Showing 9001 words to 12000 words out of 28581 words
Chapter 4 - DAN MILLIONAIRE Soyayya Ta Fi Arziki by YUSRAH MUSA ABUBAKAR
cewa zauna mana Aminu kana tsaye kamar wata bishiya".
Zama Al'ameen yai cikin hade rai yace ba suna na Aminu ba Al'ameen nake".
Hajiya dake kallonsa domin yana kama da kakansa wato mijinta tace.
"Bazance Alemin din ba da Aminu zan kira ka ya zakai ubanka Aminu ya rada maka a haka suka sha minti da goro da naman suna".
"Nidai na fada miki suna na Al'ameen"'
"To kinji hajiya ni Sadiq shi Al'ameen sai ki gyara".
"Bazan gyara ba duk wanda na kira karya amsa ".
Kallon Al'ameen tai tana cewa" Aminu ya batun aure naji har yanzu shiru"'.
"Babu ruwan ki in zanyi in bazan yiba wannan ganin dama tane".
"Karya kake sai kayi d'an kare da fari kamar...........
Sai kuma tai shiru bata karasa ba murmushi Al'ameen yai dan ya gane nufin ta yace.
"Karasa man da fari kamar wa zaki ce kuma kin manta ba d'an kare zaki ce ba saidai kice dan kwikwiyo🐩😂.
Dariya Sadiq yai yana kallon hajiya yace hajiya kinji fa saidai kice d'an kwikwiyo ba d'an kare ba".
Da sanda hajiya ta nuna shi tana cewa kai kuma kayi man shiru bansan shishshigi zuwa dangin miji da ganamasgo ka rufe min baki".
Dan zaro ido Sadiq yai ciki tsokana yace na rufe ruf🤐 hajiya me ran karfe ki shirya idan zamu koma dake zamu tafi kiga birni ki huta kiyi 'kiba".
"Ni ka rufa min asiri da zuwa birni bazan iya rayuwa acan ba".
"A haba dai hajiya me yasa"?.
"Abincin kune bazan iya ci ba gara na zauna anan naci wanda na saba dashi".
"Wanne kalar abincin ne baza ki iya ciba"?'.
Cikin tsufa hajiya tace kaga ta farko wacce na tsana andosi da kwai dinnan".
Dagowa Al'ameen yai cikin mamaki yace" me andosi kuma? abinci ne? ni ban ma sanshi ba".
Dariya sosai sadiq keyi yace hajiya kina burgeni wato indomie kike nufi itace andosi".
Hajiya tace "Eh da wannan abin me kamar tsutsa da kuke ce masa damaroni da sifagatin du bana ci ko an kawo min daga gidan muntari".
Sadiq dake rike da ciki yace lallai kam hajiya yi shiru haka ciki na ya fara ciwo makaroni da spagetti ni kuwa abinci na kenan".
"Shiyasa gaka nan kamar iska ta bushe kun 'ki al'adun hausa sam".
"To hajiya yanzu ba gani nazo ba saina cika ciki na da rama da zogale kafin na tafi"'.
"Daka kyauta Saddiqu ina iyalin taka ne Ri'kayye ko tana gida nasan da daita kuka zo da yanzu ta karaso"
Cikin mazu Sadiq yace bansan wata Rikayye ba idan mata na kike nufi sunanta Ru'kayyah".
"Ita nake nufi mana saboda bakin ciki shine ka 'ki zuwa da ita".
Batare da Al'amin ya dago ba yace hajiya meye abin bakin cikin dan kawai baizo da ita ba"?.
Hajiya data balli goro tace kai kuma kamin shiru ba dakai nake ba tuzurun banza kalleka kato dakai idan anan ne kana da 'ya'ya wajen biyar".
"Ai hajiya daina fada 'ya'ya biyar sai kace na hada dangi da kaji uku ma sun isheni shiyasa bazanyi aure da wuri ba".
"Ashsha kayi ta banza bari ai Mustaphan zaizo ya same ni zanji idan shine ma yake karanta maka kada kayi auren da wuri saiya bani amsa".
Page 17 to 18.
Basu bar gidan hajiya ba sai bayan sallar isha a kofar gida saman dakalin Al'ameen ya zauna sa'banin sadiq daya shiga cikin gida".
Yana nan a zaune Sa'adu yazo yasha wanka ya sako gwanjola irin takalmi sau ciki na roba"'.
