Showing 63001 words to 66000 words out of 97469 words

Chapter 22 - RAINON SOJA BOOK 1 COMPLETE BOOK MAMAN TEDDY.pdf

23 Nov 2025

1131

Zuciyar ta gami da Wannan baƙuwar fuskar
da ta gani a cikin a halin General Saleh Yelwa . Tum-tum mat ta zauna inda Itama mami ta
zauna gaban su shaƙe da kayan motsa baki . Ita kam jidder Resting chair ɗin dake daga gyefe
kaɗan ta nema ta zauna , tana zaman jiran mene zai fito daga bakin Hajiya Hajara. Don kaf
dangi anyi ittifaƙi da Rashin kirkinta musamman idan Abu bai mata ba .

Dan Tsawa Mami tayi tana Binta da kallo , don ganin yanda ta lula Duniyar tunani yasa ta tuno
da maganan likita don ba'a daɗe da dawo da ita daga India ba akan lafiyar ƙwaƙwalwarta , don
a shekarun baya Ta samu matsala na mantuwa, inda a yanzu ma Wasu Kaɗan ne daga cikin
rayuwarta na baya ta iya tunawa dashi , shine Rayuwar ahalinta. Ta ɗebi shekaru a wani
ƙauyen Fulani tana rayuwa da mutane masu amana , sai kuma rana ƙwatsaaam ta tuna da
Ɓangare na Rayuwar ta da Iyalanta wannan ne sanadiyyar dawowan ta har aka yi nasaran
ganin ta. Fatan su a yanzu shine kar ta tuna da Abubuwa da yawa da suka faru , wanda ya
haddasa masu baƙin ciki a rayuwar ta mara iyaka . Har kuma iya yanzu suka tuno da Wannan
mutumi babu Abin da suke bin sa dashi sai ALLAH ya isa!

Hummmm Jan numfashi Mami tayi kana tace “ Hajara tunanin me kike yi haka ? , Da Wani Abu
ne ?” . Sauke lemun hannun ta tayi tana mai dashi saman plate ɗin dake gaban ta . Kana ta kalli
Mami fuska babu walwala tace “ Ina Boy? Ya girma sosai ko? ”.


Yana tare da Ma'eesha ina zai tuna da ke Mom? Ai idan suna tare bai ganin kowa , har gwara
shi da Khalil ma , don ko me zata yi ba'a mata faɗa ”. Muryar jidder ya katse su wacce take
latsa wayar ta tana kwararo zance . Ya ishe Ni haka! Kuji mun mara kunya dake ake yi ne? .
Mami ta katse Ta cike da Tsawa , Wannan yasa Jidder kallon ta tare da kama bakin ta .
Haba Mamin Haidar Meye na wannan faɗan haka ? Jidder ce kike ma wannan tsawan nawa
duka take ? Ai wannan zaki firgita mata tunani ne , Aƙwai shekarun da idan yara basu kai ba
wani Hayaniya duka bai kamata da ayi masu shi ba. Tsayawa Mami tayi tana kallon Mom Hajara
don bata yi wani mamaki ba ,don tasan halin Hajara da son nata. Cike da San yi ta furta “ Ta
dame Ni da Ma'eesha tun da nake ban taɓa ganin masifaffiya irin jidder ba. Wai ita wannan
Ma'eesha wacece? Kai Anya??? .

Mom Hajara ta furta tana bin mami da Wani irin kallo . Yarinya ce mai kyau hankali da tarbiyya
momy ga haƙuri ba irin Wancen mummunan mai ƙaton Goshi ba .

Saurin juyawa Duka suka yi suna kallon hanyar shigowa inda Khalil ke takowa cike da takon sa
. Fuskar sa Sake yana kallon ɓangaren da Jidder take ya watsa mata Wani irin harara da sai da
ta shiga taitayin ta. Kallon su duka tayi kawai sai ta miƙe tana saka kukan sarganci da Gata tare

da cewa “ Mami nafi shekara goma a cikin wannan halin hantarar da suke yi mun , tun da
Ma'eesha ta shigo Rayuwar mu nake fuskantar tsana.....Kawai sai ta rushe da kuka da gudu
tana juyawa tare da barin falon . Kyaji dashi halin ki zaki gyara. Mami ta furta tana jan ɗan tsaki
tare da tsuwa tana gyara zama .
Zama Khalil yayi a kujeran da jidder ta miƙe kana muryar Hajiya Hajara ya katse su tana cewa “
Gaskiya Nima naji na tsani wannan Yarinyar haba..........!


