudane hakan don kara samuwar hadin kan zuri,an tasu.
Basu kara tsegumin ba saiga labarin zuwana school ya fito inda a take suka soma
tsegumin hakan kuma ya za ayi in samu karatu a gurbin jami,a.
Wanan kuma yaya Habune yayi min kokarinsa ya kuma tsaya saida yaga na soma
karatun don let addimition dana samu karatu yayi nisa a lokacin ga kuma takardana
sunyi kyau sosai ya baza kudi ya samo min a boye saiji akayi na soma karatu ai a
nan jami,a.
Anyi tashin hankali sosai a boye duk mu bamu sani ba inda yakai wani zuwa da
akayi har akayi zama a falon Iya da kawu dasu yaya da matansu har Saratu dake
gidan.
Bayan an bude taro da addu,a mama data kirasu ta soma magana kamar haka na
taraku nan don gano dalilin dayasa kai Jafaru ka nemawa yarinyar nan makarata haka
irin wanan Jami,an ta garin nan ?
Alhalin ga yan uwanka sunso karatu a nan haka kuma matan ka suma suna so gasu da
yan uwa duk baka nema masu ba sai yarinyar nan Rahama ?
Budan bakinshi yace ita Rahama ta fara karatune mama aini ban ma sani ba don ba
a fada min ba dama ina da niyar ta soma ai tunda tana tare damu kuma kowa yana
karatun nan kada tace mun mata banbamci ?
Uwar tace yaya zaka tambayeni bayan kaika samo mata abu kowa a nan ya sani yanzu
zaka nuna baka sani ba kuma ?
Saiba ta gyara zama irin wanda ke nuna a to din nan kasan komai barkado kakewa
mutane kawai.
Yace wallahi Allah mama bansan ta soma karatu ba don bani na samo mata ba amma
kuma ina da niyar hakan a ina ta soma karatun ?
Kallon juna sukayi shima kallon Habu yayi yana son sanin wani abu akai da kyat
Habu din ya hade wasu yawu don ransa ya gama baci a lokacin.
Yace a A,B U ne yaya J Awar nasa ya samo mata don takardunta sunyi kyau sosai
zata iya zuwa karatu ko ina a fadin kasan nan dama ina son hakan Anwar ya jima yana
cewa nakawo mashi takardun wanda yai kyau a bashi gurbi a wajensu shine na kai masa
nata takardun.
Hakan yayi kyau sosai Allah ya bada sa,a yasa taci amfanin abinta ita da sauran
al,umman Annabi sallalahu alaihim wasallam.
To ke nan Jafaru bakai bane don ka nuna baka da masaniya akan hakan ya sake
kallon uwar yana fadin wallahi mama ban sani ba amma ina da niyar hakan a gareta.
To ku kunji shiyasa Allah da manzonsa suka horemu da munana zato a tsakanin mu
wai tsaya mama don Allah ba katseki bayi ba a nan shike nan yanzu ba a da halin a
taimakawa iyalina kome haka yake nufi ?
Kai Habu dakata ai anbar magana baya kawu ya fada yana gyara zama yace toni Habu
bai yi hakan ba saida ya sameni ya fada min kyakyawan niyarsa na son taimakawa
yaran nan na kuma bashi goyon baya akan ya nemi shawaran mahaifiyarta da yar uwarta
ko zasu yarda da hakan.
Ka fada min yaya saidai a yadda suka hau din nan ba yarda zasuyi da hakan ba don
zasu dauka na rufe masune amma ni Habu yazo nan da takardun ya nuna min haka kuma
da zata tafi tunda dare ya sanar dani hakan.
Mama kawu don Allah ku gafarce ya J ina son barin gidan nan don Allah ka tafi
ina mama din ta katseshi da tambaya yace ko haya zan kama kafin na karasa gina nawa
mama .
Tir tir wallahi akan wa yan nan habu basu isa su raba mu da uwarmu ba muddin
mama tana raye a doron kasan nan saidai su subar muna gidan tunda zama dasu ba dole
bane.
Ko akwai wace aka haifeni da ita a cikin ku kona fada maku cewa ni din ba dan
dangi bane ke Asmau kin sani tun bude idon ki kinsan koni waye har iyayyen kunsan
yadda gidan mu yake kika yarda kika aureni a hakan kona boye maki wani a cikin
rayuwana wanda baki sani ba ?
