Showing 48001 words to 51000 words out of 62823 words

Chapter 17 - UKUBAR KISHIYATA Sirrin Da Ya Rushe Aure by Ummee Yusuf

29 Jul 2026

43

sunan sai ya tafi da katuwar jaka cike da gifts.

Ameera da twins suma sun samu gifts daga 'yan uwa kala-kala.tun daga kan uban gayya wato Al'ameen,iyayen shi da 'yan uwanshi wanda ya kara hura wutan tsana su a zuciyar Lateefa..

Bayan suna da k'wana 2 Umma tace zata tafi da Ameera gida wanka.

Bori Sosai Lateefa ta tayar wai za'a rabata da 'ya'yanta harda kukan munafurci.

Ganin yanda ta dage yasa Umma tace toh su zauna ita da Fateema kuma zata turo da Gwaggonsu ta cigaba da yi nata wanka.

Lateefa ba haka taso ba,taso ace ita kad'ai aka barwa Ameera da yaranta yanda zataji dad'in b'atar dasu ba tare da wani ya ankara ba.

Ta wani side kuma taji dad'i tunda komai zasuyi a gabanta za'ayi.

Kusan kullum a part d'in Ameera take wuni ana hira da kula da twins tare da ita.

Sosai Gwaggo take jin dad'in zama da ita kuma take yabonta harta kai tana yiwa Ameera fad'a tabi ta su zauna lafiya dan a wannan zamani kamin ka samu mace kamar Lateefa sai an tona.


Shiru kawai Ameera take in taji Gwaggo tana irin wannan magana saboda ko tayi niyyan fad'awa Gwaggo halin da take ciki a sanadin Lateefa sai taji kaman ansa super glue an like mata baki.

Satin ta 2 da haihuwa babban jikan Gwaggo ya rasu ta tattara zata tafi zaman makoki Fateema ta rakata suka tafi tare.

Gida Fateema ta wuce daga gidan rasuwan wai tayi missing Ummanta.

Wuni tayi a gida suna hira da Umma sai bayan 5 tayi shirin komawa gidan Ameera nan Umma ta had'a mata kayan gyara tare da jadddawa Fateema ta fad'awa Ameera ta kula da kanta.

Da zata tafi Abba ya kawo ruwan Addu'a ya bata yace ta kaiwa Ameera su sha ita da yaranta kullum da safe kamin taci komai kuma in zasu k'wanta su shafa jikinsu dashi harna tsawon k'wana 7.

Fateema tana zuwa tayi mata bayanin kayan da Umma ta bata dalla-dalla sanna tayi mata bayanin ruwan addu'an.

A ranan suka fara amfani dashi har zuwa k'wana 7 kaman yanda aka umarce ta.

Kuma a ranan Fateema ta had'a kayanta zata koma gida soboda zasuyi resuming school.


Da daddare Al'ameen ya maida ta gida bayan sun cika ta da sha tara na arziki harda Lateefa wacce farinciki ya cika mata ciki sun watse sun bar Ameera zata cika burinta cikin sauki.


Da washe gari da safe Ameera tana shirin yiwa Fadeel da Fadeela wanka( sunan da Fateema ta zab'awa twins a rinka kiransu dashi kenan)su Fa'iza da Shamsiyya sukayi sallama suka shigo.

Amsawa tayi tana mamakin wai yau ita su Fa'iza kewa sallama.


Gaisheta sukayi ta amsa still a mamakince.

Fa'iza ta tambaya "ina twins ne?"

"Gasu can a cikin gadonsu yanzu nake shirin yi musu wanka".


Shamsiyya tace ..." Dama Aunty ce tace ki kawo su tayi musu wanka".

"Wanka kuma" ta tambaye su.

"Eh saboda ta tayaki ne yau taga bakowa Fateema ta tafi". Fa'iza ta amsa mata.

Kaman zata kara cewa wani abu kuma sai tayi shiru.

Wani k'aramin basket d'insu ta d'auko tasa kayansu kala 2-2 dasu diapper,su mai,powder da sauran kayan amfaninsu ta mik'a musu .

Shamsiyya ta d'auki Fadeel,Fa'iza kuma ta d'auki Fadeela suka fita.

Suna fita direct part d'in Lateefa suka wuce dasu,dama tana zaune tana jiransu.

Da sananin murna ta karb'i yaran tayi ciki, su kuma suka fita zasu tafi gidan binta tare da mamakin canzawar Auntyn nasu.


Ruwan sanyi Lateefa ta tara a bathtub sannan ta saka yaran aciki ta barsu suna ta tsala kuka kaman ransu ya fita.

