Showing 114001 words to 117000 words out of 173794 words

Chapter 39 - GURBIN IDO Karyayyiyar Rai By Huguma

dake gefe da gefan fuskarsa

"Don't touch me" ya furta cikin kaushi cikin muryar mutumin dake bacci,sosai ta tsorata,ta janye hannunta da sauri tana fiddo idanu waje,dai dai lokacin da shima ya fara bude idanun nasa da kadan da kadan har ya zubesu fes kan fuskar unaisa.

Kafeta yayi da idanu wani zallar bacin rai yana saukar masa,wannan shine karo na kusan biyar da take masa hakan,kamar bazai motsa ba sai daga bisani ya miqe daga kwanciyar a hankali,cikin zuciyarsa yana karanto addu'a,saman gadon ya zauna sosai bayan ya zubo da qafafunsa qasan gadon

"Me kikemin a daki?" Ya tambayeta kai tsaye,sosai tayi qoqarin sanyawa kanta dakiya,duk da yadda jiki da kuma muryarta suke dan shaking kadan

"Zuwa nayi na duba dawowarka,ga abinci can a gama" shuru yayi na second uku

"How many times nake gaya miki ba kowanne jagwalgwalon masu aiki da sunan abinci nake ci ba?,take note please,kada ki sake shigomin daki ba tare da izini na ba" ranta ya sosu kamar kullum,ta kuma kasa hadiyewa

"Amma dai kasan ni matarka ce ko?,sannan kuma ko yaya ne ina da hakki a kanka" qas yayi da kansa,murmushi nason kubce masa amma kuma ya hana kansa faruwar hakan,don baya son raini,daga bisani ya kuma daga kan nasa ya dubeta kai tsaye

"I know,i already know, that's why na baki zabi ai tuntuni,a mutunce zan baki takardarki ki qara wuta,i assure you zaki samu dai dai dake" wani qullutun baqinciki ne ya tokare mata wuya,wanda ta kasa riqeshi,sai ta saki kuka kawai ta juya gudu gudu sauri sauri tabar dakin,yayin da shi kuma ya bi bayanta da wani kallo da tsarabar tsaki,kana ya miqe a hankali yana sanya hannunsa cikin sumarsa yana maidata baya saboda yadda ta cakude,bawai bashi da feelings ba,ko kuma feelings dinsa ya mutu ba,aah.....yana nan a yadda yake,lafiyayyen namiji,wanda wannan dalilin ya sanya ko a baya ya riga jabir aure,amma dai for now bayajin komai akan kowacce diya mace,musamman unaisar da sai a yanzu yake gano fuskarta ranar da qaddara ta fara hadasu da ita a wani club sanda yake aviation school,zuwansa club na farko kenan a rayuwarsa,shima baisan can zasuje ba,daga wajen cin abinci suke shida abokinsa kuma abokin karatunsa muslim,yace yazo ya rakashi wajen wani abokinsa,as'ad zubair,dan gida wani babbban qusan gwamnati a nijeria,acan ya gansu tare da ita,wanda shikam kallo daya ya yiwa fuskarta ya dauke kai,abinda yasa ya kasa shaida fuskarta kenan da wurwuri sai daga baya,duk da ba shigar banza ko wani abu yaga tana sha ba amma abun ya tsaye masa a rai,don yana da tabbacin cikakkiyar mace mai cikakkiyar kunya ilimin addini da tarbiyya ba zaa sameta a wannan wajen ba.

Ruwa mai dumi sosai ya sakarwa kansa,bayan ya gama yayi brush ya feshe bakinsa da turaren mouth mint mai qamshin strawberry,ya dauki babban towel yana tsane jikinsa daya jiqe da lema sosai saboda yawaj gargasar da yake da ita saman lafiyayyar fatarsa.

Cikin wasu lafiyayyun kaftan ya shirya kansa farare qal,duk motsin da zaiyi jikinsa na fidda wani irin qamshi mai taushi,ba kasafai ya fiya sanya hula ba,don haka ya riqeta a hannu bayan ya laluba key din motar da yake son fita da ita,ya kalli agogo yana duba lokaci,sai ya sanya wayoyinsa a aljihu bayan yayi kiran daya daga cikin drivers dinsa yaji yana kusa don qyuyar tuqi yakeji,har yanzu kasalar bata sakeshi ba,yayo waje cikin takunsan nan dake dauke da wani salo na dabam da zaka tsammaci tsabar jin kai ne ko izza.

