Compiled By Umar Dalha Funtua. Copied By Ummee Yusuf. [3/24, 6:46 AM] Ummee Yusuf: 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA~* 😭😭😭😭😭😭 ( its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman Yusuf) 💫*~FAGEN MARUBUTA WRITERS ASSOCIATION~*💫 *Gidan zaman lafiya, aminci hadin kai da yardar juna insha Allah🤝* Assalamu alaikum masoyana,gani yauma nazo muku da wani sabon novel dina mai dauke da soyayya,yaudara da cin amana.da fatan zai ilimantar kuma ya nishadantar daku.sannan ina fatan zaku cigaba da biyayan novel har zuwa karshe sannan ina fatan zai samu k'arbuwa daga gare ku kaman yadda kuka k'arbi *~FARHAT~*. *~ADDU'AR DA ZAKUYI A LOKACIN DA KUKA TASHI DAGA BARCI~* اَلْحَمْدُ لِلَّهِ الَّذي أَحْيَانَا بَعْدَ مَا أَمَاتَنَا وَإِلَيْهِ النُّشُورُ *~Alhamdu lillaahil-lathee 'ahyaanaa ba'da maa 'amaatanaa wa'ilayhin-nushoor.~* *~Praise is to Allah Who gives us life after He has caused us to die and to Him is the return~.* *~Part one~* Babban shopping mall ne mai girman gaske,wanda yake cike da kayan zamani kama ga kayan masarufi zuwa sutura,kayan kwalama da kayan tand'e-tand'e. Duk wanda ka gani a wajan toh tabbas babban mai kud'ine ko kuma mai fad'a a ji a kasar ko kuma d'an siyasa dan haka kana zuwa bakin mall d'in sai ka saki baki wajan kallon masu zuwa shopping d'in, saboda ka zaci ko gasan nuna motoci ake ko gasan na sutura da k'walliya ake. A'ameen da matarsa Latifa suna cikin masu shopping a wannan mall d'in,suna zagawa a hankali tare da zab'an abinda suke so fuskokinsu d'auke da murmushi kana ganinsu kasan hutu da naira sun gama ratsa jinkinsu. Latifa sai jido kaya take hankali kwance Al'ameen na biye da ita, bayansu kuma ma'aikacin wajan ne yana tura d'an keken zuba kaya,duk abinda ta zab'a ta d'auka cikin keken take jefawa har suka gama sayayyan suka zo wajan da za'ayi musu bill. Makud'an kud'in da zasu biya aka fad'a musu wanda ya ishi wani talakan yayi jari bayan na'uran ta gama lissafin kayan.ba tare da wani fargaba ko b'ata lokaci ba yaciro bounchs d'in 1k guda 2 ya ajiye suka fice zuwa parking lot abinsu ba tare da jiran canji ko kayan da suka saya ba. Suna zuwa wajan motansu Al'ameen shiya bud'ewa Latifa gaban mota ta shiga ta zauna ya maida k'ofan ya rufe sannan shima ya zagaya driver seat ya bud'e ya shiga ya zauna,sai ga yaran mall d'in su 2 ko wanne da kaya niki-niki a hannu sun biyo su.boot Al'ameen ya bud'e musu suka zuba musu kayan suka rufe,sannan yaja motan suka fito a compound d'in mall din suka mik'e zuwa gidansu dake unguwar dosa. Suna tafe suna hiransu cikin jin dad'i da annashuwa, suna wuce manyan gidaje masu k'yau har suka kawo bakin wani tangamemen gida mai kyau wanda duk layin ba gidan da ya kaishi k'yau da tsaruwa. Tun kamin yayi horn mallam isa mai gadi ya bud'e musu k'aton gate d'in ya kutsa kai ciki. Parking lot ya nufa wanda yake cike da cars birjik kala-kala kaman ta sayarwa,waje ya samu ya parker motan sannan suka fito zuwa cikin gida. Masu aikin gidan sai tururuwan fitowa yi musu barka da zuwa suke,wasu kuma suna kwashe kayan da suka sayo na cikin boot suna shiga da shi cikin gida. Cikin takun katsaita da da natsuwa suka shigo cikin waiting palour inda suka tarar da d'ika-d'ikan 'yan mata su 2 suna zaune suna charting a wayarsu. D'agowa sukayi suna musu sannu da zuwa,kai tsaye Al'ameen ya wuce main palour,ita kuma Latifa ta nemi waje ta zauna cikinsu tana "wash Allah na gaji". Har ya kai hanyar da zata sada shi da main palour ya tsaya ba tare da ya juyo ba yace" Latifa zo ki had'a min ruwan wanka" bai jira amsanta ba ya wuce ciki zuwa main palour wanda yafi wancan girma da tsaruwa komai na palourn maroon nd black ne hakan ya k'ara fito da k'yan palourn. Hanyan part d'in shi yayi,yana taka stairs d'in a hankali har ya shigo palourn shi da yaji komai purple nd white ,an tsara shi sosai dan yafi main palourn kaya masu k'yau da tsada. Bedroom ya wuce ya fara rage kayan jikinshi,hulan kanshi ya cire ya ajiye a kan side drower yayi dai-dai da shigowa Latifa,wuce shi tayi zuwa bathroom ta had'a mishi ruwan wankan. Koda ta fito ta same shi ya gama cire kayan shi daga shi sai boxer da vest,tana murmushi tace "an gama ur Highness every thing is set" Murmushi ya maida mata sannan ya wuce zuwa bathroom d'in. Down stairs ta sauk'o har zuwa waiting palour,Fa'iza da shamsiya suna zaune suna chating kaman yanda ta barsu.zama tayi cikin su tace... " ku dai kam ba kuda wani aiki sai ta latse-latsen waya,kuma me kuke jira tundazu a waiting palour?" Fa'iza tace" uhum Aunty kenan chating fa muke kuma muna jiran wata friend d'in mu data ce zata zo". "Hmmmm chatin ko,ba karatu ?yayi muku kyau". Fa'iza tace"yauwa Aunty shekaran jiya dana je gida mama tace in fad'a miki tana buk'atan wasu kud'ad'e". Harara Latifa ta balla mata sannan tace "shine sai yau kike fad'a min?" "Wallahi Aunty mantawa nayi"tace tana maida hankalinta kan wayarta. "Laifina mama zata gani taga kaman na share tane,haba aiko wannan jaraban charting d'in da kuka d'aura akan ku ba zai barku ku tuna da kanku ba bare wani abin". Shamsiya tana jinsu bata ce komai ba. Latifa mik'ewa tayi hanya part d'inta tana ta mita. Wanka ta farayi sannan ta had'e cikin arnen less maroon d'inkin riga da skirt ya zauna das a jikinta. Make up tayi mai rai da lafiya kaman mai zuwa gidan biki,perfumes masu d'an karan kamshi tayi amfani dasu wajan feshe jiki ta sannan ta tashi a gaban mirrow ta dawo kan gado ta zauna. Hannu ta mik'a ta d'auko wayanta da ta ajiye akan pillow,no mamanta ta dannawa kira,yana fara ringing,sai da ya kusa katsewa sannan ta d'auka. Sallama tayi ta amsa bayan sun gaisa Latifa tace" mama dan Allah kiyi hak'uri,wallahi ban samu sak'onki ba a wajan shamsiya sai yanzu take fad'a min kuma ashe tun wai shekaran jiya kika fad'a mata". "Haba Latifa yarinya 'yar kwalisa tauraruwan 'yan mata ba sai kin bani hak'uri ba,nasan baki samu sak'ona ba akan lokaci saboda nasan ba kya wasa da al'amarina".mama tace a d'ayan b'angaren. 'Yar dariya tayi mai cike da jin dad'in irin yabo da kirarin da uwarta take mata tun kafin tayi aure,tace "toh mama gobe insha Allah Shamsiya ko Fa'za zata kawo miki saboda yanzu dare ya farayi". Cikin farin ciki tace " yauwa Latifata godiya nake". "Uhum mama ina baba?"Latifa ta tambaya. Tabe baki Mama tayi kamin ta amsa " wannan solofiyon uban naku yana can me mataccen zuciya me ya iya banda zaman banza". "Toh Mama sai da safen ko "?"Latifa ta katse Mama duk da tunda suka taso haka taga tsakanin Mama da Babansu amma sam baya mata dad'i. " Toh Allah ya kaimu 'yar kwalisa". Ajiye wayan tayi ta kwanta rigingine a hankali kan gadonta tana tariyo rayuwarta ta baya da yanda burinta ya cika na samun miji mai kud'i dan ta zama tauraruwa a cikin familynsu,nd ra'ayinsu da tsarinsu yazo d'aya dana uwarta nason kud'i.yanzu haka ita ta d'auki nauyin wasu daga cikin 'yan uwanta,shiyasa ta d'auko shamsiya da Fa'iza kannenta su samu karatu mai k'yau da inganci kuma suyi kasuwa. Hope u will like it. ✍✍✍✍✍✍✍✍✍✍✍✍ [3/24, 6:46 AM] Ummee Yusuf: . 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA~* 😭😭😭😭😭😭 ( its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman Yusuf) 💫 *FAGEN MARUBUTA WRITERS ASSOCIATION*💫 ( *Gidan zaman lafiya hadin kai, aminci da yardar juna insha Allah*) https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ *~Gaskiya naji dad'in yanda kuka nuna min kauna da goyon baya ta hanyan comments,ina yinku sosai sosai.dan haka nima zan cigaba da antayo muku ba kakkautawa~* *~ADDU'AN DA MUTUM ZAIYI A LOKACIN DA ZAI SAKA KAYA~* الْحَمْدُ لِلّهِ الَّذِي كَسَانِي هَذَا (الثَّوْبَ) وَرَزَقَنِيهِ مِنْ غَـيـْرِ حَوْلٍ مِنِّي وَلَا قُـوَّةٍ *~ALHAMDU LILLAHI LATHEE KASAANEE HAATHAA (ATHTHAWBA)Wa RAZAQQNEE MIN GYAYRI HAWLIM WA LAA QUWATIN~* Praise is to Allah Who has clothed me with this (garment) and provided it for me, though I was powerless myself and incapable. *~part two~* Mallam Garba mai kayan miya da matarsa Hindatu cikakkun 'yan garin zaria ne.Allah ya albarkaci auransu da.'ya'ya 3 duka mata. Latifa itace 'yata farko,akwai d'an tazara tsakaninta da mai bi mata wato shamaiya ta bata kusan shekaru 10. Shekara d'aya da rabi kawai shamsiya ta bawa Fa'iza data kasance autarsu dan daga kanta haihuwar ta tsaya musu. Mallam Garba irin mutanan ne da abin duniya bata dame su ba,hasilama shi ba mai magana bane.tsabanin matarshi Hindatu da takasance mayyar kud'i gata da zunzurutun kwad'ayi,baya ga haka masiffafiyace ta bugawa a jarida. Dalilin haka ta raina mijinta take abinda taga dama,shi kuma ganin tafi karfinsa yafita harkanta tare da zuba mata na mujiya. Halinta sak na son kud'i 'ya'yanta suka taso dashi more especially Latifa da tasu tazo d'aya da ita. Duk abinda zasuyi indai zasu kawo mata kud'i toh fa batada matsala.dan haka Latifa tun tana s.s1 ta fara bin maza a lokacin ba ta fi 15years ba. Maza ba irin wanda bata huld'a dasu amma babban saurayinta wanda suke son juna da gaske shine Salees. A haka har ta kare secondry school,da cuku-cukun salees ya samo mata gurbin karatu a A.B.U zaria. Da burin a ranta ta shiga sch d'in,babban burinta shine Allah ya had'a ta da saurayi d'an masu kud'i dan dama karatun bai dameta ba. Ta shiga A.B.U da sa'a cox a lokacin an kawo musu sabbin malamai 'yan service. Al'ameen mudassir yana d'aya daga cikinsu, ya kasance crsh d'in kowace yarinya mai ji da kamta a cikin sch d'in.shi yake d'aukansu languagelanguage. Latifa tana d'aura ido akanshi taji duk duniya ba wanda take so bayan shi,bare ma da taji yanda ake zuzuta cewa mahaifin shi Alhaji Mudassir babban d'an kasuwa ne anan cikin gida da k'asashen waje.duk k'asashen da turai dana larabawa wa'yan da suka cigaba a duniya ,yana da companies da shares ba adadi akowane k'asa dan haka fad'an yawan kud'in shi dogon zance ne. Duk haukan da 'yan matan keyi akansa ko kallo basu ishe shiba,saboda classy guyne shi Alhaji mudassir inuwa haifaffen garin katsina state a batsari local govement. Alhaji Mudassir ya gaji filaye da gonaki da sauran kadarori masu tarin yawa daga mahifinshi Alhaji Inuwa wanda ya rasu tun yana d'an shekara 17. Bayan ya had'a degreensa na farko ya fara juya dukiyan shi,kuma cikin sa'a ya fara dan Allah ya sanyawa kasuwancin nashi albarka dan komai ya tab'a sai ya zama kud'i. Auren zumunci akayi musu shida matar shi Halima wacce ta kasance 'yar baffan shi.bayan auren ne ya dawo kaduna da zama. Allah ya albarkace su da yara 6 duka maza,Hafiz,Fawad,sudais,sa'ad,yusuf sai auta al'ameen.dukansu yayunsa 5 d'inan sunyi aure suna zaune suma nan cikin kadunan sai shi kad'ai ake sa ran ganin nashi in ya gama service d'inshi. Alhaji mudassir ya d'aura 'ya'yan shi kan harkan kasuwancin sa,Sa'ad shine kad'ai yake son yin aiki.doctor ya karanta ,ganin yafi son aikin shi akan kasuwanci yasa Alhaji ya gina mishi asibiti anan cikin kaduna yake aikin shi. Abinda Latifa ta lura dashi shine,Al'ameen yafi son mace mai kamun kai da shigan mutunci.saboda in yana musu lectures ta lura in akayi tambaya yafi daraja tambayan wacce ya ganta cikin shigan mutunci. Nan itama Latifa ta dage da shigan mutunci musamman tasa akayi mata d'inkunan hijabai dogaye masu hannu har k'asa,duk dan ta ja hankalin shi,sannan duk wani hanyan da zai had'ata da al'ameen kuwa shi take bi. Tayi sa'a dan sosai take burge shi wasa-wasa ta samu fada a wajan shi,har ya kai suna hira.kullum sai ta bi shi office ta fake da sunan karatu su sha hiransu. Wani abinda ya d'aure mata kai game da al'ameen shine duk shak'uwar da sukayi bai tab'a furta mata kalman so ba,dan haka ta nemi shawaran k'awarta aina'u. Labarin wani shahararren boka aina'u ta bata,dan haka ba b'ata lokaci suka isa gare shi dan neman taimako. Cikin satin da ta fara amfani da k'walli da turare da boka ya bata Al'ammen ya furta mata kalaman so kuma yace da gaggawa yake son a d'aura musu aure. Yanzu kullum shi yake kaita makaranta kuma ya dawo da ita gida da daddare kuma ya dawo suyi hira,takai ta kawo abincin dare ma agidansu yake ci wanda yasha surkullen boka. Murna a wajan Hindatu da suke kira da mama ba magana ganin irin babban kamu da 'yarta tayi,saboda har sunyi hannun riga da talauci tun kamin ayi aure dan kullum Al'ameen yana cikin jik'asu da naira. Wata 2kacal akasa na bikinsu murna wajan Latifa ba zai fad'u ba ganin burinta ya kusan cika. Ana saura 1month bikinsu yace ta shirya ya kaita ta gaishe da mamyn shi da matan yayun shi. Mamy kwata-kwata Latifa bata kwanta mata ba saboda kana ganinta zaka san idonta a bud'e yake.daurewa tayi ta.karb'eta hannu 2. ya zatayi tunda zabin d'an autan tane. Brothers d'inshi ma basuyi farin ciki da zab'in shi ba sai dai ba wanda ya nuna mishi a fili tunda Mamy ma batayi magana ba. Sa'ad shine kad'ai ya fad'a masa abinda sauran 'yan uwansu da mahaifiyarsu suka kasa fad'a mishi kuma a gaban Latifan ma ya fad'a saboda shi wani irin mutum ne mai wuyan sha'ani duk cikinsu ya fita daban,bai cika magana ba bare fara'a gashi da rashin shakka da tsoro in gasiyace ko ubanwa fad'awa yake. Latifa hankalinta ya mugun tashi jin abinda Sa'ad d'in yace,taso yi masa rashin mutunci amma ganin yanayin shi kada'i yasa ta had'iye duk wani rashin mutuncinta.atake wani tsoronsa ya darsu a zuciyarta. Ta d'an samu relief ganin Al'ameen bai kula da zancen d'an uwan nashi ba saima fushi da yayi suka bar gidan. Ana saura 2weeks bikinsu yazo gidansu Latifa as usual suna hira yake ce mata baya son su sayi koda tsinke ne saboda ya gama tsara gidanshi ya zuba komai a ciki. Cikin jin dad'i take kollon shi jin abinda yace tana yaba k'yau irn na Al'ameen gashi fari da dogon hanci sai dai bashi da manyan ido amma ya k'arawa fuskan shi k'yau gashi da pink lips,dogo ne shi mai faffad'an kirji.infact Al'ameen ya had'u over da ko wace mace zata so ta mallake shi. Yayin da Latifa kuma ta kasance bat da wani k'yau saboda d'an hasken da take da shima na kanti ne,gata gajeruwa ga jiki.amma Al'ameen baya gani dan burin shi ya auri mace saliha dan samun zuri'a d'ayyiba kuma a ganin shi ya samu. Kamin ya tafi 2millions ya damka mata wai na hidiman biki. Kasa rutsawa sukayi ita da mama a wannan daren sai jujjuya kud'in suke cike da al'ajabi,ashe duk yanda suke jin labarin dukiyansu a gari ya wuce nan. An daurauren su da Al'ameen an kashe kud'i anyi hidimomi da events na kece raini sai dai yawancin events d'in amaryace ta shirya su,wasu ango ya halarta wasu kuma bai je ba saboda shi baya son yawan hayaniya. Danginta sai mamakin irin hidimomin suke saboda basu tab'a ganin biki makamancin sa ba,duk wanda yaga lefenta da kyar yake iya tashi wajan.ak'watuna set 2 aka had'a mata komai na ciki disiners ne masu tsada ga golds birjik kaman abin banza a ciki. An gama hidiman biki lafiya ta tare a gidan mijinta wanda ya kasance kaman aljannan duniya dake unguwar dosa a cikin garin k.d Babban burinsu ya cika ita da mahifiyarta na samun miji mai kud'i,tana abinda da taga dama da dukiyar mijinta ba mai taka mata biriki. Matsala 1dake take fuskanta a gidan mijinta kuma yake gusar mata farin ciki a duk lokacin da ta tuna shine rashin haihuwa. Shekararun su 7 da aure amma ko b'atan wata bata tab'a yi ba,gashi Al'ameen da hajiyarsa sun fara k'orafi akan rashin haihuwan nata. Yasha ce su tafi asibiti ko kuma su fita outtside a duba lafiyarsu,amma sai tace mishi ai gaggawa aikin shid'an ne kuma komai na Allah yana da lokacinsa kila lokacin da Allah ya nufa su samu d'ane baiyi ba.nan zatayi ta kawo masa zancen Allah da annabi har sai taga ya hak'ura take k'yale shi. Bakomai yasa take haka sai dankar asirinta ya tonu,sabida ita kanta bata sanadadin cikin da ta zubar ba,ko cikin saurayinta Salees sau hudu tana zubarwa banda sauran samarinta.ita kanta tasan zube-zuben cikin da tayi yayi muhimmiyar bada gudumuwa a wajan hanata samun ciki a gidan mijinta. ✍✍✍✍✍✍✍✍✍✍✍✍ [3/24, 6:46 AM] Ummee Yusuf: . 