Showing 21001 words to 24000 words out of 36965 words
Chapter 8 - FUTUHATUL KHAIR Yarinyar Da Ta Zo Da Alkhairi by Xainab Y Hussain
wa, saida yaji cikinsa na shirin qullewa sannan ya haqura
Duk abin nan, Mama na kallon sa, dariya tai tace Fadeela kin kunyata, gashinan mu bamusha ba, ya shanye
Me nashanye Mama, juice en nan yanada dad'i, banta6a shan juice mai dad'i haka ba
Ya sunansa konakoma can ina siyanshi?
Fadeela dariya tafara jin yana magana seriously, Broth had'awa akayi fa, banganeba!
Wallahi FUTHA tayi shi, har ina bazaka sha ba, gashi har santi kake
Ke bafa wannan jagwalgwalon nake magana ba, wannan da aka zuba cikin jug fah
Wallahi yinsa akayi, fad'a masa tai, dariya ce ta kwacemasa Lallai mama kya kallon, indai haka ne kam, to inasonsa
Kamar ya tambaya yace wace FUTHA, sharewa yai kawai, tunda baisan taba, kuma bayason tambaya
Haka suka ringa hira da gurin aikin sa, har time yai kowa yakama gabansa
FUTHA tana sakkowa yana fita, nuni yai ina yake zata gaidashi, ya tafi Fadeela tace, naleqa ai naga kinata karatu, shiyasa bance kizo ba
In fad'a miki broth dai yashanye lemon, kuma ya tafi da sauran, aimu bamu shaba, murmushi tai
Ahaka suma suka haura d'akin su
@ut@r h@jiy@๐
๐ปโ๐ป
[11/10, 8:26 PM] โช+234 809 308 3613โฌ: [30/10 2:28 am] @ut@r h@jiy@๐
๐ป๐๐ปโ๐ป๐: *FUTUHATUL KHAIR*
*ยฎNWA*
*ยฉZainab Y Hussein*
*Dedicated to FUTHA LUV*
*Page 91-95*
Ko daya shiga d'akin sa brush yai, sannan yasaka boxer da singlet fara qal, system nasa ya janyo yafara bincike akan aikinsa
Stool ya janyo wanda ya d'ora mug na lemon Kan kana aciki yana aiki yana sha haka harya gama
Baisan ya shanyeba saidaya d'aga mug d'in yaji ba komai, dariya yaiwa kansa
Bashi ya tashi ba, sai wajan 1 na dare, bawa idan yagama aikin ba, a'a saidon wayar da Abbansa yasamasa
"hello" Abba lafiya da night haka?
"Eh naji ajikina bakayi bacci ba, so maza kayi bacci, kada aiki yasaka ka shiga bad conditions, bacci yanada nasa important en
So u better get rest plx Omar
" Insha Allah Abba yanzu zanyi
Yauwa Allah yaimaka albarka
Ameen Abba adduar ka garen tanada amfani, a kullum burina naji bakin ka nasamun albarka Allah ya k'ara girma yaja da ran ka
Ameen Omar Allah yabaka mace ta gari, yasaka maka da mafificin arziqi mai d'orewa da albarka
Ameen Ameen Ameen Abba, ayi bacci lafiya
Kit ya katse wayan, yana mai farin ciki
Toilet ya shiga, bai jima ba, ya fito sai gado, addu'a yai ya janyo bargo ya kashe light
A can Fadeela labarin santin lemon da Ya Farouq yai take bawa FUTHA, dariya tai a hakan dai take tayi magana ta kurame, tace Ya Farouq yanada kirki tunda yasha abin da nai
Huum harkin bashi lambar yabo, wallahi ba wani kirki gareshi ba da yawa ba
Kai ta kad'a kawai, a haka sukayi baccin su mai cike da farin ciki
Safiya nayi kafin Fadeela ta tashi hartayi wanka, ta taimaka wa Iya Ladi da aikin gida, kafin 7:30 tayi driver ya jata sai IMAN INTERNATIONAL SCHOOL inda nan aka maidata bayan dawowar ta gidan
Yanzu exam ba kama hannun Yaro ita take sun gama WAEC sauran NECO, lesson suke shiyasa taje
10:00 kowa ya fito cikin shirin sa, danyin break fast, Yam balls ne sai tea mai kayan qamshi da na'ana ga qamshin lemon grass dayake tashi, plantain a soye itama
Kowa zama yai, gaishe da Iyayen sukai, bayan nan Fadeela tayi saving nasu cikin plates
Madara ta d'akko da Milo ta ajiye kowa ya zuba dai dai shi
Harya janyo madara sai yaji bara dai yasha a haka, wow so sweet whts kind of tea na Mama do 4 us
Ba magana haka kowa ya sha batare da madara ba, a tare suka dire cup alhamdulillah wannan tea haka?
