© Fikra Writers Association *KASHE FITILA*💡1 *Batul Mamman*💖 *FWA Girls Secondary School Abuja* _SS 2A_ Hankalin malamin Civic Education da kusan duka daliban yana kan monita wadda aka sanya rarraba takardun test da akayi satin da ya wuce. Wannan ya bawa 'yan mata biyu cikin daliban da suke zaune a layin farko daga tsakiya damar karasa shirin abin da suke kullawa tun safe. Daya daga cikinsu ce ta rike ciki tare da kwalla kara iya karfinta sannan ta sulale a kasa ta kwanta. Kafin malamin da sauran su ankara dayar ta durkusa a gabanta tana jijjigata a hankali da muryar kuka take cewa "Rumana me ya sameki, tashi don Allah, wayyo...." Murmushi ne yaso kwacewa Rumana ai kuwa taji kyakkyawan mintsini daga wurin Yusra kawarta "don ubanki idan kika tona mana asiri wallahi cewa zanyi ba dani akayi ba" Tsabar tsoro ne yasa Yusra yin zagin. A lokacin malamin har ya iso, sauran 'yan aji duk an zagaye su ana tambayar me ya faru. Yusra harda kukanta tace haka kawai ta ga Rumanan ta fadi. Health prefect aka kirawo daga ajinsu tare da taimakon Yusra da wata malama suka kai Rumana karamin asibitin cikin makarantar. Sannan aka nemi numbar makusancinta wanda ya kasance kawunta aka kira shi. Bayan an saka mata allura ana yi mata karin ruwa ne kowa ya fita sai likita da Yusra. Suna jin shiru Rumana ta bude idanu tare da saukowa daga kan gadon ta durkusa a gaban likitan "doctor ka taimakeni idan Uncle dina yazo ka fada masa ulcer ta kusa cinye hanjina" Duk da ya dauki maganar rainin wayo amma bai san lokacin da dariya ta subuce masa ba. Sai kuma yayi saurin daure fuska. "Nayi miki kama da abokin wasanki ne ko me?" Yusra ma durkusawar tayi "idan baka taimaketa ba wallahi yunwa zata kasheta a gidansu. Ulcer din gaske ce zata kamata" Juyawa yayi zai fita Rumana wadda ta tabbatar idan hakkansu bai cimma ruwa ba yau kila banda yunwa jikinta sai ya gayamata a gida bata san lokacin da ta fizge hannu daga jikin allurar ta ruga ta tare kofar ba "idan baka taimaka min ba wallahi zanyi muku hauka a asibitin nan. Ka fada masa mugun ciwo ya kamani a kaini gidanmu kada na mutu a nan" Saroro yayi yana kallonta. Bai ankara ba ya ga ta nufi gadon dakin ta daga shi da yake ba wani nauyi ne dashi ba ta kifar. Dan tebur din kusa da gadon ma hantsila shi tayi tana ihu da kuka. Yusra wadda tare sukayi shirin ciwon karyar ma sai da ta tsorata ganin da gaske Rumana tana neman yin hauka. Suna haka likitan yana kokarin riketa taji muryar kawunta daga dan karamin reception din yana tambayar inda take. Idanunta cike da hawaye ta sake kallon likitan alamun roko da neman agaji. Tausayi ta bashi, ita kuwa Yusra kuka take yi. Awaisu yana shigowa dakin ya ganta biji-biji kamar anyi wasan kura da ita. Ga hawaye ya wanke mata fuska. Da saurinsa ya karasa inda take ya rikota "Rumana me ya same ki? dena kukan ki fada min abin da kike so" Kasa magana tayi sai kukan da ta cigaba da yi. Ba a son ranta tayi wannan abin ba amma idan ba gaban iyayenta ta koma ba bata jin zata iya cigaba da hakurin zaman gidansa. Hankali a tashe ya dubi likitan "me ya sameta?" Hadiyar yawu yayi yana kallon yadda 'yan matan suka tsare shi da idanu "uhmm a binciken da nayi yarinyar nan tana fama da ulcer sosai har tana neman lahanta mata hanji" mamakin kansa yayi da biye musu harda aron kalamansu. Girgiza kai yake yi alamun rashin yarda "Ulcer, ulcer ciwon yunwa? Mtsew, ba dai a gidana ba wallahi." "Abin da bincike ya nuna kenan ranka ya dade" Tuni likita ya fara tsorata kada a daga maganar gaba. Harzuka yayi "kasan ko ni waye zaka kira min ciwon yunwa? To ko maigadin gidana bazai kira yunwa ba balle 'yata" Gaban likita ya fadi a zuciyarsa yace 'yarsa kuma, wace 'ya ce zata yiwa iyayenta sharri irin wannan. Harara ya jefa musu duk da ba kallonsa suke yi ba. Awaisu ya katse masa tunani " kaga ka sallameta zan kaita babban asibiti." Bai jira amsarsa ba ya ya durkusa ya dauko takalmanta ya saka mata sannan ya kamata suka fita. Wani irin tausayinsa ya kamata. Sai dai ko ana muzuru ana shaho da yardar Allah sai ta koma garinsu. Suna shiga mota taji ya umarci dreba da ya kaisu asibitin kudi da iyalan gidansa suke zuwa. To kada karyarta ta kare kawai sai ta sandare masa tana mimmikewa. Hankalinsa ya kara tashi. "Uncle babu inda zani, ka mayar dani gida na mutu gaban Mama. Kada na mutu ban sake ganinsu ba" A take ta karyar masa da zuciya. Asibitin dai yasa suka karasa sai dai a binciken gaskiya an tabbatar masa da gaske bata da kuzari. Tana bukatar hutu da abinci mai gina jiki. Wannan jawabi ya sanya shi cikin rudani. Duk yadda yaso su kwantar da ita fafur taki yarda ita Mama kawai take son gani. Gida suka koma yayi ta fadan yaya akayi bata cin abinci ba'a sanar dashi ba. Maamu mahaifiyarsa ita tayi jinyar Rumana a ranar. Da gaske ta rinka sambatu tana kiran babarta ko runtsawa basuyi ba. Dole washegari yayi shiri shi da dreba zai mayar da Rumana gida. Sai dai yana tunanin me zai fadawa dan uwansa a matsayin dalilin da yasa ya dawo da ita. Suna fita Maamu ta leko ta tagar dakinta tana kallonsu. Hawaye taji ya taho mata mai zafi tana tunanin yadda karamar yarinya ta samarwa kanta mafita. Ita kuma ta yaya zata ta bar gidan dan da ta haifa a cikinta?*KASHE FITILA*💡2 *Batul Mamman*💖 *Fika LG-Yobe State* Yara ne suke ta tsalle-tsalle a tsakar gida saboda yau alhamis babu makarantar Islamiyya. Masu dan girman kuma musamman matan kowacce ta kama aikin gida tana yi. Sallamar da suka ji ce tasa suka tashi babu babba babu yaro suka tafi tarbo mai yinta. Murnar ganin Kawunsu suke yi sai dai ganinsa rike da Rumana tana tangadin karya yasa suka yi cirko cirko. Sarkin surutun gidan ne ya ruga ciki yana sanarwa ga Rumana ta dawo. Mahaifiyarta wadda ta kasance mata ta biyu cikin matan gidan bata san lokacin da ta janyo hijabi ta fito ba. Addu'a take yi Allah Yasa ba wani abin Rumanan tayi ba Kawunta ya kasa zama da ita. Ko da ta fito sauran matan gidan wato uwargidan da amaryar duk sun fito suna musu maraba. Ganin yanayin Rumana yasa suka san babu lafiya. Maman Antu kamar yadda ake kiran uwargidan ita tayi saurin riko hannunta suka shiga babban dakin da yake mazaunin falo a gidan. Tuni Awaisu ya wadata musu shi da kayan kallo da kujeru masu kyau. Bai bi bayansu ba ya wuce dakin Baaba Hure. A zaune ya sameta tana jiran shigowarsa tun bayan taji an ambaci sunansa da na Rumana. Sai da ya gaisheta cikin yarensu na Bolewan Fika sannan yayi mata bayanin dalilin zuwansu. "Kuma ka tabbata ba aljanu bane da ita?" "Ko daya Baaba, jiyan nan dai ta bani tsoro shiyasa nace bari na kawota ta huta kwana biyu. Makarantar tasu zanje sati mai zuwa duk da sun san bata da lafiya na sanar musu halin da ake ciki" "To Allah Ya sauwake, ina 'yar uwata? Kwana biyu ko a waya idan nace yayanka ya kira ba ma samunta" Dan murmushi yayi "tana nan lafiya, kinsan sai ta ajiye wayar ta manta inda take ma. Alhaji bai dawo bane?" Kafin ta bashi amsa suka jiyo muryar Alhaji Harisu yayansa. Dakin ya karaso suka gaisa inda ya sake labarta musu dalilin zuwansu. Wannan karon harda matan gidan da Rumana a wurin. "Zancen banza" cewar Alh Harisu "Shine zaka biye mata ka baro aikinka ku taho" Rumana ta tsuke baki, fatanta kada Alhaji ya bata shirin da suka kwashe sati uku suna yi ita da Yusra yace ta koma wannan kurkukun. Ita yanzu ko sunan Abuja ma bata son sake ji. Shi dai Awaisu lallabata yace ayi kuma a tambayeta dalilin kin cin abinci. Domin ko mutan gidan suna ganinta sunyi korafin ramarta. Yarinyar da ko da tana makarantar kwana kafin komawarta Abuja da kibarta. Ita ko ramar nan ta kewar gida bata yi. ***** Washegari da sassafe Awaisu da drebansa suka kama hanya. Sai da Rumana taji tashin motarsu tayi wata kyakkyawar ajiyar zuciya. Za taci karenta babu babbaka, ta mike kafa taji dadin rayuwarta. Abinci kuwa tun daren jiya take yi masa cin hauka. Bayan kwana biyu da dawowarta suna daki ita da babbar yayarsu da tazo daga gidanta. Hira suke yi Rumana tana bata labarin horon da akeyi musu a gidan Kawun nasu. Karshe ma tashi tayi tana kwatanta irin abin da tayi a clinic din makaranta. Mahaifinsu ne yazo ya tsaya yana sauraren bayaninta batare da ta sani ba. Ita kuma Maryama yayarta da ta ganshi ta kasa cewa tayi shiru sai kai da ta sunkuyar. Tana cikin nuna mata sandarewar da tayi a mota ta kula da Alhajin. Nan jiki ya fara rawa, kanta yayi yana duka ko ta ina. "Har kinyi wayon yiwa dan uwana sharri Rumana?" Ihu take yi tana kuka "Wallahi Baba ba karya nake ba. Ba'a bamu abinci sosai a gidan. Daga ni har Maamu bama koshi" "Rufe min baki sakarai mara godiyar Allah. Sharrin naki harda Maamu a ciki? To zan kira Awaisun da kaina muyi magana" A fusace ya fita ya shige dakinsa. Ko zama baiyi ba aka sanar dashi Baaba tana kiransa. Ya tashi ya fita. "Ina gidan nan kake hukunci irin haka ko? duk kiran da nayi maka kuma baisa ka dena ba" "Kiyi hakuri Baaba wallahi banji ba" Abubuwan da Rumana ta fada ya maimaita mata. Gyada kai ta rinka yi har ya gama. "Babu abin da ya dace kayi da ta fadi maganar nan sai bincike ba duka ba." Cike da mamakin rashin gaskata zancenta yace "bincike kuma Baaba? Awaisu fa ake magana" "Na sani, fada maka ne kawai banyi ba amma dan zaman da nayi kwanakin baya banji dadi ba. Kuma kasan Maamu da zurfin ciki" Kallon mahaifiyarsa yayi yana mamakin maganganunta. Fita yayi yasa aka kira masa Rumana. Ya tsareta da jan ido yace ta fada masa komai tsakani da Allah. Kamar an kunna rediyo haka ta rinka bashi labari kuwa. Tana yi tana kuka, shi kansa Alh Harisu idanunsa kamar gauta don bakinciki da bacin rai. Sallamarta yayi da gargadin kada kowa yaji maganar nan sai ya gama bincike. Wayar kaninsa ya kira suka gaisa tare da taba barkwanci sannan yace ya hada shi da Maamu. Anyi sa'a yana gida da kansa ya kai mata wayar. A zaune take sanyin AC yana neman illata ta amma ta kasa kashewa saboda karamin dansa Safwan ya kwashe batiran remote din ya saka a game dinsa. Da ya shiga hankalinsa bai kai kan rawar darin da takeyi ba balle ya taimaka mata. Wayar kawai ya mika mata. Tana karawa taji muryar Harisu sai kwalla wadda tayi saurin mayarwa. Rabon da suyi magana wane wata biyu. Gaisheta yayi ta amsa muryarta tana rawa. Hakan da yaji kawai ya fahimci tana cikin matsala. Bai zurfafa tambayoyi ba yaje ya sanar da Baaba gobe zaije Abuja taho da Maamu. Ganin ransa a bace sosai yasa ta dakatar dashi yana kokarin fita "kada ka manta Awaisu danta ne na cikinta, bata nemi taimako ba kada kayi shisshigi. Garin neman kyautata mata ka shiga hurumin da baza'ayi maraba da kai ba" Cak ya tsaya yana auna maganar Baaba Hure. "Yanzu sai kawai mu zuba ido idan har gaske ne tana cikin matsala a gidan?" "Ba ido kawai zamu zuba ba kuma bazamu yi gaggawa ba. Komai na duniya a sannu ake binsa har a gano bakin zaren. Misali yanzu Rumana karya tayi mana, da wane ido zaka kalli kaninka ko Maamu idan suka ji?" *Labarin Maamu**KASHE FITILA*💡 3 *Batul Mamman*💖 *Tuna baya* Da alamun gajiya ya shigo gidan yana daga kafa da kyar. Baaba ce ta fara ganinsa ta taso da sauri. "Yaya Awaisu an dace?" Girgiza mata kai yayi a hankali zuciyarsa a cunkushe da bakinciki. "To kada ka damu, rabon mutum komai nisan lokaci zai zo gareshi. Ka wuce dakina abincinka yana can" Cikin sanyin jiki ya wuce ta bishi da kallo. Sai da ta ga fitowarsa da kwanon abincin ta mayar da hankalinta ga Maamu da take zaune tsakiyar matan Harisu guda biyu tana tayasu tsinkar zogale. Dan daure fuska tayi cikin wasa tace "Kina kallon dana ya dawo ko sannu balle ki tambayeshi yadda akayi?" Maamu murmushi tayi "tunda kina kusa meye nawa a ciki. Da dai bakya nan sai nayi muku kara" Baaba ta hau mita ita Maamu bata kyauta mata ba. Matan Harisu suka sa dariyar rigimar surukansu. Da suka gama Maamu ta tashi ta shige dakinta ta dan turo kofar. Hawaye ne ya taho mata ta sanya habar zaninta ta goge. Tun dawowar Awaisu tana ganin yanayinsa zuciyarta ta karye. Daurewa kawai ta rinka yi tana yaken dole. Shekara biyu kenan yana neman aiki har yanzu shiru. Ita kam Allah Ya sani ta kure matakin jin kunyar Baaba Hure da Harisu. Wanda ya kawota gidan ya jima da rasuwa gashi nauyinsu ya dawo wuyan dansa. Lokacin da ta auri Mal Sa'adu Abali da danta na auren fari Awaisu tazo. Shekararsa biyu mahaifinsa ya rasu. Yana da shekara hudu ta hadu da Malam har sukayi aure. Taso mayar da shi wurin dangin mahaifinsa amma sam Malam yaki yarda yace bai ga amfanin auren mace kuma a kyamaci 'ya'yanta na wani gida ba. Zaman lafiya suka yi sosai da Baaba Hure. Ita Baaba mutuniyar Katsina ce. Cirani ya kawo iyayenta garin shiyasa ta tashi da iya yarensu. Amma duk da haka tana Hausa da 'yan uwanta. Malam da Maamu wadda ainihin sunanta Safara'u duk 'yan Fika ne, yaren Bolanci sukeyi. Kuma haka duka gidan har yara da shi suke tashi sai dai suna Hausa kadan kadan saboda cudanya da Hausawan cikin gari. Baaba Hure yaranta hudu. Baraka, Harisu, Ummukulsum da autarsu Zakiyya. Mace ce mai kyaun hali da sanin ya kamata. Sannan mai jajircewa wurin tarbiyar yara. Domin yaran sunfi tsoronta akan Maamu mai sanyi. Ita dai barta da yawan murmushi ko da ranta ya baci. Haka suke zamansu gwanin sha'awa. Malam ya sanya Awaisu a makaranta Harisu ne yake rakashi domin autarsu ma ta girmi Awaisu da shekara shida. Yana aji biyu a sakandire Malam Sa'adu ya rasu. Maamu ta shiga tashin hankali saboda bata haihu ba a gidan tana gudun su bukaci ta tashi bayan an raba gado. Sanin cewa yanzu gidansu ko ta koma babu inda zata zauna saboda yayyenta duk sunyi aure da matansu a cikin gidan iyayensu yasa Baaba Hure tace ta cigaba da zama dasu tamkar gidanta. Karatun Awaisu kuma 'yar buga bugar da Harisu yake yi da nata jarin suka hada suna biya masa kudin makaranta. A haka ya kammala ya fara shirin jami'a. Maamu ta sayar da gonarta ta biya masa kudin ya tafi Abubakar Tafawa Balewa University (ATBU) ta Bauchi inda ya karanci Banking and Finance. Lokacin nauyi ya fara yiwa Harisu yawa ya soma tara yara. A haka dai da karume karume suka rinka tallafawa har ya gama da sakamako mai kyau. Ga shakuwa tsakanin 'ya'yan gidan wanda bai sani ba bazai taba gane cewa Awaisu ba dan Malam bane. A halin yanzu aiki yake nema ruwa a jallo abu ya gagara. Maamu kullum burinta ya sami abinda suma zasu gwadawa Baaba Hure da zuri'arta karamci ba don su biyasu ba. Sai don kawai ta nuna musu cewa bata taba manta alkhairinsu ba gareta. Harisu ya kara aure iyali suna ta karuwa. Ya ciyar da dolensa ya ciyar da ita da danta. Wannan yasa take jin babu dadi. ***** Bayan kwana biyu Harisu yaje Kano saro kaya a Kantin kwari kamar yadda ya saba duk karshen wata. Sunansa yaji an ambata ya juya yana neman mai kiran. Murmushi ya saki tare da sassarfa wurin karasawa wurin wani mai shago suna dariya tare da rungume juna "Harisu Abali" "Saminun Kano" Sake rungume juna sukayi sannan Saminu ya ja hannunsa suka shiga cikin shagon atamfofi. Lemo mai sanyi yasa aka kawo masa sannan ya bayar da kudi a siyo musu abinci. "Ikon Allah, ashe rai kan ga rai" cewar Saminu yana kara kallon abokinsa. "Ga zahiri dai, sama da shekara biyar sai yau Allah Yayi ikonsa" Hira sukayi sosai ta yaushe gamo. Saminu yayi zaman Fika inda suka saba sosai da Harisu. Daga baya ya dawo garinsu Kano ya cigaba da kasuwancinsa. A hirar yake tambayarsa kaninsa ya fada masa ai har ya gama jami'a. "Aiki fa?" "Nan fa daya, yanzu ma tare muka zo zai fara tayani kasuwanci kawai kafin aikin ya samu. Yanzu ma yana Wambai wurin masu robobi" Harisu da Saminu sun sha hira sannan suka yi sallama da alkawarin haduwa washegari kafin su koma Fika. **** Washegari kafin azahar sun isa shagon Saminu yi masa sallama. Yana ta tsokanar Awaisu an girma an dena kiran Yaya da an taba shi. Ya hada musu 'yar tsaraba daidai misali sannan ya ja Harisu gefe. "Mutumina nayi maka karambani fa, jiya bayan rabuwarmu naje gidan wani tsohon dan kwangila da nake sayar wa shadda" "Kana nan da shige shigen ka mutumina" Harisu ya fada yana murmushi. "Me za'a fasa..yanzu dai mu bar wannan zance. Cikin hira nayi masa bayanin ina da kani da ya gama karatu yana neman aiki. Sai dai anyi rashin sa'a bansan me ya karanta ba. Shiyasa bayanin nawa bai cika ba" Farinciki sosai ya bayyana a fuskar Harisu " da gaske kake?" Murmushi yayi ganin abokin nasa yaji dadi "yanzu dai yace sati mai zuwa zashi Abuja wurin wani kusar gwamnati. Shine yace idan zai yiwu Awaisu ya same shi a can ranar alhamis" Kati ya dauko mai dauke da sunan mutumin da nambar wayarsa ya mika