Showing 141001 words to 144000 words out of 258256 words

Chapter 48 - Bahagon Rayuwa by Zainab Idris Makawa Seenabu

da hankali anan har in kasa yin aiki aiwatar da ayyukan
dake gaba anan.
Shiru nayi ina sauraren maganan shi karshe na kashe waya ina mai bin lafiyan gado
na tunane kuma yazo ya lulube a wirin.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:12 PM - Ummi Tandama: BAHAGGON , , , , , , , , ,


5️⃣0️⃣5️⃣
5️⃣
🧕🏿 0️⃣0️⃣5️⃣


NOVEL DINA NA KUDI NE NA FADA MAKI TUN FARKO INDAN KIN FITAR BAN YAFE MAKI
BA IDAN KIN KARANTA BAKI BIYA BA ALLAH YA ISAR MIN.


Yanzu ni yar uwa may zace dake tunda tun farko na fada maki kada ki fitar
min ai kadan kika gani ga wanda bai tsoran Allah .
Nace tun farko kada ki fitar min da novel kin dauka kalman Allah ya isa wasa ne
sai da abu ya cika dake zaki dawo kina na yafe maki.
Baki san ni ba baki kuma san inda na fito ba ina dai novel kina karantawa nace ga
yadda nake son abina baji ba yanzu kizo min da wani magana ban damu ba tunda tun
farko na fitar maku da hakkina na fada maku ban son a fitar min ke da sauran kadan
kuka gani muje zuwa indai nice kullun ya diga bibiyar ki ke nan ai tunda kin zabi
kalman Allah ya isa to ya isar min din sai may kuma ni na gama magana na ai tun
shekaran jiya ku kaka rage da raddin ubangiji kuma.
Tun safe ban tashi ba ina kwance kamar mara lafiya nake jin kaina ko abinci bam
iya fita na nemo ba din ban majin cin komai a raina.
Dawowan su anty da yara danaji hayaniyar su yasa ni mikewa na shiga ban daki
wanka nayi na fito na shirya don ina fashin sallah a lokacin.
Bayan na gama shiri ne na nufi part din anty don in mata sannu da zuwa a hankali
nake hawa steps din na kawo daidai window din ta dake bude naji ta ambaci suna na
har zan wuce sai na tsamaci ita da wani ne a dakin sai daga baya na gane waya
takeyi ashe.
Naji ta sake fadin anty uwa na fada maki na Safiya mai sauki ne nasan abinda zan
fada mata gamay da sulaiman din ta fahince ni.
Shidai sulaiman din ne yanzu shawo kanshi abune mawuyaci da sauki don ban taba
zaton zai mutu ga son yarinyar ba haka.
Shiru tayi tana sauraren maganan anty uwa din sai naji tace gaskiya anty ni
safiya bata taba yi min komai ba harda zan mata korar kare a gidana.
Don yarinya nada hali mai kyau wallahi don duk tafi min wayan nan kattan bazan
dana tara Fati da Faiza.
Ke dai ki bari mubi abin sannu dan Allah a samu a rabu lafiya da ita ba tare da
ta fahinci komai ba.
Anty uwan ke magana ta tsaya tana sauraren ta sai naji tace ba haka bane Anty
uwa wallahi wallahi sam ban kawo Nafisa a raina in ba don kinyi magana ba yanzu ai
mai sauki ne tunda ba aure aka daura masu ba dashi.
Anty uwa din ke magana sai naji anty tace gaskiya ne zaman ta haka a gida kan
baida amfana gaskiya zan san duk yadda zan yi ya koma ga Nafisan batare da an samu
matsala ba.
Shiru tayi anty uwana magana sai naji anty din tace Safiya bata da matsala zan
san yadda na raba ta da son shi ai don ba wani wayewa tayi ba sosai.
Naji tace to sai kin shigo din next week ina expecting din zuwan ku din ai kafin
nan ma tun yanzu na fara aiwatar da shirina a kan su ko may tace mata naji tace ba
hakana bane Allah anty yarinya ta bani tausayi ne don wahalan da tasha tun farko a
gidan mijin ta.
Anty uwa din ke magana ta tsaya sauraren ta alokacin na yo baya baya tare da dafe
bakina dake shirin sake kuka asirina ya tuno gaida ita da banyi ba ke nan na dawo
daki na.
Sai ranan naga amfanin rashin zaman da su fati basuyi a falo don ko yau yai min
rana sosai inba don haka ba da wani yana iya ganina a cikin su.
