Showing 78001 words to 81000 words out of 258256 words

Chapter 27 - Bahagon Rayuwa by Zainab Idris Makawa Seenabu

dani ashe ciwo in ba a dace da magani ba sai ai ta
wahala dashi.
Don yanzu na rage yawa jin abinda nake ji a jiki na so sai sannu a hankali nake
jin sauki yana shiga na.
Kwana biyar suka sallamay mu daga asibitin, har lokacin muna asibitin da yaya
Saadu da yaya sani.
Sun bani magani amin register zan dunga zuwa ansan magani a wurin su tare da
fada min mata kan da zan bi don kare kaina da sauran alumma da nake zama da su.
Aka bamu sallama na dawo gida da dan karfin jiki na sai da yaya ya sawo min
abubuwan bukata na rayuwa yai muna sallama ana ta yi mashi godiya ya kama hanya.
Yan gidan mu na dan ga dan canji a wurin su yaran mama sun rage tsanar da suke
min amma dai suna kyamana don in na taba abu sai an wake ko a yar a bayan idona.
Kauna tace ta fada min haka sai dai nai murmushi kawai na ware kayan amfanina a
gidan ban amfani da kayan kowa har da na su ummi na don na nema masu mafita.
Da sannu ina warware wa na fara harkan kasuwanci na da mutane da farko suna
kyamar saye daga baya kuma suka fara saya.

********* ********* *********
Yaya Saadu daya bar wurin mu gida ya koma direct tun da ya iso jikin su ya basu
cewa bai cikin dadin rai.
Sai da ya huta yai wanka yadan taba abinci kadan ya tashi ya fice gidan yaya
Ahmed ya nufa.
Ba kalman dake mai yawo arai sai da ya shigo dakin ummi ina kwance na dago nace
dashi yaya ya Ahmed ya cuce ni
Ya illanta min rayuwa ya kashe ni da yarinta na ya mai dani abin tsoro a cikin
yan uwana da gari sai ya runtse idanuwan shi.
Yai sallama yana ciki kwance ya taso da kyat ya bude kofan gida yaya saadu ya
shigo ciki yana mai wani irin kallo.
Zama yayi yai shiru ba tare da yai magana ba shima wuri ya samu ya zauna yana
kallon shi don yasan magana ya kawa shi .
Don tun da na bar gidan ba sake zuwa gidan ba sai yau da yazo ya tunkare shi
akan magana na.
Ya dan dago ya gyara zaman shi dakyau baiyi magana ba saida ya dan furzo da iska
daga bakin shi ya numfasa yace.
Kana da labarin Safiya bata da lafiya har ciwon yai tsanani sai da naje na kaita
asibiti, yace dashi ban sani ba, banda labarin ta tun tafiyan ta inbada ta haihu
kazo kafada muna ba, sai yace dashi
Ahmed ka cuci Safiya ka illanta rayuwan karaman yarinya a banza saboda son kai
irin nata ka zuba mata kanjamau tana ta wahala a rayuwan ta.
Ahmed din yai mai wani kallo na tambaya sai yace dashi na illanta ta kamar yaya ?
Yace kasan Safiya tana dauke da HIV kuma kaika saka mata shi don dai kai kafi
kowa sanin kamilar yarinya ce ita.
Ahmed din yace tasan dai inda ta samo abinta don dai ni banda komai normal nake
kowa ya sani.
Saadu yai saurin cewa normal kake kamar yaya aiko makaho ya lalaba yasan may
kake ciki.
Sai yace dashi sheri zakai min ko may ?
Babu sheri anan .
Don mummy da mahaifin safiya sunyi kuskuren aure maka kamilar yarinya kamar safiya
don sun san halinka na boye suka aure maka ita hakana.
In ma shi mahaifin nata bai sani ba ita mummy mu ta sani saidai ta boye masu ne.
Ahmed ba yadda ban yi da kai ba ns baka shawara ka gyara rayuwan ka ka nisan ta
kanka da fasikanci.
Ba abinda ya zama ma dan adam dole may kake nema gun mace kai da Allah ya hore ma
mace yarinya karama a gida.
Sai da na fada ma wanan matar da ka aje a gida ba alheri bace gare ka amma kaki
ji yanzu gata ta sa ka cuci yar mutane.
Ya dafe kai gami da lumshe idanu yana tunane a ran shi yana hango irin wahalan da
nake yi da ciwon a ranshi.
Ya hango surana da muryana da irin karfin halin da nake dashi wurin turzawa sai
kuma muryana idan ina son abu da tsabta na.
A take ya ji jikin shi ya mace wani na dama da tsoro ya shige shi amma sai ya
dake yace wa kanin nashi.