Kasa tayi da kanta tana fadin toni me kaji nace a nan munafukan banza da wofi
kawai mama zatayi maki karyane ?
Kyale ta dukkansu nan suka sameni da kukan su harda wanan sauniyar shakatafin
wai kana son ka fifita yarinyar nan basu san meyasa haka ba ?
Saboda ba kudin gidan ku nake amfani dashi ba yasa ban fada maku damuwata wanan
maganan idan bakuyi hankali ba wallahi karshen zamana daku yazo ke nan a gidan nan.
Kai haba meya kawo wanan maganan a yanzu ana sulhu kuma bari mama halin matan nan
ya dameni ko alheri nayiwa dan uwana suka sani sai wanan shedaniyar tayi min
korafin hakan me yasa zanyi ya nuna Saiba.
Ni ai ba kace ni kadai ke hakan ba idan kuma kaji nayi maganan abu itace tagani
ta fada min sai nayi magana tunda muna tare da kai.
Nasan Asmau munafukace ta karshe macijiyar soshiyace yar sari ki noke kawai
nasan halin kowa a cikinsu ke gaki mara kunya kece ke iya gaba da gaba dani don
baki da kunya.
To ai bamu muka soma magana ba Saarece ta samemu da zancen ita da Amina suke
fada mana kaine kakai ta wanan school din.
Suyi rikici a wajen sosai don Habu ya kafe da abarshi ya bar gidan don su din
makiyansane sai da kyat aka samu ya lafa don Jafar bai ragawa matan nasa ba harda
zancen sunan Abbati saida sukayi yace da yana da halinda yafi haka abinda zaiyi
saiya fi wanan don baida wanda yafi mai dan uwansa a duniya.
Jin hakan yasa dole habu din ya sasauta zuciyar shi har anci an sude yar uwata
bata san abinda ke faruwa ba tana part dinta sai nice dana fara jin zancen wajen
iya nake tambayan anty Nafisa ta fada min komai .
Nayi mamaki tare da tunane abinda mukai masu don wanan kiyayyan yayi yawa haka a
tsakanin mu dasu Allah ya taimaka ban faye fadawa yar uwata abinda ke faruwa a
gidan ba.
Nakan barwa kaina in shaye duk wani abinda za a fada game damu don ta zauna
lafiya da mijinta wanda kowa hakan zai mata fata a zamansu din.
Jin abinda ya faru din yasa na kara kama kaina sosai da yan gidan namu har anty
Nafisa da muke dan shiri da ita a yanzu ba komai take sani game da mu ba.
Karatuna nasawa gaba sai kuma lalurar yar uwata indai mun hadu zamu gaisa dasu
idan bamu haduba kuma a zauna lafiya.
Wanan halin ya karune a ranan wata jumma,a dana saka wasu kayan da anty salma
tabani sawa daya tayiwa kayan ta kwabe ta mika min wai dinkin bai mata ba.
Sai gashini kayan sun matukar karbuwana suna saka don girmama jumma,ata na ranan
da wuri na dawo don haka na samesu a wajen gida inda suka tsiri zama yanzu suna
shan iska.
Gaba dayansu daga can inda suke zaune suka zubo min ido tun bude get dina
shigowa gidan ban nuna nasan suna zaune ba na bude part din yar uwata na shiga da
sallamata kukan Abbati nakeji nake tambaya meya faru kuma yake kuka Yanda ?
Bansan meya sameshi ba tun dazun yake wanan kukan daukan yaron nayi na kwabe
masa kayan jikinsa don yasha iska ko zaiyi shiru saidai a banza daukansa nayi na
daurayeshi har na shafa mashi mai na sauya mai kaya na kaishi wajen uwar don ya dan
rage kukan da yakeyi.
Yaron ya kama nono sai kuma ya sake yana challara ihu yana kwandare kafa da
shure shure hakan yasa na daukeshi zuwa part din iya ina jijigashi.
Yaron a yanzu yayi wayau sosai dan kimanin wata bakwai ke nan da haihuwa anan
na sake wucesu ban tsaya duban wajen ba nashiga iya tana zaine ita kadai a falo
nasameta dashi nake gaisheta.
Bata samu amsa min ba take tambayana kome ya samu yaron saidana zauna nake fada
mata haka kawai yake kuka tundazun.
Karban yaron tayi tana fadin na dauko mata jar kanwa ta hausa shina dauko mata
tajika taba yaron yasha.