Sai da suka tsaya sukayi sallar magariba da isha'i a hanya sannan suka qarasa a asibitin,a sannan har yayi waya an musu take away na abinci awa daya kafin ya isa,qarfe takwas da wasu motsi,driver yayi parking motar tasu,ya balle murfin motar ya ficw cikin nutsuwa,iskar asibitin tana kadashi,tana kuma tuna masa wasu abubuwa sa suka shude cikin rayuwarsa.

Babu yawan jama'a sosai a asibitin,hakan ya bashi damar isa qofar dakin kai tsaye,tun bai shiga ba ya tabbatar akwai mutane a ciki,sai ya tura qofan a nutse da sallama.

su hudu ne 'yammatan gidan nasu,sai baba tabawa ta biyar dinsu,sallamarsa ta sanya su duka yin dif,yayin da wuta ta daukewa maimunatu dake zaune ta jingine bayanta da filo tana sauraren hirar tasu,sanye take da doguwar rigar atamfa wadda ta zauna mata sosai a madaidaicin jikinta,ta kuma fidda mata shape dinta saboda yadda breast curve din aka yishi cif da cif,ya kuma zauna mata sosai,dogon hannu aka yiwa dinkin saidai an yayyanka shi ya koma kamar spaghetti sleeve,tayi tayi sanda ta sanya kayan a bata baby hijab dinta data saba sakawa amma fa'iza tace a'ah,su da su waye a dakin da sai ta sanya hijab,baba tabawa ma tace

"Ki barshi kawai maimunatu,kada kije ya dameki ma ya gotar miki da canola din" kasancewar sun cire mata ruwan da ake qara matan don ta huta.

A ladabce suka gaidashi bayan baba tabawa ta miqe ta bashi kujerar da take kai ta matsar da ita gaban gadon maimunatu,maimunatun da tunda ya shigo tayi qas da kanta,ko sau daya bata dago ba,idanunta nakan Canola din hannunta.

Takalmanta baba tabawa ta jawo tana sanyawa,dai dai sanda anni ke fitowa daga bandaki

"Yaushe ka shigo?" Da hannu ya nuna mata yanzu yanzu

"Zamu wuce,dama shirin tafiya muke"

"Akwai driver?" Ya tambaya a taqaice da muryarsan nan me cike da ginshira

"A'ah a'ah,salma ta tuqomu,gani nayi tafiyar babu yawa" cikin salma ya duri ruwa,ita anni me yasa ba'a sirri da ita?,kawai tace masa eh driver dinne,na meye saita bashi labari?.

Qarasa dibibicewa tayi sanda ya watsa mata wani kallo na gargadin kinyi na farko kinyi na qarshe,baa baau mota su tuqa a gidan,saidai idan kinyi aure mijinki ya baki,suk inda zasu driver ke kaisu

Da daya da daya suka fice a dakin suna yima maimunatu sallama tare da cewa zai gobe,murya can qasa take amsa musu,gabanta na wani irin faduwa,tana jin kamar tabi bayansu sanda suka fita,dakin ya rage daga ita saishi daya sanya waya a gaba yana dannawa

[11/7, 4:14 PM] +234 813 615 2119: 43

Sai da suka tsaya masallaci sukayi sallar azahar sannan hisham ya sake daukansu wuce asibitin,gab da zasu qarasa ya soma slow da motan,jaafar dake duba wani abu a tab dinsa ya daga kai ya dubeshi

"Uhmmm,ya dai?"

"Naga masu fruit ne,akwai paw paw a ciki,zan siya ma maimunatu" sai ya maida kansa ga abinda yakeyi baice dashi komai ba,har ya buda motar ya fita yaje ya siyo,ya dawo ya tashi motar suka wuce.

Dakin babu kowa,don duka sun yoye sun tafi,daga ita sai amnan sai baba talatu data shiga bandaki zata dauro alwala,tana zaune a saman gadon amna ta zame mata dankwalinta ala dole wai sai ta yi mata kitso,tana ta jagwalgwala mata sassalkan gashinta ta kasa kitsawa saboda sulbi da santsinsa,jikinta akwai sauran zazzabi,an yima likitan bayani yace zai shigo ya dubata,tana biyewa amna dinne kawai don kada yarinyar taji babu dadi.

