Showing 390001 words to 393000 words out of 423255 words

Chapter 131 - KANWAR MAZA by Aisha cool

28 Apr 2026

388

amsa masa, sabir da gudu ya nufe shi, yana kiran daddy, har yana neman ya faɗi, yayi carf ya ɗauke shi yana murmushi.


Ya risuna ya gaida ammi, ta amsa masa cikin sakin fuska.


Ya kalli laila da a sanadin rumaisa, suke gaisawa, saɓanin da da har ta ƙaraci zamanta a gidansu faɗa suke yi.


Ya ce "Hajjaju barka da wannan lokaci?".


Laila ta ce "Mamuda kana lafiya?"


"Ki daina ɓata mini suna mana, daughter ashe tafiya ku ka yi?"


Ruma ta ce "Wallahi kuwa daddy, ya garin, ka karɓo offer taka kuwa? Wane aikin ne kuma"


"Na karɓo, an bamu ni da yayana?"


Rumaisa ta ce "Papa, to ai papa yana da aiki".


Ya harareta ya ce "Ba shi ba. Aikin coustom ne"


Ruma jikinta ya ɗan yi sanyi sannan ta ce "Allah ya sanya albarka ya tsare muku, a kula da aiki daddy, dama na san kai me gaskiya ne, ka bawa ammi ta gani".


Ya ƙarasa ya ajiyewa ammi envelope, ammi cikin jin daɗi ta karɓa ta buɗe tana dubawa ta ce "Alhamdilillah, Ubangiji Allah ya sanya alkhairi, ya sa rai da lafiya su mora, Allah ya tsare maka"


Ya ce "Amin na gode"


Laila ma sanya albarka suka din ga yi, goga Adamu kuwa kamar bai san me suke yi ba.


Iman ma ta ce "Allah ya sanya alkhairi yaya".


Ya amsa da "Amin amarya. And mutum nawa zaku gayyata na wurin dinner? Zan ɗau nauyin abinci".


Ammi za ta yi magana, laila ta ce "Godiya muke, Allah dai ya saka da alkhairi malam mamuda"


Yayi murmushi ya miƙe ya ce "Iman, bayan biki, mijinki zai je Abuja interview, offer ni da shi ne. Kar ki gaya masa yanzu, kin san halinsa zai ce saboda zai aureki ne, an raina abun da yake da shi. Interview ɗin ma kawai zai je ne, dan kar ya gane daga nan a ka samo mana aikin, saboda link ne kawai na tura masa na ce ya cike CV ɗin sa"


Rumaisa ta ce "Mai sunan baba, ya samu aiki daddy? Allah sarki baban marayu. Daddy Allah ya saka maka da alkhairi, ya biya maka buƙatunka na alkhairi, Allah ya nuna mini lokacin da zaku kalli juna kai da papa a matsayin ƴan uwa ba maƙiya ba, ku zauna a gaban ammi ta ji daɗi".


Rumaisa har da kuka, dan abun ya zo mata a mugun bazata, bata taɓa tsammani ba.


Laila ma kanta godiya take masa, iman kuwa kasa magana tayi, ammi na kuka rumaisa na kuka.


Adam kuwa jikinsa ne yayi sanyi gaba ɗaya.


Mahmud bai ce komai ba, ya rungumi sabir ya fita.


Laila ta ce "Ke kuma mimi maimakon kiyi murna, sai ki hau kuka, daga ke har ammin?"


Rumaisa ta ce "Anty laila ba zaki gane bane, baban marayu ne mai sunan baba, tun tasowarsa, bashi da burin da ya wuce rayuwarmu tayi kyau ta inganta, bai ajiye komai ba saboda mu, su kuma gaba ɗayansu basu da burin da ya wuce inganta rayuwata, ban taɓa kukan rasa abu na dai-dai talaka ba, komai suka samu ni.
Albarkacin anty iman ya samu aikin yi, lallai sirikarmu mai albarka ce, ki sa a ranki You will marry the best husband ever in this world" tayi maganar tana murmushi.


Papa ya ce "Wai best husband ever saboda son kai"


Laila ta ce "Ba son kai ta faɗa ba, nima naga alamar hakan"


Ruma ta ce "Ammi yi haƙuri, garin shirme na na saka ki kuka"


"Bari rumaisa, da ke da familynku babu abun da zan ce muku sai godiya, Allah ya ƙara mana zumunci"


Suka amsa da amin.