Ina shiga daki na rufe tare da fadawa kan gado na sake kuka mai tsuma zuciyan
mai saurare na ina kiran sunan Allah da karfi nace ni Safiya wanan irin bahagon
rayuwa da nake gani damay yai kama haka duka duka shekarana 21 amma gashi ina ta
haduwa da kaddarorin rayuwan duniya.
Yanzu idan sulaiman ya kubbace min ina zan sa kaina ko sherin inna ya isheni a
gidan mu ai da mutanen garin.
Zuciyana taban amsa da fadin ki rike Allah don yana sane dake mai hakkuri baya
tabewa a duniya.
Haka yasa naji wani kwarin gwaiwa yazo min sai na dakatar da kukan da nake yi ina
neman wa kaina mafita zancen tunane na ya tsaya akan in bar gida kawai shi mafita
gare ni.
Ban tsaya yin wani shawara ba na mike na fara hada kayana a cikin trolleys dina
sai da na shake su da kayan da anty da sulaiman sukai min guda biyu na saka sauran
komatse na a baccon da na dawo dashi daga kalaba.
Komawa nayi na zauna a bakin gado ina tunanen abinda zan fadawa anty idan zan
tafi don na fasa gudun da nayi niyar yi kada su dora min sata banji ban gani ba
tunda mafita suke nema a kaina dama.
Ina nan zaune har yamma yayi min sai na fito falo don dama ina jin motsin su a
falon ta kalloni fuska sake tana cewa dani ina kika shiga tun dazun muka dawo.
Nace wallahi barci ya kwashe ni daga dan kwantawa in huta sai na dauki lokaci
ina barci Faiza dake gefen ta zaune tace ai da banji motsin ki ba nayi tunanen
haka.
Tambayan da anty ta jefomin ya hana ni magana tace kun ko yi waya da Sulaiman yau
Safiya ?
Sai na samu kaina da yi mata karya da cewa bai kirani ba anty tace nima haka
kwanan nan akwai tsiyan da yake ji wata kila yaji wani magana ne yake son ya ja
baya kuma.
Murmushi nayi nace in haka yafi alheri a gare mu Allah ya kawo muna saukin
rabuwa tace nima shina gani dama can ba son aure yake yi ba da ayi yazo ya kawo
muna wani matsala gara tun wuri dai a watse.
Nuna mata nayi maganan bai damay ni ba naci gaba da harkana tai shiru ta shiga
dogon tunane sai can security din su ya shigo yace tana da baki a waje.
Ganin ta tashi yasa muka watse wurin kowa ya shige dakin shi kofana na rufo don
magariba yayi a lokacin gashi kuma ina fashin sallah don haka sai na jawo tasbahana
ina ja kwai.
Kiranshi ne ya shigo min na dauka a sanyaye da sallama na yayi saurin cewa dani
yaya kuma naji muryan ki kamar baki da lafiya ne ?
Kodai zancen jiya kika sa a ranki yake damun ki kuka ne ya zo min shiru yayi yana
saurare na tun yana fadin subbahanallahi har ya kyale ni ina tayin kukan.
Sai naji ya kashe wayan bai fi minti talatin ba ya kara kirana na dauka yace
look ki tsaya ki saurare ni ban son wanan kukan da kike yi kamar ance za a kwace
maki ni.
Murmushin dole yasani yi nace uncle ba haka na bane yace to yaya ne kin bi duk
kin tayar min da hankali har jirgi nace a bincika min da daren nan saboda rudani da
kikayi ba a samu ba.
Nace cikin dan kuka Uncle gida nake son wuce wa gobe in Allah ya kaimu da sauri
naji yace saboda may zaki koma gida gobe shiru nayi kawai ina sauraren shi.
Sai da ya gama cikin kuka na fara fada mai abinda naji anty da yar uwar mijinta
suna tataunawa a kaina.
Yace oho dama nufin su ke nan shiyasa tace min ba sona kikeyi ba don dan uwan
tsohonijin ki dake kalaba ke kike so.
Watau gani mutumin banza zasu gara ni yadda suke so ki saurare ni kiji ni zan
tsara yadda zakiyi tafiyan gobe zan kiraki in sanar dake yadda mukayi da ita kafin
goben kada ki kashe wayan ki kinji ko na amsa da eh.
Naci gaba da tunanen zancen nace a raina watau anty uwa ita keson anty ta hada
diyarta da Sulaiman shine suke son raba mu.
Nasan anty uwa tun zuwan mu Abuja bude company sulaiman din da mukaje yi wata
yar bariki ne don idon ta ya bude sosai don ko shigan da tayi a wurin sai da nayi
tir da ita da diya ta wai ita wayewa ke nan.
