Showing 9001 words to 12000 words out of 31076 words
Chapter 4 - HAUWA KULU Yar Cikin Badala Part 3 BY TAKORI.pdf
a wurin Allah na cewa bazatayi aure ba, tunda yarinyar nan duk da lalurar
ba ta rasa ma su son aurenta jajirtattun mazaje irin haka ba.
Yace idan ma ta hana Sarham to shi zai baiwa Salisu.
Bata yadda zaayi ya aje Hauwa a gabansa ba aure in ta kai shekaru 20 wai don kawai bata
gani. In ita bata gani su sun ganta sun ce tayi musu. Duk yadda Inna ta so ta ganar da shi abin
da ta ke hangowa wato wulakanci da tozarci take gujewa Hauwa Malam Bilyaminu ya ko ki
sauraronta, cewa yake. “Ba ki isa ki katange ta daga duk wata rubutacciyar kaddararta ba. Mai lafiya ma yana shan
wahala a gidan aure yana fuskantar kalubale kala-kala ba sai mai nakasa kadai ba.
Aure ibadah ne dama ai, ba gidan jin dadi da kashe ahu bane.
Ni dai fatana da addu’ata Allah ya ba Hauwa dacewa a cikinsa, dama kowacce irin rayuwar
aure ta samu kanta. Na yi amanna ibadah ce. Zan roki Allah yayi mata jagora a duk inda ta
shiga ba tareda Dan Adam yayi mata jagora ba.
Na yarda da wannan yaron SARHAMU dari bisa dari, daya ne tamkar da dubu, shi din mutum
ne har da rabi, ban da dan Adam butulu ne a halittarsa, ai ko wani daban Sarhamu ya kawo
miki koda kuturu ne, ya ce ki ba shi auren Hauwa-Kulu ba shi da kansa ba, tofa bai kamata ki
daga ido a kan al'amarin kina jayayya dashi ba, balle shi da kansa yace zai aureta ba wani ne
ya tursasa shi ba.
Duk abin da ki ke hango mata Allah Ubangiji da ya halicce ta ya riga ki hangowa, kuma yana
tare da ita fiye da ke".
Inna ta rasa yadda za ta yi Malam ya fahimce ta, ita kam in ba tare da ita Hauwa za ta je
gidan miji ba, hankalinta ba zai taba kwanciya ba.
Hauwan da ko Saka always pad sai da ta tsaya tsayin daka ta koya mata. Ita har gobe
Hauwa kamar 'yar goge take a wurinta, musamman da ta lura hankalin HAUWA yafi karkata ga
Jamilu ta kara tabbatarwa kanta Hauwa bata gama sanin ciwon kanta ba har gobe.
Ta kasa boye wannan tunanin nata har sai da ta furta shi ga maigidan nata. Na cewa saidai
su tafi tare gidan mijin ita da Hauwa. Wannan karon dariya Inna ta bai wa Malam Bilyaminu ya
ce,
"yanzu idan na kyaleki sai ki bar ni nikadai a Ghana, nida nake sabon angonki ki nima, tafi
taya Hauwa zaman daki a gidan miji? Kai jama’a? yaushe kika barar da kunyar malam
bahaushe har haka akan abinda kika haifa Safiyya? Bayan ni ma shekaru aru-aru ba na tare da
ke inata dokin kasancewa dake?"
Inna ta ji kunya sosai harda sunkuyar da kai, ta ce, "Malam! To ai abin ne… ni kwatakwata ya
ki zama daidai a kwakwalwata ko kankani.
Hauwa ta je gidan Sarhamu alhalin ba ido, alhalin yana da mata har da 'ya. Da dai a ce ma
babu kishiyar ko Hauwa lafiyarta kalau ko daga shi sai ita, sai na fi kowa farin ciki da wannan
al'amarin. Don jinin Sarhamu abin so ne da kauna agareni".
Malam Bilyaminu ya ce, "Ki manta da komai kike hange ki bar Hauwa a hannun Ubangijinta,
ki daina tunanin ke ce mai kare ta ko ke kadai ce garkuwarta.
Allah shi ne mai kiyaye bayinSa, kuma Shi kadai ne garkuwar bayinSa a ko'ina suke, kada
wannan ya shafi imanin ki da kaddara".
**** ***** ***
A daidai wannan lokacin, shikuma Sarham, yana durkushe gaban Mama shi kuma, wato mai
shari’a Haj. Maimunatu yana fada mata bukatar da yake da ita a safiyar yau, don Daddy ya ce
ya je ya nemo yarda da amincewar mahaifiyarsa da albarkar ta, kafin ya yarda ya je gun Baban
Hauwa sai mahaifiyarsa ta amince ta kuma sanya albarka. Mama shiru ta yi tana sauraron Sarham har ya kai aya a kan bukatarsa na auren HAUWA
KULU nan da kwana uku kafin iyayenta su koma Ghana da ita.
