Showing 21001 words to 24000 words out of 61932 words
Chapter 8 - DAN HAKIN DAKA RAINA Zuciyar Uwa BY UMMUH FATEEMAH
dukkannin 'karfin ta tana fad'in kin cuceni wlh kin gama dani faiziyya
Abban Hafsatu ne yajiyo ihun kukanta da gunjinta shine yataho yana buga d'akin da karfi, yace kibud'e Balaraba kinajina koh kibud'e maza
Kin budewa tai
Saida taji yace idan bata bud'eba abakin aurenta shine ta taho da sauri ta bud'e kofar
Shiga yay yatarar da Fauziyya kwance cikin jini, yace Subhanallahi
Wannan wani irin danyen aikine kika aikatawa yarinyar nan yanzu idan ta illata fa Balaraba
Hmm niba wannan bane yadame ni tajecan taita jigatarta indai wannan jarababben cikin zai zube ban damuba na nemaata magani
Cicc... Ciiccc.... Cciiiikkkkkk........ Cik...... Ciiccc... Ciiii... kiiiii kuma Balaraba ban ganeba
Aaaaaaa..aaaa.... Aaa..... Aaaaa'aaaaaa.... Baka fahimta bane ina jimamun yadda Hapsatu ta tafi da cikin shegen nan ne batare da'an zubar dashiba
Ok Bari Allah yakyauta kawai nima wannan kayan bakin ciki yana damuna
Amman kuma me Fauziyya tai miki kike dukanta yarinya mai biyayya
Wlh ina takaicin yadda akai tabar Hapsatu tabar gidan nan ne saikace wata sakara takasa tsaydata daga tafiyar datai
Wlh inajin kewar ta sosai wlh ina tunanin yadda za'ai muyi da abun kunyar datai
Yanzu ko ina tayi oho🤔
Alhajine yace hakane Allah yashiryata
Yanzu abunda yakamata mukai yarinyar nan asibiti sbd kinga yadda take zubar da jini sosai
Toh bari in samo d'an sahu sai mu tafi
Futa tayi tasamu anas awaje kallonsa tai ta had'e rai tace kazo ka kaimu chemist
Toh tashi yay badan yana soba suka tafi chemist din
Koda sukaje da'kar aka kar6eta suka dubata akace mata cikin..........
Hallmat ce 💖💕💖
[04/02, 7:56 AM] Ummuh Fateemah🥰💖🥰: 🍃✨🍃✨🍃✨
✨🍃DASHEN 🍃ALLAH🍃✨
WRITTER'S✍🏻 ASSOCIATION
https://chat.whatsapp.com/BHqoOEHjWQz26cyXRvt9V7
🍃ALKALAMI ✍🏻YAFI TAKOBI🗡️
بسم الله الر حمن الر حيم
✨DAN HAKIN🍃 DAKA RAENAH😏🤔✨
💞NAH💞
SADIYA ABDULLAHI UMAR
💞UMMUH FATEEMAH💞
🅿--- 3⃣7⃣&3⃣8⃣
Amman cikin nan dai yana nan babu abunda yasamesa
Balaraba jitai kamar ta mutu
Haka aka gama mata komai suka koma gida suka fara shirin kud'in dazasu shirya tafiya cikin garin kano gobe
Duk wata ajiyarta saida ta had'ata ta tattarata aguri d'aya dan ko nawane zata biya indai cikin nan zai rabu da ita
Ko baccin kirki bataiba dan abun ya tsaya mata sosai aranta
Da asussuba suka fara shirin tafiya babu wanda tasanarwa da inda zasu kama hanya tai tunkafun gari yafara haske suka d'aware ita da Fauziyya da tulin kayan su acikin leda mai ba'ki da fari
Saida suka samu mota sannan hankalin Balaraba yakwanta
Koda suka isa cikin garin kano suna sauka tasamu d'an sahu tai masa kwatancen inda aka gaya mata suka isa
Sun sha wahala kafun su ga likitan suna shiga office d'insa ya nuna musu gurin zama
Suna zama Balaraba tafara rattaba masa bayani komai ya jinjina kai yakalleta yace ok toh yanzu bazan yi mata aikiba sai an ajiyemun 500k inna gama sai acikimun sauran
Nawa kake nufi kasan nibasanin wannan yaren nai ba
Ok toh ina nufin zanyi wannan aikin ne akan million d'aya
