Showing 42001 words to 45000 words out of 52880 words

Chapter 15 - EZNAH Dan Sirri By EZNAH

EZNAH   

10 Aug 2026

16

data kame gashinta dashi
Gashin ya zuba kafadunta
Qamshin oil din Olive&aloe na gashin yashiga hancinsa ya lumshe ido sbd duniya yanason qamshi gashi ita kuma komai nata ya taba saiyaji qamshinsa.

Cup din datake basa milkshake ta aje tareda shafo gefen fuskarta cikin langabar dakai tace,

Wanka zakayi fa..

Bude baki yayi zaiyi magana wayarsa tayi qara yasaki qaramin tsaki tareda kai hannu yadauki wayar cikeda mamaki yakira sunan mum afili.

Faduwa gabanta yayi takallesa da sauri tareda kallon wayar zai dauka tayi saurin riqe wayar..

Kallon mamaki yasakar mata ta saki wayar cikin fargaba tace,

Umm me zai hana kabari idan kafito wanka saika kirata...

Wani kallon yakuma sakar mata cikeda mamaki ganin yanda take maganar hanakalinta ba kwance ba ga kamar rashin gskia atareda ita,.

Murmushin qarfin hali tasakar masa ganin kamar yana mata kallon tuhuma ta miqe tsaye tareda fuskantarsa da kyau gabanta na faduwa hannuwanta na dan rawa cikin rawar murya tace,

Mum ba yanda kake tunaninta.takeba,,

Wani kallon yasake jifanta dashi batareda yama fahimci meta fadaba.

Durqusawa tayi tareda riqo dukkanin hannuwansa biyu tana kallon fuskarsa tace,

Mum asee da kamal rayuwarka da dukiyarka suke hari....

Zame hannuwansa yayi tareda miqewa tsaye yana mata wani wawan kallo,

Tashi tayi da sauri tareda sake kamo hannuwansa ya janye tareda kallonta da kyau fuska ba wasa yace,

Karna sakejin zance mai kama da wannan abakinki...

Sake ringin wayarsa tayi ya dauka cikin 'dacin zuciya sbd zancenta na neman dagula lissafinsa wannan zance kai tsaye haka ba wani abu..

Daga wayar yayi kafin yayi magana mum tace ga kamal nan zata aiko da saqon takardun yanxu takeson yasa hannu yabayar.

Kashe wayar yayi tareda zura jallabiya yafito palo daidai kamal na knocking  ya bude fuska a daure.

Zama kamal din yayi a daya daga kujerun palon cikin ladabi ya gaidasa kamar da gske
Shikuma bedroom takardu yakoma kai tsaye da file din riqe a hannunsa
yana shiga ya aje file din a gado ya nufi toilet
Tayi saurin shan gabansa cikin qoqarin son fahimtar dashi tace,

Dan allah ka tsaya kafahimci abinda nakeson kasani nasan komai na abinda yake faruwa.....

Daga mata hannu yayi tareda rabata ya wuce toilet..

Dafe goshi tayi hankalinta na tsananta tashi abinda tai gudu kenan tun farko ba lallaine saheeb dama ya yarda kai tsayeba idan tafada masa..

File din takalla taga shine wanda tagani a mota batareda tasake dubawaba ta fice da sauri zuwa bedroom  dinta ko kamal dake zaune palo bata luradashiba ta dauko waincan takardun da sauri tadawo room din ta cire waincan tasaka nata kenan yana fitowa daga toilet

Ya tsaya cak yana kallon takardun hannunta dan tabbas yaga canje ne tayi.

Ganin yana kallon hannuwnta cikieda tuhuma da zargi hakama tuni tafara hango canji a fuskarsa ta hadiye yawu cikin dakewa tace,

Abinda nakeson fahimtarda kaine ka kasa fahimta shiyasa bazan bariba acutatarda kai..

File din ta dauko tareda biro ta miqa masa tace,

Gashi kasa hannu tukuna sainayi ma bayani.

File din datake miqo masa yabi da kallo takardar dake sama yakalla abinda yagani yasashi karbar file din idanuwansa na kadawa lokaci daya hannuwansa har wani rawa suke sbd kishi da baqin ciki..

