Showing 27001 words to 30000 words out of 37626 words

Chapter 10 - HALIN GIRMA By hafsat rano

29 May 2026

76

sai dai a duk abinda ya shafi Muhammad baya wasa, yana ji a ransa kar fa abinda tsohuwar matar ta sanar masa ya zama gaskiya, tsoron hakan ya hanashi gabatar da komai cikin sauri yake bin komai a hankali, ba kuma wai dan ya gasgata maganar ta dari bisa dari ba, sai dan yana ji da tsoron sharrin masu sharri, be san me suke shirya wa dan nasa ba, sai dai be gaza ba, babu dare babu rana kullum cikin nema masa kariya yake a wajen ALLAH, ko ma menene"

tabbas zai zo masa da sauki.

"***A falon Ajin ya same shi yana zaune fuskar sa kamar gonar auduga, da kansa zai je amma sai Bubun"

yace ya bari yazo kawai ya huta. Bayan ya zauna ne fadawan suka fice suka jawo musu kofar.

"""Na matsu na sanar da kai wannan albishir din, abinda muka dade muna jira ne, Muhammad dai yazo da"

"magana, har yana neman aje ayi masa tambaya!"""

"Fuskar Bubu ta fad'ad'a,farin ciki ya mamaye shi"

""" Masha ALLAH! A kanon ne kamar yadda Takawa yace?"""

""" Eh har binciken da mukayi, nan din ne in Sha Allah."""

""" Sai a sanar wa Takawa babu jira, in Sha Allah gobe duk abinda ya kamata ayi sai ayi, jibi sai aje musu da"

"magana, da tsayayyiyar rana domin Takawa ya bukaci ayi komai a cikin kankanin lokaci."""

""" Madallah...Hakan yayi."""

"Tattaunawa suka shiga yi har dare yayi sosai,kafin ya koma bangaren sa cikin jin dadin labarin auren"

Muhammad din.

"***Jifa tayi da kofin hannun ta, ya fashe a wajen gaba daya kwalbar ta wawwatsu a dakin, wani irin"

"bakin ciki take a duk lokacin da taji wani abu da ya danganci Muhammad din. Yau Itace a turakar Bubu amma tasan ba zata taba samun kansa ba, idan ma ta zafafa zai iya cewa ta bar masa dakin shiyasa ta yanke wa kanta hukuncin ko da yadawo daga wajen Aji ba zata je ba zatayi zaman ta tayi tunanin"

menene mafita a gareta.

"""Ranki ya dade, Yarima Muhammad yana waje yana neman iso."""

""" Uban me zai min!!"""

"Ta daka mata tsawa tana huci, sai kuma ta hau kokarin daidaita kanta"

""" A shigo dashi babban falo gani nan."""

Da sauri baiwar ta fice tana mamakin uwar dakin nata.

"Zaman sa yayi yana karewa falon kallo, an sabunta komai ba kamar zuwan sa na karshe ba. Murmushi ne"

"a fuskar sa, yana da yakinin bata da bukatar ganin shi, ko da gilmawar sa ne balle har ya kai ga zama a falon nata, yana sane yazo domin ya kara tabbatar da abinda ya sani tun tuni."

"A yadda ta fito, da yadda ta zauna kadai ya isheshi amsar abinda yazo nema, yana kallon yadda take"

satar kallon sa cikin kallon da yasan na tsantsar tsana ne tun da ya riga da ya dade da sanin bata kaunar sa ko daidai da minti daya ne

""" Barka da gida, mun sameku lafiya?"""

Ya fad'a da yanayin da yasan zai sake tunzura ta.

""" lafiya, ya aikin naku?"""

"""Babu dadi, na gudo ma na dawo gida cikin yan uwa!"""

"""Ka kyautawa kanka."" Tace a gajarce"

"Mikewa yayi yana zuba hannayen sa cikin aljihun sa, ya yi mata kallon cikin ido tace"

"""Bari na koma."""

"""Baka Sha ko ruwa ba."" Tace tana daga zaune"

"""Na yafe, bani da bukata."""

"Ya dage gira yana juyawa, da kallon bakin ciki tabi bayansa har ya fice daga falon, ta yarfe hannunta"

tana jin kamar ta kamo shi ta tayi ta jibgar shi har sai taga ya daina motsi.