Ta miko min shi nacigaba da jijigashi a hakan ya shigo ya samemu yaron yana dan
sauke ajiyan zuciya gaidashi na soma naji iya na fadin.
Ka dawo kenan Jafaru ko baka samu zuwa bane naje iya dawowan mu ke nan yanzu
duban mu yayi yana fadin wanan kuma meya sameshi haka ?
Iya tace ina ganin cikinsa ke ciwo kasan yaran yanzu ba kula suka iya ba sun
dauka kukan banzane haka kawai mutum zai dinga kuka da gangan ya fada ?
A daidai lokacin Saiba ta shigo part din itama yana fadin in miko mashi dan na
banye na mika mashi ya karbeshi yana fadin yanzu me aka bashi ?
Kanwa na jika na bashi yasha iya ta fada da sauri yace iya kanwa kuma ina
maganinsa yake da aka bashi kanwa bari a kaishi asibiti dai a dubashi.
Ai yasha kanwa ya fada mashi Saiba ta fada ke dauko mayafin ki mu kaishi asibiti
kome ya tuna kuma yace kira min Saare mukashi asibiti .
Batayi niyar fita ba yasa ya dubeta yana fadin badake nake ba ta juya cikin bacin
rai ta fita sai naji iya tace kayi dabara don gara zuwa da Saratu din.
Nasan halinsu da sheri ko yanzu abinda ya kawota ke nan ai ta dauka nasan wanan
tana part din nan bar yan iska zanyi maganinsu ne.
Kyalesu Allah ya dora masu kishine haka barsu sunyi ta haukansu akan hakan su
girman su ke zubewa gareta ina fama da yaron ba jinsu nakeyi ba don na koma wajen
kitchen dinsu ina jijigashi.
Saida suka tafine naji iya tana fada na dan fahinci abinda ke nan ni kaina
gaskiya da nasan yana gari ba zan ko shigo part din iya ba a lokacin don nasan
wajen zuwansane bansa dayana garin ba sai ganinsa da nayi a lokacin.
Sai bayan kwana biyune Nafisa ke mun hira da nasha zagi a wajensu ranan ganina
da wanan lace din da sukayi har photona aka dauka ban sani ba ana tambayan kudin
lace din aka fada masu yakai dubu dari.
Tace hankalinsu ya tashi sosai da jin kudin ga kuma wayan hannuna shima sunyi
zance akansa wai dole zasusa a canza masu waya ba zasu yarda in rike wayan da basu
rike basu.
Har cewa sukayi kila sata nayowa inda naje abuja din yanzu an hada plain din cewa
za a turo saratu ta kwashi number anty salma a wayata su binciketa sai sunyi min
sanadin da suka gujeni a can din.
A wanan lokacin anty maria tasan irin kwaran din da nake fama dashi a gidan a
wajen hiran mu da Nafisa din dole na kwashe komai na fada mata abubuwan da suka
faru dani tana asibiti.
Ance Dan Uwa Murfin Jallo guda bayayi saida dayan don duk wanda baida dan uwa a
duniyan nan yayi babban hasara a duniya.
Ran yar uwata ya baci sosai har tana ikirarin dole ya habu ya canza mata gida
kada suzo su illanta muna rayuwan mu.
Ita kyauta daga gurin yaya J ta daina amsa koda na dantane kuwa indai shine
yabada da sauri Nafisa tace kada kiyi haka Maria.
Inkinyi hakan nice zasu zarga dana fada tunda sunsan tare nake da Ramaah ko
yaushe dama kuma suna zargina gashi ba uwa daya nake da mazansu ba sai ace nazo don
in shiga tsakaninkune ashe .
Wanan yasa ta hakkura da zancen saidai itama ta dauki zafi a nata bangaren yanzu
ba sakin fuska ko wani ban girma ga matan dan uwan mijin nata kuma.
Zama dai ya rike a gidan inda har yakai mama dubu tazo don jin ba,asi inda ta
tarasu tana tambayan me yai zafi hakane a tsakaninsu ?
Bata fahinci komai a zancen ta daiyi masu fada ta kwana biyu ta koma akacigaba a
inda aka tsaya muna sha,anin mu suna nasu saidai mama din ta dauki anty Saare da
Nafisa ta tafi dasu inda tace salima zata dawo hutu ta zauna da iya kafin gani kuma
tare da iyan.