Ganin halinda yashigane yasata karbar takardun dan sake dubawa
Idanuwanta sukai mata mugun gani sbd takardune na transfarring komai na dukiyarsa da kadarorinsa zuwaga danta abdulshakur salis danja.

Kallonsa tayi cikin sauri tana girgiza kai idanuwanta na cikowa da hawaye arikice murya na rawa tace,

Meye wannan..ban fahimci mai suke nufiba,
Wlh takardune suka kawo dan mallake dukiya da kadarorinka,
Mum ta aiko dasu ne dan kasaka hannu da gaggawa....

Wuceta yayi cikin wani irin yanayi ya saka doguwar riga tareda ficewa dakin yanayinsa na qara canxawa.

Hijab ta zura da sauri tabiyosa duk inda hankalinta yake yayi mumman tashi..
Cak ta tsaya ganin kamal tsaye a palon tai saurin shan gaban saheeb hawaye na ciko idanuwanta tace,

Wlh wainnan mutanen basa qaunarka dukitarka sukeso
Mum asee bata taba qaunarkaba
Sun aikata laifuka da dama dan ganin sun cimma burinsu,
sune suka kashe......

Saukar Wani gigitaccen mari yasa zancenta katsewa
Ta dago a rikice idanuwanta suka sauka kan mum asee,

Juyowa tayi ta kalli saheeb taga idanuwansa sun qara canzawa sbd halinda yake ciki data kasa tantance kona yarda da itane kina akasin hakan.

Cikin sanyi da nuna zallar baqin ciki mum asee ta kalleta tace,

Tuntuni nasan badan allah kike zaune damu ba sbd alamomi da dama sun nuna kwadayinki da budewar idanuwanki kan dukiya,

Kin gama yaudarar kamal yayita dawainiya dake da shegen danki duk baki tsayaba idanuwanki nakan dukiyar saida kikayiwa saheeb qazafi abbansu yasa ya aure sannan yanxu kice mune muke bin dukiyarsa...

Wani banxan kallo anano ta watsa mata cikin takaici da baqin ciki tace,

Qaunarsa kike amma shine kikeson mallake dukiyarsa da kadarorinsa,

Takardun hannunta ta daga tareda miqa masa cikin son ya yarda da ita tace,
ka duba kagani takardune na mallake dukiyarka shiyasa sukeson sa hannunka..

Kamar wani wawa ya miqa hannu ya karbi takardun yana karantawa yaga takardune na komawa makarantar kamal qasar germany sukeson yasa hannu.

Kuka mum tasaki ahankali tace,

Saheeb kaine dan dana fifita fiyeda dan dana haifa,
na qaunaceka fiyeda komai,
Takardun komawa makarantane na kamal shine kanaji matarda bayan dukiyarka ba abinda take hari take ikirarin nason mallake dukiyarkane...

Zaro idanuwa anano tayi hankinta na qara tashi ta fuxgo takardun daga hannunsa ta duba jikinta na rawa taga tabbas na makarantane suka kawo ba wainda ta tsammataba,,

Wainda zayyan yakawo mata ta duba taga na mallakar dukiyane zuwaga abduk dinta
Badai zayyan haintarta yayi yabata su sbd sakata cikin.

Mum ta nufa jikinta na rawa cikin baqin ciki tace,

Mum kinsan nasan me canxa wainnan takardun suke nufi sbd saheeb yasan bazan taba kwashe dukiyarsa nabawa abdul ba,

Saheeb wlh mum itace ta kashesu abba...

Wata gigitacciyar tsawa kamal ya daka mata tana juyowa afusace tasakar masa wasu lafuyayyun marika guda biyu ajere
Sbd idsnuwanta sungama rufewa da bacin rai da baqin ciki.

Juyowa tayi gurinsa ta riqosa tana jijjigawa tace,

Saheeb please ka yarda dani wlh bansan da wainnan takardunba daaka saka sunan abdul.