"""Ciwon Ido, zanyi maganin ka!"" Ta furta tana tashi ta koma ciki"

"***Daga nan bangaren Ammin sa ya wuce, yana jin kansa kamar sabon ango, farin ciki yake ciki shiyasa"

"ma be wani damu da abinda ya faru ba. Dama yasan kafin ya isa ta samu labarin ko ta wajne Hajja ko Bubu, aikuwa yana shiga ta tare shi da murnar ta, ya zauna ya tankwashe kafarsa a gabanta tana jin yadda take lissafo masa abubuwan da za'a bukata na zuwa gidan su Fatiman. A farkon farko be so wani abu na sarauta ya shigo ba, amma kuma da ya tabbatar hakan ba zai yiwu ba, shiyasa yayi amfani da damar nan wajen hadawa Mama gadar zare, dalilin tafiyar ta da shine ya assasa bayan ya kira Khalil a waya ya karanta masa yadda duk yake so ayi, babu musu ya amsa kuma ya tabbatar masa da zai yi komai daidai. Dazu Kuma ya kira shi ya tabbatar masa da Maman ta iso tun wayewar gari. Da wannan ya yi"

gaba wajen aiwatar da saura shirin sa da ya tabbata zasu yi matukar girgiza kowa ba Maman kawai ba.

"Har dare sosaii yana shashen Ammin, ta hada komai abubuwan da ya tabbata zasu dace da tsarin"

"fatimar sa, shi din ma akwai tanadin da yayi mata amma ba yanzu ba, sai ranar da dubban mutane suka shaida, ya zama ita ta zama shi, a ranar zai nunawa duniya kalar gatan da take dashi a wajen sa."

"Da sassarfa ya karasa part dinsa, Kai kace wani uban aiki yayi saboda yadda yake jin sa a gajiya."

"Kwanciya kawai yayi bayan ya aika mata da cool night text message ya kashe wayar sai bacci, baccin da yake yi a duk lokacin da ya samu kansa a dakin sa na cikin gidan."

"Zai iya cewa ya jima beyi bacci me dadin na ranar ba, ko dan abinda ya faru a ranar ne? Ko Kuma dai"

"dan ance gida daban yake, dama bahaushe na cewa kowa ya bar gida... wanka ya soma yi, ya fito domin ya karya dan yasan komai na kammale a ajiye yana jiran sa. Zaman karyawa yayi, yayi dialing number dinta yana kallon plate din da ake zuba masa abinci, da hannu yayi masa alamar ya isa, ya karba ya soma ci jin bata daga ba, a yar mu'amular da yayi da ita, ya lura tana da bawa kowanne abu muhimmanci idan har shi ta saka a gaba, misali idan tana aiki takan ajiye wayar ta waje daban ta kammala aikin, haka idan tana wani muhimmi abun bata hada shi da komai har sai ta gama. Tunanin sa ne ya katse lokacin da kiranta ta ya shigo nasa. Murmushi yayi yana jan tissue ya goge bakin sa, yayi rejecting kiran sannan ya"

bi bayan yana kishingid'a a jikin lallausan tumtum din dake kusa dashi.

"Da sallamar ta, ta daga kamar ko wanne lokaci, ya amsa mata shima kafin ta dora da gaisuwa"

"""Ina kwana?"""

"""Lafiya lou, kin tashi lafiya?"""

"""Lafiya lou, yasu Ammi? Ka same su lafiya?"""

"""Kalou kowa, ya sister Maryam da jiki?"""

"""Gata ta samu sauki, inaga ma na tafi gida tunda naga ta warke sosai. """

""" A ah kiyi zaman ki! "" Yace da sauri"

""" Me yasa? """

""" Amm kin gane, kinga tana bukatar ki, ki dan kara mata ko da kwana biyu ko uku ne, zata ji dadi. """

""" Owk tam. """

""" Yawwa. """

""" Ina kika shiga dazu na kira no answer, kitchen? Ko shara? """

""" Ya ka sani? Ina kitchen. """

""" Na sanki ai, nasan bakya wuce wuraren nan biyu. """

""" Lallai, kasan abubuwa da yawa akaina, amma ni bansan komai ba. """

""" Zaki sani, karki damu zaki sani fiye da sanin da kowa ma yayi min. ""."

"Ya karashe maganar cikin sigar tsokana, bata ce komai ba, yasan kuma ba zata ce din ba, shima ba dan"

tace wani abu yayi maganar ba

"""Zan zauna takanas, kiyi min duk tambayoyin da zaki yi min, zan amsa, amma kafin lokacin ina so ki san,"

"nifa soja ne!"""

