Showing 9001 words to 12000 words out of 328222 words

Chapter 4 - Murfin Jallo Dan Uwa By ZAINAB IDRIS MAKAWA

fulatanci take kwalawa wata kira da YANDA yanda
yanda tana mata hannu tazo.
Sai ga wata doguwar yar matashiyar budurwa ta juyo wace aka kira da Yanda din
takaraso zuwa wajen matar tana mata fulatanci.
Ido ya kafe ta dashi yana kallon yadsa ta karaso tanawa matar magana acikin
yanayinta.
Yayi da Abubakar yake tsaye yana kallonta cikin mamaki yana fahintar me take
kokarin fadawa yarinyar.
Daidai lokacin kuma Sahibi ya juya harshe a cikin turanci yake fadin ko ya saye
yana da wuya yakai gida bai lalace ba iyakarsa idan a nan zaiyi amfani dashi kawai.
Sai sukaji muryan matashiyar na basu amsa da fadin ku saya daga nan har sati
biyu baya komai koda ba a saka a cikin fridge ba.
Kayan mu suna dakyau da inganci bawai ina yabo bane don kusaya ko don na cuce ku
saboda nasan zakuso shi ko nan gaba.
Ta kara fada a cikin turanci da alaman gajiya karara a fuskanta lokacin tana dan
kakabe kuran dake taba koren nasu da wani dan gashin dake hannunta na dabba da
akaiwa ado da duwatsu .
Tsaye sukayi galala suna binta da kallo tare da tambayan wai dama kuna jin
turanci haka ashe da zaginku mukayi shike nan kunjimu.
Ta dan kai zaune tare dan murmusa tana fadin kadan kadan ba balle nasan ba kuyi
kama da wayanda zasu zagemu ba ai.
Dagajin hausan mamanku na gane ku mazauna Nageriane don hausanta daban da wanda
kukeyi a kasan nan.
Eh daga can muke koma ince a can aka haifemu rayuwace ta dawo damu gida bayan
rasuwan mahaifiyar mu rikon mu ya dawo nan.
Sosai ta bashi tausayi tsab ya gama kallonta yana karance yanayinta turancine
neat a bakinta amma kuma gata ta saje da dabi,un mutanen wajen ba zaka taba cewa
ita din tasan ko zo inkasheka ba da hausa balle turanci.
Yanda din ta kawar da shirun take fadin ku saya zakace nace idan kuje dashi aka
saka a fridge zaiyi rabin shekara a can bai baci ba wanan karon a cikin hausa tayi
maganan tana kara bude manyan koren dake gabansu.
Sahabi bai yarda da zancen ta ba don abar zancen yake fadin wai ina zamu samu
abinci mai kyau a wajen nan ?
Ta dan juya kafin ta fara masa kwantace ganin baigane ba yasa ta kwalawa wata
yarinya kira da Maria zoki nan saiga wanan yarinyar dake firgitashi tun zuwansu
garin itace aka kira da Maria din.
Yarinya ce karama saidai da gani ba sai an tambaya ba don kamarsu da yar uwar
nata da aka kira da yanda sukayi kama sosai ita wanan din dai ta girmewa yarinyar
a shekarune kawai zace sai dan haske da karamar ta dara babban dashi.
A cikin yare take fada mata ta kaisu wajen saida abincin yan maiduguri ta amsa da
to tana watso masu idanuwanta masu kama da madaran tana wani irin juyasu alaman
suje din tayi gaba suka bi bayanta .
Zansu tafi babban matar ke fadin ya zancen sayan kayan sahabi yana kokarin
fadin su barshi kawai shi kuma Abubakar din yace dasu a bari su dawo zasu saya
hakan yasa yaga fara,a a fuskan yar budurwan data kashe zuciyarshi da mamakinsu.
Sun kama hanya tana gaba da dan kwarya karami a hannunta bata ko tsaya wani
jerawa dasu ba tasha wani kwana suna biye da ita har zuwa wanan wajen da basu san
dashi ba.
Oya mun gode ki tafi kada a nemeki Sahabi ya fada sai ta amsa da to tana
kallonsu saidai taki gusawa daga inda take.
Abubakar daya kula yace da yarinyar yaki zo nan Abubukar ya fada yana kallonta
da sauri ta biyoshi a baya zuwa inda suka nufa.
Tare suka shiga shagon yasa aka hada mata take away guda ukku ana mika mata ta
juya a guje cikin murna bata ko tsaya godiya ba ta nufi sansaninsu kai tsaye da
gudunta a cikin murna.
Murmushi yayi ya juya wajen sahabi dake mamakinshi yace mutumina yaya dai nisawa
yayi yana zama ya soma fadin tausayi suka bani wallahi.
Haka duniya take ai dama ba ko yaushe mutum ke samun yadda yake so ba a duniya
sahabi ya fada yana kallon abinci gabansa da aka aje masu.
Abincine lafiyayye mai kyau irin na hausawa ga kamshin man shanu yana tashi
acikinsa sukaci sukaiwa yan uwansu take away.
