Showing 162001 words to 165000 words out of 168506 words

Chapter 55 - luu luu Book1 by Huguma

dokar tsanar kallo da tayi
a rayuwarta.

Numfasawa tayi kadan ta kuma gyara zamanta,tana jin kamar komai zaizo
da sauqi.

"Ba wani abu me yawa kome girma nake buqata ba illa sanin wayeshi?,inason samu
cikakken sunanshi da kuma qasar daya fito,kamanninsa da wani abu nashi daban da zai
kaini zuwa ga inda yake.......sauran ni zan qarasa aikina da kaina". Murmushi ya
saki kadan.

"Aiki ne me sauqi qwarai wannan.......ki bani kwanaki bakwai kacal idan basuyi miki
yawa ba" Kai ta jinjina.

"Sun isheka?"

"Tabbas" Ya fadi yana me bata tabbaci. Kai ta jinjina.

"Yayi.......saidai akwai sharuda guda biyu cikin aikina,wanda idan ka kiyayesu nan
gaba zaka iya samun damar da tafi wannan daga gurina". Wani irin dadi yaji yana
ratsashi,wannan aikin aikine da zaiyishi koda babu ko sisi da zai rabauta
dashi,aikine da yakejin zai iya kiyaye dukkan sharuddansa komai
tsaurinsu.....wannan MATSAYIN da kusancin kawai yake buqata.

"Na farko,banason kowa yasan da aikin nan.....na biyu kuma,inason ka gabatarmin da
kowacce hujja shaida da kuma sakamakon bincike,ni zan fara dubawa da kaina.....ko
idanunka ban lamunce suga komai ba" Ta fadi da dukkan yanayin da yake nuna da gaske
take. Ta dauki wannan hukuncin ne saboda tanason zama ta farko da zataga waye
din,idan har ya zamana wani wulaqantacce ne da darajarsa batakai tata ba,zai zamana
babbana abun kunya wani ya san ta tsaya bata lokutanta masu tsada wajen yin tsere
da wulaqantaccen mutum irinsa. Idan ita tafara gani,zatasan yadda zata lulluba
komai ta kuma dauki matakin da zai gamsar da ita a sirrance.

"An gama Allah ya qara miki daukaka" Ya fada yana dunqule hannunsa a qirji alamun
dake nuna girmamawa da sallamawa.

"Jeka.......zan sa ayi maka aike a safiyar gobe".

"Godiya nake bisa wannan tarin girmamawa da karramawa da kikayimin na sakani cikin
kebantattun al'amuranki" Ya fadi yana miqewa ya juya ya fice.

Ajiyar zuciya ta sauke,tana wassafa irin yadda zata ladabtar da kuma
hukunta mutumin. Ita daya tasan a ukun da zata sakashi,wanda saiya qare rayuwarsa
yana dana sanin jaa da ita.


★★★Akwai wani sassanyan yanayi a tattare da ita wanda hatta da badee'a ta karanci
hakan.

Tana da hira wasu lokutan,duk da hirarta bata zama me tsaho da
yawa,amma bata fiya zaman shuru ba musamman ga mutanen da sabo kadan ya shiga
tsakaninsu irin ta da suke tare kusan mafi yawan awannin wuninta.

Numfashi taja kadan,tana rufe shafin alqur'aninta. Ta juya agogon
hannunta ta kalla sannan ta dora idanunta da sukayi wani irin laushi akan badee'a

"Anya yau ma zaizo?". Dubanta badee'a tayi,yadda damuwa ke son yin tasiri cikin
idanunta.

" Ina kyautata zaton zaizo,a jiya da bazai zauna ba ya sanar......yauma inda bazai
zauna din ba zai sanar,kaman yana cikin mutane masu tsari sosai da kuma girmama
lokaci" Boyayyen numfashi ta sauke tana buda tafukan hannayenta.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)


So take ta lalubo maqasudi kuma gurbin damuwar da takeji a ranta na
rashin zuwansa karatu a jiya,yauma kuma kaman gashi hakan tana shirin faruwa,qarin
mintuna ashirin,abinda bai taba yi ba tunda suka fara karatu.

Ba zata iya tuna sanda ya qara mintuna biyar bama,yau kuma ga mintuna
ashirin suna shirin salwanta.