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA~* 😭😭😭😭😭😭 ( its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman Yusuf) 💫*~FAGEN MARUBUTA WRITERS ASSOCIATION~*💫 *Gidan zaman lafiya,aminci hadin kai da yardar juna insha Allah*🤝 https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ *~ADDU'AR DA ZAKUYI A LOKACIN DA ZAKU SANYA SABBIN TUFAFI~* اللَّهُـمَّ لَـكَ الْحَـمْـدُ أَنْـتَ كَسَـوْتَنِيهِ، أََسْأََلُـكَ مِنْ خَـيْرِهِ وَخَـيْرِ مَا صُنِعَ لَـهُ، وَأَعُوذُ بِكَ مِنْ شَـرِّهِ وَشَـرِّ مَـا صُنِعَ لَـهُ *~Allaahumma lakal-hamdu 'Anta kasawtaneehi, 'as'aluka min khayrihi wa khayri maa suni'a lahu, wa 'a'oothu bika min sharrihi wa sharri ma suni'a lahu.~* *~O Allah, praise is to You. You have clothed me. I ask You for its goodness and the goodness of what it has been made for, and I seek Your protection from the evil of it and the evil of what it has been made for.~* *~part three~* Ringin d'in da wayarta ya fara shi ya dawo da ita daga dogon tunanin da ta lula. Hannu tasa ta jawo wayan tana doka murmushi saboda ko bata kalli screen d'in wayan ba tasan mai kiranta domin ringing tone d'insa daban ne a wayarta. Picking tayi tare da d'aura wayan a kunnenta tace " honey na ya akayine?" " Sunan ya fita daga bakin ki coz u dont have d right to call me with dis name,yau kwana nawa ko tex d'inki ban gani ba bare call".taji ya amsa mata a d'an fusace. Make murya tayi tace " oh! Salees darling am sorry ,wallahi zirga-zirgane suka min yawa". " nasan ni kad'ai nake haukana tunda gashi kin kasa cika min alkawari da kika min". Cikin tsigan lallashi tace " ina sane wallahi kayi hak'uri ka k'ara min kwana 2.in banyi maka ba wa zanyiwa honey?" Ajiyan zuciya ya sauke irin na ya samu relief sannan yace " hmmm kin iya dad'in baki bayan kin san nayi missin d'inki sosai yauahe rabon da inji d'umin jikinki?" Wani irin mik'a tayi akan gadon kana ta amsa da cewa " my Salees u knw i miss u 2,saboda kai na daban ne a rayuwata". Cikin jin dad'i yace " toh ya anjima zamuyi video call ko zan d'an rage zafi?" Tana murmushi tace " in dan wannane kasan baka da matsala all my time is urs.sai anjima". Katse kiran tayi ba tare da ta jira amsan shi ba. Tana shirin ajiye wayan kiran Al'ameen na shigowa,sai da ta d'an ja tsaki tukun ta d'auka tare da cewa " my ameen" Daga d'ayan b'angaren kuma Al'ameen yace " haba Latifa ya kika shige d'aki kika barni,abincin ma sai na rok'a sannan za 'a bani kuma keda wa kike waya tundazu wayarki busy?" A zuciyarta tace kaji dashi d'ansa ido.amma a zahiri kuma tace " my Ameen mama ce ta k'irani amma gani nan zuwa".tana fad'an haka ta mik'e tare da ajiye wayan ta fito main palour. A kan dinning table ta hango shi ya zuba tagumi da hannaye 2 yana kallon yaran larabawa da suke ta wasa a tashan m.b.c3. Damuwa ce k'arara shimfid'e akan fuskanshi saboda shi ya kasance mai matukar son yara. Ta iso daf dashi ta tsaya amma baima san da mutum a kusa dashi ba saboda yayi zurfi a tunani. Hannu tasa ta dafa kafad'an shi,ya juyo a d'an firgice yana kallonta,can ya d'an kak'alo murmushin yake yace " har kin iso?" Bata amsa ba sai zagayawa da tayi taja kujera dake opp da nashi ta zauna ta zuba mishi ido for some seconds sannan tace " nasan kana cikin damuwa mijina kaman yanda nake ciki nima koma ince nama fika shiga damuwa saboda ni mace ce.amma ina so kasani cewa komai yayi farko toh tabbas zaiyi karshe,saboda kullum cikin fad'awa mahallincin mu muke nasan ba zai barmu haka ba,dan ma bana fad'a maka yanda nake tsayuwar dare saboda wannan babban bukatar namu,ga malamai da nake basu abin sadaka suna taimaka mana da addu'a.ina son ka kwantar da hankalinka insha Allah komai zai zo da sauki.haba my Ameen kai da kake namiji ma kana haka ni kuma inyi yaya kenan?"tace tana mishi murmushi. Ajiyar zuciya yayi sannan yakamo hannunta na dama yana murzawa a hankali.fuskarsa d'auke da tsadaden murmushinsa dake k'ara fito da aininhin k'yan sa yace " shiyasa nake godewa Allah daya bani mata saliha mai kwantar min da hankali a duk lokacin da nake cikin damuwa,dan haka bana k'yashin baki komai nawa dan nasan a hanya mai k'yau zaki sarrafa su". Murmushin jin dad'in yanda mijinta ya yarda da ita ta saki sannan tace " toh ya isa haka ranka ya dad'e,irin wannan yabon ai sai kasa kaina ya fashe.bari in baka abinci kaci ko?" Gyada mata kai yayi still yana murmushi. Warmers d'in ta fara bubbud'ewa tace " me zan zuba maka ur highness?" " Duk abinda kika zuba min zanci".yace yana kallonta. Plate ta d'auko ta zuba rice nd stew da yaji naman rago zallah sai peppe soup d'in kayan ciki ta turagaban shi tace " Bismillah". Cin abincin ya fara suna hira sama-sama har ya gama ya kora da ruwa sannan suka dawo palour suka zauna kallo tare da canza channel zuwa al'jazeera news har zuwa karfe goma da rabi na dare snnan suka koma up stairs part d'in Al'ameen . Suna shigowa bedroom d'in bai tasaya wata-wata ba ya fad'a bathroom yayi wanka,yana fitowa Latifa ma ta shiga wankan kamin ta fito har yayi shirin bacci cikin kayan baccinsa dark blue masu taushin gaske. Yana kwance akan gado ta fito,akan idonshi ta shirya cikin wata arniyan night wear, yana kallonta yana had'iyan yawu. Yamutsa fuska ta fara tana wash-wash,bayan ta gama fesa turarukan ta masu kamshi yana kallonta amma takaici ya hana ya tanka mata mata ba. Ganin ba zai kulata ba yasa tace " my Ameen wallahi wani irin ciwon kai nake ji kuma gashi ina son yin nafilfilu cikin dare". "Uhum..." yace yana kallonta. " Zan je insha magani in d'an kwanta kamin lokaci yayi" tace tana wani dafe goshi. " Toh "kawai yace mata tare da juya mata baya. Yana jinta ta bud'e k'ofa tayi ficewarta ba tare da damuwa da halin da ya shiga ba. Yana jin ta rufo mishi k'ofa,ya juyo yana kallon k'ofan cike da takaicin hali irin na Latifa da kullum bata tashi rashin lafiya ko ibadarta sai sai sun zo kwanciya,a ko wani lokaci da abinda za ta kirkiro dan karma ya nemi wani abu a wajanta.in har ta yarda suka kwana waje d'aya toh fa lalle tana da wata tana da wata muhimmiyar bukatarta a wajan shi. Tana zuwa part d'inta ta kulle k'ofa harda murza key. Wayanta ta dauko ta kira Salees,video call suka fara, tana kwance akan gado ba sutura a jikint shima haka sai maganan batsa suke yana cewa shafa min nan murza min can.wai duk su a dole zasu biya bukatar su a haka.kuma shaid'an ya basu sa'a abinda suke nema,su basu kwanta sai wajan karfe ukun dare sannan suka.( WA'IYAZUBILLAH) Fa'za da shamsiyya suma suna can sun luluk'a tasu duniyar domin ba zaman 'yan uwa suka d'uki kansu ba face masoya saboda sun gama yankewa kansu hukuncin basu ba aure koda zasuyi toh sai dai tsakaninsu zasuyi. Ba wanda yasan wannan sirrin nasu a gida sai abokanen tambad'ewarsu. Suna kwance kan gadansu ko wacce tsirara bayan sun tabbatar da sunyiwa k'ofar part d'insu key Sai shafe-shafen da lashe-lashen juna suke duk sun fita haiyacin su. Basu samu bacci ba sai wajan karfe 2 dare suka kwanta rungume da juna ba tare da sunsa koda kayan bacci ba. Al'ameen bawan Allah yana can abin duniya ya ishe shi,da yaga kwanciyar bazata mishi ba ya mik'e ya shiga bathroom ya d'auro alwala ya kama nafila , bai kwanta ba sai da yaji idon shi yana rufewa saboda bacci kuma ga wani natsuwa ta musamman data sauko mishi a zuciya.ba b'ata lokaci ya haye gadonshi ya kwanta nan da nan bacci mai dad'i yayi awon gaba dashi. ✍✍✍✍✍✍✍✍✍✍✍✍ [3/24, 6:46 AM] Ummee Yusuf: . 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA~* 😭😭😭😭😭😭 ( its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman Yusuf) 💫*~FAGEN MARUBUTA WRITERS ASSOCIATION~*💫 *Gidan zaman lafiya,aminci hadin kai da yardar juna insha Allah*🤝 https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ *~ADDU'AR DA ZAKUYI A LOKACIN DA ZAKU SHIGA TOILET~* بِسْمِ اللَّهِ. اللَّهُـمَّ إِنِّي أَعُـوذُ بِـكَ مِـنَ الْخُـبْثِ وَالْخَبَائِثِ *~Bismillaahi. Allaahumma 'innee 'a'oothu bika minal-khubthi walkhabaa'ith.~* *~In the Name of Allah. O Allah, I seek protection in You from the male and female unclean spirits.~* *~part four~* Da washe gari Al'ameen da ya tashi har yayi shirin fita bai ga idon Latifa ba wanda ya saba da hakan,wucewa yayi abinsa zuwa office ko kallan dinning table dake shake da kayan break fast baiyi ba. Sai kusan 11Latifa ta farka sakamakon bata kwanta bacci da wuri ba,kuma sai a lokacin tayi sallahn asuba bayan tayi wankan ta shirya.sannan ta fito yin break fast Serving d'in kanta tayi cikin kwanciyar hankali duk da taga Al'ameen bai tab'a abincin ba amma ko a kwalar riganta. Bata dad'e da fara cin abincin ba Shamsiyya da Fa'iza suka fito rik'e da hannun juna suma sun sha k'yau,kujera suka ja suka zauna. "Ina kwana Aunty " suka ce a tare. "Lafiya my sisters yau baku da lec ne?"ta amsa musu. Shamsiyya ce ke zuba musu abincin a plate d'aya,ita kuma Fa'iza tace " eh yau bamu dashi sai gobe". Latifa ta saba da ganin suna cin abinci a plate 1 wani lokacin kaman suyi feeding junan su,amma ko kad'an bata tab'a kawo komai a ranta ba,gani take tsaban shak'uwa ce irin na 'yan uwantaka ta haddasa musu hakan. Sun fara cin abincin suna hira jefi- jefi ,sallaman da suka ji shi yasa su amsawa tare da kallon mai shigowa. Fad'ad'a fara'a latifa tayi ganin wacce ta shigo,cikin jin dad'i tace " Aina'u kece,k'araso mana". K'arasowa wacce aka kira da Aina'un tayi taja kujera ta zauna sannan ta jawo plate ta fara.serving kanta tace" uhum besty sai yanzu ake break fast sai kace a london muke?" " Ke bana son tsiya ko gaisawa bamuyi ba zaki fara ko?"Latifa tace tana mata hararan wasa Kamin ta bata amsa su Fa'iza suka gaisheta,amsawa tayi tana tambayan su karatu suka amsa mata da Alhamdullilah sannan suka cigaba da cin abincin. Bayan sun gama Latifa ta kama hannun Aina'u suka mike tare tace " taso mu shiga daga ciki,dama nemanki nake ruwa a jallo". Hararan wasa Aina'u ta aika mata sannan tace" kuji ta sai kace da gaske,in nema na kike baki san hanyan gidanmu ba ko baki da no wayata?" Latifa janta tayi sukayi hanyan part d'inta tana mita tace " in kika fara tsara zance ko tambaya lawyer albarka". Suna shiga part d'in Aina'u ta fara shirin zama kan kujera,Latifa ta k'ara janta tace" ke zancen sirri ne yafi karfin nan zo mu k'arasa bedroom". A kan gadonta suka zube,bud'e wani d'an karamin fridge dake gefen gadon Latifa tayi ta fito musu da drinks masu sanyi a ciki.ta rik'e d'aya ta mik'awa Aina'u d'aya. Drink d'in hannunta Latifa ta kurawa ido ba tare da tasha ba kuma batayi magana ba ,Aina'u ta dafa mata kafad'a tace " sis re u alright?" Kai ta d'ago tana kallon Aina'u tace " wallahi besty ina cikin babban matsala nd i dont knw wat to do shiyasa nake neman ki saboda nasan zaki samo min mafita.my Ameen nd his relative are worrid akan rashin haihuwata,abinda nake tsoro shine karsu gaji su tilasta mishi yayi aure.nd am sure yana auren matar shi zata haihu since dagani har ke munsan abinda ta hanani d'aukan ciki,komai zai iya rushewa muddin nayi sake wata ta shigo ta haihu coz yanda nake juya dukiyan shi inyi abinda naga dama ina gani zai zama nata da abinda ta haifa... ...wayyo bansan wani hali zan kasance ba " tace da matukar damuwa a fuskanta. Aina'u shan drink d'inta take hankali kwance ba tare da wani damuwa ba tace" ni na zata ma wani babban al' lamari ne,yanzu akan wannan d'an karamin abun kike wani d'aga hankalinki,toh bari kiji ta inda aka hau ta nan ake sauk'a.abin nufi wajan boka zamu koma sai dai wannan karan harda iyayen shi zai had'a mana" Cikin jin dad'i da kuma yarda da kawarta tace " oh my god! Sam na manta da zancen bokan nan kiga time d'in da Al'ameen yake min yanga muna zuwa wajan shi a cikin satin maganan auren mu ya kankama.gaskiya am luky to have u as a frnd". Gyara d'an karamin veil dake kanta Aina'u tayi tana smilling sannan tace " ni zan fad'i haka dan abinda kike min ko blood sister na baza ta iya min haka kinga dole nima in damu da sha'aninki beside tun muna yara muke tare". " hmm Aina'u kenan shiyasa any time nake cewa da low kika karanta in kika fara tsara zance ba magana".Latifa tace tana dariya tare da mikewa tayi hanyan sip d'inta dake cikin d'akin. Bounches na kud'i ta d'ebo a ciki ta zuba a wani black hand bag d'inta tare da d'auko wani veil shima black. Veil d'in ta yafa akanta sannan ta juyo zuwa ga ban Aina'u tace " ke tashi mu tafi tun yanzu kinsan ba'a bori da sanyin jiki". "U re right my besty muje da wuri" Aina'u tace tana ajiye drink d'in hannunta saman fridge sannan ta mik'e suka sauko down stairs. A main palour suka tarar da Shamsiya zaune akan kujera while Fa'iza tayi pillow da cinyarta suna hiran au,bounch d'in 1k guda 2 Latifa ta ciro a cikin hand bag d'inta tare da mik'o musu tace " ga wannan kusa driver ya kai ku gida ku bawa mama sak'onta,zamu je unguwa da Aina'u.ku gaishe min da ita". Amsa mata sukayi da " toh sai kun dawo" Sun fitowa direct parking space suka nufa,wata hadad'en mota ash colour Latifa ta bud'e ta shiga driver seat Aina'u kuma ta bud'e gefenta ta shiga ta zauna.nan taja motan suka fita a gidan. Tafiya suke cikin jeji Laifa ta manta hanya saboda tun zuwanta na farko kamun auren su da Al'ameen bata k'ara zuwa ba.Aina'u ce mai nuna mata hanyan har suka iso inda zasu ajiye mota domin saman dutse zasu hau,anan bokan yake. Sun sha bak'ar wuya kamin su samu nasaran hawa bama kaman Latifa da take da k'iba na fitan hankali,sai gumi take had'awa ga kuma nishi da take kaman mai haihuwa. Bukkan kara guda 1 tal suka gani a saman dutsen inda bokan yake da zama,sai da suka d'an huta sannan suka nufi bukkan. Tsawa aka daka musu akan su cire takalman su,a tsorace suka cire takalman suna waige-waige ko zasu ga mai maganan. " ku shigo ta baya-ta baya.."suka kara jin tsawan sai dai wannan yafi na d'azun. Kamo hannun Aina'u Latifa tayi ta rik'e gam sabida tsoro sannan suka fara tafiya ta bayan kaman yanda aka umarce su. Suna dab da shiga cikin bukkan suka ji muryan d'an k'aramin yaro yana cewa " wayyo zasu taka ni umma" . Nan suka suka tsaya kaman an dasa suJikin sune ya fara b'ari barin ma da boka yace kan d'an autan aljani tsibiritu suka kusan takawa.Latifa kam ji take kaman ta saki fitsari a wando . " ku shigo"aka ace musu. Da kyar suka cigaba da tafiya ta bayan har suka shiga cikin bukkan da duhu ya mamaye kaman dare,wani haske ne ya fito cikin wani jan k'warya ya haska cikin bukkan kuma sai a lokacin boka ya bayyana a gaban su cikin wasu kaya ja-jaye ga rabin fuskarsa ma ta sha fenti ja.cikin babban murya yace su zauna. Zama sukayi a inda ya nuna masu har yanzu Latifa tana rik'e da hannun Aina'u gam. Aina'u ita tayi karfin halin bud'e baki da niyan yiwa boka bayani amma ya dakatar da ita ta hanyan d'aga mata hannu. Shiru sukayi suna kallonsa yana ta wasu surkullen sa can ya d'ago kai yana kallon Latifa yace" tsibiritu da maniru su fad'a abinda yake tafe dake,kina so a rufe bakin mijinki dana dangin shi akan rashin haihuwarki kuma a kawar da idon shi akan ko wace mace ko ba haka bane?" Cikin jin dad'in hango nasara tace "hakane boka" Dariya ya kwashe da shi sannan kuma ya turbune fuska a lakaci1 yace "aikin ki mai sauk'i ne in kika kawo kitsen bakin jaki da makahon bunsuru da sauro mai ido 1shiken nan sai yanda kikayi dasu " Zaro ido waje Latifa tayi cikin tashin hankali tana kallon Aina'u bakinta yana shaking jin abubuwan da ya kirga a ina zata same su? Aina'u ce ta d'an gyra zama tace " ayi mana afuwa boka irinn wannan abu ai sai ku,zamu bada kud'i a taimaka a nemo mana". Wasu surutai ya fara da wani yare yana kallon sama can ya dawo da kanshi kasa yace " tsibiritu ya yarda zai taimake ku sai ku ajiye kud'in acan ya nuna musu wata b'akar k'warya,belt d'in yan dubu guda 2 ta fito dasu hannu na karkarwa ta jefa a ciki nan da nan kud'insukak bace bat. "Aikin ki ya kammala sai dai akwai wani d'an uwan mijinki kiyi hankali dashi zai iya b'ata miki aiki a ko wani lokaci".boka yace ba tare da ya kalle su ba. Zatayi magan Aina'u taja hannunta suka fita daga cikin bukkan. ✍✍✍✍✍✍✍✍✍✍✍✍ [3/24, 6:47 AM] Ummee Yusuf: . 