Showing 27001 words to 28581 words out of 28581 words
Chapter 10 - DAN MILLIONAIRE Soyayya Ta Fi Arziki by YUSRAH MUSA ABUBAKAR
yasa ya riketa yana yin bangaren muntari baban su da ita.
Har daki yana goge mata hawayen yace "meke damunki"?.
Kaita girgiza tana cewa babu komai".
"Amma kike kuka? fada min damuwarki".
Ganin ya zauna yasa tace "ka zauna akan gadon baban mu"?.
Gira ya dage "eh madam to mene a ciki"?.
"Amma dai gadon surukin kane".
"To Zarah surukin nawa ba ubana bane"?.
"Duk da haka".
"Ok yayi to zo mu kwanta bacci nake ji".
Zaro ido tai "anan din? gaskiya a'a bazan kwana anan ba".
Juyawa tai zata fita ya dauketa yana dorata akan gadon yace "wannan daga baya kenan kwana kam sai kinyi".
Zatai magana ya rufe mata baki da nasa yana bata kiss mai d'umi wanda yasata sauke ajiyar zuciya.
Zuge zip din doguwar rigarta yana zura hannunsa ciki da sauri Fati ta kankameshi tana kwantar da kanta akan kirjinsa".
Da yake cikinta ya riga ya tsufa saita dabara yadan karkata ta ta gefe ya shigeta yana binta a hankali sakamakon yanayinta.
Page 43 to 44.
Washe gari tun kafin asuba tayi ya tasheta suka shirya anayin sallah suka wuce Abuja.
Da safe kowa yana zuba idon yaga ta inda zasu bullo amma shiru Sadiq daya shigo jin ana cewa ko suna gidan hajiya.
Yace ai yanzu kam Al'ameen yana Abuja domin gida suka tafi shida Zarah motarsa bata nan" mamaki ne ya kama kowa ganin basuyi sallama ba.
Kwana biyu da tafiyarsu daddy ma suka bi bayansu a ranar da suka koma suka tarar Fati na asibiti.
Dukka asibitin sukaje a lokacin Fati harta haihu ansamu baby boy farin ciki kamar basu taba jika ba sai akansa mami har mamaki ta bawa kowa ganin yadda take rawar jiki.
Da aka sallameta gida mami ta wuce da ita domin ta bata kulawa Afeeyah kam tana tare da babyn.
Kulawa sosai mami take bata kuma kusan kullum saita nemi yafiyarta bisa abinda tai mata tayi kas dakai ta bata hakuri, Fati kuma tana nuna mata cewa babu komai ya wuce ita mahaifiya ce a gareta.
Ranar suna baby yaci suna LABEEB sunan abokin Al'ameen wanda sukai makaranta tare.
Zainab na shigowa gidan da yake tunda ya saketa bata gari tana zuwa ta rungume mami tana kuka.
Cikin mamaki mami tace "ke lafiya kukaan me kike".
Zainab bata iya dakatar da kukan da take ba ta rike hannun mami tana cewa "mami da gaske ne abinda nake ji wannan yar kauyen ce ta haihu tare da Al'ameen ko mafarki nake kunne na baiji daidai ba"?.
Mami tace "wanne irin mafarki kuma Zainab? Bayan gashi kinga zahiri Allah ya azurta Al'ameen da samun d'a namiji ya sanya masa sunan abokin sa Labeeb".
A rude Zainab tace "dan Allah mami kisa baki ya mayar dani dakina wallahi zamuyi zaman lafiya nayi nadama ina son Al'ameen".
Kai mami ta girgiza "a'a Zainab da dayanzu ba daya bane kada kije ki sake gurbata musu zaman su Fatima Zarah ce ta dace da Al'ameen".
"Nima na dace dashi mami kalli ki gani ya zauna da yar kauye ma balle ni tashin birni nasan komai".
"Ai Zainab da kikasan komai sanin naki baiyi amfani ba tunda kika samu damar zama dashi bakija hankalinsa ba yanzu kam saidai nace kiyi hakuri duk abinda zai takura rayuwar Al'ameen bana kaunarsa".
"Mami me kike nufi kenan na hakura dashi"?.
"Eh abinda nake nufi kenan ki barshi yai rayuwa da matarsa itace za'binsa domin wancan karon ma nice na tursasa masa baya so amma yamin biyayya dole ya aure ki nayi tunanin kece kika dace dashi ashe abin ba haka bane kawai kiyi hakuri ki kaddara iya bakin rabon zaman ku kenan ki samu miji kema kiyi aure".
