Showing 84001 words to 87000 words out of 121650 words
ciki an canza zuwa sababbi, parlon
yayi kyau sosae bedroom dinshi ya nufa da ita har lokancin bai sake mata hannun
nata ba. Shima komai an canza yayi kyau, Daga can lungu ta hango jerin trollies
Kala wajen hudu da yake Wannan ne Karo na biyu da ta taba shigowa bedroom dinsa.
Kallonta yayi yace
Jeki wanka kinji?
Kanta ta gyada ta Mike ta nufi toilet ya dakatar da ita ta hanyar fadin
Da kayan zaki shiga? Bazaki cire ba?
Bakinta ta turo tace
Mhmmm.
Kanshi ya shafa saboda yadda yake samun mugun effect a jikinshi duk lokacinda ta
turo wannan karamin bakin nata, ji yake tamkar an jona mishi electric current cikin
jininshi. Juyawa yayi ya fita don ya manta ya Bar abinci cikin mota. Tunda ta shiga
take bin ko ina da kallo, toilet din very neat and tidy, komai in place. Kayan ta
cire cikin dabara don karsu jike, ajesu tayi a tsanake ta Fara wanka, seda ta
kammalla sannan ta dauro Alwala ta fito Tana jin tamkar tafi kowacce mace sa'a.
Bathrobe ne jikinta se towel ta rufo saman kanta, yana shigowa tana fitowa,
kallonta yayi yaga ta Bata rai yasan kada yayi mata magana ne hakan yasa ya shareta
ya fara cire kayan jikinshi, seda ya kammalla sannan ya shige toilet, zama tayi ta
Fara tunanin abinda zata saka a jikinta, nan ba dakinta bane tasan bata aje komai
ba. Mikewa tayi ta bude kofa ta fice Zuwa Tsohon dakinta, Tana tura dakin taji ya
bude Sede babu komai nata, gadaje ne biyu blue da coffee se wardrobes biyu, shelf
da study tables babu tantama na Ahmad ne da Muhammad, don gasu a kwance abinsu suna
shan bacci, Atika a kwance kan karamar katifa. Ciki ta shiga ta tsugunna kan
Muhammad tayi kissing dinsu sanann ta juya bayan ta kashe wutar dakin a ranta tana
tunanin ina ya kai mata kayanta? A parlor ta tarar dashi ya shimfida praying carpet
daya a gaba daya a baya da hijab saman ta. Tana shigowa ya bita da kallo har ta
zauna baice mata komai ba seda tace
Kayana?
Tashi yayi ya shige bedroom din ita kuma tabi bayanshi har gaban trollies din yace
Ga lefenki I hope you will like them,
Ya bude wardrobe dake can karshe jikin bango se ga kayanta sun bayyana, ya cigaba
da fadin
Is that all.
Murmushi kan fuskarta ta gyada Kai. Seda ta saka sleeping dress sukai sallah kafin
brain din Sulaim ta dawo aiki, Aure fa tayi kuma idan zata tuna ba ana having
affairs ba, gabanta taji yayi mummunan faduwa har ta furzo yoghurt din da ta Riga
ta kai baki sakamaakon fara cin kaza da suka Fara, da sauri Junaid ya matso kusa da
ita tare da kokarin kama hannunta Amma ta matsa baya idanunta taf da hawaye tace
A'a!
Kallonta yayi cikin rashin fahimtar Abinda take fada yace
Menene
Kanta ta hada cikin cinyoyinta ta Fara kuka ilahirin jikinta na rawa saboda fargaba
da tsoron yadda zata kasance, ta tuna Auren Afra cousin dinsu, Washegari sukaje
tamkar ruwa haka suka sameta a kwance, to ita ta yaya zata amince ayi mata haka.
