Showing 42001 words to 45000 words out of 295847 words
gidan jiya. Dan da ta sake haifa shima babansa ya kaiwa
yarsa. Ta dawo gida an sake komawa zaman zawarci ga rashin abinyi. Bakincikinta ya
karu da yadda Mairama da yaranta suke rayuwa ta rufin asiri. Duka suna karatu a
inda take koyarwa.
Ta soma saka gilashi ne a lokacin da ta fara fama da matsanancin kaikayin ido da
gani dishi-dishi. Ta sha wahalar idon sosai ta kuma kashe kudi.
**********
Sun dawo gida da Emzee ya shiga dakunan duka matan gidan su hudu don tuni Malamijo
ya sake cike gurbi. Yadikko tana nan a matsayin uwargida Hajjo kuma ta biyu sai
amare Hanne da Binta.
A gajiye take ta kwanta tana murna anyi hutu. Sallama taji anayi ana kwala mata
kira ta tashi a zabure Salame tana kwalliya zata je wurin mamanta.
"Uwar yarinyar nan Alhihi take ko me kace Danmama?"
Danmama ya zumburo baki "Alheran amma Radhiya naji ana cewa. Ita ce ta mareni kuma
Anti batayi komai ba saboda 'yarta ce"
"Allah gamu gareka" Mairama tace a ranta kafin ta fita tsakar gidan zuwa wurin
matar.
"Hajiya kiyi hakuri rigima ce irin ta yara kuma tun a wurin an hukunta su"
Rai a bace tana nuna bayan Danmama ta ce "a hukuncin ne aka yi masa bulala biyar
ita kuma biyu saboda son kai. Dama wane adalci kuke yi idan kuna koyarwa a
makarantun da 'ya'yanku suke. Daga yau sai yau ki jawa 'yarki kunne. Idan ta sake
taba min yaro bazan yarda ba"
Hakuri Mairama ta bata duk kunya ta isheta. Radhiya ba dai dauko magana ba. Idan
anyi magana tace ita 'yar soja ce. Yadda take alfahari da aikin babanta sai ka
rantse ta tashi tare dashi. Ko ina ta tsaya ma yanzu bata sani ba. Bari dai ta dawo
yau mai rabasu sai Allah.
Ashe gidan Mal Kallamu ta bi Uncle Idris. Can taci abincinta a bangaren amaryar
Idris din sannan ta fito suka hadu da Malamijo a kofar shiga. Harararta yayi kamar
ya kwadeta jiya taje gonarsa ta sami wani sabon maikaci da yayi ta nuna masa wata
tinkiya wai Malamijo ne ya aiko ta fada masa a yanka ya dau kai da kafa. Ana cikin
fida yazo ya gani jikinsa na tsuma yayo kanta tace gani tayi ta kasa. Kunnenta ya
damko tana ihu
" 'Yar kundun uba ta ina kika ga ta kasa din?"
Ba yadda ya iya a dole jiya gidansa aka ci dafge kowa ya warwasa. Dakinsa ta bishi
yana gwawiyar kashi tace "Malamijo ashe kaima kana son naman dai. Allah Yasa in ga
wata ta kuma kasawa" da mafici ya biyota har yana tuntube.
Ita ce a gaba ta hango Umminta da Danmama da mamansa. A guje tayi niyar komawa
Malamijo ya riko wuyan rigarta ya kaita gabansu.
"Mairama ki jawa 'yarki kunne idan ba haka ba wannan karon idan kunje hutun
Sakkwato ki barta a can. Yarinya ce kamar aljana. Dubi kaninki nasa salihancin har
haushi yake bani. Ke kadai kina mace kin tattaro duk halayen kiriniyar kin dorawa
kanki"
Kallon da ta ga Mairama na yi mata tasan yau jiki zai fada shiyasa tana tura baki
da magana ciki-ciki tace "to ba shine yake wakar wai Malamijo tsolon rake ba, rama
maka fa nayi"
Jikin Malamijo da na uwar Danmama sai yayi sanyi. Danmama yayi wiki-wiki da idanu
hakan ya tabbatar ba karya take ba. Babarsa kuwa ta talle masa keya tana cewa ya
bashi hakuri. Yara kuwa sai dariya suke a hankali Malamijo yaji kunya ya shige
daki. Kunnen Radhiya Mairama ta kama tace ta wuce daki.