Nima abinda zance kenan, wallahi nidai ban tab'a shan shayi mai dad'i haka ba, Mama kina mana shi plx
To ba Mama tayi ba, FUTHA ce, dan ita ta Iya komai, kaci yam balls en nan kaji?
D'aya ya d'auka bakinsa yai, lumus aifa saida Abba ya riqe hannun sa yace kabarshi haka, bazakayimana irinta jiya ba, ka shanye duka lemon, yanzu ma Ka cinye yam balls d'in nan ba
Inasonsa FUTHA ta iya girki, tsayawa yai yace Abba wace FUTHA? new house gal ce ko kuwa
Amma koma mene ta iya girki, ace ina gaidata
Yana gama fada ya miqe bai saurari jin wace FUTHA ba
Kwanan sa goma agarin yanxu ma yana shirin tafiya wajan aiki, bai tab'a had'uwa da FUTHA ba, itama haka
Duk lokacin da zasu had'u sai wani sab'ani ya gifta, gashi girkin ta ya namasa dad'i, ya lura ta iya girki
Baitab'a neman taba, saboda a tunanin sa house gal, ce amma wataran Ji yake kamar yace a kirata yai mata kyauta
Amma baiyi hakan ba, Fadeela bata tab'a lura cewa basu had'u ba
4:00pm dai dai lokacin ne driver'n Farouq ne ke driving dan kaishi airport zai koma aiki ta Titin BYPASS suka biyo anan IMAN take school d'in su FUTHA
FUTUHATUL KHAIR ita alokacin suka fito tareda qawayenta STYLICH da PHARTY BB, tafita take tanata dariya saboda wata magana da sukai akan qawarsu NAFEE ANKER
Fuskanta smooth tana kyalli take washe baki ga school uniform d'in ya karb'eta
Shikuma daidai lokacin yasha kwana da fuskanta yafara arba Hasbunallahu wa ni'imar wakeel, Allah yayi hallita
Jiyai jikinsa ya tsaya cak, kafin ya farga ya nemeta ya rasa, ihu yasaka plx driver back back
Kayi sauri kada ta ba'ace haka yai gudu, yammatan yagani amma kamar ba ita?, hakan ce ta kasance dan babu ita
Zagaye wajan sukai amma ba ita
Haka ya qaraci duba dubensa ya ce a tafi fuskansa cikin yanayi na rashin dad'i
@ut@r h@jiy@๐ฑ๐ปโโ
[11/10, 8:26 PM] โช+234 809 308 3613โฌ: [30/10 8:42 am] @ut@r h@jiy@๐
๐ป๐๐ปโ๐ป๐:
*FUTUHATUL KHAIR*
______*ยฎNWA*_______
*ยฉZainab Y Hussein*
*Dedicated to FUTHA LUV &Anee Maman Ayman Aseef habeebaty ana bihibak bikil Hayatee*
*Page 96-100*
Shi kansa driver'n ya lura oga kamar yana d'an neman wani abu, gashi basu ganshi ba
Haka har suka isa airport ya direshi ya juya shi kuma ba wani jimawa jirgi yazo aka fara Shiga
FUTHA lokacin da suke hira adaidai nan driver ya qaraso d'aukanta shiga tai yai gaba, shine dalilin da yasaka baiganta kusa ba
Ko cikin jirgi dariyar ta yake hanga da siririyar wushiryarta mai ban sha'awa
Bayan kwana 2, yau gidan Aunty Zainab zasuje shiyasa ko Malam na islamiyya suka masa waya kada yazo, FUTHA ita tunda aka ambaci za'a gidan hankalinta ya tashi tarasa sukuni addu'a take yi azuciyarta kawai tasan duk tsanani itace maganin komai
Su Ahad da Waheed haka suka kasance suna zuwa wajan Malam addu'a kullum da saukar Al Qur'an ita ake, sai rubutu da ake yayyafawa cikin gidan
Alhamdulillah sunga sauyi dan sau dayawa damuwar da suke gani afuskan iyayen yanzu babu ita sosai
Kuma dukka pics na FUTHA da aka cire tun kafin Haihuwar su, sun d'akko sun goge sun maidasu kusa dana iyayen
Hajiyansa kanta yau sai gashi Allah yabata ikon cewa Bilkisu ta b'ace kenan babu maganar ta?