"Mami na hakura dashi fa kika ce? Tabdijan wallahi bazan iya ba shi nake so dole kisa ya maida ni".
"Dan ubanki koke maiya ce bazaki koma gidan Al'ameen ba kinji na fada miki" Hannu Zainab ta dora aka tana kuka ta fita daga bedroom din mami.
Tsaki mami taja "jimin shashashar yarinya da dinma kuskure ne da tsautsayin nima za'a sakeni yasa na nace ya aure ki yanzu kuma tayi kai keda Al'ameen saidai zumunci".
Wata hudu da haihuwar Fati akai bikin Afeeyah ,wanda Zainab tayi bi da nacin Al'ameen ya mayar da ita tayi kamun kafa tayi kuka da magiya yace bazai iya ba dole ta hakura ta auri d'an gidan abokin babanta".
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
Bayan shekara shida😉🌹 wani yaro ne tsaye a harabar wani tabkeken gida sai bubbuda fulawoyi yake daya bayan daya me gadi dake zaune dan dattijo yana murmushi yace" Labeeb".
Juyowa yai yana kallonsa da hannu ya nuna masa wata babbar flower mai blue da farin fure.
Da gudu yaje ya buda saiga Al'ameen ya fito dariya Labeeb yai yana rungume shi wanda Al'ameen ya cira shi sama yana murmushi.
Al'ameen na dire shi ya kuma sake d'afe shi yana yada teddyn hannunsa 'kin daukarsa Al'ameen yai nan suka fara zaga harabar gidan Labeeb na cewa saiya kamashi".
Fati dake palor da cikinta da tudunsa ya fara fitowa jin hayaniyarsu ta dameta yasa ta mike tana fita harabar gidan ganin abinda suke yasa tace.
"daddyn Labeeb I don't want stop you from your playing with your boy but you are disturbing me ku dan rage hayaniya ina son hutawa ne".
Kallonta Al'ameen yai ganin yadda ta tsara kwalliyar datai mata kyau yana murmushi ya kalli Labeeb yana cewa "kaji fa boy abinda mum dinka ke cewa je ka cijeta😁".
Da gudu Fati ta juya ciki jin abinda yace shima Labeeb bayanta yabi murmushi Al'ameen yai jin ihunta yasa ya shiga palon'.
dariya ce ta kamashi ganin yadda suke kokawa da boy gashi ya bude baki alamar cizo .
Zuwa yai ya dauke shi yana cewa "boy mum dinka raguwa ce kalli yadda kasa take gumi bari muzo mubar, mata gidan mu tafi yawo gurin grand-mah dinka".
Labeeb yace "daddy zanga Minal (yar gidan Sadiq ce shekararta uku Afeeyah ma nada 'ya Ni'imah)"?.
"Eh my boy zaka ganta".
Cikin murna yace "to daddy ka ara min kudi nasai mata chocolate irin wacce kake saya min nakai mata".
Zaro ido Fati tai jimin yaro da zarar magana idan ka ari kudin a ina zaka samu ka biya"?.
Murmushi Al'ameen yai yana kissing forehead din Labeeb yace" that my boy wannan gaskiya ne haka nake so kyan d'a ya gaji ubansa boy dina dan soyayya ne shiryashi muje yaga sahibarsa".
Mikewa Fati tai tana rike hannunsa suka shiga bedroom ta mai wanka da shiri ya fito dan gaye.
Harda ita suka wuce gidansu mami ranar Afeeyah tazo su Rukayyah sunzo Family ya taru'.
Suna zaune ana hira cikin annashuwa Labeeb dake kusa da mami yace "grand-mah nifa zance nazo".
Daukarsa mami tana dorashi akan cinya tace" au saurayi na ashe zance kazo gurina ban sani ba"?.
Yadda Labeeb yai da fuskarsa kamar faten dankali😕 saida kowa yai dariya a gurin sauka yai daga kan cinyarta yana cewa .
"Nifa ba keba Minal".
"Oh ita kake so kenan ni ka sani a kwandan shara dan kaga ni tsohuwa"?.
Turo baki Labeeb yai "to grand-mah kema baga grand-fa nan ba"?.
"A'a ni kai nake so daddy aiya tsufa".
Kuka Labeeb ya fara yana cewa "wallahi ni Minal nake so ba keba".
