Showing 90001 words to 93000 words out of 124042 words
ido ya rintse
ahankali......
Janye hannuwansa yayi tareda mirginawa gefe ya zube kwance tareda rintse idanuwansa
Yana sauke numfashi Mai zafi Yana kokarin dawo da kansa hayyacinsa Dan yasan yau
kam yayi loosing control na kansa gabaki daya akan Babynsa.
Itama lafewa tayi gefensa gabaki daya jikinta a mace Dan ko iya bude idanuwanta
bazataiba sbd mutuwar jiki da tsoron Daya Gama cikata koina.
Mintuna kusan Tara ya dauka ahakan Yana seta kansa kafin ya tashi zaune ahankali
batareda ya juyoba ya nufi toilet ya shige.
Ruwan dumi yakuma sakarwa kansa sbd bayajin akwai abinda zai qarasa kwantar dashi
sai ruwan.
Bai wani jimaba ya fito wannan karon da bathrobe blue ajikinsa ya kalli Inda take
kwance ta lafe da alama bacci zatai ahakan.
Boyayyan numfashi ya sauke ahankali tareda nufar gaban mirror ya Dan fesa body mist
kadan da Mai shima kadan ya nufi closet dinsa ya Ciro fararen pyjamas ya sakata.
Gadon ya nufo ahankali tareda zaunawa ya kalleta cikin kulawa yaga bacci yafara
daukanta ya sauke ajiyar zuciya tareda Kai hannu ya shafa kanta ahankali yace"
Inayah¿
Dare yayi tashi muje ki kwanta kada bacci ya daukeki anan...
Bude idanuwanta tayi ahankali tareda kallonsa idanuwanta da bacci aciki dakuma
sauran yanayin dasuka so Shiga
A shagwabe tace"
Abbi anan zanyi baccin ni.
Galabaitattun idanuwansa ya zuba Mata cikin kulawa yace"
Zakifi Jin Dadi a dakinki Nan bana kwana da AC a kunne zakiji zafi...
Maqe kafada tayi tana cewa"
Zan kwana ahakan Zan Saba ai tunda tare zamuna ringa bacci.
Shiru yayi baikuma cewa komaiba sbd zancen data fara yankowa.
Ahankali ya gyara Mata kwanciyar da rufa ya tashi yakoma kan sofa ya zauna ya zuba
tea din da aka kawo Masa tun tuni baishaba
Yafara kurba ahankali Yana Shiga tunani.
Ya jima agurin zaune tsawon lokaci Batareda yaje ya kwantaba yanajin tayaya zai iya
barin wani Abu yashiga tsananinsa da Babynsa,
Baimasan tayaya hakan zai iya faruwa tsakaninsuba.....
Maida idanuwansa yayi kan makeken Lafiyayyan gadonsa datake kwance tana baccinta
hankali kwance cikin tattausan farin quilt Mai taushin gaske.
Sai dare sosai ya tashi ya nufi gadon ya kwanta a natse gefenta yakai hannu ya
kashe hasken dakin gabaki daya.
Juya Mata baya yayi ahankali sbd Qamshin Turarenta dayake yamutsa duniyarsa gabaki
daya.
Ko ahakan Saida ta jima kafin bacci ya daukesa...
Qarfe biyun dare ta farka sbd zafin dake damunta ta zare rigarta ta koma ta shige
bargon takoma baccinta.
Lokacin sallar asuba Yana tashi da ita ajikinsa yafara cin Karo ta shige jikinsa
gabaki daya ta rungumesa tana baccinta hankali kwance.
Lumshe ido yayi tareda zubawa fuskarta Ido yayi Mata kallon kusan mintuna uku kafin
ya zame ahankali ya tashi ya wuce toilet.
Brush yafara Yi kafin su alwala yafito ya sauya kayansa zuwa jallabiya ya fice zuwa
qaramin masallacin gidan nasu.
Bayan fitarsa bada jimawaba itama ta tashi dayake dama ta saba tashin asuba kan
lokaci Kuma shine ya koyar da ita hakan harya Zama jikinta lokacin sallah nayi Zata
farka.
A toilet dinsa tayi alwala ta fasa sabon brush tayi ta fito tayi sallarta anan
Takoma ta kwantawarta....
Jin rigarta na damunta ta zareta daga saman tabarta a kirji ta shige quilt Takoma
baccinta sbd sanin abbinma baya dawowa wasu lokutan da wuri daga masallaci wani
lokacin gym yake tsayawa Yi a gym room dinsa.
