Showing 60001 words to 62823 words out of 62823 words
Chapter 21 - UKUBAR KISHIYATA Sirrin Da Ya Rushe Aure by Ummee Yusuf
yace..." muje sweetheart".
K'wasan duka tarkacen su sukayi gaba suka bar mata k'aramar jakan kud'in.
Ita kuwa Lateefa tun daga nan bata san inda take ba sakaman yawan jini dake ta zuba a jikinta.
Ameera ce durkushe a gaban mijinta tana kallon da ya rine yayi ja kamar gauta..
Hankalinta ne ya tashi saboda bata tab'a ganin shi cikin irin wannan yanayin ba.
Cikin Sanyin murya ta fara tambayan shi meya faru?
Ya dafe goshin shi da hannayen shi duka 2 yana kallon kasa.
Ya d'ago yana kallonta,itama idonta taf da hawaye yace..."wani ne ya k'irani yake min maganan banza akan Lateefa har yake cewa in ban yarda ba inje in gani da idona".
"Maganan banza?wani irin maganan ne haka?" Ameera ta tambaya da alamun tsoro akan fuskarta.
Mik'ewa yayi zumbur ba tare da ya bata amsan tambayarta ba yasa kai ya fita da saurinsa.
Da kallo ta bishi tana addu'an Allah yasa lafiya.
Yana fitowa compound gidan Bala driver ya taso yana mishi magana ko kallan shi baiyi ba balle ya tanka.
Mota ya shiga ya fige ta da karfin tsiya ya fita a gidan.
Driving yake kaman zai tashi sama zuciyar shi kuwa a cunkushe take duk da yana shakkar abinda yaji a Waya amma wani bangare na zuciyar shi kuma ta yarda bisa la'akari da rashin kulawa da yake samu daga gare ta.
Cikin lokaci k'ankani ya iso hotel d'in ya fito a motan bayan yayi parking a parking space na hotel d'in.
Bugun zuciyar shi sai k'aruwa take a lokacin da yake duba numbers na d'akunan har ya kawo room number 35.
Cak ya tsaya yana fargaban bud'ewa dan bai San abinda idon shi zai gane mishi ba.
Haka ya daure ya kai hannu kan murfin k'ofan ya murd'a ya jiya a bud'e.
Turawa yayi ya shiga ciki tare da dube-dube.
Lateefa ya gani d'aure kan kujera cikin jini male-male bata cikin haiyacin ta.
Da gudu ya k'arasa wajanta yana ambaton sunanta tare da girgiza ta amma bata san ma yanayi ba.
Waya ya fito dashi ya k'ira Ya Sa'ad da shi,shi kuma yace ya fara k'iran police tukunna suna zuwa.
yana nan tsaye cikin tashin hankali dan ya rasa dame zai fasaara wannan al'anari.
Within 15 mins ambulance da police suka zo at d same time.
Bayan 'yan geaje-gwaje da bincike da police suka yi aka saka ta a ambulance akayi Hospital da ita.
Al'ameen shima motan shi ya fad'a ya bisu a baya.
Suna isa asibitin aka wuce da ita emergency,doctors kusan su hud'u harda Ya Sa'ad suka taru a kanta wanda a dole suke aikin saboda warin da jikinta yake fitarwa.
Mamanta ya k'ira ya sanar da ita abinda yake faruwa.
Cikin rud'u da gigita tace gata nan zuwa.
Iyayen shi ya k'ira suma ya sanar dasu,nan suka taya shi jimami tare da cewa suna zuwa .
Haka yayi ta sanar da duk wanda ya dace ya sanar,bayan ya gama wayar doctors suka fito da nasaran cewa an samu dakatar da jinin kuma anyi sa'a blood group d'inta A ne dan haka har an k'ara mata zuwa nan da 1 hr zata iya farkawa.
Godiya ya musu sannan yace zai je gida ya dawo.
Ameera tana zaune ita kad'ai a parlour ta rafka tagumi da hannayenta duka 2 .
Tana ganin shi ta mik'e da sauri ganin ya dawo kaman ba yanda ya fita ba.