Tana dariya ta fito parlour ta kira Aina'u tace..." Gasu can na saka su a cikin ruwan sanyin kaman yanda kika ce".

Dariya Aina'u tayi tace..." Kai Besty baki da wasa wallahi yanzu kukan sune nake ji haka?"

Dariyan itama ta shek'e dashi tana..." Ta ina zanyi wasa da wannan babban dama da na samu".

" gaskiyane yanzu saura step 2" inji Aina'u,suka sa dariya a tare.

Tana gama wayan ta koma wajansu duk sun galabaita ba bakin kukan sai idonsu da yake a lumshe.

Fito dasu tayi a cikin ruwan ta dawo d'aki ta k'wantar dasu a kan tiles babu kaya a jikinsu balle ta lullub'e su da towel.

Kara karfin a.c d'akin tayi ta fito parlour ta k'wanta bayan ta kulle k'ofan harda murza key.

Ameera tunda aka fita da yaranta taji sam hankalinta bai k'wanta ba.

Bayan tayi wanka ta shirya ta d'an kishingid'a akan 3 seater tace bari ta bada 10 to 15 mis in basu dawo dasu ba zuwa zatayi ta karb'o kayanta.

Tana k'wanciya wani bacci mai nauyi yayi gaba da ita sakamakon jiya daddare Al'ameen ya hanata bacci da wuri da fitinan shi dama kaman jira yake Fateema ta tafi.

Bayan good 2 hrs Lateefa ta tashi cike da d'aukin ganin halin da suke ciki ta bud'e k'ofan ta shigo.


Farinciki fal zuciyar Lateefa ganin basa motsi.

Turus tayi tana kallon yanda suke fitar da numfashi a hankali da alama baccin su yayi nisa.

Cike da takaici take tsaye akansu tana tunanin abinyi wata zuciyar tana bata shawaran ta shake su kawai su mutu ta huta amma wata zuciyar ta hanata.


Basket d'in kayan su ta jawo tasa musu diaper da kaya ko mai bata shafa musu ba ta fito tana k'walawa Ameera kira.

A nan parlour sukayi clashing da Ameera da farkawarta kenan kuma ta fito neman yaranta .

Mik'a mata su tayi tace ..."wuce kije ki basu nono yunwa suke ji".

Ameera tana karb'ansu taji jikinsu sanyi kalau kaman kankara.

A razane ta d'ago tana kallon Lateefa wanda har saida itama Lateefan ta firgita jin tambayar da Ameera tayi mata.

" meye ya faru dasu naji jikinsu sanyi kalau haka"Ameera ta tambaya tana kallonta.

Wani yawu Lateefa ta hadiye na mamaki had'e da tsoron me yake shirin faruwa a gidanta.

Cikin inda-inda tace..." Ke ni kikewa tambayan rainin wayon nan?"

Murmushi Ameera tayi tace..." Ki sani ni Ameera ba zan tab'a zuba miki ido ki cutar min da yara ba,amma in kina ganin zaki ita toh bismillah kuma ina tabbatar miki in har wani abu ya samu yarana hmmm" tana gama fad'an haka ta juya tayi part d'in ta da yaranta ko d'ar babu a zuciyarta bata san dalilin da yasa ta rage tsoron Lateefa ba Dan cikin 100℅ 70℅ ya ragu.

Lateefa kam daskarewa tayi a wajan ko yatsanta ta kasa motsawa dan bata gama yarda wai Ameera ce ta gaya mata wa'yan nan magagganun ba.
🙆🙆🙆🙆🙆🙆

*UKUBAR KISHIYATA*

😭😭😭😭😭😭

(Its all about love and betrayal)

Story by *~UMMEE YUSUF~*

(Maman Yusuf)

*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION~*💫💫💫

❄~*we bearer's of golden writer's assiduously percieven No pain so Magical our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u no pain~*

https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/

*forty two*

Lateefa da k'yar ta dawo hayyacinta tana tambayar kanta meke faruwa ne?

Juyawa tayi cikin sauri ta koma part d'inta tare da dannawa Aina'u k'ira.

Bai dad'e yana ringing ba ta d'aga tana cewa..." Nasan kin kira ne dan bani good news,yah sun shek'a?"

Lateefa a hasale tace..." Ke yi min shiru wani good news zan baki yara da shegen taurin rai,ba abinda ya same su lafiyarsu k'alau.ni ba wannan ba yarinyan nan wai yau har ita take kallon tsakiyan idona ta gaya min magana".

" wacce yarinya kuma kika samu?"Aina'u ta tambaya.

