Showing 3001 words to 6000 words out of 13942 words

Chapter 2 - FARAR HAIHUWA Part1 by Batul Mamman

19 May 2026

31

ne. Zulai sai murna , uwale tace ga fura ki sha. Kafin ta rufe baki Zulai
ta janye kokon ta kafa kai. Mayunwaciya Uwale ta fada a sarari.

Tana zuwa gida ta sanar da Sabuwa yadda suka yi. Ni dai na fada musu kin gama iddah
idan ba haka nayi ba kinsan uwale da rashin hakuri kamar zawo sai ta bashi wata.
Sabuwa ta hadiyi yawo da kyar tace Gwaggo ina jin ciki gareni fa wata kusan biyu.
Muhuci zulai ta kwala mata a ka. Baki da aiki sai ciki ne duk yunwar gidan inuwa.
To bari kiji. Ranar asabar zaa daura aurenku sai kiyi shiru da bakinki. Idan kika
haihu sai muce bakwaini[truncated by WhatsApp]
[8/22, 3:02 PM] +234 812 673 9684: FARAR HAIHUWA💰6



Sabuwa ta ware idanu kai Gwaggo ai kinga auren babu iddah ma ba kyau ko? Zulai ta
banza rufe min baki. Inji uban wa aka ce ba kyau. Aure kan aure ne ba kyau kuma dai
ba shi zakiyi ba tunda ya sake ki. To cikin fa? Shi ciki ai ba matsala kinsan Uwale
babu abinda ba zatayi ba akan farin jika. To nasan tana da gonaki biyu na gadonta
kinga ko ita muka samu mun huta. Sabuwa dai bata gamsu ba tace Gwaggo zunubin fa.
Ai dan zai zama shege...kul kika kira shi shege da ubansa fa. Ina fata bai san da
cikin ba? Eh bai sani ba. Zunubin kuma zamuyi ta cewa astangafirillah sai kiga
Allah Ya yafe. Sabuwa tace Astagfirullah dai Gwaggo. To naji yanzu dai kin amince
ko. Na amince Gwaggo. Sukq zauna suka kulla duk yadda zasuyi a gidan Uwale idan
aure ya yiwu. Saar su daya kauyen da Sabuwa ke aure daban da nasu saboda haka da
wuya yaji labarin auren.

Shirye shirye ya kankama na bikin Sabuwa da Mal Yakubu. Uwale da Zulai le kidansu
da rawarsu don shi angon ko a ransa. Kullum yana rarrashin Munari ta kara hakuri
idan ya sami kudi zai raba musu gida da Inna Uwale. Ana saura kwana biyu Yaya
Salihu yazo garin Danmarka gaida iyayensa shi da matarsa Ruma. Tani na jin
labarinsa ta tafi gidan ta zayyana masa halin da Munari ke ciki. Fada ya rinka yi
iyakar karfinsa Inno tana bashi hakuri. Inna Ladi tace ni bazaka burge ni ba sai
kaje gidan kayiwa uwarsa barazana yadda zata yi shayin takurawa 'yata. Kamar jira
yake ya tafi gidan cikin fushi. A bakin kofa ya gamu da Mal Yakubu ya fara zazzaga
masifa. Mal Yakubu duk ya tsorata yana ta bashi hakuri. Har gidan ya shiga sukayi
ta da Uwale yace ke Maimuna dauko mayafinki ya kama hannun yaran..birni zamu tafi
kai kuma ka biyoni da takardarta. Mal Yakubu dai harda kuka itama Munari tana yi.
Da kyar Yaya Salihu ya aminci ya barta amma ya dauke Sadi dashi zan tafi. Mal
Yakubu yace wallahi na bar maka shi don girman Allah kada ka rabani da matata. Yaya
Salihu yace mata zan kaiwa Ruma kinji ko munari sai ta hada shi da Ali su shiga
makaranta idan sun dan kara girma. Godiya tayi masa ya kawo kudi ya bata. A waje ya
sake jaddadawa Mal Yakubu ya kular masa da kanwa sannan idan anyi auren zai sa ido
a kansa. Daidai da rana daya yaji zance mara dadi zai dauki mataki.