Koda ya dawo baiyi tsammanin zai sametaba Dan ya dauka Zata koma dakinta kodan
nauyin abinda ya faru dasu jiyan.
Bai lura da itaba sbd har lokacin dakin Babu haske sosai Dan haka ya zare
jallabaiyarsa dagashi sai dogon wandon kayan baccinsa ya hau gadon tareda shigewa
rufa sai kawai yaji mutum aciki..
Hannu yakai Dan tabbatarda ita dince ba zato hannunsa ya sauka kan tattausan
kirjinta da rigarta ta zame tabari.....
Dagashi har ita dake bacci wani mummunan shock suka Shiga Musamman shi da kusan
bugawa kansa yayi...
Janye hannunsa yayi da sauri Yana dauke Kai daga kallonta ya kwanta Yana lumshe
idanuwansa batareda yace komaiba.
Itama idanuwanta ta bude zuciyarta na Dan harbawa sbd hannun Abbinta yasata
dukkanin jikinta mutuwa.
Juyowa tayi ta zubawa kyakkyawar fuskarsa datake sake narkar da zuciyarta akan
kishinsa ta saki wani qayataccen murmushi Mara sauti tareda matsowa jikin nasa
ahankali ta shige tana zura hannuwanta ta zagayesa ahankali tace"
Good morning Abbi.
Bai bude idanuwansa ba ya shafa kanta ahankali cikin kulawa yace"
Morning.
Murmushi takuma sakewa tace"
Best morning ever...
Bude Ido yayi ya saukar akanta Yana kalla batareda yace komaiba sai lumshe ido
dayake akai akai.
Bacci takuma komawa abinta shima ahakan yayi bacci Mai Dadi har kusan qarfe goma
Basu karfaba Saida wayarsa ta ringa zuba ringing kafin ya tashi..
Wanka yafara shiga Kai tsaye sbd ganin time yaja Kuma yanada baqin dazai gani yau
din office.
Yana cikin wanka ta farka Dan haka itama Kai tsaye ficewaa tayi zuwa bedroom dinta
sbd yau garau takejinsa Zata iya leqawa asibiti.
Tana fitowa Babu kowa a main Palo Dan haka dakinta ta nufa Kai tsaye ta fada toilet
tayi wanka tana Jin farin ciki koina aranta.
Tana fitowa daureda towel brown taji salatin Haj umma na tashi da qarfi hakama umma
yaganah kaman suna magana cikin daga murya da tashin hankali.
Kasa tsayawa komai tayi ta fito a rude daureda qaramin towel din tana zaro ido
cikin tsoron meke faruwa sbd su gidan Basu Saba da hayaniyaba.
Tana fitowa dukkaninsu idanuwansu suka dawo kanta
cikeda mamaki da tashin hankali suke kallonta Baki sake..
Da sauri umma yaganah da hankalinta yafi na kowa tashi ta kalli Inayah din tace"
Ina kikaje tun daren jiyan Inayah????
Haj umma ce ta karbe da cewa"
Wlh idan Bata fada Inda tajeba yau duka Zan Mata a gidan Nan idan su Basu taba
dukankiba sbd gata Ni yau Marinki zantayi sai fuskarnan Taki Takoma jajir sbd bazan
iya kallon wannan shirmen dake faruwaba a gidan nan,
Tun tsakar dare yaganah tace taje dubo jikinki Bata samekiba,
Zuwanta uku bakya dakin bakya gidan anduba koina bakyanan,
Yanzu tunda safen Nan ankira Dr Abdul yace bakizoba Kuma baacan kika kwanaba,
Hakama hafsat ankira tace bakizoba,
To Ina kikaje?
Wace rayuwa Zaki saka MAJEED Kuma yanzu da damuwar wannan sabuwar
dabiar?????.......
Cikin takaice Inayah ta kalli Haj umman kafin ta juya ta kalli umma yaganah datake
kallon MAJEED Daya fito lokacin
Ta sake maida kallonta kan Haj umma tace"
A dakin Abbina na kwana gurinsa meyesa Baku duba canba???
Maida kallonta tayi kan Abbin tana ciko idanuwanta da Hawaye tareda Bata fuska
hawayen na saukowa tace"
Abbi Ni ko a Australia na taba kwana ba gida bane?