A daidai lokacin ne kuma, acan katsina gidan su na farko ana gyara Gidan aka tone wani qulli kamar bazasu bud'e ba masu aikin sai kawai sukai shahada, Innalillah wata laya qatuwa sai gashin akuya baqa kuma ga hayaqi daya fito addu'a suka fara anan wani yai shahada yasaka ashana ya k'one kayan
Sallah FUTHA keyi, bayan ta fito daga wanka ayi shirin tafiya gidan Aunte ZAINAB, fit taji ajikinta kamar fitar allura cikin tsoka taji zafi
Sai kanta daya juya, ahaka ta sulale ta fad'i awajan ba tareda sanin kowa na gidan ba
Fadeela akai sa'a ta shigo saiganin mace tayi yashe a k'asa ba alamar numfashi, kuka tasaka Mama kizo kiga FUTHA ta mutu wayyo Allah
Da gudu itada Abba suka haura upstairs girgizata sukai shiru, haka ya d'auketa sai Asibiti dan jin ko menene
Abdul Abdul BILKISU 'yata ina kaganta wayyo Baby were ar u?, kizo ga Mama
Nan da nan aka taru kowa kuma saiya fara tuna FUTHA, tana ina? basu sani ba shekara wajan 13 innalillah a ina zasu nemeta?
Me yasaka suka manta da sanyin Idaniyr su?, nan fa kowa yashiga tashin hankali baran pics nata da suka gani a parlour ma'aikatan gidan wajan Su 12 kowa jimami yafara
Ana maganar ne Hajiya da Aunty Meenah suka shigo suma ina FUTHA?, kururuwa aka fara ina zasu tarki nemanta?, kuma gurin wa?
Parlour suke tafiya saijin hayaniya sukai, ana dubawa CHUCHU ce ta shigo a hargitse, tana shikenan Bilkisu kin cuceni kin kassaramun rayuwa, wayace a tone wajan, boka yace bazata dawo ba, ta tafi kenan
Kutmar yau zanga shegen daya tone layar danasaka ita kuma tayi addu'a asirin jikinta ya karye
Zainab kin zama muguwa duk abinda nake saida kika tona, kai Mama kin cuceni, sumbatu kala kala
Kowa kuma ya fuskanci itace Ummul aba'isin saka FUTHA cikin bala'i tayi sanadiyyar rabata da mahaifar ta
Abdul ne kuka ya kwacemasa yace CHUCHU kin cuceni Allah ya isa tsakanina da ke, burinki ya cika ada, amma ko adan baiyi tasiri yanda kike so ba
Mari yafara bata yace ina takaimasa 'ya maqurar dataji yasa tace kayi haquri nayi dana sani, tana Niger nan nasaka aka kaita
Numeiy aka ajiye ta, aaaaร tana qoqarin magana amma takasa
Asirin ya koma kanta, tazama kurma sai kuka take dama ta yamushe tazama wata tsohuwa
Abba kuka Zainab dasu Hajiya kuka ina zasu fara nema?, Abban FUTHA shine yace ba jira aka hanya atafi Niger
Basuyi gaddama ba, Motoci aka d'iba aka tafi
Likitoci ne kan FUTHA suna qoqarin daidaita numfashinta wanda ya d'auke Idan kuma ya dawo saiyafara sama hakan yasaka su b'ata lokaci akan ta
Fadeela ita hawaye takeyi, tace Mama lafiya nabarta tana Sallah to mene ya sameta? ba amsa
Alhamdulillah FUTHA ta farka da salati a bakinta, kama bakinta tai magana tafara a hankali nan taga maganar na fita, kabbara tai da qarfin gaske
Lallai dama tanada rabon qara magana Allah Hakeem
Mama ce tashigo, FUTHA kin tashi sannu, Yauwa Mama
Eye! FUTHA kekikayi magana!, nice Mama kabbara tafara da godiya ga Allah mai iyawa, ahaka Fadeela tazo ta same su
Tashi FUTHA tai ta rungume Fadeela tace Fadeela dama zan k'ara magana Fadeela ikon Allah ya sauka a kaina ina sallah najini wani iri kafin na farga Jikina yai weak bansan komai ba, sai yanzu dana ganni maybe nafad'i ne