Ranar lahadi da karfe biyun rana bayan an idar da sallar azahar aka daura auren Mal
Yakubu da Sabuwa. Dakinsa aka saka amarya ya zama bashi da daki a gidan sai na
wadda take da girki. Da daurin gindin uwale Sabuwa ta goge da yiwa Munari wulakanci
a gidan. Kullum hakuri take saboda yadda mijinta ke iyakar kokarinsa wurin kyautata
mata. Watan Sabuwa biyu a gidan ta fara bayyana cikinta kamar yadda suka yi da
Zulai. Uwale kamar ta lashe ta don so. Kullum Zulai tana gidan abinci safe ,rana da
dare duk an mata kwano. Habaici iri iri Munari take sha idan suka hade kansu
karkashin bishiya da yamma. Kirikiri Uwale ta hana Sabuwa girki kullum Munari keyi
idan dare yayi kuma ta tubure tace sai Mal Yakubu ya shigo dakinta ranar girkinta.



Batul Mamman💖
[8/22, 3:02 PM] +234 812 673 9684: FARAR HAIHUWA💰7




Haka rayuwa ta kasance a gidan Mal Yakubu yau fari gobe tsumma a wajen Munari. Ba
don soyayyar da suke ma juna ita da mijinta ba da tuni ta bar gidan.

Sabuwa na kwance a kofar dakinta da daurin kirji tana shan rake Uwale ta fito daga
bandaki tace kai sabuwa ki raba kanki da zaki fa saboda nakuda. Kinji ki Inna kamar
wata sabon shiga? Haihuwa ta uku har sai kin karanta min yadda zanyi? Ta yatsina
fuska ke fa daya kawai kika yi ta tsaya miki cak. Munari daga cikin dakinta tace
Allah Ya kara ta cigaba da yiwa yarta Ramlah kitso. Uwale har wani tsoron sabuwa
take ta ajiye butar hannunta tace to Allah Ya baki hakuri uwar biyu. Wannan ciki
naki badai girma ba. Gaban Sabuwa ya fadi ita bata taba ciki mai girman wannan ba
ma gashi a karyar da tayi baifi wata bakwai ba. Bata sake tankawa Uwale ba don kada
a ja maganar ta cigaba da shan rakenta.