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA~* 😭😭😭😭😭😭 ( its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman Yusuf) 💫*~FAGEN MARUBUTA WRITERS ASSOCIATION~*💫 *Gidan zaman lafiya,aminci hadin kai da yardar juna insha Allah*🤝 *~part five~* Aina'u bata saki hannun Latifa ba sai ďa suka zo har inda suka ajiye mota,bude motan tayi ta tura ta a ciki san an itama ta zagayo ta bude tashiga gidan gaba. Latifa d'aura kanta tayi a kan stairyn motan ta sauk'e ajiyan zuciya. Juyo da kanta tayi saitin Aina'u tace " kin san Allah badan kina tare da ni a wajan nan ba,da abinda zai hani sake gudawa a jikina". Aina'u ta tuntsire da dariya saida tayi mai isar ta sannan tace " matsoraciya kawai harda gudawa hahaha" tacigaba da dariyanta. Had'e rai katifa tayi tana kallon yanda ta dage tana mata dariya tace " wats funny here, da zaki wani dage kina dariya haka?yauwa meyasa kika hana ni magana bayan kina ji yace akwai d'an uwan my Ameen da zai iya rusa min duk aikina.da kin bari ko sunan shi na tambaya". Aina'u tace " kada ki soma wanman gangancin saboda boka nan ba'a yi masa musu kuma ba'a wucewa gaban shi.kinga da yana so ki sani da kan shi zai miki bayani". Key tayiwa motan suka fara tafiya tace " oh god ya zanyi ne?" "Abinda zakiyi kawai kiyi taka tsan-tsan da'yan uwansa"Aina'u ta bata amsa. Shawara yanda zatayi da 'yan uwan Al'ameen Aina'u take bata har suka shigo garin k.d,direct gidan su Aina'u tayi dake kawo a bakin k'ofan wani yamutsesen gida tayi parking. Hand bag d'inta ta bud'e ta ciro bounch 200 guda1 ta mik'awa Aina'u tace " ga wannan ki rik'e ba yawa besty nagode sosai". Karb'a Aina'u tayi tana mata godiya tace "baza ki shigo ku gaisa da umma ba ?" Gurgiza kai Latifa tayi a zuciyarta tana ina zataiya shiga gidan nan amma a zahiri kuma tace " no besty kinga yamma tayi sosai yanzu kila ma my Ameeen ya dawo,soo gwara na karasa ki gaishe min da ita.sai next time in nazo zan shigo mu gaisa". Murmushi Aina'u tayi tace" shikenan sai munyi waya "daga nan ta bud'e motan ta fita Latifa taja tayi gaba abinta. Burinta na karshe ya cika dan yanzu duk cikin dangin mijinta ba mai yi nata maganan rashin haifuwa balle kuma shi uban gayyan wato Al' ameen ya zama rakumi da alaka sai yanda tayi dashi dan duk wani documents da files dinshi masu amfani da mahimmaci a hannunta suke tana wandaka da dukiyarsa yanda taga dama. Yanzu abin nata yayi gaba saboda boka ya bata sa'a har cikin gidan wasu samarin nata suke biyota a sunan yan uwanta dan haka gidan kullum a cike yake suna shagalinsu. Fa'iza da shamsiya suma abin nasu yayi nisa dan suma kullum cikin kawo kawaye suke, su shige bangaren su,tare da saka key suyi abinda suka ga dama, cikin haka suka samu wata da ake kira Binta wacce jarabarsu tazo iri daya dana su fa'iza dan haka yawanci tana gidan su kwana tare su tafi makaranta tare. Kaman kullum yauma Al'ameen ya dawo daga office ya tarar da latifa da salees da wani abokinshi suna hiran su hankali kwance a waiting palour. Sallama yayi ya shigo, tashi Latifa tayi da saurita, ta taro shi tare da karban jakan hannunshi tana mishi sannu da dawowa ya amsa cikin sakin fuska,su salees ma suka gaishe shi ya amsa sannan suka wuce bangaren shi tare da ita. Bayan ta taya shi cire kayan jikn shi ta hada masa ruwan wanka sannan ta fito tace"ruwanka na jiranka my Ameen " Murmushi yayi ya mike zuwa bathroom. Ganin haka tace"bari inje in had'a maka abincinka kafin ka fito ko?" du "duk yanda kikayi gimbiya dai daine". Wuce shi tayi tana dariya,yayin da shi kuma ya k'arasa shiga bathroom d'in. Direct wajansu salees ta dawo tazo ta rungume shi sannan tace" yanzu ku tafi sai munyi waya zaka ji komai zan san dai yanda zanyi yayi signing dinsu karkaji komai". Manna mata kiss yayi a kumatu yace " nasan zaki iya babyna, sai naji ki". Fitowa sukayi ya d'auki motan shi da latifa ta saya mishi suka fita daga gidan. Latifa dawowa tayi palour na biyu tare da duba kan dining taga an shirya komai,neman guri tayi ta zauna tana jiran fitowan shi. Sanye da kananan kaya wanda suka yi matukar karb'an shi ya fito ya zauna a d'aya daga kujerun dining. Plate ta jawo ta fara serving d'in shi, cus cus ce da miyar ganye tasha tsokar kaji har ta gaji. Fara ci yayi hankali kaman wanda baya son cin abincin. Gyara zama Latifa tayi tace " my Ameen na nayi maka maganan kwangila nan amma har yanzu bakayi magana ba,kasan k'anne na maza 'ya'yan yayan baban mu basu da aikinyi shiyasa nake son taimaka musu da abinyi". yana kallon ta yana tauna abincin dake bakin shi cikin natsuwa sannan yace " aina gaya miki duk wani abu inza kiyi na taimako ba sai kin tambayeni ba dan nasanki ta hanya mai kyau zaki sarrafa su". Tayi yar dariya tace "toh wannan d'in yana bukatan sa hannunka shiyasa". "Ok d'auko mana insa hannun". Mik'ewa tayi ta shiga part d'inta,sai gata ta fito da files a hannu. Batare da ya karantaba ya rantama hannu ya mik'a mata Karb'a tayi cike da jin dad'i saboda kwangila ce har ta million ashirin. Tashi tayi da saurita tayi d'akinta ta kira salees a lokacin yana wani hotel da wata karuwan shi suna holewan su. Ya d'auka yace "ina jinki a akayine"? Cike da farin ciki tace" my dear ya saka hannu ga files d'in a hannuna gobe aina zan sameka?" Yace inda muka saba had'uwa mana ko kin saki d'akin ne?" Tace " na isa in saki d'akin? suma 'yan hotel d'in ganin na mak'alewa d'akin har kara min kud'i sukayi" Yace "amma ai nasan kud'i ba matsalarki bace ko"? Tace"kaima kasan da hakan just sai mun had'u goben" "To bye my heartbeat". Fitowa tayi bayan sun gama wayan.Al' ameen yana zauna yana kallon bbc news Zama tayi kusa dashi suna hira sai fara'a take kaman ba ita ba. Yau dai yayi sa'a albarkacin signing d'in da yayi yau,da kanta ta kawo kanta. Gaba d'aya ya rikice ce jikin shi har b'ari yake saboda rabansa da ita ya kai sati 2,dan haka kusan raba dare yayi yana abu d'aya sannan ya samu natsuwa.ranan dai ya samu bacci mai dad'i. [3/24, 6:47 AM] Ummee Yusuf: . 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA~* 😭😭😭😭😭😭 ( its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman Yusuf) 💫*~FAGEN MARUBUTA WRITERS ASSOCIATION~*💫 *Gidan zaman lafiya,aminci hadin kai da yardar juna insha Allah*🤝 *~part SIX~* Da washe gari Al'ameen da wuri ya shirya ya fita office. Fitowa tayi cikin shirin fita da wasu english wears matsassu riga da skirt har shatin pant d'inta ana gani,ba bata lokaci ta ja mota sai prince hotel. Reception ta nufa bayan tayi parking,ma'akatan hotel d'in suna ganinta fara well come Hajiya. Duk wani ma'aikacin hotel d'in sun santa saboda regular customer ce. Bata damu da kama room daban daban ba tunda ta kama room number 35, shikenan ta makale mishi. Duk ranan da taso holewa sai dai tazo ta karbi mukulli ta wuce kuma ga kyautan kud'i da take musu shiyasa suke bala'in girmamata. Dan haka yauma suna ganinta suka hau murna,bayan sun gaisa aka miko mata key ta fito da bounch d'in 'yan d'ari biyar ta basu su raba, suka karb'a tare da godiya ta wuce d'akin bayan ta rufe ta rage kayan jikinta daga ita sai karamar vest skirt, ta kwanta akan gado tana kiran wayan Salees. Yana d'aka wayar yace mata gashi nan ya shigo compound d'in hotel. Tana ajiye wayan kaman da 10 mins sai gashi nan da kwalban wine a hannunshi ya shigo ya maida k'ofar ya rufe. Bata motsa ba daga kwanciyar da tayi ba yana kallonta da irin kallon daya saba yi mata na zallan so. Ya zauna dab da ita yace"ya dai babyna ya na ganki haka?" Kamo hannun shi tayi da karfi ta jawo shi ya fad'a kanta suka rungume juna suna ta juyi akan gadon tace"kasan nayi missing d'inka sosai". Tashi yayi ya zauna tare da d'ago ta itama ta zauna sannan ya bud'e kwalban wine ya fara sha. Ya sha kusan rabi sannan ya mik'o mata itama ta karb'a ta sha sosai dan ta kwana biyu bata sha ba. Ahaka har suka shanye gaba d'aya suka koma suka kwanta suka cigaba da sheke ayansu san ransu. Bayan sun natsu,ta bud'e hand bag ta fito da files d'in ta mika mishi tace"ina so mufara business dashi dan kud'in suyi albarka saboda haka na mika maka wuka da nama sai yanda kayi". Yaca"karki damu zanyi duk iya kokarina dan muyi nasara kaman yanda kema kikayi naki kokarin". Yace yana jujjuya file di'n a hannun sa. Sai kusa la'asar suka rabu ta wuce gida. shima ya wuce inda ya fito. A kwana a tashi ba wuya a gurin Allah,dan yanzu Latifa sun shiga 12years of marrage amma ba wanda ya k'ara takura mata akan haihuwa.tana abinda taga dama. Hajiya Halima wato mahaifiyar su Al'ameen ta shigo palour d'auke da karamin tray ta d'aura bottle water da glass cups 2 akai. Ajiye trayn tayi akan wani d'an karamin table na glass a gaban mijinta wato Alhaji mudassir. Bud'e ruwan tayi tare da zubawa a glass cup d'in ta mik'a mishi sannan ta nemi waje ta zauna kusa da shi. Ajiye cup d'in yayi bayan ya shanye ruwan,ya juyo yana kallonta yace " dazu munyi waya da Hajiyar katsina tace gobe zasu shigo ita da 'yar wajan Laure Sakeena". Hajiya cikin farin ciki tace Allah sarki ashe gobe muna da manyan baki,bari mu fara shirin tabarsu tun yanzu". Dariya Alhaji yayi cikin jin dad'in yanda matar shi take karrama mishi dangi a koda yaushe. Da safe tunda wuri hajiya tasa aka gyra d'akin da surkuwar ta zata sauka ga kuma girke-girke da sukayi na musamman aka jera su kan din ing ana jiran zuwansu. 3:00pm su Hajiyan katsina suka isohajiya ta karb'e su kamn yanda ta saba yi, Bayan sun ci sun sha kuma sun huta aka zauna hira a palour. " wai ina angwayen nawa ne banga ko d'aya ba ko kishiyoyin nawa ne suka rik'e su?"cewar hajiyar katsina. Hajiyar su Al'ameen tayi dariya tace " aiko sun rike su dole su kyale tunda uwar gida ta zo". Alhaji yana murmushi yace Sakeena ya wajan ummanki da sauran kannenki?" Yarinyan da aka kira da Sakeena ta sauke kai k'asa tace duk suna gaishe ku". " muna amsawa " hajiya tace tana shafa kanta. Alhaji ya ciro waya ya fara kiran boyz dinsa ya sanar dasu zuwan Hajiyar katsina. Bayan ya gama kiransu ne Hajiyar katsina tace ya labarin matar Aminu har yanzu shiru ko?" Hajjiya ta amsa mata " eh har yanzu lokaci baiyi ba". Tab'e baki hajiyar katsina tayi tace " hmm gobe yazo ya same ni musan abinyi tunda kun kasa nema masa mafita". Next day saturday ba aiki saboda haka Al'ameen yana gida. Suna zaune tare da Latifa yake gaya mata zai je can gidansu gaishe da Hajiyar katsina da tazo jiya. Yamutsa fuska tayi ba tare da ta kalle shi ba tace " noo my Ameen yau fa weekend ne ya kamata ka zauna ka huta a gida dan bana son ka wahala". " alright " yace kawai suka rufe zancen but kasan zuciyar shi ba haka yaso ba,yana son zuwa su gaisa dan ya dad'e bai sata a ido ba.amma ya rasa dalilin da yasa baya iya mata musu. Ita kuma Latifa tun lolacin da boka yace mata a cikin 'yan uwansa akwai wanda zai lalata mata sihiri take taka tsan-tsan da al'amuransa ta hana shi shiga cikin 'yan uwansa. " let me take a shower " tace tare d wucewa part d'inta. Tana shiga bedroom wayarta ya fara ringin kuma ringin tone d'in salees ne. Tana d'agawa tace " my only love". " i need u right now coz i missed u alot hak'uri na ya kare kizo mu had'u" salees yace. " but salees i have an important thing to do at home " " Bana son jin komai wato am not importan to u " yace cikin fushi. Jin muryan shi da alamun fushi yasa tace " pls come down Salees ba haka nake nufi bayi hak'uri gani nan zuwa". " better " yace yayi hanging call d'in. Bata son fita yau tafi son ta zauna a gida tayi gadin Al'ameen amma bata son bacin ran salees dan haka tashi tayi ta fad'a bathroom dan yin wanka. Bayan ta fito daga wanka ta sheka kwalliya da wani leshi maroon d'inkin dogowar riga sai kamshi turare take, ta iske shi a inda ta barshi yana zaune, ta zauna kusa dashi ya juyo yana kallonta dan taci ado harna fitan hankali tace"my meen kun dade baku had'u dasu hajjiyar katsina bako?" Ta sosa mishi inda yake mishi kaikayi yace"ai shekarune ma zance" Tace"hmm shikenan kaje ku gaisa,nima zaje gidan mama in dawo" Ya kama washe baki yace"toh shikenan ki gaida ta nima ba d'ad'ewa zanyi ba ke sai yaushe?" Tace"my meen kenan zaria fa zanje kaga kuma na d'ade banje ba ina ga sai kusan magrib zan dawo". " sai kin dawo," yace tare da mikewa yayi part d'in shi .ya shirya cikin manyan kaya na shadda dark green ya sha bugu sai maik'o yake. Shi kad'ai ya d'auki mota ya fita,bai nemi drivern shi ba. Direct gidansu dake unguwar rimi ya nufa,yana zuwa mai gadi ya bude mishi gate ya shiga. A parking space yaga motocin brodthers d'in shi dan haka shima cikin farin ciki ya nufi palour. Tun daga bakin k'ofa ya fara jin muryoyinsu anata hira da raha,sallama yayi suka juyo gaba 1 su suka amsa ya nemi guri kusa da kkafar hajiyar shi ya zauna. [3/24, 6:47 AM] Ummee Yusuf: . 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA~* 😭😭😭😭😭😭 ( its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman Yusuf) 💫*~FAGEN MARUBUTA WRITERS ASSOCIATION~*💫 *Gidsn zaman lafiya,aminci hadin kai da yardar juna insha Allah*🤝 https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ *~ADDU'AR DA ZAKUYI A LOKACIN DA ZAKU BAR GIDANKU~* بِسْمِ اللَّهِ تَوَكَّلْـتُ عَلَى اللَّهِ، وَلاَ حَوْلَ وَلاَ قُـوَّةَ إِلاَّ بِاللَّهِ ~Bismillaahi, tawakkaltu 'alallaahi, wa laa hawla wa laa quwwata ‘ illaa billaah.~ *~In the Name of Allah, I have placed my trust in Allah, there is no might and no power except by Allah.