masa. "Gashi Allah Yasa a dace. Idan yaje sai ya fada masa cewa shine kanin Saminu Zawachiki" Harisu ya rike hannuwansa ya ma rasa kalmar godiya "idan munje zaka ce. Ai dole na rakashi. Allah Ya baka ladan zumunci." Yafito Awaisu yayi da hannu ya matso kusa dasu ya fada masa halaccin da Saminu yayi musu. Shima godiyar yake yi kamar zasu ari baki su biyun.3[7:43PM, 1/20/2018] Sweety: *KASHE FITILA*💡4 *Batul Mamman*💖 Ranar laraba da yamma Harisu da kaninsa suka isa Abuja. Da tambaya suka karasa gidan Alh Mudi Maibuta, dan kwangilan da Saminu ya nemi taimakonsa akan neman aikin Awaisu. Gida ne babba irin na mutanen da naira ta zauna musu. Daga bakin gate din maigadi ya tambayi sunansu da abin da ya kawosu. Suna fada ya saki fuska tare da sanar dasu Alhaji ya bayar da umarnin yi musu iso da zarar sun karaso. Wurin wata katuwar bishiya ya rakasu inda Alhajin yake zaune yana shan iska. Gefensa 'yan mata ne guda biyu sanye da kaya iri daya. Tun tahowarsu Awaisu wurin babbar ciki ta kafe shi da ido tana murmushi. Shi kuwa hankalinsa bai ma kai gareta ba. Cike da girmamawa suka gaishe da Alh Mudi. Shima fuska a sake ya amsa musu sannan yace su shiga wani daki kusa da na maigadinsa. Abinci yasa aka kawo musu aka yi musu tarba a mutumce. Sai da suka ci suka koshi sannan ya dawo ya karbi takardun Awaisu. Murmushin fuskarsa ya fadada "Ikon Allah ashe kaima Bauchi kayi karatu. Kila ma ka taba haduwa da Gimbi." A ladabce Awaisu yace "Wane ne hakan?" Alh Mudi ya hau dariya "Yarinyar wajena ce, sune a zaune ita da kanwarta shigowarku dazu. Da yake sunan mahaifiyata gareta shine nake kiranta Gimbiya. To kuma kasan mutane, a hankali sunan ya koma Gimbi." Harisu da Awaisu suka gyada kai suna Allah Sarki. Alh Mudi ya cigaba da bayaninsa "Shekararnan ta gama ATBU din amma Business admin ta karanta. Nayi magana da wani sun karbeta a banki zatayi bautar kasa. Shine kaga ina dariya da na ga kaima bangarenka kenan, to zan tura masa takardunka gobe. Kaga abin ma duk zaizo da sauki" Godiya da addu'a suka rinka yi masa. Murmushi kawai yayi "Saminu akwai kirki. Kaya kawai nake saya a wurinsa amma ina jinsa kamar dan uwa saboda iya mu'amalarsa da mutane" Harisu yace hakane domin shima shaida ne. Daga nan Alh Mudi ya yace lallai sai Awaisu ya zauna a Abujan domin idan ya bayar da takardun washegari mai yiwuwa zuwa litinin a bukaci ganinsa a bankin. Sannan yayi alqawarin bashi makwanci har zuwa lokacin. Harisu ya rasa bakin godiya. Mutanen kirki basa karewa a duniya. Sai dai haduwa dasu dace ne. Duk kudin Alh Mudi Maibuta bashi da dagawa da girman kai. Da safe Harisu ya koma Fika bayan yaja kunnen dan uwansa akan ya kula da kansa kuma ya kame mutumcinsa. ***** Tun tafiyar yayansa baya fita ko'ina. Kullum yana daki sai sallah da take fitar dashi wadda Alhajin ko wani saurayi da Awaisu bai tantance matsayinsa a gidan ba suke jagoranta. Safe, rana da dare maigadi zai miko masa abinci ya karba da godiya. Yau lahadi sun idar da sallar magariba Alh Mudi yace ya shigo falonsa su gaisa da iyalin gidan. Domin idan har ya sami aiki an barshi a nan Abujan to dole kafin ya sami wurin zama nan zai cigaba da zama tare dasu. "Ni kuma ba mazauni bane, shiyasa na ga ya kamata kasan mutanen gidan suma su san ka" A baya ya bishi suka shiga wani falo wanda aka kawata da duk wani abu na jindadi. Kafin su zauna wata mace ta shigo sanye da hijabi da alamun sallah ta idar. Sai 'yan matan ranar da suka zo biyu da wani yaro da suke sallah tare wanda bai wuce shekara goma ba. Awaisu ya gaisheta ta amsa da fara'arta ta tambayi sunansa. Kafin ya amsa babbar wadda yake tsammanin ita Alh Mudi ya kira da Gimbi tace "A.S Abali, Mama shine yayi vice president na S.U.G a makarantarmu" Da mamaki ya dago yana kallonta. Shi dai bazai iya tuna fuskarta ba amma dai abin da ta fada gaskiya ne. Kyaunta kuwa tuni yayi tasiri a zuciyarsa. Maman tace "Gimbi rawar kai, ai ba ke na tambaya ba. Naga yayi shiru ne shine nake son jan shi da hira ya sake damu." Ta koma tana kallonsa "Alhaji yayi min bayanin komai game da kai. Allah Ya bamu ikon zaman gaskiya da amana" "Amin Hajiya nagode. Allah Ya kara girma" "Amin, sai dai Mama ake kirana ba Hajiya ba" Daga nan sun dan taba hira wadda hankalinsa gabadaya yana kan Gimbi. Tunda ta fadi sunansa dazu zuciyarsa take kawo masa sabon tunani game da ita. Sai dai a wurin ya yakice shi. Ai ido ba mudu ba amma yasan kima. Ina shi ina 'yar babban gida irin wannan. ***** Washegari da sassafe ya tashi ya shirya kamar yadda Alh Mudi ya umarce shi. Yana wurin maigadi suka fito tare da Gimbi. Taci kwalliya tayi kyau sosai. A bayan mota ta zauna kusa da babanta shi kuma Awaisu yana gefen dreba. Babu inda ya gane a wurin da suke tafiya sai dai kawai yaga an rubuta Zenith Bank. A reception Alh Mudi ya barsu shi da Gimbi ya wuce wurin manaja. Hira suke tabawa jefi jefi saboda shi dai ya kasa sakewa da ita duk kuwa da cewar ya fahimci sakon da yake boyewa a zuciyarsa itama shine a cikin ta ta zuciyar. Ba jimawa Alh Mudi ya fito ya bukaci Awaisu ya shiga wurin Manaja. Shi kuma suka shiga wani dakin daban da Gimbi. A nan ne aka yi mata bayanin aikin da zata rinka yi. Shi kuma Awaisu takardu ne aka bashi yayi ta cike cike. Bayan ya gama aka sanar dashi zai dawo washegari interview sannan yaje Lagos sati na sama training na wata daya daga nan ya jira posting. [7:43PM, 1/20/2018] Sweety: *KASHE FITILA*💡5 *Batul Mamman*💖 Abu kamar wasa sai gashi komai ya kankama dangane da samun aikinsa. Awaisu ya koma Fika sanar da mutan gidan halin da ake ciki da tafiyar da zaiyi Lagos. Kafin ranar tafiyar Maamu ta tura shi wurin yayanta ya karbo rago biyu cikin tumakin da ake yi mata kiwo ya sayar. Da kudin wanda ko sisi bata cire a ciki ba tace yayi kudin mota da guzuri. Kamar kullum kyakkyawar addua yayi mata tare da godiya. "Ba godiya zakayi min ba. So nake idan kaje ka dage yayi abinda ya kaika. Lokaci yayi da ya kamata ace kana da iyali kaima sannan ka fara ragewa dan uwanka nauyi. Ga zuri'a Allah Ya bashi sosai. Kaga yanzu cikin yaran sai ka rinka biyawa wasu kudin makaranta idan ka fara daukan albashi" "Maamu kenan, Allah Ya bani iko. Nifa babban dana ma sunansa Haris. Tun yanzu ya kamata ki fara kirana Abu Harith irin na Larabawa" Neman abin da zata buga masa tayi saboda rashin kunyar da yake yi a gabanta. Ba shiri ya tashi ya gudu. Bayan kwana biyu Harisu ya raka shi tasha ya wuce Lagos. Watansa daya wurin induction din sababbin ma'aikatan banki. Ana gamawa ya koma Abuja domin jiran posting. A wannan lokacin ne kuma soyayya mai karfi ta shiga tsakaninsa da Gimbi. Tun yana ja da baya har ya amince. Ji yake yafi kowa sa'a. Mace kamarta tana soyayya da talaka irinsa. Da taimakon Alh Mudi ya samu aka barshi a Abuja maimakon Ilorin da aka tura shi da farko. Ganin yana da kwanaki goma kafin lokacin fara aikin ya hada kayansa sai gida. Gimbi harda kuka da zai tafi saboda sonsa take da gaske. Alkawari yayi mata cewa bazai wuce sati ba zai dawo sannan suka rabu. Yana isa gida yara suka fito ana ta murnar dawowarsa. Ya shiga ciki nan ma su Baaba sai murna aiki ya samu. Nan yake jin kwanaki hudu da suka wuce matar Harisu ta biyun ta haihu. Kai kace shi aka yiwa haihuwar ya fita neman dan uwanansa yana murna. ***** Washegari suna zaune a bakin shagon Harisu suna hira Awaisu yace ya zabawa jaririya suna Ummu Ruman. Amma Rumana za'a kirata. "Kai kuma a ina kaji wannan sunan" Harisu ya tambaya yana kallonsa. "A littafin tarihi" "Idan munje gida sai kayi mata huduba dashi" cewar Harisu Duk da cewa ya riga yayi mata da suna Aisha amma baya son batawa kaninsa. Shima kuma Awaisun da yasan da hakan bazai taba kawo wani sunan ba. Sai yamma suka koma gida. A bakin kofa ya tarar da dansa na biyu yana shirin fitowa. "Sarkin yawo ina zaka da yamman nan" "Baba kayi bako daga Kano. Shine aka ce na kirawo ka" Harisu ya shiga ciki dakin Baaba inda suke yana tunanin waye yazo. Abin mamaki Saminu ya gani tare da matarsa da yaransu biyar. Tsabar murna ya rungumeshi suna dariya. "Bala dreban tifa ne ya fada min haihuwar nace to lokacin tada zumuncin mu fa yayi. Dole mu hada kan iyalinmu." "Sosai kuwa, sannu yaya hanya" Matar Saminu mai suna Amina da yaransa duk suka gaishe da Harisu. Ana ta barkwancin yadda zasu rinka magana tunda Hausa a gidan bata zauna sosai ba. Baaba da Awaisu sune masu Hausar sosai. Awaisun shima ya shigo suka gaisa. Fita yayi sauran kudin hannunsa yasa ya siyo lemo, kaji da kwai ya bawa Maman Antu uwargidan Harisu domin karrama baki. Yaushe zai manta Saminu a rayuwarsa. **** Kwanansu hudu a gidan duk an saba kamar sun dade tare. Yaranma kowa da abokin sa ban da babbar wadda ta girmi duka yaran gidan. Ana gobe zasu tafi ne Harisu da Saminu sun zauna hira da daddare Harisu ya sako zancen da yake ta son yi. "Mardiya shekararta nawa ne yanzu?" "Ka ganta tayi tsayi ko? Shabakwai zatayi da azumi. Badi zata gama sakandire in sha Allah" Harisu yayi murmushi "To Allah Yasa abin da zan zo dashi yayi maka. Nace mai zai hana mu hadata da Awaisu?" Saminu ya kalle shi sosai "da gaske kake yi?" "Indai ka amince. Wallahi Saminu ban taba ganin mutum irinka ba. Halayenka abin koyi ne ga wasu. Idan na bari damar nan ta wucemu ai na cuci zuri'ar Awaisu. Mai alkhairi irinka dole a kyautatawa 'ya'yanka zato" Saminu ya kama hannunsa kam "in dai haka ne na bawa Awaisu Mardiya halak malak inyi maka ta yara" Dadi ya kama Harisu suna dariya "in sha Allah Awaisu bazai bamu kunya ba. Dama watan da ya wuce na gama biyan su Zakiyya kudin gidan Malam da ya fada rabonsu a gado. Gyara shi zanyi sosai kafin shekara mai zuwa shima Awaisun ya tara abin da ya tara sai su zauna a ciki. Ba munyi maganar a Abuja zaiyi aiki ba? To muna sa rai zai sami muhalli kwanan nan. Kaga sai su koma can ya sa ta cigaba da karatu ma" Saminu farinciki ya cika zuciyarsa. Shi yana yiwa Harisu kallon mutumin kirki. Shima Harisun kallon da yake yi masa kenan. Sun yanke shawarar sanar da Mardiya babbar 'yar Saminu da Awaisu shawarar da suka yanke domin jin ta bakinsu da kuma basu hakkinsu don kada a zalinci kowa. Awaisu wanda yake bayan kofa tun bayan yaji an ambaci sunansa ya fasa karasawa wurinsu. Ji yayi kamar an dora mada dutse a kansa. Shi kadai ya soma magana a hankali "yanzu wannan yarinyar da bata gama zama mace ba za'a bani? Wallahi da sake. Ko ban hadu da Gimbi ba babu inda zan kai wannan yarinyar"5*KASHE FITILA*💡6 *Batul Mamman*💖 Tun daga wannan rana Awaisu yake wasan buya da Harisu. Duk inda yasan zasu hadu su kebe guduwa yake yi. Ranar da zai koma Abuja ma kamar ana korarsa don sauri. Haka ya tafi tasha kafin Harisu ya dawo daga shagonsa inda ya ajiye masa kayan amfani kamar su madara da ganyen shayi da yake son bashi guzurin tafiya. Baiyi sati da komawa ba Alh Mudi ya dawo daga Kano. Wata rana da yamma ya tura karamin dansa ya kirawo Awaisu. Da ya zo ne ya tabbatar masa da Gimbi ta sanar dasu abin da ke tsakaninsu. Karshe yace yana so ya sanar da yayansa cewa su same shi a Kano shi da Saminu idan har da gaske yana sonta da aure suyi magana. "Ban yarda da bata lokaci ana soyayya ba indai akwai halin yin auren gara ayi kowa ya huta." Gaban Awaisu ya fadi jin Alh Mudi ya ambaci ganin yayansa da Saminu. To da wane idon zai kallesu ma. Shi dai Alh Mudi bai san me yake faruwa ba. Albarkacin Saminu yake ganin lallai Awaisu ma mutumin kirki ne kamar yadda ya kula a dan zaman da yayi dasu. Bai sami damar komawa gida ba sai bayan sati biyar ana hutun Good Friday da Easter Monday. Haka ya tafi jiki babu kwari saboda rashin sanin yadda zai tunkari dan uwansa da maganar auren Gimbi. Gashi Alh Mudi yace su same shi a gidansa na Kano. A son ransa ayi bikin bayan sallah karama tare da na babban dansa wanda suke a Kanon tare da babarsu uwargidan Alhaji. ***** Kwanansa biyu da dawowa ya rasa abin da ke masa dadi kuma ya kasa fadawa kowa. Maamu tayi fadan da magiya duka yaki cewa komai. Gashi yana matukar son Gimbi baya fatan rasata. Da daddare yana kwance a dakinsa Harisu ya shigo. Ya tashi zaune amma ya kasa cewa komai. Harisu yayi murmushi yana kallonsa. Sai da ya zauna a gefen katifar dakin ya soma magana. "Yanzu ni kake gudu saboda ka soma aiki a Abuja kayi kudi ko. Kana ganin kafi karfinmu." Awaisu ya zaro ido a razane "Yaya me ya kawo wannan zancen kuma? Wallahi ba haka bane. Allah Ya kiyaye. Bana fatan abin da zai kawo min tunani makamancin haka" Harisu ya daure fuska "haka kawai za ka fara guduna ne idan ba kana tsoron a ganka tare da talaka irina ba." Idanun Awaisu tuni suka yi ja saboda rashin jindadin kalaman yayansa. Shi da ya dauki Harisu uba yaushe ma irin wannan tunanin zai zo masa. "Wata matsalar ce daban Yaya" Ya fada a raunane. Harisu yayi dariya a zuci domin ya samu Awaisu ya fada tarkon da yayi masa na son jin damuwarsa. "Ina jinka, menene matsalar da take hanaka walwala a gidan nan?" Babu amfani cigaba da boyewar shiyasa ya fada masa maganar da yaji sunyi da Saminu da kuma wadda suka yi da Alh Mudi. Wani dogon numfashi Harisu ya ja. Ya jima yana tunani kafin ya soma magana cikin nutsuwa. "Kai ba yaro bane da zan ce baka san abin da kake yi ba. Sannan ka wuce ayi maka auren dole. Duk yadda nake son ka auri Mardiya ba ni zan zauna maka da ita ba. Saboda haka nagode da ka fada min da wuri kafin ayi auren muji kunya. Zanyi kokarin fahimtar da Saminu. Kuskurena ne da ban fara maganar da kai ba na fada masa" Ko bai fada ba yasan ransa a bace yake kawai ya danne ne "Kayi hakuri Yaya. Itama Gimbi tana da kyawawan halaye idan ka ganta ....." Bai karasa ba Harisu ya mike batare da yace komai ba yayi hanyar fita. Tunaninsa bai wuce yadda zai fita kunyar Saminu ba. Tsayawa yayi ba tare da ya juyo ba yace "ka shirya muje Kanon gobe kafin lokacin komawarka aiki." ***** "Zancen banza kai, ina Awaisu ina 'yar masu kudi. Ko kuwa so yake ya janyo ace yayi auren jari? To ma a ina yake tunanin ajiyeta idan anyi auren. Yaushe ma ya fara aikin da zai jajibo aure irin wannan" Maamu ce take ta fada bayan Harisu ya sanar da ita da Baaba batun tafiyarsu Kano neman aure. Haka tayi ta fada yana bata hakuri da nuna mata magana kawai zasu je yi ba auren za'a daura ba. Ranar da suka isa Kano Saminu jiki a sanyaye ya tarbesu. Wannan ya dagawa Harisu hankali ko har Alh Mudi ya sanar dashi komai. Baya son abin da zai taba alakarsu ko kadan. Shi Awaisu dama ya kasa kallonsa ma. Tunda suka zo yake sunkuyar da kai. Bayan sun dan huta ne suka zauna tattaunawa. A nan Saminu ya dubi Harisu "Alh Mudi yazo gidan nan da kansa akan yana son na bawa dansa auren Mardiya. Sanin cewa munyi magana da kai nace na bayar da ita ga Awaisu. Shine yayi min wani bayanin daban da ban gama fahimta ba " A kunyace Harisu ya fada masa abin da ke faruwa. "Kayi hakuri abokina, bani da masaniya akan hakan. Da tun farko bazan bijiro da maganar hadasu ba" Awaisu duk sai yaji babu dadi. Yanzu da Alh Mudi baizo nemawa dansa ba shikenan ya bata zumuncin abokan. Muryar Saminu ce ta katse masa tunani "Babu komai, ai kaga yadda Allah Yake nuna ikonSa. Sai muje gidan ka fada masa ka bada auren Mardiya ga Fawaz a matsayin waliyinta tunda bani da dan uwa namiji. Shi kuma Awaisu sai na nema masa auren Gimbi" Sai a lokacin Harisu yayi murmushi hankalinsa ya kwanta ganin Saminu bai dauki abin da zafi ba. Washegari kuwa suka dunguma sai gidan Alh Mudi aka daidaita magana. Sallah karama da sati biyu aka sha bikin Awaisu da Gimbi. Ganin cewa bai samu muhallin kirki ba Alh Mudi ya bashi gida da sunan Gimbi a Abuja inda zasu fara zama kafin ya sami nasa. Ita kuma Mardiya suka tare a Kaduna ina Fawaz yake aiki. ***** *Bayan shekara 12* Cikin shekarun da suka gabata Awaisu ya sami budi sosai. Domin har gida ya gina kato a Abuja yana shirin tarewa. Inda Allah Ya kara taimakonsa shine kasuwanci da yake yi. Duk da yana aiki ga rashin lokaci haka ya sami yara biyu 'ya'yan kawunan sa da ya budewa shago suke sayarda atamfa da shadda. Abu kamar wasa sai da ya hada shaguna hudu a jere a Wuse market. Ga kwazonsa a wurin aiki yasa ya sami mukamin manaja a bankin. Gidan Harisu kuwa yasha gyara sosai har mota ya saya masa sannan ya kara masa jari. Zamansu gwanin sha'awa. Tsakaninsu da Gimbi babu wata matsala. Dayake itama aikin bankin take yi bata da lokaci na zuwa Fika sosai. Yaransu hudu babban ciki Haris, sai Daula mai sunan babar Gimbi, Amir mai sunan Alh Mudi da kuma auta Sa'ad suna kiransa Mu'allim. ***** A gajiye Awaisu ya shigo bayan isha yaran suna ta