Ammi ta ce "Rumaisa, yaushe su uwani zasu koma bakin aikinsu ne, baki ce komai ba haryanzu, aikin gidan nan yayi miki yawa fa"


Ruma ta ce "Ammi Asiya ce kawai zata dawo, ta isa zamu din ga aikin tare"


Ammi ta ce "Amma meyasa?"


"Kawai Ammi"


Adam ya ce "Ammi, nima ina goyon bayan hakan, mutum ɗaya ya isa"


Ammii ta ce "To shikenan"


***


Mummy kuwa abubuwa gaba ɗaya sun kwance mata, asirin ya daina ci gaba ɗaya, bata taɓa zaton akwai ranar da za ta zo, ace asirin da take yi ya daina ci ba.
Gashi yanzu sosai suke rigima da Hajiya Lubabatu, wanda ta kai har hajiya Lubabatu ta ce kowa ta je ta ji da matsalarta itakaɗai.


Ɓangaren Mahmud ma yanzu gaba ɗaya ta fara kasa gane kansa, gaba ɗaya yanzu ya watsar da shiga sabgoginta, sama sama suke yanzu.


Abun da ya sake tayar mata da hankali, bai wuce yanzu Fauziyya da duk masu neman aurenta sun gudu, ruƙayya ma sai tarkace, dan yanzu gaba ɗaya ma ta fara kasa gane kan ruƙayyan, domin kuwa wasu abubuwa take, da ta kasa gane kanta, kamar ba ta cikin nutsuwarta.


Babban abun da ya sake jefata cikin damuwa, bai wuce yadda samha ta daina zuwa ba, Fauziyya ta je har gidan turaki, sai dai fa ba a wanyeta lafiya ba, saboda yadda samha take ta cika tana batsewa.
Fauziyya ta ce "Wai Samha lafiya kuwa?"


Samha ta ce "Kin ga Fauziyya, ni fa ban san dalilinki na zuwa ma gidan nan ba, saboda na riga na raba gari da ku, na zaci Mummy ƴa ta ɗauke ni tsawon wannan lokaci da nake tayi mata biyayya, ashe raina mini hankali kawai take yi, amfani take da ni, ta caimma muradinta, dan haka ku je kuyi rayuwarku nayi tawa".


Fauziyya ta ce "Mummyn ki ke gayawa haka, duk abubuwan da tayi miki a rayuwa".


"Tayi mini uwar me? Na sakankance ta din ga cutata, muka yi da ita duk yadda za ayi, za tayi na auri adam, idan na bata haɗin kai, ƙarshe ta cewa baba uwani duk abun da ya faru kar ta din ga gaya mini, sai wanda tayi mata umarni, sa'a ta ci da ban zo har gida na zazzageta ba, na bar maganar".


Cikin fusata Fauziyya ta ce "Do you really know what you are saying samha? Mummy ki ke gayawa haka?".


"An gaya mata ɗin, ke sau nawa muke zama da ku aci mutuncin wasu, na faɗa ɗin, kuma ki fice ki bar mana gida, kuma wallahi tayi mini wani gangancin sai na tona mata asiri, fice ki bar mana gida". Haka suka rubu tsiya-tsiya dutse a hannun riga.


***
"Khadija" mai sunan baba ya kira sunan iman da ke gabansa.


"Yaya umar"


"Ki yi haƙuri da abun da zan baki, na ga ana bayar da kuɗin gyaran jiki da sauransu, ina yawan gaya miki ni ba mai ƙarfi bane ba, dubu saba'in ce a hannuna, za ta ishe ki? Ina ƙoƙarin kama miki wurin da zaki yi hidimar biki ma"


Ba tare da ta kalle shi ba ta ce "Yaya Umar, albarkar auren muke buƙata, anty laila na da event, a nan zamu yi taron biki, ka barsu ka yi wata hidimar da su kawai"


"Kin raina ko?"


Ta ce "A'a, ban raina ba wallahi, ka kashe kuɗi da yawa sosai ne"


"Ko nawa zan kashe ai ba zan biya ba, mutum sukutum fa za a bani, ban faɗi ba ki karɓa da haƙuri"


Kallonsa take tana jin tamkar ta gaya masa batun samun aikin nan, amma ta fasa, saboda gargaɗin da Mahmud yayi mata.


***
Jabir da Jamil har mamaki suke yi, yadda adam ya tattarasu yayi watsi da su kamar basu taɓa rayuwa tare ba, ya cigaba da harkokinsa shikaɗai.
Duk da takawa bai fiye samun shiga wurin aiki ba, saboda yawan tura shi assignments da ake yi, ko haɗuwa suka yi da jamil, Adam ba kula shi yake yi ba, kamar bai san shi ba.


