Showing 3001 words to 6000 words out of 36965 words
Chapter 2 - FUTUHATUL KHAIR Yarinyar Da Ta Zo Da Alkhairi by Xainab Y Hussain
tambayar Bena sukayi inane asibiti mafi kusa OPITAL shine na kusa amma wallahi Aunty baxasu karb'ekuba dan basuda kirki"mudai kikaimu Dan Allah haka suka sami mota har xasu rufe saiga FUTHA da rubutu a hannu d Ita suka tafi.Motar Na saukesu Allah ya taimakesu anturo gado,shine akasata bin bayansu sukayi atsakiyar cikin reception aka ajiye gadon ga Miemi sai kuka take danma Ita batada hayaniya Kuma batada raki da ihu irin namasu haihuwa,Aunty Yabi CE tace wa wata nurse sister Plx where is d doctor, kallonta tayi tace HAJIYA sai hakuri dan doctor ta tashi indai 3:30 tayi to bata qara ganin kowa tana cikin fad'a mata Sai gata ,yauwa gata nan ma gida xata tafi,juyawa tayi ido biyu sukayi da sauri doctorn ta qaraso tace Aunty YBK yau kece agari,me kikaxoyi Niger,dariya tace lallai *Jameela Mohd Ali*kece doctor d'in Allah y taimaka,qanwata na kawo haihuwa zatayi kuma gashi kamar ta wahala so Plx kiyi admitting nata ,labour room aka shiga da ita,addu'a FUTHA kawai take tana Allah kasa Auntyna ta haihu,wayar Jabo ta ara babanta ta bugawa,bata tayi tace ayimasa bayani kafin kace me haryaxo,Kuma har lokacin haihuwa shiru, Jabo ce tace da mariqin FUTHA dan Allah malam,ahaka aka haifeta kalleta kamar Idan ta bud'e baki xakaji maganarta,Ayya yarinya ba'a haka aka haifetaba,aduniya tasamu ba inda bamujeba Allah baisa bakin ya bud'eba,har ruwan *Tanut* mun kaita tayi wanka dashi Kuma tasha komai na Allah ne wataran bakin xaibud'e,Ameen Jabo tace rufe bakunsu keda wuya,sister Xainab tafito (Maman khadee)da saurinsu suka miqe at are suka furta ta sauka
?
_2 U FUTHA Luv_
*By @ut@r h@jiy@*💅🏻💅🏻💅🏻
®Nagarta writers association®
[11/10, 8:13 PM] +234 809 308 3613: 🌹🌹*FUTUHATUL🌹🌹 KHAIR*🌹🌹
(August 2016)
{8:30am}
*Zainab Y Hussain*
Page 17
✍🏻```Maman Khady ce tace bata saukaba,amma tana kan gab'a insha Allah .Harta juya FUTHA tajanyo rigarta miqamata rubutun tayu ,Kabeer ne yace dan Allah kibata amma FUTHA ina kika amso,kwatance tayi masa cewa gidan su Maman haneep ta karvo,OK dama Kinsan tunjiya nake burin zuwa ,Allah yayi miki abarka, Jinjina kai tayi, minti goma yayi kad'an Maman khady ta fito tace ina kayan baby,dagudu ta miqamusu kayan Allah yasa Adda Bena tace a d'akko.```
*Basu dad'e ba aka fito da Babyn kowa hannu ya miqa zai amsa babyn ,kai masha Allah abinda kowa yake fad'a kenan qaton baby namiji fari tas dashi, Jabo ce ta karb'eshi itama tamasa addu'a ,AUNTY Yabi ce taxo ,ina Maman baby lafiya take,eh! lafiyarta lou tana resting room nan da 30 minutes xata iya tashi amma ta wahala Babyn ne qato kuma badan anzo akan lokaciba dole operation xa'ayi mata ahaka ma saidatasha ruwan naquda five Leda,amma yanxu da sauqi tunda bacci take.Alhamdulillah kawai Kabeer yake cewa, waya yaf ara bugawa gida ya sanarmusu ihu suke acikin wayar na murna gidansu Miemi ya buga yana bugawa qanwartace ta d'auka hartafara Maman biyu,dariya yayi yace Sodangi to d'an d'aya kuka samu qara ta saki tace Yaya it means aunty ta haihu ofcours yace mata ,saboda haka ki ban gift din fada miki danayi,Allah xanbaka amma turan Babyn nagani nasan dani yake kama,ina d'ana dani yake kama gadogon hanci ba irin nakiba,wah? Wallahi kasan nidai kyau aguna hardana saidawa,naji xan turo shikenan? Eh tace yanzu fa xanfara shiri na tawo kace ina gaidata,xataji ya katse wayar.*
*Doctor Jameela*```ce tafito godiya suka ringa yimata,ba komai yiwa kaine ko ina gida Aunty Yabi tace naxo xuwa xanyi,Allah ya qara lafiya tace,Ameen haka tayi musu sallama, itama Aunty Yabi tafiya tayi godiya sukayi mata,tace Ba komai tare da Jabo suka tafi.