Da yamma ranar sai ga Alh Ado Indararo da kansa yazo bayan matarsa ta fada masa
abinda Danmama yayi. Sun saba ciniki da Malamijo baya son kasuwar ta watse don yana
dukan hancin Malamijo akan dabbobinsa sosai batare da shi ya sani ba.
Ya bashi hakuri ya nemi Mairama itama ta fito da babban mayafi ta gaishe shi.
Kallon farko Alh Indararo ya fada kogin kauna baya ji baya gani. Tana komawa ciki
baiyi kasa a gwiwa ba ya fadawa Malamijo bukatarsa. Zani ce ta tadda muje mu. Shima
kwadayin kudin Alhajin yake yace ya bar masa wuka da nama.
A daren ya sanar da ita tayi tsalle ta dire tace bata da sauran aure a duniya. Sun
fara rigimarsu bayan kwana biyu ta tattara ta tafi Sakkwato kamar yadda ta saba duk
hutu suna zuwa suyi sati daya ko kwana goma.
Duk gidajen 'yan uwan Zayyan na jini da makusanta irin su Mal Aminu sai taje. Kuma
bata fasa zuwa barikinsu ba ko zata sami labarin Zainab da Mami. Gidan iyayen
Zainab yanzu wasu ne a ciki. Ta matsu tasan halin da suke ciki amma babu dama. Haka
kuma har yau babu wanda ya kirasu akan wani kudi na ihsani ga jaruman da suka rasu.
Suna hira da matar Maikudi da Jume Maikudin ya shigo yana hade rai. Shi yafi kowa
sanin babban dalilinsa na kin zuwansu garin amma bazai iya fadawa kowa ba. Yaran
dama baya sakar musu fuska. Sai dai suna da kyakkyawar mu'amala da 'yan uwansu wato
jikokin gidan. Satinsu daya suka juya Jume kamar a bar mata su. Babbar damuwarta
shine rashin kowa daga bangaren Innar Zayyan wanda Jume tace har yau itama tana
zuba idanu ne.
Maikudi bai sami sukuni ba sai da suka bar garin. Sirrika biyu yake boyewa Mairama
saboda mugunta da kuma son kai irin na dan Adam.
Na farko dai wata shida da rasuwar Zayyan kawunsa Sidi yazo bisa shawarar 'yan uwa.
Ashe ya tura musu wasika da zai tafi ta tasha. Sidi yazo gari Jume da matan gidan
sun tafi Tureta biki. Maikudi kawai ya samu su Badaru basa gida. Lokacin yana tsaka
da jin haushin rashin mutumcin Malamijo kuma yasan idan mutanen nan suka san da
zamansu ba karamin alheri zasu rinka musu ba. Wanda zai koma jikin Malamijo a
karshe. Saboda haka ya matso hawaye ya sanar dashi mutuwar Zayyan da kuma hatsarin
da su Mairama suka yi ita da 'yarta suka rasu gabadaya. Wannan shine dalilin da
yasa aka dena ji daga garesu.
Abu na biyu kuma shine aike duk karshen wata daga kasar Germany wanda Retired Major
Mustapha bai taba dena yi ba tun bayan samun lafiyarsa da aiki a can din kusan
shekaru hudu. Kudi ne yake turowa ta hanyar wani soja da yake karkashinsa a da kuma
ya yarda dashi. Wannan mutumi duk wata Maikudi yasan ranar da yake zuwa har
barikinsu ya karbi kudin da suke mazaunin kudin makarantar Radhiya da kuma tallafi
ga Mairama. Soke abinsa yake ga gidan Kano ya saka 'yan haya. A takaice dai yana ta
gina kansa don ya sayi fili a cikin Sakkwato yana ta makara gini da kudin marayu.
