Showing 30001 words to 33000 words out of 39414 words

Chapter 11 - WAZAN ZABA by Amnah El Yaqoub

14 May 2026

116

Karon Kam, Alhaji ne da kansa yajasu amotar




*** *** ***



Yaya kakejin jikin Naka?

Jiki da sauqi doctor, nifa banajin komai, saide kawai inajin Tari yanadan tasomin kadan



Eh gaskiya ne soja, wato nanma de sai an nuna jarumtar, to kadaure karkayi tarin Koda kanaji din,
sannan karkayi wasa dashan maganinka



Cikin Murmushinsa Mai tsada yace babu damuwa doctor, Bayan tarin babu abinda nakeji

, zan Iya Zuwa Naga jikin Bros Dina?

Farhan dake gefe yayi sauri yace haba Yaya Dan Allah kabari kasake Jin sauqi saikaje



Murmushi doctor yayi yace eh gsky de Hakan zaifi sannan yafita

Doctor na fita me aikin su Hajiya tazo driver yakawo ta, takawo musu abinci da abubuwan buqata



*** *** ***
Tana zaune akujerar dakin tafada duniyar tunanin yar'uwar ta, Ko tana wanne Hali yanzu oho

Allah de yabasu lafiya baki dayansu



Tana wannan tunanin taga yabude idonsa, Ahankali dasauri taqarasa bakin gadon nasa tace sannu Yaya,
mekake buqata yanzu? Babu inda yakema ciwo?



Haka taita jero Masa wannan tambayoyin



Kansa yadafe da hannunsa cikin rintse ido yace kaina kemin ciwo sosai



To Bari nakira likita, tafice da gudu Daga dakin

Tare tadawo da doctor yaduba shi yace a bashi abinci yaci da magungunan sa, zai dawo yayi masa allurai



Doctor na fita, dakin yasake yin Shiru, ita Bilkisu ba gwanar rawar Kai bace irin Iman, sannan ita bawani
sabawa tayi dashi ba Kamar Yanda Iman tasaba dashi duk taga yayi kwarjini, tarasa me zata Masa, wayyo
Allah itakam meyasa Alhaji yace ta zauna da Yaya yau, Allah yadawo dasu gaskiya Suna Zuwa zan koma
gida



Tunawa tayi da maganar doctor, Ahankali tatashi tazuba masa abincin, jallop din taliya ce da tsokar
Nama aciki manya, sai turiri abincin yake, tazuba acikin flet tasa spoon

Agefen sa ta zauna tace Yaya ga abincin Kaci, kaji doctor yace zai dawo yayima allura



Ahankali yadauki spoon yafara cin abincin, cokali biyu yayi yace naqoshi



Haba Yaya, Dan Allah kaqara Ko kadan ne



Kansa yakawar gefe fuska babu alamar fara'ah yace naqoshi nace
Kallan abincin tayi, Yama za'ai yace yaqoshi, kawai de damuwa ce tasa Baisan cin abincin



Diba tayi cikin nutsuwa tanufi bakinsa d abincin



Kallan ta yayi, yaushe yafara wasa d Bilkisu dazatai kokarin bashi abinci abaki? Kota manta Cewa shi
ganin qanwarsa yake mata? Koda yaushe gani yake batada banbanci da Farhan da zainab auta

Shiyasa ma Bai wani saki jikinsa da itaba bare harta Raina shi

Kawar da kansa yayi,



Jikinta ne yayi sanyi Ahankali tace please Yaya



Haka yadaure take bashi abincin, sai wani Bata fuska yake Kamar tana bashi magani

, Saida ta tabbatar ya qoshi sannan tadau tissue ta goge masa bakinsa, tafice Daga dakin

Shide Binta yake da kallo kawai, yana aikin Bata fuska



*** *** ***



Washe gari Bilkisu tahada yanata yanata tatafi gida, itakam bazata Iya wannan Zaman jinyar ba, duk
mutum atakure, shikkenan saide ta zauna tayi dunkum itaba kurma ba, Bayan ance yadena tunani,
Amma bazai yimata magana ba saide ya shareta yana aikin tunani, wallahi Gara Hajiya Ko mamy sudawo
su zauna dashi, bazata iyaba

