Showing 15001 words to 18000 words out of 61932 words

Chapter 6 - DAN HAKIN DAKA RAINA Zuciyar Uwa BY UMMUH FATEEMAH

10 Jul 2026

109

da ramun la6ewa tae agurin dan anan ne xata tsira inba hakaba tana kara tafiya xasu ganta akan tudun dutsen



    Dasuri suka karaso gurin muryar Balaraba taji tana fadin ku nemota duk inda take nagaya muku dan baxata bar wannan kauyenva

    Sosae suka shiga nemanta ko ina da ina suka hah haskawa suna dubata
    Amman shiru babu wanda yaganta wasune suka shiga cikin kogon suka fara dubata
    Wasu kuma sukae wajen ruwan suna dubawa amman shiru

    Wanda yay gurin ruwane ya karasa gurin wani dan rami
     Yana xuwa yahaska yaganta agurin tarike bakinta idonta yana xubar da kwallah sosae
        Hada hannuwanta tae alamar roko tace dan Allah katae makamun karka fada musu ina nan kaji
     Katae maka min tana jujjuya kanta hawaye 😭😭  suna  xuba
    Tausayi tabashi sosai dan yadda yaganta koh takalmi babu duk taji ciwo akafafunta sosae
      Kada kansa yay yajuya yafuto daga gurin yana fadin babah muwuce kawai dan babu kowa acikin gurin nan naduba ciki da waje
     Daya daga cikin sune yace mujuya kawae tunda batanan
   wani yace ina baridae mukara dubawa dan kasan dubawar dan gara badubawa vace
     Haba babah ince maka basannan kace suna nan toh maxa jeka wlh ruwa yacinyeke
     Haba akwae ruwa agurin ne
Aaaa🙄🙄🙄🙄🙄 kaji rainin hankali jeka gani mana
      Aa muje kawae
Atoh muna nan ma wata kila ta yanka tawani gurin ma musata kawae kaji babah
    Hakane dan gara musata maxa kar murasata


Balaraba ce tace yanxu karfe 2:00pm tun 1100pm muke neman ta
    Toh bari in gaya muku indae kunasan kudinku to kutatbata kunyi Raping dinta kuduka Kunga takasa tashi sannan kubarta ni na wuce na


    Karki damu xamucika aikinmu kuwa kodan maekon yarinyarma dole ne mudage mucika burin mu da kuma aikin ki ranki ya dade


Tafiya tae sukuma suka kara gaba suna neman ta gajiya sukae dan awani gurin ma an fara kiran assalatu sosae

    Komawa gida sukae shikuma dan gara yaxame jikinsa yadawo gurin tarar wa yay tana ko karin futowa
    Har xata koma
Yace mata ke dallah dan garane kawo kayan naki in rakaki kibar kauyen nan dan in ba hakaba wlh dasafe kara baxa wasu xatae akan sunemoki

    Toh mika masa tae yadauki jakun kuna yacire takalmin shi
    Yace mata ungo saka maxa kitaho mutafi

    Amsa tae tasaka sannan suka Futa atare yana nausar dajin tafiya sukae sosae sannan suka je bakin titi lokacin ma an fara sallar asuba
     Wani mai napep ne yaxo wucewa yatsayar dashi yace masa tasha
    Ok kushigo
Shiga sukae suka tafi
Basu dade ba suka isa tashar
Nawa abokina
   Kawo dari kawae
  Toh ngd sosae mika masa yay sannan yadauki kayanta yakaeta ciki yace yanxu kiyi sallah kafun afara Lodi nima bari inyi sallar
     Toh
Ruwa yakawo mata sannan yajuya shima dan tayi alwalar
   Saeda sukayi sallah sannan yadauki dubu biyar yabata yace mota tana fara Lodi kisamu kihau maxa kinjini koh
   Dan nasan har tashar nan saetasa anxo anduba nasan halin Balaraba batun yau ba muke mata aiki
    Amshi wannan wayar idan kun rasa gurin xama kisaeda ita kisama muku koda daki dayane agidan haya kinji koh

     Toh kavarshi akwae kudi agurina
Amshi da allah can maxa kuje can kutsaya keda Nauphal kafin afara doli
    Toh ngd Allah yasaka da alkhairi Allah yasa kafi haka
  Ameen ngd sosae
Juyawa yay yakama hanayar barin tashar
     Taba dadeba aka saka mota nan aka fara loda kayanta sannan suka shiga ita da Nauphal xama tae tana dan dudduba kafarta da take mata xafi gani tae duk taji ciwo sosae akafar