Afara bani dubu d'ari 500 idan nagama sai acikamun sauran
Amman idan baku cikaba zanyi mata allurar mutuwa ta mutu
A'a likita duk batakai ga hakaba yanzudai menene ragi dan Allah
Bana yin ragi ninan da kika ganni idan bazaki iya biyaba toh zaku iya tafiya
Amman dan Allah katai makamun wlh yanzu dubu d'ari 700 ne agurina bani da komai wlh gaba d'aya tattalin arzikina na had'o nataho asibitin nan katai makamun dan Allah
Hhhh😁😁 tai mako lallema kinga nayi kama damai taimakonki ne
Dakinsan baki da kud'in aikin ta kika kamo hanya kika taho
Toh kinga gahanya nan maza tashi kufutarmun daga office kinaji na
Dappptahh Dappptahh dan Allah katai maka
Meeeeee?
Menaji kina fad'a?
Dapta menene kuma dapta eyeeeee?
Kayi hkr likita dan Allah karkamun haka
Toh ya zan miki?
Afara aikin zan koma gida kafun agama zan dawo in cika mata sauran kud'in dan Allah wlh inkamun haka
Asirina zai tonu
Toh kawo wanda suke gurin ki yanzu zamu fara shirin aikin in baki cikaba daga yau xuwa gobe
Toh kema kinsan sauran dan zanyi mata allurar mutuwane kin gane ina fatan kina fahimta
Ey nayarda cikin sauri tad'auko jakarta tabud'e zata d'auki kud'in tabawa likitan.............
** ** **
Ta kwanta ad'ayan d'akin saida tayi alwala tayi nafila wannan takwanta bayan tayi addu'ar bacci
Koda asuba tayi da'kar ta tashi saboda gajiya sosai datayi tad'auki ruwa tai wanka tai alwala suma tashi su tai sukai wankan sukai alwala sannan sukayi masallaci dan anata hafamar shiga sallah
Bayan tayi sallah itama karatu tazaunayi sannan ta tashi tafara shirin had'a musu abunda zasu karya sbd suje duk inda zasu sutafi dawuri sudawo kar dare yayi musu
Sai wajen 9:00am suka kammala komai sannan suka futa
Koda sukaje kasuwa zasuyi siyayya sai suka fara zuwa wajen wani mai saida shinkafa sukace zasu sara
Yace kamar yaya suke da bu'kata, hapsatu ce tace kamar kwano 10 ,yace kamata yay kuje cikin 'kauyen nan kusiyi komai akan sari Amman anan gaskiya akwai tsada wlh
Toh shikenan baba
Shin zaka iya kwatanta mana koh kuma ka had'amu da wani yanuna mana
Toh bari in had'aku da yaron shagona yasan gurin sarin sosai
Toh baba ngd sosai Allah yasaka da alkhairi
Amen yarinyata aiduk taimakon kaine idan ka kyautatawa wani kaima sai Allah yakyautata maka
Kiran yaron yay suka tafi tare saida suka hau taxi sannan suka shiga daga bakin gurin suke lodi har ciki naira 50'2 saida yakaisu har gurin sannan yafara nuna musu komai da inda yafi sauki da inda yafi kyau
Siyayya suka fara itadasu Fahat sunyi siyayyar kayan abunci danye sosai da kuma doya da dankalin hausa dana turawa
Shinkafa, wake, gero, masara, bushashshen kayan miya da d'anye da kuma kuka, ku6ewa, daddawa, barkono, karkashi,
Sunsiyi kaya sosai inda saida suka kashe dubu 60 sannan suka samu mota sukai mata Lodi takawo musu bakin titin
Yaron shagon neyatai maka musu suka samu wadda zata kaisu har gida
Hapsatu tabashi dubu 2k amman sam ya'ki amsa shiyabada kud'in motarma
Tafiya sukai bayan sun kar6i number wayarsa, sun dan juma kafun suka isa gida dan sai wajen 1:47 sannan suka isa akan layin yasaukesu suka d'auki kayan suka fara shiga dasu gida inda Allah yataimakesu babu kowa duk anyi masallaci har 'yan zaman majalisar ma babu