Kallon sa Al'ameen yai tun daga kai har kafafu lokaci guda murmushi ya 'kwace masa ganin sai wani buda kafada yake".
Fati ce ta fito tana nufar inda yake tsaye wanda ko minti biyu basuyi ba Abuh ta karaso gurin da 'kawayenta tana haki tace".
"Amma Sa'adu me nace maka ba nace kada ka sake zuwa gurin Fati ba nice nake sonka ba ka amince rannan a dandali ba saboda kai mun rabu da ilya".
Shiru Sa'adu yai cikin takaici Fati tace wai dan Allah Abu meye hakan me na tare miki da bakya son gani na cikin farin ciki"?.
A gadarance Abu tace ban sani ba bani da lokacin ki kai kuma muje ".
Kamar rakumi🐪 haka Sa'adu yabi Abu zuwa dandali kamar yadda ta bukata 'kawayen Abu na yiwa Fati dariya da habaici suka bar gurin".
Wasu zafafan hawaye ne suke zuba a idanuwan Fati gashi gobe ne gasar nuna samari yanzu ita ya zatai da rayuwar ta cikin takaici ta juya zata shiga gida".
Al'ameen dake kallon ta yace " madam ji mana ".
A firgice Fati ta kalli inda yake tana goge hawayen fuskarta"
Jitai yace mene sunan ki"?.
Muryarta na rawa sakamakon kukan da take tace suna na Fatima".
"Ok yayi jeki" kawai yace yana mayar da hankalin sa kan waya wucewa tai ta shiga gida.
Cikin shishshigi da cusa kai Saude ta shiga dakin da mami suke tana cewa Aisha a karo muku abincin ne".
"A'a ya isa haka mun gode".
"To shikenan bari na kawo miki wata kyakkyawar fura ko zaki sha".
Fita tai tana daukowa ta kawo mata sannan ta musu saida safe ta fice tsaki mami taja tana rakata da harara tace ko ina ruwanta dani mayya bazan sha ba aikin banza kawai".
'Yar dariya Afeeyah tai tana gyara kwanciyar ta yayin da mami take ta maganganu da fada ita kada kadai.
"kawai an kawo mutum wannan mugun kauyen an ajiye duk zafi babu wata ni'ima ko jin dadi ba a.c haba wallahi bazai yiwu ba dole gobe na samu alhaji idan shi bazai koma gida nikam na gaji zan tafi".
Shiru kawai Afeeyah tai tana sauraron mami da mamakin furucin ta amma batai magana ba saboda gudun abinda mamin zata ce mata saidai bata jin dadin yadda take kushe 'kauyen mahaifin nata domin itama tana son garin ".
Washe gari Al'ameen bai tashi bacci da wuri ba har rana tai saida Sadiq ya tashe shi yana mikewa ya rike kansa tare da cewa.
"Subahanallahi wannan karar haka kamar zata fasa min kunne kuma daga ina me suke".
Sadiq dake shirin fita yace bazan jira kaba domin an fara wai wani biki suke na nuna samari" yana fadin haka ya fice.
Shiru Al'ameen yai kamar kuma an tsikare shi ya mike cikin gaggawa yai wanka ya shirya yana fita yaga Salamatu ta fito daga daki.
Bayan sun gaisa yace ina Zarah".
Cikin mamaki tace wace haka"?.
Tunawa yai sai kuma yace oh Fati nake nufi tana nan".
"A'a wallahi bata nan ta dade da fita ban sani ba ko tana gurin bikin wasan samarin can nasu da suke".
"Ok" yace yana fita daga gidan harya kusa zuwa yaji kid'an na hawa kansa domin makad'a ne da yawa da maroka na gari da gari suke taruwa su zo".
Juyawa yai ya fasa zuwa hango wasu gajerun bishiya masu ni'imtacciyar inuwa yasa ya nufi gurin dan yadan huta".
Yana karasawa yaji ana shashshekar kuka cikin mamaki ya soma dube dube can ya hango me kukan zaune ta kifa kanta".
Har zai rabu da ita sai kuma ya tuna duk wanda ya sharewa wani hawayen sa Allah zai share masa shima".
Tunani ya farayi to me zaice mata zuwa wani lokaci da yaga bashi da mafita yai gyaran murya".
Da sauri ta dago a razane wanda shi yana mamakin ganinta a gurin ita ma tana mamakin ganin sa".
"Kukan me kike"?.