Rintse idanuwansa yayi sbd sunan abdul dinma datake kira qara qona ransa yake sbd shi gabaki daya takasa fahimtar inda zancensu ya dosa abu daya ya fahimta shine takardun dayaga ta canxa sune na mayarda dukuyarsa ga danta,,
To sauran maganganun kuwa sun masifar daure kansa..

Mum asee kuwa kuka tasaki sbd ganin saheeb din na Na wasi wasi bakuma hakan takesoba so rake yadau mataki mai zafi nan.

Riqosa tasake matsowa tayi yayi baya tareda watsa mata wani mummunan kallo ya nufi bedroom  dinsa kansa na mugun sarawa,

Zubewa tayi qasa hawaye na balle mata sbd bata tsammaci hakaba.

Cikin tashin hankali da takaici suma suka kalleta sbd basu tsammmaci duk abin zai birkice musu hakaba dan basu tsammaci zata iya fadar abubuwanda tafadaba.

Cikin tashin hankali suka fice sbd sunsan sarai saheeb zai dasawa maganar ayar tambaya.

Suna fita tasaki kukan datake dannewa
Saidatai mai isarta ta miqe ta nufi daki tadauki wayarta jiki na rawa danna kiran zayyan sbd bazata iya kwana batareda takirasaba taji dalilin qulla mata wannan cutar.




Vote
Comment
Share
*_EZNAH_*🌹
_wattpad@mamugee_



_karku damu da typing error banyi editing ba_..



*43*
Qoqarin kiransa take kukanta na qaruwa amma wayarsa takasa Shiva saima akashe take jinta tai wurgi DA wayar tareda zubewa qasa kukanta na fita ahankali zuciyarta na tsananta quna DA karyewa,

Tunda take kallon alamarin bats tabs tunanin zai juye hakaba amma saheeb yakasa tsayawa ya fahimci bayaninta DA inda zancen ya dosa.

Washe gari Kida gari ya waye ta fito palo KO gani sosai batayi sbd kumburin idanunwanta data kwana tana kuka..

Zama tayi palon jiran fitowarsa amma shiru har kusan awa ko motsinsa batajiba ta miqe ta nufi bedroom din tabude tashiga.

Duddubwa tai had toilet bayanan ta fito harabar gidan taga motarsa daya batanan kenan fita yayi.

Dafe goshinta tayi xuciyarta na qara karyewa sabbin hawaye suka gangaro Mata ta share tareda kallon part din mum ta nufa cikin zafi DA qunar rai.
Har zata shiga ta tsaya bakin qofa tareda kunna video recording tariqe wayar ahannu tashiga.

Cikin saa azaune ta tarar DA dukkaninsu apalon fuskokinsu ba walwala Dan kuwa ba qaramin ruwa ananon ta ballo musuba data Fa  a tona asirinsu duk DA basusan a wane ma'auni saheeb yadauki zancenba amma hankalinsu baa kwance yakeba Sam shiyasa tadau alqawarin yau din sai anano tabar gidan kafin ta jawo musu wani balain dayafi wannan asirinsu ya tonu.

Cikin qasqanci take kalll8 ,su tana qoqarin ware idanunwanta dasuka qanqance sbd kuka zatayi magana mum ta tareta DA cewa,

Karkiyi saurin cewa komai Dan gwara kije ki hada kayanki Dan wannan alqawarine na daukar miki bazaki kwana agidannan yauba sai qauye gidan tsoho..

Idan wannan shine alqawarinki
Ninayi miki alqawari ayau kafin natafi ko bayan natafi din saina bankade duk wani mugun sirrinku dake 6oye..

Murmushi mum din tasaki tareda tasiwa ta tsaya gavanta tace

Yaro man kaza,
Kinyi kuskuren wasa Dani tun farko sbd bakisan da balain dakike wasa ba,

Nuratu tasanardani zuwan DA zayyan keyi gurinki da wasu daga cikin maganganun dataji kunayi.,

Naso nayi amfani DA hakan gurin saheeb dan yakalli alamarin kamar nacin amana amma sainaga Bari nayi muku yanda zakufi ganewa,

Tabbas munyo takardun mallakar kadarori DA dukiyar saheeb saidai tunda wancan mai qwaqwalwar kifin yacemin kunyi Karo sun zube agabanki nasan wlh saikinyi zargin wani Abu kuma saikinyi bibiyarsu yasa nuratu tasaka ido sosai akanki tagano kinanan kina bibiyar kamal Dan ganosu
Shiyasa mukabar motarsa abude
Kuma abinda muka hasasa yafaru Dan kuwa kingani kinkira zayyan agaban idanuwanmu yazo yakawo miki wasu
Nuratu itace ta xanza wainda yakawo miki tasa wainda saheeb yagani
Mukuma kina tunanin zamukai na mallake dukiya saimuka canza namu zuwa na makarantar kamal.