Tasowa yayi ya nufo inda take ya rungume ta batareda ta farga ba, kuka ta kara saki
tana son kwace jikinta amma ina bai bata wannan damar ba se ma Kara kusantata da
jikinshi da yayi, seda ya tabbatar ta nutsu kafin ya sake ta yace
Muje ki kwanta.
Binshi tayi a baya har suka iso daki yace
Ki kwantar da hankalinki kiyi baccinki, Abinda kike tsoro bazan yi miki shi ba....
Matsoraciya rigimammiya kawai.
Turo bakinta tayi ta haura gadon ta kwanta yayinda Junaid ya fice a ranshi Yana
fadin "perks of marrying a baby" dama tuntuni ya shirya ma hakan don yasan za'ai
hakan. Shima shirin kwanciya yayi ya nufi dakin inda tuntuni bacci yayi awon gaba
da ita. Gyara mata kwanciya yayi cikin jikinshi amma bata farka ba, dariyar
yarintar Sulaim yayi ganin Tunda aka daura aure tare suke Kwana banda zuwanta
kaduna amma se yanzun hankalinta ya dawo jikinta. Sake rungume ta yayi Yana karewa
fuskarta kallo yadda take bacci peacefully and innocently. Murmushi yayi Yana jin
abu me karfi Yana sake bin jikinshi game da Sulaim. Inda yayi niyyar yi mata wani
abun da yi zaiyi yadda take wannan baccin.
Gyara kwanciyarshi yayi lokaci daya Subay'a ta fado mishi, Allah babu yadda baya
tsara abinshi, Subay'a ta tafi ta bashi space ya auri love of his life Sulaim.
Runtse idonshi yayi yana tunanin yadda sukai da Mami jiya da take tambayarshi ko
Subay'a tasan zancen auren yace Bata sani ba, Mami ta dinga fada sannan tace ya
tabbatar ya sanar da ita idan ba haka ba ranshi zai baci! Shi dariya Mami ta bashi
wai ya fada mata? Lallai! Kamar yadda tayi surprising dinshi da tafiya Cyprus haka
zai surprising dinta da Sulaim.
Bayan ta Idar da sallar asuba ta gyara dakin sannan ta fito dakin su Ahmad, har
lokancin basu tashi ba amma Atika Bata nan wanda ya tabbatar mata tana kitchen, da
sauri ta juya kitchen din saboda gargadi sosae Mami tayi mata akan barwa me aiki
girkin miji. Tana shiga Atika har ta Fara kokarin Fara soya Irish wanda ta Riga ta
Fere itada Laraba. Kallonsu tayi suma suna kallonta dauke da murmushi wanda ya
tabbatar mata suna farin cikin kasancewar ta uwar dakinsu. Cikeda ladabi suka
gaisheta tana ta dariya ta kullum sannan tace
Atika jeki shirya su Ahmad, Bari na karasa girkin.
To
Atika ta fada Tana ficewa sannan Sulaim ta dubi Laraba Tace ita taje ta Fara gyara
gida. Seda suka fice ta dukufa sosae tana girki Cikeda nutsuwa da kwarewa. Kamshin
turarenshi ya fara sanar mata ya shigo. Gas din ta kashe sannan ta juyo fuskarta
Cikeda murmushi tana kallonshi kamar yadda yake kallonta, ita ta Fara fadin
Ina Kwana?
Ciki ya karaso ya bude mata hannayenshi alamar ta rungumeshi ai kuwa babu musu ta
shige jikin shi, Lokaci daya suka sauke ajiyar sannan ya karkato kanshi saitin
kunnenta yace
Wannan ce gaisuwar! How's your night ina fatan ba Za'a Kara kukan jiya ba?
Ya karasa fada Yana dariya, tureshi tayi ta nufi kofa ya bi bayanta yana dariya,
dakinsu Ahmad ta nufa hakan yasa ya wuce nashi Cikeda jin dadin yadda take kula
dasu Ahmad din.