A zuciye Lateefa ta amsa mata da..." Wace yarinya kuwa banda wannan 'yar iskan gidan nan,akan way'an nan b'erayen nata ta dubi cikin idona tace in wani abu ya same su in kuka da kaina".

" wai Ameeran ce tace miki haka?"Aina'u tace cike da mamaki.

Kwafa kawai Lateefa tayi ba tare da tace komai ba.

Aina'u ta cigaba cewa..."lalle akwai matsala dole mu koma wajan boka but before then ya kamata ki koyawa shegiya hankali kamin in dawo muje dan yanzu haka ina hanyan zuwa Kano nida Alhaji nura amma k'wana 2 kawai zanyi,ki nuna mata ko ba boka kinfi karfinta".

Cike da k'warin guiwa Lateefa tace..." Off course wallahi ubanta zanci a gidan nan dole tasan ni Lateefa nafi karfin uwarta bare ita useless da ita".

Shawara sosai Aina'u ta bawa Lateefa wanda yasa mata natsuwa da courage akan gallazawa Ameera sannan suka rabu akan sai tazo jibin.

Ameera tana shiga part d'inta ta hada ruwa mai zafi sosai tayi musu wanka dashi tare da shafa musu baby oil jikin su sosai sannan ta saka musu kayan sanyinsu,ta had'a musu madara ta basu suka sha suka koma bacci.

Saka su tayi agaba tana kallon yanda suke had'a gumi a goshinsu,sai a lokacin hankalinta ya k'wanta.

Tana zaune tana accusing kanta meye dalilinta na basu yaranta bayan tasan ba k'aunarta suke ba bare abinda ta haifa.

A yanda take jin yaranta a cikin ranta zata iya yin komai kuma da kowa da yayi niyar cutar mata dasu.

Har dare basu had'u da Lateefa ba ko wacce tana part d'inta.

Al'ameen yauma ya shigo da daddare duk suka isheta da fitina da shida twins,bata samu bacci ba sai kusan asuba.

Koda tayi sallahn asuba komawa baccinta tayi tare da tura Fadeel da Fadeela wajan Rabi dan tayi musu wanka.

Tana tsakiyan baccinta kaman daga sama taji saukan ruwan sanyi a jikinta Wanda yayi sanadin farkawarta agigice.

Lateefa ta gani tsaye a kanta rik'e da k'ugu tana girgiza cike da masifa.

Tashi Ameera tayi tana gyara zaman Rigan bacci ta.

Lateefa ta fara zuba mata ruwa bala'i.

"Samun guri da k'wanciyar hankali,iyyeh har baccin safe kika samu yanzu Dan kinga k'wana 2 ina d'aga miki k'afa kina jin kanki kamar wata toh bari in gaya miki as from now hutun da na baki ya kara daga yau zaki dawo bakin aikin kamar yanda kike da.ki wuce yanzu ki had'a min breakfast kuma 5 mins na baki just 5mins ko minti d'aya kika k'ara akai kema kinsan sauran".

Tunda ta fara magana Ameera take kallonta tana mamaki .

Ganin ta ida masifarta yasa itama ta shanye nata mamakin ta fara maida mata martani.

" na farko ke wacece wama ya baki izinin shigo min har bedroom saboda rashin tarbiya,maganan ina d'aukan kaina ni wata ce kinyi kuskure anan ni ba wata bace amma ina da matsayin da wasu suna nema da milliyoyin kudi amma basu samu ba,ni UWACE nayi miki gya..."

Lateefa al'ajabi ya gama daskar da ita ta NASA cewa komai sai ido da ta zuba mata amma kalamanta na karshe su suka harzuk'ata har ta d'aga hannu da niyan marinta amma Ameera tayi caraf ta rik'e hannun.

Tana murmushi tare da girgiza mata kai tace..." Don't ever make this mistake in ur life saboda in har baki rik'e girmanki ba ni kuwa zansa k'afa in taka ta"tana gama fad'an haka tayi jifa da hannun abinka da mai kib'a tayi tangal-tangal ta fad'a kan stool din gaban mirror Ameera har ta na buge goshinta.

Ameera ko kallonta bata k'arayi ba ta fad'a bathroom tare da bango mata k'ofa da karfi.

Lateefa jiki duk jiki yayi yayi tsami more especially goshinta har ya taso haka taja jiki ta fice mata a daki.

Al'ameen mamaki fal a ranshi wai Ameera ce tayiwa Lateefa haka,tayaya hakan ta faru?amma can k'asan zuciyar shi kuma dad'ine fal.

Basarwa yayi yana wani yamutsa fuska yace.."wacece haka sabuwar 'yar aiki kika samu?"