Ko Farhan dayake kula da Aliyu batayiwa sallama ba tayi gida



Shi kuwa Farhan kalau suke fira da Aliyu, Kamar ma ba marar lafiya ba, sosai yake Daurewa Akan komai



Duban Farhan yayi yace jeka ganomin jikin Bros kaji Farhan
Zuciya daya Farhan yatafi dakin Imran, yatarar dashi Ana qara masa ruwa Amma bacci yake

Danhaka yajuya dakin dasuke, yana Zuwa yaga wayam babu Aliyu babu labarinsa

Hankalinsa ne yatashi, nan take yadinga nemansa daki daki, yafuto harabar hospital din nanma babu
Aliyu babu labarinsa, kusan minti talatin yana dube dube



Wata dabara ce tafado masa nan take yadauko wayarsa ya kirashi, bugun farko yadaga, cikin tashin
hankali Farhan yace, Yaya Aliyu kana Ina ne sai nemanka nake?



Murmushi yasaki Mai aji yace Farhan natafi India, idan kahada kayanmu kakoma gida kasanar dasu Alhaji
Cewa Nina wuce India



Sharhi please πŸ™πŸ»



Mrs Usman ce WAZAN
✍🏻 ZABA?πŸ’–



Writing by Amnah El Yaqoub



Bissmillahir-rahmanirraheem



21



Daria ce takama Farhan, yace to Yaya, tareda kashe wayar

Dakinda suke yakoma yahada komai, yaje Har office din doctor yace to likita nizan wuce gida, mun
sallami kanmu



Doctor yace ban ganeba, kamarya kun sallami kanku?
To likita majinyacin ya wuce India wajan budurwar sa



Murmushi doctor yayi, Zuwa yanzu Kam yagama Gane Cewa duk saboda soyaiya ne suka shiga wannan
halin



Toshikkenan, idan kaje kagaida Alhajin



Farhan nafita ya wuce dakin da Imran yake, yana Zuwa yaganshi yana bacci, Amma Kuma dakin babu
kowa, tunani yayi Cewa may be Bilkisu tana toilet, danhaka yaja dakin Yarufe tareda fita



*** *** ***



Hajiya na zaune a dakinta tayi Nisa cikin tunani, yanzu saboda soyaiya yaransu Har uku Suna kwance a
asbiti, saboda soyaiyar mutum daya

Babban danta datake ji dashi, yaro me kazar kazar, marassa damuwa Arai, shine kwance a asbiti harda su
hawan jini, Bata fatan ace Ko zazzabi ne yasamu Imran dinta, Amma yau gashi akwance asanadin soyaiya

Shiru tayi tana neman mafita



Wani tunani ne yafado mata, idan Dukansu maza biyun Akan mutum daya ne suke wannan jinyar, Tome
zai Hana tasamowa wannan family nasu mafita ta wata hanyar?

Bilkisu yar'uwar Iman ce, tare suka tashi, tanada nutsuwa da hankali, babu abinda Iman zata fadawa
Bilkisu ta fannin diri na hallita kokuma sura

Inda halinsu ya banbanta kawai waje dayane, Iman akwai daukar wanka, tana saka kayaiyaki na kece
raini, sannan ta kasan ce mutum ce mai nuna kyanta afili, wanda Hakan yasamo asali ne ta wajan Imran
daya dorata Akan wannan turbar



Sabanin Bilkisu datake shiga ta mutunci, gakuma sanyin Hali, kwata Kwata batasan damuwa shiyasa ma
Bata cika shiga sabgar Yan gidan ba, itade Barta da zeey auta
Bilkisu tayi ta Ko wanne fanni, saide Kuma Kash Shu'aibu yayi musu katanga da ita, saboda wani dalilin sa
can marar tushe



Tashi tayi tana zagaye dakin, afili tace wannan Karon Kam Shu'aibu saide kayi hakuri, inaji Ina gani bazan
rasa yarona ba, domin kuwa idan aka biya ta Alhaji dasunan Wai Iman saita zabi daya acikinsu, tofa Iman
batada niyyar zaba, saide Daga qarshe Alhaji yace kowa ya hakura d ita



Da wannan tunanin ta futo falo, turus ta tsaya ganin Bilkisu kwance akujera tana danna waya



Tace a a yaushe kika shigo gidan bansaniba?