Bayan sati uku wata rana Uwale da zulai sun fita unguwa tun safe nakuda ta kama
Sabuwa. A muguntar Uwale kulle gidan tayi ta waje wai kada munari ta fita saboda
taji Mal Yakubu yana cewa ta dawo da wuri tasan sarai unguwa zata. Da munari ta
shirya ta shirya yarta zasu fita taji kofar a garkame. Ta gaji da ja ta dawo daki
rai a bace. Dama gidan kanwar Inno zata je ziyara. Tana ajiye gyalenta taji kamar
ana kiranta daga dakin Sabuwa. Shiru tayi ta tabbatar sannan ta fito cikin sauri. A
kwance ta ga Sabuwa tana nishi da kyar duk ta hada gumi duk da sanyin gari. Munari
jika na rawa don itama bata saba ba tace Sabuwa kinga Inna ta kullemu ta waje kuma
saboda zurfin soro babu mai jinmu kiyi hakuri na dubaki. Cikin masifa tace kiji
dadin kasheni ko...ki fita ki nemo taimako Munari don idan na mutu sai nayi miki
fatalwa. Babu irin bugun da Munari batayi ba babu wanda yazo kashe reza ta samo a
daki ta dawo kan sabuwa. Tace kiyi hakuri inajin bakwaini zaki haifa don kai ya
fito. Da taimakon Allah Munari tana ta yi mata addua ta samu Sabuwa ta haihu.
Yarinya ce santaleliya fara tas irin wadda Uwale take so. Munari ta yanke cibi ta
taimaka mahaifa ta fito. Kai Sabuwa wannan 'ya da takai wata tara ban san irin
girman da zata yi ba. Ruwan wanka ta dora ta wanke jaririya ta kaiwa sabuwa ruwan
wanka. Sai bayan laasar Uwale da zulai suka dawo. Tun daga tsakar gida uwale ke
yiwa Munari dariyar keta ta hanata fita. Munari ko a jikinta tace Inna kinyi kawa
fa. Ko kulata bata yi ba harda tsaki zata wuce tace Inna nace kinyi kawa fa Sabuwa
ta haihu. Zulai ta yi dakin cikin sauri Uwale tana binta tana cangala kafa. Allah
Kasa fara ce, Allah Kasa fara ce. Haka take fada har ta shiga dakin. Baby ta dauka
ta rungume. Yarinyar akwai kyau ga hasken da Uwale ke buri. Zulai ta rike yarta.
Sabuwa bakwaini kika haifa? Me ya faru haka? Waya karbi haihuwar? Sabuwa tace
nakuda ce ta kamani gashi kun kulle gidan. Munari ce tayi komai, Uwale ta rungume
yar ta fita. Munari ta gani tana kwasar tuwo ta dan saki fuska nagode fa Munari
sannu da kokari. Zulai da ta gama zige yarta a cikin daki ta fito da sauri wace
godiya zakiyi mata uwale? Ashe kina fita ta kama Sabuwa da kokawa shine haihuwar
tazo ba shiri. Ai don kada a kamata da laifin kisa ta karbi haihuwar. Uwale ta bata
rai muguwa azzaluma da mai kyan zaki kashe min. To ta Allah ba taki ba baka mai
bakar aniya. Tuwon ma bazata ci ba kada kisa guba. Kwashe abinki ki bace min da
gani. Hawaye ne ya saukowa Munari ta je har kofar dakin ta leka Sabuwa na kwance a
kan gado. Cike da takaici tace Sabuwa abinda zaki saka min dashi kenan ko? Allah na
gani kuma baya bacci. Zulai tayi tsaki muguwa kinga farar haihuwa kina bakin ciki.

Mal Yakubu dai yayi farinciki daidai gwargwado yace to Inna sai asa mata sunanki
ko. Tunda kan Ramlah kika ce kada asa sunanki. Uwale tace yo haka kurum zaka sawa
wancan mummunar abar sunana? Ya jawo abarsa ya rungume suk yaransa yafi sonta. Inna
tace itama wannan bazaka sa mata sunana ba saboda kyanta. Akwai sunan gayu dana
taba ji wallahi wata rana dana je gidan Harira jikanta ya kunna talabijin. Sabuwa
tace ni fa Inna kada ki bata wa yata suna. Inna tace ni dai Hannan naji an fada ai
ko yayi dadi ko? Sabuwa ta bata fuska Hannan kamar marowaciya Hanan ake cewa. Na
yarda Malam a saka mata. Mal Yakubu yace to Allah Ya raya ya dauki Ramlah ya tashi
yayi waje.

Ranar suna aka radawa yarinya suna Hanan. Uwale sa guda ta bayar aka yanka cikin
shanunta uku. Anyi bushasha ranar suna kamar haihuwar fari. Yan uwan Sabuwa suna ta
zuba habaici ga Munari. Ga 'ya mai goshin arziki an haifa. Haka dai akayi ta taro
Munari da nata yan uwan suna daga cikin daki. Yayar sabuwa na suyar nama ta bawa
duka yaransu aka tsallake Ramlah. Ta rinka binsu da kallo har Uwale ta kula tayi
tsaki ai idan baki bata ba Hanne yarinyar nan kamar mayya sai tasa ki kone da mai.
Cillo mata kashi ta gwaigwaya. Hanne ta dauko wani guntun qashi ta jefawa Ramlah.
Qashin bai zame ko ina ba sai bakin rijiya Ramlah ta bishi da dan gudunta. Tana
zuwa bakin rijiyar takalminta daya ya zame daga kafarta santsi ya kwasheta sai
cikin rij[truncated by WhatsApp]
[8/22, 3:03 PM] +234 812 673 9684: FARAR HAIHUWA💰9