_2 u FUTHA love_
```By @ut@r h@jiy@💅🏻💅🏻```
*© NAGARTA WRITERS ASSOCIATION©*
[11/10, 8:13 PM] +234 809 308 3613: 🌹🌹 FUTUHATUL🌹🌹 KHAIR🌹🌹
(August2016)
{4:00pm}
*Zainab Y Hussain*
*Page 18*
✍🏻Maman Khady ce ta dawo tace kuna iya shiga,tom yace gaba d'aya suka shiga d'akin Adda Bena ce agaba,sai ummul fadeela don taxo a lokacin Kuma kunsan Miemi tayimata had'in turare,mutunci datayimusu yasanya suka qulla qawance.
Tare duka suka shiga da sauri FUTHA taje tayi hugging nata,sannan ta xauna kusa da ita kowa murna yayimata Allah yarabasu lafiya,babyn kamar mamanshi Kinsan Miemi da kyau Kabeer shima ba bayaba,kyakywane Babyn, basu jima ba suka tarkato suka dawo gida,gyagyara d'akin akayi har gidan tunda k'ofar gida xakasan gidan maijegone wadda takeji da gayu,dan turaren wuta akasaka ako ina,Bena andage anata aiki ,suna xaune ta shigo da flask da kayan tea had'amata tayi ,yauwa yakamata kisamu abi mai nauyi kici ko agirka miki, la Adda nayi girki d'azu saidai bansaniba ko xakuci dan gaskiya yayi sanyi,nibancin abinci Idan yai taking one to two hours balantana wannan dayajima FUTHA xoki d'oramana girki wannan Kuma abawa almajiri,haba Miemi ai wannan b'arnace bara muci shi ahaka ,d'akko ke FUTHA Idan yaso sai tayi miki naki,a'a tayi gaba d'aya kema axubamiki tunda bakiyi girkiba mai maigidan naki zaici ?ai kuwa dai tanayi tana loma,Adda Ba sauqi wajan xira abinci,flask guda suka cinye itada ummul fadeela, gara ita ciki gareta dan taci.
D'oki bai bar FUTHA tayi bacci ba,minti kad'an ta tab'a yaron,qawayenta irinsu Rash,candy,Anee QURRATU haka sukayi ta xuwa balantana candy Ita kowa tafiya yayi yabarta,tunda taga and'ora abinci ta xauna,abinnema yasa mu gurinta,kwadayi wajan ta hardana saidawa.
Maigidan kuwa gaba d'aya jinsa yake acikin wata duniyar abinda suka fidda rai gashi Allah yabasu saidai godiya ga sarki Allah. Xuwan sassafe 'yan uwanta danasa sukayi su Fido Sodangi ansamu new baby sai rawar kai take, Aunty Jidda da Mrs omar ba xama gyara nan gyara can,Afreen ce tace Aunty Nafeesa ina Mama wacce mama,Aunty Hassana (Hassy) nake magana kaddai bada Ita kuka zoba?au kinsan tanada qawa a Niger gidanta tafara sauka wai tace ta kawo kaya xataje ta duba,au Maman Bobo kike magana yauwa ita,ok tace .