     Sae wajen 6:00am Sannan motar tafiya KADUNA tacika suka kama hanya
    Kudin mota akace musu tadauko xata bayar sae wani mutum akusa da ita yace aa bari in bayar
    Kallonsa tae taga bata san saba amman yabata kudin mota godeeyah tae masa
    Yace babu komae
Haka sukaeta tafiya vasu suka isaba sae wajen 10:30pm sannan
   Suna sauka aka sakko mata kayanta dauka tae tayi shiru tana tunanin ina tace akaeta tunda ita batasan ko inaba
     Bakin wata inuwa suka xauna tacewa nauphal tsaya anan in samo maka abunda xakaci  kaji dan kirki
     Toh Ummerh saekin dawo
Tafiya tae wajen wata mae koko da kosae ayar rumfarta tace abani koko da kosae
    Toh na nawa
Kokon 50 kosan 100 fanken 50
   Dari biyu tabata kar6a tae tafara daura mata kosan tae da panke sannan tadauki leda xata saka mata Kokon aciki
    Hapsatu ce tace aa kixubamun aroba yanxu xamusha acan mukawo miki
     Toh dan Allah inkunsha ki kawomin dan 6ata suke wlh
    Toh in sha Allah amsa tae taje wajen Nauphal tashimfida xanin data goyo nauphal dashi  sannan tace xauna yaraon kirki inkawo maka ruwa kawanke hannun ka
    Toh Ummerh ai nayi alwala yanxu nayi sallah da wannan ruwan na butar can dana gani

    Toh inga hannun naka mana
Nuna mata yay
    Tae murmushi tace toh xauna kasha kaji

    Xama yay yace Ummerh musha tare kinji Ummerh ta
    Toh saka hannu tae tafara cin kosan tana shan Kokon

    Koda suka gama tashi tae takae mata robar
   Har wajen 12pm lokacin ma babah mai kosae tagama wanke wanke takeyi dakanta
    Hapsatu ce taje tace mata dan Allah koxan iya yimiki wanke wanke
    Aaa aaa barshi kawae
Kawo intayaki toh
Mika mata tae tacigaba da wankewa ita kuma tana saka sauran kayan acikin shagonta
     Haka har suka gama
Hapsatu ce tace mata dan Allah babah ina xan samu gidan haya Koda daki dayane da bandaki

    Aaaa kajimu da tsiya wani irin gida keda baku da  matsugunni kika kamo hanyar xuwa KADUNAH IYEEEE 🤔 🤔 🤔
      A'a dolece tasani xuwa babah
Toh muje gidana daganan sae afara nema muki........
   🍃🍃🍀🍀🍃🍃🍀🍀🍃

   *DASHEN🍃ALLAH*
*WRITING ASSOCIATION*


*
*DAN* *HAKIN* 🍃 *DAKA* *RAINAH😏** 🤔

             Nah
  💕Ummuh fateemah💞

🆓 *page*
   Page 2⃣9⃣&3⃣0⃣


*Wata* katuwar motace tadaki wannan nafef din nasu ta cillasu can cikin dajin daga gefen wata bishiya
    Ko minti uku basuyi dafadawa gurin ba bala da baba mai kosai suka fara yunkurin futowa aikuwa kafun sukarasa futowa nafef din yakama da wuta gaba daya saici yake
   Ihu suke suna neman tai mako Amman babu kowa agurin koh alamar motsin mutane babu bare susaka ran ceto.......


Wata motar hayace tazo wucewa hapsatu tasa hannu tana tsaydata Amman ko sauraran su basuyi ba suka wuce abunsu

   Komawa sukayi bakin Titin suna jiran ko xasuga wata tazo wucewa
    Suna zaune sukaga wuta ta kama bawwww
    Dasauri takama hannun yaran tace kutashi mutafi wuta
   Dahanzarinsu suke tafiya gashi duk sun gaji sosai gurin data saba kwanan anan taje ta kwanta ita da yaran
    Basu dadeba bacci yadaukesu suduka dan amugun gajiye suke

   Basu suka farkaba sai da gari yawaye Nauphal ne yafara tashi yaga ummerh sa akwance tana bacci
    Murza idonsa yayi yace ummerh nah kece ummerh
    Jin ana shafa mata fuska yasata bude ido cikin Sauri tana mikewa tsaye
    Ganin Nauphal ne yasata murza nata idon itama dan ganin shine ko kuwa gizau yake mata