murnar dawowarsa daga Fika. Sai da ya gama dasu ya wuce dakinsa. Sauri yake yi idanunsa su gane masa matar da yake jin bazai taba iya hadata da kowa ba saboda irin son da yake yi mata ga kuma albishir a bakinsa. Taci kwalliya tayi kyau sosai tazo ta tarbe shi tana murmushi "Ashe ka shigo maimakon ka kira kafin ku karaso na hada maka ruwan wanka" Ya shafi gefen fuskarta yana murmushi "kada ki damu, zo ki zauna kiji albishir din da nazo miki dashi har biyu. Dayan ina hanya akayi min waya aka fada min" Kaskon turaren wutan da yake gefen gado ta dauke sannan ta dawo ta zauna kusa dashi yana rungume da ita yayi ajiyar zuciya. "Gimbina Allah Ya yarda. Visa dinku ta fito" Ta dago kai da sauri cikin farinciki "wace visa kuma?" "Dama na boye miki ne sai komai ya tabbata. Na biya muku Hajji ke da Yaya Harisu, Baaba da Maamu. Sai Yaya Zakiyya tunda su Anti Baraka da Ummu mazansu sun kaisu. Kinga za ta tayaki kula dasu Baaba. Albishir na biyu kuma kuna dawowa nake so mu tare a Apo. To babban abin jindadin shine dasu Maamu zamu tare" Shiru yaji Gimbi taki dagowa bare tayi magana. Ko da ya dago kanta hawaye take yi sosai. Wani sonta ne yake shigarsa domin yasan kukan farinciki take yi. Rungumeta yayi yana shafa bayanta. "Dama nasan zakiyi murna sosai Gimbina. Shiyasa ban fada miki batun tafiya Hajjin ba sai da na gama. Tunda kinga ni naje har sauu biyu kuma last year munyi umara tare dake. Shiyasa bazan bi ku ba. " ya cigaba da cewa "Kuma fa yadda naso har da Baaba zamu tare. Sai dai lalurar idonta yasa Yaya yaki yarda. Shine na hakura ba don naso ba. Burina ya cika zan dawo da Maamu kusa in kula da ita. Itama taji dadin arzikin da Allah Ya bani. Ta dade tana jin nauyin su Baaba da Yaya Harisu. Duk da naso hadawa da Baaba hakan bai samu ba. Amma zan dauko Rumana. Gimbina da ina da yadda zanyi fa wallahi Yaya Harisu ya dena fita neman kudi. Komai ni zanyi masa" Can kasan makoshi tace "uhmm hakane." Domin ji take yi ya cikata da surutu mara kan gado. Mikewa yayi ya shiga bandaki domin yayi wanka ko zaiji saukin gajiya. Yana shiga Gimbi ta fice ta tafi dakinta ta rufe kofar da mukulli. Gadonta ta hau ta saki kuka cikin tashin hankali. Ko da wasa bata taba kaunar zama da uwarmiji ko dangin miji ba. Can daga nesa dai yayi musu kyauta suna kauye ba sai sun rabesu ba. "Tabdi, akwai matsala. Matar da ko Hausar kirki bata iya ba sai anyi magana tayi ta yankare hakora tana murmushi. Shine don kana jin ka fara kudi zaka dauko min su ka kawosu ko neman izini na bakayi ba. Da sake Awaisu....bana cikin matan da za'a hada da uwarmiji ace mu zauna lafiya gida daya" Dankwalinta tayi jifa dashi ta rasa me yake mata dadi. Ita fa shi kadai take so ba danginsa ba. Duk halaccin da tayi masa ta aureshi talaka ko gidan zama bashi dashi. Shine yanzu arzikin nasa kuma sai sun raba tare da wadda bata nan lokacin da suke nema. Ta hana kanta sukuni tana fita aiki duk domin ta taimaka masa. Ba don kada ace tayi sharri ba ma sai tace gabadaya gidan Harisu wari yake yi mata idan taje Fika. Shiyasa bata son zama idan taje.6*KASHE FITILA*💡7 *Batul Mamman*💖 Gani tayi kukan bazai kaita ko ina ba ta yanke shawarar washegari zata kira Mama ta fada mata. Dole ma a dauki mataki don ba bauta tazo yiwa kowa ba. Shirin bacci tayi sannan ta koma dakin nasa. Kwance ta same shi akan abin sallah da gani sallah ya idar bacci ya dauke shi. Tausayinsa kuma taji, ya mayar da kansa tamkar agogo. Bashi da hutu kwatakwata duk domin ya farantawa su Maamu. Tsaki taja a fili tana tunanin yadda zata bullowa lamarin da ya tunkaro ta. "Saboda zan kawo mahaifiyata gidana shine kike tsaki haka Gimbi?" Muguwar faduwar gaba taji. Shi kuwa ya mike tsaye yana kallonta rai a bace. Bakinta yana dan rawa tace "haba my dear, kada kayi min mummunar fahimta mana. Dazu da kanka ka gani ina murna harda kukan..." "Kukan bakinciki ba. Da farko har ga Allah nayi zaton dadi kika ji ganin yadda na damu da yanayin da mahaifiyata take ciki. Bata da wurin da zata kira gidanta. Sai da nayi wanka na biyo bayanki naji kina kuka sosai a dakinki." Rasa bakin magana tayi shi kuwa ya cigaba da magana cikin kunar rai "Duk duniya bayan Maamu babu wanda ya cancanci kyautatawa daga gareni kamar Yaya Harisu. Ban taba boye miki asalina ba. Amma abin mamaki kina nuna bacin ranki akan kyautatawar da zanyiwa wanda suka zama jigon rayuwata. Idan bazaki iya zama dasu ba sai na auri wadda zata iya" Tun da ya fara magana bata tanka shi ba sai yanzu da ya ambaci kishiya. "Kayi kadan kace zaka auro wata ka ajiye a gidan nan. Ko ka manta cewa nawa ne. Suna na ne a jikin takardun gidan" "Dadin abin nima ina da nawa. " Ta turo baki cike da tsiwa. Tsiwar da a da take bashi sha'awa idan tayi "Haka nan zaka kare rayuwarka kana yiwa wani kato bauta. Sai shegen aure da tara iyali. Kai kuma an barka da siyan shinkafa da ragon suna" Shiru yayi har sai da ta gama maganarta tukunna sannan ya tako gabanta fuskarsa babu annuri ko kadan. Ja ta rinka yi da baya yana binta "Yaya Harisun ne kato Gimbi?" Ya fada a hankali amma kana jin muryarsa har wani rawa take yi saboda bacin rai. Duk da a tsorace take amma ta kule da yadda yake zare mata ido akan 'yan uwansa. "Karya nayi ba katon bane? Ko baiyi biyunka ba" Bata karasa magana ba taji ya gwabje mata baki. Nan take jini ya soma zuba saboda fashewar lebenta na kasa. Cikin kuka tace "Awaisu ni ka fasawa baki?" "Idan baki fita daga dakin nan ba sai nayi miki abin da yafi wannan." Murya ta soma dagawa tana kuka "babu inda zani, gidana ne ba naka na. Idan kaji haushi ka fita ka koma naka" Fitar yayi zuciyarsa tana tafasa. Wai akan iyayensa da bashi da tamkarsu shine Gimbi take yi masa abin da bai taba tunanin zata aikata ba. Lallai ba'a shaidar mutum. Yasan halinta na kyankyami da ji da kai. Shiyasa yake mamakin irin son da take masa farkon haduwarsu. Falo yaje ya samu yaransa uku sunyi bacci sai Haris da yake karasa homework. Tashinsu yayi daga su sai kayan baccin jikinsu suka fice. Motarsa ya bude suka shiga suna tambayarsa inda zasu je. Bai basu amsa ba ya rinka dannawa mai gadi horn. Yana budewa ya fita a guje. Karar horn din ce ta fito da Gimbi. Tsoronta kada da gaske ya fita daga gidan. Sai dai abin mamaki ba shi babu yaran. Nan fa hankalinta ya kara tashi. Mai aikinsu Laminde ta shure da kafa tana bacci itama a falon ta tambayeta ina su Daula "Hajiya gasu nan suna hamok. Jiransu nake yi su karasa aje a kwanta." Ta galla mata harara "ina kika gansu. Aikin banza babu abin da kika iya sai bacci" Waje ta fita inda mai gadi ya tabbatar mata da yaran Alhajin ya fita. Haka ta rinka kiran wayarsa yaki dauka. Karshe ma kashewa yayi yana kallon yaransa suna bacci a makeken gadon dakinsa. Gidansa na Apo ya tafi dasu. ****** Da sassafe yaji ana buga gate ya leka ta taga. Maigadinsa ya gani yana ta washe baki ya budewa Gimbi gate ta shigo. Ko rufe kofar motarta batayi ba ta fito ta shiga gidan cikin sauri. A falo ya sameta yace kada ta tasar masa yara. "Wane irin wulakanci ne zaka daukar min yara cikin dare" "A iya sanina lokacin da muka tare a gidan nan ke kadai kika shigo sai akwatunan kayanki. To mene ne na bacin rai don na kwashe yaran da jinin Maamu yake yawo a jikinsu" "Wai duk saboda maganar jiya da bata taka kara ta karya ba kake min wannan cin kashin harda fasa min baki" Ya tabe baki "ina jin baki san girman uwa bane" Neman sulhu take yi domin tun aurensu basu taba samun sabani irin haka ba. Kwantar da murya tayi ta soma magana "Duk laifinka ne, ta yaya zaka shirya kawo Maamu batare da neman izinina ba? Nima fa ina da hakki akan ka. Kuma abu irin wannan sai ka fara shawara dani kaji nawa view din" "Neman izininki? Wai dama haka kike ne ko kuwa sabon salo ne kika fito dashi kawai don baki son dangina. Ba fa tun yau na san kina nuna musu kyama ba. Sharewa kawai nake yi saboda babu wanda ya taba korafi cikinsu." "Kaga ni ba rigima nazo muyi ba. Maganar fahimta nazo da ita. Idan kana so ka ginawa Maamu sabon gida a Fika is up to you. Amma batun mu zauna tare is out of the question. Zama da suruka baya taba haifar da alkhairi" Duk yadda yake son ta a daidai wannan lokacin yayi nadamar aurenta. Rasa bakin magana yayi yace mata kawai ta fita idan ta gama. Ganin wankin hula zai kaita dare ta ja motarta ta tafi gidansu. Tana kuka ta zayyanawa Mama abin da ya hadasu. Mama ta dubeta sosai ta girgiza kai. "Idan kika kure Awaisu ya sakoki zaki gane kudi da gata aikin banza ne idan aka rabaka da iyalinka. Ke da ya kamata ki nuna masa kinfi kowa farinciki shine zaki bata masa rai akan mahaifiyarsa. To yayi miki adalci ma da bai hadoki da takarda ba. Shashashar kawai. Idan ma zugaki akeyi ki sani aljannarki tana karkashin kafar mijinki. Shi kuma tasa tana tare da mahaifiyarsa. Kada ki zama mace mai kashewa mijinta fitilar rayuwarsa Gimbi. Uwa haske ce, uwa rahamace. Da kika shiga matsala ai gaki a gabana." "Mama yanzu goyon bayansa kike yi" "Ki kiyayeni Gimbi. Kuma ki wuce yadda kika bata mishi rai ki bashi hakuri ku sasanta. Idan Alhaji yaji maganar nan ki kuka da kanki. Kinsan halinsa sarai. Bar ganin yana sonki hakan bazai hana ya saba miki ba" Dukar da kai tayi ta gama jin fadan Mama ta tashi ta koma sabon gidan. Amir ne ya fada mata baban nasu yana daki ta shiga da sallama. Kafin ya amsa ta durkusa gwiwoyi a kasa a gabansa tana kuka. Kamar ya basar sai dai Gimbi matsayinta daban a zuciyarsa. Tasowa yayi yazo gabanta. Cikin kuka da nuna nadama ta rinka bashi hakuri da nuna masa ta gane kuskurenta. Kukan da tayi tana ajiyar zuciya yasa dolensa ya hakura tare da yi mata nasiha. Cikin dan kankanin lokaci ta shawo kansa suka daidaita. ***** Zaune suke cikin daki su biyu ta dubi kanwar Mama wadda take binta bayan ta bata labari. "Anti Bebi wannan ita ce matsalar da ta tunkaro ni. Kuma Mama ta bashi goyon baya" "Ki bar komai a hannuna 'yata. Indai ina raye babu wanda ya isa ya takura miki. Tun da dadewa nace kizo muje a mallaka miki shi a tafin hannuki kika ki yarda ke dadi miji. Yau ga irin abin da nake ta hango miki ya faru. Ke ko babu boka babu malam yayi kadan kinji ko. Shi din me? Mijina na uku ma duk taurin kansa sai da ya koma albashinsa ma a hannuna yake balle wani Awaisu." Kalmar karshe ta sosawa Gimbi rai sai dai biyan bukata yafi dogon buri7*KASHE FITILA*💡8 *Batul Mamman*💖 A kwanakin da suka biyo baya Gimbi ladabi take yiwa Awaisu sosai. Tsakanisu tamkar wani abu bai faru ba. Tarewarsu a sabon gidan da ake jiran sai bayan babbar sallah idan sun dawo daga hajji kuwa tuni ta rushe. Kusan duk abin da suke bukata daga tsohon gidan sun gama kwashewa. Gimbi ta gyara dakin da Maamu zata zauna tamkar wata amarya. Dayake komai sabo ne idan ka shiga kamar kada ka fita. Dakin Daula da taci burin gyaransa ma saboda tilon 'yarta sai da ta matsawa Awaisu aka karo wani gadon a matsayin na Rumana. Karshe ta yiwa Maamu da Rumana dinki kala biyar biyar ta kawowa Awaisu. Shayi yake sha yana duba wasu takardu ta kawo ledoji manya biyu ta ajiye tare da durkusawa a gabansa. "My dear ga tawa 'yar gudunmawar" Daya daga cikin ledojin ya bude. Kaya ya gani a dinke duka super holland har biyar. Ya kalleta da alamar tambaya. Rausayar da kai tayi tana kifta idanu alamun zata yi kuka. "Nasan babu wani abu da zanyi ya wanke wautar da nayi maka kwanakin baya. Amma don Allah ina mai sake neman afuwarka. Na tsorata ne da jin labaran zama da surukai har naso bata aurena akan labaran wasu da nake ji" Tayar da ita yayi sannan ya matsa yadda zata iya zama kusa dashi. Ya kama hannunta ya rike. "Bazanyi miki alkawarin cewa kullum cikin zaman lafiya zamu kasance ba idan Maamu tazo. Amma ina so ki sani ba wai don ita ta haifeni ba, Maamuna bata da rigima ko kadan. Mace ce wadda yanayin kaddarar rayuwa ta sanya mata mugun hakuri da kawaici. Ina jin ba domin Baaba ba da a sangarce ma zan tashi saboda tsabar hakuri irin nata. Tabbas banji dadin abin da kika yi ba amma na hakura. Da kinsan yadda nake mafarkin zama inuwa daya da ita nasan baza kiyi waccan maganar ba tun farko" Sake bashi hakuri tayi tana kuka da alkawarin gyara kuskurenta ta hanyar bin Maamu sau da kafa. ***** "Anti Bebi lokacin tafiyarmu sai kara matsowa yake fa. Ni wallahi bana son yin tafiyar da mutanen nan. Dukkaninsu babu wata alamar wayewa. Muje airport su janyo a rinka kallona" Dariya sosai Anti Bebi tayi sannan ta soma magana da shakakkiyar muryarta wadda tsabar gayu da make murya wurin janyo hankalin maza ta koma haka "Ki samu ya barki muje wurin da nake fada miki. Kuma kiyi a hankali kada uwarki taji labari. Kinsan dai ba shiri muke da ita ba" Gimbi ta tsuke baki jin an zagar mata uwa. Ita kanta bata fiye shiga sabgar Antin tasu ba sai da wannan abin ya faru. Yadda Anti Bebi da Mama basa kama a fuska haka suka bambanta a hali. Yanzu haka aurenta na shida kenan. Abin mamaki masu kudi take aure suyi ta mata bauta. Sai ta tara abin da ta tara ta nemi sanadin da zasu saketa. Mama ta gaji da fada da nasihar ta tsame hannunta daga lamuran kanwar ta ta. "Shi kuma mijin naki ki barni da shege, idan Wangesi na tsangaya ya fara aiki akansa ina fada miki sai juya alkalami yafi miki wahala akan yadda zaki rinka juya shi son ranki. Shi din banza..." Mikewa Gimbi tayi tana rataya jaka rai a bace. Anti Bebi tace "Me aka yi kuma zaki tafi muna magana" "Haba Anti, zamana a nan kin zagar min uwa kin koma kan mijina. Ina sonsu bazan jure zaginsu da kike yi ba" Dukan cinya tayi irin na matan da suka ga jiya suka ga yau. "Karyar banza, Amina dai zan yarda kina sonta tunda ita ta haifeki. Amma indai Awaisu ne karya kike yi Gimbi. Duk matar da take son mutum take kin iyayensa ko 'ya'yansa na wani auren kallon munafuka nake yi mata. So da ya amsa sunansa shine ki rungumi duk abin da mijinki ya nuna yana so ki taya shi ririta shi" Ganin Antin tana ya6a mata magana ta fice ko sallama babu. Dama can ba wai tana ganin mutumcinta bane. Tun suna yara sun san tayi kaurin suna a dangi saboda fitinarta. Yanzu ma dole ce ta kawota. Zata nemarwa kanta mafita. ***** Bayan kwana biyu Awaisu yake sanar da ita cewa nan da sati uku su Maamu zasu taho Abuja domin ta nan zasu tashi. Kuma an kusa fara dibar alhazai. Sanan za'a taho da Rumana tun yanzu domin taya Laminde zama da su Haris da kuma sabawa ita ma da gidan. Da murnarta ta dauko takarda tana yi masa list na abubuwan da take so a karo musu na kayan abinci da kayan masarufi domin tarbar baki. Yadda take yi masa dole duk wani sauran zargi da bacin rai da yake ransa ya kawar dashi. Bayan ya fita a gigice ta kira Anti Bebi har ta manta abin da ya faru tsakaninsu. Ita kuwa tana ganin kiran taki dauka. Sai da ta kira yafi sau biyar sannan ta amsa tana magana da kyar wai ita a dole anyi mata ba daidai ba. Gimbi bata yi fushi ba ta fada mata yadda suka yi da Awaisu. Anti Bebi tace idan zata iya ta je ta sameta a gida washegari su tafi wani kauye a Nasarawa state inda Wangesi na tsangaya yake. Da daddare kuwa ta karantawa Awaisu karya da gaskiya saboda kada ya ga bata dawo gida da wuri ba daga bankin da take aiki. Shi kuwa sanin yanayin aikinsu bai kawo komai a ransa ba sai addua da yayi mata. Washegari tana zuwa wurin aiki tayi karyar ciwon ciki ta samu manaja ya yarje mata komawa gida. Daga nan bata zame ko ina ba sai gidan Anti Bebi. Ko zama batayi ba suka kama hanya. Dreban Anti Bebin ne ya kaisu. Tayi mamaki sosai yadda taji suna hirar malamin tsibbun tare dashi. Ashe shine ya hadasu ma. ***** Wangesi ya bata layu da guraye da zata saka a cikin gidan wanda su Maamu suna zuwa zata ji ta tsani gidan saboda zafin da zaiyi mata. Saboda yarda da shirkarsa da yayi har alkawarin dawo mata da kudinta yayi idan Maamu ta iya kwana uku a gidan batare da ta matsa a mayar da ita Fika ba. Gimbi murna ba'a cewa komai. Tana zuwa gida tayi duk yadda yace ayi da kayan da ya bata ta zauna jiran lokaci. Ranar da zasu zo ta kama asabar. Tun kafin asuba ta farka ta shiga kitchen tana ta dafa kayan tarbar baki. Laminde ma a nan ta sameta. Awaisu kuwa zuciyarsa fes ganin ta sake tana nuna masa ta fishi murnar zuwansu. Dama dreba ya tura aka dauko su. Motar na shigowa yaran suka fita a guje suna murnar ganinsu. Haris tamkar ya shige cikin Harisu don murna. Ba karamin son kawun nasa yake yi ba. Maamu ce karshen fitowa daga motar. Kafar dama ta fara saukewa cikin sanyin muryarta tace "Bismillah tawakkaltu alallah"8 *KASHE FITILA*💡9 *Batul Mamman*💖 Awaisu da yaransa duk da murnarsu suka koma cikin gidan tare da su Baaba. Maamu