Showing 87001 words to 90000 words out of 215481 words
domin yar kullum ce be cin abincinta ita ma kuma bata fasa girkawa. Sai da ta fitar da kayan sannan ta dawo dakin ta nufi gurin da yake aje kayan dauda ta bude ta dauko green shaddarsa ta jiya ta zauna gefen gadon tana lalaben aljihun kowane bangaren. Domin zuciyarta bata natsu da abun da ta hango Kareem ya karba a hannun yarinyar da ta taba fasawa goshi ba jiya...
#KhadeejaCandy
PAID PAGE 8️⃣
©️KhadeejaCandy
©️®️Copyright
2024
Littafin nan na kudi ne, don't read if you didn't pay... One word kika karanta baki biya ni ba, ban yafe hakkina ba.
To be part of the journey pay 500 to 2451879008
ZenithBank
Hadiza Abubakar
And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660....
You can read my latest update on arewabooks a handle dina @KhadeejaCandy
https://www.arewabooks.com/book?id=659a94c8be87d7a51f831153
_______•••_______
Wani irin faduwa gabanta yayi a lokacin da ta yi arba da abun da ke cikin rigar aljihun Kareem. Me hakan yake nufi Kareem yana tare da yarinyar nan kenan? Ba ita kadai ba wata kila har da Safeena, matan aure yake bi kenan? Shiyasa yake takura mata a lokacin da take fita gani yake kamar ita ma gurin wani zata tafi? Anya ma wannan Amaryar Hafiz ce? Idan har gaskiya ne me zai saka yayi tarayya da ita?
Ta mike tsaye da sauri ta fice daga dakin rike da maganin da robar ta shiga dakinta sai da ta dauki wayarta sannan ta tuna bata da number matar Hafiz domin ba kowa take hulda da shi ba a cikin matan abokan Kareem, iyakar ta da wasu gaisuwa. Number wayar Samira ta nema ta kirata suka gaisa cikin mutunci sannan ta bukaci Samira ta turo mata da number Aisha matar Hafiz.
“Wai daman baki da number ta”
“Ban taba karba ba”
“Kai kawata baki da kirki, bari na turo miki yanzu”
“Yauwa na gode, Ai na san kuma good time da ita ba zaki rasa number ta”
“Okay”
Ta sauke wayar kamin Samira da ta kasance cousin dinta ta turo mata mumber Aisha har ta matsu. Sakon mumber na shigowa ta bude da sauri ta taba Number ta kira sai daf da zata yanke Aisha ta daga.
“Assalamu Alaikum”
“Wa'alaikusalam Aisha ya gida?”
“Lafiya kalau ya yaran?”
“Alhamdullahi kin gane mai magana?”
“Na so dai na gane, amman ban gane ba”
Yusura ta yi murmushin karfin hali.
“Yusura ce Maman Tine”
“Kawai ki ce min Mrs Kareem zan fi ganewa, uwargida ran gida”
“Oh oh toh ke ma ai uwargidance, ko da yake yanzu nake jin cewar Hafiz ya kara aure”
“Wallahi haka ne, kika ji ko dai Kareem ya fada miki, ai ke ma auna arziki kika yi da yanzu ke za a kawowa ita”
“Ban gane ba”
Yusura ta fada daman abun da take nema kenan. Aisha ta sauke numfashi.
“Hmmm ai mijinki ya so aurenta shi yayi sonta sosai, sai dai ban san miya hana shi aurenta ba, kwatsam Hafiz ya zo min da zancen auren, wai zai rufa mata asiri ya aureta saboda wanda zata aura an fasa auren sanadin Kareem shi kuma Kareem din yace ba zai aure ta ba, kin san mazajen na mu da hadin kai ko ma dai miye Allah kadai ya sani”
“Amman kika yarda Aisha?”