Duk abinda yake hankalinsa na gun wa yan nan mutanen don hakane ya saci jiki ya
koma sansanin nasu saidai ya samu basa nan don lokacin yamma tayi sai wata mace
dake zama a kusa dasu.
Yake tambaya take fada mai ai basu kai dare a wajen sun koma gida saidai gobe
tunda safe zai samesu sun fito insha Allahu.
Washegari kuwa rana ta biyu da taron mutane sun fara tattara kayansu don shirin
komawa garuwansu daga ciki har dasu Abubakar duk daidai su sai an rufe taron suke
son su kama hanya komai dare a ranan.
Bai manta da zancen yaran nan ba don da zancensu ya kwana a zuciyarshi yana
son ya san wani abu a game dasu din.
hanya kama ya nufi runfarsu tun daga nisa ya fara hango ita babban wacce yake
kyautata zaton mahaifiyarsuce ga wasu yan Nageria suna sayan kayansu.
Don kayan nasu gaskiya yayi kyau sosai haka ya karasa gaban ya dan tsaya yana
dakon su gama cinikaiya da wa yanda ya sama din a wajen.
Karamar ya fara gani a gabansa tana binsa da kallo kafin ya tsinkayo babban
dake tafe da amalanken shannunsu dake dauke da kore.
Yana wajen suka sauke kayan tsab suka jera kafin ta dago ta soma gaiyar dashi
a cikin dan fara,a kafin tace dashi na dauka kun muna wayaune ai kun tafi koda yake
bakai kama da mayaudariba ba kai kan.
Jiya kuma sai kukayi wahala haka kuka saya muna abinci mai yawa angode Allah kara
arziki me za a baka daga ciki ta fada tana kallonshi tana dago kai ?
Samu tayi ya zuba mata ido baya ko kiftawa sai tayi murmushi ta sake maimaita
wane kake so yace yanzu ni ina na san me zance dake ?.
Tace wanan zaka iya saya kakaiwa iyali mata ko mama da yan uwa zasuji dadin
tsaraban shi ansan ka shigo kasan cameron .
Ko data dago kai still yana kallonta sosai sai taji ta tsargu da hakan ta dan
dukar da kanta kasa tana wasa da zara zaran yatsunta.
Bakayi magana ba ta kara fada kallon yadda ake durawa mutane a jarka yayi yace
nawa duka kayan nan da kika sauke ?
Ido ta zaro waje tace dukka fa kace zasu iya kaiwa dubu hamsin da kudinku na
Nageria ga mamakinta sai taga yana kokarin zaro kudin daga jikinsa.
Kuyi min parking dinshi yadda ba zai samu matsala ba kudin abinda zakiyi amfani
dashi ayi parking yana ciki saidai don Allah ?
Saita dago ta kalloshi yayi mamakin ganin idonta da hawaye jikinshine yai sanyi
ya dan matsa kusa yana fadin.
Lafiya dai tayi kasa da kai tana fadin bansan irin godiya da zan maka ba a yau da
an watse taron nan bamu saida kayan nan ba ba karamin fitina zamu shiga ciki ba don
zamuyi hasara sosai zamu kuma shiga cikin ukuba.
Saboda me ya tambaya yana kasheta da ido donson jin karin bayani shidai yanayin
yarinyar yayi mashi sosai tana da natsuwa sosai dayake hangowa a gareta.
Murmushi tayi tana fadin dogon labarine mundai gode da wanan taimakon da kayi
muna Allah ne kadai zai sakama da alherinsa.
Amma meya dawo daku kasan nan kuda kuka saba da rayuwan Nageria kuka zabi dawowa
nan ku zauna ?
Ya zamuyi bamu da kowa a can yanzu wanda yayi sanadin zuwanmu can Allah ya
karbi abinshi dole muka dawo kasan nan tunda ba yadda zamuyi.
Kina da waya in naje mu dinga gaisawa daku tace da ina dashi wanda nake amfani
dashi a school saidai zuwan mu nan gaskiya mun kadar saboda yanayi saidai ka ban
number wata rana zan kira insha Allah.
Ai har karatu kinyi ashe kuma kika kare a nan kina tallan nono tace wanda baida
gata ai duk yadda rayuwa tazo mashi haka zai rungumeta mun rasa gatanmu tunda
mahaifinmu ya rasu Allah ya jikansa yace ta amsa da amin.
Sai wata rana kenan zaki kira ba zaki kira kiji ko mun sauka lafiya ba ko kuma
ina da bukatan wanan abin ki turo muna dashi.
Dariya abin ya bata cikin dan kunya take fadin kayi hakkuri banda wayace kona
karba ba zan kira ba din kaga ai gara dai kar nayima karya.
Kinsan wajen motar mu ko ta amsa da ehh yace a shirya komai kusamemu can ya juya
ya tafi ta bishi da kallo tana yaba irin kirkinsa da halarci.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
[5/19, 21:37] Buhainat: Open this link to join my WhatsApp Group:
https://chat.whatsapp.com/CDBG34xpZRZ5dZR86m1f


