Showing 126001 words to 129000 words out of 238465 words

Chapter 43 - Wata Kishiyar by Maryamah Mrs AM

dan ta tabbatar labari ya rigada ya isar
mata yanzu.

Cikin sanyin daya aureta yanzu ta gaida Goggon kafin tayi shiru tana jira taji ta
inda zata rufeta da fada amma ga mamakinta se ji tayi tace

"Ma'u kiyi haquri, shi aure raine dashi Idan lokacin mutuwarsa yayi koda dalili ko
babu se an rabu, sannan kowa da kika gani da irin qaddarar sa a rayuwa, mutuwar
aure bata da dadi amma kar hakan ya sa ki dauka gazawarki ce ta janyo ko kuma wani
ne silar hakan Aa babu wanda ya isa ya qulla aure ko ya kashe shi se Allah dan haka
ki dauka cewar wa'adin da Allah ya dibarwa zamanki da Bashir ne ya qare kawai.

Kar kuka ki ce zaki saka kanki a damuwa ko wani abu kinji kiyi Addu'a Allah yasa
hakan shi yafi Alkahiri, saki nawa ne?"

Cikin karyewar murya nace mata "Wallahi Goggo ma Banyi masa komai ba, kawai saboda
yace se ba bar aikina saboda Amirah Shikenan abinda ya faru"

"Na sani Suhaima ta gaya mun komai kiyi haquri yanzu dai saki nawa ne?" Ta sake
tambayata, seda naja Majina dan ta tuno mun da kukan da na bari nace mata

"Saki biyu ne kuma nayi bari dazu da safe".
"Subhanallahi Bari kuma a garin yaya daman kina da ciki ne" Goggo ta tambaye ni
muryarta cike da Alhini, seda na tsagaita kukan nace mata

"Nima ban sani ba se shekaran jiya naje Asibiti na dawo ban ma kai ga sanar masa ba
ya sake ni".

"Yanzu be san da maganar cikin bama bare barin kenan, ai kuwa ya kamata tun wuri a
gaya masa tunda kinga kenan kin gama Iddah kar yaje yayi ta lissafin Bogi tunda da
sauran igiya a tsakanin ku" Goggon ta fada, da mugun mamakin maganar ta nace

"Yanzu Goggo har kina zaton cigaban zama tsakanina da Bashir, ai Goggo ko shine
autan Maza na haqura dashi. Sakina fa yayi sakin wulaqanci akan kishiya wallahi
sedai ya zauna da ita wadda yake so har qarshen rayuwarsa ko ze mutu dan nagama
auransa, dan Allah a wannan karon kar kice zaki tilastani komawa gidan Bashir in
dai ba so kike zuciyata ta buga na mutu kowa ya rasa ba" na fada ina qara fashewa
da Kuka.

Qarshen abinda Goggo zata sakeyi mun a yanzu ta maida ni gidan Bashir, ba dan na
dena son Bashir ba wannan nasan wani abu ne da har na mutu yana raina amma na tsani
zama dashi ba kuma na fatan Allah ya kawo dalilin da ze maidani gidan sa.

Duk da yana yin da take ciki seda tayi yar dariya kafin tace
"Ni ban ce ki koma gidan Bashir ba amma idan zama be qare a tsakanin ku ba haka
zaku gama duk abinda zakuyi kuma ku koma ku ci gaba da zama dan haka duk abinda
zakiyi karki tsananta ko dan Albarkar zuri'ar da take tsakanina ku.

Sannan maganar yara idan har ya matsa ki bashi yayansa kar kice zaki tsaya ja in ja
dashi tunda yana da me riqe masa shikenan, ke kuma zamanki a nan baze yuwu ba zuwa
safiya zan kira Alhaji Qaramin kodai ki nemi transfer ki koma can Abujan gabansa ko
ki aje aikin ki dawo gidan ku ki zauna amma bazaki zauna ke kadai anan ba".

A gaba daya tsarikan na Goggo babu wanda naji yayi mun, bana jin zan iya bawa
Bashir yarana maganar Transfer kuma ko barin aiki ta manta aikin akansa aka sake ni
sannan na barshi ai kuwa na tashi a tutar babu, amma yanzu bazan musa mata ba zan
barta tayi magana da Alhaji Qaramin na tabbatar shi baze bari a rabani da yayana ba
ko aikina.