“au hanawa zan yi? Kin ji Yusura da wata magana, namiji da zai yi aure zaka iya hana shi ne? Ai idan namiji zai kara aure baya ji baya gani, shiyasa na nuna masa na fi shi tausayinta, na san waye Hafiz na gama karantar mijina daman kuma idan ka fahimci waye mijinki zaman aure ba zai yi ma mace wahala ba, shiyasa na goya masa baya dari bisa dubu aka yi komai aka gama cikin mutunci lefen ma ni na hadawa kaina na hada mata, yadda na san Hafiz ina daga hankalin na daga na shi zuciya zata iya dibarsa ya sallame ni gidanmu, amman hakan da na yi sai na siye zuciyarsa da ta yan'uwansa gashi muna zaune lafiya ni gani nake kamar ma ya fi so na yanzu sama da lokacin da be auri yarinyar ba, domin na kara value a idonsa”
“Toh Allah yasa yar gidan mutunci aka dauko miki kin san yan matan yanzu”
“Waya sani ance dai ubanta dai shegen kwadayi ne da shi ko kashe rai zai iya yi akan kudi, ita kuma gaskiya ance bata tsayawa kanta ba, kawai dai maza ne mace daya bata isarsu sun maida karin aure rayuwa, kuma basa tsayawa su duba yar gidan mutunci daukowa kawai suke, saboda tana da kyau”
“Oh Allah ya kyauta, matan zamanin nan sai a hankali”
“Ameen kedai ina nan ina lallabawa karta kashe min aure, ga yara ga ciki na tafi ina? Samun miji irin Hafiz a wannan mazanin ai sai an tona is rare gaskiya”
“Allah ya tsare miki aurenki, ni ai be fada min ba sai yanzu, na ce dole na kira na miki jaje”
“Hmmm na gode, zan yi saving number ki ai a rika gaisawa”
“Toh sai anjima”
Yusura ta kashe wayar gabanta na bugawa da karfi. What her husband got into? Ko shiyasa ta zo nemansa har cikin gidan kamar yadda Safeena ta zo? Me yake kokarin zama ne? Matan aure yake nema? Ta mike tsaye ta fara tafiya tana daga kanta. Amman ita miye nata a ciki idan ma neman matan yake yi? Kabarinsa dabam nata dabam, kuma bata fatan zama da shi har abada.
“Saboda yaranki...”
Wata zuciyar ta fada mata. domin saboda su ta dawo tana kokarin kyautata masa tun daga lokacin da Safeena ta leko gidan. Ji take indai tana raye ba zata iya bari Kareem ya auri Safeena ba ko da kuwa bata da aure domin Momy bata son Safeena ko kadan, mutuwarta kuma zai iya saka Safeena ta yi tunanin sake kulla alaka da Kareem. Gashi yanzu babu Momy babu mai masa fada idan yayi ba daidai ba.
“Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un”
Gaba daya ta rasa me ke mata dadi, ta rasa ina zata kama abun ya daure mata kai, wai saboda be sonta yake bin mata ko kuma dai wani sabon hali ne ya kirkirarwa kansa? Tunaninta ya kasa tsayawa guri daya.
KAREEM POV.
@4:11pm suka fito daga massalacin dake cikin restaurant din, Kareem na gyara hannun rigarsa ya ce.
“Ni dai da zaka dauki shawarata Barrister karka karbi case din nan, case ne mai matukar hadari kasan yadda yan siyasa suke”
“Amman za a samu kudi mai kyau fa Doctor”
“Rayuwa ta fi kudi muhimmanci, duk kudin da zaka samu idan ba zaka samu rayuwa ba ba su da amfani”
“Kusan kowane aiki akwai risk ciki, kawai dai ka taya ni da addu'a”
“Allah ya tsare, amman ni ban yarda ka karba ba gaskiya”
Hafiz ya tura kofar office din ya fara shiga yana fadin.
“Su suka neme ni fa, kuma saboda cancanta suka neme ni, ba zan oya watsa musu kasa a ido ba, abu na biyu ba a nan za'ayi ba a Kaduna ne”
Kareem ya daga kafadunsa.
“Indai ka nace sai ka yi ai babu mai hanaka, haka shi ne kawai matsalata da kai”
Yayi murmushi yana gyara zamansa a kujerar da ya zauna. Kareem yayi shiru na yan mintuna sannan ya kalli Hafiz cikin karfin hali ya ce.