Shine tambayar dayai mata kaita girgiza tana cewa" ina kuka ne saboda dazan aje abin fada zanyi abin kunya yau ranar fitar da gwani ne a dandali".
"Kamar ya"? Me kuke yi idan kunje"?.
Gyara zama tai tana cewa da farko idan kowa yaje me kira zai rika kiran suna mutum da budurwar shi su fita fili ya bata kyautar zobe da agwagi guda uku shikenan sai su fita wasu su shigo.
To kowa ya sheda ya gani wace nada saurayi kuma baza a kada mata kalangun tayi kwantai ba idan kuma baka da saurayi kowa saiya sani ayi ta maka dariya".
"Toke yanzu bakije ba kina nan idan aka kira sunan kifa kisa saurayin naki ya rude".
"Ni bazan je ba".
"Saboda me"?'
"Idan naje ma babu amfani wazan nuna wanda yake sona yayata Abu tamin 'kwacen sa bani da kowa".
"Zaki are ni"?.
Cikin rashin fahimta tace aron me".
Basarwa yai tare da cewa muje na ga abinda kuke yi a bikin.
Badon taso ba jikinta a sanyaye ta mike suka tafi dandalin shake yake sosai da mutane suna zuwa sai zance da yamud'id'i da munafirci ake ana ta kallon Al'ameen'.
Me shela ne ke cewa anzo gidan. Muntari na alhaji attajirin yan kauyen nan me taimako muntari gwani me 'kwazo ina babbar 'yarsa Abu ta fito mana fili da nata gwanin".
Fita Abu tai tana hura hanci yayin da Sa'adu ya fito ya tsaya a gefen ta yana cire zobe ya bata sannan ya bata agwagi guda biyar.
Lallai su Saude za a sha dafgen nama🍖.
Suna fita me hela ya sake rafka cikiya ina 'yar uwarta Fatima ta fito fili da nata gwanin itama".
Jikin Fati tai yadau rawa cikin nadama da dana sanin inama bata zo gurin ba .
Kaurewa akai da surutu kowa da abinda yake fada wasu na mata dariya wasu na tausaya mata".
Ina Fatima ne ko mu buga miki gangar bandaro me kwantai" maroki ya fada yana le'ke -le'ken inda zai hangota".
"Ehhhh kawai a kad'a mata mu cashe " guri ya kaure ehhh a buga ehhh a buga.
Al'ameen da abin ya bashi dariya shiga cikin filin yai yana murmushi yaiwa me hela magana".
"Heeee a saurara jama'a ina mewa Fatima dariya😂? To ka rufe bakin ka🤐 ina maison jin jarumin💪 Fatima? To bude kunnen ka👂 dakyau ina mai nuna Fatima da yatsa👉? To ka sauke hannunka ina me son ganin gwanin Fatima ya matso kusa ya bude idonsa 👀yai kallo inji wannan zankadedan saurayin yace shine saurayin Fatima"'
Me hela ya fada tsit guri yai kamar sun mutu kowa idonsa nakan Al'ameen wasu suce ba mutum bace aljani ne wasu suce daga ina ta samo wannan.
Fitowa filin Fati tai tana mamaki kare tan da Al'ameen yai a haka idan ka kalleshi zakai tunanin zaiyi girman kai.
Kudi masu yawa Al'ameen ya baiwa marokan da makadan wanda me hela da lasafika a susuce ganin kudin da baiyi zato ba yace.
"A saurara Fatima me 'kashin arziki ce tafi karfin kaji koda na turai ne balle agwagi masu wuni a cikin kwata😂".
"Sannan ku kalli zoben💍 daya bata na gwal ne babu wacce ta samu koda na azurfa dan haka dole yau a yabe ta itace ta cinye gasa a wannan shekarar musbahu ku bamu sauti".
Kid'a🎶 da algaitu🎺 ne ke tashi kamar gidan sarki suna kuma yabon Fati da mata kirari suna kod'ata sun samu kudi sosai a gurin Al'ameen saida ya tabbatar daya wanke Fati tas daga jin kunya".
Abuh na komawa gida taje ta fadawa Saude abinda ya faru tsaki Saude tai to saime inace ba saurayin nata bane idan ya tafi shikenan ta fito rana karki wani ma damu kanki".
Da salon munafirci Saude taje ta karancewa mami komai harda abinda ba'ai ba saida tai 'kari.
Mami kam bata juri zuga ba tuni ta cika tayi fam waya ta dauka tana danna masa kira yana dagawa tace duk inda kake kome kake kazo yanzu ina son ganin ka".
