Showing 57001 words to 60000 words out of 62823 words

Chapter 20 - UKUBAR KISHIYATA Sirrin Da Ya Rushe Aure by Ummee Yusuf

29 Jul 2026

42

tafi hospital taga doc ko zata samu maganin wannan bala'in da boka ya had'ata da shi.

Da washe gari da sassfe ta saka kai ta fice daga gidan dan zuwa hospital ba tare da kowa ya ganta ba.

Wani private hospital taje cikin sauki ta samu ganin doctor saboda warin jikinta duk inda taje bata hanya ake.

Tana yi mishi bayanin matsalarta amma ji yake kaman ya fita ya bar mata office d'in.
Daurewa yayi ya nuna mata gado da yake cikin office d'in yace ta hau ta k'wanta ya duba ciwon.

Hand gloves ya saka tare da rufe hancin shi da abin rufe hanci sannan yaje kanta ya tsaya a k'yamace ya mata nuni da ta d'aga rigarta ya gani.

Da gudu doctor ya fita a office d'in yana kwara amai kaman ranshi ya fita sakamakon ganin ciwon Lateefa da yayi.

Da ido tabi shi zuciyarta na suya lalle boka ya gama cutarta yasa ta zama dodo a cikin mutane.

A sanyaye ta tashi zaune tana gyara rigarta wasu securities 3 suka shigo suka tasa keyarta gaba har bakin motarta..


Shiga tayi ta tayar da motarta ta fita a asibitin ga hawaye sai tsere suke a idonta.

Tunani take a zuciyarta na ta tafi wani asibitin ne kota ta fita abroad?

Zuciyarta yafi amincewa da ta fita abroad d'in dan haka ta juya kan Motan ta tayi hanyan gida.

Tana tafe tana zancen zuci,tana gwara da tayi dabara ta bawa Salees kud'inta yana juya mata su gashi yanzu sai ta karb'i abinta taje ayi mata maganin fitinan da boka ya had'ata dashi.

Tsaki taja ganin yanda hold up yayi yawa yawanci 'yan zuwa aiki da makaranta sunfi yawa.

Juyawar da zatayi kaman daga sama taga Aina'u cikin wata luxurious car sabo dal sai sheki take.

Murza idonta tayi Dan tabbatar da gaskiya idonta yake nuna mata ko dai Aina'un da ta sani ne?

Sauke glass na window motarta tayi tana k'wala mata amma bata jiba saboda ita glasses nata a rufe suke.

Har tana shirin bud'e kofar mota ta fita taga taja motarta tayi gaba.

Da sauri ta fad'a nata tabi bayanta.

Tana bin bayanta taga Aina'u ta tsaya a wata lafiyyar gida madaidaici mai d'an karan k'yau.

Tun kamin tayi horn mai gadi ya bud'e mata gate ta shiga ciki.

Tana shiga ya mayar da gate ya rufe.

Da gudu Lateefa ta fito a nata mota ko kashewa bata tsaya yi ba tabi bayan Aina'u ta shiga ta karamin k'ofa tana kwala mata kira.

Juyowa kawai tayi tana kallonta fuska a had'e kaman an aiko mata da sakon mutuwa,ba tare da ta amsa ba har ta karaso kusa da ita tana haki da fara'a akan fuskarta.

Hanci Aina'u ta toshe tana komawa baya tana mata kallon wulakanci da kyama tace..." Lafiya kike kwala min kira haka?"

Hawaye ta fara tana..."Aina'u kin ga abinda boka ya min kin ga yanda ya maida ni na zama abin kyama a cikin mutane kowa ya ganni sai ya toshe hanci,kema kulum ina ta trying number ki bata shiga. Nayi ta jiran kiranki kaman yanda kikayi alkawari shiru sai daima alert d'in kwashe min kud'in account da kikayi gaba d'aya".

Tunda ta fara magana take binta da kallon wulakanci harta karasa kana tace..." Maganan boka ke kika jawowa kanki dama na gargad'e ki tun farko ba'a mishi musu kikayi harda cacan baki,maganar kud'i kuma nice na kwashe su kuma banje wajan wani boka ba face rabona dana kwada dan bazan tashi a tutar babu ba,saboda haka fita ki bar min gida tun kafin ranking ya b'aci ko insa yanzu ayi min waje dake".


Da gudu Lateefa tayi kanta tana..." Wallahi baki isa ba ni zaki yiwa haka?na rantse da Allah sai kin fito min da kud'i na".