Rungume juna sukai tanaimata murna, baki rahma ne, jin muryanta siririya mai dad'i saikace ana busa sarewa
Amma daga ji FUTHA ba real Hausa bace dan muryanta hausan bata fita sosai, koba komai jikin ta ya nuna itad'in wani yare ce
Allah cikin Ikonsa ya kaisu Niger lafiya, da pics nata suka fara bawa mutane ko sunsan wannan yarinyar tana qarama 13 years ago, babu wanda ya gane ta ko ya santa, harsun juya sai su kaga wani, nuna masa sukai
Yana gani yace kai ai yarinyar data cinyemun abinci ne a wannan garin
Nan yabasu labari, murna suka fara jin cewa yasan gidan mutumin daya d'auke ta dan shekara 4 ma sun had'u
Haka suka tafi garin Abalak, gidan yana nan, sai canje canje da aka samu
Tambaya sukai wani yace baisan taba, amma ga Gidan Alhaji Raheem suje
Sallama akayi dashi, baijima ba ya fito, gaisawa sukai sannan suka fara fadamasa abinda ke tafe da su
Allahu Akhbar Ikon Allah Allah mai axirtawa ashe yarinyar nan yar babban gida ce, har sun fara murna sai gani sukai yafara share hawaye
Nan ya zayyanemusu zaman datayi, kama daga zuwanta har ranar da suka tafi
Hajiya ce tace kenan sun tashi daga nan, Sokoto suka tafi, muma daga can muke
Ayya ai aranar 16-7-2013 sukabar garin nan aranar kuma Allah yai ikon sa akan hanyarsu mota tayi accident babu wanda ya shura acikin su
Gara kabeer an ganshi, ita gaba d'aya FUTHA qonewa tai ko gawarta ba'a samu ba
Tokarta da babban d'anyatsanta sune aka gani, akayiwa sallah aka bine
Mekkkkkk......kafin kace me ta tafi luuuuuuu mamanta ta fad'i
@ut@r h@jiy@๐ฑ๐ปโโ๐
๐ป
[11/10, 8:26 PM] โช+234 809 308 3613โฌ: [31/10 3:48 pm] @ut@r h@jiy@๐
๐ป๐๐ปโ๐ป๐:
*FUTUHATUL KHAIR*
*ยฎNWA*
*ยฉZainab Y Hussein*
*Dedicated to FUTHA LUV*
~*page 101-105*~
Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, wannan wace irin rayuwa ce?
Daga wannan sai wannan, ruwa aka d'ebo aka zuba mata ajiyar zuciya ta sauke hawaye mai zafi shiya ciga ba da zuba a idaniyar ta
Yanzu kenan sunga samu sunga tashi, yarinyar ta ta mutu, batada rabon ganin ta
Kuka itama kanta Hajiya tayi, saboda ayanzu taji tana qara qaunar jikar ta
Basu zauna ba haka suka kamo hanya zuwa sokoto tunda basu samu abinda suka zo nema ba
A motor sai rarrashinta suke akan ta d'auki qaddara, Hajiya wallahi inaji ajikina BILKISU tana da rai, amma nabarwa Allah komai shi yafi ni sanin abinda ya b'oye akan ta
Yauwa haka suke tafiya ransu ba dad'i, Abba kansa daure wa yake, dan shi yafi qaunar Bilkisu akan sauran yaransa tun kafin ma samu yaran
A can murna dai FUTHA baki ya bud'e, takasa sarrafa murnarta sai dariya take, a haka suka tarkata sai gida
Hajiya Zainab taji d'aci da ciwo na mutuwar 'yar ta, haka ta kasance sukuku har bayan komawar su gida
A gidan Mama sunkasa zama daga suyi ta mata magana dan suji muryanta saisiyita waqoqi, Fadeela ita ganin abin take kamar cikin mafarki
Mama da kanta tarunga bugawa 'yan uwanta waya suna tayata murna, Sahaf itama saiga wayarta sun jima suna magana
Waya Fadeela ta d'auka tace Broth FUTHA bakin ta ya bud'e tana magana I'm really happy
Huum sisto wace FUTHA kindameni da ita?, komai na abinci ace itane tayi wace ita?
