Showing 159001 words to 162000 words out of 196133 words
sanya albarka”_
Zufa ta yankowa Surry kamar ita ce Zahrah ta ce "Zahrah anya baki ɗebo ruwan dafa
kanki ba?" Zahrah ta ce
"Kamarya?" Ta miƙa mata wayar, Zahrah ta dinga kallon picture ɗin zuciyarta na
bugawa sai ta ce "They're lie, ƙarya ne" Surry ta ce
"BBC basa posting ba tare da sun tabbatar ba fa, amma bari na duba Twitter ai
Prince Khalil nayi" tana shiga Twitter tai searching.
Prince Khalil Ahmad Sarki. Sai ga profile ɗinsa ya bayyana tana shiga taga anyi
tweet 20 minutes ago, a nan taga pictures kamar hauka na Yaa Sheikh da Halisa. Ya
rubuta “Finally, the day, the most most couple's in the world, Mrs....and Mr
Congratulations My sister Princess Halisa Ahmad Nuran Sarki with her handsome
husband Yaa Sheikh Aliyu haydar Aliyu” A fili Surry ta ce
"Tab, ina ruwan saki na dafe" Zahrah ta kasa magana kishi ya mamaye mata zuciya,
Surry ko a ƙafarta ta koma ta dinga karanta Retweet na mutane, harda masu cewa Ai
Halisa tayi masa ƙarama. Ana haka taga Tweet ɗin El-bashir ya faɗo just now.
Photon Halisa da Yaa Sheikh ne ya rubuta.
“HML Abba and his wife Princess” El-bashir bai fiya son hayaniya ba, ko a sunansa
na profile haka ya saka Ahmad Sarki El. So babu mai gane cewa El-bashir ne da yawa
sun ɗauka Mai martaba ne da kan shi. Kuma shi kaf Social media twitter kawai yake.
Ana haka El ya ƙara yin twitter rubutu ne a taƙaice ya ce. _“Got Marriage_”
Lokacin da suka isa event ɗin ya cika manyan mutane masu yawa kala-kala gasu nan,
aka fara walima Halisa na zaune sai fara'a take tana ɗagawa mutane hannu, har zuwa
lokacin bata san matsayinta a wajan Yaa Sheikh ba, Zahrah fuska haɗe aka shiga bawa
Halisa gift wasu har Zahrah suke bawa sunce itama ta cancanta. Yaa Sheikh yaƙi
fitowa yana kwance bedroom yana fama da kanshi. 9 daidai aka tashi Ummul wani
diamond ring ta bawa Halisa as a gift, tunda aka fara walimar bata ga Mother dasu
Yaya Halima ba da sauransu taga dai Dada sai Fulani Atine da Fulani Balaraba. Ƴan
uwan Zahrah duk suna nan. Daga Zahrah har Halisa Ummul ta ce su zauna nan, daga
ƙarshe aka ɗauke Halisa aka shiryata cikin lafaya white mai taushi, tai kyau sosai
maimakon su tafi gida sai taji mutane sun shigo suna rangaɗa buɗa ta ce "Ummul wai
mene naji haka?" Ummul ta ce
"Yau ƴar rainon Abba zata tafi gidan Abbanta a fara zaman ibada" Wani tsalle tayi
ta rungume Ummul ta ce "Wayyo Allah daɗi, I love you Abbana, Ummul kema ina sonki
sosai da kika bani Modibbo" Ummul tai murmushi gabaɗaya bata ɗauketa matsayin
mother-in-law ba, kallon uwa take mata hakan ya yi wa Ummul daɗin.
Ummul na tsaye wayarta ta fara ringing ganin mai kiran yasa ta ɗaga tana cewa "Ya
akai Arɗo?"
