Showing 207001 words to 210000 words out of 215481 words

Chapter 70 - Ƙaunar Da Ta Zama Azaba by 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲

min kai.

“No please pleasure, ina son na yi rayuwa ne irin ta masoya rayuwar irin wadda na tsara zan yi ban samu dama ba sai yanzu”

“Okay Okay zan saka da kaina”

Na yi saurin fada sai ya sakar min riga na sauka daga kan gado ina kallon kofar bandaki, ina cira kafa da zimmar zubawa da gudu sai yayi charaf ya cafke ni, ya daga sama ni da shi muka fada kan gado muna dariya.

“I knew it, couse i know you”

“Kareem dan Allah ka bar ni na canja ba zan iya canjawa a gabanka ba”

“Ba dole sai kin bude jikinki ba, amman ina son ki sake jikinki ne da ni from day one saboda ni mijinki ne ABOKIN RAYUWARKI har bada”

“Na sani amman ba zan iya canjawa ba”

Na fada a shagwabe ina dan turo baki sai ya kama lips din nawa ya rike yana matsawa a hankali.

“Dole zaki iya Matar Kareem”

Ya kwanta lips din nawa kadan, na yi kamar zan masa kuka domin na ji zafi kadan.

“Akwai zafi fa”

Ya cire hannunsa ya mike tsaye ya riko ni ya sauko da ni daga kan gadon, sannan ya dauki rigar ya saka min ta sama ba tare da ya cire min tawul din ba, har sai da rigarsa ta sauka kasa sannan ya saka hannunsa ya zare min tawul din ya aje.

“Hey Beautiful look at you in my jallabiya”

Ya rika fuskata yana juya kaina yana dariya kamin ya daga ni sama yana juyawa kamar wata yar yarinya sai yawo nake a jallabiyar daga hannunta har tsayinta sun min yawa. Sai da ya chakwalkwala ni sannan ya sauke na dauki mayafina na rufe kaina ya shimfida carpet ya jagorance mu Sallar.

Bayan mun gama na yi addu'a shi ma yayi sannan ya juyo ya miko min hannunsa na kama, sai ya janyo na dawo kusa da shi ya kwantar da ni a cinyarsa ya tofa min addu'a a kai zuwa fuskata ya shafe min. Ya sumbanci bakina ya sunbanci goshina yana shafa hancina.

“Hey Beautiful, Good Morning”

“Ina kwana”

“Kin kwana lafiya yar kyakkyawata?”

Ba daga mishi kai sai ya sake sumbantar saman ido daya ya sunbanci dayan ma.

“Zo mu kwanta kamin anjima”

Kamin na mike tsaye ya riga ni, ya cire min mayafin ya aje gefe ya kai hancinsa a cikin gashina yana shakar kamshin dake tashi a cikin kaina.

“That's my wife”

Ya fara daga rigar jikina. Na yi saurin hana shi domin ban gama jiyar daren jiya ba.

“Aa aa aa bachi kace zamu yi?”

“Yes bachi zamu yi”

“Then ba sai na cire rigata ba”

Yayi murmushi.

“Ba abun da kike tunani ba ne, Wallahi bachi zamu yi normal bachi, but ni bana bachi da matar da nake so da tufafi a jikinta that's my number one rules, because ma'aurata need to cuddle, and duk lokacin za mu kwanta bana son naji wani abu yana taba skin di na, i just want to feel your skin touching my skin, and that doesn't mean zamu aikata wani abu, no ni haka kawai nake so kuma haka nake”

“Ni... Ni bana so.. Ni bana bachi babu tufafi”

“Beautiful baki da ikon kanki, kina da yancin ki yi yadda kike so a gidanki ko a kaina but ban da wannan bangaren ba zan baki wannan ikon ba, besides ina ce rigar nan tawa ne? So ba ni abuta”

Na girgiza masa kai.