Haj umma tace saina fada inda nakwana Ni kafada Mata agurinka na kwana...
Dan dafe gashinsa yayi daya fara Masa wani irin nauyin abinda take fada din.....
Ganin haka ta fasa kuka tana kallonsa kafin ta maida kallonta kan Haj umma datai
mutuwar tsaye zatai magana cikin kuka tana riqe towel dinta dake Neman faduwa ba
tsammani su Haj umma sukaga yayi saurin riqe Mata towel din tareda kallonta cikin
Ido a natse da qaramin sauti yace"
Ya Isa menene na kuka anan Kuma?
Ni Abbi ka fada Mata Inda na kwana taji da kanta....
Naji ya Isa kukan kije ki saka kaya sanyi zai kamaki ahaka....
Haj umma ya juyo ya kalla cikin takaita Rigimar yace"
Umma please tayaya zaku fara tunanin Inayah Zata iya zuwa wani gurin ta kwana....
Umma yaganah ya kalla Yana Dan sake kokarin danne 'dacin da zancen yayi Masa yace"
Tayaya zaku fara wannan tunanin akanta?
##MAMUH#
_ZAFAFA BIYAR_
*_INAYAH_*
_MamuhGee_
*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_
*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_
*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_
*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_
_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*
ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
Shedar biya👇
07040727902
MTN card👇
09134848107
[11/7, 1:20 PM] MG: *_56_*
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
Umma yaganah kinfi kowa sanin halinta da tarbiyarta tunda sbd ke ne kika riqeta...
Haj umma please for God sake haryanzu Inayah yarinyace ki Dena biyewa wautanta
haryanzu kaman babyna c....
Umn I mean she's too young for all ths manya manyan maganganun.."""
Haj umma kasama cewa komai tayi Dan Kuma ai kaman Al'amarin yafi qarfinta tun
bayan barin Inayah gurin takasa dauke idonta akan hanyar databi shiyasa ma
maganganunsa ba duka ta fahimtaba Dan tashiga tunani Kuma.
Umma yaganah Kam sanyi jikinta yayi duk da Daman Bata taba kawo wani banzan tunani
ko zargin komaiba akan Inayah Dan MAJEED dinne kawai zai nuna Mata sanin Inayah
Amma kome zaa fada ko akawo Mata tasan Inayah bazata taba aikata wani banzan abuba
bare kawo tunanin ta kwana wani gurin,
Dama tunda ta sanarda Haj umman Bata gantaba hajiyar ta ringa fada tana masifa
tareda fadan maganganu marasa Dadi akan Inayar shine fa tafara Kiran MAJEED din a
waya Dan ta sanar Masa komai yasan matakin dauka tun kafin 'yar tagama lalacewa ya
miqawa uwarta ita tunda so take abata 'yar saiga wannan sabuwar maganar.
Barin palon yayi Kai tsaye ya nufi dining room sbd bawani lokacin zai bataba yanada
gurin zuwa.
Yana Zama Haj umma ta iso itama ta zauna tana kallonsa fuskarta ba walwala ko kadan
magana zatai dashi.
Umma yaganah Kam Bayan Inayah tabi dakinta
Tana shiga ta tadda Inayah din na shiryawa hankali kwance sai Qamshin khumrahs masu
Dadi da Black opium dinta ke tashi.
Kallonta umma yaganah takeyi dakyau tace"
Inayah kinsan idan Baki nutsu kin Dena wannan shashancinba Zan Dena biye Miki,
Meyesa Zaki tsaya gaban mahaifiyar ABDULMAJEED kice Mata a dakinsa kika kwana?
Kallon umman ta juyo tayi a sanyaye tace"
Umma yaganah kiyi hakuri bafa Karya nakeyiba wlh acan na.....
Kinga banson ji amma ko can kika kwana be kamata ki kalleta ki fada Mata hakanba
Shi kansa MAJEED din kunya kike sakasa agaban mahaifiyarsa.
Shiru tayi umma yaganah tayita yimata fada kafin tadawo nasiha da rarrashi.
Hakuri Inayah ta Bata kaman yanda tasaba duk qanqantar lefi Bata Jin gazawa ko
nauyin cewa ayi hakuri.
Cikin fluid Palazzo black da milk Waverly wrap top ta shirya sai scarf da qaramin
veil data nado akanta suka fito tareda umman fes da ita fuskarta ba kwalliya Amma
lip balm dintanda eyeliner dinda shine abinda yake qarawa kyakkyawar farar fuskarta
kyau koyaushe.