Dariya suka rika yi masa domin duk lokacin da yazo haka suke shan drama da mami har dare suna gidan sai wajen karfe goma kowa yai sallama ya nufi gidansa.
Labeeb yai bacci amma dole saida Al'ameen ya tashe shi ya masa wanka sannan yasa masa sleeping dress ya kwantar dashi.
Fati na tsaye gaban mirror tana tattare gashinta taji anyi sama da ita murmushi tai tana sa'kalo hannunta ta wuyansa tace.
"Soulmate yaufa bacci nake ji sosai".
Sauketa yai akan gado yana hade kirjinsu cikin dauke gira yace "nima baccin nake ji madam".
Ya 'karasa maganar yana zame ribom din data fara daure gashinta dashi yana kissing wuyanta jin hannunsa cikin rigar baccinta yasa zatai, magana.
Ya dora bakinsa akan nata cikin salo yake binta ga'ba-ga'ba sauke nannauyan numfashi tai tana rungumeshi idanuwanta a lumshe muryarta can kasa tace.
"I love you soulmate".
Al'ameen dake shafa breast dinta shima cikin yanayin jin dadin kasantuwarsu tare yace.
"I love u too my heartbeat no one but u".
Yana gama fadin haka yai addu'a yana danna joystick dinsa cikin jikinta wanda lokaci guda suka 'kan'kame juna cikin yanayin farin ciki da nuna zallar kauna da soyayya🤗".
#ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH#.
#ALHAMDULILLAH#
👏 Ya rabbi salli ala sahibul-mu'kami annabin da mai so nasa bai zama a hammi sa alihi da sahabbansa zul-kirami a'alal ula duk ma'kiyin sa ya makanta.
😘 MRS AL'AMEEN AHMAD CE.
Godiya sosai gareku masoya.
👉 Zarah Musa dan adam
👉Safiyyah Aliyu wakili
👉Naja'at Musa Abubakar
👉Hajara Abdul-khareem
👉Hajara Aminu b/kd
👉Fatima Musa Abubakar
👉Sarah Yakubu
👉Batool Adam Naseer.
👉Zainab b/kd
👉Hafsat maman Aliyu
👉Basirah Muhammad
👉Badariyyah Hassan
👉Ameerah Hassan
👉Aseeyah maman Jabeer
👉Zainab sunusi
👉Saudat Yusuf
👉Salmah Hayat maman Afnan
👉Fatima Idris maman Ousman
👉Khadijat Alhaji Yusuf
👉Khadija Adams
👉Nafisat Mu'awiyyah umar
👉Hauwa Mu'awiyyah umar.
YUSRAH MUSA ABUBAKAR.
📚WRITER👇
👑 Yarima Abdul-maleek
🌹 Rayuwa biyu
🍇 Safreeyyah
🎉Haskena Sauban
🎀Minah-Umer
💰 Dan millionaire.
✌️ Husnah ko Badiyat
💕Dama kece
💘 Zuciyar Aliyu
🌃 Royalty.
💖Kowacce 'kwarya
🌹'Dawisu cikin agwagi.
🙏ALLAHUMMA SALLI WA SALLIM ALA SAYYIDINA MUHAMMADIN WA ALA JAMI'IL AMBIYA'I WAL MURSALINA WA ALA MALA'IKATUL MUKARRABINA WA ALA IBADALLAHIS SALIHINA MIN AHLIL SAMAWATI WA AHLIL ARDINA WA ALAINA MA'AHUMU AJ MA'INA BI RAHMATIKA YA A ARAHMAN RAHIMINA WA SALLALLAHU ALA SAYYIDINA MUHAMMADIN WA ALA ALIHI WA SAHABIHI WA SALLAMAN AJ MA'INA.
🌹 Yusrah Musa Abubakar
Mrs Al'ameen Ahmad ce😜
Zanyi kewarku masoya😿 sai rai da nisan kwana ya sake hadamu😭 alhamdulillah kuskuren danai a cikin wannan littafin d'an miloniya ina rokon ubangiji Allah s w t da yamin afuwa fadakarwar dake ciki Allah ya bada ikon yin amfani da aiki da itaa, ameeen.
😉See u next time,
🙏Tnk 4 ur supports
😘Be with me at always
🤗And we will meet again
🎀Domin gyara ko shawara🎀
👉 📱+234 905 527 3614.
🏵❤🔥🏵❤🔥🏵.
*Mrs Al'ameen Ahmad ce*.