Karfe bakwai duka suka iso dining, suka zazzauna ta Fara serving din yaran kafin ta
hade nata da na Junaid, he was impressed Don Abinda yake shirin fada mata kenan se
gashi tayi. Suna kammalawa yace
Mu wuce Kada kuyi latti.
Kallonshi tayi tana Kara gyara zama tace
Se next week zanyi resuming.
Idanunshi ya zaro yace
Kidding right?
Maida fuskar ta tayi very serious tace
Nifa gaskiya na gaji da karatun.
Kanshi ya girgixa yace
That will never happen kinji? Tashi school zaki tafi so kike Baba yace na Hana yar
shi karatu ko?
Turo bakinta tayi tana fadin
Dama ba sona ake ba zaace se naje school!
Yana dariya yace
Naji indai akan school ne na yadda.
Daki ta nufa Don gyara kanta, har zuciyarta bata son Zuwa saboda bacci take ji
Tunda Kwana biu duk a Wahale take. Skirt da riga tasa white and black sannan ta
daura suit a sama ta yafa veil ta dakko books dinta ta fito sukai kicibis zai
shigo, seda ya kare mata kallo kafin ya ja hannunta suka koma ciki ba tareda ya
furta komai ba. Daya daga cikin trollies din ya bude take Abaya different designs
cike fal amma Daga Fara, baka se mixed white and black. Kallonta yayi yace
Ga sunan, sukadai nayi approving Kisa.
Ita din ba Mai musu bace hakan yasa ta ciro daya daga ciki Fara heavily adorned
with sparkling stones and sequence bakake, tayi mata kyau. Kallonta yayi yace
It fits you Dove. Kinyi kyau.
Lagwanbar da kanta tayi tana murmushi a haka suka fice don kiris ya rage su Ahmad
su makara, iyayensu sun zauna soyayya. Yau kam har cikin class ya rakata kusan a
cike class din yake saboda 8 har ta dan gota donma wanda suke dashi bai samu zuwa
da wuri ba. Tunda suka shigo ajin yayi shiru idon kowa na kansu musamman ma Junaid
kowa na mamakin shi ne mijin dama? Seda ta zauna sannan ya Mika mata handbag dinta
bayan ya amsa gaisuwar su Khairi. Yana fita Aimana ta Fara dariya tana fadin
Kaga love birds, bazai iya barin ki shigo ke daya ba se an rako ki. Ta Yayan ba!
Itakam grinning take ear to ear kamar bakinta zai yage, kafin ta bada amsa
lecturern Y shigo majestically hakan yasa sukai focussing akan lectures din, seda
ya kammalla ya fice sannan suka Fara zolayarta ita dai murmushi kawai take saboda
babu baki Tun asali ita bamai magana bace dalilin da yasa bata fiye sakewa cikin
cousins dinta ba saboda ireiren wasan, Mami Tasha nuna mata tana mayarwa amma Sede
murmushi kamar sokuwa. Sunanan zaune suna revising books dinsu Junaid ya aiko
messenger shi akan tazo. Aimana ta dubeta ganin bata da niyyar tashi tace
Ke bazaki tashi kije kiran miji ba?
Hararar ta tayi tace
Ke ina ruwanki? Sa ido kawai.
Khairi tayi tsaki tace
Wannan munafukar wai kunyar wa takeji? Allah yasa bamu ba, Allah kadai yasan abinda
ku ka gama a gida shi ne xakixo kina susunke kai.
Duka ta kai mata ta Mike Don Zuwa gareshi. Lokacinda ta isa office dinshi shi daya
ta tarar har yayi Alwala zaije masjid don yin sallar axahar, kallonta yayi yace
Se yanzun ko?
Langwabar da kanta tayi a shagwabe ta hade hannayenta alamun ban hakuri , ruwan
hannunshi ya fatsa mata ya fice yana fadin
Naje sallah.