Sun shigowa dining room din akanta idanuwansa suka fara sauka
Itama kusan akansa idonta ya sauka din.
Murmushi tasake Wanda yasashi dauke Kai ahankali yana Dan gyara maqoshinsa dayaji
Yana bushewa take..
Haj umma kallonta tayi tana Dan Kama kanta Dan maganarta datayi da majeed din akan
Inayah dataga kaman Babu abinda yake ganewa idan akan lefin Inayah ne,
Tarasa masifar datafi Inayah a rayuwarta sbd akanta 'danta ya zabi yabarta shekarun
baya Kuma ko yanzu idanba bude Masa Ido yayi akan munafurcin maceba zai sake rufewa
ne.
Zama INAYAH tayi gefen Abbin tana satar kallonsa
Shikuma gabaki daya indanuwansa nakan wayarsa dayake duba Sako saidai kusan
hankalinsa baya kan wayar yanajin qamshinta na shiga hancinsa Wanda ya talasta Masa
ajiye wayar gefe tareda juyowa ya kalleta da idanuwansa dasuka sata Jin tsikar
jikinta tashi saidai takasa iya juyowa ta hada idon dashi sai kawai ta maida
hankali kan serving dinsa tanajin idanuwansa akanta Wanda shikuma idanuwan Haj umma
na kansa tana kallon ikon Allah dayafi karfin bawa.
Har aka Gama cin abincin yau Babu Wanda yayi magana sai Inayah data bude Baki
tabawa Haj umma hakurin abinda yafaru dazu cikin sanyi da son hajiyar ta hakuri.
Shiru hajiyar tayi taqi amsawa...
Aje spoon dinsa yayi tareda miqewa tsaye can qasan maqoshi yace musu saiya dawo.
Yanayinsa kobai fadaba yasa Haj umma jikinta yasake sanyi da Al'amarin Dan kuwa
tasan zuciyarsa ta sosu ne da shirun dataiwa Inayah.
Inayah ma miqewa tayi ba damuwa a fuskarta tace"
Umma yaganah na tafi Abbina zanbi ya ajiyeni,
Haj umma bye...
Handbag dinta ta sauka tareda wayarta tabi bayansa.
Ko data fito harabar gidan motar data gani setin kofa tasan shine zaiyi tuqin da
kansa Dan duk aka fiddota to shine zaiyi driving da kansa Dan haka ta nufo motar
Kai tsaye ta shiga gaba.
Zaune yake cikin motar da alama ita yake jira kenan ko Bata ambataba Abbinta yayi
niyar kaita aikin da kansa.
Tada motar yayi tareda juyowa ya kalleta
Ya maida idanuwansa ya zuwa shigar jikinta Yana kalla....
Ahankali yace"
Ina coat naki?
Gefenta ta nuna Masa tana cewa"
Gashinan tareda handbag Dina.
Motan yaja suka fice Yana maida hankalinsa kan driving dayakeyi saidai qamshinta na
neman rarraba hankalinsa Wanda ya rasa meyasa hancinsa yake daukan qamshinta komai
kankantarsa tun ba yanzuba.
Suna Isa asibitin ya ajiyeta tareda kallonta yayi Mata ta kula yaja motar ya wuce
itama ta shige akan idon umma Hadiza data Kira umma yaganah tace Mata Inayah din na
hanyar zuwa aiki.
Inayah Bata qarasa shigaba Hadiza ta iso gurinta tana kallonta cikin kulawa ta Kira
sunanta.
Inayah na ganinta ta sake murmushi tana cewa"
Good morning.
Dariya Hadiza tayi tana kallon yanda farin ciki ke kwance kan fuskar Inayah din
tace"
Yaya jikin?
Harkin warke wannan farin cikin na fuskarki fa?
Nasan bazai wuce na Abbinki Daya kawoki bane.
Kallon Hadizan tayi tareda sakin murmushin Daya qarawa fuskarta kyau tace"
Harkin sanni haka da wuri?
Dadin maganar Hadiza taji ta riqo hannun Inayah din tana sake murmushin farin ciki
tace"
Bakida wuyar fahimta Ayshatouh sbd bakida wahalalliyar zuciya da rayuwa halin
mahaifinki kika dauko baida damuwa ko kadan duk yanda rayuwa tazo Masa karba yakeyi
hannu babbiyu...