Anano so DA Dama kina qoqarin ganin kin kare saheeb Wanda bazaki iya hakanba tunda bazai taba yarda dakeba kamar yanda ya yarda Dani,

Yes nice na kashe mamarsa,
Nasa su kamal yasa su bullet suka kashe mana matarsa
And kamal shine sanadin mutuwar abbansu but anaki daqiqin tunanin kina zaton idan kinfada masa Kai tsayene zai yarda?
Zance fa ake na kisa amma kina fada Kai tsaye kamar zancen tadi kuma kiyi tunanin ya yarda Kai tsaye..hmm anano kinyi kuskure babba.

Dafe kujera tayi sbd jiri dayaso dibarta jin nuratu ce take musu aiki tana munafuntarta aboye,
Tagode Allah dayasa network yaqi Bari tasamu zayyan ajiya DA yanxu ta zargesa tagaya masa maganganu marasa dadi da komai ya ida lalace Mata kenan.

Dagowa tayi idanuwanta jajir da tsananin bacin ran datake ciki tace

Tabbas nayi kuskure babba Dana yarda da nuratu hakama nayi kuskure babba danayiwa saheeb zance bada shaidaba amma zancena nagaba dashi inada qwaqwaran shaidata cikakkiya.,

Kinsan menene idanma saheeb ya yarda dhe dukiyarsa zanyi nabawa Dana wannan ba laifi bane sbd Abdul din dansane,
Koyaushe kuna kiran yarona shege
Ina tabbatarda banice nafara abin kunyaba sbd alamu da yawa sun nuna kamal shine asalin Wanda yadace da sunan Dan 'da na halak bazai aikata abinda yayiba kenan kafin ni mum kema kinbawa bariki Dama..

Afusace kamal da zuciya tagama cinyesa ya daga hannu ta watso masa wani mugun kallo sbd idanuwanta sun gama rufewa da masifa da baqin ciki dake cinta tace,

Karka kuskura kafara Dan yau ko mahaifiyarka wannan hurumin yayi mata yawa,

Cikin qunar zuciya mum tace,

Dukkanin alamadai yanxu gashinan kin bayyana kanki,
Dama na Dade da zargi tareda wasi wasin kinada saka hannu a kisar nafeesat sbd KO jabiru cewa yayi cikin wainda suka wurgo gawarta bakin gate mace ce agaba kenan kece kika kasheta kika sace abinda ta Haifa kika kawo kanki gidan gashi yanxu kinfadi gskia cewa danki Dan saheeb ne duk wannan sbd kwadayin dukiya harki raba uwa da danta,
Ki raba mace da rayuwarta wannan ba aikinki ne kekadaiba dole dasa hannun tsoho......

Hannu ta daga cikin rufewar idanu da tsananin bacin rai na sunan baffa data sako zata sakar Mata wani wulaqantaccen Mari taji anriqe hannunta
Ta juyo a fusace sukai ido biyu da saheeb.

Qwace hannunta tayi sbd masifar dake cinta Dan ranta yariga yagama 6aci t bude baki zatai magana ya daga Mata hannu ransa amatuqar bace fuskarnan ba kyan gani.

Gyara tsayuwa mum tayi zuciyarta fes sbd tun lokacinda tace Abdul dansane yashigo tana lure dashi shiyasa ta canxa akalar zancen amma matuqa da girgixa da Marin da ananon tai niyar sauke Mata tabbas yarinyar Nada zuciya.

Kuka tasaki ahankali tareda durqushewa tana fadin yau itace matar 'danta zata Mara Dan tasan ba itace ta haifesaba..