Yaran ta mata uku tazo dasu wajen biyu sun yi aure amma sun fito ita kuma babban
ko auren batayi ba zata kai shekara talatin kila .
Itace ke nan ake son a hada ta da sulaiman nace to ke nan itama din victims ce
na HIV komay don naji sunce a huta da ita.
Ban yi barci ba zuwa goma da rabi naji ya kirani yace gobe zaki kibi jirgin safe
karfe bakwai za a kaiki airport na fada mata jikin baban ku ne ya tashi aka kirani
kuma ina son ki koma gida har yadda hali yayi.
Ta amice don naji tace abin ma yazo da sauki don haka idan ta tambaye ki ki fada
mata yadda na fada maki din nayi mashi godiya mukai sallama na kashe wayan.
Muna gama waya dashi na bi gado na lafe kamar ina barci sai gashi an turo kofan
ddakin naji tana cewa kin yi barci ne Safiya ?
Na dago da sauri ina fadin yanzu na falka tun tara barci ya dauke ni daga karatu
a waya na yanzu fitsari ya taddani ta samu wuri ta zauna tana cewa mutumin ya
kiraki ne nace bai kirani ba anty.
Tace yanzu na samu wayan shi wai an bugo mai daga gidan ku mahaifin ki jikin shi
ya tashi don haka gobe ki shirya kije gida.
Rudewa nayi ina salati tace ki kwantar da hankalin ki nace shine basu kirani ba
anty tace ai sun kiraki wai basu samay ki bane tace ai nima nayi mashi wanan
tambayan.
Ta mike tana cewa sai ki shirya goben karfe bakwai jirgi zai tashi yace a sayo
maki ticket yau da daren nan za a kawo muna.
Ta fara tafiya sai ta juyo tace dani ina ganin zaki dauki lokaci a can don haka
ki debi kaya masu yawa da zasu isheki zama nace cikin rudewa tau anty.
Tana fita na daga hannu sama inayiwa Allah godiya da ya bani mafita da saurin tun
ban wulakanta ba a gare su.
Karfe shida na gama komai ban bar komai na wa ba a gidan don nasan ko na bari ba
a amfani dashi katshen ta yarwa zasuyi ko su kona.
Security ya gama samin kaya a mota Faiza ce da tayo min rakiya take fadin wanan
uban kaya da kika kwasa haka safiya kamar wacce bata dawo wa.
Nace zan rage kayan ne shiyasa na kwasa don in bawa mutane can a gida tace haka
na da kyau kuma.
Anty dake bayan mu saye da hijjabi tace Allah dai ya kaddara saduwan mu da alheri
ki gaishe sai munyi waya inji saukar ki da lafiyan baban tana magana da gani tana
cikin bacin rai.
Na tako gaban ta nace anty na gode Allah ya saka da alheri ki yafe min zaman da
mukayi tare idan na saba maki ki gafarce ni anty nace wa Faiza ma haka tare da yi
masu sallama na shiga mota ta rufe.
Motar na fita na lumshe idona hawaye na zuba min ji nake kamar ba zamu sake
haduwa ba daga nan.
Ita ko anty tun barina gidan sai maganana ya tsaya mata a rai hartayi wanka tana
tunanen zancen mu da nace duk abinda nayi mata ta yafe mun.
Tana shirya wa dakina tayo bude ta shiga kallon gadon tayi dana gyara kafin in
wuce tace badai tsabta ba safiya tawuce wurin wardrobe dina ta bude sai wayam babu
komai a ciki sai zanin gado dana bari nasu.
Da sauri gaban ta ya fadi tace kardai yarinyar nan ta fahince ni ne ko may nake
plain a kanta da sauri ta dauki wayan ta tana kiran driver ya dauka tace bani
Safiya yace ai jirgin su ya daga gani hanya dawowa gida.
Zama tayi saman gadon tana magana ita kadai tace sam bata ji ba sai dai idan
yadda tace ne zata rage kayan a gida.
Da wanan tunanen ta mike ta bar dakin zuciyar ta fam da tunane a ranta tana fadin
haka ma yafi sauki da sai anty uwa ta zo suyi mata korar kare a gidan gashi ba
mutunci je da su ba.
Tun da muka daga babu abin da nake tunane banda zama na da ita tun farkon
haduwan mu da tazo tana tamnayan ko nan ake kitso wata yar wajen aikin su ce tai
mata kwatance dani nakai kallo na ga ayan tagwayen ta nace nan ne anty gashi kuma
yamma yayi tace ko yaran nayiwa don gobe monday nace to su zauna sai na sake kan
wace nakewa kitso na shiga na dauko ma yaran abin sha na kawo masu.