Yaya tsintar ta akayi fa, kuma tanada kirki gata kyakyawa kamar Balarabiya , maganarta kamar sarewa dan dad'i
Anya kuwa duk kyanta Bata kai 'yar makaranta ba, komai ita ta had'a, duk da kallo d'aya namata
Nan yabata labarin yarinyar, ayya broth zaka ganta insha Allah, ashe broth he fll n lv, lallai to Allah yasa aganta ko mayi biki agidan mu
Haka suka fara hira, ya manta yace abashi FUTHA su gaisa, duk da baisan taba
Tafiya dai tasha ruwa dan sun manta da wata Hajiya Zainab da gidanta da zasu, sai wajan 8 sannan FUTHA tace Mama anmanta da gidan qawarki
Wallahi kuwa aje wataran, Yau ai ranace mai tarihi da farin ciki a wajan mu
Amma FUTHA zaki Iya sanin sunan garinku da Abban ki?
Kai ta d'aga (kunsan dama harda mantau aka saka mata)(amma koda babu Mantau a shekarunta bazata iya fadar wani information Maikyau ba)
Mama nasan dai Baby Maman mu ke cewa, then a Katsina muke amma daga nan bansan komai akai ba
Mama na a Libiya take, muna zuwa, da Abuja wajan Aunty na
Yauwa to a katsina wacce unguwa Abban ki kuma ya sunan sa?Mama ke tambayar ta
Abba kawai ake cewa, haka dai sukaita tambayar ta ita kanta taso ta tuno wani abu amma ta kasa
Haka zamanta yaci gaba, HAJIYA Zainab taiwa Mama waya akan batada lafiya sun tafi garin su
Sosai ta jimantamata akan Allah yabata lafiya, bata fad'a mata cewar ga abinda yasameta ba
Saboda batason tunowa, yawan maganar shine yasamata ciwo, gashi jininta har yakai 200 abinda ba'aso kuma
Ya Farouq acan bashida tunani saina 'yar makaranta, har ya dawo yana tuna ta, wajan kwana 2 yana zuwa qofan school en amma Allah baisa ya ganta ba
Yau yana CBN qrts gidan su Leemcy wanta abokin sane, kamar ance d'aga kanka itace cikin motor suda Fadeela, motar bata Gidan su bace, ita yagani kad'ai ba Fadeela da gudu ya tashi,amma ina kan yaje sun qule
Abin tausayi ayanzu duk wanda yasanshi yasan yanada damuwa ko Mama tayi tambayar shiru
Yau wajan shopping yaje itama haka, lokacin ita tare suke da class mate nata, tunda sauran kwana 2 candy nasu shine aka zo siyayyan gift wanda zasu bawa teachers nasu
A wajan cashier suka had'u, matsawa yai kusa da ita, jikinsa har rawa yake ganinta da wata baqar abaya anyi rolling ga kanta yai tum, ga giranta baqa data qawatamata fuska
Yana qarasa wa har yace yammata........ sai qirr yaji Waya, kamar bazai d'aga ba, saboda yaga har anfara musu lissafi suna biyan bills
OMG ogansaneke kira da sauri ya d'aga dan yayi yayi yagama wayan ya juya
Saidaya qare sannan ya juya wayam, innalillah, dubawa yafara harda fita waje amma shiru ba ita ba labarinta
Hankalinsa ya tashi, sosai yafara tunanin kodai aljana take masa haka?, bashida answer
Mama ce Yau dai tasha alwashin lallai sai anje gidan Hajiya Zainab suyimata sannu da kuma gaisuwa had'e da jaje, Maigidan ta yagayamata komai
Haka kuwa duk suka shirya
@ut@r h@jiy@๐ฑ๐ปโโ๐
๐ป
[11/10, 8:26 PM] โช+234 809 308 3613โฌ: [01/11 6:09 am] @ut@r h@jiy@๐
๐ป๐๐ปโ๐ป๐:
*FUTUHATUL KHAIR*
*ยฎNWA*
*ยฉZainab Y Hussein*
*Dedicated to FUTHA LUV*
*page 106-110*
Fadeela ta riga FUTHA shiryawa, tana tsaye dai