Cikin gajiyawa ya ce
"Ban son fitina, hayaniya ki bari by 11 zan tafi dasu" yana faɗin ya kashe wayar
Ummul ta fita ta sanarwar da Hajja, Jadda ta dinga bala'i da ƙyar Yaa Sheikh yaga
daidai tunda albarkar mutane ce baya so. Ummul ta dinga yi wa Zahrah faɗa ba tare
da tuna laifin da Zahrah tai mata ba, Zahrah tai luff ta zama mage mai kwanciyar
ɗaukan rai, kamar ruwa ya cinyeta ta ce "Na gode Ummul, Ni Halisa is like a sister
to me daga ɓangarena babu wata matsala Wallahi na miki al'ƙawari" ta ce "Thank you
kije yana jira" Mimi daman ta amshi Muhammad Surry kuma ta koma gidan Abba Hakimi,
tana fita harabar gidan ta samu Halisa tsaye na buɗe murfin mota, Yaa Sheikh na
zaune a gaba fuska haɗe idanunsa akan gate ɗin da aka buɗe, Halisa ta buɗe gidan
gaba ta zauna Zahrah taji haushi sosai sai tayi kamar bai dameta ba ta ce
"Am sorry sweetheart na barka jira" da sauri Halisa ta ɗago kanta ta kalli Zahrah,
domin har yanzu an kasa samun wanda zai sanar mata cewa a yau bayan an tashi daga
sauka aka ɗaura auren Zahrah Farouk da Yaa Sheikh, ta ce "Lafiya dai?" Zahrah ta ce
"Oh ashe kece lafiya mana, gidan mijina zani" wani irin kallon kin zama mahaukaciya
taiwa Zahrah ta ce "Gidan miji? Wanne miji?" Zahrah tayi murmushi ta ce "Sorry
mijinmu, ko ba'a faɗa miki yau aka ɗaura mana aure da Yaa Sheikh my sweetheart ba?"
Halisa ta juya ta kalli Yaa Sheikh taga sam basu yake kallo ba, bai ma nuna alamar
yaji me suke cewa ba, ta ce "Abba da gaske aure kayi?" Ya juya ya kalleta da kyau
kamar ba zai magana ba ya ce
"Zan tafi" Zahrah ta gane da ita yake,ta buɗe bayan mota ta shiga, hawaye tuni ya
wanke fuskar Halisa ta dinga kallon Yaa Sheikh sai kawai ta buɗe ƙofa ta fita,
ganin haka ya buɗe shima ya fito bata shiga gidansu Ummul ba ta nufi gate zata
fita, ya yi saurin riƙeta yana cewa.
"Ƴar fillo" a hankali taƙi sauraran shi, ta fara ƙoƙarin ƙwace kanta zuwa lokacin
ji tayi numfashinta na tsayawa ta jawota ya rungometa tsam a ƙirjinsa ta kasa kuka,
sai haɗiyar zuciya Jikinta ya saki, ya durƙosa ya ɗauketa bakiɗaya zuwa mota, ya
zauna kana ya zaunar da ita a cinyarsa ya mance da batun Zahrah na motar ya dinga
bubbuga kumatunta, ta buɗe ido ta ce "Baka so na, baka so na Abba, aure kayi ka
auri Anty Zahrah? Ba zan iya ba zuciyata zata buga, wallahi gwara ka sakeni da
gaske akan naga ranar da mijina zai kwanta da wata, mutuwa zan yi idan naga wannan
ranar ina son ka Modibbo don Allah kace ba kishiya kayi mini ba" ta ƙare maganar
wani gigitaccen kuka na ƙwace mata, Yaa Sheikh was speechless ya kasa cewa komai ya
rungometa tsam a ƙirjinsa ya shiga sakar mata kisses masu zafi ta ko'ina, the only
thing da zai iya ya kashe bakinta nata shi ne samar mata da nutsuwa idanunsa rufe
ya saka hannu ya farka rigar Jikinta ta rabe biyu a hankali ya danna kujerar da
yake kai while kissing her ya kwantar da kujerar yana ƙoƙarin zame vest ɗin Jikinta
yaji ance "Ka danne mini ƙafata....