Tun safe FUTHA suka fita itada Abban ta siyowa baby kaya, batada masaniya a xuwan su,da murnarta suka shigo gidan,d'akin tax big ata shiga ta shiga kan cinyarta ta d'ora kanta,twasa taji abayanta ke dallah d'agata qatuwa dake,Allah Miemi wataran sai kinyi nadamar riqe wannan 'yar,kalleta dan Allah "Mrs Omarce tace haba Yar mutan Anker kekuwa meye ruwanki da Ita,naga alama ba kwa shiri dan waccan xuwan da sukayi haka kike mata,kefa kallone naki,itada 'yarta ko FUTHA?kai ta kd'a
2 u FUTHA Luv
*by @ut@r h@jiy@*💅🏻💅🏻
_® NAGARTA WRITERS ASSOCIATION®_
[11/10, 8:13 PM] +234 809 308 3613: 🌹💐FUTUHATUL🌹💐 KHAIR🌹💐
(August 2016)
{7:00pm}
*Na Zainab Y Hussain*
*Page 18-20*
✍🏻```Haka Mrs Omar da Aunty Jidda Aliyu suka yima Anker magana badan tasoba tayi shiru dan dai tasan sune gaba da Ita,sallama sukaji daga waje,da sauri Fulani sadiya tafito daga ciki wa alaika salam jin maganar mace yasa Anker saurin tura kwanan abinci bed room,Seemby ce budurwa Kabeer, shiga tayi bayabo ba fallasa Miemi ta amsa,qin bata Babyn tayi saida tace muga Babyn, sannan tabata,shafa kansa tayi tace tubarkallah Babyn me kyau,masha Allah Anker tafad'a dan tasan rigimar da akayi akan Seemby,Maman FUTHA baby dai yahana kixo bikina next week ne Nigeria ma xani yau nace sai naxo naga babyn ,ayya bikinki xa'ayi Allah yasanya alkhairi sai hira ta b'alle atsakanin su,tunda taji baxata auren mata miji ba ```
*Biki buduri xoka ga uwar gayya Miemi tayi kyau baby yaci sunan Abdallah futha ce taxab'i sunan,nanma saida su sodangi sukayi magana Allah yaso magana batayi tsawo ba sosai. kowa kagani yaci kwalliya,duk inda kahanga taron mutane kake gani su Kansu 'yan Niger d'in garin abalak sunsan ana suna,komai anyi ya wadata,balantana dangin Miemi irinsu Rahina (mrs Aliyu) ansha kyau,'yan exellent sunxo sosai kodan sunsan xa'ayi abin kirki,Kuma gasu da kwad'ayai,NAGARTA ma sunzo Sanah tayi qoqari tundaga kano ta taho,kowa kagani yacika baki da nama kunsan Niger da nama kamar me,su Haneepa da mama Hassy sune masu rabo, ba wargi kunsan Hassy qatuwace shiyasa batada wasa,doctor Jameela ma taje,Jabo ma haka,Anker saboda masifarta su aunty Jidda suka hanata rabo,amma dai itace mai raba take away dasu Uumu Ruman*,```HAJIYA maiJidda Musa ,da Aisha humaira admin littatafan Hausa duk sunje```
*FUTHA itama danata qawayen party guda suke agidan Adda Bena,Aunty Miemi ce ta d'ibarmata komai,da sauri ta shigo batasaniba ta bangaji Anker mari xata bata Aunty Jidda ta hana,haba batasan ta bigekiba ran sunanma,FUTHA me kike so, alama tayimata kaya xata canja Miemi tace,Swiss ne me kyau ta d'akko tasaka iri d'aya sukayi da Aunty ta.haka aka sha suna lafiya da xaman lafiya kowa yaci ya qoshi,```Maman shaheed``` nagani tana sid'e hannu gurinta aunty Hassy taje tace bakisamu abincin ba? lah nasamu,wad'an cen ne dai basu samuba suwaye nagansu haka kamar yaqi,```'yan dandalin Autar Hajiya ne ```innalillahi amma yanxu sukaxo,mun shiga uku da masifar auta ,daga baya Aunty Mamu tace d'arima kika shiga dan Auta Ba dama,Kedai bari,Allah yasa yanxu muke magna anmanta buhu uku acikin d'aki da kulan paper kitchen maqut najiyo had'iyar miyau kallan wadda tayi nayi Hulle ce ,itada Fatima ,Ga Ameera da Maryam Cavara akusa dariya nayi nace tav amma Auta tahad'a mutane haka akayimusu goma ta arziqi*
