Showing 45001 words to 48000 words out of 62823 words
Chapter 16 - UKUBAR KISHIYATA Sirrin Da Ya Rushe Aure by Ummee Yusuf
haihuwan balle in samu daman aikata abinda nayi niyya.ga cikin shima yaki lalacewa sai dai kullum tana d'aki tana murkususu".tace cike da damuwa.
Tunda ta fara Aina'u take kallonta,bata katse ta ba sai da ta kai aya sannan tace.." Wallahi kina bani mamaki yanzu ,Lateefa kaman ba kece mai bani shawara ba da komin saukin abu yanzu sai ki kasa samun bakin zar....."
Katse ta Lateefa tayi da..." Ke ni dan Allah ki bar surutun nan ki bani shawara insan abinyi dan ni kaina ya kulle na rasa wani irin tunani zanyi".
Aina'u saida ta numfasa tace..." Abune mai sauki Besty tunda kina da kudi,abinda zakiyi gobe ki samu private hospital mai k'yau ki kaita a matsayin kin kaita haihuwa daga nan ki samu babban doctor ki lallab'ashi ya mata alluran da zata shek'a kowa ya huta".
Zaro ido Lateefa tayi tana kallonta tace..."Aina'u so like asirina ya tonu?wani doctor zaka kaiwa wannan babban al'amari ya saurare ka?"
Aina'u cikin k'wanciyar hankali take cin naman kaza dake gabanta tace..." Dad'ina dake saurin karaya,a duniyan nan wa zaik'i kud'i?millions zaki bashi nasan tabbas da gudu zai share miki hawaye nima zan shigo goben sai mu kaita tare,kada kiji wani abu saboda inaji a jikina matsarki tazo karshe".
Haka tayi ta bata shawara tare da karfafa mata guiwa harta amince sannan suka rabu akan sai gobe ta iso.
Sai bayan 5:39 Lateefa ta dawo gida, ko ta kan Ameera ba tabi ba tana jiran wayewar gari su aikata barza'u.
Ameera cikin baccinta ta fara mafarkin tana jin wani azaba a mararta tun tana daurewa har ta fara juyi na azaba.
Wani irin juyi taji cikinta yayi wanda yayi sanadiyar farkawanta ba shiri,kuma sai a lokacin ta tabbatar ashe ba mafarki bane a zahiri take ji ga jikinta duk ya b'aci kaman na lokacin da Lateefa suka d'ura mata magani.
Addu'a ta farayi tana hawaye tana cewa a ranta inama ace rana ne da Baba mai gadi yayi mata tofi ta sha ko zata daina jin wannan azaban.
D'ago kai tayi tana kallon wall clock dake manne a d'akinta taga 1:30 na dare.
Tun tana hawaye tana add'uoi har hawayen suka kafe bakin ma ya mutu murus saina zuci da take.
K'ara kallon agogon tayi taga 2:00 ne kawai.
Cikin wani wahalalen murya tace " wayyo Ummata ki yafe min nasan yau mutuwa zanyi.
Gumi duk ya wanke mata jiki kaman ba a.c a d'akin.
Ita kanta ta tabbatar ciwon yau da take ji ya nika wanda da take ji da nikin ba nikin.
Har karfe uku da rabi tana nan zaune ko k'wanciya ta kasayi balle wani abu wai shi bacci gashi yau Al'ameen bai shigo ba da ya taimaka mata.
A lokacin ne kuma taji fitsari ya cika mata Mara.
Yunk'ura tayi da niyan tashi amma ta gagara da haka da rarrafe ta k'arasa bathroom danyin fitsarin amma abin mamaki ta kasa tsugunawa.
Zamanta tayi dirshan a cikin bathroom d'in tare da mimmike k'afa.
Yunkura tayi da niyan fitsarin amma taji wani abu daban da bata san dame zata k'watanta shi ba yazo ya danne ta ga wani azaba da tunda tazo duniya ko labarin shi bata tab'a jiba take ji.