08119237616
[1/31, 7:33 AM] Abk: *_Nimcyluv Writer's Queen 68 _*
IDAN BA KE
Paid book ₦500
08119237616
Zahrah ta faɗa muryarta na ɗan rawa kamar zatai kuka, Yaa Sheikh ya dafe kansa yana
rufe idanu cikin ranshi ya ce "Asstagafirullah Yaa Allah" domin gabaɗaya ya manta
Zahrah na bayan motar, ya zame Halisa daga jikinsa tare da duba yadda ya yaga mata
riga sai duk kunyar Zahrah ta kama shi domin kamar cin fuska ne, ya ɗan buɗe ido
irin Kinga abinda ki ka ja ko? A zahiri kuma ya kame fuska yana riƙe kan shi, yadda
Halisa ke jin rikici da rigima yasa sam bai tankata ba, sai kuka take mara sauti.
Tana nan jikinsa yana ƙare shigar da ita jikinsa da hannuna ya yiwa motar key tare
da nufar gate, wanda tuni gatekeeper ya buɗe masa, ya cilla motar kan titi kai
tsaye ya nufi unguwar da haɗaɗɗan gidansa yake.
Cikin nutsuwa da ƙwarewa haɗi da tsantsar kamala Yaa Sheikh yake driving motar
idanunsa akan titi, yadda hawayenta ke jiƙa masa shaddar jikinsa da ƙirjinsa yasa
time to time kawai yake girgiza kai tare da fesar da Iska.
He don't know how sad she's, bai kyauta ba, bai kyauta ba, ko wacce nada burin
tasan halin da mijinta ke ciki, tana son ta zama guda ɗaya tilo daga ita sai
yaranta wajan mijinta, ya sani ya yi kuskure irin babba ɗin nan, Ita ɗin yarinya ce
amma a karo na farko ya rasa kalmomin da zai mata bayani dan gane da kishiyar da
akai mata rana tsaka.
Zahrah tunda tayi ƙasa da kanta bata ɗago ba, sbd abinda ya zo ya tsaya mata a
maƙoshi yaƙi tafiya, ƙirjinta ya yi nauyi, suna mota ɗaya ace har Yaa Sheikh ya
mance da ita? Ko da ba matarsa bace ita, yana da kyau ya yi mata kara ya daina nuna
maitar buƙatar matarsa akan Idanunta me hakan ke nufi? Wata zuciyar ta ce
"Alfarma akai miki Zahrah, kada ki zaƙe" ta girgiza kai ɗayar zuciyar ta ce mata
"To Amma yanzu ai ke ɗin matarsa ce, kina da hakƙi akan shi ba zaki iya zuba idanu
ba, dole ki tashi tsaye"
Baya san sun ƙarasu gidan ba, sai taji ya yi parking a parking lot na gidan shi,
tare da danna horn Sannan ta dawo daga hayyacinta.
Ta buɗe idanu tana kallon mazaunin da yake kai riƙe da Matar Malam, ta buɗe ƙofa
tare da fitowa tazo daidai Glasses ɗin tare da yin knocking, slowly ya sauke
Glasses ɗin motar, ganinsa tayi jingine da kujerar motar ya ɗan lumshe idanunsa
kamar mai jin barci.
Ya ware idanun tare da zuba mata su kaɗan alamar "Ya akai?"
Ta ce "Am looking for my sister, naga kamar tayi barci ma" Ya jinjina mata kai,
nauyinta ya kama shi sbd Halisa dake kwance a ƙirjinsa, ji ya yi tayi shiru hakan
yasa ya kalleta, hannunsa dake cikin rigar Halisa take bi da kallo, ya kame fuska
yana janye hannunsa daga ƙirjin na Halisa.
Tayi murmushi mai ciwo ta ce "Is she okay?"