Matar dake zaune tace na nuna masu banbanci su da suka dade da zama ko ruwa ban
basu ba sai wanan da tazo yanzu.
Nace ai Sister dina ce ita dole in karrama su naga masu kitson harda ita kuma
naki karban kudin lokacin ne Ahmed ya dawo tana jin fadan da yake min akan na tsaya
kitso har dare .
Da na fito take tambyana mijinane na bata amsa a sanyayye da eh tace shine yake
maki fada akan neman kudi tun wanan rana mu ka saba da ita.
Gashi yau wani matsala ya gitta a tsakanin mu har yana son raba mu da ita lumshe
idanuwa na nayi ina mai ci gaba da fitar da hawaye.
Bamu dade ba muka iso abuja da sanyin safiya sai ka dauka a nan muka kwana shida
kan shi yazo dauka na yana saye cikin suit irin na maza farare kayan sunyi matukar
karban jikin shi sosai.
An gama sa min kaya a mota ya bude min na shiga sai lokacin yayi min magana naji
yace ta gudu an iso lafiya ?
A jiyan zuciya na sauke na amsa da lafiya lau yace kin sa mun yi wa baba karyan
ciwo Allah ya kara mai lafiya nace amin na gode.
Yace ina mamakin mutane yanzu son kai sai yasa mutum yayi abinda ba halin shi ba
sam na rasa gane yaya akayi madam ta yarda wanan matar tayi convices din ta haka.
Hauka nakeyi ko matsuwa nayi da yin aure ai ba zan taba auren Nafisa ba a rayuwa
na bayan ta gama watsewar ta a titi ace za a dauko a kawo min gida na barin ga iya
gudin su ai.
Get din gidan aka bude ya shiga da mota ni dai ban yi magana ba har lokacin yace
ki huta driver yana zuwa yanzu zaku tafi.
Muka fito daga cikin motar shi yayi min jagora zuwa cikin gidan a falo nan muka
zube dukkan mu yace yanzu dai hankalin ki ya kwata ko kin gudo wurin antyn ki.
Murmushi nayi ina gyara gyalen kaina nace abin ne ba dadi ni tsoro na kada anty
uwa su zo su samay ni a gidan don ban san abinda zasuyi min ba.
May zasu yi maki kuwa banda suyi haukan su su wuce ai ita madam tana da hankali
nace haka dai yafi mun an rabu lafiya gida zan koma gidan mu ya fiye min komai zan
zauna har ranan da Allah zai kawo min dauki.
Dariya yayi yana mikewa yace ko kin zo ke nan sai in bugawa baba a daura muna
aure ke kin tare ko da sauri nace hai uncle abin kuma yar zolaya ne ?
Yace Allah ba wani abu bane ai sai kawai a dauro aure ke kin riga kin tare nace
ba aikaina za a fara ba ni dai driver bai iso bane mu kama hanya.
Yace amma dai kya bari ki karya ko ga table can an hada muna tashi ki yi
breakfast ki huta sai ku wuce.
Nace ban jin cin abinci ne Uncle yace kina wasa ne maza tashi kici abinci ko in
hanaki tafiya yau da sauri na mike ban ci wani abin kirki ba sai dai na dan taba
kadan sai ga driver ya shigo yana gaida shi.
Nima gaida ni yayi tare da min sannu da zuwa na karba mai fuska sake don mun
saba dashi dan haduwar da mukeyi.
Key ya karasa inda suke ajewa ya dauka yana cewa zai fita yayi services din
motar yace mai sai ya dawo.
Yana fita ya fuskance ni tare da cewa jinan sai na tattaro hankalina zuwa gare
shi yace idan kin je gida yau ina ganin next week magaba tana zasu shigo.
Don a daidaita maganan auren mu ban son abin ya dauki lokaci mai tsawo tunda kin
ga an fara samun matsala a ta inda bamu zata ba.
Don haka next Saturday in sha Allahu iyayyena zasu zo sai a saka muna rana dan
naga amaryan nawa har yanzu hankalin ki bai kwanta ba.
Murmushi nayi tare da fafin Allah ya kaimu lafiya amma ni ai ban tayar da
hankali na ba don nasan komai Allah ke yi .
In bashi ba ina ni ina ja da yar wurin anty uwa wa yan nan yan gaye wa yanda boko
ya ratsa su ciki da bai din su ai sune suka dace dakai.
Murmushi yayi yace a naki ganin ke nan ni sam bani rayin irin su nafi son wacce
zan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login