ce karshen shigowa. Ta tsaya a waje ta karewa gidan kallo. Yau danta wanda ko rabin fuloti bai mallaka ba shekarun baya da suka wuce shi ne da dankakaren gida irin wannan. Addua tayi sosai ta neman tsari da kariya gareshi da zuri'arsa da kuma sanya albarka ga samunsa. Sai da ta gama ta shigo ciki. Nan ta tarar da su Baaba Hure suna ta kalle kallen gida su ma suna yabawa. Kayan abinci Gimbi da Laminde suka rinka fitowa dasu suna jerawa a tsakiyar katon kafet din falon. Sai da ta gama sannan tazo ta durkusa har kasa tana gaishesu tana satar kallon fuskar Maamu. Wangesi dai yace gidan zafi zaiyi mata da kanta zata nemi a mayar da ita inda ta fito. Wani murmushi tayi sannan ta cigaba da tambayar Rumana yaya mutan gida. Da yake Maamu banda amsa gaisuwa da kalmomi kadan ita ba Hausa ta iya ba shiyasa bata shiga hirarsu sosai. Baaba ma yau da gobe tasa Hausarta sai a hankali, ta iya amma sai ka zata ba bahaushiya ke magana ba. Haka Rumana da Zakiyya su duk da sun dan iya amma ba kamar Awaisu mai auren bahaushiya da kuma Harisu dan kasuwa ba. Bolanci yafi kama bakinsu. Hirar dai aka ake yinta wani abin sai kaci dariya. Idan kaga Gimbi a tsakiyarsu sai ka rantse ko goyo suka nema zata yi musu. Shiyasa basu taba korafi akan ta ba. A ganinsu yanayin aiki ne yake sawa bata zuwa Fika sosai. Dakin da aka tanadarwa Maamu nan Baaba tayi masauki tare da Zakiyya. Gado ne kato wanda zai ishi mutum hudu ma. Ba karamin kashe kudi Awaisu yayi ba. Harda tv ya saka mata da fridge. Baaba da aka soke zuwanta Abujan itama yayi shirin sake gyara mata nata dakin kafin su dawo daga Hajji. Ranar a wurinsu ya yini shi da Harisu. Da safe zai tafi aiki ya bar sallahu cewa drebansa zai dawo sai ya kai Harisu kasuwa ya ga shagon nasa. Kwananusu biyu babu wata matsala da ta taso. Ranar laraba Awaisu zai tafi aiki Gimbi take sanar dashi ta dauki hutu na tafiya Hajji. Ya nuna mata jindadinsa tunda ga baki dama a gidan. Bayan fitarsa bai dade ba Anti Bebi tazo. Da yake safiya ce babu wanda yasan tazo ta shige dakin Gimbi. Mayafinta ta cire wanda ya bayyana siraran kitson da akayi mata da karin gashi. Dama ita da wuya tasa dankwali. Dan mayafi ne guntu shara shara kullum take fama dashi. "Ke kuma sai naji ki shiru babu wani jawabi game da bakinki?" Gimbi ta tabe baki "hmmm Anti wannan anya ba kudina yaci ba. Kullum naje dakin sai tayi ta murmushi babu alamun ta soma gajiya da gidan. Ita fa fuskarta kullum a sake kamar mara lafiya. Har tunani nake ko aljanun nan ne masu sa dariya basuyi mata kamu sosai ba aka tsaya a murmushi" Dariya sosai Anti Bebi tayi "Shegiya Gimbi, ashe kema baki da mutumci, yarinya tayi gadon uwa. Kuma ina mai tabbatar miki indai zakiyi yadda nake yi to babu wanda ya isa ya taka ki" Gimbi shiru tayi. Idan da Mama zata ji abin da take yi yanzu Allah kadai Yasan fadan da zatayi mata. Balle kuma Alhajinsu da ya dauki son duniya ya dorawa Awaisu. Shi a ganinsa ba karamin dace yayi da surukai ba. Sai bayan azahar Anti Bebi ta dauki mayafinta "Tashi muje na ga bakin naki sai na wuce daga can. Idan anyi sati babu chanji da kaina zan koma wurin Wangesi" ***** A falo suka tarar dasu harda su Haris sun dawo sun tsaya basu labarin makarantarsu. Anti Bebi kallo daya tayi musu taji babu wanda yayi mata a cikinsu. Duk da cewa zata yi sa'ar Ummu kulsum 'yar Baaba Hure ta uku domin ita ce autarsu Mama amma daga tsaye ta dan dago musu hannu "sannunku" Zakiyya ta amsa mata tana yi mata wani irin kallo. Wannan mata duk inda ta fito akwai rashin kamun kai a tattare da ita. Labaran da akeyi a tashar NTA Hausa shine ya dauki hankalin Baaba Hure ga Rumana ta biyewa su Amir suna ta hayaniya. Remote din tv ta dauka zata karo sautin yadda zata ji jawabin mai kawo rahoton. Tana cikin dannawa Anti Bebi ta kwashe da dariya "Mhmmm ashe harda su kaza a cin danko. 'Yata kinyi sa'a su o'o hannu baya gani ya kyale. To gaskiya a dage a sayo musu computer" Baaba Hure ji tayi kamar an zuba mata ruwan zafi saboda yadda zuciyarta ta harzuka. Bata bukatar wani bayani tasan cewa da ita wannan bakuwar take. Ajiye remote din tayi jikinta babu kwari tana jiran amsar da Gimbi zata bayar sai ji tayi tace "Waya ga dan wake a hotal" Zakiyya da Maamu sai dan murmushi sukeyi. Ita Zakiyya duk da tana dan jin Hausa ko kadan bata fahimci inda zancen nasu ya dosa ba balle kuma Maamu. Baaba Hure ganin haka itama sai ta biye musu tana murmushin. A iya saninta Gimbi bata san cewa ita asalin bahaushiya bace. Kuma yanayin da Hausarta ke fita da wuya ace tana gane karin magana indai ba yarenta bane. Gara ta nuna musu itama bata ji ko don ta ga iya gudun ruwansu. A lokaci daya kuma tausayim Maamu ya cika mata zuciya. Ashe Gimbi ba son Allah da Annabi take yi musu ba. Indai hakane kuwa akwai matsala wannan zaman da zata yi a gidan. Da yamma da Harisu da Awaiau suka shigo. Baaba taso ta sanar da Harisu abin da taji sai kuma tayi tunanin kada ta zama uwa mai sa ido. Daga faruwar abu daya bai kamata ta yanke hukunci akan cewa Gimbi ba mutuniyar arziki bace. Hakan yasa ta fasa cewa komai. ***** Bayan kwana hudu aka kirasu sune diba na biyu. Awaisu da drebansa sukayi mota biyu aka kaisu Airport. Basu dawo ba sai da jirginsu ya tashi. Madina suka fara wucewa. Tun a hanya Gimbi ta soma zazzabi mai zafi da amai. Suna isa aibiti aka kaita likita yace taci wani abu ya bata mata ciki. Duk rashin kirkin da taso gwada musu sai ta koma abar tausayi suna jinyarta. Kwanakin Madina kaf bata ji dadinsu ba. Haka suka je Makkah can ma bata da wani kuzari. Wannan Hajjin dai bata ji dadinsa ba kwata kwata. Daga zazzabi ya warke sai mura mai zafi da ciwon wuya. Haka sukayi kwana talatin suka dawo da ita duk ta fige sai mugun nufi a zuciya. ***** Sai da sukayi sati da dawowa sannan suka koma Fika aka bar Maamu da Rumana. Gimbi ce ta samar mata makaranta wadda bata da nisa sosai da gidansu. Makaranta ce mai tsada mai kyau don kawai ta burge Awaisu. Da taga hankalinsa a kwance yake da abubuwan da take yi ta koma gidan Anti Bebi tana korafin rashin aikin maganin Wangesi. "Kwantar da hankalinki naje na same shi. Yace wannan magani ranar da suka je gidan wani abu ya bata sihirin da yake ciki." Wata leda ta dauko ta mikawa Gimbi. "Ga wannan yace ki dafawa mijinki abinci dashi. Daga ranar a hankali duk wani so da kulawa da yake yiwa uwar tasa zai fara fita daga zuciyarsa. Sai kiyi amfani da wannan damar ki gasa mata aya a hannu. Da kanta zata kwashi kafarta ta gudu gashi an daure bakin" Karba tayi jindadi ya bayyana a fuskarta "Ina fata wannan karon a dace. Idan ba haka ba kuma zanyi maganinta da kaina. Shiru shirunta irin na munafukai shi nafi tsana. Kinsan irinsu abin tsoro ne. Ga wannan yarinyar da suka zo tare mai cin tsiya. Ina tsammanin horon yunwa zan fara yi musu a gidan" *KASHE FITILA*💡10 *Batul Mamman*💖 Ranar laraba da daddare Gimbi da kanta tayi girki sabanin yadda ta saba saboda yanayin aikinta Laminde ce take yi. Maganin da aka karbo mata ta juye shi tas a miyar Awaisu ta kara maggi. Da ya dawo dakin Maamu ya fara zuwa ya gaisheta tare da zama zai fara hira ta dube shi duk da alamun gajiya a tare dashi "Ka tashi kaje kaci abinci ka huta na yafe hirar nan" "Maamu ni sai kiyi ta korata. Da Yaya Harisu ne ai sai kin gama sauraronsa" "Sannu baban kishi. Yanzu dai ka tashi, ka ga matarka itama ba zama take yi ba. Dan lokacin naku kuma bazan so na hanata sakewa ba. Ni ban zo gidan nan don takura muku ba. Abokan hirar nawa ma abinci suka tafi ci. Yanzu zaka ga sun dawo" Tashi yayi rike da coat dinsa a hannu yace zai dawo bayan yaci abinci yayi wanka. Har ya fita tana cewa ta yafe hirar yau. Wanka yayi Gimbi ta biyo shi da abincinsa daki wai falon hayaniya tayi yawa. A haka tana yi masa hira ya cinye tuwon da ta zuba masa harda neman kari. Dadi ya kamata kuwa. Yanzu abin da ya rage kawai shine ta fara gwada aikin maganin. ***** Washegari saboda fitarsu aiki da zuwan yara makaranta tun asuba suke tashi ranakun aiki. Kitchen ta shiga ta aunowa Laminde shinkafa sannan ta fito da kazar da ta tafasa tun dare. "Kiyi min jallof din shinkafa taji alayyahu da busasshen kifi. Wannan kazar kuma pepper chicken nake so kiyi. Kiyi komai cikin sauri kinsan Abbansu Daula baya son jira." Laminde ta gyada kai "To Hajiya, amma shinkafar bazata ishemu har su Hajiya Babba ba da 'yan makaranta" Gimbi ta koma store din da yake cikin kitchen din ta dawo rike da wata karmasasshiyar doya. "Shinkafar ki dafa mana ni da yara da babansu. Wannan doyar kuma fate zaki yi muku ke da sauran mutan gidan" Laminde ta kalli doyar ta kalli uwargijiyarta. Ita dai tunda take a gidan ba'a taba yi mata wulakanci akan abinci ba. Wani lokacin ma ita Gimbi take barwa zabin abincin da za'a dafa. Kasa shiru tayi ta dan rausayar da kai tana kara kallon doyar da ta bushe "Wai Hajiya nace ba, uhmm ita Hajiya Babba nake nufi ki karo shinkafar saboda ita" Daure fuska Gimbi tayi "sunanta Maamu ba Hajiya Babba ba. Wannan so kike yi wani yayi zaton ni da ita uwargida da amarya ne. Anyway, itama faten zaki zuba mata naji ance tana son doya. Ga langa can da na karbo wurin Mama. Kinsan mutanen da suna son komai irin na zamaninsu. Shine na nace har sai da Mama ta bani cikin nata tun na aure. A ciki zaki rinka zuba mata abinci. Kuma kiyi sauri tare zamu fita zan aike ki" Kasa hadiyar yawu Laminde tayi domin tsananin mamaki. Langa ce da gaske ga kuma doya da akace ta zuba mata. Ko ita da take aiki yau tasan anso wulakanta ta bare uwarmiji. Magana take son yi amma sam bakinta ya kasa hada kalma ko daya. Tana ji Gimbi tace ita zata yi musu nasu girkin wanda suke tafiya dashi wurin aiki yaran kuma suje dashi makaranta. Ita kuma tace tayi sauri tayi faten kada su makara. ***** Rumana cikin sauri ta gama shirinta tsaf saboda bata so a jirata. Tun fara zuwa makarantarta kwanaki biyu da suka wuce tare suke fita da yaran gidan da Gimbi. Dreba ne yake kaisu makaranta ya wuce da ita wurin aiki. Tunda a banki take shiyasa suke yin sammako sosai. Ko da ta fito falo Mu'allim ne kawai Gimbi take bashi abinci a baki yana ta rigima shi bacci yake ji. Har kasa ta durkusa ta gaisheta sannan ta nufi dinning table inda kayan tea suke zata hada. "Dakata Rumana me zakiyi a nan?" Murmushi tayi ta kirata yadda yaran gidan suke kiranta "Mummy tea zan sha kafin su Haris su fito" "Kinga daga yau ki rinka zuwa wurin Laminde ki sha tea din a can." Bata ji komai a ranta ba tayi hanyar kitchen. Sake dakatar da ita Gimbi tayi "Kiyi sauri kisha ki fito kada ki makara" Dayake bata san sunan dreban ba sai tace "Mai kaimu makarantar har yazo ne? Bari na fadawa su Amir suyi sauri su ma" "A'a kina jina ko Rumana, makarantarku ba wani nisa gareta ba. Ki rinka shiryawa da wuri kina tafiya. Tafiyar da mukeyi da ke tasa ina makara kwana biyu. Gashi ba'a gama abinci ba. Idan kin dawo sai ki ci. Tea din ma ruwan zafin aka juye a girkin sai an dafa wani" Sai a lokacin Rumana taji wani iri a ranta. "To Mummy bari na tafi, sai kun dawo" Gimbi harda murmushi "yauwa Rumanan Abba. Allah Ya kiyaye kinji." Rumana ta dan tsaya jim ko zata bata kudi tunda sai hudu da rabi suke tasowa. Gimbi ta fahimci dalilin tsayuwar ta dan sake fuska "ko akwai wani abu ne Rumana?" "A'a babu komai. Na tafi" Fita tayi tana tafiya a hankali. Allah Yasa makarantar a bakin titi take kuma babu wuyar ganewa. Tafiyar minti shabiyar zata kaita idan tayi sauri. Iyayenta ne suka fado mata a rai taji kamar ta fashe da kuka. Bata san yadda zata fassara abin da Gimbi tayi mata ba. Tayi kamar minti biyar tana tafiya taji mota ta tsaya a gefenta. Horn da akayi yasa ta kalli motar. Mace ta gani tasha lullubi sai wata yarinya mai uniform irin nata. Da ta sake kallonta ta tuna ajinsu daya duk da bata san sunanta ba. Gaishe da matar tayi cikin hausarta. "Shigo mu karasa kin fito cikin sanyin nan ko rigar sanyi babu. Kada kiji tsoro ga Yusra ajinku daya tace min" Bayan motar ta shiga ta sake gaisheta sannan Yusra ta juyo "Sunanki Ummu Ruman Abali ko" Rumana ta gyada kai tana murmushi. Hira uwa da 'yar suka cigaba da yi har suka iso kofar makarantar. "Umma baki bani kudin break ba fa" "Yusra bana son wannan kashe kudin da kike son koya. Ga abinci nan a jakarki" Yusra ta sake kwantar da kai "Umma ko hamsin ce saboda siyan ruwa" Dari biyu maman ta mika mata "gashi ku raba da Rumana idan kun fito. Allah Ya bada sa'a" Rumana tayi mata godiya suka jera cikin makaranta tare da Yusra wadda take yi mata tambayoyi akan makarantar da ta baro. Da haka ta manta da bacin ran da ta fito dashi. ***** Duk sun gama shiri sun fito Awaisu ya tambayi ina Rumana. Gimbi tace "Ta tafi, wai makarantar babu nisa zata rinka tafiya da kanta." Bai ce komai ba suka fice saboda ya leka Maamu tana bacci. Bata farka ba sai karfe tara da kusan rabi. Sabanin yadda ta saba ganin tray din abincinta na safe yau babu komai a wurin sai wata langa da cokali makale a hannunta. Bata kula ba ta shiga bandaki tayi wanka. Sai da ta gama shirinta ta zauna shiru Laminde bata kawo abinci ba. Fita tayi falon taji gidan tsit alamun ita kadai ce. Komawa dakin tayi tana tunanin ina Laminde taje haka. Dama ita take tayata hira kafin yaran su dawo daga makaranta. Langar ta sake kallo bayan ta koma sai ta bude. Faten doya taci karo dashi yayi wani baki ya cure wuri guda saboda rashin wadatar mai. Haka aka yi shi kandas sai kan sauran kifin da Gimbi tayi musu abinci. Mayarwa tayi ta rufe zuciyarta tana karyata cewa wannan abincin nata ne.10*KASHE FITILA*💡11 *Batul Mamman*💖 Haka Maamu ta zauna har azahar bata ci komai ba ga yunwa tana ji. Tasan dai wurin biyu da rabi yaran suke tasowa daga makaranta. Kila su dawo tare da Laminde. Da wannan tunanin ta cigaba da zama har uku ta wuce. Karfe daya da rabi dreba ya kira wayar Gimbi ya sanar da ita zai je dauko su Haris. Ta umarce shi da idan ya daukosu ya taho dasu bankin su jira har ta tashi. Da farko wurin Mama tayi niyar cewa ya kaisu. Sai ta tuna zata iya cewa me ya hana su koma gida saboda Islamiyya. Ita kuma ko tana hauka bata jin zata taba tura yaranta gidan Anti Bebi. Ita din ma da take zuwa yanzu don biyan bukatar kanta ne kawai. Shi dai dreba sai mamaki yake yi amma haka nan ya dawo cikin banki ya sami inuwa yayi parking. Nan fa daga mai kiran fitsari sai mai jin yunwa ko bacci. Haris da ya fisu hankali korafin rashin zuwa islamiyya yake yi. A haka suka yi ta zama har bacci ya kwashesu. ***** A makarantarsu Rumana kuwa da break sai ga Yusra tazo ta bata naira dari kamar yadda Ummanta tace su raba. Da kyar ta karba duk da cewa yunwa take ji. Yusra tayi mata tayin abinci taki karba shima. A ganinta basu yi sabon da zata ci mata abinci ba bayan ita bata zo da nata ba. Karfe hudu da rabi suka fito ta nufi titi za ta tsallaka. Yusra ta dakatar da ita "Rumana ki jira Umma tazo. Yanzu za ta biyo idan ta ajiye kannena a islamiyya" "Idan na tsaya za'a yi min fada a gida." Daga haka suka yi sallama ta tsallaka daya gefen ta kama hanyar gida. Tafiya ta rinka yi tana jan kafa saboda tsabar yunwa. Yau da azumi take yi ba karamar wahala zai bata ba. Daren jiya tun takwas da rabi tayi bacci ko abincin dare bata ci ba. Gashi yau bata samu ko ruwa ta sha ba. Da sallama ta tura kofar falon sai dai babu alamar akwai mutane a gidan. Dakin Maamu ta wuce. Tana taba kofar dakin Maamu tayi saurin tura langar faten karkashin gadonta. Tsoronta kada Rumana ta gani har wani yaji ayi tunanin Awaisu ko matarsa basa sonta ne. Zata yi bakin kokarinta wurin kare mutumcinsu a idon duniya. Takalmi kawai Rumana ta iya cirewa ta fada kan gado tana rike ciki. "Maamu yau naji yunwa sosai har jiri ya rinka daukana a hanya" Tasowa Maamu tayi ta dawo kusa da ita ta zauna tana dora hannu a kan Rumana "Baki da lafiya ne kika ki cin abinci?" Bata boye mata komai game da yadda sukayi da Gimbi ba da safe. Hatta kudin da Umman Yusra ta bata sai da ta nuna mata domin ko kwandala bata kashe ba. Hakan ba karamin daga mata hankali yayi ba da kuma neman tabbatar mata da zargin da take gudun dorawa iyalin Awaisu. "Tashi ki je ki hada shayi ki sha kafin su dawo. Doya aka dafa ke kuma nasan ba kya ci" Rumana ta yamutsa fuska saboda yadda ta tsani doya. Falo ta koma sai dai babu kayan tea a tsakiyar dinning table kamar yadda ta saba gani tun farkon zuwanta. Ta shiga kitchen nan ma babu wani abin kirki sai ta tafi zata dauko indomie a store. Nan fa taji kofar a rufe. Tunani ne ya isheta game da sauyin da ta gani a gidan yau. Haka ta koma wurin Maamu ta fada