Rungumeta yakurah tayi tana lallashi itama tana hawayen munafurci.

Damqar hannunta yayi ya fito da ita bai tsaya koinaba sai tsakiyar palonsu da ita ya wurgar cikin quna da karyewar zuciya ya bude baki zaiyi magana ta katsesa sbd tasan gida zaice taje,

Karkayi saurin yanke hukunci da abinda idanuwanka suka gani da ji batareda kaji yanda zancen yakeba tun farko,

Wayarta ta daga tareda Fara nemo daukar datayi ta miqo masa wayar ya daka Mata wata irin tsawa tareda wucewa bedroom dinsa Dan kuwa duk wani burin samun farin cikinsa da soyayyarsa ya karye...

Bayason wainnan abubuwan dasuke faruwa dole yana buqatar sanin komaiyanda yake saidai tashin hankalinsu yaqi Bari gashi zayyan na Lagos gurin saka ranar aurensa da akayi da nabeela.

Dole zai tura anano gida kafin zayyan yadawo baisan zancen wa zai daukaba and sam yakasa gane inda zantukan nasu suka dosa yana buqatar Wanda zai zauna yayi masa bayani yanda zai gane.

Kasa danne kukanta tayi da baqin cijinta tayi zafi bibbiyu kenan tayi Dana sanin cewa Abdul dansabe duk da basu San gskiyace tafadaba amma sun juya zancen kanta.

Maganar Samuel taji tana dagowa tagansa bakin qofa cikin ladabi ya gaidata yace oga yace za'a kaita gida.

Rintse idanuwanta tayi hawayen ciki sabbi suka gangaro ta tashi tashige bedroom ta hada kayanta Dana Abdul cikin akwati biyu tana share hawaye.

Handbag dinta da dauka tafito Samuel din yakarbi akwatinan yayi waje dasu

Gurinsu Gwaggo tanufa idanuwa suntum Allah yasa sunyi wanka harsun karya suna zaune,

Kallo daya Gwaggo tayi Mata ta miqe tana tambayarta lafiya tasaki wani sabon kuka hartana shaqewa.

Gwaggo na ganin haka tayi hanyar fita tai saurin riqota cikin dasashiyar murya tace,

Gwaggo karkije gurinsa yanxu ransa amatuqar bace yake kibari idan ya huce yanxu ni gida zanje tareda Abdul.

Cikin jimami Gwaggo tace,

Gida zaki KO gida zamu,
Bari ba hada kayana na tashi.

Cikin qanqanin lokaci suka dau hanya nan tafadawa Gwaggo takardun dukiyarsa yabata ta 6atar sbd batason zancen yafita yanxu ba'akai matsayaba.

Ba qaramin tashin hankali da damuwa su baffa suka shiga jin abinda Gwaggo tafada baffa ya Dora Mata da fada sosai ganin yanda take kuka ba qaqqautawa yasa suka saurara Mata.

Da dare kodata nemi wayarta bata gantaba sai lokacin ta tuna tabarta apalo lokacinda yayi Mata tsawa ta fadi.

Videon data dauka ta tuna saikuma ta tuna da baida amfani tunda saheeb din bai yarda da itaba ya korota su mum ya zaba ya yarda dasu Wanda hakan yayi Mata zafi matuqa ya daki zuciyarta fiyeda yanda take tsammani.

Da zazzabi ta kwana sbd kukan dataita dirza tun jiya har yinin yau.

Koda gari ya Waye sosai su baffa sukaji tausayinta sbd har lokacin takasa daina hawaye ga zazzabi mai zafi atareda ita nan aka Fara lalla6ata gashi atunaninsu tanada juna biyu.

Kwananta biyu agida duk tayi wani irin anyi KO abinci bataci sosai su Gwaggo sunyi sunyi sun kasa Dole suka qyaleta.

Ranar data tafi aranar yabar garin shima ya wuce Australia sbd sosai yakejin zuciyarsa da qurjinsa na ciwo baisan yazaiyiba baida ko Wanda zai masa sannu su mum hakanan yakejin KO fuskar daya daga cikinsu baison gani.