**********
Mairama ta koma ta tarar da babbar kura. Malamijo ya karbi sadakinta daga hannun
Alh Indararo an saka biki wata uku kafin ya gama yi mata gyaran gida. Ta shiga
matsanancin tashin hankali har Nene Marka tazo amma kowa cewa yake tayi auren ko
zata sami hutu itama.
Tayi kukan, tayi haukan duk a banza bata da mai tsaya mata. A bangare daya kuma
duniyar Salame ta juye. Mutum kamar Alh Indararo ace yana son mace kakarta ta yanke
saka. Shine wannan karon ma irin abinda take muradi ya tafi ga Mairama. Rantsuwa
tayi cewa hakan bazata sake sabuwa ba.
Gidan Malaminta da suka saba kashewa kudi domin a dawo mata da Salisu taje. Bayan
dogon bugun kasa yace ta saka ranta a inuwa akwai rabo yana iya gani tsakaninta da
Alh Indararo amma sai an kawar da Mairama.
"Malam rufa min asiri kanwata ce fa. Ni dai bazan iya kasheta ba"
Gemunsa na munafurci da suke cutar jama'a dashi ya ja yana murmushi "waye yace sai
kin kasheta. Idan kina so nakasa kawai zamu dora mata wadda zata saka ya fasa."
Kwana biyu tana tunani kafin ta hasko me take son ayiwa Mairama. Magani ya bata ta
wuce gida ta saka a inda ya umarceta.
Kwana uku a tsakani kuwa wata safiyar lahadi Mairama ta tashi bata gani sai dususu
komai yayi hazo. Cikin maganin digawarta na ido Salame ta zuba mata maganin. Cikin
wata guda idanun Mairama sai suna. Duk abinda ya rage mata ya kare a neman maganin
ciwon idon amma asibiti basa ganin komai.
Kuka ashe bai kare mata ba. Bata gane kowa sai duhun inuwa. Tashi guda Radhiya ta
koma idanunta madogararta. Alh Indararo ya canja sheka bazai iya auran musaka ba
Salame har ta tare abinta.
Karatun yaran ya tsaya yau da gobe Malamijo ya gaji da dan mikawar da yake yi. A
bisa dole ta hakura da karatun Radhiya da Emzee. Tana kuka kan kuka amma mahaifinta
bazai iya kulawa da ita ba bare 'ya'ya, iyakarsa dasu shine za'a dafa abincin gidan
dasu. Radhiya ta fara hankali tasan cewa mahaifiyarta tana bukatarta shiyasa bata
fita idan ba aike ba. Emzee kuwa dama daddawar daka ne shiyasa bata hadu da
matsalar ace suna yawace-yawace ba. Rayuwar Mairama matar soja ta cika da
wahalhalun da suka sa take bukatar a dube ta.
***********
Maza ne uku a karkashin bishiyar darbejiya wadda ta yiwa wurin yalwatacciyar inuwa.
Daya yana zaune akan kujera sauran biyun kuma suna gabansa ne kana gani kasan mai
mulki ne da wadanda yake mulka.
Gyaran murya na kan kujerar yayi suka dawo da hankula gareshi "Mal Gide"
"Ranka ya dade" wanda yafi manyanta cikinsu ya amsa.
"Habubakari"
"Allah Yaja zamaninka" na biyun ya amsa.
Dan murmushi yayi domin kuwa su biyun yayun matarsa ne Innawuro.
"Mal Gide kaine babba saboda haka ta kanka zan fara. Ba tare da jan zance ba magana
ce akan sakacinku da zumunci saboda wani abu can da ya faru shekarun baya"
Mal Gide ya hadiyi yawu yana kallon Habubakari shima kuma yayan nasa yake kallo.