Dago kanta tayi tareda ajiye wayar tace Hajiya wallahi na Dade da Zuwa, gajiya nayi da Zaman Shiru haka
ba dadi



A a kamarya gajiya kikai?



Cikin shagwaba tace Hajiya Allah nikam nagaji, Wani yaje kawai



Sallamar Farhan ce ta tsaida musu maganar dasuke



Hajiya tace a a, kaikuma yanaganka da Kaya ahannu? Wai meyake damun kune? Duk kun baro marasa
lafiya a asbiti kun iyo gida



Zama yayi Akan kujera yace Hajiya ai ni mun sallami kanmu, yayi ya fece India wajan Iman, to dawa zan
zauna? Shiyasa Nima nayo gida, Kuma yace afada muku shiya wuce India



Murmushi Hajiya tasaki, ta kwalawa mamy Kira, futowa tayi tana daura dankwali tace Hajiya ya akayi?
Wai Daga kwanciya bacci ya daukeni, kinsan jiya bamu rintsa ba
Hajiya tace kinji Wai Aliyu yatafi India, shine Farhan yadawo gida da kayansu, Wai afada mana shiya tafi,
ita Kuma wannan tagaji ne shine saboda tsabar sakarci tabarshi a asbitin ita Kuma tayo gida



Tafa hannu mamy tafara tana Cewa, la'ilaha illallahu, yanzu shi Haidar dinne yakama hanya yatafi, wato
Bai duba rashin lafiyar dayake ba



Hajiya tace to yaza'amusu, ai sai hakuri



Farhan ne yace nikam nagaji, Bari inje daki nakwanta na huta, ya kalli Bilkisu yace ainaje dakin naku
bangankiba, sai Yaya ne kawai yake bacci, jinakema kina toilet ashe kina nan



Wallahi gajiya nayi nataho gida, inji Billy



Mamy tace to yanzu waye zai zauna da Imran din Bilkisu?



Dasauri Hajiya tace nice zanje mana Hajiya fati, Tunda ita bazata Iya zamanba aini saina dauki mayafina
inje in zauna dashi



Murmushi mamy tayi data Gane gatse ne Hajiya takama Bilkisu



Tana zama akujera Itama, tace a a Hajiya, zata Koma itama, duban Billy tayi tace Bilkisu yata tashi ki
shirya, kikoma kinji, karya tashi Kuma yanemi wani Abu gashi bakya nan, Bari insa Mai aiki tayi muku
abinci, saiki tafi muku dashi



Kamar zatai kuka tace to mamy, tareda tashi tayi dakin Iman, domin shiryawa



*** *** ***
Kai tsaye Abuja ya wuce, Saida yagama abinda zaiyi sannan yatafi India



Baisha wahala ba wajan Zuwa asbitin, Kai tsaye wajan jabir yanufa, Saida suka sake gaisawa sannan suka
nufi Dakinda take ciki



Tana kwance tana bacci, qarin ruwane ajikinta, Zuwa yanzu babu oxygen Din ancire mata shi, saide tana
numfashi ne Ahankali, fuskarta fayau



Dakin babba ne, da kujera 2seater sai qaramin fridge, da gadon datake kwance, komai na dakin kalar
light blue ne Har kujerar, sai wata qaramar kofa agefe da alama toilet ne



Har gaban gadon sukaje, ya sunkuya ya zuba mata ido, Kamar wanda yakeson gano wani Abu

Sannan yadago ya dubi jabir yace, Zuwa yaushe ne zata farka ne?



Aita farka dazu, Bayan ankaita tayi wanka ne, akayi mata allurar bacci, sai nanda awa shida zata tashi,
insha Allah



OK to shikkenan babu damuwa, Nima yakama ta muje Naga likita, ayimin abinda yadace inyaso saina
dawo latter



OK ba damuwa muje

Fita sukai Daga dakin nikuma na iyo Nigeria



*** *** ***

Tsaf ta shirya laffaya, ta futo falon zata tafi asbiti
Hajiya ta kalleta tace yanzu keda zakiyi Zaman jinya, yaushe Zaki saka Kaya masu nauyi, maza koma daki
ki sake shiryawa