“Wasa dai kake”

“Okay let me show my strong Babe”

Ya rage wutar dakin ya fara kokawa da ni har sai da yayi nasarar raba ni da rigarsa, kunya ta saka ni yi masa yadda yake so wato na rumgume shi ina boye fuskata a kirjinsa. Sai ya ja blanket din da aka siya min mai kyau gurin Khadeeja Candy ya lullube mu. Bachi muka yi mai dadi ina rungume a jikin mijina, kamshin dake fita a jikinsa ya dada Mafarkina.

Sanyi da na ji a babban yatsan kafata ne ya saka na motsa ina mika, sai kuma na ji kamar an cikari yatsan hakan ya saka ni saurin bude ido, Kareem ne sanye da kananan kaya yatsan kafata a bakinsa yana cizawa.

“Da zafi ba”

“Uhmm, these are mine”

Ya dawo gurin kaina ya daga ni zaune ni kuma na riko bargon ina rufe jikina.

“Tashi bachin haka, kar mutane su fara shigowa su same ki kina bachi”

Ya sumbance ni, na kalleshi sai na yi arba da nashi idon da suka tsufa a kaina.

“What kin yi mafarkina ne?”

Na yi shiru domin ya canka daidai.

“Ai na sani zan yi ta fitinarki ne har cikin mafarki, haka zan rika binki har Aljanna”

Na fara kokarin sauka daga kan gadon ina murmushi sai ya rumgume ni.

“Na kasa yarda yanzu kin zama tawa Noor i love you so much...”

Lumshe ido na yi ina sauraren numfashinsa dake sauka a wuyana. Mun dade a haka sannan ya sake ni na sauka na nufi gurin da lace din na jiya yake na dauka ina jan bargon dake rufe a jikina.

“If you don't want me to see my halal then, zan bar miki dakin sai ki canja”

Ya fada ganin na nufi kofar toilet. Na daga mishi kai sai ya mike tsaye ya nufo gurin da nake tsaye ya sunbance ni.

“I love you”

Ya fice ina kallonsa fuskata da murmushi. Lace din na saka na shiga bandaki na yi fitsari na sake gasa kaina sannan na fito.

“Is my beautiful already?”

Na kalli kofar ina girgiza kai, sometime Kareem yana abu kamar yaro.

“Can i come in Babe?”

“Yes”

“Thank you”

Ya turo kofar dakin na shigo, ya zauna kusa da ni ya saka hannunsa ya kwanto da ni a jikinsa.

“Me kike son mu karya da shi?”

“Tea?”

“And”

Na yi shiru ina tunani, shi kuma sai kallona yake yana mursa yatsun hannuna.

“Come here”

Ya daga ni ya zaunar da ni a saman cinyarsa ya sumbance ni.

“Bari na nuna miki yadda ake order abinci a restaurant din mijin Noor a Online”

Na yi dariya mai sauti, yadda ya fadi Mijin Noor in just one day da daura aure abun dariya.

“Oh i need more”

Ya fara min cakulkuli ina dariya har sai da ya shi ma yayi dariyar sannan ya sake maida ni jikinsa ya min rumfa da kirjinsa ya saka hananyensa biyu yana nuna min gurin da zan taba, a duk lokacin da nake bukatar wani abu.

“Kin gane?”

“Eh”

Ya juyo da fuskata yayi min wani French kiss with his soft sweet lips, har sai da hankalina ya kusa gushewa. At that time na gane wa na aura and i what i have been missing for my whole damn life.

“My direction”

Ya fara min idonsa cikin nawa, kamin ya kwantar da ni a kirjinsa ya rumgume..

“My innocent girl”

On that day na gane i found my missing rib, because when ever he hug me i feel something that i have never felt before.
He feed me ya kuma gyara ko'ina da muka bata ya gyara gadon, sannan ya riko hannuna muka fito yana nuna min ko'ina na gidan, sannan ya fita shi ma saboda yan uwa sun fara kawo min ziyara ne.

Idan na cire kamshi, kissing, cuddle, saying i love you, hugging na cikin abubuwan da na fahimci mijina yana so a zamantakewar aurenmu, domin a tsawon kwana uku da na yi a gidan ba ma rabuwa da dayan abubuwan nan sai idan ya fita.