```Anshare suna, Aunty Jidda Sune kan haba wajan irga abinda aka samu,wata atamfa aka d'aga,Sodangi ce tace wallahi wannan kalatace ,Miemi kuwa tace kalar 'yatace FUTHA saidai kizab'a awata ,haka dai sukayi hira irin Na 'yan uwan juna.Shirin kwanciya sukayi, FUTHA waje tafita tayi kwanciyarta,a tabarma,Miemi ce tafito ta ganta ahaka ,tashinta tayi suka tafi Kan katifa suka kwanta,3:00 dai dai FUTHA ta tashi fitsari Har ta kwankwanta,tajiyo nishi sama sama, sharewa tayi amma saita qara jin kamar qara yi ake tana juyowa Aunty Miemi riqe da ciki da sauri tayi kanta tashin su tayi baba d'aya jikinta ya jiqe da gumi kuka sukasaka FUTHA ce tafita takirawo Kabeer yana xuwa kanta yai yana Miemi yadai meke miki ciwo ,cikin ta ta nunamasa,,Plx kufito da Ita Na d'akko mato,hannunsa ta riqe ta had'a dana FUTHA,tace plx hayatee ga amanar FUTHA ka riqeta kasamamata kyakyawar rayuwa kayimata xab'i da miji nagari,Idan Kuma nasamu iyayenta kace ina gaishesu Allah baiyi nixan sadasu d 'Yar suba,kaji ka taimakan ga da'na kula dashi wani irin nishi tayi da sauri 'yan uwanta sukayi kanta No!```
Loading .....................21
*2 U FUTHA Luv*
_@ut@r h@jiy@_💅🏻
® NAGARTA WRITERS ASSOCIATION®
[11/10, 8:13 PM] +234 809 308 3613: 🌹🌹*FUTUHATUL*🌹🌹 KHAIR🌹🌹
*(August 2016)*
*Na Zainab Y Hussain*
*page 21*
✍🏻```Kabeer ne yatabata yaji shiru, aunty Jidda tace lafiya,asanyaye ya kalleta ganin idaniyarta na xubarda hawaye,bai iya cewa komai b,ya miqe ganin haka yasa Mrs Omar d Mama Hassy xuwa gunta da sauri,tatrabata sukayi suma,amma basuji wata alama wadda take nuna akwai rai atattare da ita ba.Anker ce tace Yaya Hassana matsa kugani,kinsan ciwan ciki yanasa mutum ma ya shiga comma, maybe kuma suma ne,itama dauriya kawai take,duk wani iyawarka da basirarka Idan kwana ya qare ba makawa Sai ka tafi,Allah sarki Miemi duniya lokacin datake qaunar xaman cikinta lokacin Allah ya d'auketa cikinta,lokacin da take burin gani Na sanyin idaniyarta,lokacin Allah yara basu, lokacin da d'anta yake bid'arta lokacin Allah ya amshemasa ita,Allahu akhbar Lokaci yayi,ganin dai dagaske ta amsa kiran ubangiji gaba d'aya suka fasa wani irin kuka,FUTHA kanta taje tafara jijjigata tana wani irin kuka mai tsuma rai,y'an uwansu ne sukaxo kanta da kyar suka banbareta ajikinta,so take tayi magana amma takasa,sai ayau taji tausayin kanta,takumaji inama tana magana,ganin d'aukanta ne yasa kowa kuka,'yan uwa akayi tabugawa waya,kafin safiya anmata wanka,qarfe 7:00 'yan uwa suntaru Fido ba'a magana saboda ta shaqu da Meimi sosai```