mata. Hankalinta ya sake tashi sosai. Duk da tana jin yunwa itama amma tausayin Rumana ne ya kamata. A ranta tana adduar Allah Yasa ba wani sabon salon zama zasu koma yi da Gimbi ba. Da wane ido zata kalli su Baaba Hure. "Dauko wayata ki duba nambar Gimbi ki kira" Rumana ta aiwatar da abin da aka sata. Tana zaune Maamu tana fada mata abin da zata ce a wayar. ***** Zaune take tana cike wasu takardu taji waya. Tana dubawa ta gane numbar Maamu ce. Tsorata tayi ta kasa dauka sai a karo na biyar ta dake zuciyarta. Muryar Rumana taji ta gaisheta sannan tace "Maamu ce tace na kira wai yau lafiya kuwa. Ko wani abin ya faru?" "Kice mata babu komai nima na kusa tasowa" "Su Haris basu dawo ba har yanzu sannan ni da Maamu bamu sami abinci ba. Shine tace ko zaki fadi inda key din store yake" Maamu daga gefe tana 'yar dariya tace "yau zanyi musu girkinmu don dadi duk wanda yaci sai ya manta hula da takalmi" Itama Rumana duk da yunwar da take ji jiki babu karfi dariyar tayi tana fassarawa Gimbi abin da Maamu ta fada. Shiru tayi ta kasa bata amsa daga baya ta fara cewa "hello, Rumana bana jinki." Daga haka ta kashe wayar ta cigaba da harhada kayanta a jaka. Tunaninta daya kada aikin ya baci ta sami matsala da Awaisu. Ta san yadda yake son Maamu da su Baaba. Tsoro ne sosai ya kama ta. Lokacin da ta fito shida saura ta fake da cewa dreban ya sha fama da rigimar yara ta sallame shi. Duk sun bata motar da abincin da ta bayar da kudi aka siyo musu a wani gidan abinci mai tsada na kusa da bankin. Gidan Anti Bebi ta wuce ta bar yaran a mota da gargadin kada wanda ya fito. Tare da maigidanta ta sameta ta gaisheshi yana ta bin ta da ido har suka shige daki ita da Anti Bebin. "Me ya faru na ganki da yamman nan ko waya babu?" Muryarta har rawa take yi tace "tsoro nake ji kada Awaisu ya sakeni wallahi. Yau baki ga abincin da na bar musu ba. Ina tsamani bata ci ba" Yadda tayi a gidan tun safe zuwa wayarsu da Rumana ta sanar da Anti Bebi. "Mtswww, ni kin bani haushi ma. Matsoraci baya zama gwani Gimbiya. Idan baki shafawa idonki toka ba a yadda nake ganin take takenta tunda har ta fara tambayar mukullin store saura tasa yayi miki kishiya ko ta rabaku gabadaya" Gimbi ta kara shiga tashin hankali "wallahi bazata yiwu ba. Awaisu da taimakon Alhajinmu ya zama mutum. Duk wannan aikin da nake yi da wahalar da nake sha dominsa ne. Babu wadda ta isa tazo mu zauna taci arzikin da bata san samuwarsa ba" Anti Bebi tayi dariya "yanzu kike magana, to kada ki damu idan kinje gida ta fadawa Awaisu kinga alamun zaiyi fada. Meye amfanin Laminde? Kafin ya fara fadan kiyi kanta da duka idan ya kama kina kuka kina cewa tana son kashe miki aure zata wulakanta miki uwarmiji. Daga nan ki dauki laifin duka ki nana mata ki sabule kanki ki koreta. Idan kin tashi neman wata mai aikim kizo zan hadaki da mai kawosu daga kauye" Sai yanzu Gimbi ta sami nutsuwa da kwanciyar hankali. Harda murmushinta ta fita suka koma gida. ***** Maamu ta kai wuya wurin bacin rai jira take yi su dawo. Bazata bari wannan abin yayi nisa ba gara Awaisu ya taka burki idan ma bisa kuskure ne a tunaninta ya kamata da wayar ta katse lokacin da suke magana da Rumana ta sake kira. Shirun da suka ji har Rumana ta sake kira wayar a kashe shine ya bata mata rai. Gimbi na shiga gida ta tarar da Awaisu shima shigarsa kenan. Yana son tambayarta inda ta tsaya kuma ga yara da kayansu tun na boko ya ga Maamu ta fito. Kana ganinta yau babu wannan fara'ar wadda da wuya ka ga fuskarta a hade. Jikinta gabadaya babu kwari saboda yini da yunwa. Ruwa kawai suke sha ita da Rumana. "Yanzu nake shirin shigowa dakin naki" cewar Awaisu yana matsawa kusa da ita. "Na hutar da kai. Dama nace ko kun manta damu a gidan ne yau baku ajiye mana abinci ba" Dayake da yarensu take magana Gimbi duk ta tsargu. Kallon Gimbi yayi "garin yaya kika fita ba'a ajiyewa Maamu abinci ba? Ina Laminde?" Hantar cikin Gimbi ta kada ta fara in'inar da bata san tana da ita ba "uhmm-dama-da-fate-eh faten doya aka yi mata kafin-kafin mu fita" Maamu sarai ta fahimceta sai kawai ta koma dakin ta dauko langar faten doya. A harzuke take sosai ta bude a gaban Awaisu, har wani ruwa ruwa ta fara ga baki da tayi sosai "Wannan abincin zamu ci Awaisu?" Yadda tayi maganar muryarta ta karaya domin kuka ne yake barazanar kwace mata saboda takaici. Ko aiki take yi a gidan aka bata wannan abincin tabbas anso cin mutumcinta ne. Dagowa yayi da zafinsa zaiyiwa Gimbi fada. A lokacin ba karamin tsoro ne fal a zuciyarta ba sai ta tuna hudubar Anti Bebi ta daure fuska. Kamar anyi ruwa an dauke haka ya hadiye fushinsa ya koma yana kallon Maamu. "Ai kuwa da gani faten nan zaiyi dadi. Gimbi ko zaki dumama mata a microwave yadda zata ji dadin ci" Duk da tayi mamakin saurin sauyawarsa amma saboda tana son tabbatar da aikin Wangesi tace "to my dear, dan tambayar min idan tana son manshanu sai na saka mata ma. Kasan Laminde gwanar girki ce" Haka kuwa ya tambayi Maamu hankali kwance. Kasa bashi amsa tayi saboda a take a lokacin wani irin abu taji ya soki zuciyarta. Tana kallo Gimbi ta wuce kitchen da langar wai zata dumama ta dawo mata dashi. Awaisu kuwa yana murmushi yace mata zaije ya watsa ruwa yazo suyi hira. Bayan tafiyarsa Maamu ji tayi jiri zai kwasheta ba don yunwa ba sai don yadda zuciyarta ta karaya da halin da ta tsinci kanta daga zuwa gidan tilon danta abin alfaharinta.11*KASHE FITILA*💡12 *Batul Mamman*💖 Da kyar Maamu ta kai kanta daki inda Rumana take kwance duk sauran kuzarinta ya kare. Tana turo kofar Laminde wadda babu wanda ya lura tana tsaye a bakin kofar shigowa gidan ta dafe kirji. Duk abin da akayi a kan idonta ne. Wannan abu ya kara daure mata kai har ta rasa da me za ta kwatanta shi. Ko ma menene akwai wani abu da uwar dakinta take yi game da surukarta. Tun safe da suka fita Gimbi ta aiketa kasuwa. Daga can ta ce ta wuce wurin kanwarta da aka kawosu aiki Abuja tare. Haka ta tafi cike da mamaki musamman da ta fada mata kada ta koma sai ta kirata a waya. Wayar da ba'ayi mata ba sai da ta baro gidan Anti Bebi. Gimbi ta gani ta dawo da langa tana tiriri ta dorata akan wani tray na silver kasanta kuwa duk yayi baki. "Yaushe kika dawo ban sani ba?" "Shigowata kenan" "To aje ayi min wanke wanke" Laminde tace to ta juya kitchen. ***** Bayan fitar Gimbi Maamu ko bude abincin bata yi ba ta dauka ta kai kitchen. Lokacin Rumana bata farka daga baccin yunwar da take yi ba. Tana shiga ta ga Laminde ta bude wani flask da shinkafa a ciki tana shirin zubarwa. Abincin Awaisu ne na office ko rabi bai ci ba. Maamu ta rasa yadda zata kwatantawa Laminde ta bata abincin. Can dai ta nuna abincin tace Rumana. "Rumana zaki bawa?" Maamu tace eh. Laminde ta mika mata flask din. Karba tayi ta koma daki ta tashi Rumana. Duk da tana so haka ta bar mata. Ita kuwa tana ganin abincin haka ta soma ci babu wanke hannu bare kuskure baki. Maamu na gefe sai hawaye take sharewa batare da ta bari Rumanan ta gani ba. Yarinyar da gidansu ba'a san yunwa ba itace yau ta bawa ragowa. Da Harisu zai ganta yanzu bata san inda zata saka kanta ba. Rumana ta cinye abincin tas ta sude flask din kamar almajiri yaje bara an bashi lomar tuwo uku. Tana gamawa sai amai tun a dakin ta fara Maamu ta kama ta zuwa bandaki. Tana yi tana kuka domin tun tana fitar da abinci sai da ya koma yawu kawai take zubarwa idan ya yunkuro. Haka Maamu ta gyara wurin tace Rumana ta kwanta. Babu bata lokaci wani baccin ya dauketa baki a bude. A daren Maamu tayi kuka har kanta ya rinka ciwo. A kusa da Rumana tayi bacci. ***** Bayan asuba Gimbi ta shiga dakin ta tarar da Maamu akan abin sallah ita kuma Rumana tana shafa mai. A ladabce ta gaishe da Maamu kamar bata yi musu komai ba. "Rumana jiya kika bar kanwarki ta kwana ita kadai. Ko kinfi son kwana a nan ne?" Kai kawai ta gyada don ta fara tsoron Gimbi yanzu. Murmushi tayi a ranta tace tafi nono fari. "To ai babu komai hakan ma yafi. Zaki rinka debewa Maamu kewa" Daga haka ta fice zuciyarta cike da nishadi. Yanzu zata gyarawa Daula dakin yadda ta tsara tun farko. Kitchen ta wuce ta samu Laminde har ta gama farfesun kayan cikin da ta sakata. Ta zubawa mijinta da yaranta sannan ta dauko langar Maamu ta soma zubawa. Laminde tana goge gefen gas cooker din ta saki tsumman tana kallon ikon Allah. Hanji ne Gimbi take ta za6ewa tana zubawa ya kusa rabin langar. Jikinsa duk kitse yayi wani narai narai babu kyaun gani. Kasa hakuri Laminde tayi "Hajiya nace ko kin manta wannan langar kince ta Maamu ce" Fuska a hade saboda bata son bada kofar tsawaita zancen tace ban fahimceki ba. "Na ga kina ta zuba hanji ne a ciki." "Hanjin ba nama bane? Kinga ki kiyayeni da shisshigi wallahi. Kin saka min ido ni da gidana sai nayi miki bayanin abin da nake yi. To binciken likitoci ya tabbatar da cewa cin dafaffen hanji yana matukar taimakawa tsofaffi da kara musu lafiya" Awaisu yana daga falo suna jiran ta kawo breakfast shi da yara ya jiyo muryarta tana fada. Kitchen din ya shiga "Me ya faru kuma kike fada da safen nan?" Rufe langar tayi tace "kyaleni da ita, ina jin ta fara gajiya ne da aikin" Laminde sai faman bada hakuri take yi. Ya so jin abin da ya hadasu sai dai shima bai ga fuskar tambaya ba. Yana kallo ta dauki langar tare da bread wanda ta yanka gida hudu ta dauki bari daya sai tea a kofi ta kaiwa Maamu da kanta. Bayan fitarta Rumana ta gama shirin makaranta. Duk da bata da kwari sosai amma a ganinta fitar zata fiye mata. Kafin ta fita Maamu ta mika mata dari biyu cikin kudin da Harisu ya bata wanda a lokacin tayi ta cewa ya barshi. Ashe zai musu rana. "Ki sayi abinci a makaranta kici kinji ko. Zan yiwa baban naku magana sai ya rinka baki kudi da safe ko kuma a baki abinci kema" Rumana tayi mata godiya ta fito falo. Suna zaune dukkansu suna cin abinci suna wasa da yaransu. Awaisu ta gaisar yaran suna tambayarta ina taje jiya basu ganta ba. Murmushi kawai take yi. "Zauna ki hada tea kuyi sauri kada ku makara" inji Awaisu. Gimbi ta dan juya ido "har ka manta na fada maka za ta rinka tafiya da kanta. Rumana shiga wurin Laminde kiyi brealfast kinji." "Me yasa bazata ci a nan ba?" Awaisu ya tambayeta harda dan daga murya kamar zaiyi fadan gaske. "Bana so Laminde ta ga kamar muna wareta ne. Shiyasa nace su ci tare. Banyi laifi ba ko?" Ta rausayar da kai tana masa fari. Shiru yayi yana ta auna maganar. Har ransa baiji dadi ba kuma fada yaso yi sai dai yana bude baki yaji bazai iya ba. "Bakiyi komai ba. Kuyi sauri bana so kowa ya makara" Daga haka kowa ya karasa cin abincinsa suka tashi zasu tafi. Rumana itama ta fito bayan ta gama cin nata hanjin da bread. Sai tea wanda tana sane ta tsula masa ruwa don ya kara yawa ko zata dade bata ji yunwa ba. Suna fita itama ta fito ta tafi. Yau bata hadu da su Yusra ba sai a aji. Da break ta hada da kudin da Maamu ta bata da na wurin Umman Yusra ta sayi fanke na dari da meat pie 'yan hamsin guda hudu. Yusra ta rinka kallonta, ina zata kai wannan abincin ita kadai. Meatpie daya taci da fanke biyu ta saka sauran a jaka zata kaiwa Maamu. ***** Da farko Maamu kin cin abincin tayi sai daga baya da yunwa ta cigaba da cinta ta dauki kofin tea din ta shanye. Ta bude langa sai ga hanji da romon ya daskare ya hade jikinsa. Idan jiya tana kokonto yau ta tabbatar Gimbi da gaske wulakanta ta take sonyi. Tasan karshenta gidan ne bata so ta zauna musu. To amma komai wahala zata jure. Ta cinye rayuwarta a alfarmar gidan Harisu da Baaba Hure. Yanzu kuwa da kunya ta koma. Idan ta koma din ma ace nata dan ya kasa riketa. Shawara ta yankewa zuciyarta idan ya dawo zata ji ta bakinsa game da wannan gashin kuman da aka fara yi musu. Ko aikatau tazo yi a gidan a tunaninta bata cancanci a wulakanta ta ba. Sai yanzu take kara godewa Allah da aka ki yarda su zo da Baaba. Da bata san da idon da zata kalleta ba don kunya. Haka nan ta rinka cin hanjin tana hawaye. ***** Da rana Laminde bata kawo abinci ba zuwa da tayi suyi hira. Duk da ba komai take fahimta a zancen ba amma tana jindadin yadda take mutumtata. Rumana tana dawowa ta dauko abincin jakarta suka ci ita da Maamu. Wannan abu ya tsayawa Maamu a rai sosai. Bakinciki yasa ko fanken hannunta bata gama ci ba ta ajiye. Sai karfe shida su Gimbi suka dawo. Yau ma yaran basu je islamiyya ba. A lokacin ta bude store ta mikowa Laminde semovita tace ta dora tuwo. Cikin sauri tayi ta gama domin itama ta horu da yunwa. Gimbi da kanta ta raba abincin ta zubawa Maamu tuwo da miya a hade. Rumana itama a plate aka hada mata ta ajiye a kitchen. A haka suka kwashi sati biyu tana musu kisan mummuke sannan tana auna karfin mulkinta akan Awaisu. Da ta tabbatar aiki yayi kyau ne ta kira Anti Bebi akan tana son na mallaka domin tun a haka tana ganin yadda baya iya yi mata musu ko kadan.12*KASHE FITILA*💡13 *Batul Mamman*💖 Anti Bebi ta rinka yiwa Gimbi dariya " 'yar gari waye ya fada miki haka nan mata suke zaune, duk wadda tace miki bata dan lekawa wurin neman taimako domin samun zaman lafiya a gidan aurenta karya take yi. Abin da naso uwarki ta fahimta kenan sai ta rinka gayamin maganganu" Gimbi na jin haka ta daure fuska "nifa kinga abin da yake hadani dake kenan, akan zagin Mama fa sai naci..." shiru tayi sanin cewa yanzu sirrinta a tafin hannun Anti Bebin yake. "Karasa mana mara mutumci. Ni zaki zaga Gimbiya. Lallai wuyanki yayi kauri. Yadda na kaiki wurin Wangesi akan mijinki kinsan ba karamin aikina bane na koma akanki ko" Gaban Gimbi ya fadi a tsorace ta soma bata hakuri. Sai dai tana cikin magana taji ta katse kiran. Da ta sake kira kuwa a kashe taji ta. Yanzu ko da wuka a wuyanta bazata iya kwatanta hanyar zuwa wurin Wangesi na tsangaya ba. Kuma ba karamin aikin Anti Bebi bane taje tasa ayi mata wani mugun abun. A da bata gama sanin wacece ita ba sosai sai yanzu da suke tare. Ban da mijinta da ta shanye hatta mahaifiyarsu wato kakarsu Gimbi bata taba yi mata musu. Duk yadda tace haka ake bawa su Mama umarni kuma dole suyi idan ba haka ba ta nuna musu fushinta sosai. Kuma bata taba yi mata fadan abubuwan da take yi da aure aure ba. A ranar ta bita gida tayi ta bata hakuri daga karshe suka daidaita. ***** Watanni biyu kenan da shigar su Maamu cikin kunci a gidan Awaisu. 