Faɗan da Mummy suka yi da Hajiya Lubabatu, ya sanya jabir daina zuwa gidan gaba ɗaya, dama ɓangaren Mummy ne ko na ammi, ammi yayi mata rashin mutunci, Mummy kuma sun samu saɓani da mahaifiyarsa, dan haka ya daina zuwa gidan gabaki ɗaya.


Iman ta sha gyara yadda yakamata, kamar wata balarabiya, fatar nan tayi kyau. Nusaiba ma joining ɗin su tayi a shan sabayar maman Khadija, da maganin maman ilham mai tula-tula, ammi dai tana shan kunun sabayar, kasancewar baya cutar da lafiya, suka yi kyau abun su.
Mussman Iman da ya ƙara fito da kyawun fatarta, gashi ta ƙara cika gwanin sha'awa.
Abu kamar wasa Nusaiba har tallatawa ƙawayenta maganin maman ilham take yi, da maman Khadija mussman ƙwailayen nan, tare da basu cikakken adreshin su.
Maman Ilham na zaune a no. A1 kawo road Kaduna state 0813 561 3021.
Maman Khadija kuma, na zaune a garin zariya Bayan federal palladan08033411249 , haka zalika tana tura kayanta ko ina a faɗin Nigeria, masu shirin yaye da basa son nono yayi musu ciwo ya zube, wanda basa son bayan yaye yaransu jikinsu ya lalace, ga maman Khadija da maman ilham sun shirya tsaf domin tabattar sun gyara ku.


Rumaisa tamkar amarya, takawa ya gwangwajeta da kayan fitar biki, na gani na faɗa, har da zobe da abun hannu na gwal.


Yanzu baya ƙaunar dalilin da zai sanya ace masa ga tafiyar da zai bar gari, saboda rumaisa.


Yau saura kwanaki huɗu a fara bikin mai sunan baba, ruma tana can tare da iman da anty laila wurin gyaran jiki.


Takawa ya dawo gida, sai shikaɗai a gidan yana falo yana duba wata magazine, kawai ya ga Samha a tsakiyar falon.
Mamaki ne ya kama shi, ya tashi zaune saboda ya baje sosai yana hutawa, kuma baƙi ba sa hawowa saman sai dai su tsaya a ƙasan bene, sai in ruma ce ta kawo su saman benen.


"Samha lafiya ki ka shigo babu ko sallama?"


"Adam zuwa nayi na ji matsayina a wurinka"


"Matsayin me fa?"


"Adam baka san me nake faɗa ba, ko raina mini hankali kawai ka ke yi? Ka daina ɗaga wayata kayi blocking numbers ɗina, Adam zuwa yaushe zan cigaba da jiranka?".


"Samha dama ni na ce zan aureki ne? Samha meyasa ba zaki ɗauki ƙaddara ba?"


Cikin fusata ta ce "Amma kai ka ce zaka aureni bayan ka auri wannan yarinyar"


Adam ya ce "A'a, ni ban ce ba Samha, cewa na yi idan Allah ya ƙaddara, bana sha'awar tara mata a gida, iyalina su tashi kamar yadda tsarin rayuwar gidanmu take, dan Allah Samha ki yi haƙuri, na san kin so ni, amma Allah bai ƙaddara zan aureki ba, dan Allah kar ki haddasa mini matsala a rayuwar aurena".


"Matsala Adam, shikenan bani da makoma kenan?"


"Kina da makoma mana, matsayinki ba zai taɓa canzawa na ƴar uwata ba, kuma na san a manemanki ba zaki rasa mai sonki da zai aureki ba, kiyi haƙuri"


Samha ta ajiye jakarta, ta saka hannu ta ɓalle botiran abayarta, matsatsiyar t-shirt ɗin jikinta ta bayyana, ƙirjinta tamkar zai yi magana.


Ta ce "Adam kalleni da kyau? Me na rasa? Meye ban fi wannan ƙwailar yarinyar ba? Da me ta fi ni ne adam, shikenan wahalar banza nayi a rayuwata".


"A'uzubillah" ya faɗa da sauri sannan ya ce "Samha ba iya sura ce dubawa a mace ba, qualities sannan sannu-sannu ba ta hana zuwa, ita ma ɗin za ta zo in da ki ka je. Abunda rumaisa tayi mini a rayuwa, ko meye ba ta da shi, zan iya haƙuri na jure, saboda martabarta da mutuncinta a idona, idan har kina son na aureki, sai dai ki nemi iznin rumaisa, idan har ta amince ba wani abu".