Wai may ya damay ka da nine rayuwan ka ko nawa kuje can kai da ita ku nemi inda
ta kwaso cutan ta.
Please ka rabu dani don Allah da zancen wata safiya can kwakwalwata yana son hutu
dan Allah kazo min da wani zancen ka na bazanza.
Yace okay haka kace ya mike ya fita zuciyar shi kamar wuta yake jin shi ba abinda
yake tunawa sai halin da ya barni ciki.
Gidan su ya koma inda ya samu mahaifiyarsu da zancen, tun shigowan shi ta sha
jinin jikin ta don tasan da abinda ke damun shi.
Sai daya zauna take cewa dashi ina kafito ne aikai ma abin kari baka nan ka
fita.
Ya nisa yace da ita daga wurin Ahmed nake mummy kin san Ahmed ya cuci yarinyar
nan safiya a rayuwan ta .
Tace may ya faru kuma da Safiya din zancen wai har yanzu bai kare ba a gare ka
kana bin dan uwanka da maganan ta rayukan ku na baci ga banza kasan fa yace bai mai
da ita.
Mummy yazu wake batun komawan ta bayan ya illanta ma yarinyar mutane rayuwa har
abada.
Wani kallo taimai nason jin ba a sin maganan shi yace Safiya fa HIV ne gare ta
kuma ba kowa ya samata ba shine.
Innallilahi ta furta da karfi tace H may yanzu kana nufin har shi Ahmed din yana
dashi komay ?
Yace ai yasan yana dashi mugu shiyasa ya sake masu ya don kar asirin shi ya tonu.
Hannu ta fara tafawa tana salalami tana cewa wai ta shiga uku ta lalace Ahmed na
da kanjamau ko may ?
Yace mummy Ahmed kawai kike ji mawa ita diyan mutane da kuka cuta fa ita ba abin
tausayawa bane ?
Sai ta kama inda inda tana cewa ai dukkan su abin tausayawa ne itama ai dole a
tausaya mata.
Yace mummy dake da mahaifin yarinyar nan kuna da kamisho cikin ciwon yarinyar
nan.
Amma shi mahaifin da yasan kun cuce ta ai kuka yake kuma yana nadaman abinda kuka
kulla sai dai ko kadan bai kufulece kiba.
Amma ke gaki yanzu dan ki kawai kika sani kika damu da damuwar shi ita ko ko
oho ?
Idan zaki kirashi ki masa magana yaje ya duba diyar mutane tun wuri ki masa.
Ahmed din bai shigo ba saida yamma ya shigo rai a bace shi aladole an bata mashi
rai.
Nan ya zauna da uwar ta dauko mai zancen da cewa abinda naji da gaske ne ko karya
ne yazo ya fada min.
Nan ya shiga fada wai Saadu na binshi da mugun nufi har yana lakaka mashi mugun
ciwo.
Tai ajiya zuciya tace yanzu naji magana amma yazo ya tayar min da hankali ga
banza ya hanani sukuni a rayuwana duk yinin yau ko ruwa ban sha ba.
Mummy kazafi yake min ta san ida ta dauko cutan ta can ni bani da masaniya akan
haka.
Uwar ta hau ta yarda da maganan shi nan ta shika fadin mugun zance akaina da
mahaifana yana tayata fadi.
Sun yanke yiwa yaya Saadu kaca kaca kan maganan da yake so ya dora wa dan uwan
nashi wai yana son ya bata mashi suna ga banza.
Ya shigo sunyi kaca kaca dashi a gaban mahaifiyar tasu tana tayashi zagin shi
yace dasu OK haka kukace .
Time will soon come da gaskiya zata bayyana kan ta indai ana boyon komai ba a
boyon ciwo ai muje zuwa ni daku.
Macucin banza da wofi kawai kawai ka cuci yar mutane kazo kana wani kamay kamay
azzalumi banza da wofi sai Allah ya tona maka asiri ai.
Yace dai naji kuje can ku nemi wanda yasa mata cuta idan ma kaine ka fito fili
kafadi yafi don naga zakewan ka yayi yawa akan ta dama.
Wani irin shock ya kama shi ta juyo yana duban dan uwan da mamaki sai kuma yai
murmushi yace ni ba dan akuya bane irin ka.
Ina dai kokarin sauke hakkin da kai ka kasa saukewa ne akan ta amma baku ganewa
sai lokacin ku gane gaskiya inyayi.
Ya fice ya basu wuri bai kara shigowa gidan ba har ya tafi bai koma wurin aikin
shi ba sai da yaje gidan maman biyu ya sanar da ita halin da nake ciki.