Yana zuwa ta balbale shi da masifa Al'ameen kana hauka ne? Akan me zakaje ka 'barnatar da kudin ka saboda ka kare wata banzar yarinya".
Tun kafin yai magana Afeeyah tace kai mami kamar ya banzar yarinya yar uwar sace fa kuma koba haka ba duk wanda ya taimaki wani Allah zai taimake shi".
"Ke kuma rufe min baki bake nake tambaya ba dakai nake".
"Gashinan ta fada miki mami duk wanda ya taimaki wanI Allah zai taimake shi"'.
"Hummm shiyasa kaje ka zubar da ajinka a gurin yan kauye a gaban mutane sama da kirge wai yaushe ka lalace da shashanci haka ne".
"Mami ki fahimta yarinyar nan sister nace fa yar uwa tace jinina ce da ita da Afeeyah duk daya ne".
"A wajen ka sakarai ba wacce kuke uwa daya uba daya da wacce kuka hada kakanni saboda mutuwar zuciya kace daya suke".
"Maamii gaskiya maganar sa koni Fatiman nan tana burge ni wallahi amma komai mami idan ba kece kika zabe shiba baiyi miki ba " Afeeyah ta fada da yanayin damuwa".
"Ke dalla 'kyale ni yar iyawa gwana saina fadi abinda ke raina ".
Mikewa Al'ameen yai yana cewa good night mami".
Ya fita daga murya tai yadda zai jiyota tace kowa ya kwana lafiya shi yaso" murmushi yai yana rokon Allah daya shirya masa mahaifiyar tasa.
We will meet👪 again.
See👀 you next time
Typing📲 +234 905 527 3614.
Yusrah Musa Abubakar Gimba.
Page 19 to 20.
Tun asuba Saude da Abu suke gyaran agwagin nan kamar wanda suke gyaran saniya gari na wayewa Abu takai markade aka dafe su"'.
Wani abin mamaki a fanteka aka zuba guda uku wai gidan me gari za'a kai haka suke yi biyun sune na budurwar .
Dariya sosai Afeeyah tai ita bataga abin farin ciki dan an baka wadannan agwagin ba tunda babu riba".
Kai da kafa harshi Saude ta dafe duk kayuwan ta debo a wata langar kwano me tsatsa tana kaiwa Salamatu ".
Kai Salamatu ta girgiza tana cewa" a'a alhamdulillah na gode".
" iheee bakin ciki kike ne Salamatu dan 'yarki bata samo ba kome"?.
"Eh shi nake yi".
"Aiko zaki mutu da bakin ciki domin Abu sai zaman gidan me gari su o'o kuwa bamusan inda za'a hara ba ko kuturu ko makaho waya sani".
Ta fada tana dariyar mugunta tare da daukar langar kayukan ta koma dakin ta".
Daddy na zaune tare da Muntari daren da ana gobe zasu koma Abuja muntari ke cewa'.
"Nikam yaya inaso yara na suyi ilmi sosai amma sa idon 'kauyen nan ya hanani sakat gashi ita Zainaba har ana zancen aurenta".
"Daddy yace toba tana da 'kanwa ba 'yar gidan Salamatu ko har ita za'ai auren"?.
"A'a iya zainabun ce ita har yanzu bata samu tsayayye ba tukuna dai".
"Ok mezai hana mu tafi da ita tunda kana so tai ilmi sai a sai mata makaranta".
Muntari yace da naji dadi yaya wallahi inason dana yai karatu".
"Shikenan babu damuwa ka sanar da mahaifiyarta gobe da wuri kafin mu wuce ya kamata ta sani".
"Eh zan fada mata duk da nayi shedar Salamatu bata da matsala".
Washe gari jin harda Fati zasu tafi yasa saude tace tab kace su Aisha zasu debi masifa yarinyar da kauye ma idonta a tsaye yake balle tana birni .
Nasiha sosai Salamatu taiwa Fati duk da a ranta bata son rabuwa da yarta ta kamar yadda itama Fatin bata kaunar binsu.
Da kukan ta tashiga mota suka tafi yayin da Afeeyah ke mata dariya tana cewa ayya keda dawowa sainan da shekara uku Allah sarki".
Da fati iya hawaye take jin abinda Afeeyah ke cewa yasa ta soma shashsheka".