MURFIN JALLO DAN UWAN TAFIYA,,,,,,,,,,,,

ZAINAB IDRIS MAKAWA

BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM,,,,,,,,,
5️⃣
GA MAI SON BANI HAKKINA ZAI IYA TURA KUDI NAIRA DUBU DAYA KACAL A WANAN LAMBAN
2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO A KIRA WANAN LAYIN WAYAN 08036959257
NAGODE ALLAH YA BADA IKON BIYA MUN GODE NAKU HAR KULLUN YAR MAKAWA, , , , , ,

YAR UWA KADA KI RAINA NAUYIN HAKKIN WANI A WURIN ALLAH DOMIN AMANACE HAKKI,WANI A
WAJENKA , , , , , ,


HAKKIN MALLAKAN JUYAWA AUDIOVISUAL S ZARIA TV KEDA WANAN HAKKIN KADA WANI KO WATA
YAYI GANGANCIN JUYASHI ZUWA AUDIO PLEASE,,,,,,,,,,,,,


A tsaye ta sameshi suna hada kayansu sallama tayi daga bayanshi cikin yar siriryar
muryanta ganin kalkon mamakin da Sahabi ke mata a bayanshi yasashi juyawa da sauri
yagame sahabi din ke kallo a wajen ?
Kasa tayi da kai tana kokarin gaidashi da aiki ta hada da fadin ga kayan ka an
hada komai yadda ya dace daga nan ko lagos zaka ba zaiyi komai ba insha Allahu.
Ba lagos zani dasu ba zariya zan kaiwa mahaifiyata ya bata amsa tace Allah sarki
aiko yayi daidai da bakin tsofi don komai baida tsami da zai hanata bukatansu.
Mungode kwarai wallahi yadda ka taimaki rayuwan mu Allah ya taimaki naka kaima
ta fada cikin yar siririyar muryanta.
Wai tsaya Habu wanan duk kayankane wanan haka kome nifa ban gane ba wuceshi
yayi yana fadin ba zaka gane ba kuwa kai matso ku saka min a bayan mota kunji ?
Lokacin ibrahim ya karaso yana fadin oga kace da shirinka dama muma bari mu debo
namu ashe dama ina son saya ina jin tsoro.
Kaje gunta kayansu yana da kyau sosai tace dariya sosai Sahabi ya kwashe dashi
yana fadin ashe mun saura dawowa garin da alama zamu dawo wani karon kenan kuma ?
Yar filo akwai saura a wajen ku tace eh za a samu bari na duba idan akwai a
wajen maman mu ta juya ta soma tafiya .
Kai dan iskane yacewa Sahabi dake ta kwasan dariyan shakiyanci sahabi din yace
dariya nake don yadda na hasko kayi tsaye ana shadinka kasan wanan aiba karamin
shadi zakasha akanta ba wallahi.
Shima zancen sahabin saida ya sakashi dariya in akwai abinda ya tsana a taba
lafiyan jikinshi balle shadi ta ina zai tsaya kan mace ai mai shadi ko gudane balle
ba adadi.
Zama yayi saman motan yana sauraren Sahabi dake bayani akan shadi da yadda
akewa wanda ya gaza motsin wayarshi ce da tayi dan tsuwa daga Aljihunshi hakan yasa
yaciro ya duba alert ne na lokaci har yayi niyar mayar da wayar sai kuma ya fasa
hakan sim din ya debe daga cikin wayar ya mike tsaye.
Wani wuri dayaga ana sayar da waya ya dosa layin waya ya saya duk da tsadansa bai
tsaya neman ragi ba ya biya ya juya ya koma inda ya fito.