For now zan iya cewa Kareem yana gudun bacin raina kuma yana kokarin ganin ban samu damuwa a kamai ba. Na kara fahimtar hakan ne a ranar da yaransa suka zo tare da kanwarsa, ina ta jin tsoro haduwa da su musamnan yaransa gani nake kamar ba za su taba so na ba. Amman Kareem ya kwatar min da hankali ya fada min ba zai yarda su tsane ni ba, ba kuma zai bude min kofar da ni ma zan tsane su ba.

Suna zaune falo na fito da dan tsoro na zauna kusa da shi ina kallon babbar domin ita ce mai wayo.

“Hey Beautiful....”

Ta fada tana dariya na kalli Kareem da sauri sai ya girgiza kai ya dafe kansa yana dariya.

“Two days before a daura aurenmu kika kira ni a gabanta sai na manta na ce Hey Beautiful shi ne fa ashe ta rike”

Na yi murmushi na mika mata hannu sai ta taso ta dawo tsakiyarmu ta zauna.

“My mommy said ke ce New Momy mu a yanzu, kullum idan muka zo mu rika yi miki biyayya mu rika natsuwa”

Na rumgume ina jindadi har cikin raina. Areef ma ya taso ya dawo saman jikin Babansa ya zauna, mun wuni da su babu wani tashin hankali karamin mai kiriniya a yadda na fahimta, Tine din ce mai hankali. And na yi mamakin da na ji cewar mahaifiyarta tace su yi min biyayya, ko dan ta san aurenta da Kareem ya kare ne ko kuma dai ita ma irin Aysha ce.

Sai dare suka tafi gida na yi zaton bayan sati da amarcina a gidan zai dawo da su amman ban ga alamun haka ba, domin be yi min zancen ba, ni ma ban masa ba. Satina biyu a gidan ya dauke ni muka tafi gidan iyayensa na gaisa da Hajiyarsu wato Hajiya Hassana wacce ita ce tamkar uwa a garesu yanzu, ita ma ta tarbe ni da girmamawa kanensa ma haka.

Ba kamar Aryam da yake fadar wai na kusa haukata masa dan'uwa, bayan sallah Isha'i Mahaifinsa ya dawo kanwarsa Khadija ta shiga da ni bangarensa muka gaisa yayi min nasiha, kuma ya ce idan Kareem yayi min abun da be yi min ba na yi gaggawar kawo masa kara kar na tafi gidanmu domin a yanzu su ne family na.

Sun yi min alheri sosai na kuma jidadin haka. The following day ya kai ni idanmu na wuni gurin Mama, muka sha hira ta tsefe min kai aka min kitso, sai dare ya dawo ya dauke ni yayi mata alheri sosai, ta yi mana addu'a muka dawo gida. Yana fakawa harabar gidan yayi saurin fitowa ya bude min kamar yadda ya saba na fito, sai na rumgume shi hawaye na taruwa a idona.

“Allah yasa hakan ya daure Kareem”

“Babu abun da zai canja, an hallicce ni ne domin ke, aka hallicce ki domin ni, i love you”

He hold me har sai da na samu natsuwa sosai sannan ya sake ni ya rufe motar ya riko hannuna muka shiga falon.

“Yunwa nake ji sosai”

“Bari na saka order”

“No need bana son abincin waje”

Na dan ji wani iri domin tun zuwana gidan ban taba gwada girki ba, sai dai mu yi order abinci a kawo mana.

“Amman ka san ban iya girki mai kyau ba”

Ya jefar da keys dinsa a kujera ya kama duka hannayen nawa ya sumbanta.

“Babu abun da zaki girka da wannan blesse hands din be yi dadi ba, put that in your head”

“But i don't know how to cook”

“Baki taba mamakin miyasa mijinki ya bude restaurant ba?”

Na wara ido.