Don Allah kar ki karanta mun idan baki biyani ba . Ga masu buƙatar payment regular payment
₦500 Vip group ₦1000 SPC payment ₦1500 via 6037312299 mohammed Aisha keystone bank
ko katin MTN ta Wannan number 08081202932 tare da shaidar biya evidence of payment .idan
Vtu transfer ne sai ki tura ta Wannan number 09061466409 .#Antymmnteddy. [1/21, 8:12 PM] Anty Aisha Mmn Teddy Marubuciya: *(Book 3 three)*
*Love and Amazing story*
*Written....✍ Aysha Mamanteddy Mrs Usm*




_________________________

*RAINON SOJA*
*Through the gate of love a valiant fearless heroical and Sympathetic Story*



*Littafin na kuɗi ne please ban yarda wata ta karanta mun ba tare da Ta biyani ba , regular
group ₦500... Vip group ₦1000... SPC payment ₦1500 via 6037312299 Mohammed A'isha
keystone bank ko katin MTN ta Wannan number 08081202932# .*




37~38
_________________________


Gaba ɗaya kun fifita yarinya yar tsuntuwa ce fa? Meye kuke yi ne haka ? Gaskiya raina ya fara
ɓaci yanzu zan tashi na bar cikin gidan nan , kuma dana san Wannan Zan taho na tadda da
banzo ba . Hajiya Hajara ta furta tana miƙewa tare da Ɗaukar fankacecen Gilashin idon ta
wanda ta Ajiye a gyefe . Sanin hali yafi sanin kama ,wannan yasa Mami saurin riƙo hannun ta ,
don ta san ta da zuciya irin na Haidar a yanda mami ke cewa ita ya ɗebo a saurin ƙufula da

fushi . Habawa Hajara me yayi Zafi? Don Allah ki zauna . Yanzu ya gida ya kuma Hajiyar ta mu
?. Mami ta furta zancen cike da Sanyi da kuma rarrashi .

Ɗan jimmmm Hajiya Hajara tayi kana tace “ Kowa lafiya amma ba fa zaki gane kan gadona ba
sai naji kin rarraso mun Jidder ta dawo mun cigaba da Hira ”.

Murmushi Mami tayi kana ta gyaɗa mata kai tana furta “ Shikenn Bara naje da kaina ma na
rarraso Miki ita . Amma....Aaaaaammmm Khalil taho ka kira mun Boy yanzu tun da shi bai neme
Ni ba . Hmmm. Wani guntun Numfashi Ya sauke , a hankali ya fara tuno da sihirtaccen
ƙyawunta da Wannan murmushin nata . Gani suka yi ya saki Murmushi yana furta “ I miss You
so much ”. To! Kai kuma da Wane? Matar da zaka Aura Maryam ko kuwa wacce kake
magana? Mom Hajara ta katse shi tana bin sa da kallon rashin fahimta .

No mom , Ma'eesha nake nufi nayi kyawarta da Wannan murmushin nata.....mtswwwww! Mom
Hajara ta ja dogon tsaki kana tace “ Anya Wannan yarinyar ba maƙiya ne ba suka jefo ta cikin
gidan nan don wani mugun Abun?. Subhanallah! Mami ta furta tana ɓata rai ƙwarai wanda
hakan yasa Hajiya Hajara miƙa masa waya tana cewa “ Kira mun shi yanzu ”.
Amsar Wayar yayi bai ce mata komai ba, don ransa sa ya fara sosuwa da maganan Mom
Hajara ɗin . Gani tayi ya fara kiran Wayar Haidar ta Wayar sa , duk da yasan ba wani jituwa ke
tsakanin su ba . Wata ƙil ya ɗaga ko kuma akasin haka ”.

