Showing 60001 words to 63000 words out of 258256 words
Chapter 21 - Bahagon Rayuwa by Zainab Idris Makawa Seenabu
inda kasan nauyin da maihaifin yarinyar nan ya danka min banda
yadda na iya ne.
Baka san nauyi da rikon amana kedashiba da matukar wahala duk abin nan ina sane
dasu amma son dana ya rufe mun ido.
Shiko dan waje ya koma yana jigina jikin shi ga mota yana tunane ya dinga kuna
wiwi yana zuka yana wa kwakwalwan sa caji tare da neman mafita akan matsalar mu.
Ya nisa yana cewa a ranshi hakika Safiya ke yar uwata ce ta jini kuma mata ga dan
uwa na zan tabbatarb kin kasance cikin farin ciki zan fuskaci duk wanda ya nemi ya
kawo maki kunci a rayuwan ki.
Burin mahaifinki akan hadin auren ki shine da dan uwana yaga an hada zuria mai
dorewa a tsakanin shi da yar uwar shi amma dan uwana yana son yaga rushewan wanan
alakan saboda rayuwan duniyanci daya dauka.
Ya Allah ka tabbatar da farinciki da kwanciyan hankali a rayuwan ku kar zumunta
ya baci a sanadin auren ku.
Iya sani na mummy bata da gidan zuwa a arewa wanda ya wuce gidan mahaifin Safiya
don ko sako ne ta gareshi take turawa a sayo mata abu a aiko dashi nan.
Haka dai ya kwana yana yawan tunane barkatai da samo fita ga matsalar mu .
********* ********* *********
Fitanan sune ya farka damu daga barcin safe da muka samu mukeyi a gidan nida
Sadiya.
Fada suke yi sosai shida ita hakan yasa mu fitowa da sauri dakin mu danbe suke
yi a tsakanin su.
Suna ta faman fashe fashen kayan falon da suke fadawa da gani har sadiya ba mai
iya raba su don sun fimu karfi.
Sun dauki lokaci suna abu guda saida sadiya takira yaya saadu yazo ya raba su ta
kwashe kayan ta tana mai zagin kaskanci irin na yan duniya.
Wani magana da ta fada sai da yaya saadu ya kadu bayan tafiyanta ne sadiya ta
taimaka min don mu gyara gidan mu mai da komai inda yake.
Kuka nake ban iya aiwatar da komai ba a lokacin sai gasu sun shigo gidan da shida
dan uwanshi.
Sun zauna suna fuskantar juna yaya saadu yace dashi matan bariki dama haka suke
su raba ka da ta kwarai su kuma daga karshe su guje maka.
Kamayi arziki bata kai ga kore maka mata ba ta tafi ya dago ya kalli dan uwan
nashi ai ba tafiya tayi ba barazana ne kawai.
Yaya Saadu yace yar bariki ne zata iya dawo ma rayuwana in yau ta ga dama ko gobe
sai dai ka sani.
Yarinyar na Safiya yar uwan muce jinin mu ne ita kamar yar cikin mummy take a
wurin mu infact dai kasan wanan auren naku anyi shine don kara zumunci.
A ganina bai kamata ace abinda iyayye sukai maka gata akan saba shikake
wullakantawa.
Na tabbatar da mahaifin yarinyar nan na kusa ko yasan halin da yarsa take ciki da
tuni ya raban auren ku da ita.
Ya kamata ace Safiya ta samu kulawan ka fiya da komai a gidan ka bata isa ta
hanaka barikin kaba amma kabata kullawa yadda ya dace don kauce ma shiga hakki.
Nasan da mahaifinta yasan halin da yarsa ke ciki a gidan ka da duk wanan abin
bakai ga yinsa ba.
Don basu san halinka na boye ba mummy ta rufe massu kokai waye ta aura maka
karamar yarinya da yaci ace yanzun tana karatu ne.
Please Ahmed ka gyara rayuwan ka duk wani abinda kasan yana kawo nakasan rayuwan
ka nesance shi.
Ba abinda ya zamo ma dan adam dole a rayuwa mussamman abinda zai nesantakan da
ubangijin ka yazama dole ka yakeshi a ranka.
Musamma giya da mata ba alheri bane ga rayuwan dan adam ba dole bane ba kuma inda
yazama ma dole sai kayi shi.
Don Allah bros ka rabu da wanan rayuwan ka rugumi matarka ka rike yarinyan nan
amana zaka ga yadda rayuwan ka zai canza duk wanda ya samu mace kamar safiya yayi
saa a rayuwa shi ga tsabata ga hakkuri da biyyaya.
Ya sa hannu ya dafe kanshi kamar maganan yana shiga zuciyar shi can ya lumshe
idanuwan shi yana hango kyakkyawan fuskan na da suran da Allah yaimin da natsuwa da
hakkuri.