“Saboda ya samu kudi”

“Ba kudin ne kawai bukata ba, saboda mijin kwararen mai girki ne, so i got you covered”

Ya kashe min ido daya kissing my cheek both side. Bedroom muka shiga na canja atamfar jikina zuwa short jean dake bayyana fararen cinyoyina da wata yar karamar vest da bata rufe cibiyata ba na saka hula, yana ganin haka sai ya cire hujar ya aje ya sunsuna kaina.

“Ina bukatar ganin sabon kitson nan”

Shi ma short ne a jikinsa sai vest ya riko hannuna muka shiga kitchen, duk wani abu da na yi ina cikin kirjinsa ne ina fuskantar girkin shi ma yana fuskantarsa sai dai na jingina da kirjinsa ne. Zuba wannan kara wannan yanka wannan be saka min hannu ba sai dai ya fada min har mu ka gama with the support of kissing and cakulkuli from him har muka gama fried rice.

Falo ya dawo ya zauna.

“Now i want you to serve me”

“Okay”

Na samu karamin plate na zuba masa na dauko cikin fargaba na kawo masa domin kamshim abinci ba shi ne dadinsa ba. Na aje masa na tsaya a gabansa ina kallonsa, ya dauki spoon din ya debi abinci ya kai bakinsa ya tauna ya hade, sai ya lumshe ido.

“Hmmmm...”

“Abincin nan yayi dadi Babena”

“Da gaske rate me”

Ya bude ido.

“I can't rate you, you taste like heaven i can only rate the food”

Na rufe ido da hannayena ina jin kunya, na buga kafa a kasa kamar zan yi kukan shagwaba.

“Hey Beautiful bude idonki, abincinki yayi dadi na baki 8”

Baki sake nake kallonsa ina jindadi sai ya debi abinci ya kai min spoon din a baki. Lokacin da na ci abinci sai na ji yayi dadi sosai kamar ba ni na girka ba. Na gudu na je na haye kujerar dake kusa da wanda yake zaune ina tsalle na bude hannayena ina rawa da su.

“Okay hug hug hug”


KAREEM POV.

Kallonta yake da murmushi a fuskarsa farinciki da yake gani a tattare da ita ya saka shi jindadi, dukawa yayi ya aje Spoon din ya nufi gurin da take, madadin ya rumgume ta sai da riko cinyoyinta ya daya ta sama.

“Here I am beautiful”

Ya sumbanci cibiyarta sai ta kyalkyale da dariya mai burgewa. Ya sauke ta sai ta rumgume shi.

“Thank you for Kareem”

“Uhmm.. This is just the beginning”

Shi ya shiga kitchen din ya zuba musu abinci ya dauko ruwa da lemu ya aje, sannan ta zauna suna fuskartar juna ita da shi suka ci abinci. Da suka gama ya kwashe kayan suka wanke komai a tare suka gyara kitchen din a tare. Then suka yi wanka ta shafe jikinta da turare shi ma haka, da suka je kwanciya bata jira ya jaddda mata number one rules dinsa ba.

He hug her yana ta bata labarin abubuwan da bata sani ba a rayuwarsa, yadda ya koyi girki yadda aka fara kafa restaurant din har ya kawo yanzu and so on...
Da safe ma tare suka shirya abun karyawa sannan yayi wanka ya fita gurin aikinsa.

Misalin karfe daya na rana kiran Yusura ya shigo wayarsa, yayi mamakin ganin kira kusan tun da suka rabu idan ba rashin lafiytar yara ba shi ma sai yayi tsanani take kira, wannan karon ma sai yayi zaton ko wani ne babu lafiya.

“Hello...”

Ta amsa kuma ta gaishe shi with respect. Sai kuma ta yi shiru.

“Yara ba su da lafiya ne?”

“No Kareem ka san zan yi aure”

“Yeah congratulations, akwai abun da kike bukata ne?”