"Gashinan" Taji badee'a ta fada mata saitin kunnenta ta sigar rada.

Wani matsanancin faduwa taji gabanta yayi,zuciyarta ta fara qara yawan
bugunta. Tanason daga kai ta tabbatar,amma kuna tana tsoron wannan kwarjinin nasa.

Gaza jurewa tayi,a hankali ta daga idanun nata da zummar koda a sace
ne ta kalleshi,idanun nata suka sauka a kansa daidai sanda yake takowa cikin
ginshira da qasaitar da baisan tana bayyana kanta da kanta a tattare dashi ba.

A gajiye yake,irin gajiyar da hutu kawai yake buqata. Tun goma na
safe ya fita,suka hadu da omari dasu beeno,har kuma qarfe uku suna tare suna duba
abubuwa masu yawan da suka bawa kowa a cikin su tabbaci tare da yaqinin NASARAR
AIKINSU tana rataye masarautar agadez,amma hakan baya nufin kuma su saki sauran
masarautun da kowannensu ya saje da ita yana rayuwa a cikinta.

So samu yayi zamansa cikin sassansa,ko gidansa dake waje,amma kuma bayason
ko yaya yabar wata shaida ko digo ko wata alama komai qanqantarta da zata bar sahun
zargi. Iya haduwarsu dasu a jiya kawai yana jin cewa dole ya sake matse kowanne
motsi nasa. Indai abinda yake zargi akai ya tabbata to ya sani zai zama ana
binciken bincike ne.......kallon kallo,idanu kan wasu idanun,wannan ya tilasta masa
watsa ruwa me dumin gaske,sukayi jam'i shida abdii daya zube a nan saboda gajiya
yana fadin bacci zaiyi,ya duba closet dinsa ya shirya cikin Moroccan jallabiyya
maroon color da aka yiwa adon milk din zare.

Hula dara ya dora saman kansa ja data dace da kalar rigar sak da
sak,wannan ya sanya sassalkan gashinsa ya samu yadan fita kadan ta qasan
hular,abinda ya qara masa wani irin ajiyayyen kyau da kuma kwarjini na musamman.
Kusan yau duk inda ya gifta cikin gidan sai idanu sun bishi da kallo,kallon da
baisan mafarinsa,tun daga cikin gida abdii ya soma,bakinsa ya lura taf yake da
magana yanason kuma tankawa amma yayi masa birki,dole abdii ya hadiye yana satar
kallon yadda kayan suka zauna masa,yaso ya bashi fuska ya fadi abinda idanunsa suka
gani,amma rashin samun fuskar ya tilasta masa kama bakinsa.

Taji wani irin kunya da nauyi sun saukar mata sanda idanunta suka fada
cikin nashi.

"Innalillahi" Ta fadi cikin jin kunya na hada idanu da sukayi,da yadda kyan da
shigar yayi ta wafci idanunta da hankalinta,sai tayi qasa da idanunta tana maidashi
saman qur'anin hannunta.



zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki
kamar haka da naira (700) kacal*


*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

09166221261
KO
08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

09166221261


*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261

*SHAIDAR BIYA*
09166221261

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

✍🏽
*HUGUMANKU CE*


💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎


*H U G U M A*


PAGE 81
____________________________
*_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa
wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group
namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_*
https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX
___________________________



Shima idonsa ya dauke yana karantar wani abu tattare da yanayinta.
Akwai abubuwa da yawa idan tayi da suke kasa kama da dabi'u da kuma yanayin
saamee,abinda sam baya son tunawa ko hadawa kenan guri guda,don sam baya mata fatan
ta fada yanayin da saame din ta fada.

Ya karanci tasirin nutsuwa da kunya sosai tattare da ita,baisan me
yake neman fusgar hankalinta ba?,tunanin daya sanya yaji zuciyarsa ta quntace guri
daya,yana neman amsa da laluben dalilin da yasa irin hakan ke faruwa,duk da yadda
yake yawan kaucewa duk wasu abubuwa,dukkan wasu dalilai da zasu sanya mace tayi
falling a kansa.

Wannan dalilin ya sanya me yawan daure fuska.......mara fara'a me
fusataccen yanayi. Mutum me mugun nesa da dukkan al'amuran mata,don ya sani a yanzu
bai shirya aure ba,dole ya kiyaye duk wani abu da zai sanya a shiga soyayyarshi.