**
Ɓangaren Aliyu kuwa yana Tsaye yana kange da Waya a kunnen sa suna Magana da Aminin
nasa Areef wanda yake ta cewa “ Ina jinka, tun tuni kana ta Wani kame kame da fa magana a
bakin ka amma kana mun shiru ya dai? . Ƙwanciya Areef yayi yana ɗan sosa ƙyayarsa don bai
san ta ina zai fara masa bayanin lamarin ba . Mtswwwww! Dogon tsaki Ali yaja cike da fushi don
bai san shiru Gashi dai ɓakin Miskili amma shi sam bai san ayi masa shiru wannan yasa shi
cewa “ Zan kashe waya na fa”. I'm sorry Ali kana jina? . A'a ban jinka ”. Ya basa amsa dai dai
yana kallon shigowar kiran Khalil amma ya watsar bai bi takai ba. Hummm Babban yayan mu
kenan! Areeef ya furta yana wata yar dariya wanda Aliyu kai tsaye yace “ Kaje maganan ka
Yallaɓai ”.

Hummmm Aliyu Ni kuwa nace kunyi ma Ma'eesha miji ne?ƙitttttt! Yaji Aliyu ya katse kiran ,
wanda shi kan sa bai san dalilin da yasa shi yin hakan ba . Bai tsaya kuma jin ƙarikon mai zaice
ba ,don tuni ya fahimci inda ya dosa a kalmar sa guda ”. Tsayawa yayi yana cizan laɓɓansa na
ƙasa tare da dunkule hannun sa Zuciyar sa na masa zafi da Huci. Me yasa sai Ma'eesha? Ya
furta cikin Tsawa yana saurin juyawa tare da nufar Bedroom ɗin sa inda ya barta tana shan
Cofee don shi titir a shan Cofee yake . Hummmmm! Da ƙarfi taji saukar Ajiyar zuciyar sa kana
cikin sauri ta juyo tana kallon sa .


Mamaki ne ya kamata ganin yanda gumi ke karyo masa Wannan yasa ta miƙewa daga tsaye ,

amma sai da hannu cike da Wannan isan nasa ya dakatar da ita yana mata Alama da ta zauna .
Babu musu ta ja ta zauna , Amma Bata daina kallon sa ba , haka bakinta ya kasa shiru wurin
furta “ Uncle motsa jini kayi naga Gumi ne a fuskar ka da jikin ka?”. Girgiza mata kai yayi kamin
a ɗan daƙile yace “ No”. To wannan gumin fa? . Cike da Arrogant voice ɗin shi ya furta “ I hate
Norse ”. Gummmm tayi da bakin ta tana komawa tare da shan Cofee ɗin tana kallon sa a sace
a sace . Keeeee!!! Kin ma iya Cofee? . Ya furta cike da neman ta da laifi don ya fanshe Haushin
shi ya bata Wahalar don yau ji yake tamkar ya bugi banza! A ganin sa itace take sakar masu
fuska har su samu damar tunanin son ta .


Kin iya Cofee?? Ya kara Tambayar ta fuska Gimtse babu fara'a . Dan kallon sa tayi tana lumshe
lumsassun idanun ta kamin ta girgiza masa kai tana cewa “ Aa ban iya ba , Mami ke yi sai kuma
yanzu kai da kayi mun . You Are very stupid , kina nufin Common thing Cofee baki iya
ba???..........Good night lavs yau dai Ma'eesha taga banu a hannun Aliyu , Allah ya
ƙwaceta don yau da wuya bata daku ba . Mu tara a next page 39~40 .