Fasa fitsarin tayi tana yarfe hannu ta rasa ina zata saka ranta taji sanyi.
Sau uku tana gwadawa amma sai ta kasa na hud'une taji wani nishi mai karfi yazo mata wanda saida ta toshe baki da hannu dan ji take kaman ta k'wala ihu saboda zaba.
Maimakon taji tayi fitsari sai jin wani abu daban tayi ya fad'o harda kuka.
A firgice ta kalli wuri yaro ta gani fari sol dashi.
Mamaki da tsoro ya hanata tab'a yaron.
A wautarta bata San cewa labor take ba ta d'auka irin ciwon nan me da take yi yana lafawa.
Zuba mishi ido tayi tana kallon yanda yake tsotsan hannu tare da bin bulb light dake bathroom d'in.
Sababbin azaba ta fara ji tana juye-juye,ba'a d'auki lokaci ba ta sankato da baby girl.
Cikin ikon Allah tare da mabiyan suka fad'o ta fara cancara kuka.
Motsi mutum taji a cikin d'akinta wanda ya haddasa mata tsoro da fargaba.
Motsin na kara kusanto bathroom d'in yayin da zuciyarta me kara lugude.
Ba kowa take tsoro ba illa Lateefa,cikin daren nan ta same ta da yaran nan komai zai iya faruwa.
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
πββπββπββπββπββπββ
*~UKUBAR KISHIYATA
ππππππ
(Its all about love and betrayal)
Story by *~UMMEE YUSUF~*
(Maman Yusuf)
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATIONπ«π«π«~*
*~βWe beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u no pain~*
*part thirty nine*
Knocking k'ofan bathroom d'in taji anyi wanda saida hanjin cikinta ya kad'a saboda tsoro.
Murya k'asa-k'asa taji yace..."Babyna are u alright? "
Ajiyar zuciya ta sauke mai nauyi sannan ta saita muryanta da ya dashe tace..."Yayana kaine a wannan lokacin?"
"Mafarkai nake tayi akanki shiyasa na kasa daurewa nazo in duba lafiyarki".
Murmushi tayi jin furucin shi tace..." Ka shigo mana".
"Me kike yine a cikin bathroom at this time har kike cewa in..." Maganan ce ta mak'ale mishi a mak'ok'oro ganin Ameera zaune da 'ya'ya 2 a tsakanin k'afanta.
Da sassarfa ya shigo ciki jikinshi har b'ari yake.
Idon shi cike da kwalla ya tsuguna kusa da ita.
Hannun shi yana karkarwa ya kai yana shafasu cike da so.
Juyowa yayi yana kallon Ameera da hawaye shame-shame a fuska dan yama kasa magana.
Girgiza mishi kai tayi tana murmushi,kasa daurewa yayi ya jawota jikinshi ya rungume yana kukan farincikin k'yautar da Allah ya bashi,yau shekara goma sha hudu da wani abu da yin aure bai samu haihuwa sai yau.
Wani sabon k'aunarta yake jin yana ratsa ko ina na jikinshi.
Da k'yar Ameera ta k'wace kanta tace.." Yayana ya isa haka,kaji ana kiran an k'ira sallah tashi ka tafi massalaci".
Girgiza mata kai kawai yake yana k'ara matse ta a jikinshi.
"Pls ka tafi zaka makara a jam'i don't worry we will be fine".
Da k'yar ta samu ya sake ta ya nufi hanya fita,har ya kai bakin k'ofa ya dawo yace..." Kin iya yanda ake yankan cibi?"
"Ban iya komai ba amma ka bani Waya in k'ira Umma dan ta iya har gida ake zuwa ana kiranta tana taimakawa masu haihuwa".
Bata gama rufe baki ba ya fita da gudu ya d'auko mata wayan ya bata.
Wajan da yaran yaje India suke k'wance suna tsoson hannu.