Mama ta dade tana kallonsa kansa a sunkuye, kafin ta gyara zama tace, Sarham ni abin da
ka zo da shi yanzu bai zamo bako a gare ni ba, ko da ma na san watarana makamanciyar
wannan na nan tafe tsakanin ka da ‘yar mutanen Badala. Na kyale ka ne in ga iya gudun
ruwanka a kan mutanenka na Badala. Sarham ka daina fakewa da cewa za ka auri Hauwa don kada a koma Ghana da ita, wannan
hujja ce wadda hankali ma ba zai taba kamawa ba. Ka fito kai tsaye ka ce min za ka auri
yarinyar da ka dade kana so, ba tare da kai kanka ka san son nata ka ke yi ba….".
Dagowa ya yi cikin mamaki yana kallon bakin Mamansa wato Mai Shari'a da ke wannan
furucin da shi bai taba sani ba, wadda a dabi'arta yasan ita bata daukar abubuwan da bata da
hujja, sannan kuma ita mama bata kallon abubuwa sakaka yadda kowa yake kallon su, komai
da muhimmancin da take bashi, yana son tabbatar da sahihancin maganarta a tsakiyar
kwakwalwarsa; Anya yana da digon soyayyar HAUWA komai kankantar ta cikin ransa kamar
yadda iyayensa duka biyu suke ikirari? Kamar yadda Mama ke jaddadawa bayan na Abba
Prof.? A saninsa duk wata soyayya dake zuciyar dan adam ya gama mallakata ga matarsa first
love dinsa MADINAH.
Ba wata mace da zai so a bayanta. Ba ayi ba, kuma baza’ayi ba. Mama ta yi murmushi ta ce,
"Sarham, Allah ya bada sa'a, Allah ya sanya albarka a ciki, amma hakika ina jiye maka wahalar
dake cikin auren nan, musamman dai ido, da ake kira mutuwar tsaye, saidai na san ladan da ke
ciki ya fi wahalar dake ciki yawa. Sannan ka tsayar da adalci a tsakanin matanka ba zancen mai
lafiya da marar lafiya, duk sunansu matanka.
Madina ba za ta karbi al'amarin nan da sauki ba na sani, don haka sai ka aro hakuri ka kara
akan wanda kake dashi. Na dade da sanyawa a raina duk ranar da ka zo min da batun auren
Hauwa ‘yar mutanen Badala zan mara maka baya a bisa dalilaina na kashin kaina masu yawa”.
Mama bazata daina shayar dashi mamaki ba sai sauraron ta yake da sukunin zuciya, a yadda
take magana kamar dama tana jiran zuwan wannan ranar ne. Tace.
"Na farko son da ka ke yi wa Madina ya yi min yawa Sarham, ban sani ba ko saboda baku
da wani tsiran shekaru masu yawa ne tsakanin ku, kuma matakin ilmin ku daya kaida ita, yasa
nake kallon auren naku wani abnormal, zan so kwarai ka auri macen da ka girma nesa ba kusa
ba, sannan wadda kafi ilmi da wayewa sosai, kuma wadda ka ke yi wa matsakaicin so.
Sannan ne zaka san dadin aure Sarham da jin cewa ka isa a gidan ka. Amma yanzu kam!
Ban san sunanka ba banda mijin Madinah.
Wannan din ra'ayina ne kawai na fada ba lallai sauran mutane su yarda da abin da na fada
ba. wasuma cewa zasu yi na yi son kai. Amma iyaye irina zasu yarda dani.
Sannan in har ba auren yarinyar nan ka yi ba 'yar mutanen Badala ni na san ba za ka taba
samun kwanciyar hankalin da kake bukata ba a ko’ina kake.
Ko don yadda ka damu da su, zamanta tare da kai matsayin iyalinka shi zai ba ka kwanciyar
hankalin da kake nema shekara da shekaru, da albarkata nake cewa Allah Ubangiji ya sanya
alkhairi a auren ka da Hauwa”.
Sarham, ya ma rasa inda zai sa kansa don farin ciki, kamar ya goya Mama, ya rasa ko
wadanne irin kariman iyaye Allah ya albarkace shi da samu. Wadanda kullum bukatarsa da
kwanciyar hankalinsa sune farkon abun dubawar su bata kowa ba. Har sai da ya yi kwallah
saboda farin cikin amincewar su farad daya, abin da bai taba tsammani ba. Musamman Abba
Prof.