Sanyi jikin Inayah yayi ta zame hannunta ahankali tana cewa"
Allah yaji qansa"
Amma zuciyarta har lokacin batajin Hadizan da mahaifinta data ambata kaman yanda
takejin Abbi daya cike gurbindaya kamata su zauna a zuciyarta duk da ko ahakan
yanzu tanajin kaunar Hadiza aranta.
Bata shigaba daganan ta juya tabar Inayah itama Takoma gida.
Inayah ma shigewa tayi tana waya da Neesah datake kiranta suna maganar wani abun
dabam.
Sai yamma tadawo gida a Dan gajiye Kuma Hadiza ce tadawo da ita gida batai Mata
tayin shigowaba sbd haryanzu Abbinta baice komaiba akanta da Hadizan itama Hadizan
Bata damu da shigarba sbd tanason bashi lokaci da kansa ya sauko ya Bata Daman
kasancewa da yarta aduk lokacinda taso hakan.
Tana shigowa ta taradda Dr farhat a gidan Bata wani damuba sbd Abbinta yace Mata ba
auren zeyiba Dan haka Babu abinda ya shafeta da Dr farhat.
Fuska ba laifi ta tsaya ta gaidata tunda sosai ta girmeta ba kusaba.
Haj umma ta kalla itama cikin girmamawa ta gaidata kafin ta qarasa gurin umma
yaganarta ta Dan rungumeta tareda Mata sannu da gida ta wucewarta zuwa bedroom
dinta.
Wanka tafara Yi ta sanya gajeran wando Mai Fadi blue da light vest ta fito bayan
tayi sallar la'asar ta nufi kitchen gurinsu zubbi tasa Salimat ta dafa Mata noodles
da kwai taci acan suna Dan Mata fira tana dariya sbd tanajin dadin firarsu
Suma sunajin dadinta sbd ba ruwanta acikinsu sakewa take tana dariya idan suna Mata
fira da labari masu ban dariya.
Sai gab da magriba ta fito kitchen din sbd ta Dan saka hannu a aikin tace Zata fara
koyan girki sosai sbd Abbinta tanason Nan gaba itace zatana Masa abinci.
Koda ta fito har lokacin Dr farhat Bata tafiba Haj umma tace tunda magrib tayi ta
tsaya tayi sallah anan suyi dinner da ita tukuna.
Itama Bata wani musaba ta zauna din sbd tanason ganin MAJEED koba komai sbd gobe
tafiya zatai zuwa Abuja daga can Kuma Zata koma Australia Amma duka daka bazata
wuce wata dayaba zuwa biyu Zata dawo gida gaba daya tunda aurenta da MAJEED din
yanata sake kankama.
Wanka Inayah tafara Yi kafin tayi sallar magriba ta zauna tana yiwa Abbi txt din be
dawoba.
Tana tura sakon reply dinsa ya shigo Mata Ada alama wayar ba hannunsa sakon
yashiga.
Murmushi tasake tana karanta abinda ya turo,
"Ina tareda cm"
Love you my Abbi" kawai ta tura Masa tareda ajiye wayar ta miqe ta nufi dakin umma
yaganah.
A Palo ta taddasu har Haj umma da Dr farhat Dan haka gurin umma yaganah ta Isa ta
zauna tareda kwantar da kanta a cinyarsa tana cewa"
Umma kaina na ciwo kadan..
Dan fara massaging kan tai tana cewa"
Rigimarkice datai yawa
Ki rage sai kan ya Dena ciwo akai akai.
Dr farhat ce ta saki murmushi cikin kulawa tace"
Gaskiyar umma ne Inayah kullum cikin daga hankalinsu Haj umma kike da umma da
rigimarki kaman ba likita ba...
Dariya Mai kyau Inayah tayi tana cewa"
Babyn Abbinta ce fa Ni,
Idan na Dena Masa rigima waye zai masa?
Kullum Ni zanyi tayi Ni kadai,
Kuma haj umman ce take daga hankali akaina?....
Cikin raba Kai da wahala Haj umman itama tace"
Daman Kam bazan iya daga hankali akankiba na na Hana kaina bacci a banza,
Su dai dazasu iya suyita fama...
Amma Kam maganar rashin ji da kema kike sane kike gashinan kina cewa zakici gaba
dayi,
Yana Tara qananun Yara Dole Zaki dawo hankalinki.....