Kanta ta girgixa a ranta farin ciki ne fal tana jin ya isheta rayuwa idan kuma ya
wuce haka kila kwakwalwar kanta ta zauce. Aje handbag dinta tayi, tayi Alwala tayi
sallah sannan ta zauna jiranshi. Shi daya ya dawo bayanshi dasu Ahmad da yasa aka
dakko su, suna ganinta suka yo kanta suna fadin
Ammiey!
Kansu ta shiga shafawa tana tambayarsu school da komai, yana tsaye Yana kallonta
taji kaifin kallon hakan yasa ta dago fuska dauke da murmushi, gefenta ya dawo ya
zauna tareda sauke ajiyar zuciya me nauyi yace
Your only concern is Ahmad and Muhammad. Papansu fa? Kin manta Mami tace ki kula
Dani.
Bata fuska tayi tana shafa kan Muhammad dake cinyarta tace
Bakajin tausayinsu, Mamansu bata nan, kai kuma kanada Mami sannan kana Dani ko?
Janyota jikinshi yayi gaba daya tausayin yaran na Kara ratsa shi, basu ma tambayar
Mamansu ko sun manta da ita ne oho!
Wasawasa haka rayuwa ta mika, soyayya me tsayawa a zuciya, kwanciyar hankali Marar
misaltuwa haka Sulaim da Junaid suka samu, matsalarsu daya duk dare se Sulaim ta
birkice mishi ta dinga fushi ko kuma yana kusantar inda take ta bare baki tana
kuka, se kawai ya biye mata yadda take so hakan yasa take ganin ta fishi wayo. A
haka sukai Kwana hudu, a ranar ya kai gejin da hakurinshi ya Kare, he wants her
Amma yasan Za'ai rigima ba karama ba amman ya shirya wa koma me zatayi.
Tunda ya fita sallar maghrib bai dawo ba dama yace mata se anyi isha'i zai shigo,
dakinsu ta wuce tayi wanka tazo ta shirya bayan ta barar da turarruka jikinta,
trollies dinnan ta nufa Don dakko kaya, English wears take so don ta gaji da saka
native. Budewa tayi da wani bakin trouser ta Fara cin Karo hakan yasa ta dakko shi
sannan ta hado da silk shoulder off half gown kalar milk, sakawa tayi ta kalla
jikin mirror yadda kayan suka amshe ta sukai mata kyau tamkar bakuwar foreigner,
tayi masifar kyau. Gashinta tayi combing ta daura scarf baki sannan ta maida
trolley ta rufe tana mitar rashin inda zata jeresu don yace mata zamanta gidan is
temporary wannan gidan Subay'a ne, ai fadar Subay'a da yayi Harda kukanta hakan ya
tabbatar mishi tsananin kishin da take dashi.
Ammiey!
Ta jiyo jin Ahmad na kiranta, da sauri ta zura flat milk vine ta fito don jin
dalilin kiran da yake mata. Cikeda nutsuwa ta bude kofar parlon ta fito bakinta na
fadin
Yaron Ammiey......
She couldn't finish the sentence saboda mutanen da ta gani a tsaye suma fuskokinsu
tsoro, mamaki da tsana, Hajiya ce yes Hajiyan Subay'a! Surayya da Samina Sun sakata
tsakiya. Wata muguwar faduwar gaba ta ziyarce ta amma haka ta hadiye mugun yawu ta
nufo inda suke, Bata kai ga karasowa ba taji knocking a kofa, ba tareda ta zauna
kamar yadda tayi niyya ba ta wuce don bude kofar, Junaid ne tsaye hannunsa rike da
ledoji, kallonta ya tsaya yi saboda masifar kyau da tayi mishi don wannan ne Karo
na farko da ya ganta cikin ireiren kayan, kayan ya aje ya rungume ta tsam tareda
Daga ta sama yana juyi da ita, ita kanta yadda taga sonta me tsanani cikin
idanunshi sam ta manta da ruwansu Hajiya cikin gidan. Se dan kanshi ya ajeta sannan
ya jawo ta ciki, shima da fuskokinsu yayi arba wanda kana kalla zakaga tashin
hankali da tsoro ya karu akan tsanar, mamakin da da suke ciki. Hannunta ta zare
Tare da jansu Ahmad don kaisu daki Samina tayi saurin shan gabanta tace
Ina zaki kaisu? Karuwa ka......