Hankad'ata Aina'u tayi sai gata ta zube a kasa kaman kayan wanki.

"Isa isa!!" Aina'u ke kwalawa masu gadinta k'ira tun karfinta.

Da gudu suka zo gabanta suka zube.

Cike da masifa tace..."Ku fitar min da matan nan a gidana kuma wallahi in kuka k'ara barin irin wa'yan nan suna shiga min gida a bakin aikin Ku"tana gama fad'an haka tayi cikin gida abinta.

Ciccib'ar Lateefa da take ta faman zage-zage da tsine-tsine harda fizge-fizge amma hakan baisa sun sarara mata ba saida suka fito da ita da karfin tsiya suka jefar tare da maida gate suka rufe.

Ta dad'e zaune a bakin gate d'in gidan tana cigaba da masifa har tana bubbuga gate ba wanda ya kulata saima jama'a da suka fara taruwa suna mata kallon sabuwar mahaukaciya.

Gajiya tayi da masifar ga zafin rana da ya ishe ta yasa taja tsuman jikinta ta shiga motarta ta bar anguwan.
πŸ™†πŸ™†πŸ™†πŸ™†πŸ™†πŸ™†

*UKUBAR KISHIYATA*

😭😭😭😭😭😭

(Its all about love and betrayal)

Story by *~UMMEE YUSUF~*

(Maman Yusuf)


https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATIONπŸ’«πŸ’«πŸ’«~*


*_~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~_*


*part forty eight*


Kuka take kaman ranta ya fita wai yau ita Aina'u zata yiwa haka?duk abinda tayi mata a baya bata gani ba?

Cak kukan nata ya tsaya kaman d'aukewar ruwan sama sakamakon abinda idonta ya gane mata.

Fa'iza da Shamsiyya ta gani a bayan moton sojoji fuska duk a kumbure.

Bata san lokacin da ta juya kan motan ta ba ta fara binsu a baya har zuwa jaji.

Zata shiga wasu manyan sojoji masu kama da samudawa suka dakatar da ita.

Rokonsu ta farayi kan suyi hak'uri su barta ta wuce kannenta ta gani an shiga dasu ciki.

D'ayan yace.." wa'yan nan ne k'annenki?"

Amsawa tayi tana k'ara kusanto su.

Tsawa suka daka mata kan ta tsaya inda take.

Duk baya sukayi suna toshe hanci tare dayi mata kallon k'yama.

D'ayan cikin su yace...
"Hey chidimma make u call oga and tell him".

Wani k'aramin d'aki ya shiga ya d'auki waya irin lane line d'in nan yayi k'ira.

Bayan sun gama magana ya fito yace..." Joseph escort her in".

Mota ta shiga tace shima ya shigo su tafi.

Kallon banza ya fara aika mata sannan yace..." Ban shirya mutuwa ba ji yanda kike wari kaman mushe in na shiga motarki suna na marigayi".

Bata ce k'ala ba ta fara Jan motanta a hankali take bin bayan shi har zuwa wani area mai ban tsoro wajan tsit baka jin motsin komai sai wani k'aton soja mai manyan idanu gasu jawur dasu kaman barkono da suka gani a wajan da alamu shi yake tsoron wajan.

Tambayar Joseph yayi daga ina?

Nan Joseph yayi mishi bayanin komai.

Ido ya tsura mata na wani lokaci sannan ya tambaya..." K'annin ka ne?

"Eh dan Allah kuyi hak'uri ku sake su" tace tana mai zubda hawaye.

Girgiza kai yayi yace..." Kasan menene sunyi kana cewa a sake su? "

Da sauri ta girgiza kai dan gaba d'aya ta gama tsurewa ganin wasu d'ika-d'ikan sojoji sun zo wajan da manyan bindigogi a hannun su.

"Those bloody bitches an kama su a gidan oga kuma a cikin bedroom na oga wit his wife suna yin iskanci,or I think u re among them abi?" Yace yana zaro mata manyan idanu shi.

Jiki na karkarwa ta fara basu hak'uri tace..." Wallahi ban san suna aikata irin wannan mummunar d'abi'a ba dan Allah ku rufa min asiri ku bar ni in tafi".

"Then get out before oga come and sees u here" yace mata cikin tsawa.

Da gudu ta fad'a motarta ta fita daga barack d'in tana kukan bakin ciki na ba yanda zata yi ta fita dasu daga wannan bala'in,koda yake su suka jefa kansu a ciki.

Toh ya akayi suna cikin irin mutanen nan amma bata tab'a sani ba .