Ya gama turo komai a dayan wayan nasa kafin ya goge na wanan wayan yana gamawa
tana karasowa wajen da kayan ibrahim.
Kudi ibrahim ya ciro ya bata yana fadin Allah yasa dai yadda kika yaba haka
yake don kada muje gida mu samu ba gaskiya bane yana da matsala ?
Irin duban mamaki din nan ta danyi masa kafin ta rausaya kai tana fadin Allah
ya tsareni da cutar daku idan na cuceku ina zan ganku ku yafe min ?
Daga haka tasa kai ta juya ta zoma tafiya inda kayansu yake daga bayanta muryan
Abubakar ne yake tsayar da ita a bayanta ta juyo ta dakata har ya tako zuwa inda
take.
Baiyi wani magana ba wayan hannunshi kawai ya mika mata bata karba ba kallonshi
tayi cikin mamaki ki karba mu rika gaisawa idan nakoma gida.
Kaita fara girgiza mashi tana fadin ka barshi bayan wanan alherin dakai muna mai
yawa zaka kuma mika min waya ?
Ko haka mun gode kasan girman taimakon da kaimuna a yanzu har in mutu ba zan
manta da hakan ba a rayuwata zan kuma cigaba dayima addua a kullum kan wanan
alherin.
Haba dai ya fada yana dan dariya kafin ya saita kansa yana fadin wai zaman me
kike a wanan kasan yanzu ko wasan nan ya kawo kuma nan ?
Yanayin fuskanta ta sauya lokaci guda tana fadin na fadama kaddaran zaman mu nan
sanadin mahaifinmu daya rasu shine zaman mu ya dawo nan kasan don bamu da kowa can
Abuja da muke zaune.
Nan kuma mun dawone a cikin yan uwa saidai duk da mun dawo cikinsu da zama har
yanzu suna,,,,,, Yanda warre ?
Wata bakar mace ta sa mata kira daga wajen saida kayansu hakan yasa ta juya da
sauri da zumar ta wuce saka mata wayan yayi a cikin kwaryan dake rike a hannunta ya
juya ya koma inda ya fito ta dan tsaya ta kalleshi kafin ta nufi wajen nasu saidai
kafin takai tacire wayan cikin dabara ta kada a kasan lalitan dake rataye a
wuyanta.
Basu dauki lokaci a wajen ba taba da umurnin su shirya su soma hanya don ganin
yadda mutane keta haramar bin hanya tunda wuri kada suyi dare.
Lagos Nageria.
Tafe yake cikin motarsa kiran kiran benz wace bai dade da mallakanta ba a yanzu sai
kira,a dake tashi a cikin sautin malam Ahmed sulaiman kano.
Yake dan bin kira,an shima kafin wayanshi ya dauki kara hamnu yakai yana rage
sautin dake tashi na muryan malamin addini a Nageria don ya dauki kiran Saiba
amaryansa daya gani din saman layi.
Ya akayi Saiba i will call you bank idan na isa yanzu ina hanya ina tukine don
Allah ?
Sweet J kada ka kashe don Allah ka saurareni don bansan idan ka kashe wani ya
rigani kiraka a fadama abinda bashi ba.
Meya faru kuma ya fada cikin kaguwa da yaji kome ke bakinta a lokacin dama akan
wanan Asmaun ne wallahi idan Asmau bata kama kanta dani ba sai na illanta mata
rayuwa.
Tseweeee ya tsoki yana fadin akan sakarcinku kika kirani ina saman hanya haka