~* *Part seven* Gaishe da Hajiyar katsina ya farayi sannan ya gaishe da iyayensa da brothers d'in shi tare da matansu. Bayan gaisawan ne ya d'auki babyn yayan shi Sa'ad wanda bai wuce 6months ba yana masa wasa. Hajiyar katsina ce take tambayarsa ina Latifa me ya hana ta zuwa su gaisa ko taji tsoron uwar gida ne? Dariya yayi yace " a'a ba ko mzaria 1ta tafi dubo mamrta bata jin dad'i". Allah ya suwak'a kowa ya mata sannan suka cigaba da hiran su cikin raha da zolayan juna. Ganin yanda Al'ameen hankalkn shi ya tafi kan affan yana ta mishi wasa yasa Hajiyar katsina magana tace " kai k Ameenu matarka har yanzu ba labari ko?" Bai tsaya da wasan ba yace mata " eh Hajiya lokaci baiyi ba kinsan komai lokaci ne". Hajiyar su itama tace " haka ne komai lokaci ne". Shiru hajiyar katsina tayi na d'an lokaci kana tace " toh me zai hana ka kara aure ko rabo 'yar uwarta ce ya danne nata kadan hakan yana faruwa". Al'meen gumi ne ya fara karyo mishi ta kowane hujin gashin jikinsa.ga wani irin damuwa da tashin hankali da suka bayyana karara akan fuskan shi lokaci guda. Hajiyar katsina ce ta lura da halin da ya ahiga tace "mai gidan lafiya kuwa daga maganan aure sai ka birkice haka?" Share gumin da ya tsatsofo mishi a goshi yayi sannan yace " gaskiya a bar maganan dan ni ba wani aure da zan iya k'arawa.haihuwa ài na Allah ne,a yanda muka dage da addu'a nasan Allah zai share mana hawaye lokaci ne bAiyiba". Rik'e baki Hajiyar katsina tayi tana kallon shi a matukar mamakince can dai ta daure tace " dan nace ka kara aure shine kake min suratan banza,ni zaka gayawa Allah?toh tun kafin a haifi ubanka nadan Allah.in yarinyar da zaka aura ne baka samu ba sai ka duba nan cikin 'yan uwa ka aura" Cikin firgici yake kallonta yama rasa me zaice mata,yana zaman-zamansa zata zo taja mishi bala'i dan in Latifa taji zancen nan ya shiga 9 ba 3 ba. Alhaji ya kalla yace ",dan Allah ku fahimtar da ita ta rufa min asiri ni ban tashi aure ba.pls leave me alone". Hajiyar katsina ta kasa magana saima hangame baki da tayi tana kallon 'yan palourn duka saboda bata ga wanda ya d'auki maganan serious ba saima ce mata da sukayi ta bar maganan tunda bai tashi auren ba. Sa'ad ne kad'ai yayi shiru bai tanka ba sai da suka gama magana sannan ya bud'i baki ya cewa Hajiyar katsina " karki damu zamu tafi gidana dashi zansa shi ya fahimta". " Oh ni 'yasu yau naga abinda yafi karfina".inji Hajiyar katsina tana girgiza kai cikin jimami dan tabbas taga alamu 'yan gidan ba cikin haiyacinsu suke ba. Hankalinta bai kwanta ba saida suka keb'e da Sa'ad ya fad'a mata abinda yake ranshi.nan itama tace ba Al'ameen kad'ai abin ya shafa ba harda sauran 'yan uwansa da iyayensu. Fita Sa'ad yayi bayan sallahn azahar,sai kusan la'asar ya dawo da wani jerry can cike da ruwan addu'a da yasha ganyen magarya. Tambayansa Alhajinsu yayi z ruwan menene wannan?" " Ruwan addu'ace ta kariya na kawo dukkan mu muyi amfani dashi".ya amsa mishi a ladabce. Ba b'ata lokaci mai aiki ta kawo cups,duk suka sha sannan yace musu " mallam yace kullum zamu rinka sha har zuwa 7days dan haka daga yau duk wanda ya tashi tafiya office ya biyo yasha kafin ya wuce". Yayi hakan ne sabida shi tun kamin aurensu shi bai yarda da Latifa ba,bare ma da yaga yanda kaninshi ya birkice lokacin da yaji maganan aure,bayan b4 yayi aure bashi da wani buri da ya wuce ace yayi aure ya tara ya yara amma yanzu ko zancen baya so. Ga Ahajin su yasan halin shi yana d'an zafi wani lokacin gashi yau Al'ameen yana fad'awa Hajiyarsa magana amma ko kallon banza bai mishi ba ga Hajiyarsu itama a baya bata da buri da ya wuce taga jinin autanta,sai gashi itama ta canza. Addu'ansa 1ce Allah yada duk wani surkullen da tayi ya warware albarcin wannan addu'an. Da daddare da zasu rabu sauda yajawa Al'ameen kunne kan yaja bakin shi kar ya bawa Latifa labarin ruwan addu'an da zasu rinka zuwa sha kullum. Yau kwana uku kenan kullum Al'ameen da safe sai yaje yasha ruwan add'ua sannan ya wuce office. Da wuri yau ya tashi a office ya dawo gida asual ya tarar da gidan cike da samari da 'yan mata da samari ana ta hira,a karo na farko da yaji ba dad'i a zuciyarshi amma ya danne bai nuna ba ya wuce ciki bayan yayi wanka ya zauna ya fara aiki a system d'in shi. Haka kawai ya rinka jin shi wani iri yau. Latifa ce ta shigo ta zauna kusa dashi tace " my ameen lafiya yau baka sauko kasa ba?" " Lafiya lau ina wasu aiyuka ne shiyasa".yace mata. Kallonsa tayi tace " abincin fa ?" Yace " naci a gidan ya Sa'ad kamin inzo". Shiru tayi tana mamakin yaushe har ya far zuwa gidan wasu ba tare daya gaya mata ba? Kawar da zancen tayi a ranta tace " toh ni zan sauka kasa sai ka fito". " Toh " kawai yace ba tare da ya dube ta ba ya cigaba da aikinsa. Saukowa tayi ta kyale shi. Yau friday kuma yaune kwana 5 da fara shan ruwan addu'an,yana zuwa ya tarar da duk brodas dinsa suma sun zo. Bayan sun gaisa kuma sunyi abinda ya kawo su Ai'ameen yace " nifa Hajiya na kasa gane me Latifa take nufi dani,ta mayar min da kaman wani bariki kullum cikin tara min mutane take baya ga haka rabin danginta a.gidan suka tare". "Hajiya tayi caraf tace " wannan shashanci ne bangane rabin dangin taba". Alhaji yace " Wanna ai zancen banza ne kuma laifinka ne kai ka sake mata" Murmushi mai kayatarwa Sa'ad yayi tare da cewa "ALHAMDULLILAH Ala kulli halin". Alhaji ne ya kalle shi yace " d'an uwanka yana cikin matsala abinda zaka ce kenan?" " ba haka nake nufi ba"yace " Toh me kake nufi?" Hajiya ta katse shi. Nan ya kwashe komai ya fad'a musu sannan yace " Alhamdullih sauki ya samu tunda har ka fara ganin laifinta saidai abinda nake so da kai ka bar maganan a zuciyarka ka cigaba da pretending har yanzu asirin bai bar ka ba dan bamu san iya lokacin da ta d'eba tana aikatawa ba in ba haka kayi ba ba zamu samu bakin zaren ba. Cikeda takaici Al'ameen ya fara magana yace " wallahi bazanyi shiru ba yanzu zanje in nuna mata bokanta yayi kad'an dan bazata kwana min a gida ba. Alhaji ne ya shiga tausan shi akan Sa'ad yana da gaskiya abi komai a sannu. Kowa yayi na'am da shawaran Sa'ad tare da add'uan Allah ya tsare gaba. Haka ya wuce office cikin k'unan rai tare da tsanan Latifa a ran shi. [3/24, 6:47 AM] Ummee Yusuf: . 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA~* 😭😭😭😭😭😭 ( its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman Yusuf) 💫*~FAGEN MARUBUTA WRITERS ASSOCIATION~*💫 *Gidsn zaman lafiya,aminci hadin kai da yardar juna insha Allah*🤝 https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ Alhmdllh mama ta samu lafiya ina mika godiyata gare ku my fans kan addu'oin ku Allah ya bar kauna😘😘 *~part eight~* Al'ameen yan zuwa office ya samu mutane da yawa masu son ganin shi ga aiki sun taru sunyi yawa,dan haka sake ranshi yayi ya cigaba da harkokin shi hankali kwance. Bayan sati Sa'ad yaje har company Al'ameen inda tace yazo ya raka shi unguwa,barin aikin shi Al'smeen yayi ya bishi suka fita su 2 a motan Sa'ad. A sabon gari gidan mallam nuhu yake,a kofar gidan Sa'ad ya tsaya suka shiga ciki wajan mallam. Yana kishingid'e a palourn shi sukayi sallama,daga ciki mallam ya amsa ya basu izin shigowa. Zubewa sukayi gaba 1suka kwashi gaisuwa a wajan mallam sannan Sa'ad ya nuna Al'ameen yace ga kanin shi da ya kab'awa magani kwanaki kuma Alhmdllh sauki ya samu shine suka zo godiya. Gyran murya mallam yayi sannan ya tashi zaune shima yayiwa Allah godiya tare da basu wasu addu'oi da zasu rik'e saboda kariya.kuma yace kar suyi wasa da azkar na safe rana dare shima in mutum ya rik'e babban kariyace. Godiya suka karayi mishi sannan suka bashi abin sadaka suka fito. Yau Al'ameen ya dawo daga aiki da wuri,ya tarar da Latifa suna zaune a waiting palour tare da Salees da abokanen shi 2 suna hira. Wani rirn bakin cikine ya tokare mishi zuciya. Suna mishi sannu da zuwa amma ko kallonsu baiyi ba ya wuce part d'inshi a zuciye. Zama yayi a bakin bed ya dafa kashi da hannaye 2,magana ya fara cikin bacin rai shi kaf'ai. " i cant tolarete dis nonsence in my house,i have to do somting.wa yasan lokacin da ta d'auka ta tara min kartin banza a gida,sai kace ita kad'ai ce mai dangi......" Ringing din wayarsa ce ta katse shi,ciro phone d'in yayi daga aljihu.sunan da ya gani yana yawo akan screen ya sa shi sauke ajiyan zuciya sannan yayi recieving. " Salamu alaikum Hajiyata,barka da yamma". " Lafiya lau Al'ameen ya gida,ya naji muryanka wani iri hop dai kana lafiya?" Hajiya ta tambaye shi cikin kulawa. Tana ji cikin wayan yana sauke ajiyar zuciya wato yana kokarin calming kansa yace " Hajiya na gaji am fed about Latifa,gaskiya i cant take it any more.ace wai any time na shigo gida sai raina ya baci". " nasan akwai ciwo amma fa dole ne ka danne zuciyarka for some time muga abinda Allah zaiyi karka manta Alhajin kuma ya bada goyon baya kan hakan so pls ban yarda ka kula taba.zan samu Alhajin inji me ya kamata kayi next,kaji ko?" cewar Hajiya. " naji kuma insha Allah zan kiyaye " yace cikin sanyin murya. " yauwa d'an albarka Allah ya tsare ka daga dukkan abin ki". " Ameen Hajiya nagode sai anjima" yace tare da ajiye wayan. Latifa tana can wajan su Salees,Al'ameen yana shigewa ciki abokansa suka mike jiki na rawa akan suzo su wuce dan basu san hukuncin da d'auka ba akan su. Salees ya kalle su ya murmushi yace " kwantar dahankalin ku guys ba abinda zai faru". Latifa kuwa dariya take sosai harda rik'e ciki tace " wai me ya tsorata ku haka?kun d'auka dan ya ganku ne yayi haka,ina ganin a office ne wani ya tab'a shi saboda haka kusha zaman ku". D'ayan hanyan waje yayi yace " no lets get going tunda ya dawo,just kema ki bishi kar yayi suspecting wani abu". Salees mik'ewa yayi yace " yeah hakane baby kije kawai mu zamu wuce sai munyi waya,but pls kisan yanda zakiyi yayi signig documents d'in". " dont worry kai ma kasan wannan yafi komai sauki " tace tana tashi danyi masa good bye hug,a lokacin abokanen saless har sun tsufa a mota. Da fara'anta ta shigo part d'in Al'ameen tana " waue ya tab'a min my Ameen ne ya shigo ba fara'a haka?" D'an murmushi ya kakalo yace " bana jin dad'i ne kuma ga ciwon kai da nake ji". " eyyah sorry let me get u drugs cikin first aid box". Paracetamol ta ballo mishi guda 2 ta kawo had'e da bottle water. Ba musu ya karba ya sha dan da gaske yake jin ciwon kan saboda bacin rai da suka saka shi. Driving yake a hankali shi kad'ai a mota sakamakon ya aik8 drivern shi bai dawo da wuri ba,ya kama hanyan gida. Yamma tayi lis a lokacin pass 5 ne,ya biyo ta tudun wada gun wani frnd d'insa da sukayi karatu tare a anguwan. Kamin ya isa gidan abokin nashi ya hango wasu samari sun kai 6 sun sa wata yarinya a tsakiya,sai faman kuka ,rok'o da magiya take musu akan su bata hanya ta tafi amma sai wani dariyan mugunta suke mata. Parking motan shi yayi ya fito ya nufi inda suke,a lokacin har har daya daga cikinsu ya kama hijabinta yana ja. Uniform ne a jikinta na islamiya kuma hijabin har kasa. Al'ameen yana zuwa yace musu " ya dai,me ta muku ne haka?ku bata hanya ta wuce mana". 1 ne ya juyo ya bashi amsa ga kayan maye a hannunsa yace " kai dallah ina ruwanka damu,ko kanwarkace?" " eh kanwata ce ku kyaleta ta wuce" Wani d'an dogon cikin su yace" nd so wat in karwar kace,yau sai mun tafi da ita dan rainin wayon nata yayi yawa". Al'ameen ganin ba zasu saurare shi ba gashi kafa ya d'auke saboda irin tsukukun lungu ne. Hannu yasa a aljihu ya kwaso duk kud'in dake ciki wanda shima baisan adadin suba ya mik'awa dogon yace " ga wannan ku sha ruwa da shi pls ku kyaleta ta tafi". Kusan wawa suka dakawa hannun shi,suna ihun murna tare da jinjina mishi harda kirari.nan suka dubi yariyan da yanzu har ta durkushe a wajan tana kuka. Wani mai katon kan cikin su yace mata " ke wallahi kinci arzikin oga,badan shiba da yau sai kin yabawa aya zakinta.kuzo muje yau akwai hawa network dan yau ni service zan hauma ba network ba". Haka suka tafi suna ta iface-ifacen da suratansu har suka sha wani coner. Al'ameeen zubawa yarinyan ido yayi for some seconds yajhna kallonta duk da ko tafin hannunta baya waje ko ina na jikinta a lullub'e suke sai shasshekar kukanta yake tashi. Lumshe ido yayi ya bud'e yace " meye ya had'aki da wa'yan kuma?" Cikin kukan ta bashi amsa tace " wallahi ban musu komai ba,sun ce in tsaya in saurare su dan.....da....."kuka yaci karfinta ra kasa karasawa. " ya isa haka tashi in karasa dake gida saboda kar in tafi su kara dawo kinsan wa'yan nan ba hankali ne dasu ba".yace still idon shi kanta. A sanyaye ta mik'e tsaye kanta a kas'a tana share hawaye,ganin haka shima ya juya ya nufi mota. Bin bayansa tayi har zuwa inda yayi parking motan shi,bud'e mata front seat yayi ta shiga ta zauna.shima ya zagaya ya shiga yaja suka bar wajan. Driving yake yana satan kallonta amma taki d'ago da kanta bare ya samu daman kallon fuskanta. [3/24, 6:47 AM] Ummee Yusuf: . 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA~* 😭😭😭😭😭😭 ( its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman Yusuf) ✍✍✍✍✍✍✍ GOLDEN PEN WRITER'S ASSOCIATION ✍✍✍✍✍✍✍ *~part nine~* Dai-dai wani rugujajjen tsohon gida tace ya tsaya,tsayawa yayi ya juyo gaba 1 ya zuba mata ido. " Nagode Allah ya saka da alkhairi" tace a hankali kaman bata so kuma ba tare da ta d'ago ta kalle shi ba. Kamin ya samu abin fad'a har ta bud'e murfin motan ta fita. A sukuwane ya fito shima saboda yana da burin koda sunanta ne ya sani. Wani wawan birik yaja ya tsaya ganin wani d'an dattijo ya fito daga gida da buta da tabarma a hannun shi. D'an rusunawa tayi ta gaishe da tsohon sannan ta shige ciki, ganin yanayinta yasa tsohon kallon A'ameen cikin tuhuma yace " bawan Allah meye had'inka da 'yata har zaka d'auko ta a mota?" Har kasa Al'ameen ya durkusa ya gaishe shi,a taikaice ya amsa yana jiran yaji amsan tambayan shi. " Baba wallahi nima a hanya na samu wasu yara suna kokarin hi mata rashin mutunci,shine na tsaya na raba su kuma tsoron karsu k'ara biyota yasa na kawota gida". Yace cikin ladabi. " toh-toh madallah d'an samari Allah yayi albarka nagode kaji?"wannan tsohon yace masa cikin jin dad'i. Sallama yayi masa sannan ya shiga motan shi yayi gaba.shi kuma wannan tsohon ya shimfid'a tabarman shi tare da fara alwala. Da sallama ta shiga cikin gida Umma tana ganinta ta bar kwashe tuwo da take a bakin murhu tace " AMIRA me ya same ki na ganki haka ga yanda idonki da fuakanki suka kumbura?" Share gutun hawaye da ya gangaro mata tayi sannan tace " wallahi Umma wasu ne ina dawowa a hanya dan sunyi min magana naki kulasu shine suka tare min hanya da kyar wani bawan Allah ya shiga tsakanin mu suka barni.shine ma ya kawo ni har kofar gida dan karsu kara biyoni". Umma tana tafa hannu tare da salati tace " kema Amira ba kya ji bance ki daina bin wannan layin ba,kuma daga yau kar in kara jin kin shiga motan wani dan duniyan nan yanzu ta zama abin tsoro". " kiyi hak'uri Umma insha Allah zan kiyaye".Amira tace cikin maraicewa. "Allah ya tsare gaba" Umma tace tare da cigaba da aikinta. D'akinsu Amira ta shiga dan cire uniform,k'anwarta Fateema ta taso cikin sauri tace " tab Ameera ashe yau kin auni arziki". Murmushi Ameera tayi " hmmm sis bari kawai da Allah bai kawo mutumin nan ba da ban san wani hali zan kasance ba". Allah ya kiyaye fateema tayi mata ta amsa tare da d'aukan buta zuwa toilet. Mallam yawale shine maifin Ameera,da mahaifarsu Hadiza wacce suje kira da Umma dukkan su cikakkun 'yan Kaduna ne. Malam Yawale talakane bashi da komai illa gidan da yake ciki,shima gada yayi a wajan mahaifinsu shi k'anwarsa basira.itama tana aure a nan cikin garin kaduna da 'ya'yanta. Mallam Yawale ya kasance masani ne shi ta fannin adsinin islam dan yayi saukan alqur'ani tun yana shekara sha bakwai a duniya sannan yayi karatun litattafai da dama,dan haka kullum kullum kofar gidan shi cike yake da masu d'aukan karatu manya da kanana. Malam ya bawa 'yan matansa ilimi na boko da arabi ga kuma tarbiya da ya basu,kowa yana sha'awar su a anguwan su. Al'ameen kuwa yana tafiya cikin motan shi zuwa gida amma hankalin shi gaba d'aya yana kan yarinyan da ya gani domin shi asalima yana son mace kamila gata tayi shigan mutunci wanda matan aure ma da dama basayi suna