Ya dai yi mata shiru yana kallon yadda haske ya ƙawata harabar gidan nasa tamkar
rana, ji ya yi tana kiran sunan Halisa tare da ɗan bubbuga hannunta. "Wake up
Sister, we're at home"
"Kije, zan tashe ta"
Ya faɗa not looking at her, tayi kamar bai dameta ba ta ce
"Ok Sweetheart, catch your life" tana faɗin haka ta nufi ƙofar da zata kaita asalin
cikin gidan wanda yake ɗauke da Main parlour.
Halisa daman akwai gajiya tare da ita, ga zafin da zuciyarta ke mata, ga kewar
mijinta da gangar Jikinta take, suna fara tafiya kuma Yaa Sheikh ya fara hura mata
iska a fuska da kunne, tare da zura hannunsa cikin rigarta yana shafa cikinta wanda
yake jinsa har zuciyarsa, daga nan kuma ya haura da hannun dama wannan dalilin yasa
tun kafin su yi nisa barci ya ɗauketa.
Ya zareta daga jikinsa yana kallon yadda ta ɓata fuska ko a cikin barci, ya faɗaɗa
fuskarsa yana ƙara jinjinawa rigimarta, fitowa ya yi da ita a jininsa bayan ya rufe
ƙofar ya nufi cikin gidan, suna zuwa bakin ƙofar parlour Halisa ta ce
"Sauke ni" daman ba barci take ba she was pretend kamar barci take ko mene, bai ja
batun da tsayi ba ya sauketa, ta ce "Ina ne part ɗina?" Tayi maganar ko inda Yaa
Sheikh bata kalla ba, sbd raɗaɗi da baƙin da zuciyarta ke mata, yau ita zatai
sharing mijinta da wata banza? wacce bata da tabbacin ko lafiya lou take bata da
H.I.V ba.
Da hannu ya nuna mata part ɗin dake dama, wanda ƙofar take a rufe, ta juya ta nufi
wajan taji ya kaɗa mata key a hankali ya ce "The key"
Ba yabo ba fallasa ta amshi key ɗin ta buɗe ƙofar part ɗin, tana shiga ta murza
mata key tare da zubewa a baƙin ƙofar tana sakin wani irin kuka mai cin rai.
Zahrah tayi wani irin murmushi tare da takawa cike da gwalli ta ƙarasu wajan Yaa
Sheikh ta ce "Lafiya lou take kowa?" Tayi maganar tana ƙoƙarin rungome shi da
tafiyarsa ta ƙasaita ya matsa yana haurawa saman bene ya ce
"Laá adari" ta bisa da idanu ta ce "Ka duba ta mana, bana son damuwa" ya tsaya cak
yana kallon Zahrah daga upstairs ɗin bai magana ba, sai jinjina mata kai kawai da
ya yi.
Ta dubi haɗaɗɗan parlourn wanda gabaɗaya Yaa Sheikh shine ya zuba komai dake
parlourn, milk and Brown colours ta buɗe part ɗinta ta shiga, parlour ta fara cin
karo da shi, shi ma ya haɗu sosai daga nan kuma sai bedroom , bathroom da kitchen
duk akwai a part ɗin kowa, sharp-sharp tayi wanka ta shirya cikin wata nightgown, a
hankali ta dubi ƙirjinta koda ta haifi Muhammad ƙirjin bai yi cikar da ake tunani
ba, shi yasa batai wasting time na shayar da shi ba, sunan tana shan magani amma
har yanzu bata sauya zani ba, ta ɗauki wata bra mai tudu ta saka ƙirjin ya tashi
kaɗan ta fesa perfume ta saka slippers tare da fitowa ta haura upstairs part ɗin
Yaa Sheikh. Tayi tsaye bakin ƙofar tana riƙe handle ita burinta yau bai shige ta
kwanta da Yaa Sheikh, har mafarkin wannan rana take ranar yau kuma ta kasance
ranarta domin ita ce amarya.