Don't! Don't!! Don't you ever call my WIFE with that name, Matata ce aurenta Nayi
kamar yadda na auri 'yar uwarku.
Kutmar uba kenan!
Fadin Samina wadda kirjinta har ya fara sama da kasa saboda yadda masifa ke Cinta
dama copy din Suhaila ce idan bata nan to Samina ce substitute dinta.
Juyawa Junaid yayi ya dubi Sulaim wadda idanunta kamar su fado saboda firgici se ta
bashi dariya saboda he has never in his life cikin wannan tsoron.
Kuje daki Dove Keda yaran.
Kanta ta gyada ta ja yaran suka wuce shi kuma ya zauna tareda Fara gaida Hajiya
amma bata ansa ba tace
Junaid abinda idanuna da kunnuwana suka jiye min gaske ne ko kuwa? Aure kayi?
Kanshi ya gyada yace
Eh gaskiya ne Hajiya.
Wata ashar Surayya ta saki tace
Amma Junaid Bakada hankali! Wa kake tunanin a cikinmu zai zauna da kishiya? Subay'a
Wallahi baka isa ba se ka saki waccen matsiyaciyar!
Har cikin ranshi yaji zagin da Surayya tayiwa Sulaim hakan yasa ya dago idonsa da
suka Fara canza kala yace da Hajiya
Ki ja musu kunne kada wadda ta kara zagin Matata, yadda sukejin Subay'a 'yar uwarsu
ce nima haka nake jin SULAIM
To fa people kunji wannan? Tun kafin Subay'a uwar Boko taji labari kenan! Inhar
Samina zata iya haka on behalf of Subay'a then wanne mataki Subay'a zata dauka a
karan kanta? Let's go people.....
shatuuu ♥️ *MACE A YAU*
43
✍️Shatuuu♥️
🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATION
#⃣Shatuuu095@wattpad
Hajiya ta riga ta sanya wa zuciyarta duk yadda takai da takatsantsan akan abu to
se ya faru musamman kan Subay'a wadda duk cikin 'ya'yanta ita ce me bata matsala
saboda son da takewa Junaid. Numfashi ta fizga tare da duban Junaid tace
Amma ka taba ganin anyi aure ba'a sanar da Matar gida ba, me yasa gaba daya maza
Bakuda adalci? Bakuda alkawari? To Wallahi 'yata bazata zauna da kishiya ba, ban
zauna da ita ba haka babu Wacce a cikinsu zata zauna da ita!
Kallonta yayi a ranshi Yana bakin cikin kasancewar yaranshi sun fito daga
tsatsonta, bai taba ganin sallamamiyyar uwa ba Irin hajiya ba, kallonta ya karayi
har bazai bata amsa ba se kuma yace
Wanda bai yiwa wani adalci ba, Hajiya ta ina yake tsammatar ayi mishi adalci. Aure
na riga nayi shi, idan zata zauna kanta idan ba zata zauna ba aure mutum biyu ke
yinshi zata iya tafiya babu damuwa! Zancen baki zauna da kishiya ba wannan tsarin
Alhaji ne ni kuma nawa tsarin shi ne aje mata biyu a gidana.
Idanu waje Hajiya take kallon Junaid kamar taji yace Subay'a can go, itakam Tunda
ta Fara haduwa da Junaid matsayin siriki abubuwata ke lalacewa.
Mu zuba mu gani!
Murmushi yayi yace
Allah ya kiyaye hanya, gashi ko ruwa baku sha ba.