A tare suka zauna akan kujera 2 seater yace ..." Ki shirya muje hospital "
"Hospital kuma meya faru waye ba lafiya?"Ameera ta katse shi da tambaya.
" Lateefa ce"ya bata amsa a gajarce tare da bata labarin abinda ya gani .
Salati ta rinka maimaitawa tare da mamakin waye yayi mata wannan aikin.
A gurguje ta gama shiryawa harda twins d'inta cikin kaya masu k'yau suka nufi hospital gaba d'ayansu.
A can suka tarar dasu Alhaji da sauran 'yan uwa duk sunyi jugum dasu .
Bayan sun samu waje sun zauna Hajiyar shi take tambayar shi ya akayi hakan ta faru?
Nan itama ya maimaita musu abinda ya gani.kowa ya rink'a tofa albarkacin bakin shi,sun d'an jima zaune suka hango Maman Lateefa wujiga-wujiga tana tahowa.
Idonta ya riga da ya rufe dan haka bata ma lura dasu ba har zata wuce Al'ameen yayi mata magana ta tsaya ta dawo wajansu .
Hajiyar Al'ameen ta sauke Fadeela dake kan cinyarta ta kamo hannunta suka zauna tare da tambsyar ya jikin'yarta?
Hajiya tace..."gamu nan dai muna jiran farfad'owarta dan sunce nan da awa 1 zata farka amma gashi har awa 2 ta wuce".
Kuka tasa tana..."dan Allah ku gaya min ko ta mutu ne?"
Hajiya ta bud'i baki da niyan bata amsa wata nurse tazo tana tambayar INA Al'ameen da Ameera?
A tare suka mi'ke suna kallonta.
"Ta farka kuma tace tana son ganin ku"
Gaba d'ayan su suka d'uru cikin d'akin.
A take sauran suka koma baya suna toshe hanci sakamakon warin da suka ji ya tare su.
Kuka take kaman ranta ya fita tana duban su d'aya bayan d'aya .
Cikin kuka tace..."Al'ameen,Ameera ku yafe min nasan alhakin kune yake bibiyata na cuci kaina na cutar daku a bata ta fanni da yawa".
Nan ta fara zaiyane musu abubuwan da ta shuka tun kamin auren ta da Al'ameen har zuwa yanda Al'ameen yazo ya same ta a hotel.
Tunda ta fara jawabin Al'ameen yake ji kaman ba shi ba kuma sai a lokacin ya fara tuno abubuwan da suka faru wanda da yake ganin kaman a mafarki ya faru ashe da gaske ne.
Wani irin tsanan ta ya rinka ji wanda baya tsammanin akwai wani halitta da ya tab'a tsanan abu kaman yanda ya tsani Lateefa ba a yanzu.
Rokonsu ta farayi tana magiya harda hawaye kan su yafe mata wanda Al'ameen yake ji kaman ruwan dalma take zuba mishi.
A zuciye Al'ameen yayi kanta ya shake mata wuya yanda ko numfashi bata iya shak'a nan da nan idonta suka firfito waje tare da firfitowa.
🙆🙆🙆🙆🙆🙆
*UKUBAR KISHIYATA*
😭😭😭😭😭😭
(Its all about love and betrayal)
Story by *~UMMEE YUSUF~*
(Maman Yusuf)
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~*
*_~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~_*
*part fiffty*
*last page*
Da gudu yayun shi sukayi kanshi suna kokarin b'anbare hannun shi daga wuyanta amma suka kasa.
Alhaji ne yazo ya k'washe shi da mari tare da hankad'a shi gefe.
Bango ya nausa da duka karfin shi na haushin bai samu nasaran halakata ba inama ace Alhaji baya wajan da sai ya raba ta da duniyan inyaso duk abinda zai faru ya faru.
Lateefa sai tari take Mamarta tana rik'e da ita gaba d'aya ta fita haiyyacinta.
Ameera tana gefe sarkin tausayi sai sharar hawaye take tace...Anty kiyi shiru ni kam na yafe m....".
Tsawan da Al'ameen ya daka mata yasa ta katse maganarta tana kallon shi a tsoro ce saboda a iya zamansu hakan bai tab'a faruwa ba.