“Thank you, but ba na kira dan ka taya ni murna ko bukatar wani abu ba, kawai na kira ne saboda maganar yara ina za su zauna yanzu, because ba kasar nan zamu zauna da wanda zan aura ba for now saboda yana aiki a New York ne”

“Yara za su zauna gurin Hajiya, zan dauki Nanny da zata kula da su kuma kanena suna nan Hajiya ma tana nan, babu abun da za su rasa, already sun saba da gidan yanzu, zan dawo da su gurina but sai Noor ta haihuwa tukuna”

“Okay ba matsala”

“By the way na gode da kika bar su suka so Matata, hakan shi ne tarbiya”

“I'm just doing my job as a good mom, and thank you for giving me the opportunity to find my love, wish you happy married life”

“Wish you the same Yusura, enjoy your life”

Ya sauke wayar, sai kuma ya ji babu wanda yake bukatar gani ko ji sai Noor dinsa. A take ya aika mata kira tana picking ya ce.

“Hey Beautiful”

“Hey handsome”

Ta amsa mishi with awesomeness, ya kwanta jikin kujerar yana shafa kansa da murmushi a fuskarsa feeling so heart warming.

“I miss your hairy chest, i need cuddle”

Ta fada a shagwabe. Gaba daya sai ya ji ya rikice.

“I will be there right away my beautiful”

Ya sauke wayar ya dauki abubuwan bukatarsa daman lokacin tashinsa yayi sai ya fice daga Asibitin da sauri. Tun kamin ya fara harabar gidan ta fito sanye da hijab yana ganin haka ya san kananan kaya ne a jikinta domin ya fada mata idan zata fito harabar gidan ta rika rufe jikinta saboda mai gadi.

Waving dinsa ta rika yi daga bakin kofar falon da take tsaye har ta karaso ya sauke gilashin motarta.

“Hey Beautiful”

“Hey Handsome”

A kokarinsu na rigen rigen futarwa juna suka fada a tare, sai duk suka saka dariya. Yana fitowa motar sai ta zo a guje ta daka tsalle ta fada jikinsa ya cafketa ya daga sama ta lake kafafuwanta a kunkurunsa.

“I miss this face, i miss this girl”

Ya fada yana jan kumatunta, ita ma sai ta ja nashi tana fadin.

“I miss this hug, i miss this guy”

Yayi dariya ya nufi entrance din da ita. Suna shiga falon ya fara kissing dinta, sannan ya sauke ta kasa.

“What's up Beauty”

Ta yi dage ta lakaci hancinsa.

“I cook something delicious...”

“Let me smell it then”

Ya fara kokarin cireta mata hijab yana shinshinar kamshin dake tashi a jikinta.

“I said i cooked not in my body”

“Ouoooo, my bad, i have dirty mind”

Ya daga ta yana dariya...
Bayan Shakara Daya...


NOOR POV.

Na bullo da kaina gurin wuyan rigarsa na tura hannuna da gun da hannunsa yake, sai ya zama na ni ma na shiga cikin T-shirt din dake jikinsa, shi yana daga kwance rairai ni kuma ina samansa na lafe a jikinsa skin dina yana taba nashi.

“Baki karasa min ba, sai aka yi yaya?”

Na dan yi shiru ina tunanin a ina na tsaya da labarin da nake ba shi na sabon littafin Khadeeja Candy mai suna ABOKIN RAYUWA.

“Yauwa sai be aureta ba, ita fa yarinyar christen ce, bayan ya musuluntar da ita sai kuma yan'uwan shi suka rika cewa ba bahaushiya bace saboda ita din igbo ce amman tana da kyau, sunanta Emily”

“Ta yi kyaunki?”

Na daga na kai masa cizo a gemu har sai da yayi kara.

“Ita fa kyakkyawa aka ce”

“To ni yanzu akwai mace mai kyau da ke burge ni irinki, kin mamaye zuciyar kin hana ni ganin kyaun kowa ai, da zarar na motsa nan sai na ji ana Noor idan na juya can na ji ana Noor, to ya zan yi? Kin saka kwado kin kulle idon da zuciyar gam”

Na yi dariya mai sauti.

“Kuma na jefar da makullin ya bata”

“What ever ni dai abun da nake so na samu, Noor kin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login