Ita kuwa Mama dalilinta na amincewa farad daya shine har gobe ta kasa yafe abinda Baban
Madinah yayiwa Sarham na rainin arziki, wato bai bashi ita cikin mutunci da darajjawa ba sai
bayan ya wulakanta shi ya kuma maida ita bazawara, da kuma gorin arzikin da yayi musu kafin
ya basu auren 'yar sa. Sai yau ta samu abunda ya tsaya mata tuntuni a kokon rai, akan auren Madinah taji sukuf! Ya
fada cikin cikinta.
Ta kasa yafe wannan sai yau dinnan da a wurinta Sarham zaiyi aure daidai shi. Kuma inda
ake ganin darajarsa da tasu. Inda za’a mutunta soyayyarsa.
Da daddare suka shirya tafiya Kofar Na'isa shi da Abba Prof. don haka tun bayan isha Abba
Prof. ke shiryawa. Sarham ya kira Madinah a waya ya gaya mata yau da dare ba zai samu
shigowa Sorondinki ba, yana da uzuri wanda ba da jimawa ba zai sanar da ita ko mene insha
Allahu. Ya kare zancensa da cewa, "Ina fatan Munawwarahta, Giwar Sarham, za ta kasance mai
fahimtata a wannan karon ma, kamar koyaushe".
Madinah taji jikinta yayi sanyi haka kawai, don bata ga dalilin wannan jirwayen ba, amma dai
ta daure ta ce, "Insha Allah. Take care of yourself for us, good night Sweetheart".
Ya ce, "Night!".
Karfe takwas na daren ranar a kofar gidan Malam Bilyaminu ta yi musu shida mahaifin sa Abba
Prof, Abbas Shanono. Abba ya zauna a mota har Sarham ya shiga ya yi wa Inna da Malam
bayanin tare suke da mahaifinsa.
Malam ya kara yarda da cewa Sarham da gaske yake, “wannan kai ne sha yanzu magani
yanzu”, ya saka hularsa yana cewa, "Ikon Allah, ni da nake shirin ka zo ka kai ni in kwashi
gaisuwa in kuma yi godiyar zumunci da kyautatawa, sai ka dauko shi da kansa tun kafin ni in
fara zuwa? Baka kyauta ba". Da rawar jiki Malam ya yi wa Abba Prof. shimfidar darduma a nan tsakar gidansu ya je da
kansa ya shigo da Abban.
Abba ya ga mutunci da karrama dan Adam da sanin halacci wajen iyayen Hauwa, duk yadda
yake tunanin talaucin nasu sai ya ga ba haka ba, kuma ba su da wata makusa da za'a kushe
har aki auren jinin su akanta. Da gaske sunansu talakawa a bakin malam bahaushe. Amma fa
ba irin talaucin da ya zama illa ba, tun daga soron gidan ka san ka zo gidan mutane masu
tsaftar muhalli da tsaftar zuciya.
Ko'ina ka duba tsaf tsaf yana tashin kamshin turaren wuta. Suka gaisa cikin karrama juna,
Malam ya yi masa godiya a kan Sarham, ya kuma yaba masa a kan irin tarbiyyar da suka ba
shi. Sannan ya tabbatar musu alkhairi zai yi ta bibiyar su har zuri’ar su. Shi kuma Abba ya ce,
"ai babu komai don ya gine gidan kakannin jikokinsa, tunda gashi yanzu ya zo neman auren
Hauwan ma dungurugum.
Shi kuma Malam Bilyaminu da dukkan zuciyarsa ya jaddadawa Abba cewa ya baiwa Sarham
auren Hauwa, ya sake jaddadawa, “ba Sarham ba ko wani daban Sarham ya kawo zai ba shi
aurenta. Fatansa kawai a tausaya mata, ayi mata adalci a kuma dauke mata wahalhalun aure
da hidimar da aka san bazata iya ba saboda lalurarta. Abba Prof. ya ce, Kada su ji komai, Sarham likitan ido ne, ya san komai a kan lalurar makanta,
kuma tunda shi ya ce ya ji ya gani to ya ga zai iya ne.
Ta fanninsu su iyayensa za su taya su kula da Hauwa kamar tana gabansu.
Abba Prof bai bar gidan ba sai da suka tsayar da cewa, lallai kafin komawarsu kasar Ghana
za a daura auren Dr. SARHAM da HAUWA.
Malam Bilyaminu ya yi rantsuwa a kan bayan sadaki ba zai karbi komai ba, kuma ba za'a yi
taron komai ba, aure kawai za a daura Hauwa ta tare a gidanta.
Da Abba zai tafi ya ce a kira masa uwar sa wato Hauwa, yana so ya ganta. Inna ta shiga har
dakinta ta same ta tana barci sadidan bata san wainar da ake soyawa ba sai da Inna ta tashe
ta, "Ke Kulu, Kuluwa, Hauwa, taso ki sa hijabinki ki biyo ni".
Hauwa ta mike cikin nauyin barci tana lalubar hijabin nata, ba tare da ta san ina za su je ba.