Cikin 'kan 'kanin lokaci suka kwashe komai suka shiga dashi gida
Acikin d'akin da Hapsatu ta kwana nan suka ajiye komai sannan suka fara gyagy gyarasu
Fahat ne yadaura musu taliya da manja sukuma suka 'karasa aikin
Sai wajen 4:30 sannan suka samu nutsuwa lokacin sun gama komai sunyi wankama sun gyara gidan
Washe garima kasuwar suka tafi sukai siyayyar kayan had'a lemo da manja, man gyad'a, omo, sabulun wanda dana wanki, maggi had'i kala2,dasu citta, kanin fari, masoro,sukai had'in kori,
Kayan shayi suka siya masu yawa
Sannan tad'aura su Fahat da Nauphal zuwa gida ita kuma taje gurin shagon baba mai hatsi tayi masa godeeya inda take tambayar yaron sa
Yace mata tad'an jira yanzu zai dawo
Zama tai bata dad'eba yadawo da bandir din leda ahannunsa
Murmushi yay sosai yace Ummerh'nsu Fahat ce
Itama murmushin tai tace ey nice
'Karasowa yay suka gaisa suka d'anyi hira, anan take tambayar sa shin yasan inda ake saida waya
Yace mata sosai ma kuwa ai shima yanada shago a kasuwar waya, tace Allah, ey
Dan Allah kaga waya tace nakeson saidawa sbd inasan kud'i
Amman bansan ko nawa bace yazu gaskiya tunda nayi amfani da ita
Toh mugani wacce irice Ummerh
Ciro wayar Hapsatu tai daga cikin jaka ta nuna masa
Amsa yay sai yaduba yace Ummerh wannan ai babbace sosai ma kuma gashi ba'a ta6a bud'e taba sannan kuma bataji jikiba sosai
Ey nawa zaka siya
Gaskiya Ummerh bani da kud'in dazan siyi wannan wayar, amman akwai wani mai gidana acan muje shi nasan zai iya siya
Toh ngd katambayi baba saimu tafi
Toh zuwa yay yagaya masa cewa zai rakata tasaida waya yace toh babu damuwa suje sai sun dawo
Tafiya sukai yakaita shagon ogan nasu yabashi wayar yakalla, yace nawa zaki siyar
Tace a'a kafad'a mana idan naji yayimun sai in siyar idan kuma baiyiba sai in ce kad'an 'kara
Toh ni gaskiya magana d'aya nasiya dubu 65k
Toh amman ogah bazaka 'kara komai ba gaskiya d'aya nagaya miki banasan muzauna kace nace
Yaron babane yace ogah adai duba wayar nan bata dad'eba matsalace ta taso mata ta kud'i dabazata siyar ba
Toh gaskiya daga wannan bazan kara ba inta siyar dubu 70k to
In kuma bata siyar ba toh kawai ta amsa
Amman oga kasan wayar nan zatakai 85k fa amman kad'an 'kara mana
Nidai nagaya maka indai bazata siyar hakaba toh shikenan
Toh yaya kika gani Ummerh
Toh yabari zan dawo jibi
A'a hjy kikawo zan siya 75k basai jibi ba
Toh amman saidai zan baka wayar amman transfer zakamun zanje bank yau inyigyra
OK to Allah yakaimu
Toh ngd
Bashi wayar tai ya rubuta mata komai na yarjejeniyarsu sannan ita da Habu yaron baba mai hatsi suka tafi yarakata banki anan Allah yataimaketa dayake yasan wasu akai mata wasu abubuwan da sauki
Sai wajen karfe 6:00pm sannan tasamu ta taho gida akan gobe takoma ta amshi account number dinta
Lokacin dataje harsunyi komai sunkira mai yin yar rumfa yazo yarufa musu
Kudin tabashi tace gaskiya tayi kyau sosai amman saidai tana bu'katar 'yar karamar kwantena wadda zasu zuba kayan shago aciki
Haka sukai ta fad'i tashi akan su...........