Haka mukayi sallama tana sakeyi mun nasiha na kuwa ji dadin magana da ita sosai
muka rabu tana jaddada mun dana sanar da Bashir maganar ciki da kuma Barin da nayi
dan gudun abinda kaje ka dawo, haka na kwana da niyyar gobe idan yazo kai yara
makaranta zan gaya masa tunda da alama bega takardar dana ajiye masa ba.

BASHIR
Yauma dai a hanya ya siyo abincin sa haka ya dawo gidan na nan a yanda ya barshi
sema qarin datti da yayi saboda qurar qasan gado da suka watso masa palour dazu.
Haka ya shiga dakinsa yayi wanka gaba daya gurin ya hargitse masa ya rasa ta yanda
ze fara mayar da kayansa cikin wardrobe tunda ya saba da an kawo masa guga Ma'u ce
take jera komai a inda ya dace.

Haka ya zura jallabiyya ya dawo palour ya kade kujera ya zauna ya bude abincin,
loma uku yayi ya ture gaba daya abincin ya fice masa daga rai dan bakinsa ya saba
dame dadi, dukda wannan din ma me dadin ne amma dandanok girkin Ma'unsa ya banbanta
dana kowa shikadai ne abincin da ko iya qamshinsa yana rage masa yunwa dan shi fa
abinci indai ba nata ba ko yaci baya jin ya qoshi sedai kawai cikinsa ya cika
maganin yunwa amma ba wai dan ya gamsu da cewa abinci yaci ba.

Yana zaune yana dannan waya su Ahmad suka shiga gidan da gudunsu, Ganin sune ya
debe masa kewa har aka kira sallah suka tafi masallaci tare, yana kallon Aliyu ko
inda yaje yaron be kalla ba yayi murmushi kawai da suka dawo zaau tafi ya dakko
Chocolate ya basu harda ta sauran kafin ya raka su har qofar gidan suka shiga, yana
jiyo qamshin abinci da alama girki sukeyi.

Badan kar mutunchinsa ya zube ba babu abinda ze hana ya shiga yaci amma ya qudurce
a ransa dole ya koyawa Ma'u hankali ta yanda da kanta zata bishi ta bashi haquri, a
qalla se tayi kusan kwana dari da wani abu kafin cikar Iddarta dan watan ta me
kwana talatin da shida ne kafin sannan kuwa ta biyu liqis ta yanda ko kara ya ajiye
bazata sake tsallakawa ba. Haka yaja jiki ya wucw yana hadiyar yawu, qarshe se se
shayi yasha da wani guntun cake da Allah yasa basu dauke ba ya hada da dambun nama
shima a irin wanda take masa ne ya ajiye a office ya tuna yana mota ya dakko shi.

Seda yaje kwanciya idonsa ya kai kan farar takardar da tun jiya ya ganta amma be
duba ba, daga kwancan ya janyota ya bude yana mamakin ko tasa ce ma ya manta sedai
tambarin Asibiti da sunan Ma'u daya gani yasa ya qara hasken fitila dan ya gani da
kyau.

"Kai Allah na gode maka, Wallahi Allah yana sona" ya fada a fili cikin farin ciki,
wannan wata dama ya samu ya tabbatar se Asma'u ta kawo kanta da kanta musamman da
yawancin cikinta suna qara mata buqata yana zaune zata zo har inda yake ta bashi
haquri kai wannan abu ya masa dadi.

Hotonsu dashi da ita da yake akan bedside drawer ya dakko yana shafa fuskar ta,
ranar Anniversary dinsu na shekara Goma suka duke shi daga shi har ita suna dariya
ya manta dariyar me sukeyi a lokacin.

Sumbatar fuskarta yayi kafin yace
"Kiyi haquri Ma'una, nasan sena fiki azabtuwa da rashin ki a kusa dani amma ke kika
jawo mana, taurin kanki da kafiya ya saka komai ya faru amma yanzu ga dalilin da ze
dawo mun dake cikin ruwan sanyi na samu, Ina son ki Ma'una".



🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah Farouk
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)


Wattpad @MaryamahMrsAm

Page 42

Ranar Juma’a Amirah ta tafi Lagos, da yake saukar Yamma tayi seda Bashir ya tashi
daga gurin aiki sannan ya biya ya dakkota suka wuto gida.