Hannunta Inna ta kama har gaban Abba Prof. ta zaunar da ita tana gaya mata "Baban Likitana
ne, ki gaishe shi".
Hauwa ta gaida Abba, ba wata kunya a idonta a kansa don bata san ma me ya kawo shi
gidan su ba, shi kuwa ya amsa fuska a sake, a ransa ya ce, Ban da rashin idon ai wannan ta ko
ina matar aure ce. Tsari da zubin halittar jikinta shigen na mutanen Senegal.
Ya koma gida a ranar ya gama magana da ‘yan uwansa waliyyan Sarham a kan ranar asabar
su zo su je a daura auren.
Wani ikon Allah tunda aka tsaida maganar auren Sarham da Hauwa ranar asabar Sarham
bai iya ya kara zuwa gidan su Hauwa ba, kunyar Inna ya koma ji sosai. Sumayyah dai sai ji ta yi
Mama ta ce mata asabar za a daura auren Bhaiya da yar mutanensa na Badala.
Sumayyah a zaune take amma wani dan karamin ihu data saki hadi da juyi nan take, ya
baiwa Mama mamaki, ta yi ta taka rawa daga tsaye, sannan ta zauna ta rangada guda wadda
ta tashi Aunty Surayyah daga barcin la’asar din ta wanda ya zame mata farillah duk da kullum
Mama na hana ta. Surayyah, data farka tagine me suke cewa, kamar kusan ace a sama ta tsinci zancen,
bagatatan, wai Bhaiya zai kara aure, ta kuma tabbatar Madinah ba ta sani ba, don ko dazu sun
yi waya da ita lafiya-lafiya ko kadan ba ta yi mata zancen nan ba.
Surayyah gabadaya rudewa tayi, tana son ta kira Madinah ta labarta mata tana tsoron Yayan
nasu da abida hakan zai haifar, kada ta yi masa riga-malam masallaci. Ta sani shi kuma baya
so ka shiga sabgarsa musamman in bai s aka ciki ba. Shi ya sa ta yi shiru tana ta kawa zucin
maganar. Haka ta wuni bugun cikin Sumayyah tana ta tambayar ta ko wace ce zai aura din?
Sumayyah da ya ke ta san Surayya sarai, kuma ta san tsakaninta da Madina sai ta ce mata, “in
zan baki shawara ki dauka, duk da nake kasa dake, ki fita daga abinda babu ruwanki. Nima ban
san ko wace ce ba, amma ina backing maganar dari bisa dari sai me za’ayi?”
Surayyah dai bata hakura ba, kuma bata dauki shawarar Sumayyah ba, ta sake bugun cikin
Mama kan wace ce Bhaiya zai aura da Sumayyah ke ta murna haka??? Ta nuna kamar bata da
issue da abin. Abinka da Uwa, sai Mama ta zauna ta bata labarin su kaf! Da irin kusancin da
suke dashi da Sarham shekaru masu yawa a baya. Sai lokacin Surayyah ta tuna su, ta kuma gane yarinyar da yace yayiwa aiki ta makance ne
wadada ya likewa tun daga lokacin, ta kuma gane sune wadanda yake turowa kudi tana
cinyewa wadanda sabida su dan uwanta ya kusa daina gaisawa da ita.
Surayyah cikin tsananin bacin rai ta ce, “kuma Mama shine kuka amince masa? Saboda
Allah duka-duka yaushe Yaya Doctor yayi auren fari, wannan ai zalama ce da hadama, kuma
me Madina ta rasa ko ta ragemu dashi da za’a yi mata kishiya ko arba'in ba ta yi da haihuwa
masa ba?" Numfashin Surayya har sarkewa yakeyi don tsananin bacin rai. Mama na observing dinta a
hankali don bata ga dalilin daukar zafinta akan maganar haka ba, na farko ba itace Madinah ba,
na biyu ta san dai bata isa ta sa Sarham abu ko ta hana shi ba, ta ce. Mama ta nuna ta da yatsa
tace "Surayyah bana son ki da shiga harkarsa, ke me guntun kashi a katara a idonsa, amma
yace ya ayfe miki duk da nasan har abada bazai daina kallon ki da abin ba, ki rufawa kanki asiri
ki fita daga harkar aurensa da duk matan da zai aura anan gaba ma.
Ni na amince masa don auren soyayya Sarham zai yi wannan karon ma, kamar yadda ya
auri Madinah don yana sonta, ba kuma don Madina ta gaza dashi ba ko mu tayi mana wani laifi,
a’a kaddararsa ce auren mace fiye da daya, wadda shikadai yasan karfin dalilinsa".
Tun magana na kankanuwa, wato abinda Hausawa suka ce abu kamar wasa karamar
Magana ta zama babba