Hallmarth ce 💖💕💖
Keep waiting my fan's👨👨👧👧👨👨👧👦👨👩👦👨👩👦👦👨👩👧👩❤️💋👩💑💃💃💃💃💃
Love you [04/02, 7:56 AM] Ummuh Fateemah🥰💖🥰: 🍃✨🍃✨🍃✨
✨🍃DASHEN 🍃ALLAH🍃✨
WRITTER'S✍🏻 ASSOCIATION
https://chat.whatsapp.com/BHqoOEHjWQz26cyXRvt9V7
🍃ALKALAMI ✍🏻YAFI TAKOBI🗡️
بسم الله الر حمن الر حيم
✨DAN HAKIN🍃 DAKA RAENAH😏🤔✨
💞NAH💞
SADIYA ABDULLAHI UMAR
💞UMMUH FATEEMAH💞
🅿--- 3⃣9⃣&4⃣0⃣
.............. Haka sukaita fad'i tashi akan suga sun gina kansu sosai hapsatu take 'kori ganin ta gina rayuwar yaranta guda biyu
Kasuwanci kuwa sosai yake gara mata gasu Fahat, Nauphal suna suna goyon bayan dukkan abunda ta bullo musu dashi
Har kwantaina ta siya ta shago anzuba kaya sosai acikin sa
Runfar kuwa anan Nauphal yake saida so6o, jusi, lemon Ginger, kunun aya, da kayan snack's kowanne akwai
Suna girmama dukkan wanda suka had'u dashi
Agida kuwa Hapsatu tanayin abunci dafaffe nasiyarwa ko kwano nawa ta d'aura saiya 'kare kafun dare
Yau yakama ranar alhamis suna zaune aphalo lokacin Fahat ma ya rufe shago yadawo gida
Bayan sunci abunci dan akwano d'aya sukecin abunci
Hapsatu ce takallesu tace Fahat, Nauphal kubani aron hankalin ku da nutsuwarku
Atare sukace toh Ummerh
Hapsatu tace inasan ku koma mkrnt yaya za'ai
Mkrnt Ummerh
Ey kuke had'a baki mkrnt nakeson ku koma tunda Allah ya hore mana kuma muna da halin da kowannen ku zai koma mkrnt in sha Allah ta dai2 tamu
Toh Ummerh ni takadduna basanan suna gida
Toh yanzu yaya za'ai
Ummerh kawai in hkr
A'a Fahat zuwa zamuyi kad'aukosu
Ummerh so kike suganeni
Aa Fahat ba haka zamujeba ai nasan yadda zamuje babu wanda zai gane ka
Toh Ummerh
Gobe juma'a saimu tafi da wurwuri, yadda zamu dawo acikin lokaci
Toh Ummerh
Kai kuma Nauphal sai mun d'auko nashi sannan zamuje taka tunda kai nataho maka da naka
Toh Ummerh Allah yakaimu
Dahaka suka kuma kama hira sai wajen 12:00pm sannan suka tafi kowa ya kwanta
Koda gari yawaye kamar yadda tafad'a haka kuwa akai dan sun gana had'a kayan lemon Nauphal sun fasa 'kan'kara akai sun rurrufe kulolin
Hapsatu kuwa fankasu kawai tai sai wainar da suka soya tayi miya suka zuzzuba akula aka sakawa Nauphal acikin shago sannan suka d'auki hanya itada Fahat wanda aka canja masa kala tahanyar yi masa make up irin na buzaye itama Hapsatu tayi shiga irin ta buzayen
Sosai kamar su ta canja suka tafi tasha, Nauphal kawai suka bari agida suka kama hanya su kuma
Basu dad'e da zuwaba suka samu mota aikam 7:00am suka tashi
Sund'ansha hanya kafun suka shiga cikin garin abuja, babu wani 6ata lokaci suka samu mota sukai unguwar wuse2 a'kofar gidan aka saukesu suka biya sannan suka isa bakin 'kofa suka fara nock, baba mai gadi ne yace waye, sukace mune, daga ina kuma, hjy tasan da zuwankune?