    Shidinne dai wata muguwar runguma takai masa tana kan kame shi gam ajikinta kamar za'a kwace mata shi
    Kuka suka saka atare dan sun rasa mezasuyi idan ba kukanba
    *FAHAT* dayake bacci kukansune yata sheshi yazauna yana kallon ikon Allah dan shi dai yakasa gane musu
    Duk da yafi Nauphal girma dan zaikai shekara 15 Nauphal kuma yanzu yake 13 banbancin kadanne

   Shima hapsatu kamosa tayi tarungumesu gaba daya tanaci gaba da kukan sosai saida sukayi mai isarsu sannan sukayi shiru

    Cewa tai kujirani anan inje in samo mana ruwan alwala kunji
    Toh ummerh
Tafiya tai tasamo musu ruwan alwala dayake babu nisa da jama'a fiyo wata tasiyo musu Leda daya sannan tadawo alwala sukayi sannan sukai sallah tanajin kunyar yin sallah gari yayi haske amman yanzu babu yadda ta iya haka tayi tanata istigfari

    Ce musu tayi mukoma can dinnan ko kuma muzauna anan dan niyanzu tsoron mutane nake

    Cewa sukai A'a muzauna anan kafun musamu gurin zama
    Toh bari inje in siyo mana abunda zamuci
   Tafiya tai cikin garin tana duddubawa har taga inda ake shinkafa da miya ta tsaya ta siya musu ta dari biyar sannan ta siya ruwan shayi dauri uku da bread sannan tadawo
    Zama sukayi sukaci suka koshi sannan tace muje gidan wanka muyi ko
   Kunga mafi kyau shiga cikin mutane neman inda zamu zauna

    Aikuwa haka akayi gidan wanka sukaje sukayi wankansu tadauko kayan *Nauphal* tabawa *FAHAT* yasaka itama tasaka wasu kayan suka daure wanda suka cire aleda suka saka abakkonsu

   Shago taje ta siya musu takalma da man shafawa sannan suka shafa
    Shiga suka farayi cikin garin suna dan zazzaga garin *KADUNA* kozasuga inda yayi musu sukama haya

   Wani mutum suka gani yatsufama sosai suka gaidashi sannan sukace masa dan Allah suna tambayar shin ina xasu samu gidan haya agarin nan koda mai daki dayane da ban daki
   *Babah sa'idu* yakallesu yace 'yata inake ina iya kama haya
   Tace Babah zan iya insha Allah
Yace to shikenan ni dillaline ina bada hayar gida amman muje kiga wanda suke ahannuna kozasuyi miki saiki za6i daya daga ciki

    Toh *Baba* muje tafiya sukayi mai dan nisa kadan sannan suka shiga cikin gari sosai unguwace ta jama'a
    Nan yafara nuna mata gidajen kowanne da mutane acikin sa sannan kuma yakaita wasu Gidajen
    Sukuma daya mutum dayane aciki dayan kuma mutum biyune aciki amman matsalar duk vandaki dayane dasu

  yace toh acikinsu wanne ne yayi miki
Toh baba duk sunyi amman matsalar ta bandakice wlh Baba daso make dasan samune ko zamu samu mai ban daki daban
   Ey Yar nan zaku samu amman da tsadafa sosai dan duk wadannan gidajen dana nuna miki dukkansu dubu 10 ake biya duk shekara
   Amman mai ban daki daban da phalo da daki biyu da kicin shikuma dubu 20-30 ne duk shekara
    Yakike gani shidin zankaiki ko kuwa
Toh baba muje in gani
   Nafarkon da sukaje d'aki biyu, ban d'aki, kicin, babu phalo kuma part biyune kowa da nasa shine dubu ashirin #20
   Shikuma dayan d'aki biyu, phalo, ban d'aki, kicin sai dan karamin tsakar gida shikuma part 4 aciki shine me dubu 30# kuma akwai mutane aciki guri dayane ba'akama ba inda ya nuna mata

    Toh gurin yayi amman itakam tsoron mutane take sosai dan haka yasa tace suje dayan wanda bashi da phalo suzauna kawai tunda shi kofar shiga part dinkama daban take data daya 6angaren kuma akwai katanga data shiga tsakaninsu kowa kofarsa daban
   Nan taza6a tace masa nan yayi Baba bari muzauna anan kawai
   Toh shikenan amman kinsanfa nan dubu #20 ne koh duk shekara
   Ey baba zan biya yanxu bari in baka rabi zuwa nan da sati biyu zan cika maka to shikenan