****** ****** *****
*Haba d'aya 'yan uwa antaru masu karatu nayi masu laximi nayi,FUTHA itama Qur'an ta d'auka tana karantawa,qawayen ta suxo,Rash itace tafara xuwa sannan Qurratu da candy, Kabeer ba'a magana dan tunda yadhiga d'aki ko qafarsa bawanda yaqara gani,yana cikin d'aki kuka kawai yake yanxu Miemi ta mutu,dama Ba sonsa takeba,shiyasa ta tafi ta barshi,tun yana kuka har kukan ya qafe,saida lokacin kaita makwancinta yayi sannan akafara tambayar ina mijinta yaxo suyi sallama, haka babansa ma yace ina yarinyar datake riqewa haka FUTHA taxo nifa kanta tayi, akan gawar shima da yaxo kasa komai yayi,haka aka d'auketa,lokacin da xasu fita gaba d'aya aka rud'e FUTHA xubewa tayi bataqara Sanin kantaba sairan sadakar uku,haka ta tashi ganin yawan mutanen dake cikin gidan ya tuna mata da abinda ake,kuka takeyi,'yan uwan Kabeer sune suka rarrasheta,amma 'yan uwan Miemi ko kallo garama manyan.*
**** * ****** ******
```Yau akayi sadakar bakwai ayaune Kuma dangi suke shirin tafiya 'yan uwan Miemi Aunty Jidda itace ta d'auki Babyn,amma su bayau xasu tafi ba,'yan uwan Kabeer dai sune suka tafi,kafin tafiyarsu nan ne suka xauna ,akayimasa naaiha,sannan mahaifiyarsa tace Kabeerkasuwanci yakawoka Niger,har Allah ya axurtaka kayi aure ,bakada kowa a Niger saboda haka kayiwa Allah kabar garin,Kuma duk wani abu dayake banakaba kayi qoqari kasada shi damai abin,dan bansan kakai nan da sati biyu a garin dan xamanka baxai amfaneka da komai ba,tunani ma kad'ai ya isheka abinda KA Tara kataqo gida,Allah nikuma yabamu ikon riqe amanar da matarka yabaka ta wannan yarinyar.haka sukayi fad'a masa sannan suka tafi```
*Yau dai aka d'ebe komai Na Miemi Kuma 'yan uwanta mota biyu sukayi suka tafi,Sodangi kamar tace sutafi da Miemi kodan son datakewa sistern ta,Amma tasan baxasu yadda ba,itama FUTHA kuka take kamar tace xata bisu amma ba hali,haka duka tafi suna kuka,kamar yaune suka ka 'yar uwarsu amma gashi suntafi batare da itaba,ko tunanin dawowa,dominta ba,qanqame Babyn Hassy tayi, haka mota tana Sai 9ja.*
*Gidan Adda Bena FUTHA ta tafi,anan take kwana ,shi kuma gaba d'aya yanzu komai nasa yake saidawa din har gidan Alhaji Raheem ne yasiya,Kuma gashi ayau sunyi bankwana dashi a komai, don ya bashi mukullin shagonsa,sannan shima yabashi sallamarsa.*
*2 U FUTHA LUV*
*by @ut@r h@jiy@*💅🏻
*NWA*
```Allah kabawa Miemi lafiya,Dan acigaba da Fannah```
*Welcome back home my lovly Freind, Hauwa Jabo*
🌹💅🏻 FUTUHATUL🌹💅🏻 KHAIR💅🏻🌹
*Xainab Y Hussain*
*Page 22-25*
✍🏻```A yau tun safe suke shirin barin garin,gaba d'aya jikin su yayi xanyi,ita kanta Bena sai yau taqara jin mutuwar qawarta,haka tahad'awa FUTHA goma ta arziqi,gaba d'aya qawayen FUTHA sun fito domin rakata kuka suke sosai dan FUTHA qawace tagari mai kuma gudun fad'a da abin hannun mutane,Rash da candy sune manyan qawayenta Idan kagansu alokacin babu abinda xai hana KA zubarmusu da hawaye,saboda yadda suke kukan rabuwa da FUTHA.```