Kamar zata fashe haka Takoma dakin, tana cire kayan tana mita, Tunda nadawo Daga katsina ban
zaunaba, Daga wannan matsalar sai wannan, haka tasaka doguwar Riga ta atamfa, Daga Sama dinkin
yakama kirjinta, Daga qasa Kuma abude take



Dan qaramin mayafi tadauka tayafa, tana Kallan kanta amadubi tace Tunda nasaka babban Kaya ance
incire, yanzu Kuma nasaka qarami nasan Shima Hajiya dawo Dani zatayi tace Ina tafe tsirara Kamar Yaya
Iman



Hakade ta futo falon, tadauki kwandon abincin tace Hajiya natafi



ga mamakinta saitaga Hajiya tayi mata Shiru, batayi mata fada Akan shigar datayi ba, Tunda tasan
bahaka tasaba fitaba, Dade Iman ce



Saima Cewa datayi, Wai miye kike ta Bata raine? Ko asbitin ne bakya son Zuwa?

Kamar tasan Bilkisu Dama jiran qiris take, nan take tace to hajiya shi yayan ne saiyayi banza ya qyaleni,
dazu da safe abincin Dana bashi ma daqyar yaci, sai hararata yake, ni wallahi Hajiya dande kince saina
koma ne



Murmushi Hajiya tayi tace, haba Bilkisu, keda dan'uwanki? Lallabashi zakiyi, idan yaqi ci saiki lallasheshi
kibashi, idan Kuma kin gwada lallashin yaqi saiki zare masa ido ki Bata fuska, idan bazai ciba, saiki
qyaleshi



Cikin Zaro ido tace Hajiya yayan zan zarewa ido? Um Hajiya sai anjima

Tadauki kwandon tayi gaba, cikin ranta tana mita ita kadai

taga alama Hajiya sotake taja mata fada awajan Yaya Imran, inba hakaba harda Cewa in lallabashi, in
rarrasheshi, saikace wani jariri
Hajiya kuwa Daria ce takamata, da niyya tabarta tafita da wannan kayan, saboda Hakan yana daya Daga
cikin abinda Imran yakeso, wato daukar wanka, afili tace kuje de can ku qarata



*** *** ***



Ga magungunan Naka, Amma inaga da kazo munje gida gobe da safe idan Allah yakaimu saimu dawo
kafin lokacin ma tafarka



Cikin Murmushi yace no doctor jabir karka damu, zanjira harta tashin insha Allah, zan taho gidan Daga
baya

ok to saimun yi waya, inji jabir tareda fita Daga dakin



Ajiyar zuciya yasauke Bayan fitar jabir, ya ajiye magungunan sa, sannan yanufi fridge din dakin yabude,
acike yaganshi da kayan marmari da ruwa sai lemuka, yasan wannan duka aikin doctor jabir ne

Lemon kwali yadauko guda daya, yadau cup yakoma Kan kujerar dakin yazauna, idonsa akanta yafara
ballar maganin sa yanasha



Saida yagama Sha sannan yatashi yakoma Kan gadon datake yazauna Agefen gadon, idanu yazuba mata
yana jiran tafarka

Haka yayita zama Shiru shi kadai, da lokacin sallah yayi yatashi yayi sallah yakoma, yana zaune harya fara
gyangyadi, Amma Bata farka ba, kansa yadan Dora danyaji dadin gyangyadin, nan kuwa bacci ya
daukeshi



Can cikin dare tafarka, Ahankali take Bude idonta harta Bude gaba daya, kansa dayake dab danata
hakanne yasa numfashinsu haduwa, da tsananin mamaki take kallansa, yaushe Yazo? Kode gizo yake
mata? Anya kuwa soyaiyar Aliyu Batasa yafara yi mata gizo ba?



Domin ta tabbatar da ba mafarki takeba yasa Ahankali takai hannunta Kan Lallausar sumar kansa tashafa
Jin Ana shafa kansa ne yasa yabude lumsassun idonsa dake cike da bacci, yazuba mata ido



Itanma kallansa take domin ganin Cewa tabbas shine ba mafarki takeba



(um jiyakam kunjini Shiru sakamakon wani babban uzuri daya riqeni, 😱nasan mutane dayawa sun jirani,
Amma inaso kuyi hakuri please πŸ™πŸ»πŸ™πŸ»)



Mrs Usman Ce WAZAN
✍🏻 ZABA?πŸ’–



Writing by Amnah El Yaqoub



Bissmillahir-rahmanirraheem



22



Hannunta dake kansa yadauke, ya damqe hannun nata cikin nasa yace "kin tashi?"