Ardo Barkindo ya dan duku da kansa kadan daga kan kujerar "wannan zumuncin da kuka
banzatar ina mai tabbatar muku sai Allah Ya tambayeku akansa. Kune kuka ci bashi
kamar yadda naji a bisa dole. Dole tasa kuka biya bashin da kanwarku sai gashi daga
karshe ya sakota ya bukaci kudinsa ko. 'Yar uwarku ta sadaukar da farincikinta
saboda ku amma shekaru sun tasanmu talatin marainiyar da ta bari baku san cinta ba
baku san shanta ba"
Habubakar wanda abin shima ya dame shi amma tsoron Gide ya hana shi furtawa ya
sharce kwalla "Ardo zamu gyara, wallahi nima abin ya dameni. Ali bashi da kirki ko
kadan. Allah ma yasa tana da rai yarinyar nan"
"Yarinya da ranta amma tana cikin mawuyacin hali. Yanzu da na kiraku dama sanar
daku zanyi cewa zan daukota ko dan kwanciyar hankalin Innawuro"
Nan ya sanar dasu komai game da Mairama kamar yadda yaji daga bakin mijin Nene
Marka bayan ya soma binciken nemota.
Mal Gide sai hawaye. Bakar zuciya tasa ya umarci 'yan uwansa da babu su babu
zuri'ar Malamijo, ciki kuwa harda 'ya daya tilo ga kanwarsa Mairo wadda ya yiwa
auren dole da Malamijo.
"Da kaina zanje in daukota da yaran su zauna a gidana Zan gyara wannan abu duka
laifina ne"
Ardo Barkindo ya kada kai yana murmushi "haba dai Gide ai bazamu yi haka da kai ba.
Yarinya a wurin babarta zata zauna. Duk na gama wahalar neman sannan kace zaka
daukota ka kwashe ladan"
Murmushi ya maida masa "duk yadda kace ranka ya dade, kamar yaushe zamu tafi?"
"Jibi in sha Allahu. Ina so ku tattaro kan 'ya'yanku har na gidan aure da suke
rugar nan da kewaye maza da mata. So nake muje mu cika musu ido mu wanke gorin
dangin uwa da na tabbatar ansha yi mata."
Sun tashi da fara'a kowa yana jin kamar an sauke masa nauyi daga zuciya. Ardo
Barkindo ya nisa yana tunanin ya boye musu makantar Mairama saboda yasan duka
hankulansu zasu tashi. Idan sun je zasu ganewa idanunsu. Ko matarsa ya kasa fadawa
ita da ta uzzura masa akan neman 'yar yayarta da take bi.
Mal Gide kuwa har ya isa gida yana tunanin da yardar Allah zasu kula da ita bakin
iyawarsu su daidaita tsohuwar baraka. Tunawa yayi da umarnin Ardo ya tura guda
cikin 'ya'yansa da yaje ya fara sanar da yayyensa cewa suna da zuwa Kano jibi daga
rugarsu wadda take cikin karamar hukumar Giade a jihar Bauchin Yakubu."Ahayye
nanaye, wallahi mutum ya yi min ba kyalewa zanyi ba don kaji in gaya maka yaro"
tafa hannuwa tayi sannan ta rike kugu tana girgiza jiki a dole ranta ne a bace.
Abokin fadan nata wani sangamemen yaro ne don shima akwai kuruciya sai girman jiki.
"An fada din" yace sannan ya cigaba da wakar da ta hadasu fada "Malamijo Malamijo
tsolon rake. Ga kwadayi ga rowa yaki yin gaba"
Wani kukan kura Radhiya tayi ta dire a gabansa ta nuna kasa "in ba tsoro ba
dangwali" ta nuna masa kasar wurin. Dabi'arsu kenan 'yan makarantar wadda ta
kasance firamare ta gwamnati idan ka yarda zaku dambace to kowa ya dangwali kasa.