*Haka suka hau mota xuwa tashar Niger, asibitin da aka amshi haifuwar Aunty Miemi shi suka wuce kallon asibitin tayi hawaye ta goge axuciyarta tace kamar ba rana irin tayau aka kawo aunty labour Kuma tafito da qafar ta haka suka wuce gidan aminiyar Aunty duk inda suka wuce hawaye kawai take goge wa,inda kukanta ya qaru shine gurin Anee toilor wadda tare su kaje da aunty before sunan Abdallah, haka taqara saka kuka,hannunta ya damqe ahaka har sukaxo inda xasu hau mota xuwa Nigeria🇳🇬. Kallonta yayi yace FUTHA kina kukan rabuwa da Auntynki,?kai takad'a murmushi ya saumata wanda yafi kuka ciwo yace kina kuka na rabuwa da ita ad'an shekarun da kikayi tare da ita, kina kuka saboda yadda kika shaqu da Ita,kina kuka saboda yadda take kula dake take lallashinki ko ? kai taqara kad'a masa,kallonta yaqara yi yace to FUTHA kinyi kuka saboda haka,nikuma nayi kuka nida mukayi shekara sama da goma tare,why Miemi! meyasa kika xab'i ki horani ta hanyar tafiya ki barni,bayan kinsan kina sona nima haka.rungume shi tayi haka suka sha kukansu.*
```Hannunta ya matse yace FUTHA kiriqi amana duk inda kika shiga,ki riqe mituncinki da qimarki ta d'iya mace ki darajata kanki sannan xa'a darajataki,kiriqi Allah aduk inda kike, hawaye ne kexuba a idaniyarsa,Naxo Niger dan nema,naxo tare da Miemi duka da 'yan uwanta basu so tafiyata da itaba naxo Niger a banda komai nasamu abin kaina,naxo Niger tare da mahad'in rayuwana Miemi amma gashi xan barta batare da itaba,Allah kayimata rahma,gaba d'aya 'yan motar suma hawaye suke don tausayinsu,da qyar ya rarrashi kansa.```
*Tafiya suke wasu na bacci wasu na danna wayarsu,wasu na ciye ciye amma Idan kadubesu ba abinda suke Sai Jan carbi,yanayi yanamata nasiha da yadda xata tafi da rayuwarta, haquri jigone FUTHA kikasance mai hakuri da rayuwa,xaki iya tsintar kanki awata rayuwar daban,ki hakuri d yadda taxo miki, sun shigo gari sosai dan har waya yayi gida sun kusa sauka,Dan sauran baifi minti talatin su isa garin sokoto,wata mota ta tawo da gudu,ba yadda drivern beyiba dan y kaucemata amma ina Allah ya tsara, dan gaba d'aya motar suka gangara kafin kace me, sunkama da wuta,jama'a ne sukayi Kansu amma ina ko alamar tsayuwa wutar batayiba duk iya qoqarinsu saida motar kwana kwana suka xo,haka aka fito d mutane wasu sun mutu wasu da sauran ransu,cikin wad'an da suka mutu harda Kabeer,hankalinane ya tashi ganinb haka nace OMG!FUTHA yaxakiyi wannan qaddarar Allah ya d'oramiki,haka nafara raba idanu koxanganta amma duk hangena banga mai kama da itaba ma,INA tayi to?Waya d'auketa ban ganiba?kotanacikin motar haka natafi da sauri amma ko takalmi bangani nataba.Innalillahi wa inna ilaihi rajiuun"abinda nayita cewa kenan, duk hangena bangantaba ina tayi to kodai taxama qarwashi ko toka ?*
*2 u FUTHA Luv*
*® @ut@r h@jiy@*💅🏻
®NWA®
🌹🌹FUTUHATUL🌹🌹