Daga masa Kai tayi alamar eh, itade duk mamaki yacikata



Tashi yayi Ahankali yasa hannu yadauketa cak, yanufi toilet da ita



Duk da batada kuzari Saida tayi kokarin sauka Ahankali tace zan Iya tafiya, kasaukeni



Kallanta yayi baice mata komai ba, Saida yakaita cikin toilet din, yabata brush da toothpaste, sannan ya
fita tareda rufe mata kofar



Yana fita ta jingina da bangon toilet din, sai Murmushi take ita kadai
Shikuwa fridge din yanufa yahada mata fruit yakai mata gaban gadon, yahada mata magungunan ta



Bude kofar toilet din tayi Dan kadan tace Yaya hijabina



Dube dube yafara shine baiga wani hijab ba, sai wani mayafi, danhaka yadauki mayafin yameqa mata

Kallan mayafin tayi, sai yau tayi Dana sanin rashin yawo da hijab



Towel din jikin ta ta kalla Dan qarami, da kadan ya wuce Rabin cinyarta, haka tayafa mayafin Har kanta,
ta futo Daga toilet din tana Jan towel din qasa



Yana ganin futowarta yakalleta, cak ya qame a zaune yana Kallan ta

Ganin taqi miqewa ne yasa yagane Cewa atakure take

Shiyasa ya miqe yace Bari nafadawa doctor kin tashi, kiyi sauri ki shirya, yafice daka dakin

Yana fita tasaki Ajiyar zuciya, dasauri kuwa ta zira kayanta, tatada kabbarar sallah



*** *** ***

Ahankali ta turo kofar Dakin tashiga tareda sallama, yana kwance idonsa biyu, Amma yadafe kansa da
hannunsa guda daya,dasauri ta qarasa wajansa tazauna dab dashi, tace sannu Yaya, yajikin Naka?

Bece mata komai ba sai rintse idonsa dayake danyi kadan kadan



Hannunta tasa tajanye hannunsa Daga Kan goshin, sannan tadora hannunta awajan

Dasauri ta dauke hannunta Jin zafi sosai



Tashi tayi tace Bari nakira doctor Yaya, Ahankali yace Yazo yanzu yafita, yace zai dawo nanda 30minutes
Dawowa tayi tazauna, tace to Yaya tashi Kaci abinci kafin yadawo



Ahankali yatashi zaune, still hannunsa na dafe da goshinsa



Zuba masa abincin tayi, tadawo kusa dashi tazauna

Dakanta take bashi abincin, duk ta damu, tadebo a spoon takai bakinsa

Babu musu yafara ci, goshinsa tasake tabawa tace sannu Yaya



Zuba mata ido yayi yana Kallan ta, ganin da gaske take komai duk ta damu



Lumshe idanunsa yayi alamar amsaba



Abincin taci gaba da bashi, wayarta tadau qara, Kallan wayar tayi Amma Bata daukaba, Saida ta tabbatar
ya qoshi sannan ta qyaleshi



Dan qaramin handkerchief ta dauko a handbag dinta, taje toilet din dakin tajiqashi da ruwan sanyi,
sannan tadawo tace kwanta Yaya, babu musu kuwa ya kwanta, shi Har yanzu mamakinta yake, Kamar ba
Bilkisun daya saniba



Yana kwanciya ta linka handkerchief din gida biyu, ta Dora masa Akan goshinsa, sannan ta dubeshi tace
Hakan zai taimakama wajan rage Jin zafin Yaya



Ahankali yace thanks



Kujerar dake gefen gadon taja ta zauna, sannan tadau wayarta takira number data kirata dazu



Hello ya Haroon kakirani Ina busy shiyasa ban samu dama nayi picking ba
Shima Daga nasa bangaren yace wanne irin aiki ne wannan dazai Hana kidauki wayata?