Ta murɗa handle ɗin tare da shiga, wani ƙamshin ya ratsa hancinta ta rufe idanu a
hankali ta ce
"My sweetheart ɗan gayu I love you Beb" baya parlourn dan haka ta shige cikin
bedroom ɗin da taga ƙofar a buɗe, kai tsaye ba tare da sallama ba ta shiga yana
zaune saman doguwar kujerar dake kusa da bed ɗin shi, ya ɗora ƙafarsa saman table
hannunsa riƙe da gorar ruwa yana tsiyayawa cikin glasses, jikinsa na zubar da ruwa
alamar bai jima da fitowa daga shower ba.
Ta dinga binsa da kallo, domin wannan shi ne lokaci na farko data ganshi sanye da
wata milk armless mai buɗaɗɗen ƙirji, sumar ƙirjinsa luf ɗauke da danshi ruwa, haka
gemunsa, ta kalli farar dogwayen ƙafarsa har zuwa cinyarsa, ko'ina na jikinsa
kwance da gargasa, shekaruna suka ɓoye sai samartakar shi data bayyana, nutsuwa da
kamewar shi a fili.
"Ba a shigo mini ba sallama" ta dawo daga kallon maitar da take masa ta ce "Oh My
bad, I screwed up"
Ya yi mata uzurin domin babu mamaki bata saba ba, ko wanne tsuntsu kukan gidansu
yake, wani abun baya blaming nata, a haka a reneta.
Bai ce mata komai ba harta nemi waje kusa da shi ta zauna tana cewa
"Thank you" Ya ɗaga kai ya kalleta alamar ƙarin bayani ta ce "Yau zan kwana tare
dakai, mafarkina zai zama gaskiya, naji daɗi yau Halisa zata bar min kai, we'll
spend the night together zamu raya First night ɗinmu" ita kaɗai take magana bai ce
komai ba, ta zame ta ɗora kanta a ƙirjinsa ta rungome shi ta ce.
"I love You to the rest of my life.....,"
"Tea" ya katse da faɗin haka, ta ce "Tea kuma?" Ya jinjina kai ya ce "Ban son suger
sosai, ki saka honey" gabanta ya faɗi ita kam ai batai zaton haka ba, she don't
know how to make tea, ita kunna gas na bata wani iya sosai ba ta ce
"Sweetheart tea yanzu? Why not safiya" ya duba time yaga kusan 11 na dare ya zareta
daga jikinsa yana miƙewa tsaye ya ce "Good night"
Da mamaki ta ce "Night? But I want to sleep on your arms Beb" ya kama hannunta har
zuwa baƙin ƙofa murya can ƙasa ya ce "We'll talk tomorrow In sha Allah" hawaye ya
cika a Idanunta gashi ta shanye maganin da aka haɗa mata tass ta shirya amsar
mijinta da hannu bibbiyu, a sanyaye ta ce
"Ban taɓa ganin aure haka ba, at least mu kwana tare koda babu komai tsakani, daman
nasan alfarma kayi mini ba so na kake ba, ka tasauyawa halin da nake ciki da bana
son ka ba zan nace ka aureni ba" ta saki kukan makircin tana riƙe ƙirjinta ta soma
tari tayi kamar ciwonta zai ta shi. "Stop Zahrah"
Ta tsaya tana kallonsa ya harɗe hannayensa a ƙirji yana binta da kallo da kayan
data saka, bashi da wani feelings ko kaɗan a kanta, amma ya san hakƙinta ne kuma
dole Allah zai tambaye shi. Kamar an tilasta masa ya yi magana ya ƙasa da murya ya
ce
"Me ki ke so?" Da sauri ta ce "You" Ya rufe ido ya buɗe in a romantic style ya ce
"Gani" kambala'i yana nufin bai fahimta ba? Ko yaya ne? Wasu hawayen ya taro cikin
Idanunta tayi murmushi ta ce "Good night"
Zata juya ya kama hannunta sbd shi har ranshi tausayinta yake ji, musamman idan ya
tuna watanni biyar suka rage mata a duniya sbd ciwon Cancer babba abune da yake
kisa cikin lokaci ƙanƙani, ya ɗan rungometa ta gefe murya ƙasa ya ce "Am not in the
mood" kamar jira take ta rungome shi sosai tana sakin kuka wanda duk rabi na kissa
ne, ta fahimci hankalinsa baya tare da ita, kamar yadda ta sani haka ne domin
gabaɗaya tunaninsa yana ga Matar Malam da kuma halin da take ciki, yana son zuwa ya
kwantar da rikicin ta tun kafin safiya tayi ta rikice masa ya kasa fahimta..