*Don girman Allah kar ki karanta indai baki biyani ba . Ga Masu buƙatar payment regular group
₦500 Vip group ₦1000 SPC payment ₦1500 via 6037312299 Mohammed A'isha keystone bank
ko katin MTN ta Wannan number 08081202932 Vtu transfer Kuma ta wannan number
09061466409* [1/22, 1:36 PM] Anty Aisha Mmn Teddy Marubuciya: *(Book 3 three)*
*Love and Amazing story*
*Written....✍ Aysha Mamanteddy Mrs Usm*




_________________________

*RAINON SOJA*
*Through the gate of love a valiant fearless heroical and Sympathetic Story*



*Littafin na kuɗi ne please ban yarda wata ta karanta mun ba tare da Ta biyani ba , regular
group ₦500... Vip group ₦1000... SPC payment ₦1500 via 6037312299 Mohammed A'isha
keystone bank ko katin MTN ta Wannan number 08081202932# .*



39~40
_________________________

Yayi zancen yana wani irin haɗe giran sama da ƙasa . Kallon ta ya kuma yi a karo na biyu ganin
yanda jikin ta ke tsuma da kyarma yasa shi cike da Miskilalliyar Murya wanda ba don tana gab
dashi ba sam ba zata ji mene yake furtawa ba. “Cofeee??? Ya nanata cike da Muryar damuwa,
kana yace “ Maza zauna ki haɗa mun Wani yanzu ”. A hankali ta zauna tana fara jan flask ɗin
ruwan zafi kamin ta fara ɗaukar Cofee cup tana kallon sa a ido ido . Gimtse fuska yayi yana
hura hanci tare da tattare gida . Wayyo Mami Daddy Uncle yau duka ne yake son yi . Ta furta a
Zuciyar ta dai dai tana ɗagowa zata zuba sugar kenan taji tsawar sa yana furta “ Meye kuma na
Damuwa a dai dai Wannan lokacin? ”.

Mtsww! Yar ƙaramar tsaki yayi yana kallon ta ganin yanda tayi masa ƙurrr da ido . Kin gama ne?
Ya furta yana kallon cup din hannun ta. Sam ta manta da sugar a tunanin ta ta zuba ashe babu
sai one tea spoon da ta sanya . Cikin Sauri ta miƙa masa tana ja baya , amsa yayi yana motsi
da ƙafarsa kana yace “ zo ki mun massage! Ko shima baki iya ba?”. No! Na iya ,Ai ina yi ma
Mami idan ta dawo Aiki ta gaji kuma tana cewa na fa iya sosai . Kauda kan sa yayi yana miƙar
da ƙafansa tare da cewa “ Oya zo ki fara ”. Matsawa tayi da wannan lukutar jikin nata tana
zama daga ƙasan carpet tare da Kama Ƙafarsa tana matsa masa a hankali. Laushin hannun ta
ne yasa shi fara mancewa da damuwar sa . A hankali yake sauke Ajiyar zuciya, Wanda ita kan
ta tunani ta fara yi kodai Allurar sojan ce zata motsa masa ? , Amma a haka cike da Ɗari ɗari ta
furta “ Uncle baka sha Cofee ɗin ba?”.


A hankali ya ware Lulun idanun sa yana kallon fuskar ta dake fidda masa da Annuri , hummm
jan numfashi yayi yana kauda idanun sa daga gareta tare da kai Cup din Cofee ɗin zuwa bakin
sa . Ɗan kurɓa yayi ƙafan yayi saurin kallon ta yana Aje cup ɗin tare da furta “ Oh my God!
Ma'eesha meye wannan kika yi? Wai da gaske Cofee baki iya ba? . Ya furta a matuƙar zafafe ,
kina mace ko Cofee baki iya ba bare kuma akai ma tea da Kayan karin kumallo . Yau zan shiga
jikin ki da ƙyau zan yi maganin rawar kan ki . Ai kin iya soyayya!. Cikin Muryar kuka tana
shirin ƙwarma masa ihu ta furta “ Innalillahi wa.....yi mun shiru daga nan ko yanzu bakin ki yayi
jini, ai baki da macece sai ALLAH daga Ni yau sai ke a cikin gidan nan .

Cikin dakakkiyar Muryar sa ya furta “ Oya! your knee should be Down ”.