Sai da cikin Munari yayi wata shida Uwale da sabuwa suka san dashi. Gaba daya
Sabuwa hankalinta a tashe yake tana tsoron kada Munari ta sake haihuwa hankalin Mal
Yakubu ya koma kan abinda ta haifa. Yanzu ma kamar yasan Hanan ba yarsa bace baya
bi ta kan ta sai Inna Uwale ta dame shi. Ita kuwa kullum tana rike da ita a tsakar
gida ko dakinta tana mata waka. Hannan farar jikar Uwale. Zaki auri mai kudi mai
mota,zaki kaini makka da madina.

Duk wahalar da Munari ke sha saboda cikinta yakai watan haihuwa Uwale bata daga
mata kafa akan girki ba irin yadda aka yiwa Sabuwa gata. Ganin aka Mal Yakubu ya
siyo risho har biyu yasa a kitchen din. Uwale bata san dashi ba sai da ta fito da
goyon Hanan tana ta cangala yar kafarta. Eyye me zan gani haka? Fito fiti kinibabbe
ta kirawo Mal Yakubu daga daki. Wato don munafurci shine zaka wani siyo risho
saboda matarka ta dena wahala ko? To ban yarda ba. Ni nafi son abincin da aka dafa
da itace. Yafi dadi da inganci. Sabuwa tace a'a fa inna waye baya son sauki ni
gaskiya nafi son rishon. To...to ai shikenan saboda kada fatarki tayi duhu a bakin
murhu ba. Ta harari Munari kunyi sa'a uwar mai kyau tana son rishon ba don haka ba
da kunga tsiya wallahi. Kamar kullum shi dai Mal Yakubu sai aikin bada hakuri.

Tun dare Munari ke fama da ciwon baya kadan kadan tana daurewa. Zuwa asuba abin ya
ta'azzara gashi ba girkinta bane. Da kyar ta iya mikewa ta bude kofar dakinta.
Dakin Inna uwale ta nufa tana tafiya da kyar. Tana ta kwankwasawa Uwale na jin
muryarta ta sake gyara kwanciya....aikin banza haihuwa ta hudu ai zaki iya da
kanki. Haka ta koma kofar dakin Sabuwa tana bugu. Mal Yakubu ne ya fito ya kamata
zuwa dakinta yace Sabuwa ta tashi Inna su kula da ita sannan ya fita zuwa gidan
makocinsa mai akori kura ya taimaka masa su tafi asibiti. Yana dawowa daga bakin
kofa ya jiyo kukan jariri. Da gudu ya karasa ya ganta kwance kan tabarma ita kadai
da baby a gabanta. Duk ya rude yace bari na kira Inna...hannu ta daga masa barshi
kawai Malam ga reza can dauko ka yanke cibiyar.

Su kadai suka yi abinsu su Inna ko leqe. Ya fita ya bawa makocinsa hakuri ya dawo
ya buga kofar daki cikin fushi. sabuwa ki fito kafin na shigo dakin nan don wallahi
na shigo jikinki zaiyi tsami. Ta fito tana mika...yanzu don wulakanci ince ki tashi
inna ku taimakawa Maimunatu sai ku barta ita kadai? Inna ta fito dan nan ni kake
cewa munyi maka wulakanci? To mungode Baba sai ka fadi me kake so muyi yanzu. Inna
ni ba haka nake nufi ba amma ai ko sannu ayi mata. Sannu maigida to me aka samu?
Mace ce ya fada ya kasa boye murnarsa.