Sai yanzu idonta yake hasko mata yanda suke rayuwarsu su 2 kaman wasu masoya ta d'auka zallan shak'uwa ce ashe su abinda suke aikatawa kenan.

Da haka ta k'araso gida cikin tashin hankali.

Addu'a take Allah yasa ba kowa a parlour.

Cikin sa'a kuwa babu kowa ta samu parlour sai t.v da yake ta aiki shi kad'ai.

Ba b'ata lokaci ta fad'a part d'inta tare da murza key.

Zama tayi dirshan a k'asa ta rushe da kukan nadama,wai yau su duniya ta juyawa baya haka? Daga ita har k'annenta suna cikin *UKUBAR* rayuwa.

*UKUBAR* da suka jefa wasu a ciki yau gashi suna cikin wanda yafi karfin tunaninsu.

Ga wacce suke wulakanwa a baya yau gata cikin k'wanciyar hankali.

Dama haka duniya take?.

Har karfe 2 tana zaune a wajan ta kasa tashi.

Dama ba damuwa tayi da sallah ba,amma yau ganin azabar rayuwa yasa ta tashi tayi sallahn azahar.

Komawa tayi ta zauna kuma a lokacin ne ta tuna ashe ba taci komai ba tun safe.

Tunanin ya zatayi ta fita ta samu abinda zata ci take,can ta tuna ashe tana ajiye kayan tea a cikin d'aki.

Jiki na rawa na nufi drower ta bud'e taga kayan tean suna nan harda su snacks.

Bata damu da ta nemi ruwan zafi ba.

Bathroom ta shiga ta taro ruwa a cup tazo ta had'a tea tasha da snacks ta koshi.

Gado ta hau ta k'wanta tana tariyo tarihin rayuwarta.

Ta dad'e a k'wance sannan ta tashi ta d'auki wayarta ta k'ira number Salees.

Saida ya kusan tsinkewa ya d'aga yace..."yah ne Babyna?"

"Ba lafiya Salees i na cikin wani yanayi na tashin hankali ga rashin lafiya ya sani gaba" tace muryanta na shaking alamun tana kuka.

"Subhanallah!! Babyna meya faru,meke damunki?" Salees ya tambaya cikin tashin hankali.

Saida ta face hanci sannan tace ..." Labari ne mai tsawo honey amma ina bukatan kud'ad'ena na wajanka saboda in samu daman fita abroad neman lafiya".

Cike da tashin hankali yace.."abun har ya kai haka Baby na?kada ki damu gobe mu had'u a hotel sai in zo miki dasu ko?"

Wani sanyi taji ya ratsa ta na jin ya rik'e mata alkawari tace..."nagode Salees daz y I love u".

" I love u 2 my Lateefa".yace mata tare da katse wayan.

Tana k'wance a part d'inta taji Al'ameen yazo yana knocking amma tayi biris dashi kaman bata jiba.

Shima bai damu ba ya juya yayi kowan shi dama Ameera ce ta takura mishi lalle sai yazo ya duba lafiyarta duk da abinda Lateefa tayi mata bata rik'e ta a zuciya ba illa damuwa da tayi da ita.

Gari na wayewa tayi sammakon ficewa daga gidan ta tafi hotel inda sukayi alkawari da Salees kan zai kawo mata kud'i.

Anan tayi ordern kayan breakfast tayi ta zauna har zuwa 9am sannan tayi mishi waya.

Shi kuma ya tabbatar mata da ba matsala yana nan zuwa.

Zuwa thirty minutes sai gashi nan ya shigo jaye da wata katuwar trolly da wata madaidaiciyar jaka a kafada.


Tana ganin shi ta mik'e cike da murna dan ta tare shi.

Warin daya ji ya tare shi,shiya hana shi shigowa ya tsaya a bakin k'ofa yana yatsina fuska.

Ganin haka yasa itama tayi turus ta tsaya ba tare da ta k'arasa wajan shi ba.

"Kaga babban dalilin da yasa nake neman kud'in kenan Salees"ta fad'i haka tana duban shi tare da marairaicewa.

Ta cigaba da cewa..." Banyi zaton kaima kana cikin masu guduna ba,saboda kai kad'aine hope d'ina Salees".

"No don't say so Lateefa" ya fad'i haka yana k'arasowa ciki.

Sannan ya cigaba..."kema kinsan bazan tab'a gudunki ba no matter how, saima in k'ara tausaya miki".