“Hafiz ya iyalinka?”
Wani kallo Hafiz yayi masa a cikin kallon da yake masa idan yana tuhumarsa da wani abun.
“Lafiya?”
“Ka tabbata?”
Hafiz ya gyara zamansa.
“Akwai abun da kake son mu tattauna?”
Kareem yayi murmushi domin shi da abokinsa kowa ya san halin kowa, da zarar dayan ya fuskaci wani canja ko da na magana ne zai fahimci akwai manufar aikata hakan.
“Amm... Ban san ya zaka dauki abun ba, na so na bar maganar sai kuma nake ganin kamar zaka kone kanka ka cutar da iyalinka, be kamata na shiga cikin maganar ba amman dole ce ta saka”
Hafiz ya mika masa duka hankalinsa yana kallonsa.
“Lokuta da yawa idan ka ga In aikata wani abu da be dace ba kana yawan jan hankali kuma ka lurar da ni gurin da illar abun take”
“Ka wuce duk wannan Kareem fada min kawai”
Kareem ya zauna da kyau.
“Hafiz akwai wata matsala tsakaninka da Noor ne?”
Hafiz ya kalli wani gafen alamar tunani sannan ya kalli Kareem.
“Ta zo nan ne?”
A madadin Kareem ya amsa masa sai ya dora da abun da yake jin kamar shi ne matsalar.
“Hafiz ka rika bincike kamin ka yi fushi ko yanke hukunci”
“Kareem ta fada maka abun da ta yi?”
“I don't think Noor zata yi abun da kake tunani, she's very innocent, Hafiz bata ma san amfanin abun da ka gani a jakarta ba bata san me ake yi da shi ba, kuma abun mamaki ne ace ta san wannan a yanda take da kananan shekaru, she's too young for that ita ba karuwa ba ba matar da ta shekara hudu gidan miji ba”
Hafiz ya nade hannayensa.
“Idan bata sani ba taya suka zo a jakarta? Kasan dai ba za su kawo kansu ba ko? Idan ba ta siya ba maybe wani ya bata wani like Zafeer amman ta ki yarda ta fada wanda ya bata, ko kuma ya fada mata ta siya, ranar da na kaita gidansu ta wuni a ranar da ta dawo ne na karbi wayar da na bata kawai wata zuciyar ta raya min na bude jakarta and i did na ga abun a ciki”
“Taya zata amsa laifin da ba nata ba, bata san ya aka yi ya zo jakanta ba”
“Kai kuma ka yarda da ita?”
Kareem ya kasa cewa komai wannan babin saboda baya son ya janyo mata laifi gurin Hafiz.
“Ya kamata dai ka yi bincike, ta rantse bayan aurenta bata hadu da Zafeer ba ko ta yi magana da shi”
Hafiz ya kwanta jikin kujerar.
“Wa kake zargi? Aisha saboda ta fada maka Aisha, shiyasa na kirata ai lokacin da ta zarge ta kuma ta rantse a gaban Noor ba ta saka ba, sai me?”
“Maybe the way you confront her zai iya sakawa ta rantse ko da akan karya ne saboda ta wanke kanta”
“Me yasa ka yarda zata aikata amman baka yarda Noor zata aikata ba?”
“Saboda Noor bata waye duniya, da zaka ce min ta shiga gidan mutane ta yi arba da nama ta sata ko ta dauki wani abun dadi ta boye a jakarta zan fi yarda, amman ko kudi bana saka ran Noor zata dauka a dan fahimtar da na yi mata na kankanen lokaci Noor ba zata san miye abun da ke jakarta ba, kuma mace makira ce Hafiz na ga hakan a zaman da na yi da Safeena da Yusura, baka iya ganewa kansu, yanzu idan ka ga yadda Yusura take min a gaban mutane ba zaka tana tunanin akwai wani abu na rashin so ko zaman lafiya a tsakaninmu ba, yanzu kuma har wani hali ta kirkira saboda Safeena ta zo gidan har dakina take kawo min abinci idan zan fita tace Allah ya tsare idan na dawo tace min sannu da zuwa, na fara tsorata da lamarin matar nan”
Hafiz yayi murmushi.