"Don Allah sweetheart yau ɗaya, yau kawai ka barni na kwanta tare da kai don..."
Sai ta fara tari tana riƙe ƙirjinta tare da ɗauke numfashinta.
Yaa Sheikh ya riƙeta tare da janta gefen gado ya kwantar ya ce
"Clam down, it's okay" ta jinjina kai tana kallonsa ya ja mata duvet yana miƙewa ta
ce "Ina zaka?" Ya nuna mata ƙofa alamar rufewa zai, ƙofar yaje ya rufe, abu biyu
sukai haɗe masa, idan bai sha tea ba sam baya jin daɗin, ga tunaninsa yana ga
matarsa da cikinsa dake Jikinta.
Zahrah kallon sumar kansa kawai take yadda ta kwanta har wuya, gashi ta rabo gida
biyu, six packs ɗinsa a murɗe full options. A jikinsa yaji kallonsa take kuma shi
ɗin take jira, ya kashe hasken bedroom ɗin ya dawo ya zauna bakin gado yana jingina
da frame, yana kwanciya ta dawo kusa da shi tare da ɗora kanta a ƙirjinsa ta ce
"Ina son ƙare rayuwata dakai, amma na kusa barin duniyar nan ko yanzu na mutu don
Allah kada ka bawa kowa Muhammad ka riƙe shi na bar maka har abada, burina yanzu
bai huce na samu farin ciki tare dakai na tsayin lokacin da suka rage mini a
duniya" ya saka hannu ya rufe bakin tare da faɗin "Shhhha"
Yana zaune har barci ya ɗauketa tana shafa lips ɗinsa da take jin kamar tayi
kissing amma ya kame fuska babu dama, gently ya zame jikinsa daga nata tare da
miƙewa ya buɗe wani bedroom, haɗaɗɗene sosai a ciki kuma harda bene wanda zai mayar
dakai downstairs.
A nutse yake taka strais ɗin har ya sauka, ya nufi wata ƙofa tare da saka key ya
buɗe, shiru bedroom ɗin sai ƙarar karatun Alkur'ani dake tashi da kuma sanyin a.cn
dake ratsa ko'ina, ya duba saman bed ya ga bata kai, harya juya zuwa bathroom ya
hangota kwance saman prayer mat ta cure waje guda, ya durƙosa ya saka hannu tare da
ɗaukanta bakiɗaya ya cire hijabin har lokacin kayan da tazo dasu ne a Jikinta ko
wanka ba tayi, Jikinta zafi zau alamar zazzaɓi ne ke damunta, ya zauna da ita a
jininsa ya shiga ƙarasa zame raguwar kayan ya rage daga bra sai under wear a
Jikinta, sai kuma cikinta daya fara girma tare da nuna kansa a fili, ya saka hannu
ya shafa cikin yana ƙara shigar da ita jikinsa da kyau, idanunsa rufe da suka fara
rikicewa ƙamshin turaren Jikinta na rikita shi ga wani laushi da tsantsi da fatar
jikin nata ta ƙara, Ɗumin da Halisa daji na shigar ta ya sanya ta ƙara shigewa
jikinsa ta luff tana narke fuska cikin magagin barci ta ce
"Zan mutu Abbana, ka gujeni ka zaɓi wata, You left me"
Ya ɗora fuskarsa a tata yana goga mata tsinin hancinsa a hankali ya yi kissing lips
ɗinta with all his heart ya ce "Bbyn