Ey, toh bari in bud'e muku
zuwa yay yabud'e musu suka shiga, saida suka gaidashi sannan suka wuce direct phalon gidan suka tunkara
Lokacin da suka shiga babu kowa acikin phalon sallama sukai amsawa mai aikin tai sukace hjy fa, tace tana tare da ba'ki
Toh sai yaushe zata futo, gaskiya ban saniba
Toh inta futo kice mata tanada ba'ki, toh shikenan, ruwa da lemo takawo musu ta futa
Fahat ne yatashi yayi wajen part din mom d'insa yana turawa yaga gurin yayi datti sosai yayi 6ura kwallace ta zubo masa ya share sannan yashiga d'akin sa yafara dubawa, inda ya ajiye takaddunsa yaga babu, hankali tashe yashiga cikin d'akin mom d'insa anan yagansu awatse dan ranar dazasu d'aukesa ranar ne yaje neman aiki bai samuba
Haka tafara tattara su yana had'awa dukkansu yagansu acikin 'yar jakar data zuba anan yamayar dasu yad'uki wayarsa daya ganta acikin durowa Wadda shiyay tunanin ma yasaida ita ashe tana nan
Futowa yafara shirin yi sai yaji muryar amaryar daddy ita da 'kawayenta suna hira harda shewa da'lama futowa suke
Maza yay yasaka jakar takaddunsa acikin 'katuwar jakar daya taho da ita yasassaka komai aciki sannan yad'an leko yaga suna bakin kofar phalo suna saka takalma
Futowa yay ahankali yalalla6o yabar bakin part d'insu
Amaryar daddy ce taganshi tace kai daga ina suwaye ku kuka shigomun gida har phalo
'Kawayen ne suka juyo sukace daga ina kuke
Hantar cikin Hapsatu saida ta kad'a
Kai kuma meya kaika wannan part d'in waye kai................
**** **** ****
Cikin sauri tad'auko jakarta tabud'e zata d'auki kud'in tabawa likitan Amman me babu kud'i babu dalilin su
Ihuuuuu ta rapka saita sulale tafad'i 'kasa sumammiya
Likitanne yayo kanta yana fad'in baba, baba, lpy kuwa
Fauziyya itama kan mama Balaraba tai tana kuka d'aukarta akai aka d'aurata akan gado aka fara duddubata da'kardai tadawo dai2 anan likita yasallamesu, yace maza tabiyashi kud'in dubata dan kati dana magani da allurar da akai mata
Tace bata da kuma ita yanzu batasan yaya zatai ba ankwashe mata kud'in data taho dasu gaba d'aya
Da'kar likitan nan yahakura da kudin maganin daya bata suka tafi, shima saida mutane suka saka baki sannan yabarta
Haka suka tafi gashi babu nasara kuma babu kud'i, kuma ciki yana nan ba'kin cikin ne yayi wa mama Balaraba yawa
Lokacin da sukaje tasha basu da kud'in mota dan dama dan canjin dayake hannun Fauziyya ne sukai kud'in zuwa tashar dasu haka suka wuni tsurrr acikin tasha basu samu wanda zai biya musu kud'iba
Daga 'karshe bara suka kama itada Fauziyya da'kar suka samu d'ari 500 suka siyi abunci suka d'an ci na d'ari sannan suka roki alfarma da'kar suka yadda akan zasu kawosu dari 400 amman saidai suyi goyo amaleji
Haka suka hkr dan babu yadda zasuyi, lokacin da suka shiga garin rano abakin hanya aka saukesu da 'kafa suka isa gida duk sun gala baita sosai dan ba'kar wahala
Suna zuwa abunci suka d'auko suka kamaci suka sha ruwa agurin sukai bacci