Sauke jakunan da yazo dasu yayi tare da zuge zip d'insu duka.

Dollars ne tab a cikin babban trollyn,sai k'aramar kuma dubu Dubu ne a ciki.

D'ago kai yayi yana murmushi yace..."ga dukiyar ki nan na dawo miki dasu kaman yanda kika bani amana".

Durkushewa tayi a wajan tana hawaye tace..."da za'a samu irinka a duniyan nan da duniya bata lalace haka ba dan rik'on amana yayi k'aranci a wannan zamanin .ban san da wani baki zan gode maka ba Salees sai dai ince Allah ya barmu tare.insha Allah in na sami lafiya na dawo zan baka sharen ka".


Murmushi yayi yace..."don't worry Baby just buri na ki samu lafiya.let's go in kinsan nayi missing d'inki sosai".

Cikin murmushi tayi ciki yana binta a baya ta hau gado ta k'wanta.

"Oh gosh " yace yana dafa goshin shi sannan ya cigaba ..."na manta ban rufe kofa ba ,bari in rufe in dawo kuma nazo miki da surprise sai dai ina so ki rufe idonki har sai nace ki bud'e sannan ki bud'e kinji Babyna?"

Cikin zumud'i ta saka tafin hannayenta ta rufe fuskanta.

Tana ji ya fita zuwa parlour har ya rufe k'ofan ya dawo ya tarar har yanzu fuskarta a rufe yake.

"Babyna bud'e idonki...." Yace cikin romantic voice.

A hankali ta bud'e idonta tana murmushi.

A zabure ta mik'e tana nuna su da yatsa bakinta yana motsi amma sauti yaki fitowa saboda kid'ima.

Salees ya k'ara rugumo Aina'u suna mata dariya yace... " haba Babyna meye na kid'imewa haka?wannan shine first surprise saura na 2 kenan".

Kukan kura tayi tayo Kansu da gudu.

Tun kamin ta k'araso Salees yasa mata k'afa ta fad'i.

Kamota sukayi suka fito parlour da ita Salees ya zaunar da ita akan kujera, Aina'u ta bud'e hand bag da tazo dashi ta fito da igiya ta bashi.

Karb'a yayi tare da d'aure ta a jikin kujeran.

Hannu yasa a aljihun wandon shi ya fito da gum ya manne mata baki dashi.

Durkusawa yayi daidai fuskarta yana murmushi yace..."ni bawan ki ne da zaki ce kin bani ajiyar irin wannan kud'in kuma kice in dawo miki dasu?harda wai sai kin dawo zaki bani rabona?hmmmm gaskiya kin raina min wayo ke da baki kare amanan mijinki ba har kike zaton wani zai kare miki amana?kinyi kuskure babba Lateefa cos tunda muke dake ban taba sonki ba koda na second 1 ba.look at this"yace yana nuna mata kud'in da ido.

Ya cigaba..."sune dalilin da yasa muke tare,na da kuma sabida Kore sha'awata nake tare dake.but I regret every second I spent with u"ya k'arasa yana huci.

Dariya Aina'u ta sheke dashi harda rike ciki tace..."kasan me?wai ni ta bawa blank check akan in cire kud'i,dakikiya kawai saboda duk zaman da mukayi dake Lateefa ban tab'a sonki da alkhairi ba ,wajan boka da shawarwari da nake taimaka mini dasu Salees ne yake tilasta min inyi dan Mu cimma burin mu,but Lateefa i terribly hate u".

Tayi kaki ta tofa mata a fuska.

Rintse idonta tayi da karfi saboda wani rad'adi da take ji a k'asan zuciyarta da take ji kaman ya fashe.

Meye zata iya yi musu balle taji sauki a ranta?

Babu shine amsar da ta bawa kan ta sabida tasan sun gama cutarta a rayuwa kuma gata a d'aure.

Saukar lafiyayyar mari taji shiya dawo da ita hayyacinta.

Salees tagani yana nunata da yatsa yace...ni zaki rainawa hankali INA magana kina jina?"

K'aramar jakan ya jawo gabanta yace..."ga rabonki sweetheart sai dai nake ganin kaman d'aukan zaizo miki da matsala,let me call wanda zai taya ki d'auka kin san bana son inga kina wahala".

Wayar ta ya dauka ya fara scrolling yana neman Wanda zai kira.

Yana zuwa kan sunan da yake nema ya kece da dariyar mugunta tare da nuna mata screen d'in wayar.

Sunan da ta gani ne ya k'ara jefata cikin tashin hankali da ya d'ara na yanzu.