Farinciki ne ya lullub'eta ganin har yanzu asirin bai bar jikin shi ba.

" ka kirata yanzu ka korata gidansu dan nagaji da ganinta cikin gidan nan".ta fad'a in a commanding way.

Mik'ewa yayi ya nufi hanyan part d'inshi yace..."tunda a karkashin ki take ke ya kamata ki Kore ta bani ba dama me kike d'ebo 'yan aikinki".

Takaici duk ya cikata ta rasa ya zatayi can wata zuciyar yace ta k'ira k'annenta su dawo mana tasan su zasu iya maganinta.

Nan take ta k'ira Shamsiyya tana d'auka ta fara sauke mata bala'i da take dannewa a ranta.

"Bansan wani irin hankali gare Ku ba,in banda shashanci daga yiwa k'awarku aure sai kuje Ku tare mata a gida haka akeyi?toh ina gaya muku duk abinda kuke Ku bari Ku dawo gobe ina nemanku kuzo Ku min maganin k'aramar 'yar iskan gidan nan".

" Aunty wa kike nufi wai kuma meya faru?"

Nan ta basu labarin abinda ya faru tsakaninta da Ameera.

Fa'iza sai huci take har ji take kaman ta faso ta cikin wayan .

Hakuri suka bata suka ce gobe da sassafe zasu shigo su gyara mata zama.

Al'ameen daya sauk'o k'asa yaga Lateefa ta tashi bata parlour,bai tsaya bata lokaci ba ya fad'a part Ameera ya same ta tanawa babies d'inta wasa hankali k'wance .

K'arasowa yayi ya zauna tare da sa hannu ya d'auki Fadeela ya fara mata wasa yace...."Maman twins kin ganki kuwa kullum k'afa k'yau kike meye sirrin ne?"

Ajiye Fadeel tayi ta juyo gare shi haba d'aya tana fuskantan shi..." Kaine sirrin Yayana".

Kanne mata ido d'aya yayi yace..."kin tabbata?"

Dariya tayi tana gyad'a mishi kai.

Zama yayi sunsa yaransu a tsakiya suna ta hira,anan yaci abincin shi na dare.

Shi bai koma part d'inshi ba sai bayan sallahn asuba.

Wanka yayi ya shirya ya fita office.

Ameera zama cikin d'aki ita kad'ai ya isheta,yau suka fito ita da yaranta main parlour dan shan iska.

Canza channel tayi daga MBC Bollywood zuwa saudi2 tana sauraron karatun alqur'ani.

Bata dad'e da zama ba Lateefa ta fito tana yamutsa fuska.

Daram zuciyarta ya buga da karfin gaske ganin Ameera ta baje tana kallo.

Tana son tanka mata amma wata zuciyar ta hana ta ,kar ta gama zubar da ajinta bari ta hira zuwan su Fa'iza.

Kan dinning ta wuce ta fara breakfast tanayi tana satan kallon Ameera da take harkokinta ta d'auke kai kaman bata san da ita ba a parlour.

Tana mamakin yanda abin ya juye lokaci 1 haka kaman ba Ameerar da bata iya mata magana sai a duke ba kamar ba Ameerar da in ba cewa tayi tashi anan ba bata isa ta motsa ba kaman ba Ameerar da...shigiwar su Shamsiyya shi ya katse mata zancen zuci da take.

Suka wuce Ameera suna mata kallon banza ita ko ta bawa banza ajiyarsu.

Bayan kus-kus da sukayi da Auntynsu suka nufo ta gadan-gadan dai-dai lokacin kuma Fateema tayi sallama ta shigo.
🙆🙆🙆🙆🙆🙆

*UKUBAR KISHIYATA*

😭😭😭😭😭😭

(Its all about love and betrayal)

Story by *~UMMEE YUSUF~*

(Maman Yusuf)

*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION~*💫💫💫

https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~*


*_~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~_*

*part forty three*


Shigowan Fateema bai hana su Fa'iza k'arasowa gaban Ameera ba kowacce tana k'okarin kai mata bugu.

Da gudu Fateema tazo ta shiga tsakaninsu tana..."me zan gani haka wani irin dabbobi ne ku?"

Ameera ko k'ala bata ce musu ba saida ta k'washe yaranta ta kaisu safe place sannan ta dawo ta samu har sun fara gabazawa da Fateema,Lateefa tana gefe tana suyi kasa-kasa da ita sannan su bi Ameera data gudu.

Ameera tana zuwa batayi wata-wata ba ta finciko Fa'iza ta gashin kanta da yasha Brazil.