'Yar hirar da yake zuwa suyi ma sai yayi kwana biyu bata sa shi a ido ba. Ranar da ya zo kuma zai sake yayi ta bata labarai batare da kula ko tambayarta idan tana da damuwa ba. Ya riga ya sakarwa Gimbi komai da ya shafi Maamu da Rumana. Hatta kudin makaranta ko abinci da ta nemi a rinka bawa Rumana cewa yayi zai fadawa Gimbi. Sau tari ya kan tsinci kansa da tunani akan rashin dacewar abin da yake yi mata. Amma ko a bayan idon Gimbi bai taba kuskuren canjawa zuwa Awaisun Harisu da aka sani ba a gaban Maamu. Yau Rumana ta dawo da yunwa saboda dan kudin hannun Maamu tuni ya kare. Abincin rana kuwa dama an soke shi a hankali. Da safe take sawa Laminde tayi musu girki wanda take tafiya wurin aiki dashi a zubawa yaranta. Da rana tace ba zama suke yi ba Laminde ta huta. Sai biyar zuwa shida idan sun dawo a dora na dare. Kana ganinsu har sun fara rama. Idan sunyi waya da Harisu sai tayi ta kokarin danne damuwarta. A matsayinta na uwa ga Awaisu duk yadda suke da su Baaba Hure akwai abin da dole kaji kunyar fadawa duniya. Yau da wata aka yiwa haka da sauki sai ta iya shiga ciki domin tsawatarwa. Amma ita mahaifiyarsa da kanta wurin wa kuma zata kai kara. Suna zaman jiran abincin dare a dakin Mu'allim ya shigo yana buga ball. Da karfinsa ya mako ta bata fada ko'ina ba sai fuskar Maamu. Rumana ta tashi da sauri ta kwada masa mari. Dama tuni Gimbi tasa yaran suka dena shiga dakin wai bata so suna damun Maamu. Jin zafin marin yasa ya kwalla kara. Sai ga Gimbi ta shigo a guje ta dauke shi tana tambayar me aka yi masa. Yana rike da kumatu ya fada mata Rumana ce ta mare shi. Batare da neman ba'asi ba ta sauke shi a gaban Maamu tace ya rama. Rumana ta zaro idanu "Mummy kinga fa wannan katuwar ball din ya bugawa Maamu." "Shine zaki mare shi saboda mugunta bayan kinsan ba da gangan bane. Ki bari ya rama ko kuma ni na rama masa" Rumana ta kalli Maamu tana hawaye saboda irin wannan cin zarafi da akeyi musu. Idan da kara ko cin zalinsa akayi tunda Maamu tana wurin bai kamata tayi magana ba. "Gara ke ki rama masa akan na bari kanin bayana ya mareni" ta fada tana kuka Motsin tahowar Awaisu Gimbi taji ta rage sautin muryarta "Bazaki bari ya rama ba?" "Wallahi bai isa ya mareni ba" fushi da bacin ran da take boyewa ne ya fito yau. Ita bata ki ace ta tattara ta koma gida ba. Awaisu ya shigo rai a bace ganin yadda take kallon Gimbi ido cikin ido ya daga hannu zai mareta. Sai a lokacin Maamu ta tashi ta rike masa hannu. "Idan ka taba yarinyar nan zaka hadu da bacin raina Awaisu" "Maamu kada ki bari Rumana ta tashi a sangarce. Baki ga yadda take yiwa Gimbi rashin kunya bane" Gimbi dai bata jin me suke fadi da yarensu. Jin an ambaci sunanta ta matso 'yar kwalla "Abban Haris ka bar maganar nan haka. Bana so Maamu tayi fushi da kai akan wannan 'yar matsalar. Rumana kiyi hakuri kinji" Tsabar mamaki yasa ta kasa magana ma. Shi kuwa Awaisu ficewa yayi rai a bace a ganinsa sangarta Rumana za'ayi tunda tana yiwa matarsa rashin kunya kuma an hanashi hukunta ta. Da suka fita Rumana ta fashe da kuka Maamu ta kasa rarrashinta. Ita da idonta har ya kumbura ya kankance cikin dan lokaci amma Awaisu ko kula baiyi ba me zata ce mata a wannan lokacin. A haka Laminde tazo ta kawo musu tuwonsu. Dole suka ci tunda sun wuni da yunwa. ***** Kallo suke yi a falo tare da yaransu suna taba hira. Hankalin Awaisu ne ya tafi wurin Mu'allim da yake fadawa 'yan uwansa ya iya buga ball da karfi har Maamu ya bugawa a fuska. Daga kashingidar da yayi ya tashi da sauri "wa ka bugawa ball kace?" Gimbi tayi saurin tarewa "ku tashi ku tafi ku kwanta dare yayi" Awaisu ya janyo hannun Mu'allim. Fuskarsa babu alamun wasa ya tambayeshi me ya faru a dakin. Gimbi ya fara kallo sai dai bata da ta cewa a wurin. Dolensa ya fadi abin da yayi da marin da ya sha. Da sauri Awaisu ya tashi yayi hanyar dakin Maamu. Gimbi ta soma kiransa sai dai ko juyowa baiyi ba. Yana shiga ya tarar da Maamu a kwance ta rike kankarar pure water a daidai idonta yayin da Rumana har yanzu kuka take yi. Kankarar ya karba ya ga idon ya suntume. "Subhanallahi Maamu kiyi hakuri. Yanzu nake jin abin da ya faru" Tashi tayi zaune idonta cike da kwalla tace Rumana ta fita "dama irin zaman da kake son yi dani kenan ka takura muka taho?" Kansa ya sunkuyar kasa yana bata hakuri. "Yaushe rabon da ka shigo dakin nan balle ka duba lafiyarmu? Bance kada kaso iyalinka ba amma ka tuna cewa nima ina da hakki a kanka. Bana neman komai a gareka da ya wuce ka bani girman da Allah Ya bani akanka sannan ka kula da amanar Rumana. Idan ka wulakanta zuri'ar Baaba Hure kafi kowa sanin irin kallon da duniya zata yi maka. Sannan a lahira ka tashi cikin masu tozarta zumunci." "Kiyi hakuri, nasan nayi kuskure amma zan gyara in sha Allahu. Na rasa abin da yake damuna ni kaina" Duk da ranta a bace yake amma taji dadi yau ya nuna damuwarsa garesu "Ka tashi ka tafi ya wuce" "Asibiti zan kaiki saboda idon. Shi kuma zai gamu dani wallahi." A fusace ya fita daga dakin. Rumana da take tsaye a gefe yace mata daga yau ta rinka fitowa da Maamu falo suna shan iska baya son suna kulle kansu. Dakin yaran ya wuce Gimbi tana tambayarsa me zaiyi da wayar chaja bai kulata ba sai gani tayi ya fara laftawa Mu'allim dan shekara bakwai a jikinsa. Yana dukansa duk ya cika gidan da ihu Gimbi ta kasa karbar chajar sai ma rabonta data samu a baya. Maamu tana jinsu ta kwanta abin ta. Bata kin jikokinta amma ta kula da yadda suka bi sahun babarsu wurin banzatar dasu a gidan. Ranar Awaisu da Gimbi barambaram akayi babu mai kula dan uwansa tun bayan da ya gama hukunta Mu'allin tare da ja mata kunne sosai akan Maamu. Da safe a motarsa suka dauki Rumana zuwa makaranta ya bata dubu biyar yace ta ajiye sauran a gida. Yaso kai Maamu asibiti ma tace ta warke. ***** Gimbi tana fita da suka kai yara makaranta gidan Anti Bebi ta wuce. Tana kuka ta fada mata irin dukan da Awaisu yayiwa Mu'allim. Gashi tana ganin kamar maganin ya fara sakinsa. "Ni dai kawai kizo muje gidan Wangesi kada komai ya lalace min" "Gimbi kenan wato mugu baya so a dandana masa zumarsa sai ya birkice. Don yau daya anyi miki meye na fushi. Can wurin aikin naki fa?" "Ni dai kawai kizo muje zan san karyar da zanyi musu" Ko mijinta bata sake lekawa ba ta dauko dan gyalenta suka fice. Gimbi ta sallami nata dreban suka wuce da dan koran Anti Bebi. Wangesi ya bata wasu kwayaye guda hudu duk anyi musu zane da jar tawwada da wasu layu da kulle kullen magani. Komai yayi mata bayanin yadda zata yi amfani dashi ta kawo kudi ta ajiye masa. Suna komawa gida ta wuce. Kwai daya a kofar dakin Awaisu ta fasa shi ta rufe da door mat. Sauran biyun kuma daya a bayan dakin Maamu dayan kuma ta dafa shi ta cinye. Da ta gama ta dauki motarta ta koma gidan Anti Bebi sai lokacin tashin yara ta dawo. Manajan bankin da take ya kira Awaisu kan cewa yayi mata magana akan fashi da rashin zuwa da wuri ko kuma fita kafin a tashi. Don ma yana ganin kimarsa ne da tuni ya bata takardar jan kunne. Hakuri ya bashi tare da godiya. Yana dawowa ya hauta da fadan sai ta gaya masa inda take zuwa. Ta rasa amsar da zata bashi. Abincin da ta zuba rabin maganin kuma yaki ci. Daren ranar yaransa yasa a gaba suka taya Maamu da Rumana hira a falo. Gimbi kuwa Anti Bebi ta kira tana kuka Wangesi ya ci kudinta a banza. "Kin fiye wutar ciki. Haka aka ce miki asirin yana kama mutane kamar a fim? A hankali zai cinye shi ya dawo miki tamkar sakarai shashasha" Tsaki tayi ta ajiye wayar. Ita Anti Bebi bata da aiki sai fadin bakar magana. Awaisunta ba sakarai bane ta fada a zuci tana huci ita kadai. Sai bayan sati ta kula ya fara sanyi fiye da yadda yayi a baya ma. Sa idonsa akan lamarin su Maamu da suka fara shanawa yanzu babu. Gidan jiya aka koma inda take horasu da yunwa wai don kada suji dadin gidan su cigaba da zama.13*KASHE FITILA*💡14 *Batul Mamman*💖 *Bayan Sati Uku* Zaune take gaban madubi tana kwalliya taji kamar ana kiranta. Jagirar hannunta ta ajiye ta fito daga dakin tare da leka falon ta saman bene. Mijinta ne ya shigo rai a bace sai huci yake. "Shuhada kina ina ne?" Saurin saukowa tayi har tana hada bene biyu a lokaci daya "Me ya faru T?" Mugun kallo ya bita dashi kafin yayi magana "kizo ki fice daga gidan nan na sakeki" Ji tayi kamar an sakar mata guduma a tsakiyar kanta "Ka sakeni? T kalmar saki fa ba kalmar wasa bace" Idanunsa kara rinewa sukeyi suna yin ja saboda bacin ran da ya rasa dalilinsa. "Ni zaki rainawa hankali, to zamana dake ya kare. Ki tattara ki fita kafin kiji hannuna a jikinki" Shuhada rasa bakin magana tayi. Anya mijin nata hankalinsa daya kuwa. Ya fita suna farinciki da juna. Me ya kawo wannan chanji haka. Dan matsawa tayi kusa dashi "T ka zauna don Allah muyi magana. Na rasa gane abin da yake faruwa. Abokanka sun baka wani abu ne kasha da baka sani ba?" Saukar mari taji har biyu "kina nufin ina shaye shaye ne." Dafe kuncinta tayi tana kuka "Tajuddeen kana cikin hankalinka kuwa. Nice fa, me nayi maka haka" Girgiza kai yayi yana yamutsa fuska "tsanarki kawai nayi S. And I want you to get out now kafin raina ya kara baci" Kuka ne sosai yaci karfinta. Gabadaya kwakwalwarta ta toshe. Mutum ya fita lafiya ya dawo a birkice. Ba karamin so yake nuna mata ba tun kafin aurensu har zuwa yanzu da suka sami shekara daya tare. Gani tayi ya hau sama ya fara cillo mata kayanta ta saman bene. Lallai da gaske yake. Tana kallo ya gama ya sauko ya bude wallet dinsa. Kudi ya debo ya watsa mata a fuska. "Now get out" Itama nata ran ya gama baci "babu inda zani Tajuddeen, a musulunce ma dai mace a dakinta take yin idar saki daya ko biyu. Sannan a daren nan ina kake so naje? Ba fa Nigeria muke ba inda zaka sakeni na tafi gida." Cikin halin ko in kula yace "tafi wurin kaninki" Bude baki tayi "yaron da yake hostel din maza" "Indai don ki kwana ne to na sakeki saki uku. Ai dai babu sauran igiya tsakaninmu." Karo na biyu kenan da Shuhada ta shiga tashin hankali dalilin saki. Na farko a gabanta ita da kaninta mahaifinsu yayiwa babarsu saki uku. Yau gashi anyi mata batare da wani kwakkwaran laifi ba. Jiri ne yake dibarta amma a haka ta fara hawa benen zata koma sama. Tajuddeen yayi saurin tareta yana cewa bazata kara shigar masa daki ba. Bata da kuzarin fada saboda duk abin da ya faru tamkar mafarki haka take jinsa. A sanyaye tace "wayata zan dauko da mayafi. Sannan ka bani passport dina" Saman ya hau ya dauko mata wayar da passport. Mayafi kuwa kayanta da ya watsar ya nuna mata. A nan ta durkusa ta dauka ta fita. Wani sanyi ne ya ratsa ta ga dare karfe goma da rabi. Da kyar ta sami taxi wadda ta kaita jami'ar da Suhail kaninta yake karatu a nan Singapore. Da ta sauka ta kira wayarsa tayi sa'a ya dauka a kiran farko. Tana jin muryarsa ta saka kuka mai cin rai. Nan hankalinsa ya tashi da kyar ya samu ta fadi inda take a wajen makarantar ya fito. "Sis me kike yi a nan a daren nan ke kadai?" "Ya sakeni Suhail, har saki uku." Wani kukan ta soma sai gashi ya koma babban yana ta rarrashinta. Bayan ta dan nutsu ta labarta masa abin da ya faru. "Hotel zanje na kama sannan na kira Daddy ya turo min kudi. Kaga last week ka ranci kudi a hannuna yanzu bani da enough da zan sayi ticket na koma Nigeria." Suhail ya sunkuyar da kai yana ajiyar zuciya "Sis ko kin kira bazai aiko miki da komai ba. Kudin da na ranta wurinki ciko nayi na biya kudin registration." Shuhada ta zaro ido "me kake nufi?" "Na fi wata ina cewa ya turo min kudin registration yana cewa babu. Dana matsa masa rannan sai yace wai dama ai saboda mijinki yana aiki a nan ya turoni karatu. Tunda bashi da kudi meye amfaninku. Ganin kada su dakatar min da karatu yasa na ranta kafin ya turo min sai na baki" Dafe kai tayi tana mamakin wannan abu. Tasan waye mahaifinsu a Nigeria. Babu yadda za'ayi yace kudin makarantar dansa ya gagare shi. A yadda yake ko da da gaske babu bazai taba bari su sani ba zai nemo ko bashi ne. Hankalinta ne ya kara tashi ta ce masa zata nemi wurin kwana washegari yazo ya sameta. A dakin hotel din baban nata ta kira kamar yadda ya fadawa Suhail itama cewa yayi ta nema ko ta bawa mijinta hakuri ya biya mata. Tayi kuka a daren har asuba bata runtsa ba. Da sassafe ta koma gidanta da sunan kwashe kayan sawarta. Tajuddeen ta roka ko zai biya mata kudin jirgi ta koma gida. Nan yayi mata rashin mutunci ya koreta. Dole ta kira mahaifiyarta mai fama da hawan jini ta sanar da ita. Da dan kudin hannunta take biyan hotel din. Kullum suna tare da Suhail suna shawarwari. Bayan kwana takwas mamanta tasa aka turo kudin jirgin. Filinta ta sayar domin duk wani abu na kadara da ta samu wurin babansu sai da ya karbe bayan sakin. Ana gobe zata tafi Suhail yana tayata hada kaya harda kukansa. Shekararsa ashirin da biyu ita kuma da hudu. Text ne ya shigo wayarta daga numbar da batayi tsammani ba. _Kada ki kuskura kizo min gida da sunan zawarci. Kamar yadda kika kirga min aure da na auri ubanku kema yanzu kika fara. Ke da duk wani naki baku isa ku ja dani ba_ Sai yanzu ta gane dalilin sakin da Tajuddeen yayi mata. Yadda aka raba iyayenta itama haka akayi mata. Gashi an rabasu da mahaifinsu. Bata nunawa Suhail komai ba. Sai dai ta kuduri niyar canjawa daga Shuhadar da mai shiru shiru da hakuri. Washegari da daddare jirginsu ya tashi. Uku na yamma suka sauka a Nnamdi Azikiwe Airport Abuja. Tana saukowa daga jirgin tana saka yadda zatayi maganin Anti Bebi matar babanta. ***** Gimbi na kwance a daki yau asabar tana hutawa taji waya daga Mama. Bayan sun gaisa take sanar da ita cewa ta fita unguwa ne kuma suna hanya zata biyo su gaisa da Maamu. Zumbur Gimbi ta mike daga kan gadon. Karfe biyu da rabi ko abincin da za'a dafa bata aunowa Laminde ba. Da sauri ta shiga kitchen din tana kwala mata kira. Dama tasa tayi miya tun dare. Shinkafa tace ta dafa ita kuma ta hau aikin salad. Bayan ta gama ta dauko dabinonta wanda ya kwana biyu a jike cikin fridge tare da kanunfari da dakakkiyar danyar citta ta hada da kwakwar da tasa Rumana tayi mata grating ta zuba a blender. Nan da nan ta gama markadesu ta tace ta kara madara. Kankara ta fasa ta hada a jug ta jera a tray. Bayan an gama shinkafar ta cika mata cooler madaidaiciya ga miya taji nama. Cikin awa daya sun gama komai sai jiran Mama. Abincin Maamu a langar nan ta zuba ko salad bata samu arzikin a zuba mata ba. Laminde a ranta tace lallai uwa tafi uwa. Suna kitchen din suka ji sallamar Mama. Gimbi ta kalli Laminde tana ta murna "kinsan Mama bata son zuwa gida 'ya'ya ba kamar wasu tsofaffin ba. Shiyasa kika ga na hada mata wannan. Ki biyoni da abincin nata. Maamu ki kai mata nata daki ba sai tazo falo ba" Da murna ta taro Mama suka gaisa sannan ta tashi tana rike da hannun Amir "Kinsan ba wurinku nazo ba. Kaini dakin Maamu" Yayi mata jagora har dakin. Gimbi ta koma dakinta da sauri ta sake gyarawa ta fesa air freshner sannan ta shimfida katuwar dadduma a kasa. Fitowa tayi zata je kitchen ta hango Laminde a kofar dakin Maamu da katon tray din kayan abincin Mama. Da sauri tace "Ke, ke, ke Laminde dawo" Laminde tana ji tayi biris da ita ta shige dakin. Maamu ta samu da Mama suna taba 'yar hira da kalmomin da Maamun take fahimta. Har Mama tana cewa ta rame ko kewar babban danta take yi. Laminde ta ajiye musu abincin a tsakiyarsu. Mama tayi ta korafin meyasa basa gama abinci da wuri. Maamu ta bude ido tana kallon wannan gara wadda ta manta rabon da ta ga abincin arziki irinsa. Ita kuwa Mama plate din da ta gani guda daya ta zuba musu abincin tare. Tuni idanun Maamu suka fara cika da kwalla da Mama tace mata su ci. Ita da gidan danta ta koma tamkar almajira. Mama ta rinka kara musu suna cinyewa tare. Maamu ta saki ciki taci ta koshi tasha lemon kwakwa. Rumana da take dakin ma sai da Maamu ta cika kofi taf ta mika mata. Gimbi kuwa daki ta koma tana ta kai kawo. Ta rasa wane hukunci ya dace da Laminde. Sai daga baya ta fito ta koma dakin Maamu. Laminde tana hango shigarta ta bawa Mu'allim langar abincin Maamu tace ya kai mata. Haka ya karba yana turo baki yaje ya dangwarar mata a gabanta. Mama ta daka masa tsawa "nifa shiyasa bana son wasan jika da kaka, wani lokacin sai raini yayi yawa. Abincin waye wannan duk kanzo" Maamu tayi murmushi ta mika hannu "nawa ne" Gumi ya karyowa Gimbi saboda kallon da Mama ta jefa mata. Baki na rawa tace "Mu'allim dauki ka cewa Laminde wai wa ta zubawa wannan abincin" Da yake gwanin tsiwa ne yace "Mummy langar abincin Maamu ce fa." Sannan ya fice abinsa. Maamu da yarensu ta fadawa Rumana ta ajiye a gefe zuwa anjima idan ba'a gama na dare da wuri ba sai suci. Mama ta ritsa Gimbi da idanu, ita kuwa taki yarda su hada ido saboda tasan yau me rabasu sai Allah.14*KASHE FITILA*💡15 *Batul Mamman*💖 Laminde tana daga kitchen ta hango Mama a gaba rai a bace Gimbi na bin bayanta suka shiga hanyar dakinta. Rufe kofar kitchen din tayi ta kwashe da dariya. "Haka kawai kin mayar da mata almajira a gidan danta. Allah Ya budi idon Alhaji dai ya gane irin matar da yake aure" ***** Mama ko zama bata yi ba ta juyo tana hararar Gimbi. Kana ganinta ta gama tsorata sai dai kuma a yanzu jan ido bazai hanata kudirinta na ganin Maamu ta bar musu gida ba. "Gimbi me yaron nan yake nufi da cewa abincin kakarsa ne a wannan kodaddiyar langar?" "Haba Mama yanzu shine duk kika bata ranki? Har kin tsorata ni. Dambun nama ne na zuba mata a ciki kwanaki to shine suke ganinsa a dakin" Mama ta danyi jim kamar bata yarda ba "Yanzu surukar taki kika zubawa dambun nama a ciki don wulakanci. Idan nice kinsan jifanki zanyi dashi. Ko da wasa wallahi kada ki kara" Gimbi tayi mamakin saurin saukowar Mama ta bata hakuri da alkawarin bazata kara ba. Mama tace "na kula dai ba karamin ci tayiwa abincin nan dazu ba. Ki dena barinta da yunwa. Abincin rana ace sai hudu saura babu dadi" Tabe baki tayi saboda samun wuri "mhmm Mama don ba a gidan nan kike ba. Haka take wannan cin abincin. Kuma Abban Haris na dawowa sai kiji tana cewa bata ci abinci ba " "Ni dai na fada miki gara uwarmiji ta cuceki akan ki cutar da ita. Mijin da kike takama dashi aljannarsa tana tare da farincikinta dashi" Zama Gimbi tayi tana ta fadin karairayi duk tace Maamu ce take yi mata. Sai dai tana kula tamkar zancen bai shigar Mama. Suna nan ta jiyo muryar Awaisu ta tashi. Bata jima da fita ba wayarta da ta bari akan gado ta hau kara. Mama ta mika hannu ta dauko *Anti BB* ta ga an rubuta. Zata amsa kenan Gimbi ta shigo, kusan fizgar wayar tayi daga hannun Mama har ta bata tsoro. "Wata mata ce da nake bi bashi take kin daukar wayata shine ta kira yanzu." Dauka tayi tace zata kira tana tare da mamanta. Anti Bebi tana jin haka tayi dariya kawai a ranta tana mamakin Gimbi. Ita kaifi daya ce babu kumbiya-kumbiya. Gimbi kuwa fuska biyu gareta. Wato sai tana da bukata take nemanta. Zasu gamu ne. Mama abin