Ina zaune dakina Jafar ya shigo da gudu yana cemun

“Mami Abbi ya dawo”.
“To sannun sa Jafar” na fada ina duba wani document da aka turomun daga gurin aikin
mu.

“Ai Mami ba shi kadai bane ma tare suke da Anty Amirah” Jafar ya sake fada, se naji
kamar an saka mun stop, na dago na kalli yaron kamar me son tabbatar da abinda ya
fada se kuwa ya daga mun kai yana sake cewa

“Ita ce tazo gasu Ahmad can ma sun tafi gurinta kuma naga da Akwatunan kayanta qila
ta dawo gidan kenan ko Mami?”

“Kaje ka kirawo su magriba tayi” na fada kafin na mayar da kaina kan abinda nake yi
amma sam ban gane komai ba. Idan nace zancen zuwan Amirah be dake ni ba nayi qarya
ta tabbata kenan dagaske saboda ita Bashir ya sake ni tunda ga ta nan ya kawo ta
nan din.

“Allah kaine Allah, kayi mana sakayya akan duk wanda ya cutar damu” na fada a fili
bayan na ajiye Tab din hannuna dan sam na dena gane abinda nakeyi. Tagumi na rafka,
se kuma na janye nace da kaina “Tagumin fa be ganni ba, tun wuri gara na tattara
shirgin Baban Ali a gefe na fuskanci abinda ze tun karo ni a gaba” ina fadar haka
na miqe na shiga Bayi nayi wanka.

Ina cikin shafa mai Muhammad ya shigo da leda a hannunsa da ban san ko menene a
ciki ba.

“Mami wai gashi inji Anty Amirah ta kawo miki tsaraba” ya fada yana ajiye ledar a
kusa dani, har ya juya ze fita na janyo shi, se da na zare masa ido kafin nace

“Dauki ka fitar can bola kayar, idan na kuma ganin ka shiga gidan nan idan sena
cire maka kunne, wuce kaje ka kirawo Ahmad daman kune masu shegen yawo ai bini bini
kun tafi can”.

Haka na cigaba da shiryawa ina mita, seda na sake tara su gaba daya naja musu kunne
akan babu su babu zuwa gidan Amirah, idan ma uban suke son gani se su jira ai yana
fitowa su ganshi a waje su wuto gida amma ban yarda wani ya sake ya je gurinta ba.

Washe gari da yake Asabar ne bamu tashi da wuri ba se gurin goman safe dan haka
kafin muci abinci muyi wanka an fara kiran sallar Azahar.

Aliyu ne ya sa su a gaba suka wuce masallaci da suka tashi dawowa shi kadai ya
shigo ba tareda sauran ba.

“Aa Yaya ya naganka kai kadai ina qannen naka” na tambaye shi ina gyara Hijabin
jikina dan zan leqa gidan Anty, bata jin dadi kwana biyu itama.

“Mun taho a hanya sukaga Abbi shine ya jasu gidansa” Aliyun ya fada yana zama akan
kujera, se nayi qwafa nace “wato basuji abinda na gaya musu jiya ba ko nasan Jafar
ne ze jasu za kuwa su dawo su same ni, Faridah taso ki rakani ke kuma Amna idan kin
gama cin abincin in zaki zo toh” na fada ina nufar qofa.

Kallo daya nayiwa gidan Bashir shima bisa kuskure na shige gidan Anty, ban zauna ba
ganin Baba yana gida dan a zatona yana gidan uwargidansa ne yau dan haka a
tsatstsaye nayi mata sannu yana ta in zauna mana nace Aa anjima na dawo muka fito,
ina sako qafata waje nayi kyakyawan gani da Bashir tareda matarsa saboda tsabar
sabon salon munafunci ta dauki Ahmad se rinjayarya yake kamar zasu fadi suka shiga
mota, inajin Ahmad din yana cewa

“Mami, Abbi ga Mami nan ba tareda ita zamu je ba” ko iskar su ban waiwaya na kalla
ba na shige gida. Ban kai ga cire Hijabi na ba naji an turo qofar an shigo ga kuma
qarar takalmi qwas qwas alamar dai macace se na waiwaya naga waye ido na ya sauka
akan Amirah.