Shafa gashin Kansu dake k'wance har wuya ya shiga yi,dariya ce ta tsubuce mishi wanda baisan lokacin da yazo mishi ba ji yake kaman ya maida su ciki yake jin.
Dawowa yayi ya k'ara k'amk'ame Ameera yana mata godiya tare da kissing d'inta ko ta ina.
Da sud'in goshi Ameera ta samu ta kora shi massalaci dan har an tada iqama lokacin.
Number Fateema tayi dialling,a lokacin Umma ta shigo tashinta yin sallah.
Ido ta zaro tana kallon Umma tace..." Umma Ameera ce fa".
"Ameera kuma da asuban nan,lafiya kuwa?"Umma ta tambaya da damuwa k'arara akan fuskarta.
" wallahi bansani ba nima"ta amsa itama cikin damuwa.
"Yi maza ki d'auka inji ko lafiya ".
Fateema tana d'agawa tace..." Aunty lafiya kuwa?"
"Lafiya lau" Ameera ta bata amsa sannan ta cigaba ..."ina Umma?"
"Gata nan,ko in bata wayan?"ta tambaya.
Amsawa tayi da a bata d'in.
Mik'awa Umma tayi tace" ke take nema".
Karb'a Umma tayi tasa a kunnenta tace..." Ameera lafiya kira da asuban nan?"
Gaisheta ta farayi,Umma ta amsa cikin kotsawa dan ita ba gaisuwarce a gabanta dalilin k'iran take son ji.
"Umma in kinyi sallah Ku taho yanzu".
A rikice Umma tace..." Inzo yanzu lafiya?"
A kunyace tace... " Umma ban iya yanke cibi bane kuma....kuma..."sai tayi shiru.
A take damuwar kan fuskarta ya koma fara'a tace..." Masha Allah!! tun yaushe kika haihu?"
Murmushi kawai tayi ba tare da tace komai ba .
Umma tace.." Toh gamu nan zuwa amma kamin zuwan Mu ki samu towel ko zani ki lullub'e su saboda iska".
"To Umma sai kun iso" nan sukayi sallama ta ajiye wayan.
Umma ta juyo tana kallon Fateema da take dariya alamun taji zancen ba sai an mata k'arin bayani ba.
Had'a rai Umma tayi tace..."ba washe baki zaki tsaya yiba,yi maza ki yi sallah Mu tafi".
Da gudu Fateema ta d'auki buta tayi bayi.
Al'ameen yana idar da sallah ya dawo wajan 'ya'yanshi ya saka su a gaba yana kallo.
Saida tace mishi Umma da Fateema suna hanyan sannan ya hak'ura ya tafi part d'inshi.
Ya fita bai jima ba su Umma suka iso.
Umma ganin jikoki har 2 a lokaci 1 yasa ta kasa rufe baki sai sannu take ta hero mata.
Yanke musu cibi Umma tayi tare da musu wanka ta nannad'esu cikin d'an k'walin Ameera kasancewar ko wando ba'a saya ba.
Itama mai jego Umma ta had'a mata ruwa mai zafi sosai tayi mata wanka tayi fes da ita kaman ba ita ta haiho yara 2 nan ba.
Fateema kasa ajiye su tayi, tana rungume dasu saii jijjigasu take.
Suna zaune suna hira Rabi ta shigo dan dubata.
Turus tayi tana kallon su cike da al'ajabi tace..." Ikon Allah mu da muke cikin gidan ma bamu san anyi haihuwa ba,har kuda kuke nesa kunji kun iso?"
Umma ta dubi Ameera tace..." Dama 'yan gidan naku basu san kin haihu ba?"
Girgiza kai tayi tare da sadda kai k'asa tana murmushi.
Ladi tana k'arasowa ciki tace.." Da mun sani ai anan zaki same mu Hajiya".
Hannu tasa ta karb'i d'an dake hannun Fateema tana kokarin zama ta hango wani jaririn akan gado.
Fara'arta ne ya k'aru tace..." Dama wai 'yan biyu ne?"