Yayanmu ne baida lafiya, aika ganeshima Yaya Imran, shine nake kula dashi



Cikin bacin rai da nuna kishin sa afili yace, OK kina kula dashi shiyasa ni kika qyaleni, to menene amfanin
Iman, aida saita zauna dashi



To yanzu ya Haroon idan Yaya Iman din tana nan harna zauna anan? Batada lafiya Itama, an fitar da ita
India ma



Cikin nuna ko'in kula yace ok, sai anjima, yakashe wayarsa



Wayar Tata tabi da kallo, ikon Allah, wato shi kawai maslahar kansa yasani, nafada masa yar'uwata
batada lafiya Amma Ko Allah yasawaqe baiyi mataba



Tsaki tasaki ita kadai, Imran dake kwance Baisan Sanda yayi Murmushi ba, Ahankali yace keda saurayinki
Bilkisu, menene abin fishi



Cikin shagwabar da batama San tayiba tace haba Yaya kanajin fa abinda Yamin, shine ya kashe min waya



Murmushi yayi baice mata komai ba, Baisan dalili ba kawai de yaji aransa Yanda tayi shagwabar ta
birgeshi

Harma baiso ta daina ba, domin tasakeyi yace bani labari



Kallansa tayi qasa qasa, tace labari Yaya
Shima yace eh



To wanne irin labari zan baka?



Na samarinki



Yaya ni banda samari sai Haroon, saide nabaka labarinsa



No banaso



To ai Kai kace na samari na,



Tona fasa kibani wani labarin daban



Toshikkenan Yaya Bari nabaka labarin soyaiya



Babu Bata lokaci Billy tafara bashi labarai na soyaiya, tun yanaji yana gyada Kai harya dawo yana Daria,
kawai aikin kallanta yake, Dan qaramin bakinta dake motsawa shiya zubawa ido yana kalla, yana ta
mamaki aransa dama Bilkisu tana da surutu haka? Meyasa da baisaniba?

Ita kuwa batasan ma yanayi ba, Zuciyar ta daya, kawai labari take bashi, Bata tunanin komai



*** *** ***

Yanzu saboda wannan yar allurar kike kuka?



Dazai Gane dayadan matsa Daga kusa da ita, kusancin nasu yayi kusa da yawa, gashi yanayi mata
magana qasa qasa Kamar Baisan wani yaji shi
Wajan allurar da doctor yayi Mata yanzu yafita tashafa tace Allah Yaya akwai zafi



Shikkenan naji, zauna nabaki fruit



Babu musu ta zauna, dakansa yake Bata tanasha, tace inasu Hajiya? Ya akai suka yarda kataho?



Waye yafadamiki sun sanma nataho? Basu saniba, nadai fadawa Farhan yasanar dasu Cewa natafi India



Zaro ido tayi tace yanzu fa sunsan wajena kataho



Kafadarsa yadaga yace so what, inasanki ne, bazan Iya ganin kinyimin nisaba, Bayan nasaba kullum saina
ganki a gida

Kuma kawai yanzu saisu dauke minke in zauna?



Dadi takeji acikin ranta Wai yau Aliyu ne yake fada mata wannan maganganun



Ahankali tace nagode da nuna soyaiyar ku agareni



Um kekuma kin Kasa nuna manaba



Da mamaki ta kalleshi tace kamarya? Bangane ba



Emana gashinan Alhaji yace ki zabi daya acikinmu kin Kasa, kawai Daga yar wannan tambayar kin kwanta
jinya



Cikin shagwaba tace Kai Yaya Aliyu Dan Allah, Niba wata jinya
Kawai kifito fili kice Alhaji Aliyu nakeso

Kinga Daga lokacin Alhaji zaisan Cewa idan daddy yayi loosing ummanku ninayi winning Akan yarta



Hararar wasa tayi masa tace dasu umman kake?



Shima cikin Murmushi yace emana ai gaskiya nafada



To nide idan Alhaji yaji kataho wajena Allah babu ruwana



Aikuwa sonake yajima, Dan yasan Cewa mun matsu yayi mana Aure



Fillo tadauka ta rufe idonta dashi



*** *** ***



Meyasa Zaki tafi?



Da mamaki ta kalleshi tace ai dare yayi Yaya, Kuma akwai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login