fito da tsaraicinsu a ganin su wayewa ce amma kuma b'atace babba Allah ka shirye mu baki d'aya ameen. Da irin tune-tunen nan ya isa gida,sallama yayi ya shigo waiting palour,cikin ikon Allah yau ba taron mutane da ya saba gani kuma hakan ya d'anji sanyi a ranshi. Kai tsaye main palour ya shiga ya samu Latifa da k'annenta suna kallo,tashi tayi cikin fara'a ta tare shi.sannu da zuwa k'annenta suka mishi sannan suka wuce part d'in su. Bayan yayi wanka ya fito sanye da jallabiya fari kal,dinning ya wuce cikin jagorancin Latifa yaci abinci sannan suka dawo palour suka zaune kallo. Suna cikin kallo Latifa ta tashi ta shiga part d'inta,jimawa kad'an ta fito da wasu files a hannunta ta zauna kusa dashi. Mik'o mishi tayi tace " gashi yi signing a nan" Karb'a yayi yana jujjuyawa yace " what for?" Kin kula shi tayi ta cigaba da kallonta hankali kwance. Ganin haka yasa ya bud'e ya fara karantawa...... "Ai ba sai ka karanta ba, taimako nake sonyi kasan 'ya'yanGwaggona na can garin mu basuda aikin yi shiyasa". Kallonta kawai yake yandatak koro bayani tare da maimaita a ranshi 50 millions!!!.kuttt toh wai wani tsawon lokaci ta d'auka tana cutansa?coz da alamu ba yau ta fara ba. Murmushin takaici ya mata yace " good my Lateefa,taimako abune mai kyau amma ki bari zan samu contract na 100 millions next month sai in baki kinga sai kiyi yanda kike so kin huta da kad'an-kad'an daga nan ki taimakawa duk wanda kika ga yana bukatan taimako". Washe baki tayi cikin murna tace " gaskiyane my Ameen hakan yayi min sosai zan jira zuwa next month d'in". Tashi tayi cikin sauri tayi hanyan part d'inta. Shi kuma kallon takaici ya.bita.dashi a ranshi yana aiyana matakin da ya kamata ya d'auka a kanta kamin next month d'in.daga nan shima ya mik'e zuwa part d'insa. Kallon system d'in shi yake kaman mai neman wani abu amma a zahiri a shi yake kallo ba yarinyan d'azun yake tunani kuma ba abunda yake so kaman kallon fuskan yarinyan. Rufe system d'in yayi ganin ya kasa tab'uka komai,kwanciya yayi flat akan gadon shi yana wasi-wasi yaushe rabon da ya kalli mace a matsayinta na mace har ya manta amma yau yar yarinya k'arama da ko fuskanta bai kalla ba bare ya san sunanta ta hana shi bacci. Daga baya ya yanke hukunci gobe zai koma gidansu ya tambayi koda sunan tane. [3/24, 6:47 AM] Ummee Yusuf: . 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA~* 😭😭😭😭😭😭 ( its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman Yusuf) ✍✍✍✍✍✍✍ GOLDEN PEN WRITER'S ASSOCIATION ✍✍✍✍✍✍✍ *~part ten~* Da washe gari Al'ameen da wuri ya shirya ya fito cikin wani shadda light blue wanda ya k'ara fito da k'yansa. Ko kallon dining area da yake cike da kayan break fast baiyi ba yayi ficewarsa.saboda ya matsu ya kalli fuskan yaruyan nan dan jiya ko baccin kirki bai samu ba. Latifa kuwa ko tashi ba tayi ba daga bacci. Musa driver yana ganin fitowan shi ya taso cikin sauri ya bud'e mishi owner seat ya shiga ya zauna. Duk'awa yayi ya gaishe shi sannan shima ya bud'e driver seat ya shiga ya zauna tare da yiwa motan key suka fita a gidan. Al'ameen ne yace " ammm musa mu fara zuwa tudun wada kafin mu wuce office". " toh ranka ya dade" musa yace cikin girmamawa. Nuna mishi hanya ya fara har suka iso k'ofar gidan mallam Yawale,nan yace mishi ya tsaya anan Brick Musa yaja ya tsaya tare da mamakin meye mai gidansa zaiyina wannan rugujajjen gidan. Fitowa Al'ameen yayi daga cikin motan ya jingina da jikin motan yana kallon gidan. Ganin haka yasa Musa daga motan shima ko akwai wani abinda zaiyiwa mai gidan nashi. Shi kuwa Al'amewn tunani yake ya zaiyi yaga yarinyan da ko sunanta bai sani ba. Wani almajiri ya gani ya fito daga cikin gidan da k'wanon baran shi a hannu, kiran shi Al'ameen yayi,nan ya taho da gudun shi. Al'ameen yace " kasan mutanen cikin gidan nan ne?" " a'a nima bara na shiga yi kuma ban samu komai ba" almajirin ya amsa mishi. "Da ka shiga kaga wata yarinya a cikin gidan " Al'ameen ya kara jeho mishi tambaya. " eh nagani ai su 2 ne" shima ya amsa mishi. Tunani ya tsaya yi,ya zaiyi tunda ance su 2 ne kuma gashi bai san sunan wacce yake nema ba. Dabara ce ta fad'o mishi ya kalli almajirin yace " yi maza ka koma kace ana sallama da 'yan matan gidan". Da toh ya amsa ya koma cikin gidan yayi sallama, Umma ta sauke uban tagumi da zabga tace " haba almajiri nace maka Allah ya bafa sa'a tundazu ko?" " ni ba bara nazi yiba wani ne a waje yace ana sallama da su 2 nan" yace yana nuna su amira dake zaune da yatsa. " su 2nan?" Umma ta k'ara tambaya tare da dafe kirji. " eh da mota ma yazo " yace tare da ficewa abin shi. Zuciyar Amira sai bugawa yake tace " oh! ni Amira kar dai mutumin jiya ne ya dawo?" Umma ne ta katse mata zancen zuci da take tace " sai kuje ku gani dame yazo kuma kar ku mantavda maganan Babanku". Dogayen hijabansu suka sa sannan suka fita suka bar Umma da tunanin waye yake neman 'yan matan ta duka 2 kuma harda mota. Al'ameen yana nan tsaye almajirin yazo yace " wai suna zuwa". Hannu Al'ameen yasa a aljihu ya ciro 200 note ya mik'a mishi tare da cewa ya gode.shima karb'a yayi yana ta murna ya tafi. Tun a zaure Fateema ta fara yiwa Amira magana " kina ganin waye zai zo neman mu anya ba mutumin da ya taimake ki jiya bane?" Ganin sun fito k'ofar gida yasa Amira k'ara yin k'asa da kai ba tare da ta amsa mata ba. Tunda suka fito ya kafe Amira da ido yana kallon yanda take taku cikin natsuwa. D'an nesa da shi suka tsaya a tare suka d'an duk'a suka gaishe shi. Amsawa yayi cikin murmushi yace " dan Allah wacece a cikin ku jiya muka had'u da ita ta taso daga makaranta?" Fateema ce ta d'ago kai suka had'a ido ta kalli k'yawawan mutumin nan tayi murmushi tace " gata nan yayata ce". " ok good ya sunanki please?" " Fateema" " yayarki fa ?" ya k'ara tambaya. " Amira sunan ta" ta bashi amsa. Murmushi ne ya kwace mai jin sunan ta mai dad'i yace " toh fateema nagode dama Amira nake son gani". Sallama tayi mishi ta koma ciki. Musa ma ganin haka yasa yayi gaba ya basu waje. Kallonta yake ba ko kitawa ganin har yanzu tak'i d'ago kai. Gyaran murya yayi sannan ya kira sunata cikin sanyin murya. Amsawa tayi da tsiririn muryarta still kanta a k'asa. " tunda nake ban tab'a ganin mai suna amira marowaciya ba sai a kanki". A d'an razane tace " rowan me nayi maka kuma?"still kanta yana k'asa at d same time tana mamakin wannan mutumin ita meye gare ta da har zaice tayi masa rowa. " kusan 24 hrs da mu amma kin hana ni kallon prity face d'inki". Bata san lokacin da ta saki 'yar dariya ba har tsiririn wushiryan ta ya bayyana sannan ta d'ago kai a hankali suka had'a ido. Tasbihi ya fara a zuciyan shi ganin k'yaunta mai firgitarwa. Amira fara ce sol wanda har ja-ja take gata da dogon hanci da ya dace fuskanta ga maidaicin bakinta tare da idanun ta masu oval shape.in short Amira tayi 100%. Kanta ta mayar k'asa dan ba zata iya jure irin kallon k'yakyawan fuskan shi ba. Cike da tsokana yace " woah ashe da 2 kike b'oye min fuskan ki dan u re so ugl....."yasa hannu ya rufe bakin shi yana dariya tare da hana bakin shi k'arasa maganan. B'ata fuska tayi ta d'ago tana kallon shi dan ta rasa bakin magana. Shi kuwa shagala yayi da kallonta dan gani yayi tkaman ma tafi k'yau da ta b'ata fuskan. Dariya yayi yace " am sorry just kidding u re d most beautiful girl dat i hav ever seen in my life". Batayi magana baba sai dai murmushi da tayi tanan kallon gefe. "Duk da baki damu ki san suna ba i'm Al 'ameen nazo ne mu gaisa kuma mu san juna ". Hannu yasa a aljihu ya ciro bounch 'yan 200 yace " ga wannan ki sayawa k'anne na choculate ni zan wuce office". Kallon kud'in tayi ba tare da ta karba ba tace " nagode ka barshi kawai dan in na shiga ciki da shi Umma zata min fad'a kuma ko fitowan nan da nayi in Abba yazo shima fad'a zaiyi". Ji yayi ta k'ara burge shi tare da samun special place a hrt d'in shi.yace " toh shike nan ki turo min Fateema muyi sallama". Amsawa tayi tare fa yi mishi sallama ta shiga ciki. Tana shiga ta tarar da Fateema ta zage tana bawa Umma labarin wanda yazo gun Amira . Waje ta samu gefen Umma ta zauna sannan ta kalli Fateema tace " wai kije kuyi sallama". Cikin zumud'i Fateema ta fice. Umma kallon Amira tayi tace " da fatan kin fada mishi Abban ku baya so ko"? Tace " na fad'a mishi Umma". " yauwa gara ki ki fad'a in ba haka ba koni ba fita zanyi a wajan Abban ku ba". Fateema tana fita ta same shi yana tsaye a inda suka barshi,tace " gani" " Fateema dama dan muyi sallama ne kuma ga wannan ki sayi choculate". Zaro ido tayi gani kud'i sabbi fil suna d'aukan ido tace " lah-lah Abba zai min fad'a ba zan karb'a ba". " ki kaiwa Umma " yace . "A'a itama ba zata karb'a ba " tace tana baya dan sisai kud'in sun tsoratata. " in kince injini zata karb'a " yace yana kara mik'o mata kud'in. Hannu 2 tasa ta kar'ba sannan tace " ka jira ni anan dan in tace ba zata karb'a ba zan kawo maka kud'inka ". Murmushi yayi ganin yarintar ta yace mata " na yarda je ki kai mata ina jiran ki" Da sauri tayi hanyan cikin gida. Yafito musa yayi da gannu suka shiga mota suka bar anguwan. [3/24, 6:47 AM] Ummee Yusuf: . 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA~* 😭😭😭😭😭😭 ( its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman Yusuf) /✍✍✍✍✍✍✍ GOLDEN PEN WRITER'S ASSOCIATION ✍✍✍✍✍✍✍ https://www.facebook.com/groups/1569379426621615*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~* *~part eleven*~ Fateema tana shiga cikin gida ta mik'owa Umma kud'in tace " gashi Umma wai yace in kawo miki" Fad'a Umma ta hauta dashi kan ta mayar mata da kud'in shi tun kan ranta ya b'aci. Ba musu ta juya ta fita mayar mishi da kud'in shi kaman yanda Umma ta umarce ta. Sai dai me tana fita taga wayam ba Al'ameen ba motan su,cikin sanyin jiki ta koma gida. Tana shiga ta tarar har yanzu Umma bata daina fad'a ba. Zama tayi kusa da Amira tace kiyi hak'uri Umma dana fita bangan su ba sun tafi. Amira ra saci kallon Umma da ta kasa magana saboda takaici tace " mesa kika karb'a Fateema nima ya bani kin karb'a nayi". Girgiza kai Umma tayi cikin takaici tace " kinsan hankali bai ishe ta ba inba haka ba me yasa kika karb'i kud'in shi me zancewa Abban ku in ya dawo?" "Umma ki rik'e kawai tunda ya riga ya baki kawai mu sayi abin karyawa dashi tunda tun safe bamu ci komai ba". Duka Umma ta kai mata a cinya tace " taya zamu tab'a kud'in da bamu san daga ina ya fito ba,duniyan yanzu ba abin yarda bane bamu san daga ina yake ba dan haka ajiyewa zanyi mujira zuwan Abban ku ya yanke hukunci.kuma ina son ku kasance masu hak'uri a duk yanda kuka sami kanku a ciki dan ba yau kuka saba zama ba abinci ba,dafatan kun fahimce ni". " eh Umma " suka ce a tare. Al'ameen kuwa tunda yaje office ya kasa tab'uka aikin kirki gaba d'aya tunanin Amira nan ya addabe, shi wani special feelings yake ji akanta wanda bai tab'a ji a kan ko wace mace ba.ji yake kaman ya koma ya k'ara kallonta ko zaiji d'an ji relief. A daddafe yayi sallahn la'asar yana idarwa ya fad'a mota ko ta kan musa driver bai bi ba sai tudun wada gidansu Amira. Abba ne yayi sallama ya shigo cikin gidan shi. Fateema ce ta tashi cikin sauri ta karb'i 'yar ledan da ya shigo da ita ta mik'awa Umma tare da kawo mishi ruwa a randa mai sanyi a kofin silver. Sannu da zuwa Umma ta mishi,sai da ya sha ruwan da Fateema ta kawo mishi sannan ya amsa. "Ya kasuwan Mallam" tace tana bud"e ledan da ya shigo dashi. " kasuwa alhmdllilah kin ganni sai yanzu ko,ina Amira take?" "Amira ta tafi islamiya" Umma ta bashi amsa. " haba ya zaki barta ta tafi bata ci komai ba " Abba yace cikin damuwa. Umma tana juye garin rogo da suger da ya kawo a k'wano tace " toh ya zanyi?nace ta hak'ura da zuwa makarantan amma tace dole taje dan yau zasu bada hadda shiyasa na k'yaleta ta tafi". "Allah sarki Amira akwai kok'ari Allah ya musu albarka" Abba yace . "Ameen " Umma tace sannan tacigaba da cewa " bayan ftanka Mallam wannan mutumin da ya taimaki Amira jiya ya dawo ya nemi su gaisa,bayan sun gaisa ya bata kudi da taki karb'a shine yayi wannan mai rawan kan dabara wai ta kawo min inna k'i karb'a ta mayar mishi da kayan shi.tana shigowa na hauta da fad'a nace ta mayar mishi da kud'in shi,tana fita taga sun tafi shine na ajiye nace idan ka dawo sai kasan yanda za'ayi dasu.ke tashi ki kawo yagani" tace tana hararan Fateema. Tashi Fateema tayi jiki a sanyaye ta kawo kud'in ta mik"awa Abba. Cike da mamaki Abba yake jujjuya kud'in a hannu,ya bud'i baki da niyan magana sallaman wani yaro ya katse shi. " wai ana sallama da Mallam inji wani a waje" yace bayan sun amsa mishi sallaman. Tabarma Abba yace a bawa yaron ya shimfid'a a zaure kuma yace yana zuwa saboda ya d'auka cikin irin mutanen nane masu zuwa neman sani. " karb'i ki ajiye ina zuwa " yace tare da fita zuwa zaure. Had'e rai yayi sosai ganin Al'ameen zaune kan tabarman da yaron ya shimfid'a. " d'an samari lafiya,me kake buk'ata me yasa kake bibitan gidana?"Abba ya jero mishi wa'yanan tambayoyin. Kasa da kai Al'ameen yayi yace " Mallam kayi hak'uri bakomai a raina sai alkhairi,ammmm dama......nace Amira nagani nake...in ba'ayi mata miji ba"ya karasa cikin ladabi. Kallon shi Abba yayi da k'yau sannan yace " waye kai kuma daga ina kake?" Gyara zama Al'ameen yayi yace " suna na Al'ameen mudassir kuma ni d'ane ga Alhaji mudassir Inuwa". Nan da nan fuskan Abba ya washe fara'a ya cika fuskan shi saboda ba wanda bai san shi ba a cikin garin k.d saboda halayyarsa masu k'yau ga taimakon talakawa " Alhaji Mudassir da sani ?" Murmushi kawai Al'ameen yayi ya sunkuyar da kai. Abba yace " kasan san samarin yanzu ne basu da tabbas sai ka d'auki shekaru kana bawa 'ya'yanka tarbiya wani yazo lokaci d'aya ya rusa maka shiyasa kaga nak'i baka fuska tun farko amma yanzu tunda naji daga inda kake ba komai sai ka nemi amincewanta dan banyi mata miji ba Allah ya zab'a abinda yafi alkhairi" Godiya Al'ameen yake ta zabgawa kaman wanda aka mishi albishir da gidan aljanna. cike da farin ciki ya tashi ya fad'a mitan shi sai gida. Abba yana shigowa yacewa Umma " ke mik'o min kud'in nan inje bakin kasuwa in sayo mana balangu" Umma tace " haba Mallam yanzu kaima cewa zakayi ma tab'a kud'in nan?bayan bamu san daga inda ya fito ba". "Waya fad'a miki ba'asan daga inda ya fito ba?"nan Abba ya k'washe yanda sukayi da Al'ameen ya fad'a mata. Shiru Umma tayi dan ita maganan bai mata ba ina au ina gidan Alhaji Mudassir. Fateema kuwa dad'i kaman ya kashe ta 'yar uwarta ta samu mijin nunawa sa'a. Sallama Amira tayi ta shigo tayiwa Abba da Ummanta sannu da gida ta wuce d'akinsu ran cire unifirm. Kaman wacce aka tsikara haka fateema ta mike tabi bayanta da gulsa mata abinda ya faru [3/24, 6:47 AM] Ummee Yusuf: . 