Fuskarta dauke da Fara’a ta qaraso cikin palour nidai ina tsaye har ta samu kujera
ta zaune tana waige waige. A lokacin Allah kadai yasan abinda nake ji a cikin
zuciyata amma na rigada nayiwa kaina fada, badai ni na sake yin wani tashin hankali
akan Bashir ba tunda dai yanzu babu abinda muka hada dashi dan haka nima sena fasa
cire Hijabin na zaune a kujerar da take kallonta fuskata a hade ba tareda nayi
magana ba.

“Ina wuni Anty” ta fada tana wata dariya kamar kwarkwar, seda sake tsuke fuksa
kafin na amsa da “Lafiya” a taqaice.
“Tun jiya naso na shigo wallahi na gaishe ki kuma se gajiyar hanya ta hanani ga
gidan nazo na tarar dashi duk ba a kintse ba shine fa nayi yan gyare gyare har yau
da safe, yanzu ma fita zamuyi wai twins ne suke son Ice cream zamu je a siyo Ina
Farida da Amna ban gansu ba su” Amirah ta sake fada tana bin lungu da saqon palour
da kallo duk ina ankare da ita, zanyi magana Farida ta fito daga dakinsu, kallo
daya kuwa tayi mata ta zumburi baki ta juya ciki ma ta fasa fitowar ita kuwa Amirah
se wani murmushi takeyi na ala dole ita ta iya bariki.

Jin bata sake cewa komai ba yasa nace mata
“Zaki iya tafiya tunda mun gaisa ko, amma mu nan bamu saba da shige shigen maqota
ba. Kowacce mace a gidanta take zama dan haka karki sake shigowa mana mun gode”
nayi maganar raina a sake kai ba kace mun hada wani abu nida ita ba.

Na sani gulma da munafunci ne ya shigo da ita dan ta nuna mun tazo, sannan taga
yaya na zama tunda Autan Maza ya sake ni ko? To gani dai garas a cikin hayyacina,
sema fari da kyau danayi saboda ni idan na rame ido na da hanci qara fitowa sukeyi
ga kuma hutun dana samu kusan kwana nawa ina zaune a cikin Ac sannan da wani hadin
ridi da Madara da Anty takeyi mun duk yamushewar da nayi a kwanaki biyun nan na
warware fatata ta nuna jin dadi.

“Uhm toh shikenan bari naje nasan Yaya yana ta jira, se mun dawo” ta fada tana
miqewa, har ta kusa fita ta waiwayo tace
“Anty gurin nan yayi kyau har yafi can gidan ma wallahi”.

“Allah ko, se ki gayawa Bashir ya zuba miki irin kayan idan kuma nan din kike so se
mu baki” na fada ba tareda na daga kai na kalleta ba, itama bata ja maganar ba ta
fice tareda ja mana qofa.

Naga qoqarin ya kwarai da tsantsar rashin kunya da har ta iya dakko qafa ta shigo
mun gida ko kuwa tana nufin tace mun bata san bana tareda Bashir bane, koma dai
yaya yau daya dai na danne zuciyata duk irin abinda ta ringa ayyano mun da nayi
mata na daure amma tabbas duk randa ta sake gigin shigowa ban san abinda zanyi mata
ba, su kuma dan uban su zasu dawo su tarar dani se sun gaya mun me suka rasa a
gurina da suka tafi yawon roqo gurin Bashir.

AMIRAH
Ganin da tayiwa Asma’u lokacin data fito daga gidan Anty sam be gamsheta ba. Bata
zata cewa a dan tsakanin abinda be ko kai sati daya ba Ma’un zata iya dangana da
abinda ya sameta har ta ganta tana yawo akan qafafun ta kamar babu abinda ya faru.
Mantuwa Bashir yace yayi ya koma cikin gida, yana shiga itama tayi saurin fita daga
motar tabi bayan Ma’u.

Ba qaramin girgiza tayi da ganin tsaruwar sabon gidan Ma’un ba tunda dai tasan babu
silan Bashir a ciki wato ita wata sabuwar duniya ma ta bude ta qawata gida kamar ba
wadda aka saka ba tana walwalarta, ta kuma yi zaton ganinta ze batawa Ma’u rai har
tayi fada ko wani abu daga nan ta samu damar da zata sake qunsa mata takaici dan
sosai su Addah da Sa’adah sukayi mata hudubobin tsiya tunda suka ji Ma’u tana kusa
da gidan.