Yana sane yayi furucin don ya kara tunzurasu, aikuwa Surayya ta juyo Tana fadin
Bazaa sha ba, Kaga mun zo maka a tsiyace, Allah ya kiyaye Wallahi.
Dakyar ya iya controlling dariyar da tazo mishi, hajiya haka jikinta a sanyaye ta
fito suka mara mata baya, suna shiga mota Samina ta dakko waya don sanar da Subay'a
halin da ake ciki, hajiya ta kwace wayar ranta a mugun bace tace
Kada wanda ya sanar mata halinda ake ciki, taje ta dawo ta samu abinda ta bari, ba
ita mai biyayya Ba? Tafi kowa bin miji se ta dawo ta tarar da sakamaakon abinda ta
bari.
Surayya hankali tashe tace
Haba Hajiya ta yaya? Babu Abinda zamui mata kenan?
Me zaki mata? Mijinki ne? Duk yarinyar da na aurar se nayi mata kokarin da babu
macen da zata kara burgeshi amma bansan inda subay'a take Kai Nata ba.
Wani abu da Hajiya bata sani ba, itafa Subay'a su kadai take nunawa tana bin miji
sau da kafa hatta Abinda suke bata na kayan gyaran mata ba sha take ba wasu lokutan
idan suka taru flushing dinsu take, kuma se ranar da ta ga dama sannan take Zuwa
turaka wasu lokutan se tafi sati bata je ba.
Ina ganin lokaci yayi da zanbi shawarar Hansa'u.
Wacece Hansa'u?
Surayya ta tambayi Samina wadda a lokacin mafita kawai take nema.
She's a neighbor, wajen wani malami da take Zuwa nan zamuje a raba auren, don indai
ina numfashi cikinmu babu Mai zama da kishiya.
Kada na sake Naji, ko by mistake wata taje gurin boka to ban yafe mata ba, boka
idan yana maganin matsala shi yayiwa kanshi mana.
Turo Baki Samina tayi jin furucin Hajiya, tace
Bafa boka bane hajiya Malam ne.
Ubanki nace kinji! Akan duniya zaki salwantar da lahirar ki, ni dai Allah ya sani
ban taba kai kukana wajen wani ba kuma ban yadda wata takai ba, idan har kissa da
kisisina ba zata zaunar daku ba, to duk Ku kashe Auren kuzo mu hada kafada. Kuma na
maimaita Kada wanda ya fada mata halinda ake ciki!
Tunda ta furta hakan kowa yayi shiru har suka isa gida. Acan gidan Junaid ya jima
Zaune a parlour yana mamakin zuri'ar su Subay'a, gabaki daya babu hankali a cikin
su, dukkansu taron tsintsiya ne babu Shara.
Sulaim na zaune kan kujera ta kammalla koyawa Ahmad homework dukda hankalinta baya
jikinta, ko kallonta kayi kasan a tsorace take, a haka Junaid yayi sallama ya
shigo, idanunta ta dago Tana kallon shi kamar yadda yake kallonta, Yana Zuwa inda
take Zaune yasa hannunshi ya rankwashi kanta, da sauri ta Mike hannunta akai Tana
turo Baki tare da kwabe fuskarta saboda zafin rankwashin har brain dinta. Bata
fuska yayi yace
Wuce muje ki bamu abinci Tunda ke matsoraciya ce, kin tsaya Kina zazzare ido saboda
su samu gut din Yi muki abu ko?
Banza tayi mishi ta kamo hannun yaran Don fita ya fuzgo ta, ta fado jikinshi,
rungumeta yayi ta Fara kokarin kwacewa har tayi nasara don kuwa bai saka karfi ba,
kallonshi tayi tace
Ahmad fa suna nan.
Bakinshi ya tabe Irin who cares dinnan ya wuce ya barta a wajen tana zumbure
zumbure. Tunda ta dawo daga kwantar da yaran