Batayi zato ba bare tsammani sassanyar muryarsa ta furta sautin sallama hadi da turo qofar dakin gaba daya,tashin farko kuma idanunsa suka sauka a kanta lokacin data rude ta kuma tsorata tana neman dankwalinta,wanda bata sani ba amna ta jefa mata shi qasan gadon,shi yasa ta kasa ganinsa,idanunsa ya dauke ya waiwaya baya inda hisham ke biye dashi

"Wait for a while"

"Okay" hisham ya amsa masa ya kuma ja baya ya tsaya ba tare da yasan dalilin ja'afar na fadin hakan ba.

Koda ya shigo din gaba daya ya maida hankalinsa ga amna wadda ta diro a gadon fa kuma rugo da gudu zuwa gareshi tana kiran sunanshi,haka kawai yaji baya son ganinta haka,ya budewa yarinyar hannayensa bayan ya durqusa yana jiran qarasowarta,zuciyarsa kuma na tuna masa da lokuta irin haka a baya,lokuta mafiya farinciki a rayuwarsa,lokutan da ita da twin sister dinta amra ke rige rigen isowa gareshi,mamansi shahida na tsaye tana kallonsu tana kuma murmushi,sai gashi a yau yarinyar ita daya ta rage masa a cikin guraben farinciki guda uku da yake dasu,tana qarsowa kuwa yayi sama da itama ya cillata kan ya rungumeta cikin jikinsa.

Kafij su gama ganin murnar ganin juna ta lalubo dankwalin da qyar ta yane kanta gaba daya zuwa saman qirjinta,duk da hankalinsa na kan amna amma yana ankare da ita,baisan me yasa take tsoronsa haka take kuma rudewa duk sanda yazo wajen ba,tun ranar daya tsorata tan randa suka baro gembu zuwa gombe,sauke amna yayi a hankali

"Kice da uncle ya shigo yana waje" da dan gudunta ta fice,sai a sannan ya sake maida dubansa kanta,ta nutsu guri guda,wanzuwarsa a wajen tana sata jin kamar wani zazzabin zai sake qaruwar mata,kwata kwata batason ganinsa a waje idan tana nan

"Ina wuni?" Ta fada da muryar nan tata dake da tsananin zaqi da sanyi,shi kansa ya yadda da hakan,idan tayi magana wani sauti take bayarwa na musamman

"Ya jikin?" Ya tambayeta ba tare da ya amsa gaisuwarta ba,yana bin ledar qarin ruwa da aka cire mata da kallo

"Da sauqi" ta bashi amsa dai dai da fitowar baaba tabawa daga bandaki.

"Barka da zuwa,yaushe ka shigo?"

"Yanzu" ya amsata yana waiwaya ga hisham dake shigowa dakin da sallama,kanta ta daga tana amsa sallamar,yadan kalleta ta gefan idanu,akwai dan qaramin murmushi saman lebanta tana dubansu shi da amna,gaisawa shima sukayi da baaba tabawa,ta tayar da sallah,sannan ya matsa inda maimunatu take

"Yanzun don kada a bamu tsarabar boarding shine aka kwanta ciwo?" Shima tana jin nauyinsa sosai,amma ko kwatar na miskilin yayansa me fuskar shanu bai kai ba,akwai dan sabo haka a tsakaninsu,don haka murya can qasa ta yadda take zaton ja'afar bazaiji ba tace

"Kaidai tunda sai yau kk zuwa dubiyan ai shikenan"

"Am sorry.....wallahi ayyuka ne suka yimin yawa kwana biyu,ga teaching hospital da nake zuwa musu sau biyu a sati suma kyauta...."

"Allah ya taimaka" ta fadi duk a darare,ita inda zai fita ya basu waje ma da sai tafijin dadin hakan,ledar gwandar ya tura mata

"Nayi dubiya me kyau,tunda.na kawo miki mutuniyarki ko?" Ya fada yana dubanta yana murmushi,maganar da ta sanya ja'afar karantar fuskarta a fakaice,wanda a zahiri zaka dauka kacokam hankalinsa na ga surutun da amna ke masa,sai yaga fuskarta ta washe sosai,karo na farko da ya taba ganin irin haka tattare da ita

"Na gode sosai,Allah ya saka da alkhairi,ya bada lada" maganar ta tsaya masa a rai,kwatankwacin addu'ar shaheeda kenan duk sanda aka yi mata alkhairi komai qanqantarsa.