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA~* 😭😭😭😭😭😭 ( its all about love and betrayal) https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman Yusuf) ✍✍✍✍✍✍✍ GOLDEN PEN WRITER'S ASSOCIATION ✍✍✍✍✍✍✍ Sis zara Allah ya raya mana baby samha Allah ya albarkace ta da sauran zuri'an mu baki daya ameen. *~part twelve*~ "Sis ya k'ara zuwa".Fateema tace cike da zumud'i. Kallonta Amira tayi tace "waye yazo kuma?" "Al'ameen ". Zuciyarta sai da ya buga jin sunan amma ta dake tace " waye kuma Al'meen kuma?" Matsowa Fateema tayi kusa da ita tana washe baki tace " wanda yazo wanki d'azu da safe". Dafe kirji tayi tana zaro ido tace " Allah yasa Abba bai ganshi ba". " na nawa kuma Abba ya ganshi har sunyi magana". "Innalillahi wa inna ilahi rajiun!! Na shiga uku me Abba yace?"ta tambaya a rud'e. Dariya Fateema tayi ganin yanda Amira ta rud'e tace " k'wantar da hankalinki sis bcos Abba ya amince dashi 100% dan yanzu ma kud'in da ya bayar.yana hannun shi wai zaije bakin kasuwa ya sayo mana balangu". Dariya itama Amira tayi tace " ke Fateema bakin nan naki akwai son cin dad'i". K'asan ranta kuwa fap farin ciki dan itama tun da ta had'a ido dashi ta kasa daina tunanin shi a ranta. ******************** Bayan 2 days Al'ameen ne zaune a palourn gidansu suna hira da parent d'in shi sai dai hajiya hankalinta gaba1 yana kan wani program na larabawa da take kallo. Al'ameen ya gyra zaman shi kusan yafi a k'irga dan baisan mesa ba yake jin nauyin maganan da yazo dashi kaman wani sabon shiga. Alhaji yana ankare dashi yace " yaya dai kaman kana da magana ko?" Murmushi yayi ya sunkuyar da kai yace " eh toh kusan hakane nazo neman shawara ne akan wata yarinya da muka had'u da ita 2days ago and da ikon Allah tun daga lokacin sha'awan k'ara aure ya shiga raina". " masha Allah!!"Alhaji yake ta makmaitawa. Hajiya kuma cikin farin ciki ta juyo tace " Alhamdullilah naji dad'in maganan nan Allah ya sanya alkhairi yasa muga jikokinmu". "Ameen ameen a ina yarinyan take ne?"Alhaji ya tambaya. "A can tudun wada take 'yar gidan Mallam Yawale ". " toh masha Allah zan sa a min bincike akanta gudun fad'awa gidan jiya,in har ba'a samu zamu je bayan k'wana 2". Hajiya ta gyra zama tace" Al'ameen abinda nake so da kai kar ka kuskura matarka taji labarin nan kasan halinta ba abinda ba zata iya aikatawa ba,saboda haka k rufe maganan har saikomai ya kammala sai ka gaya mata". Cikin gamsuwa da maganan Hajiyarsa Al'ameen yayi godiya sannan ya musu sallama da sunan zuwa office office ya wuce. A wani babban shopping mall Al'a.een ya tsaya ya saya mata waya iphone 7 pink colour,ya had'a da kayan ciye-ciye yayi hanyan gidan su Amira. Parking yana neman d'an aiken da zai tura dan kira mishi ita. Cikin sa'a yaga wata yarinya da tallan awara akanta. Ba b'ata lokaci ya kirata tazo da gudunta ta ganin mai mota zai sayi awaranta. "Na nawa zan baka"ta tambaya cike da jin dad'i. Dariya yayi yace mata " na nawa ne a ciki?" " na 350 ne "ta amsa cikin gaggawa. 500 ya mik'a mata yace taje tayi sadaka kuma ta shiga gidan can ta k'ira mishi Ameera. Karb'an kud'in tayi sannan ta ajiye roban ta ruga da gudu zuwa cikin gidan tayi sallama. Fateema ce a tsakar gidan tana wanke-wanke ta amsa mata. " wai wani mai mota yana kiran Ameera" tace tana haki. " mai mota kuma" Fateema ta tambaya" Kamin ta amsa Umma ta lek'o a dak'i tace " je ki gani mana ko yaron nan ne ?" Da sauri ta tashi tayi hanyan fita bayan ta zura hijabinta. "Tana zuwa akace kuma banida cangi dan banyi ciniki ba tun d'azu na fito". Kallon tausayi yayiwa yarinyan yace " jeki abinki ngode ". Da murna ta d'auki robanta ta tafi. Fateema tana lek'owa zaure suka had'a ido dashi murmushi tayi ta koma cikin gida da sauri. "Umma shine yazo" "Toh d'auki tabarma ki kai mishi zaure bai kamata su tsaya a waje ba yanzu tunda Abbanku ya amince dashi".Umma tace mata. Tabarman ta d'auka ta fita zauren dashi ta shimfid'a sannan ta fita zuwa insa yake tsaye. Sallama tayi mishi ya amsa yana tambayanta mutanen gida. Amsawa tayi da lafiya sannan ta.mishi iso cikin zaure. Gaba tayi ya biyo bayanta har cikin zauren nan ya zauna kan tabarman ita kuma tayi cikin gida. D'akinsu ta shiga ta tarar da Ameera tana k'wance ta lumshe ido kaman mai bacci sai da a zahiri ba baccin take ba tana dai tunanin ya zatayi in ta fita wajan shi dan bata tab'a tsayawa da wani namiji da sunan zance ba. Tashinta Fateema ta farayi ta bud'e ido tana kallon Fateema tace "lafiya ina baccina zaki tashe ni?" " sis nasan fa ba bacci kike ba u re just pretending tashi mai sonki yazo yana jiranki". " nifa Fateema bansan ya zanyi ba in na fita nifa kunya nake ji "tace kaman tayi kuka. " kunya?haba sis sai kace a zamanin su Umma kike?tashi kiyi light make up kije dont keep him waiting". Kamin ta bata amsa Umma ta d'aga labulen d'akin tace " zaman me kike Ameera tundazu kin bar bak'o yana jiranki?tashi ki wuce bana son shashanci". Tashi tayi tana tura baki tasa wani white long hijab d'inta sannan ta nufi zauren. Tundaga bakin zauren take jin fitinannen kamshin turaren yana tashi sallama tayi mishi da sweet voice d'inta,amsawa yayi yana kallonta da murmushi akan fuskan shi.can gefe nesa dashi ta samu waje ta zauna kanta a k'asa. Jin idanun shi akanta yasa ta d'ago suka had'a ido turo baki tayi tare da kallon gefe dan ta tsani yawan kallo. " ina wuni "tace ba tare da ta kalle shi ba. Kallonta kawai yake cikin shauk'in sinta dan turo bakin nan da tayi saida ya.jefa shi wani hali da k'yar ya tattaro natsuwa yace" rik'e gaisuwarki dan bazan amsa.ba,haba prety haka ake gaisuwa?" Satan kallon shi tayi ta gefen ido taga har yanzu idon shi akanta,kara turo bakin tayi cikin ranta ta mitan yana bata kunya.cike da shagwab'a tace " toh ya akeyi ?" Ya Salam yace a ranshi dan yanda yarinyan take sashi rasa natsuwa. Mik'ewa yayi ta ajiye shopping bag d'in a gabanta yace toh shi kenan tunda na lura kunyata kike ji ga waya nan a ciki ki sakata a charge zan kira ki anjima maybe zaki fi sakewamu gaisa sosai ta wayan". Tana nan zaune ya juya yace " saina kira prety na wuce office". Har yasa kai zai fita yaji muryanta a bayan shi tace " nagode Allah ya kiyaye". Juyowa yayi ya fasa fitan yana kallonta saboda yanda yaji dad'in addu'an data mishi har cikin ranshi dan duk tsawon zaman shi da Lateefa bata tab'a mishi addu'a dan yayi mata wani abu ko dan zai fita ba.amma yau gashi 'yar k'aramar yarinya tayi mishi nan yaji ta k'ara samun waje na musamman a zuciyar shi. " Ameen prety nima nagode " yace sannan yasa kai ya fice. [3/24, 6:47 AM] Ummee Yusuf: . 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA~* 😭😭😭😭😭😭 ( its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman Yusuf) ✍✍✍✍✍✍✍ GOLDEN PEN WRITER'S ASSOCIATION ✍✍✍✍✍✍✍ *~part thirteen~* Saida taga fitan shi sannan ta tashi tare da nannad'e tabarman ta shiga cikin gida bakinta d'auke da sallama. Jingine tabarman tayi a jikin bango sannan tazo ta mik'awa Umma shopping bag d'in a hannunta. " shi baya gajiya da hidimane?" Umma tace lokacin da take bud'e bag d'in. Ihu Fateema tayi had'e da salle sai gata a gaban Umma ,cikin tsananin murna take magana " lah sis iphone 7 nefa". Harara Umma ta banka mata tace " ke ko Fateema ba zaki natsu bako?" Komawa tayi ta zauna tana "kiyi hak'uri Umma na daina". Mik'awa Ameera ledan wayan Umma tayi,aiko kamin ta karb'a har Fateema ta rigata. Rik'e baki Umma tayi ta bita da ido tana "Allah ya shirya min ke Fateema". " Ameeeen Ummana" ta amsa daga ciki tana dariya. Kiranta Umma ta k'arayi ta basu kayan ciye-ciye da Al'ameen ya kawo. Zama sukayi dirshan a d'aki suna cin kayan ciye-ciyen Fateema tana taya ta oprating wayan dan duk gidan basu da waya sai Abbansu da yake da k'aramar tecno. Fateema ta fita sanin kan waya dan tana karb'an na frnds d'inta a school.tsab'anin Ameera bata da karambani shiyasa bata wani iya kan waya sosai ba balle wannan mai tsadan. Saida sukayi mai isarsu sannan ta jona ta a charging suka fito tsakar gida dan taya Umma aiki. Kusan 11pm Ameera ta kasa bacci sai latse-latsen wayarta take. Wani irin zabura tayi jin ringing d'in wayan saura kiris ya tsub'uce a hannunta. Tsayawa tayi tana kallo kaman ba karta d'auka. Saida ya kusan tsinkewa sannan ta d'aga cikin sanyin muryarta tace " Assalamu alaikum". Wani irin sanyine ya ziyarci shi wanda ya haddasa mishi sauke ajiyan zuciya har tana jiwo shi ta cikin wayan. "Wa alaikis salam my prety,me kike yi har yanzu bakiyi bacci ba?" " na fara bacci ringing wayan ya tashe ni " A rud'e yace " Ya Salam i'm soo sorry pls ki koma baccinki kinji?" Dariyama ya bata ganing yanda ya wani rud'e dan tace tana bacci ne ya tashe ta. Jikin shine ya mutu murus jin dariyarta kunnen shi,how he wish a gaban shi tayi baisan halin da zai shiga ba bcos yarinyan nan komai nata daban yake. Shi baisan wani irin so yakewa yarinyan nan ba dan abinda yake ji akanta bai tab'a jin ko quatern haka akan matar shi Lateefa ba balle wata macen. "Wasa fa nake maka banyi bacci ba " ya sake jin muryanta ta katse mishi zancen zuci da yake."keko hmmmmm' ina Fateema?" "Gata nan tana bacci"ta bashi amsa. "Ameera...."ya k'irata da wani irin murya da baisan yana da ita ba. Da k'yar Ameera ta iya amsawa da ummm dan bakin ta yayi mata nauyi jin yanda ya kira sunanta for d first time kuma in a in a special way. "Bansan ta ina zan fara ba prety but all i knw is dat i totaly fall 4 u since d day met.shiyasa na kasa hak'uri har nazo wajan Abba da fargaban ko anyi miki miji,sai dai Alhamdullilah Abba ta tabbatar min da bai bada ke.so its only me in d field kenan?" Shiru tayi mishi ba tare da tayi magana ba,but murmushine k'wance a fuskanta. " y re u silent prety bani amsa mana ko sai nazo da kaina zaki bani amsan?" A hankali ta bashi amsa da " eh". " ok gani nan zuwa yanzu". Cikin sauri ta katse shi da cewa " kasan karfe nawa ne yanzu?" " koma karfe nawa ne i don't care dole inzo inji amsata bcos i can't wait till morning dan kona k'wanta bazan iya bacci ba". 'Yar dariya tayi tace " yi hak'uri ba sai kazo ba". "Then" yace yana d'aga gira 1 kaman yana gabanta. Still shiru tayi tana murmushi. Canza topic d'in yayi na yanda zata saki jiki suyi hira. " kina j.s.s 2 ko 3 a secondry school?" Dariya tayi.dan tambayan dariya y ya bata "Oh na d'ebo dayawa ko" " na gama dis year ko Fateema tana s.s 2".ta bashi amsa tana dariya. " woah ashe da babban yarinya nake magana wat abt islamiya?"ya kara jeho mata da tambaya. " hmmm mun kusa had'a haddan mu " " afuwan yaah mu'allima" yace yana sassauta murya. Nan ma dariya ta rink'ayi,kaman wasa sai gashi cikin dabara ya sa ta saki jiki suka sha hiran su har kusan 1:30am sannan ya hak'ura ya k'yaleta dan tayi bacci ba dan ya gaji ba. Yana ajiye wayan ya kalli wall clock dake manne a jikin bangon d'akin,tsiririn tsaki yaja a ranshi yana mita kana da mata amma ba kada maraba da gauro. Ameera sai juyi take tana murmushi ita kad'ai ta kasa bacci sai wani nishad'i take a ranta tana mamakin dama haka so yake?da k'yar ta samu bacci ya d'auke . After 2 days Alhaji Mudassir ya samu duk wani information da yake son ya samu akan Ameera kuma ya gamsu sosa dan haka ba b'ata lokaci ya k'ira Al'ameen yace ya sanar da ita zasu je gidansu gobe da yamma. Cikin tsananin farinciki ya k'ira ta a lokacin suna d'aki ita da Fateema tana tayata drawing d'in heart da aka basu assignment a makaranta. Murmushine ya sub'uce mata ganin kiran hrt beat d'inta dan yanzu ta sake dashi suna shan hiran su yanda ya kamata amma fa a waya. D'agawa tayi tare da sallama,amsawa yayi cikke da nishad'i dan ji yake kaman har an d'aura auren. "Guess wat" " i'm not gud at guessing just fad'a min nima in taya ka farinciki da alama abin farinciki ne ya samu" ta bashi amsa. "Hakane kince u re nit gud at guessing but gashi kuwa har kinyi". "Hmmmm ta muryarka na gane kana cikin nishad'i yau". "Ba kad'an ba kuwa ki sanar da Abba gobe Alhajina zasu zo gidanku". Sassauta murya ya k'arayi yace sunga na fara zaucewa akanki shi zasu taimaka su kawo min ke dan kar in ida zauc......". Katse wayar tayi tana murmushi dan wani lokacin kunya yake bata. Zungure ta Fateema tayi ta juyo da sauri suka sa dariya. " kin fad'a dayawa sis " Fatema tace tana dariya. " Fateema kenan ba zaki gane ba a yanzu har sai kema Allah ya had'aki da real love d'inki,kinga yanzu je ki fad'awa Umma yace gobe Alhajin shi zasu zo wajan Abba". Cikin tsananin murna Fateema ta rungumeta sannan.ta sake ta ta fita da.gudu zuwa tsakar gida tana kiran Umma. Fitowa Umma tayi daga d'aki har tana tuntub'e saboda rud'ewa. Clashing tayi da Fateema tana washe baki,cikin fad'a Umma ta fara mata fad'a. Hak'uri ta bata tare da fad'a mata sakon Al'ameen. " Allah sarki ameera ita kunya ya hanata fad'a sai ke ko uwar rawan kai". Komawa tayi daki tana dariya. Alhaji sun cika alkawari sun zo neman auren d'an autan shi tare da jama'rshi. Sun samu tarba mai k'yau wajan mallam Yawale da mutanen shi.nan akasa sa ranan aure 3weeks kacal bisa umarnin Al'ameen. Mallam Yawale yaso a k'ara mishi lokaci saboda yanayin rayuwa amma Alhaji mudassir yace su basa bukatan komai daga gare shi dan su .ata suka nema kuma an basu shikenan. Nan taro ya watse kowa cike da farinciki more especially Al'ameen da yake jk kaman ya zuba ruwa a k'asa ya sha. [3/24, 6:47 AM] Ummee Yusuf: . 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA~* 😭😭😭😭😭😭 ( its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman Yusuf) https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~* *~part fourteen~* Lateefa tana can tana budurinta hankali k'wance bata san wainar da ake toyawa ba dan ko kad'an Al'ameen bai nuna mata wata alama ba. Ana saura 2weeks biki,aka kawo kayan lefe na gani na fad'a.akwati set 2 masu k'yau da tsada kuma fad'an kayan cikin b'ata lokaci ne. 'Yan uwan Abba da Umma abin ya basu mamaki dan basu tab'a ganin lefe haka ba. A wannan lokacin kuma wani irin soyayya da shak'uwace ta shiga tsakanin Ameera da Al'ameen dan kullum sai yazo da safe ya ganta before ya wuce office,haka ma da yamma sai yazo sun sha hiransu sannan zai wuce gida. At night ma suna manne a waya sai sun kusan raba dare suna yi sai dai in Lateefa ta shigo ne ba zasuyi ba. Ana saura 1 week biki Al'ameen ya har ya gama gyara gida duk da gidan da k'yansa amma hakan bai hana shi yiba more especially part d'in amarya yafi ko ina shan gyara. Tun ana saura 2 weeks musamman yayi ordern kayan funutres daga italy kayan kitchen kuma daga dubai. Ameera amarya itama tasha gyara ciki da waje dan kullum Umma cikin yi mata d'ure-d'ure take. 