Yace kai baka ko gudun ka dauko maku cuta ka manna wa yar mutane matar nan fa
baka san iya mutanen da take hurda dasu ba har wata kasa take zuwa.
Yaji zuciyar shi da jikin shi yai sanyi saboda maganan da dan uwanshi ke fadi
gaskiya ne ko abokan shi sun sha fada mashi hakan.
Gaba daya jikin shi yaji yai sanyi amma kuma yasan abu mai wuyane ya iya rabuwa
da lilliya ko ya rabu da kowa bai iya rabuwa da ita wasan dadi.
Ya kalli yaya Saadu yace na gode daka tunarta dani wasu abubuwan da na manta dasu
a rayuwa.
Yaya saadu bai tafi ba sai da ya tabbatar da ya daidata komai a tsakanin mu yabar
gidan .
Abinda bai sani ba shine na kudiri aniyar kwatar kaina daga gare su bazan kara
yarda da irin cin fuskan da yake min ba agaban matan bazan shi da yake kwasowa.
Kwana biyu kamar komai ya lafa sai dai a raina nasan kwanton bauna yayi kawai na
kwana biyu.
Yana kawo min abinci kai da kai kuma idan zai fita zai sallamay ni kuma idan ya
dawo nakan taso daga dakina ko nabar abinda nake yi nazo na gaida shi da dawowa.
Wata rana zai fita na tambaye shi zuwa wurin maman biyu indubata kamar ba zai
barni in tafi ba sai dai kuma yace kada in dade.
Na gama shiryawa na rufe gidan na kama hanyan gidan ta nayi saa ta dawo wai ashe
bata garin duk wanan dadewan da tayi.
Take tambaya na ko nazo bata nan ne sai nake fada mata irin kullen da yasani da
dauko Lilliya da yayi ya kawo gidan.
Da irin horon da na sha a wurin su har yaya Saadu yazo ya kwace ni a hannun su
daidai lokacin da nake ganuwan shan wahalan su.
Ta nisa tare dacewa safiya wanan mijin naki bariki ta aure shi rashin sani yasa
mahaifinki ya nace da ki zauna dashi hakana.
Amma wanan da kike gani tuban mazuru yai maku kawai may yuyuwa ya canza mata
gidana suna haduwa baki sani ba.
Nace inma gida ya canza mata baida may ni ba don ban gani ba abinda sukeyi bisa
ga yadda suka zauna min gida ana iya shege a gabana.
Nifa anty yanzu cikin nan ne kawai matsalata badon ciki ba da duk abinda baba zai
mun sai dai yai min ba zan zauna ba.
Sai dai nakan tuna furucin baba sai jikina yai sanyi da yake cewa indan aurena
ya mutu in tabbatar da zaman ummina ma ya kare a gidan shi.
In badon wanan ba aida tuni na gudu na koma ga iyayyena ko don maganar kine
wallahi don da dan uwanshi kemai magana ya rabu da Lilliya cewa yayi.
Wai abinda yasa ba zai rabuda itama ba sun jima tare ni tun baida komai suke tare
tabar maza da yawa take zaman shi shi kadai.
Wai cewa yayi har musulunta tayi saboda shi saida sukai alkawari da ita cewa
bazai wullakantataba kuma ba zai taba rabuwa da ita ba shi dalilin da yake duba.
Sai dan uwan ke tamabayan shi yana ganin Lilliya ta musulunts ne matar da ko
shiga irin na musulmai batayi kuma ita bata daina hurda da wasu mazan banza ba har
yanzu.
Kai amma mijin nan naki wani irin soko ne wallahi indan ka gan shi a fuska kamar
mutumin kwairai inji anty.
Tace yanzu shi baiji kunyan fadar wanan dalilin nashi na bazan ba shi watau baiyi
tunanen harcin da iyayyen ki sukai mashi ba sai na wata matar banza can.
Nace ai haka dan uwan ya fada mai idan yana son zaman lafiya da kwanciya hakali
sai ya rabu da matan bariki.
Sai cewa yai mai wai bayajin zai iya rabuwa da lilliya ko ya rabu da kowa don
baida matsala da ita tana binshi shi sau da kafa tana mashi komai ko wanan akasi
aka samu suka sami matsala.
Kanin yace mai aiko ya zama dole ya rabu da ita don farin cikin gidan shi nace
kin san may ya cewa kanin ?
Wai mau zai sa kanin na shiga mai harkan shi wai ai lilliya ma tarsa ce don haka
zai zauna da wacce ya ga dama a cikin mu ya saki wacce yake son saki ko kuma ya
zauna da mu dukkan mu.
Sai cewa yayi dan uwan ya rabu dashi kar ya caja mashi kwakwalwa don yana bukatan
hutu tare dashi.