    Shiga sukayi da kayansu taduba tadauko masa dubu goma acikin kudin ta sanann tafuto tace gashi Baba
   Yace A'a Yar nan bari in kira dayan abokina sai mu amsa kinga saboda yanayi na rayuwa yau kaine gobe ba kai bane ko yakikace
    Hakane kam
Wayarsa yadauko yacdanna kira wata number aka dauka nan yayi masa jawabi sosai yadda zai gane sannan yace gashinan zuwa
   Bai dadeba  yakaraso nan akayi komai akan idonsa
   Nan sukace taciko dubu biyar kawai tarinka biyan dubu shabiyar 15 duk shekara taji dadi sosai kuwa
   Baba sa'idune yakalleta yace yata kije asibiti aduba miki kafar nan taki dukta kumbura gashi taja ruwa ko kuma kiduba kiga ko sartse kikayi
   Toh baba IN SHA ALLAH zanduba in gani kafun inje koda chemins ne
   yace mata yanxu kingani kowa yanada nasa shaidun koh ke da danki daya da Malam baba
   Nima nida danki daya koba hakaba
Kinga hakan yafi kai waye
   Ey Babah ngd sosai
A'a karki damu ai duk wanda yataimaki wani shima Allah zai tai makesa
   Hakane kam ngd
Sosai Allah yasaka da alkhairi
   Ameen tafiya sukayi itakuwa Hapsatu suka fara duba yaya zasu fara aikin gidan yanzu
    Cewa su Nauphal tai ina zuwa kujirani zanje in siyo mana tsintsiya da allura in duba wannan kafar
    Toh Ummerh saikin dawo
Toh ngd
   Futa tayi taje wani shago data gani acan bayan unguwar su tasiyo abunda duk zasu bukata sannan tadawo gidan
    Lokacin sukam harsun fara futo da "Yan tarkacen da suke cikin dakin harda wasu kodaddun labulaye da tar kacen kwanuk da tukwane da farantai da wasu fasassun robobin ruwa da kuma jarka guda 6 yalaye nazuba ruwa

   Cewa tayi toh wadannan kayan banamu bane amman bari inje in gayawa Babah sa'idu cewa munga kaya yaya zamuyi dasu

   Toh ummerh kibari muje mugaya masa mana
   A'a kubari inje dan yanzu nikam tsoron garinnan nake sosai wlh
   Toh ummerh
Futa tayi tana futa tag...........


***     ***      ***

A6angaren su *Balaraba* kuwa haka suka koma gida babu wani farin ciki ko kwanciyar hankali atare da ita
   Koda gari ya waye sun shiga tashin hankali sosai dan dukkan tashoshin garin Rano lungu da sakonsa saida suka duba amman babu su Hapsatu babu dalilin su ko kuma alamun su

   Hankalinsu yayi matukar tashi dan Alhaji daya dawo yatambayi Hapsatu
   Sun rasa mezasu ce masa
   Kawai sai fauziyya tai katsa landan tace muma bamusan inda ta tafiba
   Tun jiya mun kasa bacci sbd nemanta da muke
   Wlh mun gaji da halin wannan banzar yarinyar ta tafi yawon karuwancin ta sanann tabarmu da nema haka kawai
      Kema dai kyafad'a haka kawai muyi tafaman wahala akan karuwa
   Wlh mama wadda batasan ciwon kantaba ma kuwa wadda bata da aiki sai karuwan..........
   Wani wawan mari aka dauketa dashi wanda yadauke dukkan wani jinta kanta ankara aka kara dauketa da wani marin saida yayi mata kwarara guda 4 sannan yakyaleta shima ganin tafadi kasane hancinta yana futar da jini shine yasashi kyaleta
   Duka yakai mata da kafa yana fadin akwai wanda yakaiki karuwanci ne eyeee
   Tunda anriga angur6ata miki rayuwarki
   Kuma kisani wlh dukkan sharrin da ake kullawa akan Hapsatu kanku zai koma
    *WLH IN GAYA MIKI*
*DAN HAKIN DAKA RAINA* *SHINE ZAI TSONE MUKU IDO*
   Karkuyi tunanin kuna cutar da ita da kaninta dan ganin bata da kowa
   Toh ina mai tabbatar miki da cewa Allah yana tare da su akoda yaushe
    Kuma dukkan wanda Allah yatsaya masa to bashi dasauran Kuka
    Har lokacin dukanta yake kamar jaka
Da gudun tsiya s.......