ya kara daure mata kai yadda Gimbi ta canja. Awaisu yazo ya gaishe ta suka rakata har mota. Dreba na janta tunaninta yayi nisa. Kokonto take yi anya Gimbi bata yin wani abu domin takurawa Maamu? Sannan haka kawai take ji a ranta Bebi kanwarta ce ta kira Gimbi. To me ya hadasu. Da wannan tunanin ta isa gida. ***** Taxi ce ta ajiye Shuhada a bakin gate din gidansu maigadi ya taho da murnarsa ya tarbeta. "Hajiya hala babu wanda yasan kina hanya ba'a turo an dauko ki ba daga filin jirgi. Ina Suhailu dan makaranta?" Murmushi tayi tana janyo jakarta ya karba. Da ta shiga ciki tamkar ba gidansu ba. Duk wani abu da zai nuna sun taba rayuwa a ciki babu shi. Daga kan doguwar kujera ta hango Anti Bebi tana danna waya. Muryar maigadi yana tambayar Shuhada ina za'a kai mata akwatunan yasa ta dago kanta. "Da na ce kada ki taho gidan nan kinsan ba wasa nake yi ba ko. Zuwa yanzu yaci ace kinsan ni ba tsararki bace" Zama Shuhada tayi ta dora kafa daya kan daya "idan ban taho nan ba a titi zan kwana?" Anti Bebi ta mike tsaya tana kallonta. Yaushe ta fara sa'in'sa da ita. "Ki tattara ki koma inda gyatumarki take" "Itama gidan mahaifinta ta koma da kika kashe mata aure. Nima da kikayi nasarar kaso min nawa kinga sai nazo mu zauna a gidan nawa mahaifin." Da yatsa Anti Bebi ta nunata "ba'a ja dani Shuhada. Barin gidan nan shine kwanciyar hankalinki." Yatsan da take nunata ya kusa tsokale mata ido tasa hannu ta doke shi. "Kinyi kadan ki koreni daga nan. " Da yake ta juyawa kofa baya bata ji shigowar Alh Maitama ba babanta. Ita kuwa Anti Bebi ta riga ta ganshi sai kawai ta rike hannun da Shuhada ta doke ta soma ihu. "Kiyi hakuri don Allah kada ki sake dukana. Indai gidan nan ne yau zan barshi har abada" Tunani ta fara ko zautuwa Anti Bebi tayi sai taji tsawa daga bayanta. Kafin ta ankara har ya shigo yazo ya rungumeta yana mata sannu. Ita kuwa babu kunya ta cigaba da makale masa a gaban 'yarsa. Bakinciki fal zuciyar Shuhada ta juya zata bar wurin ya dakatar da ita. "Ba dole miji ya sakeki ba. Ina kallo kika kai mata duka sannan har na shigo ko gaisuwa babu zaki bar wurin" Hawaye take yi tace "Daddy kayi hakuri ina wuni" "Rike gaisuwarki bana so. Kuma ki sani indai zaki zauna a gidan nan ko kallon banza kika yiwa Bebi sai na saba miki." Anti Bebi ta langabe a jikinsa tana kallon Shuhada kasa-kasa. "Alhajina ka karbo albashin?" Jakar hannunsa ya mika mata yana murmushi "gashi amma na cire kudin mai gyaran mota da yayi min last week. Idan kin kasa kudin sai ki bani nawa ina son siyan wasu abubuwa" Shuhada kasa tafiya tayi don tsananin mamaki. Da gaske akwai mata marasa imani masu juya miji kamar waina. Ji Daddy dinsu mutumin da ake gani da mutumci da kima a waje ya dawo tamkar yaron goye a gaban mace. Kashewa Shuhada ido tayi sannan a hankali tace kadan kika gani. Da wannan bakincikin Shuhada ta ja kayanta hanyar tsohon dakinta. Anti Bebi ta tace cikin kissa "ki kai kayan dakina kafin nasa a gyara miki naki" Daddy ya juyo "Bebi kenan, kirkinki yasa kullum nake kara sonki." Shuhada ko waigowa batayi ba don kada ta ga karin kayan takaici. ***** Bayan tafiyar Mama da daddare Awaisu da Gimbi suna daki tana masa korafin jikinta na ciwo yace ta kwanta yayi mata tausa. "Shiyasa rannan Maamu take cewa da ma zan nema miki aikin da zaki tashi da wuri saboda ta kula ni da ke duk aiki yayi mana yawa." Tashi tayi daga kwanciyar "so take yi na dena aikin?" "Tace dai tana tausayinki ne. Tun farkon zuwanta ne muka yi hirar" "Uhmm humm" kawai tace bata kara magana ba. Zuciyarta tana kitsa mata nan gaba Maamu kokari zatayi ta fara juyasu. Wato har aikinta ya tsaya mata a rai. ****** Washegari Maamu ta tashi da gudawa. Tun dare Gimbi tace ayi miyar zogale. Awaisu yana wurin yace Maamu bata ci yana bata mata ciki. Sai Gimbi tace zata yi mata miyar kuka. To dama yanzu komai ta fada ya zauna sai ya amince zata yi din. Da ta tashi bata ce Laminde tayi mata wata miyar ba domin a ganinta barna ne akan 'yar miyar da ake zubawa Maamu kadan a sake kada wata. Haka aka kai mata tuwon da miyar zogale. Duk da tasan yadda yake yi mata amma dole ta ci saboda yunwa. Har su Rumana suka tafi Islamiyya karfe uku tana fama amma ta rasa wa zata fadawa saboda rashin Hausa. Shi kuma Awaisu tun asabar bai kara shiga dakinta ba. Laminde ta shiga kai mata abincin rana ta ganta tana bin bango saboda rashin kuzari zata shiga bandaki. Taimakawa tayi ta shigar da ita ta koma bakin kofa tana jira ta gama ta fito da ita sai ta fadawa masu gidan. Gimbi ce ta kirawota zata aiketa karbo dinki. Tana zuwa ta fada mata halin da taga Maamu. Gimbi tace to zata duba. Daga nan Laminde ta fita ita kuma ta manta. Shiryawa taje tayi tace Awaisu yazo ya kaita unguwa. Daya tambaye ta ina zata je tace gidan Anti Bebi. Shi dai yasan da bakinta take fadin halayen Antin wanda yasa basa hulda da ita. Amma ya kasa cewa komai sai mukulli da ya dauko. So take yi yau ta nunawa Anti Bebi yadda ta fara juyashi sannan idan da hali a dauke hankalin Mama daga sake yi mata tambaya akan Maamu. Bayan fitarsu Maamu tana kan toilet seat ta kasa tashi saboda gwiwarta duka babu kwari. A hankali cike da kasala ta rinka kiran Rumana da Laminde shiru babu amsa. Tun tana iya kiran har ta koma kuka. Tayi yunkurin tashi ta kasa sai taji kamar zata fadi. Haka ta koma ta zauna tana ta kiran mutanen gidan harda Gimbi. Bacci ne ya dauketa a wurin saboda gajiya da yunwa ga matsanancin ciwon kai. Harisu da Baaba Hure tayi mafarki wai sunzo daukarta. Ta farka a firgice. Rabonta dasu tun ranar da wayarta ta fada ruwa a bandakin. Kwan fitilar ya mutu tasa Rumana ta fadawa Gimbi har sau biyu ba'a gyara ba. Shine suke haskawa da wayarta. Tsautsayi yasa ta fadi har yanzu bata kunnuwa. Tun Maamu tana tunanin wani zai zo har ta hakura ta soma kokarin tashi. Tana mikewa ta zame a wurin ta fadi.15*KASHE FITILA*💡16 *Batul Mamman*💖 Shuhada ta zuge wata 'yar madaidaiciyar jaka bayan ta gama hada kayan da zata bukata. Tun washegarin dawowarta ta yanke shawarar tafiya Kaduna wurin mamanta. Zama a gidan nan ko kadan bata jin zata tsinci wata riba. A kwana biyun da tayi babanta tamkar hoto haka take ganinsa. Bashi da wani motsin kansa sai abin da Anti Bebi tace. A wani firgice yake idan yana gabanta. Wannan abu ga rabowa da masoyinta Tajuddeen suka hadar mata suka karawa gidan zafi. Tana share hawaye yayar Tajuddeen ta kirata a waya. Tana dauka kuka suka saka a tare. Ko sati hudu Yayar batayi da dawowa Nigeria ba bayan ta raka mijinta conference Singapore. Kuma a gidan Shuhada suka zauna. Hakuri tayi ta bata sannan ta sanar da ita suna hanya ita da Gwaggonsu zasu zo bayar da hakuri har gida. Babansu ma yanzu zai bi Alh Maitama office ya bashi hakurin wannan cin fuska da aka yi musu. Shuhada cewa take yi babu komai ba sai sun zo ba amma suka dage. Tunaninta kada Anti Bebi ta wulakanta su. Zama tayi jefi jefi tana leka taga da ta ji karar mota. Tafi son ta fara hangosu idan sun iso taje ta tarosu. Tana cikin leken saboda jin an bude gate ta hango wata mota dark green ta shigo. ****** Kafin isowarsu Gimbi ta yiwa Anti Bebi text tana fada mata zasu shigo ta fito ta ganewa idonta yadda ta mayar da Awaisu. Dan mayafinta da ta saba ta dan rufe rabin kanta ta fito waje. Yana gyara parking Gimbi tace ya fita su gaisa da Anti Bebi. Kallonta yayi shiru yana nazari sai kuma ya fita din. Da sauri Anti Bebi ta karaso tazo gaban motar. "Oyoyo, oyoyo yau ga Awaisu a gidana" Dan rissinawa yayi zai gaisheta tayi saurin dafa kafadarsa. "Haba Awaisu dana. Ina kai ina durkusawa, sai kasa a kalleka ai" Hannunta da tasa a kafadarsa taki cirewa harda karkade masa wani dan zare daga wurin wuyansa. Wannan abu duk a idon Shuhada. Duk da bata kaunar Anti Bebi batayi zaton mugun halinta harda bin wasu mazan ba sai yanzu. Kuma tasan ko ta fadawa Daddy bazai yarda ba. Abu daya zatayi shine taje taci mutuncinsu daga shi har Anti Bebin ta huce haushi. Gimbi tana daga cikin mota murmushin fuskarta ya dauke ganin Anti Bebi ta dafa mata miji. Fitowa tayi ba arziki tace su shiga ciki. A nan suka bar Awaisu yana jiran fitowarta. Suna shiga Shuhada tana fara saukowa daga sama taji Anti Bebi tace "na manta uwar kishi ce kin wani bata rai don an taba miki miji. Dadin abin nima gidan aurena kika zo" Cikin tsiwa ta amsa mata "Anti kece sai wani dafa shi kike yi. Ni yanzu dai babu yadda za'ayi Maamu ta bar gidan lokaci guda? Kafin na samo kanshi wallahi duk dare yana dakinta ki rasa me suke yi. Wani lokacin sai na fara gyangyadi yake dawowa" "Gimbi anya baki fini tsiya ba. Wannan da nono na kika sha maza sun shiga uku mata sun ga ta kansu. Yanzu uwa da danta ma sai kin zargi wani abu. Ko don irinku Gimbiya da ina da da wallahi matarsa bata isa ta juya shi ba" Tafawa sukayi kamar sa'annin juna. "So nake yi ta koma garinsu kawai ya rinka yi mata aike. Zaman tare damu ne bana so. Duk abi a sawa mutane ido. " Sai ta dan rage murya har sai da Shuhada ta dan kara bene biyu domin taji da kyau. Dayake wurin zagaye ne basa ganin juna "Kuma ina so ko za'a dauke hankalin Mama daga kan gidana. Ai na fada miki ranar da tazo yadda muka kare" Anti Bebi ta hangame baki " Iyye, Gimbiya kina burgeni. Kin cika mace wadda tasan meye 'yancin rayuwa. Wasu 'yan bokon miji da danginsa suyi ta gasa su amma sai su rinka iyayi wai basa bin malamai. Kuma duk karya ne. Tunda da kanki kika nema to kisawa ranki Amina ta bar shiga sabgar da baki sakata ba" Duk da Gimbi bata so abin ya kai haka ba amma ta fara jindadin mallaka da juya miji. Burinta karuwa yake yi domin yanzu har ogansu a banki take son ya dena mata maganar latti. Shuhada tana tsaye zuciyarta har bugawa takeyi don tsoron matan nan. Wannan wace irin masifa ce muke daukarwa kanmu akan duniyar da bazata dore ba. Komawa tayi saman a hankali jikinta a sabule. Sai a lokacin taji tausayin mutumin da hannun Anti Bebi ya taba. Lallai ya aurowa kansa masifa. ***** Karfe biyar da rabi Laminde ta dawo gida. Tasan dama yaran suna Islamiyya. Rashin ganin Gimbi yasa tayi tunanin ko sun kai Maamu asibiti, kwarai taji tausayinta dazu. Ku6ewa ta zauna gurzawa kafin su dawo a bata shinkafar tuwo ta dora. Tana aikin su Rumana suka shigo. Dakinsu ta wuce ta cire kayan makaranta sannan ta shiga bandaki yin alwala saboda an fara kiran magariba. Tana budewa ta ga Maamu a kwance ko motsin kirki bata yi. Ga jikinta alamun ta sake yin gudawa a wurin. Ihun kuka Rumana ta saka tana kiran Laminde. Sai gata a guje tare da su Haris. Duk su biyun sun rude suna zaton ta mutu ne. Suna kokarin dagata su Awaisu suka dawo ya tsaya wurin maigadi Gimbi ta shigo. Daula ce ta fada mata Maamu babu lafiya tabi bayanta. Daga bakin kofar bandakin ta toshe hancinta. "Hmmmm warin meye wannan haka" Tana kallo da kyar Maamu take bude ido ta jingina da jikin Rumana ita kuma Laminde tana tara ruwa a bokiti da zata dauraye mata jiki tace . "Maamu ce babu lafiya, a kwance nan muka ganta" Tabe baki tayi "Toh, to Allah Ya sauwake. Gyara mata jikin kafin na dawo" Tana fita ta ga Awaisu a falo Haris yana fada masa. Da sauri ta karaso da alamun gigicewa har tana jifa da mayafi. "Abban Haris juya mu kai Maamu asibiti bata da lafiya." Duk yadda yake nuna rashin kulawarsa damuwa ce ta ziyarce shi ya ruga dakin a guje. Ganin Rumana ta kasa rike Maamu sosai kafin Laminde ta dauko musu nata sabulun saboda nasu saura guntu da suke amfani dashi anki basu wani. Mantawa yayi da kayan jikinsa ya shiga ciki ya dagata ya saka a bahu sannan ya soma dibar ruwan yana wanke mata jiki da hannunsa yana kiran sunanta cikin tashin hankali kada ta mutu. Da Laminde ta kawo sabulun hannun Rumana ta ja suka fita ta rufe kofar. Rumana tana son komawa Laminde ta girgiza kai. "Ki bar Kawunki ya sami ladan mahaifiyarsa Rumana. Dauko mata kaya kafin ya gama" "Namiji ne fa" ta fada tana yatsina fuska. Tuni Kawun nata ya fice mata a rai. Laminde tayi murmushi "to naji bari naje ya bani nayi mata wanka" Gimbi ce ta shigo tana tambayar yana ina suka nuna mata bandakin. Muryarsa taji yana cewa "Gimbi zo kiyi mata wanka zan chanja kaya muje asibiti" Gabanta har faduwa yayi, wannan kazantar ta jikinta zata taba..... Laminde tana kallonta sai ta shiga tace zata yi mata. Tsoro taji kada da gangan Gimbi ta saketa ta fadi. Bayan anyi mata wankan ne Laminde ta kula hannunta daya ya kumbura ta wurin babban yatsanta ga dukkan alamu tayi targade. Haka ta shiryata Awaisu da Gimbi suka kaita asibiti. Suna can ya kasa zama har likita ya fito yace suna mata karin ruwa sannan anyi mata gyaran targade. Hankalinsa duk baya jikinsa sai da ya ganta. Da kyar take magana idanu duk sun fada ciki tace ya kirawo mata Harisu a waya. Gimbi jin an ambaci sunan daya makiyin nata ta kasa kunne sai dai bata jin me Awaisu yake fada da yarensu har ya gama wayar. Juyowa yayi yace "Gobe in sha Allah Yaya Harisu zai zo da daya daga cikin matansa da Baaba Hure. Ina tsammani zasu taho da kanin Maamu ma. Ki kira Laminde a gyara musu dakin baki kafin mu koma gida" Kirjinta ne ya buga, mutanen da ta raina zasu cika mata gida.16*KASHE FITILA*💡17 *Batul Mamman*💖 Awaisu bai lura da yadda Gimbi ta chanja da wuri ba daga jin maganar zuwan su Harisu ya mika mata mukullin mota. "Kije gida ki taho muku da kayan bukata na kwana. Idan kin dawo sai na tafi da motar" Zaro idanu tayi tana neman amsar da zata bashi domin gujewa kwana da Maamu. Itama Maamu da ta gane me ya fada murya can kasa saboda ciwo tace masa ya tafi da matarsa a kawo mata Laminde ko Rumana. Da ta ga zaiyi gardama tace saboda yara ne. A ranta kuwa cewa take gara ta kwana ita kadai da a barta da Gimbi. ***** Harisu dakin Baaba yaje ya fada mata Maamu babu lafiya. Hankalinta kuwa ya tashi tace to yaje ya sanarwa 'yan uwanta. Har zai fita ta sake kiransa. "Dangin mahaifin Awaisu ma ya kamata ka fada musu. Ai kana jin yadda suke yada mana magana wai ya tare a jikinmu baya musu komai" Harisu ya sha kunu "haba Baaba har yaushe zaki bari zancensu ya dameki. Allah Yana gani yadda duk zuwansa garin nan sai yaje kuma yayi musu alheri. Neman rigima ne kawai" "Duk da haka kaje ka fada musu ko zasu tura wani yaje dubiya". "Har na fadawa Awaisun kila muje da kanin Maamu ko wani dai cikinsu. Mu da zamu je dubiya kada kuma a dorawa iyalinsa wahala" Baaba Hure tayi wani murmushi wanda ita kadai ta san ma'anarsa. "Baka saba yi min musu ba Harisu. Nace ka fada musu yadda zasu tura wakilinsu dubiya. 