Na kinga kenan bazai iya rabuwa da ita ba ni ko yana iya rabuwa da ni inya so.
Haka dai dan uwan ya lalaba shi har suka samu suka rabu lafiya dashi ya wuce in ba
haka ba ranan nasan ba karamin tashin hankali za a yi ba a tsakanin su.
Tace kin ga ni yanzu so nake ki kwantar da hankalin ki ga komai ki kula da kanki
sosai don ki haihu lafiya.
A hankali na daga mata kai alaman na gane ta kawo kudi masu yawa ta bani da zan
koma tare da kwantar min da hankali.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:11 PM - Ummi Tandama: BAHAGGON, , , , ,
2️⃣
0️⃣
YAR UWAN NOVEL DIN NAN NA KUDI NE IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU
PLEASE, , , , , ,
Abin yai min yawa a tare da ni ga yunwa ga ciwo ga ciki sai yar dadiron gida da
tazo ta kakace gidan da zama .
Ga miji dani da babu duk daya a gare shi bai san cina ba bai san sha na ba ko
ciwo gashi har wanan lokacin maman biyu bata zo gidan mu ni kuma ban fita ba.
Don da zaran nafita da ya dawo fada mai take yi ya samay ni yaita jibgana sai ya
ga dama ya yabar ni.
Suna zaune falo sun sayo kaji gassasu suna ci ga kayan shaye shaye nan mai sanyi
agaban su wasu ansha wasu ba a taba ba.
Kayan abincin da maman biyu ta bani duk sun kare banda komai da zanyi dabara dan
kitson da nakeyi ya hanani wai ana cika masa gida.
Jin motsin su a falo da dariye dariyen su yasa ni fitowa na samay shi, da farko
da nai magana tankar bai jini ba.
Sai da na kara cewa yaya wurin ka fa nazo tun jiya ban ci komai ba a gidan nan
sai ya dago ya dubeni wani irin yai karfin halin daga Lilliya daga jikin shi.
Ido ya zubamin na sake cewa tun jiya da safe banci komai ba a gidan nan, Lilliya
ce ta sake kwanta mai a jiki tana wani iri da idanuwanta.
Yai karfin halin sake daga ta daga jikin nashi again yace baki ci abinci ba mai
kike jira da baki dafa ba.
Nace wanda ka saya min ya kare sai ya juya ida take zaune yana kallonta ya zuba
mata ido yana kallon ta.
Yace baby kin san ba a horo da yunwa a bari ta dinga dafa abinci tunda akwai shi
kuma ke ba damuwa da dafawa kikayi ba.
Ta wani ya mutsa fuska tace abata badon halin ta ba don albarkacin wanan baby
dake jikin ta.
Tsayawa nayi ina masu kallon mamaki abincin ma da zanci wai sai ya nemi yardan
karuwasa idan ta yarda a bani indafa.
Ganin ban wuce ba yasa yace bakiji ba abinda tace kinci albarkacin cikin jikin
ki tace eh don kuwa babyn dear na ne kinga kuwa bazamu barshi da yunwa ba.
Kije mana ya daka min tsawa yana harara na wai na wuce mana tunda an bani na
kalle shi nace haba yaya kaji tsaro Allah.
Yanzu cikin daren nan karfe goma ya wuce wani abinci kake son na dafa inci a
wannan lokacin.
Ya zuba min ido yana kallona da idanuwan shi da sukai ja amma ya kasa fadin koma
sai bina da kallo da yake yi.
Sai a lokacin Lilliya da ke jin mu ta dago jajayen idanuwanta da suka rine tace
wannan abinda muke ci kike so komay
Kasan mai ciki da gwada zai yiyu kamshin shi taji tafito daga dakin ta, idan har
shi ko kika biyu wallahi kwalelen ki idai wannan ne.
Kofan da aka turo ne yasani juyawa bani ba harsu din suna diban kofan don suga
mai shigowa lokacin.
Bakowa bane illa yaya saadu ya shigo gidan fuskan shi a daure da alaman har yanzu
yana cikin zafi da maigidan.
Tunda yai sallama ya shigo gidan jikin shi ya bashi cewa akwai wani tsiyan da aka
shukawa a gidan.
A hankali murya a sanyaye na gaida shi da zuwa sabanin yadda na saba gaida shi
abaya idan ya zo.
Tambaya na yake a gagauce yana yi yana kallon inda suke zaune a ciken hasala
maynene matsalan safiya may sukai maki nace , ?
Ganin shi yasa kuka da banyi niyar yiba yazo min a lokaci guda .
Durkusawa nayi a gaban su ina tsananin kuka kamar na fita yacina Yaya Ahmed ya
daga zaune ya zuba min idonsa da suke jawur , ya kasa fadin komai, .