Yanaso yayi aure a sanda yake da cikakken lokacin kansa......don
dausayin aljanna yake son ginawa......tattausar shimfidar soyayya qauna da rahama a
cikin gidan sa kwatankwacin yadda annabi muhamamd S A W ya koyar. Bayaso yayi aure
a sanda baida lokacin matar......bayason yayi auren da matar zata yita sadaukar
masa.......zata yita haquri dashi da irin busy dinsa alhalin kuma ita tana cutuwa.

Yanason yayi auren da MAWADDA da RAHAMA zasu zama shimfidar cikin
gidan sa. Yanaso ya bawa matar da duk zata zama macen aurensa wani kebantaccen gata
da zata sha banbam da kowacce mace a DUNIYA. Yana da tarin tsari da buri me yawa a
gidan aurensa. Gidan SOYAYYA yakeson ya gina,ba gidan ZAMAN HAQURI ba.

Kamar ko yaushe,tana jin yadda Aeera ke riqeshi da kyau tamkar taga
mahaifinta,surutunta da bakinta cakwai tana iya jiyota. Abu daya dake sake zama ado
a gareshi.....duk yadda Aaera takai ga zaqin surutunnan nata ba zaka taba jin nashi
muryar ba. Wata irin cikakkiyar nutsuwa da kamalar zance gareshi,yana biye mata
yana kuma amsa ta,amma sautinsa daga Aaera sai Aafreen dake kusa dashi sosai
sukejin abinda yake fadi.

Akwai ranar da badee'a ta matso saitin kunnen falaak da itama fiye
da rabin hankalinta yana kansu,duk da littafi ne a hannunta a bude take dubawa.

"Idan ina ganin mutumin nan,saina dinga raina ajin duk wata mace me aji.......jan
ajinsa yayi yawa.......gaskiyarki fa uwar dakina,komai nasa cikin sarauta
yakeyi......sai naga kamar mu ba mata bane,yadda namiji keda aji irin wannan,anya
akwai macen da zata burge wannan?" Idanu qasa qasa falaak ta juya ta watsawa
badee'a harara.

"Dama ba karatu kike zama dauka ba?,yanayinsa kike karancewa?". Ta qarasa fada
tana jin wani abu yana taba zuciyarta. Dan murmushi badee'a ta saki tana janye
jikinta.

"Afuwa nake bid'a,na tuba bazan qara ba,na gagara yin shuru ne wallahi".

" Banason irin haka"

"Ba za'a sake ba" Ta fada tana komawa ta zauna sosai.

To amma sai maganar badee'a ta tsaya mata a rai. Maganganun badee'a
suna shige da abinda ya jima yana kai kawo cikin ranta. Ta tashi gidan
sarauta,cikakkiyar d'iyar gata gaba da baya,wadda ta mallaki dukkanin siffofin kyau
da aji irin na cikakkiyar mace me tarin quruciya,cikin shekarun da duka duka suke
sha shida zuwa sha bakwai. Tun a yanzun akwai masu kamun qafa da momma da kuma
sultane a kanta,mutane masu yawan da batasan adadi ba,amma a duk sanda suka wanzu a
muhalli daya ita dashi sai taji ta raina komai data mallaka.

Kyan,quruciyar.....mulkin......sarautar dama ajin gaba daya.

Ko a yanzun daya nutsu yana musu qarin qur'ani cikin muryar nan tasa
dake shigen kama data sheikh afif muhammad taj,sai takejin a duniya ba wani sauti
da yakai wannan dadi. A hankali ta zama aminiyar sauraron karatun qur'ani a yawan
lokutanta na rayuwa,da kuma qira'ar sheikh afif din,kafin ta fara fitowa da wayarta
tana recording karatun daya zame mata abokin fira. Abin yana yiwa momma
dadi,nutsuwa ta sake shigar falaak din saboda abotar data qulla da sauraren
qur'ani,tana sake samun tabbaci da yaqinin halayenta zasuyi kyau fiye da yadda take
mafarki,domin shi qur'ani waraka ne daga dukkanin cututtukan jiki zuciya dama ruhi
gaba daya. Ta dinga godewa Allah daya shigo da sheikh muhammad haisam cikin
rayuwarsu a sanda take fafutukar inganta rayuwar 'yarta da jikokin da Allah ya
azurtata dasu.