Da taji hankalin ta ya tashi sosai ya kwantar mata da hankali da cewa ya kaini
asibiti yanzu ina samun sauki an daiyi arziki cutan baiyi nisa sosai ba aka tare
shi.
Ranan haka ta wuni a cikin bacin rai tana ta tsine ma Ahmed din da uwar shi ta ma
kasa kirana don in ta kirani ma may zata fada min banda karin tashin hankali.
Sai dai ta kasa daurewa bayan kwana biyu ina zaune daki da ummi wayana yai kara
na dauka na ga itace take kirana.
Na dauka tare da fadin Anty kwana biyu kina a raina ban samu kiran ki ba banda
lafiya ne.
Asanyaye tace safiya naji komai yayan ki yazo nan ya fada min halin da kike ciki
Allah ubangiji ya isar maki.
Sai na kama kuka tace bari kuka haka Allah ya kaddara da rayuwanki Allah ya nufe
ki da rayuwan BAHAGGON AURE.
Komai da bawa ya gani yana cikin littafin sa rubuttace ne ga ubangiji dama sai
dai muyi fatan Allah ya baki lafiya.
Nace amin anty tace ki kwantar da hankalin ki ki sha magani kada kiyi wasa da sha
magani sosai don kada cutar yayi galaba a kanki.
Nan nake jin yadda yaya Saadu suka kwashe da yaya Ahmed din da uwar su tace min
barsu ai Allah ba azalumin kowa bane.
Da sannu gaskiya zatai halinta in sun ce su mahainta ne ciwo ai ba a boyon sa
shi zai baiyana kasa agani watarana.
Ta dade tana lalashina ina kuka tace ina ummi nace gata a kusa dani tace inba
ummi waya su gaisa.
Nabata wayan suka gaisa tai mata jajen akan abinda ke faruwa tare da kwantar mata
da hankalin ta takumace duk lokacin da muke da damuwa mu tutube ta zata taimaka
muna.
Nai sallama da ita har take tambaya na sana, a ta nace yana nan ina yi tace to
karki daina shine zai tallafa maki kina samun dan kudin sayen abinda zai gina maki
jiki kiji ko nace na gode kuka ne yaci karfina na kasa magana na kashe wayan ina
tunane a raina.
Bayan mun gama wayan na dade ina kuka ina tunane a raina karshe na hakkura na
kyale na barwa Allah komai shi zai mun mafita da yardan ubangiji.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:11 PM - Ummi Tandama: BAHAGGON , , , , , , , , , ,


2️⃣
9️⃣

YAR UWA NOVEL DIN NAN NA KUDINE IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU
PLEASE, , , , ,



Wurin motar muka nufa gaba dayan mu saadatu na kwace a ciki sheme kamar bata
numfashi kuka muka saka a lokaci daya.
Dayan dan sanda ke fadi ba kuka zakuyi ba ayi niya akaita asibiti tun lokaci bai
kure ba a take baba da yaya sani suka fada motar da inna.
Suka nufi asibiti da ita har lokacin mu ba mu san may ya samay taba asuban fari
baba ya dawo gida rai a bace.
Da mukaji shigowan shi lokacin mun tashi muka firfito waje mama ne ke cewa malam
lafiya may ya faru da Saaden ne ?
Cikin takaici yake fadin fyade akai mata wai kuma bata san ko su waye ba tadai ce
sunkan zo cin kasuwa su sai sana ar ta.
Kowa ya dafe kirji da firgici a cikin mu ta sake tambayan shi da ta farfado dai
ko yace a takaice da ta falka yanzu sai dai bata san inda take ba.
Nan ya shige ya barmu a cikin tashin hankali ba kwanta ba da mukai sallah cikin
kayan abinci na na diba na hada masu abin karyawa.
Na gama da wuri muka isa asibitin tana kwance sharkaf kamar bata da rai Inna na
zaune a gefen ta cikin tashin hankali.
Munyi mata sannu da yaya mai jikin tace da sauki na bata abinda nazo dashi nace
su mama suna nan tafe.
Maganin da likita ya rubuta ake neman kudin saye baba yace baida shi inna kuma
tace dama dan abinda ke gare ta ne nan ta juya dashi sukai sana a.
Na bude post dina na kirga kudin na bayar sai lokacin aka sawo magani da ruwan da
za a karamata.
Anyi mata allurai da sauran abinda ya dace a taimaka mata dashi bayan kamar awa
daya ta farfado da kuwan wayyo inna zasu kashe ni.
Tana fisge fisge nan dai muka taru muka taushe ta nurse tazo ta kara ba ta allura
sai aka samu tayi barci.
Ranan dai asibiti muka wuni ba dadi kafin wani lokaci labari yabi gari mutane sai
shigowa suke yi dubata.