Da gari yawaye balaraba tashin Fauziyya tai suka tafi gurin nakan tsauni, nan suka gaya masa komai daya gabata, yace musu mafuta d'ayace ta auri jazuli sai akwantar da cikin idan ankwana biyu sai atashi cikin
Balaraba tagirgiza dajin abunda nakan tsauni yace ta'auri jazuli kuma nakan tsauni nida nakeson ayi wacce za'ai Fauziyya ta auri doctor faruq din nan
Hhhh hhhh aikinbar gini tunran zane abunda yafi sauki kenan amman indai kinasan ta auri wannan likitan saidai kikawo ba'kin alade da mage da bunshuru
Amman da sharad'i cewa saita auri jazuli ta haihu tukunna idan ba hakaba wannan aikin dazamuyi bazai yuyu ba
Toh zanyi kamar yadda kace, haka suka taho duk ba'kin ciki yayi mata yawa, wai Fauziyya ta auri jazuli wannan d'an tashar da ba'asan asalinsaba, dan shaye shaye kuma
Wannan wace irin 'Kaddarah😭 ce
Tun kafun su'karaso sukaje shagon su jazuli amman baya nan haka suka dawo badan tasoba
Tabarwa Anas sallahun inya dawo agaya mata, ace tana neman sa
Sai wajen karfi, 10:00pm sannan suka shigo shida jazuli, sallama sukai anan kofar daki suka tarar da su azaune
Kallon Anas tai tace, toh ngd maza jeka , Toh mamah sai anjima
Futa yay abunsa kallon jazuli tai tace zauna mana tsinanne, zama jazuli yay duk ya tsorata dan yasan Fauziyya tarugada ta tona masa asiri
Zama yay ahankali kallonsa tai tace yawwa magana nakeson yi dakai
Too...... Too........ Toooooooottttt...... tooo ina jinnnnnki mamah
Maman uwaraka, inasan ka'auri Fauziyya sannan asatin nan nakeson ad'aura aure ku
Aure kuma
Tabbas aurenta zakai dan bazaka zubarmun da mutunciba katozartani agaban jama'a
Wulakanci kamar yaya kuma
Ey kaje kai mata ciki shegen gora sannan har kake tamabayar wani abu
Ai mamah ita tazo tace in rage mata zafi bani nace tazo ba
Inna lillahi wa inna ilaihi raju'un yanzu abunda kika aikata kenan Fauziyya kinsanda kinasan hakan ai saiki gayamun in samar miki miji kiyi aure, amman saiki zubarmun da mutunci na
Kiyi hkr mamah
Hkr'n uwarki
Tashi kiban guri
Kai kuma ina zaka sakamun "yata dan wannan aure yazama dole sai anyishi shine rufun asirina danaku
Toh nidai bani da inda zan ajiyeta sannan kuma bani da kud'i amman idan kece zaki kama mana haya to sai ayi wannan auren idan kuma ba haka ba saidai ahakura, dan ni nan ma gaba zanci dankar asirina yatonu
Haba.... Habaaa..... Aibaza'ai hakaba jazuli kabar zancen tafiya
Ninan zan nema muku haya koda d'aki d'ayane da band'aki da kicin
Aaaatooooo danni uwatace zata gindayamun doka kawai inbi
Toh yanzudai ka shirya asatin nan za'ayi auren nan
Toh ni nayi nan, Tashi yay yafuta abunsa
Mamakine yakamata tana tunanin yadda zatai haka taje tafara buga nan buga can tana neman yadda zata tara kud'in dazata kama musu haya
Yau yakama ranar asabar and'aura auren jazuli da Fauziyya wanda hakan yabawa su Anas da Baban su Hapsatu mamaki dan yashiga rud'ani dajin