Juya gwandar kawai take,tana son sha amma dashi da hisham din duk sun cika mata waje,sanda baba tabawa ta idar da sallar likitan ya shigo,maimunatu ta daga kai a hankali gabanta yana faduwa,ta tuna maganarsa ta jiya,yace indai yazo yau ya samu da sauran zazzabin a jikinta to lallai duk qinta da allura saidai tayi haquri ayi mata ita,a duniya allura itace abu na farko data tsana ta kuma qi jini,daada tafi kowa sanin hakan,don tun kafin rasuwarta akwai sanda bata da lpy,ta takura sai anyi mata takusa shide mata,abinda yasa tun daga ranar bata qara bari anyi mata ba.

"Dr hisham marwan?" Likitan ya fada yana diban hisham,da alama akwai sanayya sosai a tsakaninsu,don shima hisham din yana kallonsa ya kama sunansa,hira suka barke da ita,yana duba file din maimunatu,da treatment din da aka bata daga daren jiya zuwa yau,sai ya daga kai ya dubeta

"Har yanzu da zazzabin?" Kafin ta amsa baba tabawa ta rigata

"Akwai likita,ai har magana aka yo muku dazun"

"Ba damuwa,zai sauka yanzun in sha Allah,qila ma idan akayi wannan allurar basai an sake wata ba" fadin haka kawai sai idanunta ya fara tara hawaye,cikin mamaki a kuma sace ja'afar ke kallonta,bawai tana nufin kiran za'a mata allura ke shirin sanyata kuka ba?,ya hangi zallar tsoro baro baro a idanunta,ta kuma kasa sukuni sanda taga yana hada ruwan allurar waje daya.

Kida wayarsa ta farayi,sassanyar busa me ratsa zuciya,ya cirota ya duba me kiran,sai ya soma takawa a hankali yana ficewa a dakin yana amsa wayar.

Daya daga cikin amintattun ma'aikatansa ne,suke gaya masa motocin da ya siya sun iso,suna lagos,za'a biya kudin clearance da sauransu

"Ayi duk abinda ya dace"
"Okay sir" ya amsa masa a ladabce,ya kashe wayar yana juyowa,dai dai sanda baba tabawa ta iso riqe da hannun amna

"Manya inaji fa sai kaje maimunatu zata tsaya,taqi bari ayi mata allurar nan sam" a mamakance yake duban baba tabawa,wanne irin abune haka kamar qaramar yarinya?.

"Daddy tsoro takeji wallahi,ka cewa dr ya rabu da ita" kallon amnan yayi,yadda tayi maganar har zuciyarta,hakanan itama fuskarta kamar zata saki kuka,baice mata komai ba,yadai saka hannunsa saman kanta ya shafa,sannan ya wuce zuwa ciki.

Ba wanda ya lura da tsaiwarsa a bakin qofar,da gaske ne tsoro takeji,don gashi nan a bayyane baro baro saman fuskarta

"Tsaya dr" ya fadi yana takowa zuwa cikin dakin,dukkansu suka waiwayo suna dubansa,sai hisham ya sulale ya fice,shigowarsa kadai ta sake sanyata jin kamar alqiyamarta ce ta tsaya,yaci gaba da takowa fuskarshin nan sam babu annuri,hannayensa zube a aljihun wandonsa.

Dab da ita ya tsaya,har tana jin yadda numfashi ke zarya a qirjinsa,ya kafeta da idanuwansa wanda har cikin jininta take jinsu,abinda ya sake sakar mata da jiki kenan,qasa qasa cikin murya me kama da rada yace

"Kar naga kin motsa.....if not......" Bai qarasa yadan ja qwafa

"Matso kayi mata" ya fada da heavy voice dinsa dake nuni da seriousness dinsa,sannan ya waiwaya ga likitan,ya masa magana da ido kan ya taho.