Batul Mamman💖
[8/22, 3:05 PM] +234 812 673 9684: FARAR HAIHUWA💰8



Salati da ihun mata yasa su Munari fitowa daga daki. Mata na ganinta suka yi cirko
cirko an rasa mai magana tana ta tambayar me ya faru. Uwale tace ni dai ba
ruwana ,fa bani bace. Munari tace wai meye ne? Me kuke leqe a rijiyar? Wata
makociyarsu ce tayi karfin halin fada mata...Ramlah ce ta fada.

Wata kururuwa Munari tayi cikin zafin nama ta nufi rijiyar ana rirriketa. Tani tace
cikin rudewa garin yaya ta fada? Wata yar cin shinkafar sunan tace qashi ne Hanne
ta jefa mata bakin rijiya shine ta bishi ta fada. Mal Yakubu aka fita kira a
majalisarsu. Munari tun tana kuka da sauti har muryarta ta dashe....wayyo Allah
kawai take cewa. Abin tausayi ta zama.

Mal Yakubu ya shigo yana tambayar me ya faru ake nemansa. Munari ta mike ta rije
wuyan rigarsa. Baban Ramlah idan na rasa 'yata bazan zauna a gidan nan ba. Yi
hakuri ki fada min abinda ya faru. Wani yaro yana cin nama yace 'yarta ce ta fada
rijiya. Mal Yakubu yace Ramlah? Babbar riga ya tube zai shiga shima aka rike shi.
Uwale ta soma kuka don Allah dan nan kada ka shiga kaima ka mutu. Suna haka Sabi
mai hakar rijiya ya shigo da wasu maza. Igiya mai kauri aka daura masa ya shiga.
Duk sakan a wurin su Munari tamkar shekara suke jinsa. Kamar wata zautacciya haka
ta koma. Sai bayan kusan minyi goma ya fara jan igiyar. Cikin sauri aka jawo shi da
Ramlah a kafadarsa. Mal Yakubu ya karbe ta ya kwantar akan tabarka. Cikinta ya
danna ruwa y rinka fita ta bakinta da hanci. Munari ko wurin bata je ba tana zaune
inda wasu mata suka riketa ta share hawaye Allah Ya jikanki Ramlah kawai take fada.

Duk yayi iya yinsa ya tabbatar yarsa ta rasu. Cikin kuka ya bude hannun da yaga ta
damke sosai. Qashin data dauka ne ashe ba rabonta bane. Wace 'yar....din ce ta jefa
kashin bakin rijiya? Jin kowa yayi tsit ya sake kunduma zagi cikin tsawa. Aka samu
wata ta nuna Hanne. Kanta yayi kamar zaki cikin fushi wani abokinsa ya rike shi. A
tsorace tace Uwale ce tace min mayya ce na jefa mata qashi shine tautsayi yasa na
jefa bakin rijiya. Suna wannan fadan Munari ta dauke gawar yarta ta kai daki ta
fara shirin yi mata sutura. Taron suna ya koma na mutuwa ita dai Uwale tayi tsit
don yau dan nata ya bata tsoro. Yana matukar son Ramlah sosai. Bayan an tafi kaita
ne Munari tana zaune gaban iyayenta da suka zo ta fara jan numfashi da kyar. Mal
Yakubu aka kira ya zo ya fitar da ita a rude. Ya kalli innarsa cikin bacin rai.
Idan itama ta mutu yau zan saki Sabuwa kuma ta tafi da yarta bana so. Asibiti suka
nufa inda likita ya tabbatar jininta yayi mugun hawa kuma tana dauke da ciki na
wata daya. Duk da bakin cikin dake damunsa Mal Yakubu yayi matukar murna. Ta taga
yake leken matarsa saboda ance a barta ta huta sosai. Yana adduar ta sami lafiya.