Kai ta fara girgiza mishi hawayenta na k'ara k'aruwa.

Shafa gefen fuskanta yayi yana murmushi yace..." Haba Babyna kar ki d'aga hankalinki just dakon kud'inki zai mini kin gane?"


Tana gani ya danna k'iran number.

Fizge-fizge ta fara ko zata iya kunce d'aurin da yayi mata amma ko motsin kirki ta kasa yi.
πŸ™†πŸ™†πŸ™†πŸ™†πŸ™†πŸ™†

*UKUBAR KISHIYATA*

😭😭😭😭😭😭

(Its all about love and betrayal)

Story by *~UMMEE YUSUF~*

(Maman Yusuf)


https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATIONπŸ’«πŸ’«πŸ’«~*


*_~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~_*


*part forty nine*


Al'ameen yana rik'e da Ameera da take ta k'wara amai kaman ranta ya fita.

Sannu yake ta jero mata kuma at d same time yana ta masifan shi..." Dama saida na hana ki zuwa d'akin nan amma kika nace ke sai kin kai mata breakfast, ita yarinya ce da sai an kai mata?gashi kin jawowa kanki aman dole.wannan warin jikinta dana d'akin nata zai iya kisa,kinyi sa'a da kika tsaya a amai".

Ameera dai tana jinshi ba tace komai ba saboda aman yaci karfinta .

Da k'yar ta samu ya tsaya ta kuskure bakinta tare da wanke fuskarta ta dawo kan kujera ta zauna tana maida numfashi.

Shima zama yayi a kusa da ita yana yi mata sannu.

Ringing d'in wayar shi da yaji yasa ya tashi zuwa kan center table inda ya ajiye wayoyin shi.

Sunan Lateefa da ya gani yana yawo akan screen d'in wayan yasa yaji kamar kar yayi receiving saboda yanzu babu wanda ya tsana kaman ita ga sabon al'ada da ta samu na fita da shiga a duk lokacin da taga dama ba tare da izinin shi ba.

Saida k'iran ya kusan tsinkewa sannan ya daure ya d'aga.

Maimakon yaji muryarta sai yaji murya wani namiji yace.... "Alhaji Al'ameen mudassir mijin Lateefa ko?"

Da k'yar ya bud'i baki ya amsa da..."eh nine meye ya kawo wayar mata ta hannunka?"

Dariya ya kece dashi sai da yayi mai isar sa sannan yace....matarka ko matar mu?"

Tsawa Al'ameen ya daka mishi wanda yaja hankalin Ameera gare shi yace..."bana son zancen banza waye ne kai?"

Salees yace..." Easy man stop shouting yanzu zaka ce baka sanni ba?sau nawa kake zuwa ka same ni a gidanka koda yake raina maka hankali take tace maka no d'an uwanta ne,ga files da kake saka hannu ana kawo min.no need of explanation tunda kasan wannan wayar matar kace yanzu haka tana (prince hotel)room number 35 wannan d'akin matarka tana rik'e da shi fiye da 15years.u can come and see for urself saboda ka tabbatar da abinda na fad'a maka in kaki kuma kayi zamanka,maybe zakayi mamakin dalilin da yasa nake fad'a maka haka ko?ta gama yi min amfani shiyasa".yana gama fad'an abinda yayi niyya ya katse wayan yana kallon Lateefa fuskar shi d'auke da murmushi yace....

" mijinki yana nan zuwa ya d'auke ki,mu zamu tafi sai wata rana.

Juyowa yayi wajan Aina'u yace mik'o min abin muyi mata suprice na 3.

Wata sharb'eb'iyar wuk'a Aina'u ta ciro a cikin hand bag d'inta ta mik'awa salees.

Karb'a yayi yana jujjuyawa daidai fuskan Lateefa wacce tuni tayi suman zaune dan hawayen ma bata san lokacin da suka kafe ba.

Kan wuyanta ya d'ora yana dariya yace..."am sorry Babyna".

Rude idonta tayi tana jiran mutuwarta .

Hannunta na dama ya kama daidai wajan yatsunta 5 yace..."bazan kashe ki ba amma zan miki abinda zaki rinka tunawa dani always ".

Sare hannun yaji wanda nan da nan hannun ya guntule ya fara tsalle a cikin parlour ga jini yana ta tarwatsuwa a parlour.

Kafa yasa ya danne gutun hannun daya guntule har ran ya fita.

Ya juya yana kallon Aina'u

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login