Dariya Umma tayi tace..." Wancan kishiya ce shiyasa kika ganta a yashe".
Dariya suka k'washe dashi dukkansu,Rabi tace.." Ungo mai gidanki dan ni k'awata zan d'auka"
Nan ma dariyan suka saka.
Saida suka tab'a hira mai cike da bark'wanci sannan Rabi ta fita zuwa kitchen dan had'owa mai jego da bakinta abin kari ta kawo musu sannan ta fara had'a na masu gidan
Al'ameen tunda ya koma part d'inshi ya kasa zaune balle tsaye sai zagaye d'akin yake yana ta buga waya yana fad'awa 'yan uwa da abokan arziki.
Jinshi yake kaman anyi mishi albishir da gidan aljanna.
Sallahn nafila ya rinka jerowa yana mik'a godiyarshi ga Allah na nuna mishi wannan babban rana a rayuwarshi.
Wanka yayi ya shirya dan tafiya office.
Lateefa yau bata samu baccin safe ba dan ta k'wana da maganan da sukayi da Aina'u a ranta.
Tana zuwa parlour taga kan dinning wayan ba komai.
Bud'e murya tayi ta fara k'walawa Rabi k'ira.
Da sauri Rabi ta iso gabanta ta zube a k'asa tace..." Gani Hajiya".
"Wani irin rashin mutunci ne yasa har yanzu baki gama breakfast ba?" Ta tambaya tana harararta.
Rabi kai na kasa tace..." Kiyi hak'uri Hajiya gidan ne da baki shiyasa".
"Baki,wani irin baki kuma ya ban gansu ba?"
"Suna can sashin Amarya" ta bata amsa.
Zuciyarta ne ya buga da karfi can kuma wata zuciyar tace..."ko Allah ya takaita mata wahala ta shek'a cikin dare.
Atake taji wani dad'i ya ziyarci zuciyarta,tana murmushi tace..."meye ya faru a part d'in nata?"
" *HAIHUWA* tayi Hajiya"Rabi ta bata amsa.
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
πββπββπββπββπββπββ
*~UKUBAR KISHIYATA
ππππππ
(Its all about love and betrayal)
Story by *~UMMEE YUSUF~*
(Maman Yusuf)
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATIONπ«π«π«~*
*~βWe beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u no pain~*
*part forty*
Wani abu mai kama da mashi Lateefa taji ya soke ta a kirji,ga wani d'aci daya taso mata Wanda bata san ta ina yazo ba saiji tayi ya cika mata mak'ok'oro.
Da k'yar ta saita kanta gudun kada Rabi ta fahimci halin da take ciki tace..."naji tashi ki tafi ki k'arasa aikinki"
Mik'ewa Rabi tayi tana dariya a cikin ranta tace..."duk *UKUBAR* da zaki gana mata baki isa ki canza abinda Allah ya tsara ba.
Rabi tana b'ace mata ta fad'a kan kujera ta baya dab'as ta zauna dan dama jiri take gani daurewa kawai take..
Ta rasa wani irin tunani zatayi,wani sashi na zuciyarta yace kije ki gani da idonki kamin ki yanke hukunci.
A zabure ta mik'e kaman wacce aka tsikarawa allura tayi part d'in Ameera.
Tana shiga ta samesu sun saka kayan breakfast da Rabi ta kawo musu a gaba Umma tana yiwa Ameera fad'an ta shanye tea d'in da ta had'a mata.
Zama tayi kusa da Ameera tana dariya wanda yayi kama da mai nishin kashi.
Gaida Umma ta farayi sannan ta juyo tana duban Ameera tace... "Haba k'anwata muna cikin gidan nan amma ki haihu ke kad'ai ba k'ya tsoron wani abu ya faru dake?"
"Yanzu na gama yi mata fad'a kada ta sake irin wannan koda a gaba ne"Umma tace mata.
Lateefa ji yayi kaman an watsa mata tafashasshen ruwa ajiki.