Bayan kwana takwas da rasuwar Ramlah Inna Ladi tazo gidan da sauran yaransu mata
hada kayan Munari. Mal Yakubu yana ta bada hakuri yana zubar da hawaye. Inna Ladi
tace kaga ka bari mu tafi ta laluma kafin yayanta ya zo kaima tunda baka ganshi ba
kasan baya gari ne. Kiyi hakuri inna ya zan saki Maimuna a wannan lokacin ga rashin
'ya ga kuma rabo a tare da ita. Inna Ladi ta kalle ta Munari da gaske ne? Kanta ta
sunkuyar kasa sai hawaye. Yi shiru kinji kada ciwonki ya tashi. Ta dubi Uwale dake
zaune tana yiwa Hannan rawa Sabuwa tana bacci a daki. Yakubu kasan kashe min jika
akayi da gangan muka hakura yanzu haka zata zauna cikin bakin cikin rayuwa a
gidanka? Kiyi hakuri inna babu fa wani yanayi mai dorewa. Zan kula da ita muddin
raina bazan bari wani ya wulakanta ta ba,yana magana yana kallon Inna Uwale. Ta
dago kai nasan dani kake dan nan ka cigaba da zargina don kawai yarka ta mutu. Ba
ga wata Allah Ya baka ba? Girgiza kai yayi ya cigaba da bawa su Inna hakuri.

Tun daga lokacin babu me shiga harkar Munari a gidan saboda yadda iyayenta suka sa
musu ido. Sai habaici daga gefe. Mijinta kuma yana nuna mata so da kulawa sosai
suna ta rainon cikinta cikin sirri. Wata rana suna cin abinci tace ni kuwa Mal
meyasa baka so su inna su san ina da ciki? Munari kenan ai ba murna zasu yi ba.
Karshenta a rinka yin abinda zaa bata miki rai har ciwonki ya tashi. Ko kin manta
Yaya Salihu yace duk ranar da jininki ya hau ko zanyi kukan jini sai na sakeki.
Dariya tayi masa aikuwa gobe zanyi masa aike. Au tsokanata ma kike ko? Zan rama
ne... yanzu dai kiyi ta sa hijab da zaman daki so nake kawai Inna taji haihuwa.
Allah ba don darajar ta haifeni ba da tuni nasa an daure....hannu tasa ta rufe masa
baki. Haba Mal? Ka manta Allah Yace kada mu fadi kalma mara dadi game da iyayenmu?
Kada ka manta kwananta ne ya kare mu kuma hakurinmu shine ladanmu. Hakane Munari
nima yau na dana. Allah Yayi miki albarka Ya saukeki lafiya. Amin M[truncated by
WhatsApp]
[8/22, 3:06 PM] +234 812 673 9684: FARAR HAIHUWA💰10



Inna uwale ta tabe baki sai mace ta takarkare ta haihu amma karshe kaga bakin
jariri. Allah Ya raya dauko min abin na gani a nan bana son doguwar tafiya saboda
kafa. Ba musu ya je ya dauko mata 'yar da kansa ya kawota. Ba yabo ba fallasa itama
dai bakar ce amma ba sosai ba gata kyakkyawa kamarsu daya da mal Yakubu. Inna tana
kallonta ta mika masa gata nan bari naje nayi sallah. Ita kuwa Sabuwa ko kallon yar
bata yi ba ta juya zata koma daki. Dawo nan ya daka mata tsawa. Wuce kije ki dora
mata ruwan wanka. Inna uwale tace ka ma isa...ita da take da jaririya. Dama ai gasa
ce tasa munarin haihuwa yanzu. Girgiza kai yayi cike da takaici yaje ya dora ruwan
da kansa.
Daga ranar 'yan uwan munari ke yi mata komai. Ana saura kwana biyu suna tace Mal
wane suna zaka saka mata ne? Haba munari ai shawara zamuyi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login