Wani abu da falaak ta lura dashi shine,muryarsa tana qara daguwa ne da
qara kaifi a duk sanda yake rera karatun qur'ani. Ta lura sautin yana kaiwa nesa
kadan da inda suke,sai taji kaman komai na gurin ya sake nutsuwa ne da rerawar
karatunsa cikin gwanancewa da hikimar sarrafa harshe dake kan harshensa dama wadda
ke cikin littafin me tsarki.


*_DAIDAI LOKACIN_*


Da take zaune cikin balcony dinta,zama ne na jiran tsammani.......zama
ne na jiran isowar mammina da ta shaida mata ta sake shiga gurin sultane a karo na
biyu don karbo mata sassauci. Ta zabi ta kebe kanta a nan,ta kuma qona dukkan
lokacinta ta jirayi mammina,don shine kawai abinda ya rage mata.

A hankali sautin ya fara kai mata har inda take zaune,ya kuma fara shiga
mata kunnuwa. Idonta ta lumshe sannan ta bude,sautin ya danyi nesa daga inda take
jiyoshi,amma yana da wani irin kaifin tasiri daya soma sauka kai tsaye cikin
zuciyarta. Inda ace inda take zaunen akwai hayaniya da ba yadda za'ayi ma ta iya
jiyoshi.

A hankali take bin kowanne harafi dake fita,tana kuma qoqarin zaqulo
surar da ake karantawa,amma sai taji kwanyarta ta gaji gaba daya,ta kuma gaza gano
komai.

"Biftu" Muryar mammina ta haye saman sautin karatun,ta kuma fusgi hankalinta,saita
waiwaya da sauri tana duban mammina dake tsaye.

A hankali a sanyaye kuma ta miqe tana dubanta,jikinta ya bata,hakanan
alamun rashin samun nasararsu ya bayyana saman fuskar mammina din.

Hannuwanta ta sanya ta kamo mammina tana duban idanunta dake cike da
tashin hankali.

"Bai janye ba ko?" Ta tambayeta a sanyaye. A qa'ida yayi tayi maganan ya kamata
taji tausayinta ko yaya,duk da cewa itama tana cikin tashin hankalin samun tasgaro
kan hanyar data shareta fetal take kuma hangen babu wani sauran datti ko tsiro da
yayi saura da zai bata matsala,sai gashi sultane yana neman zame mata BABBAN
DALILIN DAMUWAR.

Wannan tashin hankalin da take gani saman fuskar Akhnan shine
garkuwarta......wannan tashin hankalin dake gauraye da fusata shine nata makamin
guda d'aya daya rage.....amma hakan bazai hanata daidaita takunta ba,don haka ta
kama dukka kafadunta ta maidata tana zaunar da ita.

"Rashin samun nasara a kanshi yau ba shine yake nufin gobenmu ta saraya
ba......idan bamu amintar dashi a yau ba gobe ko jibi tabbas zata sauya mana
shi......amma dai....." Saita dakata sannan itama ta zauna tana fuskantarta.

"Sultane ya kafe da irin nau'in kafiyar da ban tana ganinta a tattare dashi
ba.....kici gaba da haquri,zanci gaba da qoqarina muddin mumfashina". Jijiyoyin
kanta dana idanunta tuni suka motsa,ta kama hannun mammina din tana jin duk wata
qwarin gwiwa da nasararta ta dogara a kanta.

"Yayi abinda bai taba yi ba,bawai saboda rad'in kansa ba.....yayi ne saboda an
sakashi,an dorashi a hanya an nuna masa.......bazan taba yafe mata b......"

"Akhnan mana" Mammina ta kirata da yanayin dake nuna bata qaunar qarasa fadin
abinda zata fadi din,yanayin da yasha banbam ainun da abinda ke qasan zuciyarta.
"Ko ban fada ba a nan a gabanki.....zan fadi watarana.....watarana a
gabanta,watarana a gaban kowa da kowa.....ta rusamin mafarkaina.......ta maida
farincikina zuwa baqinciki na.....indai ni halastacciyar d'iya ce,kuma haifaffiya
ga MUHAMMAD HAMMUD.....wannan zuciyar ba zata taba sonta ba".