"""Soja!"" Tace gabanta na faduwa sosai, bata son aikin soja ko miskala zarratin, bata kuma taba tunanin"

"auren soja ba, dan tasan yadda suke very busy da aikin su"

"""Eh ni soja ne, amma fa irin kurtun nan."""

"""Soja dai ai duk soja ne, sunan daya ne."""

"""Amma rank din daban daban ba."""

"""Uhummm. "" Ta ja ajiyar zuciya, ya sammace ta, kenan dai zaman kadaici be rabu da ita ba, dan sojoji"

"basu da lokacin kansu balle na matan su, yanzu ita kenan..."

""" Karki damu, ba zan dinga nisa ba kinji? Zan zama ko yaushe kika bukace ni Ina kusa, nayi miki alkawari."""

"""Allah yasa, dan da gaske bana son aikin soja wallahi."""

"""Saboda me? Aikin taimakawa kasa ne fa, aikin lada ne idan har ka yi yadda ya dace."""

"""Na sani, ni kawai bana so ne, basu da time din kansu ballanta na ..."""

"""Na matan su? Haka ko yaushe aka cewa dama, toh ni dai Ina da time dina Ina kuma da na matata, har"

"sai kin gaji kin koreni daga gidan ma wataran."""

"""Shikenan."""

"""Zaki gani ai, ki zuba ido."""

Shigowar Ya Maryam ya sakata yin shiru

"""Ki fito falo ya tafi wallahi, ni kadai kamar mayya."" Tace mata tana rik'e kofar, tun dazu tace tazo falo"

"taki sboda maigidan yana nan, shiyasa Maryam din tazo kiranta da ya tafi, ko yar hira sa yi"

"""Kice ina gaishe ta, ya jikin nata."""

"""Da sauki."" Tace tana janye wayar daga kunnenta."

"""Ashe waya kike shine kika yi luf, toh ki gaishe shi, in kin gama Ina jiran ki."""

Ta fita ta ja mata kofar

"""Bari na barki kuyi hirar ku, zan sake kira anjima."""

"Kamar ta tambaye shi maganar zuwa gidan amma ba zata taba iyawa ba, sallama tayi masa ta ajiye"

wayar ta fita wajen Maryam.

"Yana sane sarai yake ce mata komai, baya so tasan komai sai anyi komai ya kammala, ba zai ma gaya"

"mata zuwan nasu ba, Abba kawai zai wa text ya sanar masa, idan yaso sai ya turo Musaddik ya sameshi ya sake fad'a masa Incase ko be ga message din ba. Haka kuwa akayi, yana masa text din ya gani, yayi saurin kiran kowa ya sanar dasu zuwan bakin, anan suka fara tunanin abinda ya kamata suyi, baki daga irin wannan babban gidan dole ne ayi abinda za'a fita kunya. Sun dade suna shawarwarin su kafin su"

"tsaida matsaya, nan da nan suka shiga shirin tarbar su cikin tsarin da suka san ba zai zama wani iri ba."

"Abba na zaune kiran Mama ya shigo wayar sa, shi kadai ne a gidan sai Habib ta tafi da Zeenat da Marwan,"

"shiru gidan babu kowa kallon tv yake a zahiri amma a badini tunanin masu zuwa neman auren Iman yake a gobe, yaso ya sanar wa mahaifiyar ta zuwan nasu da komai akan maganar sai dai baya samun ta a waya wajen kwana uku kenan, yasan tana business sosai kamar ma tana fita kasashe saro kayayyaki"

shiyasa yayi tunanin ko kila bata k'asar ne.

"Kallon wayar tasa yayi, har lokacin haushin Maman yake ji musamman abubuwan da ya gano akan irin"

"rikon da tayiwa Fatiman tsawon lokaci be gane komai ba, har Marwan ya titse ya tambaya ya kuma gaya masa komai abinda ya sake daga masa hankali sosai kenan. Kiran ne ya sake shigowa ya daga ba dan yaso ba, dan dai kawai be san ko wani abu bane emergency ya taso, sallama tayi ya amsa ciki ciki. Dama"

tasan za'a rina shiyasa kawai ta tafi kai tsaye akan dalilin kiran

"""Dama Zeenat ce ta ce na sanar da kai iyayen Bashir zasu zo gobe idan Allah ya kaimu."""

"""Su bari jibi gobe Yaya yana da abinda zai yi."""