"Baki da hankali ne?kina jin abinda tace ta aikata miki harda yaran mu da bakinta amma ki wani ce zaki yafe mata?" Ya k'arasa maganan cike da takaici yana huci.
Ta bud'i baki da niyar magana kenan police duka shigoda hakan kud'in da Sslees ya bar mata.
Gaishe da mutanen d'akin sukayi sannan d.p.o ya fara bayani kan cewa basu samu evidence d'in komai ba,da alama mutanen sunyi da gloves amma dai zasu cigaba da bincike har sai sun gano wanda yayi wannan d'anyen aikin.
Juyowa Al'ameen yayi wanda tunda suka shigo ya juya musu baya yace..."kaga d.p.kuyi tafiyarku ba sai kun wahala ba na yafe binciken Ku bar shi kawai".
"Amma yallabai aiko kace mu bari ba zaiyu ba saboda dole hukuma ta nemo mai laifi a duk inda yake a hukunta shi and ga kud'in da muka samu a d'akin" ya k'arasa gaban Al'ameen ya ajiye jakan.
"Ku d'auka bana bukata " yace Yana juya musu baya.
Matsowa d.o.p yayi yana..." A gaskiya yallabai ba zamu iya d'auka ba saboda...."
A harzuke ya juyo yace...." Nace ku d'auka in bakwa so ku jefar a hanya is not my problem but pls leave me alone ".
Alhaji ne yasa baki yace su tafi kawai tunda yace baya so.
D.p.o yace..." Shikenan Alhaji mun gode zamu tafi mu cigaba da bincike".nan suka juya suka fice,constable sai murna suke kaman suyi tsalle ganin makud'an kud'in nan ance ya zama nasu.
Suna fita Al'ameen ya dawo da duban shi kan Lateefa da ta gama shan jinin jikinta yace..." Kina wani cewa kin cuce mu toh ki sani bamu kika cuta ba face kanki kuma ba wajan Mu zaki nemi gafara ba sai wajan mahaliccinki Dan shi sab'awa ba wani ba,anan kuma a gaban kowa zan fad'a in Al'ameen na saki Lateefa saki 3...."
"Kai!!! Haka da hankali ne" Alhaji ya katse shi a tsawace.
Hajiya ce tayi saurin cewa..."haba ya zaka hana shi?wannan shine dai-dai da ita sai taje can ta samu irinta ta aura ba dai d'ana ba wallahi kuma tsakanin Mu dake Allah ya isa macuciya kawai".
Tana gama fad'anta ta fice a zuciye,alokacin ita da Alhaji ne kawai suka saura Dan Al'ameen da yayun shi sun dad'e da barin d'akin.
Alhaji ma fita yayi ba tare da yace komai ba saboda shima hukuncin yayi mishi dai-dai ya dai yi magana ne kawai a matsayin shi na babba a wajan.
Mama kanta a k'asa tayi shiru ba tace komai ba har suka gama ficewa a d'akin suka bata daga ita sai 'yar ta.
Ita kanta abin ya bata mamaki da takaici dan duo shekarun nan bata tab'a sanin wannan mummunan halin 'yarta ba,ta d'auka tunda tayi aure ta watsar da komai a titi ashe abin ba haka yake ba.
Jiki a mace Mama tace..."ina su Fa'iza ban gansu ko basu san abinda ya faru dake ba?"
Murmushin takaici tayi sannan ta bawa Mama labarin abinda ya faru dasu.
Kuka Mama take sosai irin kukan nadama nan.
Lateefa tana kallonta tace..."lokacin kuka ya wuce Mama tunda kece sila na duk wani rayuwa da muka tsinci kan mu a ciki,run farko me kika lalata mana rayuwa Dan muddin zamu kawo miki kud'i ba ruwanki komai ma muyi gashi yau wa gari ya wayewa? 'Yan Mayan ki 2 sun halaka ni da nake rayen ma gwara mutuwata kan rayuwar da zanyi a gaba".
Mama kass cewa komai tayi sai kuka da take rizga saboda ita tasanmaganar da Lateefa ta fad'a gaskiya ce da hannunta ta watsar da yaran ta gashi yau duniya da rayuwar sun juya musu baya.