Kallon likitan take sanda taga da gaske matsowa yake inda take,bata manta yadda taji kamar zata mutu ba sanda aka sanya mata canular,sannan yanzun yace ta ciki zai mata allura?,ai batasan sanda ta kalleshi da shanyayyun idanunta da suka bude sosai ba,suka kuma cika taf da hawaye ba

"Don Allah......dan Allah" tayi maganar tana girgiza kai muryarta tana rawa,idanu ja'afar ya zuba mata,mamakinta na sake cikashi

"Tsaya" yace da likitan sanda yaga ta dunqule waje daya,hawaye na gangaro mata lokacin da yazo gab da ita ya daga allurar,wani abu me kama da tausayinta ya tsarga masa,halitta ce qin allura,ta tuna masa da marigayiya amransa,haka ake shan daga da ita idan zaa mata allurar.

A hankali ya sanya hannunsa guda daya ya kamo tafin hannunta ya saka cikin nashi,tsigar jikinsa ta zuba gaba daya,tun daga tsakiyar kansa zuwa tafin qafarsa,karon farko da hannunsa ya sake taba wata mace tun bayan rasuwar shaheeda,laushi da dumin da tafin hannun ke dashi ya ratsa kowacce gaba ta jikinsa,a hankali ya soma murza tafin hannun,abinda ya daukewa maimunatu wuta kenan gaba daya,ta kuma wara dukka idanunta dake jiqe da lema akan fuskarsa dKe gab da tata,idanu ya zubawa fuskarta data yi wani kyau saboda lemar data jiqe eyelashes dinta,abinda ya basu damar yin wara wara,har yanzu da cikarsu da kuma tsahonsu

"Relax....babu zafi fa,yanzu zai gama,just a few seconds" yayi maganar da wani irin sound da yasa taji zuciyarta ta sauya bugu,idanunta ta lumshe cike da kwarjinin daya ma idanun nata,tana kuma jin shigar qarfen a hannunta,saidai kuma kamar ya dauke duk wani tsoro fargaba da kuma zafi da take zaton zata ji.

Batasan an gama ba,tadaiji ya danne mata wajen,likitan kuma na tsokanarta

"Randa zaki haihu bansan ya zata kasance ba" murmushi gefan baki ya subucewa ja'afar,shima yayi wannan hasashen tun dazun,sai ya samu kanshi da daga kai yana kallon fuskarta,wadda ta fito clearly very close to him,jajayen lips nata suna motsawa a hankali kamar wadda ke karanto addu'a,har yanzu idanunta a kulle suke,taqi ta budesu,quruciyarta na bayyane saman fuskarta,lips dinta suka ci gaba da daukar hankalinsa,ya samu kansa da ci gaba da kallon fuskartata kallo irin na qurilla,jira yake ta bude idanuwanta yaga yadda zatayi,akwai wani irin haske da kyau da idanunta ke qarawa a duk sanda ta tsorata,abinda ya kula dashi tun a ranar,bakinta yana sake tsukewa,idanunta na dada girma da haske,abinda ke sashi cikin wani dan qaramin nishadi da gajeran tunani.

Hannunsa dukka biyun ya sanya yana yafa mata mayafinta saman kanta sanda ya jiyo muryar hisham da jabir gab da dakin,da alama shigowa za suyi,kafin yace wani abu sun turo qofar sun shigo,hisham a gaba,abir din na dauke da amna,sai fatiman jabir din,sai ya janye baya a hankali,suna hada idanu da jabir din ya sauke masa wani murmushi,tuni ja'afar din ya fahimci abinda yake nufi,tsananin shaquwarsu ya sanya suke saurin karantar juna koda basuyi magana ba,murmushin da ya sanya ja'afar sake dinke fuskarsa tsaf

"Allah ya taimaki boss" jabir din yafada cikin qan qan da kai,kamar yadda yaron gida ke magana da uban gidansa,amma saidai can qasan ran ja'afar yasan bawai yayi bane da gaske,akwai manufa na wannan gaisuwar,duka salon tsokana ne,don haka bai wani nuna masa ba ya bashi hannu sukayi musabaha.

Jin baqin murya ya sanyata soma bude idanunta da suka sauya kala saboda rufesun da tayi gam da kuma kukan data fara a dazun,idanunta akan fatima tanason tuna inda tasan fuskar,muryar jabir data ji ya tuna mata,wannan shine haduwarsu da ita na biyu tunda sukayi aure,tayi qoqarin sakar mata murmushi duk da yadda

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login