Ta nuna kanta da yatsa ta ce "Adam, ni ce zan nemi iznin wannan ƴar talakawan wai ta bari ka aureni?"


"Babu wata mafita idan ba hakan ba, ba abun da na nema na rasa a wurinta, dan haka dan Allah Samha ki tafi kawai, bana son yi miki wulaƙanci, amma dan Allah ki tafi".


"Papa, yau ko nemana ba ka yi ko, ka sallama ni in gama gararambata, sai yanzu aka gama gyaran gas.... Sai dai rumaisa ba ta ƙarasa ba, idonta yayi mata mummunan gani, Samha a tsaye a gaban mijinta ta turo ƙirji, kamar ta rungume shi, shi kuma daga shi sai dogon wando, da riga armless.


Zagaye su tayi ta wuce, yayin da ya ji wani irin abu mai kama da tsoro da rikicewa ya kama shi.


"Kin ga Samha, dan Allah ki kama hanya ki fita, kar ki haddasa mini matsala a gidana tsakanina da matata muna zaman lafiya"


Samha ta yi murmushi ta ce"Kamar gaske, wai matarka, ayi dai mu gani" ta figi jakarta tayi waje, tare da mamakin girman da rumaisa ta yi, ga abun arziki duk ya fito dai-dai da jikinta.


Rumaisa kuwa kai tsaye ta shige ɗakinta, ta jefar da jakarta da mayafinta, kawai ta faɗa toilet ta shiga ta rufe ƙofa, tana jin yadda zuciyarta take yi mata zugi da raɗaɗi, ta dinga kokowa da wani abu mai zafi da ɗaci, da yake mata kai komo, yaƙi wucewa.


A rikice Adam ya shiga ɗakin yana kiranta, amma tayi masa banza a banɗaki, yafi ƙarfin mintuna ashirin, yana yi mata magiyar ta fito, amma tayi burus da shi.


Sai haƙura yayi ya tafi, tana jin fitarsa ta fashe da kuka, saboda yadda take jin zuciyarta tamkar tana ci da wuta, saboda ɓacin rai.


Adam bai ga rumaisa ba sai bayan sallar magariba, ya faɗo ɗakin unexpectedly ya tarar da ita a zaune tamkar zata fashe, gashin nan ya sha gyara, ya kwanta sai ƙyallin mai yake yi. Gashi ta wani ƙara fresh, dan gyaran jiki suke sha tare, an yi mata lalle kamar ita ce amaryar, ɗakin kansa sai ƙamshin turare yake yi.


Cikin sanyin jiki ya ƙarasa, ya ce "Mimi dan Allah ki saurareni, i will explain to you"


"To hell with your explanations, bana son ji" ta yinƙura za ta tashi, ya sha gabanta.


"Rumaisa kin fi kowa sanin ni ba mutumin banza bane ba, wallahi bani na gayyato Samha gidan nan ba, kawai ganinta nayi unexpected".


"Dama na ce kai ka gayyato ta, idan ma gayyato tan kayi ina ruwana? Dan Allah ka rabu da ni, bana son jin duk wani bayani naka"


"Kiyi haƙuri dan Allah"


"Ai ni baka yi mini komai ba, ƙarewa saura tayi tsirara ka kalleta, shi ma duk cikin kuskure ne" Duk yadda ya so ta tsaya ta fahimta ta ƙi, tayi mursisi ta din ga yi masa rashin mutunci.


Tun da ake faɗar fitsararta, bata taɓa gwada masa tijara muraran ba kamar yau, sam tayi burus taƙi fahimtar sa.
Ƙarewa ma, yana fita ta kulle ƙofarta.


Gaba ɗaya Adam ya rikice, ya rasa abun da yake yi masa daɗi, rarrashin duniyar nan, ruma tayi burus da shi, da sassafe ta fita ta tafi gidan ammi, aka cigaba da shirin biki, tamkar babu abun da ya faru.
Rashin ganinta a gidan bayan ya tashi, ba ƙaramin ɗaga masa hankali yayi ba, ya fara zuwa gidansu, amma ya tarar da ita tamkar ba abun da ya faru, tana ta hidimominta, ƴan uwan su ammi na gombe, duk sun hallara. Daga nan gida tayi tafiyarta gidansu, nan ma gida ya cika mutanen katsina duk sun hallara.