Tana yiwa Umma wani irin kallo ta k'asan ido kuma tana magana a zucoyarta tace kaji min munafukar tsohuwar nan har wani haihuwa 'yar taki zata k'arayi a gidan nan wannan ma sakaci nane but zan baku mamaki a gaba.
K'ara had'iye damuwarta tayi tace..." Ina jinjiran ko jinjiri muka samu?"
Umma ce ta bata amsa da.."gasu can kan gadi"
Cike da fargaban me Umma take nufi gasu can ta juyo ta dubi kan gadon.
Idanunta kusan zazzagowa suka yi ganin twins a kan gado,zuciyarta kuma kaman ya fashe take ji.
Da k'yar ta daure ta rarrashi kanta ta mik'e ta iso bakin gadon tana lek'ensu.
Wannan karan da k'yar ta hana bakin ta kurma ihun da yazo mata ba shiri.
Umma da Fateema suna cin abinci basu lura da yanayinta ba amma Ameera tana kallonta ta k'asan ido.
Ko d'aukansu batayi ba tace..." Ina zuwa ta fice cikin sauri saboda ta tabbata tana k'ara minti 2 a gaban yaran nan zata iya aikata abinda bashine ba a gaban mutane.
Tana fita yayi daidai da sauk'owar Al'ameen daga part d'inshi.
Ya lura da yanda ta birkice amma ya basar yace.." Ya naga kan table bakomai ko masu aikin basa nan ne?"
Da gudu Lateefa tayi kanshi tare cin k'walan rigan shi tana jijiga shi ta fara bala'i.."Al'ameen wallahi kayi kad'an ka wulakantani a gidan nan daga kai har ita baku isa komai a wajena ba,munafuki kawai in banda munafurci kaida nayi maka iyaka da wannan yarinyan ta yaya ka ka tsallake kaje kayi mata ciki? Iye tambayarka nakeyi"
Murmushi kawai Al'ameen yake yana kallonta,a haka Aina'u ta shigo ta same su.
Da k'yar Aina'u taja ta zuwa part d'inta.
Gyara zaman rigan shi yayi ya shige part d'in Ameera hankalin shi k'wance.
A parkour ya iske Umma da Fateema suna kintsa mata.
Durk'usawa yayi har k'asa ya gaida Umma,Fateema ma ta gaishe shi sannan ya wuce ciki bedroom inada Ameera da twins d'inta suke.
Ameera tasa twins a gaba tana ta kallo tana mamakin wai a jikinta suka fito.
A haka Al'ameen ya shigo ya same ta.
Zama yayi a bakin gado suka sakarwa juna murumushi ya shafa gefen fuskarta yace..." Maman twins kinyi kokari ya jiki ?"
"Da sauki" ta bashi ansa.
D'aukan Baby boy d'in yayi yayi mishi hud'uba yayi pecking goshi shi sannan ya rungume shi yana k'ara jin k'aunar yaron yana ratsa ko'ina a jikin shi.
Da k'yar ya ajiye shi sannan ya d'auko Baby girl itama yayi mata d same thing ya ajiye ta.
Yana juyowa yaga Ameera ta zuba musu ido tana murmushi,gira d'aya ya d'aga mata yace..." Ya dai?"
"Bakomai kallo nake" ta bashi amsa tana murmushi.
Dungure mata kai yayi yana dariya yace ..." 'Yar sa ido kawai".
Dariya itama tayi batayi magana ba.
Nan yake tambayarta abinda ya kamata ya sayo musu.
Cewa tayi ya tambayi Umma ta gaya mishi.
"OK ke bazaki gaya min ba?"ya tambayeta.
Amsa mishi tayi da..."kasan tafini sanin abinda ya dace".
" hakane,na tafi saina dawo"yace tare bata Peck sannan ya fito parlour wajansu Umma.