Zayyan baidawoba sai bayan kwana biyar da faruwar alamarin.
Samuel yasanardashi anano na gida hakama oga baya qasar.

Tunda safe washe gari Yakama hany  qauyen zuciyarsa ba dadi sbd baisan abinda yafaruba.

Koda ya isa su aliyu ya tarar a qofar gidan cikeda sakewar fuska suka tarbesa nan suka shiga ciki dashi.

Gwaggo na ganinsa tasaki fuska tana masa sannu da zuwa Abdul dake kan qafafun anano tana basa madarar shanu yatashi da gudu yayi gurinsa sbd yasaba sosai dashi.

Cikin sanyi ta gaidasa ya amsa yana gaida Inna data fito daki lullube da qaton mayafi.

Furar sabuwar madara aka kawo masa yasaki jiki sosai yasha suna fira dasu Yusuf dasu Gwaggo har baffa yadawo nan suka gaisa shima aka kawo masa furar suna cigaba da firar.

Saida sukayo sallar la'asar yasanarda baffa anano yazo dauka sbd makaranta suna gab da Fara jarabawa.

Da farko baffa baiso bariba yaso ace saheeb din ya sauka takoma gabaki daya amma sbd jarabawar da zayyan din ya nace saiya yarda ta zauna gidansu nabeela shidima saida Gwaggo tasa baki tace tasan nabeelar sosai.

Gab da magriba suka baro qauyen suka Kama hanya.

Cikin kulawa ya tambayeta nan tazayyano masa abinda yafaru alamarin ya juye.

Recording din datayi ya tambaya tace tabaro can.

Shiru yayi cikin mummunan yanayi Dan bai tsammaci hakaba kwata kwata gashi duka wayoyin saheeb din ba'a samu amma tunda anyi haka ai komai azo qarshe sbd yatabbadarda itama mum din tanacan hankalinta ta tashe sbd dole komai yafara fitowa saheeb kuwa yasan dole next week zai dawo sbd aurensa dazaai next week din.

Tunda tadawo gidansu nabeela damuwarta tadan rage sbd kullum bata zama tana school idan tadawo kuma shiri suke sbd bikin yagabato sosai Dan Lagos za'a wuce can za'ayi bikin adauko amarya adawo da ita,
Tun bata Saba da zama gidanba harta Fara sabawa saidai haryanxu saheeb da abinda yamata na maqale cikin ranta ga wata irin fitinanniyar kewarsa dake damunta.

Dinkuna sukai sosai na manyan laces marasa nauyi ta bangare daya kuma anata shirya amarya kusan komai tareda ita mummy kesawa ayi
Shiyasa nan take suka canza musamman ma ita dayake farace sosai tafi nabeelar haske.

Ana gobe zasu wuce Lagos akai musu qunshi da komai
Suna isa Lagos aka Fara sha'anin biki Kai tsaye.

Tunda sukazo garin tafara ja baya tana nonneqewa sbd jikinta na bata KO saheeb bai isoba yana gab da isowa garin.

Kusan satinsu uku kenan da rabuwa tasan har lokaci bai isa buqatar dawowarta ba qilama rabuwar kenan.

Yau Daren daurin aure kuma aranar ake dinner
Batai niyar zuwaba shiyasa tayi wankanta ta kwanta.

Nabeela nafitowa wanka taga sauran friends dinta duka suna next room ana musu kwalliya ita kadaice kwance
Ta qarasa gaban mirror tana goge jikinta da qaramin towel fuska a daure tana cewa,

Sometimes ba abinda ke wahalardamu Mata sai Barin damuwarmu tana fita harta sakar mana rauni.,

Nasan kina cikin damuwa amma atleast karki bari damuwarki ta fito kusamu rauni sbd mutane zasusan halinda kike ciki afterall nasan na cancanci ki danne damuwarki ta Dan wani lokaci kitayani farin cikin wannan ranar after all Wanda zaki qi zuwa dominsa haryanxu bai isoba so Idan kinason amarya taje just kwashi kanki kije kishirya.

Murmushin qarfin hali tasaki sbd zancen nabeelar ba qarshe kafin ta tashi sbd

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login