Tuni kukan ta ya ƙaru tsoron sa ya ƙara kamata , zubewa tayi a ƙasa tana Ɗaura Gwiwowin ta
bisa tiles ɗin falon tare da haɗe hannayen ta tana furta “ Don Allah Uncle ɗina kayi haƙuri pls
uncle Aliyu Wallahi zan haɗa maka Wani me Daɗi kaji Uncle Haidar?”. Kamin ya bata Amsa ne
kiran Khalil ya kuma shigo masa a karo na uku wannan yasa shi Ɗagawa a ƙufule yana furta “
What?”.

Yanda Khalil yaji Muryar sa yasa jikin sa ɗan yin sanyi , don yasan halin Ali kar yazo yana jin
masifa ne ya sauke akan ma'eesha don wannan sababben sa ne , idan yana fushi to akan kowa
sauke Haushin sa yake yi . Please Ali ka rage Faɗa , Ka tambayi ya nake? Ammmm.....Sorry ya
akayi ? Muryar Haidar ya katse shi , wanda jin hakan yasa Khalil furta “ Ya kake? Ina amanar
mu? . Ɗammm jim Haidar yayi kana ya kalli inda Ma'eesha ke matsar ƙwallah, cije labɓan sa

yayi na ƙasa kana yace “ Khalil Amanar mu ko Amanata? Meye haɗin ka da ita? .

Saurin kallon sa Ma'eesha tayi tana furta “ Ya Khalil ne ?. Wani irin mugun kallo Aliyou ya watsa
mata wanda ya sata ja baya tana cigaba da Abin da ya sata amma idanun ta basu sauka akan
daina kallon sa ba .

Kai kana da matsala wallahi Aliyu , dama Mom ce tazo tana son magana da kai , sai ka bata
Ma'eesha su gaisa kamin ku dawo ta ganta”. Ɗannnnnnnn ...................✍.
[1/22, 6:43 PM] Anty Aisha Mmn Teddy Marubuciya: *(Book 3 three)*
*Love and Amazing story*
*Written....✍ Aysha Mamanteddy Mrs Usm*



_________________________

*RAINON SOJA*
*Through the gate of love a valiant fearless heroical and Sympathetic Story*


*Littafin na kuɗi ne please ban yarda wata ta karanta mun ba tare da Ta biyani ba , regular
group ₦500... Vip group ₦1000... SPC payment ₦1500 via 6037312299 Mohammed A'isha
keystone bank ko katin MTN ta Wannan number 08081202932# .*



41~42
_________________________

Ɗannnn jim yayi kana yace “ Mom Hajara ce? Bara na kira”. Kai da'alla malam dakata mana ,
gafa ta kuyi magana kana ƙoƙarin ɓata mun lokaci? kana Wani mun magana kaman kai ne
gaba dani.....? Shiru Aliyu yayi yana jin tafarfasa amma babu yanda ya iya dole yayi haƙuri don
ya lura shima Khalil ɗin ya fara Hasala ”.
Ɓangaren Mom Hajara kuwa da Mami dake Gyefen su bin su take da kallo kana tace “ Wai
wannan Abubuwan da kuke yi duka na Meye haka , bani Wayar mana’ . Miƙa mata Wayar yayi
yana kauda kai ransa a ɓace ya juya yana ficewa daga falon . A Zuciyar sa yana kisima
abubuwa da dama da zaiyi ganin ya raba Haidar da Ma'eesha don a ganin sa zalunci ne irin na
Haidar yake gwada mata .

**
Falmata! Falmata.....!! Fito a yau Wallahi indai na cika Adamu sai kin bar mun cikin gida na ”.
Muryar Alhaji Adamu ya tsinke Hajiya Falmata dake kishingeɗa a tsakiyar falon ta , gigif tayi

tana miƙewa daga tsaye ganin Alhaji Adamu a kan ta yana cigaba da Sababin inda yake shiga
ba nan yake fita ba . Tsaye ta miƙe tana bin sa da kallo yana tsiyaya ruwar tijaran da tun da
take bata taɓa ganin yana yin shi ba ,bare kuma ace wai itace yau yake yi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login