Sai zaman gidan a lokacin ya soma fita min rai don ba abokan hira a gidan yanzu
da zaran na dawo ina dakin iya ko wajen yar uwata ba zan fito ba kuma sai
washegari.
Allah ya taimakeni iya da kanta ta bugawa mama waya da Nafisa ta dawo mata idan
ban nan zama ita kadai yana gunduranta.
Hakan yasa nafisa ta dawo ita kadai amma ta kiyayyi duk wani abinda zai kaita
part din yaya j a yanzu har na yar uwar tawa bata shiga ko ina a gidan.
Har yakai mazajensu sun fahinci akwai abinda ya faru iya yaya j yake tambaya
itace take fada mashi dan abinda ta sani ga zaman matan nasu.
Ranshi ya baci sosai ga abinda iyan ta fada don tace hassadane kawai da kyashin
juna ya kawo masu gaba a tsakaninsu.
Rasa abinda zasuce sukayiwa iyan kowa da abinda yake kiyastawa a zuciyansa
tsakaninsu dai komai lafiya yake tafiya koda akwai baraka basu yarda ko
mahaifiyarsu ta sanda hakan amma ga iyalinsu nason kawo masu matsala kuma a hadin
kan nasu.
Saidai mama bata yarda da hakan ya faru ba a yanzu kan ta daura dammara wanan
zuwan da zatayiwa iya data dameta ta kwana biyu bata zo ba zasu ga canj a wajan ta
baki dayansu duk wace ta kuskura tayi wani abinda ba daidai ba a gidan.
Basu kadai ba har saare ta shiga wanan fadan na mama a yanzu don gaba daya ta
hanata shiga ko wani part a gidan.
Saidai hakan bai hanasu hurdansu ba a boye tunda gulmane akwai waya a tsakaninsu
sun dai kaucewa idon ita mama dubu din ne.
A yanzu ko yaya Habu yana gari a nan wajensu nake kwana don na dawo da rayuwana
gun yar uwata baki dai shigowa part din mu kiga wani abin kazanta a garemu ko wani
abinda bai dace ba can.
Yayin da arzikin mazajen nasu keta bunkasa sosai wai ashe ita anty saare ta samu
matsala a karatun ta wanda yasa ta bar makarantar da takeyi a farko na gane hakan
ne wajen jin ta koma da karatunta a nan F C E zaria.
Saidai a hostel zata zauna tace kuma suka yarda amma tasha fada sosai wajen yan
uwan nata don har shi J yana ikirarin idan bata tsaya tayi karatu ba wana katon ba
zai sake bata kudinsa akanta ba.
Kwatsam zancen auren ummah ya taso hakan yasa mu zuwa garinmu da tun zuwan mu
bamu taba marmarin komawa ba.
Munje kafin bukin inda yaya Habune ya kaimu da kanshi zamu dawo mu taresu a nan
kamar yadda naji suna fada ba zance nayi farin ciki ko bakin ciki ba nidai na kasa
tsayar da zance daya a zuciyata akan auren.
Gaba dayan mu bamu so zuwa wajen baffa ba amma aka rinjayemu muka tafi dole
ganin sa munyi arziki ya tafi Adamawan cameroon a lokacin hakan yasa bamu samu
ganin shiba saidai mutumina kan Dage manga juna dashi har na karbi lamban wayanshi
rakani toilet dayake shan kida dashi.
Ban yarda na bar garin ba saida ya ban kata,un makaru da yayi ikirari dashi yace
idan naje na juye a kyale kar na barshi a leda.
Kudi na dauko na mika mai tare da gargadinshi akan kada kowa yasan hakan don na
kara masa gobe nasan matsalan dan uwana wajen kwadayi.
Jin dadin hakan yasa yace kai amma Ramatu kin kasheni yau to jo kiji wani magana
na matsa ya soma magana kamar a cikin rada zakice yana tsoron wani yajimu duk da
matarshi saida ya turata cikin gida ta samo leda ya san min dankali.
Wanan daman muka samu ya fada min wasu sirika da zamu fito na dankawa matarshi
itama dubu biyo don nayi mata faein sani dani akai nemanta a lokacin bayab mune
akai aurensu.
Na kurune da dani aka hadashi amma uwarshi tace sam bata yarda da hakan ba ita
don idon mu ya bude da yawa zanwa danta wayau na hanashi aje Nagge.
Nikan taimakona tayi a lokacin da irin gulman nasu da camfi na kauye da