Shigowarsa batasa Inayah fasa maganaba tace"
To ai Ni nayi Rigimar nawa 'yayanma idan sunzo suyi tasu,
Mune zamuyita Masa rigima Yana rarrashinmu.....
Dangwale bakinta umma yaganah tayi tana hanata karasa fadar sauran maganar.
Yallaban kuwa yi yayi tamkar baiji abinda suke fadarba sbd zancen nasune dan ya
lura Haj umma ita kesa Inayahn fadan wasu maganganun batareda taji nauyin
fadarsuba.
Kallonsa Inayah tayi daga kwancen datake tareda sakar Masa murmushi tana cewa"
Abbi sannu da shigowa.
Kallonta yayi tareda amsawa cikin kulawa.
Su Haj umma ya gaidar shima tareda zaunawa a 2 seater Yana amsa gaisuwar Dr farhat
batareda ya kalletaba sbd idanuwan Inayah dake kansa kaman ta taso ta rufe Masa Ido
Dan kada ya kalla Dr farhat din Kuma yanajin idanuwan nata akansa.
Kasa Haj umma ce ta kallesa cikin kulawa da murmushi kan fuskarta tace"
Kaman gobe ne naji kace zakai tafiya Abuja right?
Dr farhat ma goben Abuja Zata acan gidan juwairiyyah Zata zauna munyi magana da
juwairiyyahn kafin jibi tabi flight dinta na wucewa gaba daya...
Tunda kaima can din kayi inaga zaifi sauki ku wuce taren ka gaisa sosai da 'yan
uwanka daga can..
Washe Baki Dr farhat tayi cikin Jin dadin maganar tana kallon MAJEED din a natse.
Dan gyara murya yayi kadan kafin ya kalli Haj umman Kai tsaye yace"
Flight din yamma zanbi ba buqatan ta tsaya jiran tafiya Dani.
Miqewa yayi zai wuce ciki Umma yaganah tace"
Angama shirya dining bazaka tsaya kaciba kafin ka shige??
Sai alokacin ya juyo Yana kallon Inayah yace"
Ok.
Inayah yake kalla ta hade fuskarta sosai idanuwanta ma kokarin cikowa da hawaye
suke.
INAYAH...."ya Kira sunanta a natse Wanda hakan yasa su Haj umma kallonta
Umma yaganah Kuma miqewa tayi ta nufi dining Dan qarasa duba abinda aka jera kafin
kowa yazo.
Kasa dagowa tayi Saida yakuma Kiran sunanta cikin kulawa sbd yasan Zata iya
rikicewa da rigima yanzu..
Dagowa tayi tareda miqewa tsaye batareda ta kalli kowaba ta nufi gurinsa ta tsaya
gabansa ta dago ta kallesa da idanuwanta dasuke yagar zuciyarsa da dafinsu tace"
Abbi Nima zanje abujan kaga bantaba zuwaba.
Kallon Zaki kasheni yayi Mata ahankali kafin ya girgiza Mata Kai ahankali Yana
cewa"
No,
Muje dinner is ready.
Wucewa yayi gaba ta tsaya zuciyarta na shiga damuwa da rigima saidai wlh batajin
Zata yarda yaje ba da itama saidai yafasa tunda Dr farhat bazata iya hanata
tafiyarba suje can su qarata a gidan anty juwairiyyah din Amma Abbinta tunda Zata
iya hanasa tafiya Koda rigimarta bazata Bari yajeba saidai yaje da ita.
Haj umma ce ta kalleta tace"
Karki yarda naji kin tada rigima akan tafiyar Nan ki dagawa bawan Allah hankali a
banza ko tausayinsa bakyaji sai anyi magana kice Abbinki ne ke Babynsa ce.....ba
baby ba wlh 'yar tsana.
Kallon Dr farhat tayi tace muje kici abinci kafin ki tafi farhat kinji.
Ajiyar zuciya Dr farhat ta ajiye kafin tace"
Haj umma inaga Bari kawai na tafi basai na tsaya cin abincinba zanje na qarasa
shirina kafin kigama magana dashi akan tafiyar idan ya amince.
Ok shikenan Saida safen Inshallah Zan sake Masa magana yanzu.
Kallon Inayah Dr farhat tayi tace"
Bye Inayah.
Batareda ta nuna bacin Rai ko wani abunba itama ta juyo bayan tafara tafiya tace"
Allah ya tsare hanya Dr farhat.
Tana fadar