Yace mata kai tsaye

"""Amma da ka barsu sunzo goben ba dole sai wajen Yayan ba ai."""

"""Haka tsarin mu yake tun farko, babu Kuma dalilin da zai saka na chanja yanzu dan anzo auren nawa"

"yayan, idan har ba zasu iya bari sai jibin ba sai ki nema musu wanda zasu gani a goben."""

"""Abin be kai haka ba ai, Allah ya kaimu jibin."""

"""Amin."""

"Yace ya katse kiran yana Jan tsaki, wato duk dadewar ka da mace ba zaka taba sanin wasu daga cikin"

"halayen ta ba har sai abu ya faru, lallai. Shi kadai yake ta wannan tunanin har lokacin da zai kwanta yayi, ya kwanta da addu'ar Allah yasa komai ya tafi dai-dai goben."

"***Duk cikin su babu wanda ya makara, suka tashi aka hau gaggayara gidan harabar da lungu da sako su"

"Habib suka taimaka aka tsaftace ko ina, dama dai a gyara yake saboda takanas aka dauki me aikin kula da wajen amma duk da haka idan suka tuna bakin da zasu zo sai suga ya kamata a sake gyara ko ina."

"Wajajen sha biyu cikin jagorancin Musaddik suka iso, cikin manya manyan motocin alfarma da aka"

rubuta Emir Kano 1 guda biyu sai guda biyu dauke da tambarin Adamawa Palace.

"Cikin kankanin lokaci unguwa ta dauka, mutane suka dinga lekowa daga gidajen su dan tabbatar da"

"abinda yaran su suka je suka fad'a musu, kowa ya leko sai ya rik'e baki cikin tunanin abinda ya kawo irin mutanen gidan."

"Cikin matuakr girmamawa Abba suka karbe su, sai dai sunyi tunanin zasu gansu a matsayin mutanne"

"da basu kai ba ko kuma level dinsu ba daya ba, amma sai suka ga akasin haka, cikin girmamawa, karamcin da dattako suka zo musu, suka nuna Halin Girma, halin babban gida babu fariya ko nuna su din wasu ne, cikin tattautasa harshe da girmamawa suka nemarwa dan su kuma jikansu Muhammad auren Fatima. A take Abba yace an bashi. Su kuma nan take suka gabatar da ranar da suke so a saka, babu musu nan ma Abba ya amince suka tsaida wata daya kachal, shi din ma saboda Muhammad din ne ya"

"bukaci haka, amma idan sune toh sati biyu zasu saka."

"Babu wani bata lokaci abinka da manyan mutane, masu Halin Girma, suka yi komai cikin sauki sannan"

"da zasu tafi suka gabatar da kyaututtuka daga iyaye da kakannin Muhammad din da yake cikin al'adarsu idan za'a zo neman auren. Tarin kayan da suka kasance mota guda sai da suka bawa su Abba mamaki, a gefen Abba aka ajiye mukullin motar nufin su har da motar da duk abinda yake ciki kyauta ce ga sirikar"

"Sarki Ahmad Santuraki, da iyalan gidan sa kafin zuwan ta, sannan suka yi musu sallama suka tafi."

#HafsatRano

#ZafafaBiyar2021

Not edited

Ignore typos

"Masu sharing sannun ku da kokari kunji? Allah ya shirye ku idan masu shiryuwa ne, idan kuma ba masu"

shiryuwa bane toh... Kun san sauran dai

"[1/13, 4:25 AM] +234 803 765 3189: Halin Girma"

13

"*Zafafa biyar na kudi ne, idan kina so ki karanta ki tuntubi 08184017082 or 09134848107*"

I'm on Instagram as @zafafabiyar5. Install the app to follow my photos and videos.

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=1ft46u5twk6r3&utm_content=nj79azb

"***Sai da suka ga tafiyar su sannan suka dawo ciki, kowa da abinda yake cin sa a zuciya. Tabbas sun"

"amsa sunan babban gida, haka sun nuna Halin Girma da dattako na irin manyan mutane da suka san mutunci da yakana."

"Fadar irin tarin kayan da suka zo dashi ba abu bane me sauki, hakan ya dan tarsa tsoro a zuciyar Abba,"

"yake jin tamkar siyar da Iman din zai yi, wannan uban dukiya a matsayin tambaya, ina ga idan aka zo auren? Basu da talaucin da arziki zai tsorata su, sai dai dole ne suyi mamaki ganin uban dukiyar da aka lafto da sunan na Iman din ne, tun daga kan sutura zuwa kayan kawa na mata, da kyautata gwala-gwalai"

tamkar ba'a san darajar su ba.