'Yan uwanka ma zan sa a kirasu a waya ko mutum biyu a samu. Cikin matanka ka dauki babar Rumana saboda ta gano 'yarta tunda ka hana a kawota hutu. Sauran suma a hankali sai kaje dasu tare ko daya bayan daya" Harisu kasa motsawa yayi jin wannan hadi na Baaba. Duk girman gidan Awaisu idan sukayi yawa zasu takura musu ne. Ga mara lafiya kuma ga baki da wanne zasu ji. "Yaya kaki tafiya ne?" Takalmansa ya saka yayi waje. Ita kuwa Baaba Hure ta gyara kwanciyarta tana jira ya dawo ya kira mata Awaisu ta ji yaya jikin Maamu. Ba komai yasa take son tarawa Gimbi jama'a ba sai bakar maganar da suka yi mata ita da Anti Bebi a rashin sanin bahaushiya ce. So take ta tabbatar Gimbi bata son dangin Awaisu da gaske ne ko kuwa dai 'yar tsama ce irin ta mata da dangin mijinta. ***** Gidansu Maamu ya fara zuwa inda duka yayyenta maza da kanne suke tare da iyalansu. Bangaren wani cikin 'yan uwan yaje suka gaisa ya sanar dasu abin da ke faruwa. Nan da nan 'yan uwa suka taru ana jajantawa sannan suka ce zasuyi shawara wanda zaije a madadinsu. Harisu yana fita Hajja Jume matar babban wan Maamu wanda ya dade da rasuwa ta dogaro sandarta ta taho. "Yanzu labari yazo min za'a tafi wurin Safara'u dubiya ko" Bashar wanda yake matsayin babba yanzu ya hade rai yana hararar Atika jikar Hajja uwar hada gurmi. "Tikeke akan gulma zanyi maganinki" Hajja ta daga sanda tana fada "wanda ya fasa Bashar, nace wanda ya fasa. Yarinya duk kun takura mata kamar ita kadai ce jika. Duk abinku a nan gidan zata zauna. Bani da kowa a gabana sai ita. Tunda tazo ku da iyalanku kun hade mata kai kamar ka jininku ba" Tikeke ta sunkuyar da kai ita a dole a bar tausayi ce "Hajja babu komai dama na fada miki ne kada a gama rabon waye zaije Abuja gidan Kawu Awaisu a barmu a nan" Hadi yayi caraf yace "kada ma kusa rai, ni da Yaya Bashar zamu je. Ai ba gayya za'ayi musu ba" "Wallahi baku isa ba Hadi. Ni zaku nunawa wariya don nawa mijin ya rasu. To ni da Tikeke kamar munje mun gama. Idan da kara ni ya kamata na fadi masu zuwa tunda yaron nan dana ne. Malam da Safa'ra'u ciki daya suka fito ba kamar wasu 'yan uba ba" Hayaniya ce ta kaure sosai a tsakaninsu karshe aka tsaya akan za'a tafi da Tikeke, Kawu Bashar da matar Hadi. Idan basuyi haka ba tijarar Hajja bata tsallake kowa. Ba karamin aikinta bane ma tasa danta baban Tikeke ya kaisu tunda dreba ne. **** Kasuwa Harisu ya koma can wurin masu gwanjo ya hadu da Bomai kanin baban Awaisu. Dattijo ne rigimamme na ajin karshe. Yana cikin masu yiwa Harisu habaici wai sun shanye Awaisu baya bi ta kansu. Bayan jarin gwanjon ma shine ya bashi. "Alh Harisu kenan, yau an leko mu" "Kawu Bomai yaya kasuwa?" Kan benci ya zauna yana zukar sigari kafa daya kan daya. "Gata nan muna fama. Yaya akayi ne?" Kamar yadda ya sanar da 'yan uwan Maamu haka ya fadawa Bomai. Wani tsalle ya daka ya tashi dama shi ba jiki ba sai tsawo. "Maamu tamu ce babu lafiya? Kace ban ga ta zama ba. Kayi kyan kai sosai da ka fada min. Asubar fari zanzo nan gidan naka mu tafi" "Sai wuraren karfe tara zamu tafi. Nace su sauran zaka sanar dasu ko naje na fada musu. Awaisu yace jikin da sauki dai" Matsowa yayi daf da Harisu "Tunda na sani ka bar maganar kawai ni zan sanar dasu." Sai kuma ya gyara tsayuwa yana kwantar da kai gaban Harisu "Maamu mutun ce, wato ba don haduwarta da Mal Sa'adu mai rasuwa ba dama ni naso na aureta saboda kula da maraya. Kuma gashi ni ban haihu ba. Shiyasa nake jin yaron nan a raina sosai. Kaga sau biyar fa yana bani jari. Yaro yayi halin iyayensa wurin karamci" Harisu gyada kai kawai yake yi ya samu ya bar wurin. Baaba Hure ta hadashi da aiki. Me zai sa tace kowa sai yaje. Tausayin Awaisu da Gimbi wadda za'a hada da baki ne ya kama shi. Yana kallo Bomai ya kulle gwanjonsa ya saba a kafada yayi hanyar titi. ***** "Hinde maza maza fito ki fara hada kaya" Hinde na bandaki ta fito da sauri bota a hannu. Ajiye botar tayi ta sa hannu ta toshe gefen hanci ta rangada guda tana tafa hannuwa "Ayyiriririiiii, sai yau kaga damar sakin nawa, to ka sani kuma ka jira ina gama idda zan sami miji da ya amsa sunansa ba irinka ba kashi da rai. Nawa kayi min ne sakin" Botar da ta fito da ita ya dauka ya kafa a baki ya sha ruwan sannan ya kuskure baki ya tofar. "Dadina dake wutar ciki, baki ji bayani ba kin hau suki burutsu. To ai sai ki tafi nima na huta" "To dai gaya min me ya faru idan ba sakin bane kake min wannan kiran" Kan kullin gwanjon ya dare ya zauna "Abuja zamu koma gidan dana" Wata muguwar shaka Hinde tayi masa har yana zaro idanu "munafuki ashe har da gareka ban sani ba. A wace tashar ka hadu da babarsa" Hannunta yake duka da kyar yana cewa "Awai,aaaaw,awsu" Sassauta rikon tayi yace "AWAISU ne fa dan marigayi yayana. Kasheni zakiyi ne?" Hinde ta zauna shirim a gefensa tare da murza masa wuyan. "Kaine baka iya kawo labari ba. Kace Awaisu na Maamu" Nan ya labarta mata yadda sukayi da Harisu da kuma kudurinsa "Yace kwana biyu zamuyi. Amma so nake ki hada kayan kamar na sati. Sai kuma mu saka kamar uku uku a jikinmu kada a ga Ghana mazigo din kayanmu da girma. Idan munje zan sa ya nema min aiki. Kema ki rinka yiwa Gimbiyar nan ladabi. Kinsan durkusawa wada ba gajiyawa bane." Hinde sai murna zasu Abuja. Ko Bomai bai fada ba bata ga dalilin da zaisa idan sun je ta dawo Fika ba. Kallonta yayi ta shige daki ta fara fiddo kayansu zata wanke yace "Hinde don Allah idan munje kada ki nuna hali, banda dauke dauke kinji ko" Harara ta galla masa idonta kamar ya fado. Me zai kaita sata kuma yanzu, ita da tayi a gidan biki 'yan mata sukayi mata duka sai da hakorinta na kasa ya cire. ****** Daren ranar Gimbi kasa bacci tayi. A haka ma don bata san mutum nawa ne masu zuwa ba. Sau biyu Awaisu yana farkawa ya ganta a zaune sai tace masa jikin Maamu ke damunta. Gashi likita yace harda rashin cin abinci sosai. Harda kukanta tace "My dear ko zaka tambayi Maamu me tafi so sai na rinka dafa mata. Gobe zan dauki hutu ko na sati ne na kula da ita" "Kema kinsan bazasu baki wannan hutun ba. Ki bari kawai tunda akwai masu zuwa" Murmushi tayi, don tana tunanin a goben Anti Bebi zata kaiwa Wangesi bukatarta akan ogansu. Sake marairaicewa tayi "Duk laifina ne da nake zuwa aiki bana iya kulawa da ita yadda ya kamata. Kullum da safe idan naje fada mata zan fita Maamu sai tayi min addua. Yanzu idan suka zo aka ce na barta da yunwa fa." Kuka ta fashe dashi Awaisu ya rarrasheta. Karshe tace masa zata bar aikin kawai ta kula da gida. Ga mamakinta sai taga ya bata goyon baya. A zuci tace wato shima bakinciki yake da aikin. To yanzu ta fara. ***** Da safe tunda babu Laminde gashi tana son burge Awaisu haka tayi farfesun kayan ciki da dankali ta hadawa Maamu Awaisu ya kai asibiti. Bayan su Haris sun tafi makaranta ta fadawa Anti Bebi halin da take ciki da bakin da zasu zo. "Zage damtse zakiyi ki kyautata musu kada wani ya sami bakin magana akanki" inji Anti Bebi. Ai kuwa ta wuni a kitchen tana girkin tarbar baki mutum hudu ko dubiya bata samu zuwa ba. Sai yamma likis suka iso mota biyu. Awaisu ma shigowarsa kenan kuma Haris yayi masa waya ya sanar dashi karin da aka samu yace ya amince duka su taho tare akwai wurin kwana. Sai dai kuma ya manta bai fadawa Gimbi ba. Jin tsayuwar mota tabi yaranta suka taho da gudu tarbarsu Baaba Hure. Sai ga Gimbi murmushi ya makale a gefen baki. Mutane ta gani wanda ta sani da wanda bata taba gani ba. Baaba Hure, Anti Ummukulsum, Harisu, Maman Rumana, Kawu Bashar, Ammu matar Hadi, Tikeken Hajja, Bomai da matarsa Hinde. Mutum takwas. Tun a zuci ta fara kuka.17*KASHE FITILA*💡18 *Batul Mamman*💖 Zuciyar Gimbi harbawa ta rinka yi sosai saboda wani bacin rai da ya danneta. Kasa daurewa tayi duk iya kokarinta ta fashe musu da kukan bakinciki mai sauti. Ai kuwa hankalinsu Baaba Hure ya tashi matuka sun zata ko Maamu rai yayi halinsa ne. Da yake ta fara kwarewa da kissa irin ta Anti Bebi sai tayi saurin goge hawayen harda rungumo Baaba tana kallon Harisu a zatonta shi kadai yake jin Hausa. "Wallahi tsabar murnar ganinku ne Yaya. Tun jiya da yace zaku zo nake murna. Allah Sarki Maamu yau zan gani ni da ita wa yafi murnar zuwanku" Daga gefe taji ance "kissa adon mata, Bomoi ka ga wadda ta fini" Hinde ta fada da sunan rada duk da tasan ana jinta kuma da hausa. Bomoi ya galla mata harara ya kalli Gimbi yana murmushin dole. Daga zuwansu zata nemi janyo musu bakin jini wurin matar gida. A razane Gimbi ta kalli Hinde har cikinta yana kadawa. Sakin fuska tayi ba arziki kamar bata fahimceta ba tace su shigo ciki. Mukullin wani daki ta waje ta bawa Harisu inda ya taba masauki lokacin zuwansu Hajji. Nan suka shiga shi da Kawu Bashar da Bomoi wanda yake ta zuba surutun haduwar gidan dansa gudan jininsa. Daula ce tayiwa Baaba Hure jagora zuwa dakin Maamu inda zata zauna. Wani daki a gefensa kuma Gimbi tace Ummukulsum, Maman Rumana, Ammu, Hinde da Tikeke su shiga suyi wanka sannan su fito cin abinci. Tikeke ta zumburo baki "Haba Hajiya ko ruwa bamu sha ba zaki ce muyi wanka. Allah Ya gani sai naci abinci nake iya komai." Ammu ta riko hannun Tikeke tana kokarin fita daga dakin zata koma falo inda ta hango kwanukan abinci an jere su. Kokawar fizgewa Tikeke ta somayi Ammu ta canja harshe tace zata fadawa Kawu Bashar. Rai a bace ta kwace hannunta ta shiga bandakin tare ta bugu kofa. Jiki a sanyaye Gimbi ta fita daga dakin. Yau kuma irin bakin da tayi kenan ta fada a zuci. Falon taji kamar yana warin gumi a cewarta ta dauko air freshner ta shiga fesawa. Juyawar da zatayi ta hada ido da Baaba Hure tayi saurin ja da baya. Baaba ta saki fuska "Dama kwan fitilar bandakin ne naga ya mutu. Idan akwai wani ki taimaka a saka min don in yamma tayi ba gani nake sosai ba bare kuma a duhu" Mamaki ne ya bayyana sosai a fuskar Gimbi jin Baaba tana hausa. Dazu ma taji wata tayi a waje. Yanzu bata isa ta juya harshe tayi gulmarsu a gabansu ba kenan. "Baaba bari idan Abban Haris ya dawo sai a saka miki ki shiga" Baaba ta dafata da hannu daya tana dan tafiya "muje ki kaini naki sai nayi alwala a can. Banyi sallar la'asar ba ga magariba tana gabatowa" Ba'a son ranta ta kai Baaba bandakinta ba. Maamu kuwa ko hanyar dakin bata taba takawa da kafarta ba. Tana zaune tana ji Baaba Hure tana kaki. Takaici ya isheta ta fita ta koma dakin Awaisu sannan ta kira Anti Bebi. "Na shiga uku Anti, su takwas kamar ance musu ta mutu. Ina zan kaisu" "Ba na son shirme kinji ko. Ki tashi ki je duk yadda suke so kiyi musu. Idan kika bari suka gane wani abu to karshenta su ki tafiya da wuri. Kinga garin neman gira kin rasa ido" Maganar Anti Bebi gaskiya ce. Da saurinta ta shiga kitchen ta dora macaroni tunda dama shinkafa da miya tayi da kuma tuwon dare. Kafin ta gama Awaisu ya shigo ya tafi wurinsu Harisu suna gaisawa. Sai da sukayi sallar magariba suka ci abinci sannan suka fara shirin tafiya asibiti gabadayansu. Gimbi tana ta raha da rawar kai ita me son surukai. Sun firfito waje Awaisu ya kira drebansa da yake kai yara makaranta ya bashi mukullin mota "Sunday gashi ka debe su Yaya Ummukulsum ka wuce dasu asibitin da aka kwantar da Maamu. Zan tsaya a atm ne sannan na taho da su Baaba" Sunday ya dan rissina a ladabce "Oga yaushene Hajiya babu lafiya, wane asibiti ne.?" Awaisu yaji kamar ya raina masa hankali yace "Inda ka kai musu abincin rana mana" "Ban fita ba tunda mun dawo da su Haris" Idanun Awaisu suka kankance yana kallon Gimbi "da kanki kika kai musu abincin rana? Ina na daren ne ma ban ga an dauko ba" Idanun Gimbi nan da nan suka yo waje ta rasa amsar bayarwa. Baaba Hure tana kallonta tasan bata da gaskiya "Gimbiya kada kice min ba'a kaiwa Maamu abincin rana ba bare na dare" "Uhmmm, uhmmm" nan fa jikinta ya soma rawa ganin idanu a kanta ga Awaisu yana wani huci kamar mayunwacin zaki. Irin wannan fushin nasa ba kasafai yake ba. Kuma a tunaninta yanzu da Wangesi ya gama masa aiki bai isa yayi mata ko da mugun kallo ba. Tsawa ya daka mata kamar ya kai mata duka "ki bani amsa mana" Harisu ne yayi magana ganin ransa da na Baaba Hure a bace yake. Yaran ya fara cewa su shiga motar Sunday sannan yace "Awaisu meye haka ne kake yi mata tsawa gaban yara. Gimbiya an kai abincin?" Kuka ta saka saboda tsabar bata damu da Maamu ba shaf ta manta da batun abincin. Na safe ma da tayi saboda ta burge mijinta ne yaji dadi. "Wallahi Yaya Harisu ina ta aiki ne na sha'afa." Ummukulsum tace "wannan ba magana bace Gimbi. Akwai wani aiki da zai sha kanki sama da nata da take asibiti? Yanzu ga jinya ga yunwa daga ita har Rumana" Ido sharbe da hawaye ta rinka basu hakuri. A ranta kuwa duk tsine musu take yi suna neman jaza mata masifa wurin miji. Baaba Hure tamkar ta cinyeta da fada. Tana yi Awaisu yana yi don ya kule karshe. Harisu ne ya rinka basu hakuri. Su Tikeke kuwa an sami abin kallo da gulma. Marasa jin hausa sosai babu damar tofawa. Duk wani haushin Gimbi da yake ji kwanakin baya ya kasa magana tun jiya da ya ga Maamu a wannan yanayin yaji kamar an bude masa ido. A fusace yace mata taje ta dauko abincin. Wani tsoron ya sake kamata domin batayi dasu ba. Hasali ma dai babu sauran abinci a gidan. Awaisu yayi fadan da hausa ya koma saka yarensa kamar ya kai mata duka. Baaba Hure ko a jikinta saboda tun maganar da sukayi akanta take jin Gimbi ba matar kirki bace. Harisu ya ja shi gefe ya soma nasa fadan "Wani sabon salo ne ka koya zaka zubarwa matarka mutumci a gaban baki. Dubi yadda suke kallonka. Kana tunanin wannan labarin bazai je Fika ba" Kwalla ce take barazanar fita daga idonsa saboda tunanin yaya Maamu ta wuni. Yaje da azahar daga wurin aiki amma ita dasu Laminde babu wanda ya fada masa "Yaya ace tun abincin safe saboda Allah" Harisu ya dafa shi yana murmushi "to kuka zaka yi min? Awaisu 'ya'yanka hudu fa. Muje su koma suyi girkin kafin dare ya karayi a hanamu shiga" "Bari kawai ma saya a hanya. Karfe tara suke hana shiga sai goma na safe kuma" Tare suka koma suka shiga motocin. Wasu na motar Sunday tunda babba ce school bus sauran Awaisu ya diba. Gimbi tayi turus a waje ganin Bomoi ya shige gaba abinsa. A dakile Awaisu ya nuna mata bus din "Idan zaki je ki koma bus din inda mata suke" Ranta na kuna kamar tace bazata ba ta koma ta shiga tsakiyar Ammu da Hinde. Kallonta suka rinka yi ta kasa motsin kirki saboda sun matseta. ***** Suna zuwa a kwance suka sami Rumana a gadon da yake gefen na Maamu tana bacci. A kasa kan abin sallah kuma Laminde ce take cin dafaffiyar gyada. Naira hamsin gareta shine ta siyo musu ita da Rumana suka ci suka sha ruwa. Maamu taki ci tana kwance tana hawaye. Yaushe ne danta zai waiwayeta??? Muryar Baaba Hure taji ta soma yunkurin tashi. Maman Rumana ke rike da hannunta ta karasa da ita bakin gadon saboda dishi dishi take gani. A haka ma don anyiwa idon aiki ne. Hannu ta mika tana laluben Maamu. Ji tayi Maamu cikin muryar dake nuni da tana jin jiki tace "Baaba" Baaba Hure sai hawaye "Maamu sannu, sannu 'yar uwa. Kai Awaisu ku zuba mata abincin nan" Gimbi ce tayi saurin mika hannu zata karbi ledojin ya harareta sannan ya bawa Maman Rumana. Ummukulsum tace "Maamu kin rame sosai" Riko hannun Ummukulsum din tayi "hmmm kayya Ummu jikin tsufa ne kawai, Ina yaran , yaya wajensu Auta Zakiyya" Rumana cikin bacci taji kamar muryar babanta. Firgigit ta tashi. Abin mamaki harda Mamanta da Baaba. Wani tsalle tayi ta diro ta kankame Harisu. Shi kam kunya ma ta bashi a gaban mutane. Ta tafi zata rungume mamanta ta harareta irin abin 'yar fari. Sai kawai ta koma jikin Baaba ta kankameta. Sun gama gaisawa Laminde da Rumana suna gefe suna cin abinci sauran suna ta hira. Basu bar asibitin ba sai shadayan dare. Nurses suna ta zuwa ana cewa su bar hayaniya. Likita ya bukaci ganin Awaisu kafin su tafi. Fada sosai yayi masa duk da karancin shekarunsa akan shi na barin Maamu da yunwa. Duka allurai da maganinta tun azahar ba'a yi mata ba saboda bata ci abinci ba. Sannan jikinta ma yana nuni da alamun rashin kuzari saboda tana bukatar wasu sinadarai a jikinta. Shi dai sai hakuri yake bayarwa yana tunanin wai me Gimbi take yi har Maamu take zama da yunwa. A wani bangaren tuhumar kansa yake da rashin kulawa wadda bai san dalilinta ba ****** Wurin shabiyu da rabi kowa yaje ya kwanata Awaisu da Gimbi suna ta fada. Bashi hakuri take yi amma kamar tana ingiza shi. Bandaki ta shiga tayiwa Anti Bebi text ta sanar da ita. Shawara ta duk da batayi mata dadi ba haka ta karba kafin gobe ta nemi Wangesi. Wurin Baaba taje tayi sa'a bata kwanta ba. Nan ta kwantar da kai ta bata hakuri ta roketa akan ta bawa Awaisu hakuri. A zatonta tuban gaskene tacewa Awaisu magana ta kare daga lokacin. Ya dai ce to amma juya mata baya ma yayi da suka kwanta. Kafin nan kuma yasa ta bawa Ammu da Maman Rumana dakinta saboda wancan yayi musu kadan. Ita Ummukulsum ta canji Laminde zata kwana a asibitin Da safe matan suka tayata girki tana ta kokarin jansu a jiki. ***** Anti Bebi karfe bakwai ta fice daga gida sai kauyen Nasarawa state inda Wangesi yake. Magunguna ya bayar da wasu layu da za'a binne a gidan. Kafin shabiyu ta dawo gida. Wanka tayi ta shirya sannan tace Alhaji yazo ya kaita dubiyar surukar Gimbi. Tun tana chan zazzabi ya kamashi a office ya dawo gida. Wani nau'in asirin akayi masa. Da ya dawo Shuhada ce ta tarbe shi ko kallonta yaki yi. Kudin mota take so ya bata itama ta bar musu gidan. Suna fitowa daga daki Anti Bebi ta marairace wai yace Shuhada tazo suje tare saboda zaman gidan bazai mata dadi ba. Har ransa yaji dadin ta damu da yarsa amma ita Shuhada bata sonta. Dolenta ta fito suka tafi tare. Anti Bebi ta hakimce a baya Shuhada na gaba. Daga bayan mota take ta bashi umarni yana toh kamar wani bawanta. Kafin su je asibitin Shuhada har kuka tayi ganin yadda Daddynta ya koma a gaban mace. ***** Alh Mudi da Mama suna bayan mota dreba na jansu zasu je duba Maamu. Fada sosai yayiwa Gimbi a waya bayan ya sami labarin rashin lafiyar a bakin Saminu. Su da suke garin ace basu da labari har su Harisu sun zo shi kuma Saminu yana hanya. Gimbi hakuri ta bayar kawai. Yadda bata damu da Maamu ba bata ga dalilin da sai sunzo dubiya ba. Dakin yau a cike idan kaga Maamu da Rumana tamkar ranar sallah. Su Mama ne suka fara zuwa ana gaisawa sai ga Anti Bebi ta shigo tana fara'a. Tuni Gimbi ta rikice ganin kallon da Mama da Alhaji suke yi mata. Ita kuwa Anti Bebi don ta bawa Mama haushi ta tafi ta rungumo Gimbi "Gimbiya yaya mai jikin. Tun shekaranjiya da kika fada min hankalina ya tashi. Jiya da kika min waya kuma baki ne dani ban samu nazo ba" Mama ji tayi kamar ta rufe Gimbi da duka a wurin.18