Ana ta shirin biki, da daddare su habiba suka zo ita da mamanta, idan da aikin da za a kamawa su mama, ga su Hauwwaliya, ai tuni ruma ta manta da damuwarta, ta shiga cikinsu suka cigaba da taɓararsu.


Aliyu tun da yaga Habiba yake shiga yana fita.


Ruma ta ce "Habiba baki da mutunci fa, ki ke soyayya da yaya Aliyu ba labari, kuma ko gaisheni ba kya zuwa yi"


Habiba ta ce "Sannu mama" suka tuntsire da dariya.


Habiba ta ce "Kamar in janyo lokacin candy rumaisa, ina ƙaunar Yaya Aliyu kamar me, Ruma aure da daɗi dan Allah?"


Hauwwaliya ta ce "Eh ɗan gaya mana"


Ruma ta ce "Eh to, ba nace babu ba, bana ce akwai ba, idan kun je kwa gani, idan ku ka yi sa'a ku ka auri irin mijina, to kun dace, ni da mijina bani da matsala, sai danginsa 'yan bala'i. Ku san kowa da kalar jarrabwarsa a gidan aure".


Hauwwaliya ta ce "To, Allah ya sassauta mana"


Suka amsa da Amin.


Da Adam ya koma gida, aka ce masa ruma ta tafi gidansu, dan haka ya tafi yana fatan Allah ya sa ba ta faɗi wani abun ba.


Wayar mama ya kira, suka gaisa ya ce mata rumaisa ta zo, zasu tafi.


Ba ta son tayi musu ko wani abu da zai sanya, a gane saɓani suka samu, dan laila ta gargaɗeta sosai a kan haka, ta ce mata duk wata matsala, in dai za su iya warwarewa a tsakanin su, kar ta bari wani ya ji, balle ya shiga. Galibin aure yana samun matsa a dalilin sako mutum na uku a cikin matsalolin auren.


Bayan motar ta buɗe ta shiga, ko kallonsa ba ta yi ba.


Har suka je gida ba ta kula shi ba, shi ma kuma bai iya ce mata komai ba, duk da ƙasan zuciyarta har ta fara jin tausayinsa, dan a kiɗime yake sosai da sosai.


Da suka je gida ma, a buɗe ta bar masa motarsa ta yi shigewarta cikin gida.


Ko tayi niyyar daina fushin, da ta tuna yadda ta ga Samha a tsaye a gaban sa, ta turo ƙirji sai wani irin baƙin ciki ya turnuƙeta.


Wanka tayi, ta je kitchen ta damo kununta, ta koma ɗaki tana sha. Ita kanta missing ɗin sa take yi sosai da sosai, saboda sun yi wani irin sabo sosai da sosai.


Kamar mara gaskiya haka yayi sallama a ɗakin, ta amsa masa ƙasa-ƙasa.


Ya ƙarasa ya zauna a kusa da ita ya ce "Rumaisa".


"Na'am" ta amsa a daƙile.


"Yanzu kina tunanin zan iya aikata abun da bai kamata ba kenan? Yakamata ki fahimce ni, ya ci ace kin san halina, wallahi rumaisa babu wani abu da ya faru, abun da ki ka gani ma is not intentionally ban san me ma zan ce miki ki yarda da ni ba. Amma dan Allah kar ki kawo komai a ranki".


"Amma fa tsayawa ka yi kana kallonta, fisabilillahi".


"Rumaisa a rayuwata bana tunanin akwai wanda na taɓa bi ina bawa haƙuri, kamar yadda nake binki a yanzu, dan Allah ki yi haƙuri, ko sai na durƙusa ɗin a kan gwiwoyina?"


Ta girgiza masa kai alamar a'a.


"To ki dube ni mana, kiyi haƙuri Please" yayi maganar yana riƙe hannunta cikin nasa.


"Na haƙura amma dan Allah kar ka sake kulata, wallahi ji na yi kamar na je kitchen na samo taɓarya na zo na rotse mata kai. Kawai ta wani tsaya ta gantsare a gabanka, wallahi na ji haushi"


Ya ce "Subhanallah, duk ba ta kai ga haka ba, nima ban ji daɗi ba amma ki yadda da ni, ai ni namu sun isheni, me zan kalla a na wata"


"Abun da bai fi murfin jarkar faron ba?"


Yayi murmushi ya ce "Har laifukana na baya za'a tayar kenan?".


"Eh ɗin, ka je ka kalli naka ko na Samha"


Yayi murmushi ya

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login