'Yar gwaggonta basira kuma itace ta d'auki nauyin gyaran fata da kamshin jiki,cikin lokaci kad'an ta canza fatanta yayi wani irin k'yau abinka da farin fata har wani shek'i taje ga kamshi da jikinta yake na musamman. Duk irin gyaran da ake a gidanta Lateefa bata kawo komai a ranta ba saboda tasan abinda ta taka. Ana saura 1 week kayan da Al'ameen yayi oder suka iso. Lateefa da k'annenta suna zaune a palour suna hira suka ga aka fara shigowa da kaya nik'i-nik'i. Cikin tashin hankali Fa'iza tace " Aunty wai meye yake faruwa ne naga anata shigowa da kaya ?" Shamsiya tayi carab tace " ko dai Ya Al'ameen ne zaiyi aure?" Zabura Lateefa tayi daga kishingid'en da take tare da yayimo wata uwar ashar ta d'ura sannan tace " ke daina irin wannan maganan a cikin gidan nan,yama isa yace zaiyi aure a gidan nan". Fa'iza ta girgiza kai tace " Aunty maganan Shamsiya fa abin dubawa ne,ki tuna how many days akayi ana gyara a gidan nan ga kuma kayan da yanzu ake shigowa dasu ma sun isa shaida". Jiki a sanyaye take binsu da kallo can tace " amma fa kunsa jikina yayi sanyi but bari ya dawo ya same ni,wallahi in dai da gaske auren zaiyi wallahi Allah ya d'ebo ruwan dafa kanshi. nan fa suka rinka masifa ita da k'annenta kaman zasu ari baki. 5pm dai dai Al'ameen ya dawo gida bayan ya biya wajan Ameeransa suka sha hiransu,dan haka ran shi fari kal ya shigo gidan rik'e da brief case d'inshi. Sallama yayi ya shigo su Fa'iza ne kad'ai suka amsa sallaman banda Latifa da sai cika take tana batsewa ga wata uwar harara da take wurga mishi. Ko kulata baiyi ba ya wuce up stairs abinshi. Da saurinta ta tashi tabi shi part d'inshi. Jikinta har rawa yake saboda tsabar masufa da yake cinta. Banko k'ofanta tayi da karfin gaske wanda har yasa shi d'an razana. A fusace yace " meye hakane Lateefa,wani irin rashin hankali ne wannan?" " eh lalle Al'ameen dole kace banida hankali,meye nufinka na gyara wancan part d'in harda canza kayan da suke ciki?" tace tana huci. " aure zanyi " yace a takaice a lokacin da ya nufi hanyan bathroom. Da gudu Lateefa tasha gaban shi " what did u jst saida,aure or wat?" " eh ko haramun ne?" ya jeho mata tambaya yanakallon cikin idonta. K'walan shi taci a masifance tace " wallahi baka isa ba ni kake gayawa zakayi aure? Fizge hannunta yayi daga jikin rigan shi ya shige bathroom ya barta a tsaye sai huci take kaman maciji. Da gudu ta fito tayi part d'inta wayanta ta d'auka ta fara dialing number Aina'u. Ringing 2kawai yayi Aina'u tayi recieving tana " Hajiya ya akayi ne?" " Aina'u ba lafiya"tace murya na rawa. " Subhanallah meya far najiki haka?" "Komai ya warware Aina'u wai yau ni Al'ameen yake cewa zaiyi aure?" A kid'ime Aina'u tace " uban shima yayi kad'an,shi Al'ameen d'in ne har ya bud'i ya gaya miki zaiyi aure?" "duk yanda za'ayi gobe kizo muje wajan boka dan insan halin da nake ciki.dan Allah kizo da wuri Aina'u kinji?"tace cikin marairaicewa. Cikin rarrashi Aina'u tace " karki damu besty zan zo da wuri ai bamu gata zama ba dole mu koma ki k'wantar da hankalinki kema ai kin san aikin boka kaman kaifin wuk'a yake". Sai alokacin ta samu sauk'e wani ajiyan zuciya dan ta san tabbas aikin boka ba wasa nan tace " shikenan sai kin zo goben". 10am a gidan Lateefa yayiwa Aina'u. Lateefa dama tun 8 ta gama shiryawa ta zauna jiran Aina'u yau ba baccin safe. Ba b'ata lokaci suka kama hanya zuwa wajan boka. Suna isowa wajan boka tun kamin suyi mishi bayani ya daka musu tsawa yace " auren nan ba makawa sai anyi shi,sai dai zan taimaka miki ya zamti ta zama hoto a gidan balle ta kai gahaihuwa da kike tsoro.karki damu ki k'wantar da hankalinki in anyi auran da wata 1 sai ki dawo komai zai tafi dai-dai kaman yanda kike buk'ata". Zuciyar Lateefa ta d'anyi sanyi akan bayanan boka,sai dai bata so ace anyi auren ba amma Aina'u tayi warning d'inta tun farko akan cewa ba 'yi mishi musu dan haka ta tsuke bakinta tayi shiru badan taso ba. Kud'i suka kawo mai yawa suka bashi tare da yi mishi sallama suka fita. Akan hanyarsu ta dawowa Lateefa tace " Aina'u inba dan kin hanani yiwa bokan nan musu ba,gaskiya banso ayi auren nan ba.saboda a ganina in an d'aura komai zai iya faruwa". " besty some time ki n cika surutu,ki hak'ura mana tunda yace komai zai tafi dai-dai kaman yanda kik so.kinsan akwai wata k'awar k'wata datavtab'a yiwa boka musu,,hmmmm kinga abinda ya same ta?" A d'an tsorace Lateefa ta juyo ta tambaya " meya same ta besty?" "Hmmm wallahi sai data zama kare ya fita daraja,ta zama abin k'tama cikin mutane.ke in short uwarta ma saida ta guje ta saboda wasu kuraje da suka fito mata duk jikinta ga wani da take,hankalunta ma saida ya zama ba dai-dai ba". Wani irin yawu Lateefa ta had'iye tare da cewa " kice nayi babban sa'a". " offcourse yes sai ki kiyaye sosai". A haka suka iso gida,Aina'u itama ta wuce gidansu bayan Lateefa tayi mata sha tara na arziki kaman yanda ta saba. Yau saturday kuma a yaune duban jama 'a suka shaida d'aurin auren Al'ameen da amaryan shi Ameera . Toh koya zaman nasu zai kasance? [3/24, 6:47 AM] Ummee Yusuf: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA~* 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman yusuf) *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen xBe hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~* *~part fifteen ~* Al'ameen bakin shi yaki rufuwa saboda farinciki,yanda yake rawan kai sai ka zaci auren na farko ne wannan. Bangaren amarya ameera ma hakan take tana can cikin 'yan tsiraru frnds d'inta na makaranta sai cousin sisters d'inta da suka zazzo sai shewa ke tashi a d'akin da suke taro. Lateefa kuwa tunda suka dawo daga wajan boka hankalinta ya gaza k'wanciya,more especially yau.dan tunda ta tashi gabanta yake ta fad'uwa saboda haka take kunshe a can cikin bedroom d'inta ko palour ta kasa fitowa. Amarya tasha nasihohi daga wajan Ummanta da Abbanta kan zamanta kewar aure tsakanin ta da mijinta da abokiyar zamanta,sai kuka take kaman ranta ya fita. Da aka zo fita da ita da k'yar aka b'anb'areta daga jikin Fateema aka sata a mota.nan abokanen ango suke sanar da 'yan matan akwai dinner da za'ayi before akai amarya gidanta. Nan 'yan mata suka hau shiri ciikin farinciki. Ameera sai kuka take a cikin mota ji take a cikin ranta zata ta hak'ura da auren,ta koma ga Ummanta. Ido kawai ya zuba mata yana kallon yanda take kukan kuma ga dukkan alamu bata san yana cikin motan ba. Hannu ya kai ya kamo hannunta na dama,a firgice ta juyo ganin angonta ne yasa ta k'ara sautin kukanta. Jawo ta yayi ya rungume yana sauk'e ajiyar heart saboda kullum suka had'u ba k'aramin yaki da zuciyar shi yake wajan kar ya tab'ata ba. Mutsu mutsu ta fara nason k'wace kanta amma ta kasa. D'ago kai tayi suka had'a ido ko wannensu ido ya canza yayi jawur dashi Ameera nata na kukan da tasha ne Al'ameen kuma na tsaban fitina ce. Kallon d'an k'aramin lips d'inta da yake bala'in k'wad'ayi yake,ganin tak'i barin kukan yasa ya had'e bakinsu ya kama tsotsa kaman ya cire su. Motance ta tsaya a bakin wani lafiyayen beauty saloon amma Al'ameen gaba daya baisan ma inda suke ba har ya fara fita hayyacin shi. Gyaran murya da bilal abokin shi yayi shi ya dawo dashi hayyacin shi ya tuna ashe fa a mota suke kuma basu kad'ai bane. Da k'yar ya sake ta yana maida numfashi tare da zuba mata ido yana murmushi,wasu special feelings yake ji akan yariyan nan shi kan shi bai san adadin son da yake mata ba. Ameera kuwa wannan abinda ya faru tsakanin su yasa wani irin kunyar shi ta gama rufeta sai sunne kai take tana blushing dan tunda take hakan bai tab'a faruwa da ita ba. Leken fuskanta yake yana murmushi yace " woah my prety bride ashe dama kukan bana gaske bane na in........ ko? Bata san lokacin da ta zaro ido waje tana kallon shi jin wannan sharrin da ya mata. Dariya Al'ameen ya k'yalk'yale dashi tare da hure mata ido yace " haba mana prety ko irin kunyan nan na amare babu kika tsare ango da ido haka?" Rasa abinyi tayi ganin kome tayi sai ya musu negetive fassara. Shi kuma he was enjoying every part of the time they spend together but na yau is diffrent ji yake kaman su dawwama haka just d 2 of them. Gyara mata lullubi yayi shima ya gyara rigan shi sannan ya bud'e motan suka fito zuwa cikin saloon d'in. Nan ya barta bayan yayi musu bayanin to do there very best amarya ce,sannan suka wuce shi da bilal dan suje su shirya kamin a gama mata. Kasa gane Ameera nayi saboda yanda ta canza completely cikin wani material golden colour ga havy make up data sha.kanta yasha gyara amma an yafa mata wani hadadden net a kai,poss da high hills duk white tayi bala'in k'yau ta fito a amaryarta sak. Koda Al'ameen ya dawo suka kama hanya,ba k'aramin dauriya ya nemo yasawa zuciyarshi ba na ganin bai bata mata k'walliya ba. Hall ya cika tam su kad'ai ake jira,dan haka ana cewa sun iso d.j ya saki wakan aurensu. Ameera ji tayi kaman ta zura da gudu ta koma bcos bata saba shiga cikin jama'a haka ba ga kuma idon mutane duka a kansu bama kamar ita dan 'yan uwanshi da frnds d'inshi sai yabonta suke suna cewa sai yanzu Al'ameen ya samu mata. Shagali akayi sosai a wurin,anci ansha sannan aka tashi kowa ya tafi cike da farinciki. Lateefa tana k'wance a cikin bedroom d'inta tana wondering me ya hana Al'ameen dawowa har yanzu,sama-sama kunnenta yake jiwo mata gud'a. Firgita tayi ta tashi zaune bcos kaman a mafarki take ji dan haka ta k'ara kasa kunne.aiko wata mai murya cikin 'yan uwan Umma ta rangad'a gud'an dai-dai sun shigo main palour dan haka har tsakiyan kanta taji shi. Zumbur ta mik'e tsaye tare da dafe kirji tana " na shiga uku dama yaune auren nashi?shikenan na kad'e na lalace ". Goge hawayenta tayi tace " wallahi Al'ameen ya d'ebo ruwan dafa kanshi dan wallahi sai auren nan ya zama fitina a rayuwanshi sai yayi nadama dan zan goge sauran son da nake maka nayi maganinka "haka ta cigaba da sumbatu kaman zararriya,sai kaiwa da komowa take a tsakiyan d'akinta. Su kuwa 'yan kawo amarya sai mamaki da jinjina suke sunga gida kaman aljannan duniya,suna zaune sunata hira da bark'wanci anata dariya da shewa harda gud'a wanda Lateefa take ji kaman mashi suke dab'a mata a zuciya. Basu wani jima ba aka maida su,aka bar amarya ita kad'ai sai kamshi take. Jin gidan ya zama shiru ya tabbatarwa Lateefa 'yan kawo amarya sun tafi nan taji wani b'angare na zuciyarta na ingizata taje taci ubanta d'ayan kuma na cewa k'yaleta tukun. Tana zaune a bakin gadonta sai tsaka da warwara take.sallaman Al'ameen ne ya katse mata tunani. Juyowa tayi cike da tsiwa da masifa tana mishi kallon wulakance. Bai kulata ba ya zauna kusa da ita a bakin gadon tare da ajiye mata ledan hannunshi.kamin ya bud'i baki yayi magan ta wawuro ledan ta jefa mishi a jiki,kaji da drinks da suke ciki suka zube a k'asa. " wallah Al'ameen baka isa ka wulakanta ni ba a gidan nan daga kai har wannan 'yar iskan nan da ka kawo gidan". " karki k'ara yunkurin kiran mata ta da makamacin suna irin wannan dan wallahi zan iya miki abinda baki tab'a tsammani ba"yace yana kokarin danne fushinshi. Cike da mamaki take kallon shi tace " Al'ameen ni kake zarewa ido ? wallahi bari kaji kamin kamin abinda kake....." Wucewa yayi ba tare da ya tsaya jin sauran maganganun ta ba dan a yanda yake ji zai iya karyata ne in ya cigaba da sa insa da ita. Part d'in amaryan shi ya bud'e ya shiga tare da sallama,ba kowa a palourn dan haka bedroom d'in ya wuce. Sallama ya k'arayi ko motsi batayi ba balle ta amsa.wani sanyayan ajiyan zuciya ya sauke daya hango ta can karshen gado cikin lulub'i,d'akin yana fitar da wani ni'imantaccen kamshi Murmushi yayi tare da maida k'ofan zai rufe yaji an banko k'ofan da karfin tsiya. A razane ya juya sai ganin Lateefa yayi ta shigo tana dube-dube a d'akin. Ameera itama duk ta rikice ta rasa inda zata sa kanta dan a rayuwa ba abinda ta tsana irin tashin hankali. A guje Lateefa tayi kan Ameera da ta hango can ta mak'ale a karshen gado. Cikin zafin nama Al"ameen ya cafkota yana " meye haka baki da hankali ko Lateefa,me kike shirin aikatawa?" Hayayyak'o mishi tayi " a tsammaninka zaka Iya shigowa da wata karuwa ku k'wana a cikin gidan nan?wallahi sai......". Tagwayen maruka da tasmu a fu Kanta shi ya katse mata masifan da take . Dafe da kuncinta take kallon shi tace " Al'ameen ni ka mara?" "Abinda yafi mari ma zaki gani in dai akan mata tace,ke har kina da bakin kiran wani da mugayrn suna?" Zatayi magana ya fizgota da karfin tsiya duk kokarinta na ganin ta k'wace hannunTa kasawa tayi dan ba k'aramin rik'o ya mata ba. Bai tsaya a ko ina ba sai a main palour,jefata yayi kan kujera ta bugu da karfin gaske sannan ya nunata da yatsa yace " wallahi in kin cika mahaukaciya ki koma d'akin nan ki ga abinda zan miki,banza dabba mara hankali".ya juya ya koma d'akin amaryanshi cikin tsanan halayyarta. Lateefa kasa motsi tayi saboda ta tsorata da yanayin shi gaba d'aya ya canza lokaci 1 kuma tunda take bata tab'a ganin shi cikin irin wannan yanayin ba dan haka tashi tayi ta koma part d'inta da gudu tana kuka. [3/24, 6:47 AM] Ummee Yusuf: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA~* 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman yusuf) *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u no pain~* *part sixteen* Wani irin suya take ji zuciyarta nayi mata yau ita Al'ameen ya wulakanta akan wata? Dialling no Aina'u tayi cikin kuka da tashin hankali take magana " Aina'u kin ganshi can da ita har sun rufe d'aki,ni daman nasan na shiga uku.i'm finished Aina'u pls help me". " Lateefa wats going on,pls ki daina kuka ki gaya min me yake faruwa,waye a d'aki da yarinya kuma wacce yarinyan?Aina'u take jera mata tambayoyin nan a rude sabida yanda take jin k'warta na kuka. Da k'yar ta saita muryanta da ya fara dishewa sannan ta zaiyane mata abinda yake faruwa,tun daga farko har karshe. Ajiyar hrt Aina'u tayi tace " haba Lateefa kiyi hak'uri mana ko kin manta dama boka yace mana ba makawa sai anyi auren,yanzu fa dole ne ki daure ki danne zuciyarki har lokacin da boka ya d'iba mana yayi,nd if u continiou like dis zamu sha wahalan aiwatar da aikin mu in lokacin yazo.nuna musu zakiyi ba ruwanki sannan kija ta ajiki by then komai zai zo mana da sauki hope kin gane". " nagane Aina'u but bazai gane bane abin akwai ciwo".tace tana danna saitin zuciyarta inda take jin zafi kaman ana hura mata wuta. " Lateefa kenan nasani mana tunda nima wanda nake so kullum yana tare da wata amma na daure saboda abinda nake hangowa gaba yafi na yanzu,shiyasa nake so kema ki daure yanda duk abinda zai faru ba wanda zai zarge ki". " i will try my best but waye kike so baki tab'a gaya min ba?" D'an dariya Aina'u tayi tace " zan gaya miki but for now k'wanta ki huta,sai da safe".hanging d'in call d'in tayi ba tare da ta bawa Lateefa daman magana ba. K'wanciyar tayi zuciyarta kaman ya fito take ji wai yau Ameen d'inta ne zai k'wana d'aki 1 da wata kuma a cikin gidanta. Al'ameen yana komawa part d'in Ameera,a tsaye ya same ta a tsakitan palourn sai rarraba ido take. Murmushi ya sakar mata lokacin da yake kulle k'ofan da key. Tana tsaye ya gama ya shigo yazo dab da ita ya kama hannunta suka shiga cikin bedroom ya zaunar da ita a bakin gado,shi kuma ya durk'usa a gabanta yana lek'en fuskanta. K'ara jan mayafin tayi ta rufe fuskanta. Murmushi yayi yasa hannu ya bud'e mayafin tayi saurin rintse idonta,matsowa yayi yayi kissing d'in saman idonta. Waro su tayi ta sauke su a kanshi suna had'a ido tasa hannayenta ta rufe fuskanta tana murmushi. " *AMEERA*"ya k'ira sunanta kaman mai rad'a,bata amsa ba kuma bata bud'e fuskanta ba. " ki k'wantar da hankalinki kar wannan abinda ya faru ya dame ki bcos tana da matsalan jinnu yanzu haka na bata magani tayi bacci,dan duk lokacin da ya tashi haka muke fama da ita"yace yana zama kusa da ita. Batace komai ba amma har cikin zuciyarta ta tausayawa Lateefa kuma at d same time ta samu relief na cewa ashe ba haka halinta yake ba,da har ta fara tunanin ya zamansu zai kasance. Tashi yayi ya shiga bathroom d'inta yayi alwala ya fito yace itama taje tayi ta fito suyi sallah nafila. Batayi musu ba itama ta shiga ta d'auro alwalan ta fito. Shi yaja su sukayi raka'a 2 sannan ya sallame,ya dad'e yana k'wararo musu addu'an zaman lafiya tana amsawa da ameen sannan suka shafa. Tashi yayi ya fita palour sai gashi ya shigo da ledodi har 2 ya ajiye a tsakiyan rug carpet da yake shimfid'e a tsakiyan d'akin. Fita ya k'arayi ya shigo dasu plates cups nd knife akan wani k'aramin tray ya ajiye tare da jawo ledodin ya juye musu gasassun kajin da suke ciki ya yanyanka sannan ya d'ago kai ya kalleta ta wani ta wani takure waje d'aya ko kallon inda yake ma batayi. "Bismillah sauko muci nasan yunwa kike ji" yace still idosa akanta. Girgiza kai tayi a hankali tace " um-um na koshi" Cike da tsokana yace " kin isa ma kice kin koshi,bayan