Kumshin naman kazan daya rage guda daya basu taba ledan shi ba shi ya dauka ya
miko min yana fadin.
Indai wanan ne kikewa kuka don ba a baki ba gashin nan kije kicke baby bari zan
saya maki wani kafin mu kwanta.
Ban karba ba kuka kawai nake yi ya sake cewa karbi mana kibani wuri da kukan nan
naki hakanan.
Yaya Saadune yace safiya in nama kikewa ki karba gashinan ya baki sai na dan
tsagaita kukan da nake yi nace yaya tun jiya ban ci komai ba a gidan nan .
Na fada mashi yace wai wanan ta bani indafa yanzu yaya yaushe zan dafa har inci
da daren nan .
Na juya ina fuskatan shi nace yaya ina cikin wani babban matsala da tashin
hankali da ban taba tunane ko tsanmanin zan shige shi ba.
Yaya Saadu ka mai dani gida inyakani baba zai yi kan naki zama gidan dan yar
uwanshi sai dai ya yankani a kan hakan ko dabba aka daure a gida ana bata abinci
taci balle mutum.
Yaya saadu kai kadai nake jin saukim rayuwa a wurin ka sai kuma maman biyu da tai
min tsaye, .
Ita ma bakin ciki da takaici ya sa ta dauke kafanta da zuwa dubana bani da kowa
dake zuwa dibani sai kai da kazo yau din nan.
Ya tausaya min sosai yace kinyi hakkuri safiya tun jiya na dawo motana ne keda
matsala sai na tsaya gyara da na dowa nike tambayan mummy ke sai take fada min wai
kina nan da ciki kuma kuna samun matsala.
Ya juya wurin dan uwanshi yana cewa yanzu kai rayuwar daka zabawa kanka ke ga ka
dauko karuwa har cikin gidan kana sunna kana fifita ta sama ga matar ka.
Yaushe zaka girma kasan ana mutuwa ayi hissabi wai har ace kace matar ka ta
zubar da cikin da kuka samu wai har ka tsaya kana mata wullakanci akan hakan.
Wanan matar banzan daka dauko ka kawo mata gida fa a matsayin may take ita in ma
har zakuyi abin ku , ku tsaya can kuyi inda bata ji balle ta gani.
Yanzu bakajin nauyi da kunya kana ciyar da matar banza abinda kake so ka kasa
ciyar da matarka ta sunna ga ciki ga bakin cikin ka da yunwa yaya kake son tayi.
Tsawa ya daka mai yace ya isheka Saadu ya isa haka gidan ka ko gidana ka sani
matar da kake kira da matar banza matatace.
Mata mata fakace yai masu wani kallo yana tafa hannun shi yace dakyau wanan ce
matar kake nufi ko may .
Tun wuri idon ka ya bude akan wanan ya nuna Lilliya yace wan yan kaddangarun
bariki masu ma mutum shigo shigo ba zurfi.
Yanzu ka dubi wanan yarinya wata take dashi garin nan bayan mu bata da kowa Allah
ne gatan ta kaine gatan ta amma ga ciki jikin ta kuma ga horo da yunwa.
Nice na katse su nace yaya bansan yaya zanyi da matsala ta ba ya zama wajibi na
zubar da cikin nan dake jiki na.
Gaba daya suka dubo ni nace shine kwanciyan hakalina a yanzu ina ni kadai ban
san yaya zanyi da kaina ba ina ga mun zama mu biyu nan gaba.
Na san idan na zubar ina da daman yin wasu abubuwa , ban kai ga fadin abinda zan
fada ma sai naji yaya Ahmed yace duk kika taba cikin nan a yanzu bakin auren ki.
Nai mai wani irin kallo na juya ina fuskantar shi nace tsaron mutuwar aure na
shine zai hana ni fitarwa ba, indai zubarwa zai kawo min kwaciyan hankali..
Matsala ta guda shine baba don nasan bazai barni in zauna mai gida ba don ya
rantse kan haka.
Tausayina ya kama shi baisan lokacin da idanuwan shi suka kawo hawaye ba ya
kalli wan nashi da yake hassale shima yana sauraren mu .
Wani kallon yake min ga alaman yunwa a tare dani da rashin kwaciyan hankali, kai
bashi ba ma duk wanda ya ganni sai ya tausaya min saboda nayi kankanta da shiga
irin rayuwan nan.
Shi kanshi lokaci na farko da yadan tausaya min kenan a gidan don wanan shine
lokaci na farko a rayuwan shi da yaji ya tausaya min ya sake kallona ina cikin kun
ci da tashin hankali.
Shiko yaya Saadu wani irin radadi da bacin rai ya dinga ji a zuciyar ji yake
kamar ya samay su yai ta dukan su a lokacin.
Do yana tausaya min ya son abani kulawa yadda ya dace amma