Suna asbitin kafin a sallamota sai ga yan gidan mijin da zata aura wai a basu
kayan su yace ya fasa dama itace ta biyu zata shiga.
Wani sabon tashin hankali kuma nan suka shiga hayaniya da su mama tace aiko baku
da imani kwa tsaya har a sallameta dai ko koma may ye sai ayi shi hankali kwance.
Nan dai aka samu suka tafi suna bakaken magana wai dama ai shi yaji yagani a
kanta ina ba haka ba me zaiyi da ita ma.
Andai samu an lalaba su suka tafi baba ya shigo gidan ake mayar mashi ranshi ya
baci yace ai sai su bari inda ta dawo ita data karbi kayan su sai ta mayar masu da
abinsu.
Inna na can labari ya samay ta nan ta sa hannu akai tana kuka wai so suke su
tozarta ta in bashi ba ai wanan abindaya faru da yar ta kaddara ne kwai.
Ji fa inna na kalleta a raina nace ashe tasan akwai kaddara shine ni taki yarda
da nawa kaddaran da yazo min.
Na yar tane abin yarda ke nan mu dai hakkuri muka bata kawai muka bar dakin muka
koma waje muka zauna.
Washe gari aka sallamo su suka dawo gida an basu wata uku su koma ai mata awon
ciki dana HIV nan hankalin inna ya sake tashi sosai tana kuka tana fasin Alah ya
tsine ma wa yanda sukaiwa yarta fyade.
Da yamma bayan sun dawo gida tana cikin jimamay maganan likita sai ga ya gidan
mijin na saade sun dawo wai sun samu labarin an sallamata ta dawo gida shine suka
zo karban kayan su.
Nan suka hau da inna tace baza ta bayar ba aiba ita tace ta fasa ba don haka bata
yarda shi mijin yace bai yi ba sai dai in sherin yan uwan shine.
Suka tafi basu gane komai ba nan suka barta ta na halakatai a tsakar gida wai
basu da imani yarinya na fama da abinda ya samay ta zasu zo masu da wani fitina
kuma.
Mu dai muna daki muna sauraren ta sai baba ne ya shigo yace da ita don may bazata
basu kayan su ba tun da sunce sun fasa.
Nan ta shiga kamay kamay Ummi tace dani wasu kaya kayan da ta sayar wasu kuma
yarinya ta sa ajikin ta.
Nace ashe akwai cakwakiya don naga mutanen basu da alaman mutunci tare dasu.
Ummi tace na dai kallo kawai ai mun yi imani da mukai mata jajen abinda ya faru
in wasu ne aiko kallo bata ushesu ba.
Da itace ba abin da zai sa ta kalle mu dama haka Allah yake ai yanzu in tana da
imani tayi ai ta daina aibanta kin da takeyi a gidan.
Murmushin takaici nayi nace badai inna ba ai laifi tudu ne katake naka ka hango
na wani watarama kiji tayi min fade in halin ta ya tashi.
Ummi tace dako tajini don yanzu nima Allah ya bani abin fada mata ai kowa ya ji
da nasa abin fade.
Kwana biyu Saade bata ko iya fito tsakar gida koda yaushe tana daki ranan mukaji
Inna na mata fada wai ta fito ta kunkumay acikin daki.
Mai ciwo ma ta fito tana walawa sai ita zata tsiri zaman daki muna jin ta ummi
tace anzo wurin .
Sai ko ummi tai wuf tafita waje tace may zaki fada min bayan Allah ya nuna maki
bakin halin ki tun a nan duniya.
Ai ni gara tawa ansan gidan miji ta kwaso shi ke ko fa daba a ko san suwaye sukai
mata kaca kaca ba a gari.
Baba yana jin sun fara ya fito tare da daka masu tsawa yace ke Rakiya yaushe ne
zaki hankali yanzu duk wanan isharan da Allah ya gwada maki bai isheki ba sai kin
tsaya jan magana.
Sai cewa Inna tayi Allah ne ya nufe ta da ganin haka a rayuwan ta kuma ba zai
zama abin fade ba ai.
Yace ita ko itace ta saya da kudin ta ko ke in kina da kunya har zaki kawo irin
wanan magana haka wanan abin bai isheki ba.
Ko tafiya nake na koma ana gwada ni a gari banda sukuni a cikin mutane gida kuma
babu dadi.
Wanan karon bazan lamunce ki ba duk kika haddasa min fitina a gida zan dauki
mata mumuna akan ki ne.
Jin abin daya ambata yasa tai sanyi don ta zaburo wa ummina sosai kamar zata
cinye ta danya ya kara da fadin .
Ke wata irin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login