Daga nan sai a kaure karfinka ya kwace ka.
Dukawa yayi zai dangwala ga tsirarun abokansu da basu bar makarantar da wuri ba sun
tsaya kallo. Sai da ta daidaici yayi kasa da fuskar nan kawai ta dauke shi da mari
ta ranta a na kare. Kai tsaye staffroom ta wuce inda malamai suke wurin Umminta.
Tana shiga ta cukwikuye jikin Mairama tana kuka wai su Danmama ne suka dake ta.
Tahowa suka yi Danmama ne a gaba kayansa duk kura saboda faduwar da yayi garin bin
Radhiya. Kofar staffroom din taje ta saka su kneeldown har Radhiya sannan ta nemi
jin ba'asi. Sai aka rasa me fada mata. Duk fitsarar Danmama yasan da kunya dai ya
maimaita wakar a gabanta. Radhiya dama ko me zata yi mata bazata fada ba don kada
ranta ya baci.
Daga bayanta taji wani malami yace "Anti barni dasu kiyi tafiyarki gida. Idan na
gama zanesu zan taho da wannan mai kunnen kashin"
Mairama ta gyara zaman farin gilashinta tayi dan murmushinta da ta saba yanzu da
wuya kake ganin bacin ranta ta koma ta dauko 'yan tarkacenta tayi hanyar fita daga
makarantar don dama an riga an tashi. Daga karkashin wata katuwar bishiyar marke
take hango yara suna 'yan wasanninsu. Idanunta suka sauka akan Emzee yana zaune
yayi shiru yadda ya saba yana jiranta.
"Karami zo mu tafi" tace da dan karfi don ta kula bai ganta ba sai gashi ya taso da
saurinsa.
Kayan hannunta zai karba tace ya barsu su tafi "Ummi ina Adda?"
"Kyale wannan yau ma fada tayi"
Sunyi gaba wasu 'yan ajinsu suka rinka kwalo masa kira suna Emzee sai an dawo hutu.
Wannan suna da Mairama ta hakura da yakar sa dole shine sunan da yabi Muhammad
Zayyan har gida. Mutane kalilan ke kiransa Zayyan ko Karami kamar yadda take fada.
Yace wani malami da suka yi a firamare two ne yake kiransa MZ Tureta. Shikenan abu
na yara ya koma Emzee.
A makaranta kuma gurfane gaban Uncle Idris su Radhiya ne da Danmama. Sai da Mairama
ta tafi Radhiya ta fada masa sunan da suke kiran kakanta dashi. Uncle Idris ya
tabbatar zasu aikata yayi musu bulala biyar biyar mai zafi da dorinarsa ita kuma
biyu ladan biye musu. A waje ta jira shi shima ya dauko kayansa tunda yau take
ranar hutu suka tafi yana mata nasihar fada da maza.
A cikin shekarun da suka gabata rayuwar Mairama sai dai godiyar Allah. Zamanta a
gidan Malamijo tamkar zaman gidan haya ne. Iyakar gaskiyarsa shi nauyi ya masa yawa
fitar da kudi kamar ana mintsininsa ne. Ya kara kudin cefane da kyar da sudin goshi
amma daga nan fa ko me mutum ke bukata mace ko namiji cikin iyalinsa sai dai su
nemawa kansu.
Abu na farko da Mairama ta fara yi shine adana kudaden gadonsu a ranta tana
tanadinsu ne domin karatun yaran a gaba. Sai da ta fuskanci sabulun wanka wannan
idan bazata saya ba sai dai su watsa ruwa kawai ta fara taba kudin. A hankali kudi
suka fara samun gibi dole ta fara neman sana'a. Tashin farko ta saro zobo tunda ta
tsira da firig dinta ta soma yin zobo da lamurje na saidawa. TV da bidiyo da duka
kayan gadonta banda katifar da ta ajiye kusu suke kwana da yaran duka suma saidawa
tayi don ta kara jari. Allah Ya dubi halin da suke ciki ya buda mata kasuwa tana
ciniki sosai.