"Ba wannan keda muhimmanci a yanzu ba......abinda ya fishi muhimmanci shine
ki.maida hankali wajen cikar burinki.......". Waiwayawa tayi bayanta,ta kuma
qwalawa birra kira data tabbatar batayi nisa da gurin ba.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)


"Ki tabbatar baki bar kowa ya shigo gurinta ba.......a barta ta zauna ta nutsu ita
kadai,a samar mata da dukkan abinda zata buqata har sai zuciyarta tayi sanyi".

" In sha Allah" Birra ta fadi a girmame,tana jin tsananin tausayin uwar gijiyar
tata yana ratsata. A kwanakin tasan bata samun wani cikakken bacci,duk wasu
yanayinta ba irin wanda ta sani bane a baya,ta juya tana bin bayan mammina don
itama ta bata space sanda taga ta cusa yatsunta dukka goma cikin gashinta me
santsi.

Murmushi takeson ta saki na yadda hannu daya ke tafiya da yanayin daya
dace,amma kuma har yanzu tana jin lokacin da zata saki murmushin bai qaraso ba.
Agogon hannunta ta kalla sanda yalwa data bari a qofar farko take biye da ita.

"Ki koma cikin gida.....anaso naci gaba da samun labari akan komai......idan nace
komai ina nufin kowanne irin nau'in baqon motsi,babba ko qarami,banajin zan sake
fitowa yau duka haraba,motsina da kai kawona a kwanakin nan yana yin yawa,yana kuma
sauyawa daga yanayin da aka saba ganinsa a tare dani,banason zargi ko
d'iso,wanzuwarsa a guri komai qanqantarsa MATSALA ce,ita kuma matsala kalma ce da
mukayi hannun riga da ita". Kai yalwa ta jinjina.

"Angama" Ta fadi tana juyawa gami da sauya hanya daga ainihin hanyar da suke kai.

Su biyu suke takowa zuwa sassan nata,daga ita sai shehnaz din da bakinta ya
kasa hutawa daga qorafin da mitar da takeyi tunda suka fito daga sassan nannie.

"Duk yadda zaka yiwa nannie bayanin kafiya da taurin kan akhnan ba zata fahimta ba"
Abinda aisa ta fada kenan bawai don hankalinta yana kan maganganun shehnaz da
mitarta dari bisa dari ba,sai nisa da hankalinta yayi kan wani abu na daban.

Tun daga waccan ranar da mammina ta gaya mata,ita zata bude office din
akhnan,ta kuma ci gaba da tafi dashi hankalinta ya gaza gamsuwa da hakan. Tayita
qoqarin ganin akhnan amma lockdown din data sanyawa kanta ya hanata faruwar hakan.

Taje don ganinta sau babu adadi amma bata samu dama ba,ba kuma wai don
batayi isar da zata karya tsarin akhnan ta shiga har inda take ba.....aah,tayi
hakanne saboda kare aikinsu birra wadanda a sanda suke mata bayanin ta kafa musu
sharadin kada subar kowa ya kusanci inda take tsoro ne fal idanunsu. Tsoron irin
tashin hankalin da zasu fuskanta idan suka karya mata doka daya cikin tarin
dokokinta. Tana respecting mutanen,don sun sadaukar da rayuwarsu da lokutansu gurin
kula da buqatunsu,wannan ya sanya tabi umarni itama don kare musu aikinsu da
mutuncinsu.

Kwana daya tsakani kuma suka tafi diffa da nannie,sai dazu da azahar
suka iso,ta kuma tarar da abubuwan da basa nan wasu a ciki suka kasance.

"Mammina tace kada kowa ya shiga,a barta ta samu nutsuwa ita daya" Birra take sake
shaidawa aisa a karo na biyu,tana jin nauyin girma irin na aisa amma a karo na biyu
tana sake gaya mata ba zata samu ganin akhnan din ba,duk da tarin matsayi da
kusanci da take tare dashi.

"Wannan karon zan dan taba tsarin aikinki birra ki haquri......tana buqatar wani a
kusa da ita" Aisa ta fada cikin qarfin gwiwa. Matsa mata birra kawai tayi,saboda
ita a karan kanta tana ganin gaskiya a maganar aisa fiye da maganan mammina.



zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki
kamar haka da naira (700) kacal*


*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

09166221261
KO
08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*

*SAIKU TURA

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login