Dukawa yayi ya tambayi Umma abinda ya dace ya sayo,nan tayi mishi bayanin abubuwan da ya dace ya sayo irinsu madaran da zasu sha towels,kayan sawa,kayan sanyi da sauransu.
Ya mik'e da niyan fita Hajiyar shi tayi sallama ta shigo.
Komawa yayi ya zauna suka gaisa ya mata jagora zuwa d'akin mai jego sannan ya fita siyan abinda aka lissafa mishi.
Lateefa tana zaune sai cika take tana batsewa tana ciccize leb'e.
Aina'u tace" wai meya faru na ganki haka,ki tashi tunda ya fita mu kai shegiya ayi mata alluran mu huta".
"Komai ya lalace Aina'u komai ya wargaje"
Cikun rashin fahimta Aina'u take kollonta tace..."bangane komai ya lalace ya wargace ba".
Murmushin takaici Lateefa tayi tana kallonta k'awarta tace.."ta haihu,ta haifi 'ya'ya har 2".
D'ora hannayenta duka 2 Aina'u tayi tana salati tace..."2? Lateefa bama d'aya ba?"
"Saima kin gansu zuciyarki zata iya bugawa" Lateefa tace tana goge hawayen daya zubo mata.
"Haba dole in ganki cikin tashin hankali,kuttt ya akayi kika bari ta haihu baki kashe shegiya ba?" Aina'u ta tambaya cikin tashin hankali.
"Cikin dare ta haihu kawai ganinta nayi yara da safen nan,ita kuma munafukar uwarta harda cewa nayi mata fad'a haihuwa ita kad'ai koda gaba ta nemi mutum kusa da ita" ta karasa maganan cikin k'waikwayon muryan Umma.
"Kaji 'yar abu kazan uba,kinsan abinda zamuyi wajan boka zamu koma ya kashe yaran shima munafikin mijin naki muyi maganin shi ya kasance naki ke kad'ai".
Ajiyar zuciya Lateefa tayi tace..." King Aina'u na fara tsinkewa da al'amarin nan kuma...."
Pls kuyi manage da wannan.
ππππππ
*UKUBAR KISHIYATA*
ππππππ
(Its all about love and betrayal)
Story by *~UMMEE YUSUF~*
(Maman Yusuf)
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION~*π«π«π«
β *~we bearer's of golden writer's assiduously percieven No pain so Magical our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u no pain~*β
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*Part forty one*
"Ke dallah dakata" Aina'u ta katse ta tana huci.
"Karki bani kunya mana sai kace ba Lateefa 'yar k'walisa ba,ta yaya zaki basu chance suyi winning akanki.just ki bani wuka da nama kiga abinda zai faru but for now dole ki daure zuciyarki karki sake ki nuna musu ba k'ya farinciki da haihuwan nan yanda koda daga baya wani abu ya faru ba wanda zai zarge ki.bayan suna sai mu koma wajan boka"....
Lafuza da shawarwarin Aina'u sunyi tasiri wajan k'wantarwa Lateefa hankali tare da d'aukan alkawari zata daure ayi komai da ita.
Al'ameen yana fita wani babban shopping mall da ake saida kayan babies suka je shida driver.
Kaya Al'ameen yake ta k'wasa kaman ba gobe,yawanci bala ke nuna mishi abinda ya dace ya saya kasancewar shi yana da yara har 3.
Saida suka cika trolley 3 da kayan babies sannan suka dawo gida.
A lokacin gidan a cike yake tap da 'yan barka,kama daga matan brother's d'in Al'ameen da 'yan uwan Ameera duk sun iso gani.
Haka gidan ya kasance kullum cike da 'yan barka.
Lateefa ta daure zuciyarta akayi ta hidima da ita mutane sai yabon k'yan halinta suke.
Ranan suna yara suka cika sunan parents d'insu wato Mudassir mai sunan Alhajin Al'ameen sai Hadiza wacce taci sunan Umma Ameera.
Anyi shagali kaman ba gobe an bawa naira kashi sosai kowa da yazo