Salame tana gefe kullum tana yawo tsakanin nan gidan nasu da wurin Ta Madina wadda
da fari ta dauki fushi mai tsanani da ita sakamakon mutuwar aurenta. Har gida suka
tura aka nemo Salisu ko zai maidata yace idan ta sami miji tayi aure shima auren
zaiyi.
Zaman gaba, bakinciki da hassada ta dauka tana yi da Mairama. Kayan dakinta Ta
Madina ta sayar ne ana bin malamai domin karkato hankalin Salisu. Shiya janyo ita
bata da komai gashi jiki ya saba da jindadi an manta wanki, shara da wanke-wanke.
Wahalar gidansu a yanzu har tafi ta da tsanani ko don zawarci suke oho. Hankalin
Mairama yana kan inganta rayuwar 'ya'yanta, na Salame yana kan me zata yi ta kere
Mairama ko ta hanata cigaba. 'Ya'yanta musamman Radhiya sun tsole mata ido. Abu
kadan ne zata yi ta kai mata hannu da duka amma Mairama bata taba tankawa ba.
Lokuta da dama wurin Yadikko suke zama ko Hajjo idan 'yan mutumcin suna kusa.
Wata rana ta gama zobonta da lamurje ta kukkulle a leda santana suna cikin wani
katon baho a nan bakin famfon tsakar gidan inda take aikinta ta tashi ta tafi jawo
ruwa a rijiya zata wanke wurin. Salame tana ta fakonta don dama ta gane yanayin
aikin nata. Idan ta gama kullewa sai ta janyo ruwa ta wanke wurin sannan ta dauka
ta kai firig dinta ta jera. Su kan wuni da wuta amma da wuya ta kwana.
Tafasasshen ruwan zafi Salame ta taho dashi a bokiti tayi daurin kirji kamar mai
niyar shiga wanka sai da tazo daidai bakin bahon da kayan Mairama suke ta sheka
musu ruwan nan. Ledojin dole suka yi laushi sunyi tsamo tsamo babu dadin tabawa.
Salati ta soma yi wai wucewa zata yi ta sirka ruwan wankanta don ta ga kamar famfon
wurin yana diga an kawo ruwa. Mairama ci gaba tayi da diban ruwanta sai da ta ciko
bokiti tana zuwa ta ajiye shi sannan ta cira hannu ta kwashe Salame da mari mai
gigitarwa don tana kallon yadda komai ya faru.
Ihu ta kurma gidan da suke neman abin gani kuwa aka fara fitowa bawa ido abinci.
"Ni kika mara Mairama?"
Rai a bace Mairama tace "ko zaki rama ne?"
"Kan bala'i, billahillazi baki mari banza ba sai na rama"
"Gaki ga kumatun Adda Salame. Na gaji da wannan abubuwan da kika tsira tun kafin
muyi aure har yanzu ana abu daya. Kece dukan min yara, yada min habaici da bakaken
maganganu duk akan me? Me na tsare miki?"
"Dole kice haka mana tunda kin rabani da wanda nake so"
Yadikko na jin haka ta kora yaran gabadaya tace su shiga dakinta. Hajjo ba kunya ta
bisu don jin ba'asi. Salame kasa karasa bayanin tayi don tasan ita ce da jin kunya.
Tabarmar kunya ta nade da hauka wai Mairama tana yi mata gani gani saboda ta fara
rike kudi.
Da daddare da Malamijo ya dawo Yadikko ta bashi shawarar ya raba musu daki mana.
"Babu wadda ta bani ko asi domin ginin gidan saboda haka idan zasu cinye kawunansu
ne ma