******************
Driving yake cike da nishad'i sun taso daga night club ya d'an kalli inda take yace..." Swthrt yau jina nake wani fresh dani".
Dariya tayi tare da k'wantar da kan ta akan kafad'an shi tace..." Nima haka nake ji my love yanzu said Mu bud'e sabon rayuwa da zunzurutun kud'i naira million 150".
Dariyan mugunta ya k'washe da ita yace..."kuma a banza muka same ta ba?"
Hirar su suke sosai cikin jin dad'e har suka zo gidan su.
Masu gadi har 2 sukayi rige-rigen bud'e musu gate suka wuce ciki.
Wanka suka fara yi sannan Aina'u ta jera musu abinci akan table.
Bayan tayi serving d'in shi yace..." Me ba zaki ci ba?"
Girgiza kai tayi tace..." Zuciyar ta tashi take ba zata iya cin abinci ba ruwan Lipton zata sha tasa ruwa a kettle.
Salees ya fara cin abinci suna hira yanda gobe zasu kai kud'ad'en su bank.
Aina'u tace..." My love dole Mu raba k'afa in ba haka ba akwai matsala.
D'an dariya Salees yayi sannan ya d'auki ruwan dake gaban shi ya shanye tare da ture gutun abincin da yake gaban shi ya dube ta yace..." Me meye tabbacinki na zan sure ki da har kikayi saurin amincewa haka?Ku mata k'wak'walwan Kifi ne daku,ita da taci amanar mijikin ta ta fifitani akanshi bai hana ni ci mata mutunci da wulakanta ta ba sai ke?kema kin San banida mutunci ko kad'an more especially akan money"
Murmushi Aina'u tayi tana kallon shi ko d'ar babu azuciyar ta tace..." Na sani ba sai ka tuna min ba kai kare ne mara mutuncti how can I trust u? But tunda kaci abincin nan plan na ya taxi dai-dai saboda ko 10mins ba zakayi a raye ba balle evil plans d'inka suyi aiki a kaina" ta k'arasa tana yi mishi dariyan mugunta.
Dariyan shima ya cigaba da taya ta dashi yace...." Wow!!! Kin birge ni sosai but u re too late ".
Had'e rai yayi kaman ba shine yake dariya yanzu ba
Pistol ya zaro daga aljihun wandon shi kamin Aina'u ta ankara ya d'auke goshin ta dashi.
Nan Aina'u ta fad'i ko shurawa ba tayi ba.
Tashi yayi yazo gaban trolleyn kud'in ya bud'e ya durkusa a gaban yana dariya yana shafa kud'in yana aiyana yanda plan d'in shi ya tafi kaman yanda ya tsara saboda yayi imanin Aina'u a yanda take matukar son shi ba zata iya Sa mishi wani abu a abinci ba.
Tari ya fara yi babu kakkautawa jini ya fara fitowa daga baki da hancin shi.
Nan ya fad'i yana shure-shure mutuwa ko minti 2bayi ba ya sandare a wajan .
Parlour ne ya fara tururin hayaki ,ruwan zafin da Aina'u ta saka a kettle ya kone adalilin haka wuta ya kama gadan.-gadan.
Kamin masu gadi su ankara had wutan yaci karfin gidan.
Fire fighters sunyi nasaran kasbe wutan amma Aina'u da Salees sun zama toka.
Lateefa da Mamar ta sun koma zariya sakamakon Koran kre da akayi musu daga asbitin Ya Sa'ad.
Lateefa taga rayuwa kasancewar ta zama mai larura ga rashin hannu ga gyabonta da kullum k'ara gaba yake dan haka a waje tske k'wana Mama taki yarda su k'wana d'aki 1a Cesar ta zata iya mutuwa in suka zauna wake 1.
Ko tana nema taimako ba mai taimaka mata duk sanyi da iska hard a damina akan ta suke k'arewa,in mutum ya ganta sai ya rantse da Allah ba Lateefa bace 'yar k'walisa tayi kuka har ta saddakar.
Yanzu sosai abin nata yayi gaba saboda har kayan cikinta ya tab'a bata iya ci balle sha.
Tana jefe a cikin gidan sauro ba mai kula ta had tsutsosi saida suka fara cinyeta.