Hallmarht ce💞💖💞
[04/02, 7:56 AM] Ummuh Fateemah🥰💖🥰: ✨🍃DASHEN 🍃ALLAH🍃✨
WRITTER'S✍🏻 ASSOCIATION
https://chat.whatsapp.com/BHqoOEHjWQz26cyXRvt9V7
🍃ALKALAMI ✍🏻YAFI TAKOBI🗡️
بسم الله الر حمن الر حيم
✨DAN HAKIN🍃 DAKA RAENAH😏🤔✨

💞NAH💞
SADIYA ABDULLAHI UMAR
💞UMMUH FATEEMAH💞



🅿--- 3⃣1⃣&3⃣2⃣


🆓 page

   Da gudun tsiya sukayi kansa suna cewa bazaka denan dukan taba ANAS wannan wani irin haukane eyeee


Gajiya sukayi dan sunkasa kwatarta daga Alhaji har mama Balaraba sunkasa amsarta dukan ta yake kamar an aikoshi

   Balaraba ce tace wlh ANAS idan baka daina dukan taba saina tsine maka kaji narantse wlh kuma baka isa ka karyamun rantsuwata ba

   Jin hakan ne yasashi tsayawa da dukan nata Amman fa tadaku sosai dan bakaramun duka yayi mata ba
    Dan tunda take aduniya bata ta6ajin irin wannan dukan ba gashi kuma yau ta d'an d'ana

    Kamata sukayi itada Alhaji sukayi waje dan zuwa asibiti dan tahancin ta, tabakin ta, ta goshi, duk jini zuba yake
    Sannan  gawani nan yana zuba ta kasanta kamar an6alloshi
    Dak'ar take iya taka kafarta saboda muguwar azaba
    Amugun wahale take dan jitake kamar jiri zai dauketa babu yadda suka iya dole yasasu suka je chemist dan afara dubata kafun suje asibitin

   Da'kar suka shawo kan Baba iyabo yadubata sosai yayi mata kokari sosai nan yake sanar da Balaraba tana da ciki dan Allah yataimaka sun kawota da wuri dabasu kawota da wuriba daya zube

Tashi tayi amugun razane tana fadin CIII MEEEEEE............



***        ***        ***

Tana futa taga abokin Baba sa'idu gaisawa suka karayi take gaya masa kayan dasuka gani acikin dakin nan yace mata wlh matar data kama haya agidan ce tayi arziki shine tace duk kayan dasuke shiki tabar mana tofa shine muka tsinci na tsinta mukabar sauran
   Kiyi amfani dasu kawai in kina so Wanda basu da amfani kuma ki xubar
   Toh Baba ngd sosai Allah yasaka da alkairi
  Amen "Yar nan
Komawa tayi cikin gidan ta tarar harsun fara sharo dakunan da ban dakin sunata cire yanar
   Ita ma fara tayasu tayi aikin dansu gama da wuri saida suka share ko Ina nan suka kwashe sharar suka saka abuhu
   Lokacin da suka bude kichin dinne sukayi mamaki dan jerene aciki nakomai tsaf Ba'ata6a ba harda sababbin kuloli acikin sa fara dubawa sukayi ahankali nan sukaga harda shinkafa buhu 2 da taliya da maka roni
   Kayan avunci sosai ne acikin gurin harda mai doyarce dai tafara hun huna da dankali saidai 6ura da sukasha sosai
    Ce musu tai bari inje in gayawa Baba kayan dayawa sosai fa

   Sukace Toh
Tafitai gidan tayi sallama
Amsa mata sukayi nan take fada masa komai akan kayan dasuka gani sosai dana abunci
     Babane yace mata kiyi amfani dasu Hapsatu wlh muma mun samu arziki sosai acikin wannan gidan
   Wadannan Allah yayi rabon kine Hapsatu karki damu kinji
   Toh Baba ngd sai anjima
Sannan ko kinga wani abun ma karki dawo kidauka kawai
    Toh Baba
Tashi tayi danta futa kafarta ta rike gam takasa takata
   Salati tasaka
Baba Hasiyace tace lpy "Yar nan meyasameki
   Wlh Baba kafatace nakasa taka ta
Assha LAHAULAH
   BARI MUGANI
zuwatai tafara tai maka mata tazauna sannan tace muga kafar taki
    Mika mata tayi
Inna lillahi ni Hasiya mezan gani haka saikace ba mutum ba dawannan katon hakin akafa fuwanki har kusan 3 Amman kina tafiya haka nan

    Binta Binta kina inane
Ganinan Babah lpy nikam wannan kira haka
   Dauko mun matse fata da leta da kuma allura maza kinji yi sauri
   Dauko mata tayi dan aleda take ratayesu tasa asaman sip

   Yawwa daukarsu tai ta konasu da letar nan sanan tadauki wata auduga tagogesu tas
   Ahankali tafara cire mata sartsen duk inda tacire sai yayi feshin ruwa sosai
    Haka saida tacire mata su tsap sannan tafara buda gurin da allura tana yankewa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login