Haduwa suka yi suka tattauna yadda zasu adana komai saboda yadda rayuwar yanzu ta zama ta rashin

"tssro, shawarar farko shine su bar maganar tsakanin su domin mata akwai sakin baki musamamn idan abun da ya sha musu tunani ne, yanzu zasu yi ta kwazozotan sa har wasu dake waje su samu damar"

aiwatar da mummunan kuduri akan su.

Tabbas shawarar tayi dan da gaske komai na iya faruwa idan maganar ta fantsama shiyasa kawai a take

aka fita da motar da duk abinda yake ciki daga gidan zuwa in da zai fi zama safe kafin bikin yazo kusa

"sosai sai ayi abinda ya dace dasu, ko bata kayanta ta tafi dasu tunda dama su chan babu wani tsoron"

"rashin tsaro ta ko ina zagaye suke da Jami'an tsaro. Karshen magana kuma ma shi Muhammad din kansa, su ne tsaron ma baki daya. Da wannan shawarar suka tashi bayan Abba ya sanar musu da zuwan iyayen"

Bashir a gobe kamar yadda Mama ta shaida masa.

"Sake gwada kiran Maman Iman din yayi bayan ya koma gida, cikin sa'a kuwa kiran ya shiga, bata wani"

"jima tana ringing ba ta dauka a nutse cikin sallamar ta da muryar da yake jin ta kullum a bakin Iman din, maganar da sak ta mahaifiyar ta, hatta nutsuwar ta irin ta uwarta ce shiyasa yake jin ba zai iya mantawa da ita ba ko da shekaru sun ja, duk da yanzu babu batun soyayya a tsakanin su tun da be riga yasan matsayar da take a yanzun ba ko da aure ko babu, a dai kwanakin baya ya samu labarin tayi aure har da"

albarka Yaya a tsakanin su.

"""Ina wuni Abban Iman?"" Ta gaishe shi jin yayi shiru bayan amsa sallamar ta"

"""Lafiya Lou Maimunatu, ya gida ya kowa da kowa?"""

"""Kowa lafiya Alhamdulillah, Iman fa?"""

"""Tana nan lafiya."""

"Shiru sukayi baki daya, kowa da kalar tunanin sa a ransa, shine ya katse shirun ta hanyar cewa"

""" Inaso zan kawo miki ita kamar yadda nayi miki alkawari idan auren ta ya tashi, ta samu miji har an"

"tsaida rana wata daya, in sha Allah a tsawon wata dayan nan zata zauna a wajenki, a matsayin ki na mahaifiyar ta sai kiyi duk abinda ya dace, kiyi hakuri da Kaddara, kiyi hakuri!"""

"Wani irin yar taji har cikin kanta, Iman dinta har ta girman da zata yi aure, rayuwa na gudu sosai, tana"

"tuna lokacin da ta dawo masa da ita, da irin tashin hankalin da ta shiga a rashin ta wanda bata taba tunanin zata dawo daidai ta cigaba da rayuwa ba, a lokacin tunani take rayuwarta ta kare gaba daya, amma kuma sai gashi ta cigaba da rayuwa duk da babu ranar da zata fito ta fadi bata tuna yar tata ba,"

amma ya zatayi? Mutane na fifita al'ada akan addini. Ta sani sarai uwa ce taka da ikon rik'e yarta har

"zuwa aurenta, tare da sharadin kula da duk wata bukatar ta daga mahaifin ta, sai dai idan anji tsoron"

"tarbiyyar da zata samu a wajen uwar, toh amma a lokacin wa take dashi da zai tsaya mata? Bayan iyayenta da take ganin su a matsayin gatan ta sun kekashe kasa sun ki amincewar da rikon nata a wajenta? A lokacin da akwai karancin shekaru a tare da ita, amma da ace yanzu ne, babu me raba ta da yarta kuwa, duk yadda zatayi zatayi ta tabbatar da ta rik'e ta a wajen ta. Ta bata kulawa da dukkan gatan"

da take bukata.

"""Allah ya sanya alkhairi, ya nuna mana lokacin."""

"Kawai tace dan bata kuma san me zata ce masa ba, taji dadi da ma ya cika alkawarin sa,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login