Kwana 2Mama bata ji motsinta ba tazo ta duba ta taga ashe rai yayi halin shi da dad'ewa dan harta fara kumburi.sakamakon in da gyambon ta yake fitarwa shiyasa basu lura da mutuwar ta balle suji warin gawa.
Allahu Akbar!!! Shiyasa ake so mutum ya shuka khairi in kayi akasinta kuma tun a duniya zaka fara gani kamin muje kiyama.duk abunda mutum zaiyi ya tuna akwai Allah yana ganin mu kuma mu kuma mutuwa dole zata riske Mu ko kana so kp baka so.Dan haka Mu koyi rungumar kaddara a rayuwa mai dad'i ko akasinta Mu kai zuciya nesa.*ALLAH KA SHIRYA MANA ZUKATAN MU AMEEN.
Al'ameen sabuwar rayuwa mai tsabta suke shida Ameerar shi da k'yawawan twins d'in su hankali k'wance.
Duk Wanda ya gan shi zai San ya canza daga Al'ameen d'in baya.
Iyayen shi sunfi kowa farinciki saboda kullum said yaje ya gaishe su ga 'yan uwan shisuna zumunci sosai bakaman da sai sunyi kusan shekara basu ganshi a gidajen su ba.
Katafaren Gida Nagani na fad'a ya ginawa iyayen Ameera suka koma, aciki akayi auren Fateema,ta samu miji na gari a can garin gombe ba laifi shima yana da rufin asiri rayuwar suke gwanin sha'awa.
Matan Yayun Al'ameen su duka 3 suka kawo musu ziyara da yaransu suka wuni har dare mazajen su suka zo d'aukansu .
Nan ma suka dasa Sabon hira sannan suka raka su har bakin mota,basu bar wajan ba har saida suka ga tafiyarsu.
Shigowa parlour sukayi tare da twins d'insu da suka k'ara girma da wayo nan suka zube kan kujera Ameera tace..."wash na gaji".
Hararan wasa ya aika mata yana..."gaya min aikin da kikayi harna gajiya"?
Cike da shagwab'a tace" haba Yayana ai wayan nan ma sun isa su gajiyar da mutum" ta k'arasa rana nuna twins da hannu.
"Kuma fa hakane amma kin san me? Ya kamata ace suna dak'ani". Yace yana d'aga mata gira 1.
" kani!!! Haba wallahi saina huta".
"Wani Hutu kuma yara sun kai 3 years?" Yace yana tsare ta da ido.
Cunno baki tayi ta juya mishi bata tana..." Ni kam ban shirya ba".
Dariya yayi yana.." zaki ga shiryawa yarinya".
K'iran twins yayi yace suje wajan Rabi ta basu ice cream su sha.
Da gudu sukayipart d'in masu aiki suna tsallen murna.
Tana ganin haka tasan nufin shi dan haka da gudu ta tashi tayi hanyan part d'inta tana dariya
Shima mara mata bata yayi yana dariya yana "baki isa ba yarinya" kamin ta kai har ya kamo ta ya daga ta sama yana juyi da da ita suna dariya.
*tammat bi hamdullilah*
Alhamdulillah INA mika godiya ga rabbi da ya nuna min karshen novel d'ina lafiya kaman yanda na fara shi lafiya.
Ina godiya gare Ku my fans na yanda kuka rinka bibiyar novel nan tun daga farko har karshen ta.INA mai Baku hakuri akan masu msg both fb and watsapp in kuka ga banyi reply ba toh abinne yafi karfina amma ina son Ku Sani INA kaunar Ku sosai fiye da tunanin saboda in babu Ku babu ni luv u all.
My special thanks goes to big brother *UMAR DALHA*
Godiya da jinjina zuwa ga *SIS NABEELERT* golden pen tana matukar alfahari daku without u guys things seems to b difficult..
Ban manta daku ba yan *GOLDEN PEN* kun amsa sunan Ku golden saboda yanda kuke haskawa a ko INA kun fita daban Allah ya kara baseera da karfin ido.
At d end INA rokon Allah daya nuna mana azumi lafiya tare da wadata Ameeen.