“Safeena ta zo gidan fa ka ce Kareem? Amman ban taba ganin mutumen da ya raina matarsa ba irinka”
“Ba zuwa na yi da ita ba, kuma na gayyato ta na yi ba saboda na daina daukar wayarta ne ya saka ta zo da sunan ta zo min gaisuwa, amman dai na taka mata burki. So ni ina ganin ya kamata ka yi bincike ko kuma ka yafe mata ka rufe maganar kawai ba wai ka dauke mata kafa ba, kuma ka daina magana da ita a halin da take karkashin kulawarka. Ka ga duk yadda nake da Yusura bata so na bana sonta ba ma zaman dadi amman a haka idan na ga ta wuni bata fito shiryawa yara abu ba, ko kuma ban ji motsinta ba na kan leka na duba lafiyarta domin hakkinta ne da ya rataya a wuyana, please ka gyara”
“Zan gyara, amman kamar yadda baka yarda Noor bata san komai akan samun maganin a jakarta ba ni ma ban yarda Aisha ta saka mata ba, na san wacece Aisha shekara nawa muna tare da ita, mace ce mai kirki mai mutunci”
Kareem be sake cewa komai ba, domin baya son ya zafafa kasancewar ba shi da hujja kuma baya son Hafiz ya dauki abun ta wata sigar. Sai dai abun da be sani ba Hafiz ya gama fahimtar har yanzu akwai Soyayyar Noor a zuciyarsa hakan kuma ya saka shi jin kamar aurenta ba shi da amfani a gareshi. Sai bayan Sallah Magariba suka rabu da juna Hafiz ya nufi gidan Kareem kuma ya fito ya zauna a harabar kamar yadda ya saba domin baya shiga gida sai bayan Isha'i lokacin da yake tare da Safeena gidansa da suke badala yake tafiya sai kusan 11 ko 10pm suke rabuwa...
A hanya yayi sallah Isha'i sannan ya shiga gidansa, yana faka mota yaransa suka fito da gudu suka tarbe shi sai ya daga su sama yana ajewa yana dariya.
“Baku yi bachi ba”
“Eh Daddy me ka siyo mana”
“Ban siyo komai ba amman dai akwai chocolate a daki muje na baku”
Ya kama hannunsu suka shiga ciki babbar ta rufe kofar falon, Yusura ta mike tsaye daga zaune da take.
“Sannu da zuwa”
“Yauwa Sannu”
Yana rike da hannun yaransa ya haura sama suka shiga dakin, gaban maduni ya tsaya ya fara cire agogonsa akan Areef ya hau gado yayi tsalle ya haye masa baya yana dariya, shi ko yana juyowa ya fara masa chakulkuli sai dariya suke har shi gogan. Gurin da yake aje kayan dadin ya bude ya dauko ya mika musu. Yusura ce ta shigo dakin hannayenta a baya tana kallonsu.
“Tine ku je falo zan yi magana da Daddy”
Ya juyo ya kalleta, su suka sauka daga kan gadon suka fice daga dakin. Karasa ta yi kusa da shi ta dora masa abun da ta samu a aljihunsa kan gado. Ya kalli maganin da sabuwar robar ya kalleta irin kallon nan na me aka yi? Ita ma ta yi masa irin kallon ya aka yi suka zo aljihunka. Ya dan tabe baki
“Ba nawa ba ne”
“Su suka kawo kansu?”
“Ni ban taba amfani da condom ba a rayuwata, da maganin da cdm din ba nawa ba ne, dalili ya kawo su”
“Dalilin nake son ji”
“Miye matsalarki da shiga hurumi har kina bincikar kayana? Ki tsaya matsayinki kar ki sake yi min haka”
“Okay so kake na zuba maka ido ka lalace? Matan auren har gida suke zuwa nemanka? Ka ba su fuska na nuna musu ba ni da muhimmanci a gurinka?”