Al'ameen dake driving Sadiq na kusa dashi ya joya yana cewa mene haka zan sa'ba miki ba jiya kika gama cewa she's our sister ba".
Murmushi Afeeyah tai tana kallon Fati tace sorry sis ita kam Fati babu bakin magana har sukaje gida".
Cikin fushi na sun taho da Fati yasa mami ta fice fuuu daga motar daddy ko kasheta baiyi ta shige cikin gida".
Afeeyah kam bedroom dinta takai Fati tana cewa sannu da zuwa gidan mu ki kwantar da hankalin ki nan tamkar gidan ku ne ki dauke ni matsayin 'kawarki".
Murmushin dole Fati tai tana cewa nagode".
"No baki da matsala Afeeyah ta fada tana shiga toilet tayo wanka da alwala sannan ta fito tana cewa fati kema kije kiyi wanka".
Shiga toilet Fati tana mamakin kyausa kamar ka kwanta a kasan tayis din sai 'kyalli yake kamar mirror.
Ganin bata ga ruwa ba ta leko tana cewa wai ina ruwan kuma banga baho ba sai wani kwale-kwale😀 ko a ciki ake wanka"?.
Dariya ce ta kama Afeeyah saida tagama shiryawa sannan taje ta kunna mata ruwan ta fito.
Sanin datai cewa bada son ran mami Fati ta biyu su ba yasa tasa kawai aka kawo musu abinci part dinta".
Kwanan Fati biyu daddy ya sai mata school ta fara zuwa itama driven ta daban .
Korar yan aikin gidan mami tai mutum uku tabar biyu cewa meye amfanin fatin idan ba bauta ba".
Tasa ta a cikin 'yan aikin batare da sanin daddy ba hakan datai ya 'kona ran Afeeyah dan haka itama take shiga kitchen din tana koyawa fati wasu abubuwa.
Ina Fatima ban ganta ba jiya da yau lafiya kuwa"?.
Kau dakai mami tai tana cewa tana kitchen ita da su nana".
Cikin mamaki daddy yace me take yi a kitchen din"?.
Rasa abinda zatace mami tai ta kama kame-kame daidai Afeeyah sun fito ita da Fatin jikin su duk a 'bace.
Daddy da ransa ya soma baci ganin yadda suka fita hayyacin su ya kalli mami cikin fushi yace".
"Aisha yanzu sune kika mayar kitcinonin ki yara nane fa amma zaki wani tura su kitchen sun zama kuku ne".
Ganin daa Afeeyah tai daddy ya damu da yawa yasa cikin son kare mamin tace.
"Lah daddy ba ita ta tura muba kasan ban iya girki ba kuma gashi kullum lokaci yana ja gidan wasu zanje shine nace bari na koya abin kunya ne ace kamar ni ban iya komai ba".
Sauke ajiyar zuciya mami tai a boye jin Afeeyan ta ceceta mikewa daddy yai yana cewa shikenan amma ku rika aikin baya baya sannan ku rika lura da wuka kada ku yanke.
"To daddy mun gode zamu kiyaye" cewar Afeeyah.
Barin gurin yai mami dake shirin tashi ita ma tace tunda kin biyewa wannan yar kauye wahala yanzu kika fara shanta ".
Kai Afeeyah ta girgiza ba tare datai magana ba shigowar Zainab kenan ko zama batai ba ta kalli Fati a 'kyamace tana cewa".
"Ke village girl dauko min abin sha a fridge sannan ki wuce kitchen ki zubo min abinci me zafi".
Wani kallon baki da hankali Afeeyah ta mata tana cewa itace zatai miki bauta aiba yar aiki bace idan bazaki nemi nana ta kawo miki ba ki barshi".
Ke na sako dake ne gada wacce nake yinan".
"Kin sako dani tunda kika ambaci yar uwata bazatai ba kinji na fada miki".
Tsawa mami ta saki tana hararar Fati tace ke dalla wuce ki mata abinda take so sa'ar kice ita".
"Maamii" Afeeyah ta fada ranta a bace.
Ke kuma zaki ci ubanki Afeeyah idan baki min shiru ba".
Barin falon Afeeyah tai yayin Fati ta wuce kitchen ta zubo mata abincin tare da dauko juice ta kawo mata .
Banza jaka yar kauye akuya" zainab ta fada tana dauko spoon.
Juyowa Fati tai tace duk sunan kine gaskiya kin more jaka akuya toga dusa nan da ruwan tsami na kawo miki saiki fama".
"Keee