bashi bafa Sweet J mama mukayiwa laifi muka kifa mata abinci saman jikinta.
Yana kokarin kashe waya yaji karshen furicinta a dan razane yace wata maman dai
kodai Iya kike son kira kikace mama ?
Mama dai ta tudun wanda ita nake nufi ta fada a sanyayye innalillahi taji yana
ta maimamitawa son bai taba zaton iskancin matan nasa har zai iya kai haka ba ai ?
Wallahi Sweet J ba,,,,,,,,,
You are very stupid idiot of you don kina yar iska kuyiwa mahaifiyana haka ki
kirani kina fada min sai ya kashe wayar gabaki,daya yana jin wani tukuki a
zuciyarshi.
Fuskanshi ya shafo da hannunsa yana gyara zama a cikin motan don yadda yake jin
zuciyarsa ya kasa samun natsuwa da zancen data fada din .
Duk yadda akayi wani abu mara kyau ya faru da mama din akansu shikan wai wani
aurene yayi a rayuwanshi da kullum baida natsuwa a tare dashi kan matan nasa daya
tara agida ?
Yanzu wazai kira yaji meke faruwane wai don baima son ji daga bakin ko dayansu a
yanzu wanan karon sam ba zai kyalesu ba iskancin nasu yayi yawa har abin yakai ga
mahaifiyarsa haka ?
Wa,iyazu billah a ina sukaga mama din har take fadin sun mata wani abu mara dadi
hakane tunawa yayi tsakiyan watane ake a lokacin don haka mama tazo gidan ke nan
gyarawa iya daki .
Dama daga tsakiyan wata zuwa karshen wata take zuwa wajen mahaifiyar nata
taimata kwalema don samun ladan mahaifiya a gareta.
Har in mama zata iya tsayawa akan nata mahaifiyar haka su da karfin su mai zai
hanasu tsayawa akanta har inda karfinsu ya kare akantasu mahaifiyar.
Oh shet yanzu wa zai kira yaji abindake faruwa har ya shiga haraban nasu da
mota sai a lokacin Abubakar ya fado mashi a rai .
Da sauri ya lalubi waya yana neman layin Abubakar din sai gashi ya samesa ya
dauka yana fadin na dauka ka manta da dan kanin nakane ai gamu nan yanzun muke
shigowa Nageria ai.
Sam ya manta da cewa Abubakar din baya gida ya kirashi ya sheda mai zasu shiga
kasan Cameroon wani shutting don haka bai gida ke nan a lokacin.
Saiya waye da fadin masha Allah Allah ya kawoku gida lafiya sai zuwa gobe dai ke
nan zaku iso yace insha Allahu nagode yaya J .
Suka kashe wayan yace common wazan kira ke nan kafin yakai karshen tunane aka
buga glass din motan nasa meiyabi ce don yana kallonta ta bangarenshi.
Kallon tsab yai mata kafin ya sauke glasa din yana kako murmushin dole a
fuskanshi yace hey how are you tayi murmushi tana fadin .
Mr handsome ka boye da yawa kwanan nan duk bani ganin ka na dauka kayi tafiyane
ai da ban ganka ba kana jin dadin kafa garin nan ?
Dan murmushin yake yayi mata kafin yace in baki ganni ba aini ina ganinki
sometimes tare da wanan dogo saurayin naki.


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login