“Babu wata alaka tsakanina da su, can you excuse me please...”
“No idan wani abu ya faru yanzu ai ni za a zaga saboda Momy bata raye ni za a dorawa laifi”
Da mamaki yake kallonta wato gata uwarsa.
“Me ya same ki ne? Why are you behaving like this? Ba ma shiga hurumin juna, me ya canja yanzu”
“Babu abun da ya canja, kawai duk abun da nake ina yi ne saboda yarana, kuma ba zan sake daukar wata karuwa ta shigo cikin gidan nan nemanka, ka tsaya can waje ka yi tun da ka lalata rayuwarka, ka dauki hakkina ga hakkin yara ga hakkin Momy ga hakkin Daddy ga hakkin Allah ga hakkin matan da kake lalatawa ga hakkin mazansu da yayansu kana zuwa lahira wuta a a saka ka kai tsaye...”
Shi dai kallonta kawai yake har ta gama balbalin bala'in ta fice daga dakin. Because he's not a fan of argue. Juyawa yayi yana kallon kofar be taba aikata wani abu da ya shafi rayuwarsa ya ga Yusura ta fusata haka ba irin wannan, kuma ta nuna a fili sai wannan karon, and the most funniest part is yadda ta jero masa hakkin kowa a kai kamar ita zata kai shi wutar. Kai ya girgiza sannan ya shiga bandaki yayi wanka ya fito ya shirya cikin Pajamas.
NOOR POV.
Yadda nake kwana sati biyu da suka wuce haka na kwana a yau ma. Wato kwanan bakinciki da damuwa da kuka da kuma kadaici. Da safe na fito na gyara falon da be yi dattin komai ba na shiga kitchen na hada tea na fito falon na zauna ina sha. Muryar Aisha na ji tana yi ma Hafiz Allah ya tsare. Hakan ya saka ni mikewa tsaye na isa gurin windows din na bude sai na hango shi zai shiga mota ita kuma tana tsaye da murmushi a fuskarta sai hannu take daga masa. Har ga Allah bana son Hafiz kuma bana jin zan iya son sa ba shi kadai ba har zuciyata ba zata taba kaunar wani namijin ba bayan Zafeer amman tabbas ina jin zafi sosai yadda ya aje ni a karkashinsa amman ya kasa yi min inuwa kuma yana min ba ni muhimmanci a gurinsa.
Ina kallonsa ya tuka mota ya fice daga gidan ba tare da ya shigo bangarena ba, na yi tunanin zai shigo ko da fada ne yayi min ya tambayi ina na tafi ba tare da izininsa ba.
Kuka na yi har sai da numfashina ya fara sakerwa na kasa cin komai a wunin sai kuka. Sallah ma daker na yi saboda jikin babu karfi, I'm so hopeless babu mai taimakona, ko da zan mutu a wannan halin na kunci da nake ciki babu wanda zai kawo min dauki.
A falo na yi sallah magariba ina sanye da hijab dina milk color na ji tsayawar motar Hafiz, sanin ba zai leko bangarena ba ya saka ban leka waje ba, kar na yi arba da bakinciki. Sai dai abun da ban yi zato ba ne ya faru, ganinsa na yi a falon kamar an jefoshi gabana ya shiga bugawa da mugun karfi ganin yayi tsaye a kaina yana kallona ni kuma na gagara cewa komai.
“Ina kika je jiya?”
Gabana ya fadi na gagara cewa komai sai hade yawu nake.
“Gurin Kareem? Office kika same shi ko gida.?”
Na sauke kaina kasa nan ma bana iya fadar komai.
“Ke wai sai yaushe zaki yi hankali?”
Na ji sanyi hawaye ya jika fuskata.
“Ta so muje”
Na dube shi da sauri. Kamin na yi wani yunkuri har ya mike tsaye, a dole ni ma na yi tsayen na bi bayansa sai ya juyo ya kalleni.
“Je ki saka talkaminki”
Na nufi gurin da talkamin suke na saka shi kam tuni ya fice daga falon ma. Ko da na fito ya tashi motarsa da kansa ya bude min front na shiga na