Sun karanta mata yanda duk zatayi ta uzzura mata ta yanda ita da kanta zata bar
kusada Bashir idan taga bazata iya daukar abubuwan da Amiran take yi mata ba amma
se gashi ko a kwalar rigarta bata ga alamar ganin ta ya daga mata hankali ba, kai
ita se take ganin kamar ma qarya ne babu wani sakin ta da yayi dan daga ita har shi
din bata tsammaci ganinsu a hayyacin su ba har gara Bashir ya rame amma Ma’u fa
kyau ma taga ta qara abunta.

Haka ta ringa cizon yatsa a mota ga Bala’in da yakeyi mata akan wane dalili ta
shiga gidan, ta qudurce a ranta tabbas seta gallabi Ma’u ta bar unguwar nan dan
bazata juri haduwarsu da Bashir kullum ba sannan ga wadannan mayun yaran da tun
zuwan ta jiya suke zurubtu a gidan, gara suyi can nesa dan in ba haka ba ze zamana
an kashe miji ne ba’a sare kansa ba.

Fitar da tayi niyyar warwasawa yau itama gata a gaban motar Bashir a Lagos sun fita
shan Ice cream qarshe haka suka dawo kowa yana hada rai yaran ne kadai suke ta jin
dadinsu shi kuma ya biye musu har wadanda ba’aje dasu ba seda akayiwo wa tsaraba.

Da suka dawo gidan ma kayan sa yace ta shiga ta gyara masa sukuma suka baje a
palour da yaransa suna ciye ciye da buga game baqin ciki kamar ta fashe daga zuwa
rana daya za’a fara haka lallai dole a sake sabon lale.

Wayar ta ta dauka ta shiga kiran Sa’adah tunda itace malamar tata, bugu biyu ta
daga tana tsokanarta da cewa

“Uwargida Amaryar Engineer, ashe kin kunna waya ai bari nayi ku gurji Amarci kwana
biyu tunda an dade ba’a hadu ba daga baya se musha labari”

“Wayake ta zancen wani Amarci yanzu Anty Sa’adah” Amirah ta fada tana jan tsaki,
daga dayan bangaren Sa’adah tace

“Bangane me kike nufi ba, kardai ki cemun period din dawowa yayi bana ce miki kisha
pills ba ze dauke ko baki sha ba”.

“Duk fa ba wannan bane yanzu, ni kin ganni tunda nazo jiya ma nake aiki kamar jaka.
Gida kaca kaca ga gyaran dakina tsabar wulaqanci masu saka gadon a ciki suka bar
kwalaye da sauran tarkace, haka ya tasani a daren sena gyara, dan ma na taho da
Miya kin gani sefa da na dafa mana taliya mukaci, ga shegun Yayansa sunzo sun tasa
mutane a gaba saboda haushi ma nayi bacci na barsu ban san lokacin da suka tafi ba.

To kin ganni yanzu ma dai na taqaita miki tun safe aikin nake, harfa fita mukayi
wai ze siyowa Yaran Abu gasu can mun dawo suna palour ni kuma ya saka ni ninkin
kaya” ta qarasa maganar cikin tsantsar takaici, badan hudubar da aka mata akan ta
kwantar da kai ba da wallahi tun a yau gayyayar zata watse dan ita fa ba aikatau
tazo yi ba, zuwa tayi ta mori miji taji dadi a toh.

Dariya Sa’adah ta ringa sheqa mata abinda ya sake qular da Amirah kenan tace

“Wannan ai wulaqanci ne, na gaya miki matsalata kuma kin mayar dani abin dariya
shikenan, bari na kashe wayata, barima kiga na gaya masa nifa bazan yi ba dan na
gaji wallahi sekace jaka”.

Seda Sa’adah ta tsagaita da dariyar kafin tace “toh ai Amirah dole nayi dariya,
nifa bari kiji wallahi na dade banga sakaryar mace irin ki ba amma fa kiyi haquri.

Ce miki akayi a banza kake mallake mijin daman ai se kin zama jakar, a gabansa ki
zama kamar baiwa se yanda yayi dake ko takaki yayi kar kice komai shine zaku zauna
shiru bame jin kanku ki zama ta gaban goshi yanda ko wani ne ya kawo aibun ki ze
tare miki kuma ki more shi yanda kike so tunda yana juya ki shima, ko bakiga ni
har wanki nakeyiwa Yallabai ba, idan kuwa ina gabansa biyayya ko ubana Albarka”

“Tab wallahi bazata sabuba kuwa dan ni

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login