Ihu Fa'iza tasa tana neman k'watan kanta amma ta kasa ga bakinta yaki mutuwa sai zagi take aikawa Ameera.


Buge bakin zagin Ameera tayi da iya karfinta sai ga bakin yana tsiyayan jini,wancalar da ita gefe ta fad'a kan glass center table.

Kasa tashi Fa'iza tayi illa dafe goshinta tayi da yake ta zubar da jini tana kula.

Tana juyowa d'ayan side sai ganin Fateema tayi ta haye ruwan cikin Shamsiyya sai bugu take kai mata kota ina.

Murmushi Ameera tayi ta juyo arean dining inda Lateefa take zaune.

Suna had'a ido Lateefa ta mik'e jiki na b'ari tayi hanyan part d'inta dama a tsorace take tana mamakin wani irin karfine dasu duk sun raunata mata k'anne.

"Ina zaki je?ki tsaya ki nuna min jarumtar ki,ki tsaya nace".Ameera ce ke fad'an haka lokacacin da ta bin bayan Lateefa da gudu.

Tsantsin tiles ne ya k'washi Lateefa sai gata tayi zaman 'yan bori a kasa.

Dakewa tayi ta juyo ga Ameera duk da a tsorace take hakan bai hana ta fara cika baki ba harda zagi..."Dan ubanki karki ga ina kyale ki ina nan a Lateefa ta da kika sani ba zan tab'a canzawa ba Kuma dole ki kasance a karkashin iko na in mulke Ki dan Abu Kazan ubanki.."


Ameera batayi niyyana tab'ata ba amma jin zagin da take antayo mata yasa ta jawo wire receiver da yake gefen kayan kallonsu ta shiga lafta mata ta ko ina.

Lateefa duk iya kokarinta na ganin ta kare kanta kasawa tayi.

Ganin in batyi da gaske ba zata sha wiya,hankad'a Ameera tayi da duka karfinta tayi hanyan part d'inta da gudu.


Tsayawa Ameera tayi tana dariya har da fad'uwa kan kujera ganin yanda Lateefa take k'wasan gudu jiki na rawa.

Da k'yar ta d'aga Fateema akan Shamsiyya da tasha mazga.

Zama Fateema tayi tana huci tace..." Wallahi Aunty ke kike sake musu har suke k'okarin tab'a lafiyarki,wallahi kun ci sa'a yau ina cikin mutunci if not hmmm mayu duk kunsa min 'yar uwa a gaba ganin ba abinda 'yar uwarku ta iya sai katon kashi."

Ameera dai dariya take tayi mata tace..." Haba Fateema duk suburbud'an da kika yi mata kike cewa haka?"

Fa'iza da Shamsiyya da k'yar suka ja jikinsu suka fece daga gidan gaba d'aya ba tare da kowa ya lura dasu ba.

Lateefa tana cikin d'aki sai kaiwa da komowa take ta rasa me yake mata dad'i a rayuwa jikinta duk yayi rud'u-rud'u da shatin wire.

Waya ta d'aga ta k'ira Aina'u tasa mata kuka.

Hankali tashe Aina'u take take tambayar ta me yake faruwa?

Da'kayar ta tsagaita kukan ta bata labarin abinda ya faru dasu yanzu.

Ashar Aina'u ta fara d'urawa tana kunfan baki tace yau d'in nan zata taso wallahi sai sun koya mata hankali sannan su koma wajan boka yayi maganinta.

Da washe gari da sassafe Lateefa ta fita sannan ta k'ira Aina'u tace ta fito tazo su wuce.

Bata wani dad'e ba tazo ta same ta suka tafi.

******************

Dariya boka ya bushe da ita yana kallon yanda Lateefa da Aina'u sukayi tsuru-suru suna sauraron shi.

" dukansu 2 kike son akashe?"

Da sauri ta amsa da..."eh boka dan rayuwar yaran nan tashin hankaline a gare ni".

"Za'a kashe su duka amma ba yanzu ba sai mun tura bak'ak'en aljanu suyi ta azabtar dasu zuwa shekara d'aya sai a kashe su,kin amince da wannan shawaran?"

Cikin jin dad'i ta amsa.." Na amince boka dan ni hakan ya min dad'i sosai kuma boka ina son a mantar da Al'ameen yaran nan da ita uwarsu gaba d'aya".

Wani d'an k'aramin sanda da aka laulaye shi da guraye ya mik'o mata yace...bansan ya akayi kikayi sake har tasha abinda ya karya kusan duka sihirin da yake jikinta ba kuma a halin yanzu ba wani aljani da zai iya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login