tundazu naga kina ta bin late din da kallo ta kasan ido kina had'iyan yawu.zo kici yarinya ki bar yin fulako". Waro ido tayi tana kallonshi kaman zatayi kuka,fisabillilahi in banda sharrin Al'ameen yaushe ta kallima inda yake bare ta had'iyi yawu?ita dai kam ta kasa sabawa da halin nan na Al'ameen komai tayi sai ya fassara shi nagaetive. Sunkuyar da kai k'asa tayi tare da yin rau-rau da ido kaman zatayi kuka. Jawota jikinsa yayi yana dariya yace " noo my baby don't cry nine ko?sorry na daina". Gutsuro naman yayi ya sa mata a baki yana rarrashi tare da lallab'ata,tun tana nonnokewa har ta sake taci d'an dsyawa bcos ba laifi tana jin yunwan .cup ya cika fresh milk ya bata ta sha sannan ya k'yaleta. Zagewa yayi shima ya cika cikinsa dan rabon shi da abinci tun safe,hidimomi basu barshi ya samu zama ba balle ya tuna da abinci.saida ya gama sannan ya tattara wajan ya fad'a bathroom yayi wanka ya fito daga shi sai 3quater da singlet farare tas. Tana zaune a inda ya barta ta takure cikin hijabin da tayi sallah,zuwa yayi ta bayanta ya rugume ta tare da bata wani hot kiss a wuyanta sannan yace " tashi kije kiyi wanka kema zaki fi jin dad'in bacci". Murya na cracking tace " a'a ba sai nayi wanka ba zan iya k'wanciya a haka......"bai jira ta karasa ba ya shure ta sai cikin bathroom ya dire ta. " zakiyi ko inyi miki da kaina?" Ba shiri tace " ba sai kamin ba wallahi zanyi da kaina ". Fita yayi yana mata dariya " yace matsoraciya kawai". Bata dad'e ba ta fito cikin wani zurmumemen hijab da tayi sallah dashi, Shi kuma yana ta aikin feshe wata arniyan red night gown da performes masu d'an karan kamshi. Juyowa yayi suka had'a ido tayi saurin sauke nata k'asa tasiwa yayi da rigan a hannun shi yazo gabanta yace " meye haka Ameera da hijabin zaki k'wanta?" Gyad'a kai kawai tayi ba tare da ta d'ago ba " ga riga nan kije ki canza ko kuma inzo in canza miki da kaina". Ba musu ta karb'a tayi bathroom a ranta kuma tana jin ba dad'i dan gani take ya takura mata dayawa shi ko kunya baya ji. Kallon gown d'in take baki sake ganinta 'yar k'arama da ita dan da k'yar ya rufe mata cinya kuma ba shi da maraba da net cos ba abinda zai rufe mata yana show sosai. Haka ta daure ta saka gudun kar yazo yasa mata da kanshi kaman yanda yace. Gaban dogon mirrow da yake cikin bathroom d'in ta tsaya kallon kanta,ganin she's half naked yasa ta nemi wuri ta zauna dan bazata iya fita gaban shi haka ba. Al'ameen yana zaune zama jiranta shiru har zuwa 15mins,hakan yasa ya tashi ya bita,cikin sa'a ya samu k'ofan a bud'e bata saka key ta ciki ba. Tura k'ofan yayi ya shiga ciki,tana ganin shigowar shi ta fara kokarin rufe jikinta da hijabin da ta cire. Zuwa yayi kusa da ita ya k'wace hijabin yayi wurgi dashi. Wani wahalallen yawu ya had'iye saboda ganin had'add'en surarta a waje dan bai tab'a sanin haka take da sura mai d'aukan hankali ba sai yau saboda kullum cikin hijab take. Cikin sassarfa yazo ya rungumeta tare da bin jikinta da hot kisses gaba daya a juye ya zama wani mutum.daban kaman ba Al'ameen da ta sani ba. Ameera duk ta rud'e ta fara hawaye dama daurewa take. Cak ya d'agata yayi kan bed da ita ya k'wantar shima ya k'wanta a gefenta tare da jawota jikinshi ya ruungume, sak'onni masu wuyar fassara ya shuga aika mata da zafi da zafi. Daga nan nima nayi waje sai dai muce asha amarci lafiya *AMEERA*. [3/24, 6:47 AM] Ummee Yusuf: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA~* 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman yusuf) *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u no pain~* *part seventeen* Har kusan asuba Al'ameen bai samu bacci ba sai kallon fuskan Ameera da yayi kaca-kaca da hawaye yake yi cike da zallan nishad'i dan sai yau yasan cewa mata suna suka tara,saboda bai tab'a samun natsuwa haka ba tare da Lateefa kuma sai yau ya k'ara tabbatar da zargin shi na cewa Lateefa bata kawo mishi budurci gidan shi ba.yayi shiru ne dai kawai dan yana sonta yayin da ita kuma ta d'auka tushe-tushen da ta kashe mak'ud'an kud'i a kaine sukayi tasiri. Dak'yar ya samu bacci mai dad'i ya d'auke shi. 6:30am ya farka daga bacci mai nauyi daya d'auke shi,a gurgije ya fad'a bathroom yayi wanka tare da d'auro alwala ya fito ya zura farar jallabiya. Komawa yayi kan gadon inda Ameera take baccin wahala,gefen fuskanta yake shafa a hankali.ture hannun tayi tare da turo baki gaba tacigaba da baccinta. Murmushi yayi ya kawo bakinshi saitin kunnenta ya hura mata iska,magana ta fara cikin bacci tana " Fateema meye haka,Umma kin ganta ko?" Kamo bakin da ta turo gaba cike da shagwab'a yayi ya d'an ciza. Bud'e ido tayi da sauri ta sauke shi a kanshi da ya tsura mata ido yana murmushi. Waro idon tayi sosai tana kallonshi tare da mamakin me ya kawo shi gidansu,can ta tuna ashe fa jiya ba gidansu ta k'wana ba. tana tuna abinda ya faru tsakaninsu ba shiri ta rintse ido dan wani irin kunyanshi taji yana shigarta. " tashi kiyi sallah prety " yace yana kokarin d'agata. 'Yar k'ara ta saki jin wani rad'ad'i a kasanta ga cinyoyinta kaman wacce tayi tsallen k'wad'o. A rud'e yake mata sannu,tare da kamata har zuwa cikin bathroom ya had'a mata ruwan dumi sannan ya barta ya fito sannan ya tada sallah. Yana fita ta shiga cikin ruwan ta k'wanta lamo tana jin dad'in yanda yake gasa mata jiki, Saida taji ruwan ya fara sanyi sannan ta had'a sabo tayi wanka tare da alwala ta fito. Yana zaune yana azkar d'inshi ta fito,murmushi ya sakar mata mai d'auke da sakonni kala-kala Saurin kawar da kanta tayi,da sauri ta nufi kan sallayan da ya shimfid'a mata ta tayar da sallah. Tana idarwa ta matso kusa dashi kanta a kasa tace " ina k'wana ". Jawota jikinshi yayi ya rugume tare da manna mata peck sannan ya rad'a mata kunne " haka ake gaisuwa my prety nd thank u so much for d gift Allah ya mii albarka". Shiru tayi ta manne a kirjinshi dan bata so ta d'ago da kanta su had'a ido. D'agata yayi suka koma kan gado ya ja musu bargo,ya shiga wasa da ita. Gaba d'aya Ameera ta gama tsurewa dan bata manta wahalan da tasha jiya ba,saidai baiyi abinda take tsoro ba yaja musu bargo suka koma bacci. 11:20am suka farka,rad'a mata yayi a kunne " tashi muje muyi wanka".da sauri ta girgiza kai tana k'ara shigewa bargo. Bata ankara ba taji ta a sama,wutsil-wutsil ta fara da k'afa tare da magiyan ya sauketa amma bai direta ba sai cikin bathtube. Gaba d'aya kunya ya hanata motsi yayin dashi kuma ko ajikinshi saima fitina da ya isheta shi. Haka suka gama wanka suka fito suka shirya,batayi wani make up ba just powder ta shafa sai wet lips da tasa amma tayi k'yau cikin riga da skirt da tasa na atamfa blue nd white. Riko hannunta yayi suka fito palourn ta suka tarar an cika musu kan table da kayan breakfast. Kujera yaja ya zauna,itama taja na kusa dashi zata zauna yayi saurin riketa yace " me zakiyi?" "Zama zanyi" ta bashi amsa a takaice. "A ina " ya kara tambaya,kujeran ta nuna mishi da hannu. Jawota yayi ta fad'a jikinshi,ya sunkuya ya bata peck a goshi sannan ya gyara mata zama akan cinyanshi yace " as frm today ga wajan zamanki nan". Batayi magana ba sai murmushi da tayi Bud'e warmers d'in yayi d'aya bayan d'aya yana lek'en fuskanta yace " me zan zuba miki". " kowanne ma ka zuba zanci". Shi ya zuba musu abincin a plate 1,yana bata a baki shima yana ci har suka kammala sannan suka dawo kan cushions d'in palourn suka zauna ya kunna musu kayan kallo. D'ora kanshi yayi akan cinyanta suna kallon arewa 24,wata masifaffiya aka nuno tana ta bala'i a cikin shirin da suke haskawa. Ganin matan yasa ya tuna da Lateefa koya ta k'wana oho mata. Rungumo cikinta yayi daga k'wancen yace " prety bari inje mu gaisa da yayarki". " inka je kace nima ina gaishe ta "tace tana kallon gefe dan da gaske taji wani iri a zuciyarta. Saida yayi pecking d'in goshinta sannan yayi hanyan fita. Kallon shi take tana murmushi bata san tayi nisa a sonshi haka ba sai yau, har ya kai k'ofa kaman yasan tana kallonshi ya juyo suka had'a ido da sauri ta d'auke idonta tana kallon gefe tare da murmushi. Kamshin turaren shi taji a kusa da ita, ta juyo da sauri ta ganshi a gefenta yana murmushi yace " na dawo dan naga baki yarda da tafiyata ba". Da gudu ta tashi tayi bedroom ta kulle tana dariya,shima dariyan gayi ya fice daga part d'inta cike da nishad'i. Yana zuwa part d'in Lateefa ya nemi wannan farincikin ya rasa saima fargban ya zasu k'washe da ita, abu d'aya yasa a ranshi ba zaiyi tolarating rashin hankalinta ba. Sallama yayi ya shigo palourn ya tarar suna hira da k'annenta,sai dai suna ganin shi suka mik'e bayan sun gaishe shi suka fita zuwa nasu part d'in. Cikin fara'a ta tare shi tana ango kasha kamshi. Kallon mamaki ya bita dashi na yanda ta rikid'e one time kaman ba ita bace jiya suka rabu b'aram- b'aram ba. " mesa ka fito da sassafen nan ka bar min k'anwata ita kad'ai"tace tana murmushi. Kallon aggon d'akinta yayi yaga 12:30pm take cewa safe?koda yake ya gane magana ta fad'a mishi a fakaice. Bai kula da magan ba dan yaji dad'in canzawarta dan haka zama yayi a d'akin suna hira sama-sama har aka kira sallahn azahar yayi alwala acikin bathroom d'inta sannan ya fita zuwa masallaci dan gabatar da sallah azahar. Yana fita ta k'washe da dariya tace " zaka gane kurenkane yaro dan sai na gana muku bak'ar *UKUBA*a gidan nan daga kai har k'aramar karuwar da kawo cikin gidan nan". [3/24, 6:47 AM] Ummee Yusuf: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA~* 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman yusuf) *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u no pain~* *part eighteen* Part d'in k'annenta ta nufa dan fad'a musu abinda yake faruwa cos basu san da maganan auren ba. Knocking ta fara jin k'ofan nasu a rufe. Su kuma a wannan lokacin suna kan gado a tub'e suke tsirara suna aikata masha'ansu da suka saba. Buggun k'ofan ne ya dawo dau cikin haiyacinsu,da k'yar suka suka rabu Shamsiya ta fad'a bathroom dan kar Lateefa ta fahimci wani abu. Fa'iza kuma kayanta ta mayar sannan tazo ta bud'e k'ofan tana kikiro murmushin dole tace..." Aunyty kece da kanki?ai kin k'ira waya zamu zo mu same ki". Bata bata amsa ba tabi ta gefenta ta shiga ciki ta nemi kujera ta zauna sannan ta kai dubanta ga Fa'iza da ta kasa zama tace..." ina Shamsiyya?" "Ta shiga wanka". " and u wat happen to ur eyes?naga sunyi ja".Lateefa ta tambaya tare da kafe ta da ido. Cikin in-ina ta amsa da cewa..." ammmm b...bacci na fara Aunty bugun k'fan ne ya tashe ni". "Ok ko kunsan cewa Al'ameen yayi amarya?" A zabure Fa'iza ta kunduma ashar sannan tace..."amarya fa kika ce Aunty,ya akayi haka ta faru bamu sani ba?wallahi ubanta zamuci a gidan nan,wai Mama ta sani kuwa?" " hmmm ban gaya mata ba dan nima bai gaya min ba,jiya ina zaune naji an shigo da ita".ta bata amsa. Shamsiyya ta fito daga bathroom d'aure da towel tace..."dama na gaya miki tun lokacin da ake gyara wancan part d’in". Murmushi Lateefa tayi ganiñ yanda k'annenta suka tada hankalinsu tace..."ku kwantar da hankalinku dan na gama shiri na,inaso ku zuba ido ku sha kallo kuma kar kuna wani tashin hankali ko canza fuska just kuyi abinda nace hope kun gane?" " shikenan Aunty tunda haka kike buk'ata amma da kin k'yale mu dasu sai sun gane shayi ruwa ne"tace tana huci. " don't worry komai zai tafi tafi yanda ya kamata,yanzu zan k'ira Mama mu tattauna b4 inje gida in same ta"nan suka cigaba da kulla makircin akan Al'ameen da Ameera. Al'ameen yana fita daga masallaci direct gidan iyayen shi ya nufa. Alhaji da Hajiya suna zaune a palour suna hiran yanda biki ya kasance,sallamar Al'ameen ne ya katse su. Shigowa yayi ciki bayan sun amsa mishi, neman guri yayi a kasa kusa da k'afan Hajiya ya zauna sanna ya gaishe su. Cike da farinciki suka amsa ganin wata natsuwa da farinciki da suka gani kan fuskan d'an autan nasu. "Ya naga gidan ba kowane?"ya tambaya yana k'arewa gidan kallo. " tun 11am 'yan katsina suka koma,munso su k'ara k'wana amma suka k'i saboda auren 'yar kawunka baffa da za'ayi next week" Hajiya ta bashi amsa. B'ata fuska yayi yace..."wai harda tsohuwan nan suka tafi itama bata tsaya taga amarya ba?" Alhaji yayu dariya yace..." ai itace ta hura wutan tafiya sauran ma suka bi bayanta". K'ara shagwab'e fuska yayi zaiyi magana,Hajiya ta katse shi ta hanyan cewa..." Kai dai baka girma, ina amarya?" Nan da nan fara'a ya cika fuskar shi yace..." tanan nan lafiya" Nan hira ta b'arke tsakáninsu kan yanda bikin ya kasance har zuwa la'asar sannan suka fito zuwa masallaci shida Alhaji dan gabatar da farali. Suna idar da sallah gida ya nufa yana tunanin ya barta ita kad'ai. Bayan tafiyan shi Fateema da sauran frnds d'inta suka zo suka taya ta yini suna mata tsiya,sai kusan 4 suka koma gida. Suna tafiya ta shiga bathroom tayi wanka ta fito daga ita sai bath robe wanda kpo cinyarta bai gama rufewa ba. Da yake tasan gidan bakowa yasa ta saki ranta ta fara shirinta cikin k'wanciyar hankali. Zama tayi a gaban mirrow tayi shafe-shafenta sannan taje gaban sip d'inta ta ciro inner wears ta fara sawa. Zame bathrobe d'in ta fara kokuwan saka brezia amma ta kasa, kaman zatayi kuka take ta trying saboda ko a gida Fateema ce mai taimakata kullum. Kaman daga sama taji hannun mutum ta bayanta ya had'a mata mata abinda ta kasa. A razane ta juyo sai ganin shi tayi a tsaye yana mata dariya. Tsaban rikicewa rasa abinyi tayi,durkushewa tayi a wajan ta takure waje guda. Dariya Al'ameen yake harda rik'e ciki yace..." dama ganina ne yasa kike shiga wanka da hijab? Tohyau Allah yau ya kamaki cos akan idona kikayi komai nd dis kunya zanyi maganinta"yace tare da zuwa gaban sip d'inta ya ciro mata wani gown na material maroon mai adon black flowers a jiki ya ajiye mata akan gado ya fita zuwa palour ya barta dan taji dad'in shiryawa. Yana fita ta sauk'e wani ajiyan zuciya sannan tacigaba da shiryawanta,perfumes masu sanyin kamshi tayi amfani dasu wajan feshe jikinta dasu.bata saka d'an k'walin kayan ba sai wani black veil da tayi rolling kanta dashi sannan ta nufo palourn tana taku a hankali cikin natsuwa. Zuba mata ido har ta k'araso gefe shi ta zauna ba tare da tace komai ba,shine yace..." i'm sorry my baby na tafi na barki ke kad'ai ko?" Murmushi tayi tace" a'a su Fateema sunzo bayan fitanka,tare muka yini dasu dan basu dade da tafiya ba". K'wantar da ita yayi akan cinyan shi ya zame mata veil d'in yana wasa da gashin kanta yace" ni ina can na wuni da tunanin na barki ke d'aya ashe ke wunin dad'i ma kikayi". Dariya tayi tare da gyara k'wanciyarta a jikin shi suka cigaba da hiran su na masoya har aka k'ira sallahn magrib sannan suka mik'e dan gabatar da farali. Bai shigo cikin gida ba saida yayi sallahn isha'i sannan ya shigo ya sameta ta canza k'walliyarta,doguwar rigar shadda dark blue yasha aiki har kasa ga d'an k'walin tayi mishi irin d'aurin nan mai steps ya matukar yi mata k'yau. Tana zaune a kan kujera ya shigo ya karaso gabanta ya tsuguna tare da rik'o hannayenta yayi kissing sannan yace " irin wannan make up haka ai sai kisa in manta kaina,kin ganki kuwa kaman mai zuwa beauty contents ". Waro ido tayi tace " haba mana zaka fara ko?" "Fad'an gaskiya ba"yace yana dariya. Hannunta ya kama zuwa kan dinning table dan cin abinci,kaman yanda sukayi breakfast yanzu ma haka akan cinyanshi ya d'aurata ta zaunasuka rink'a ciyar da juna a baki har suka gama. " zoki rakani inyi wanka "yace yana mik'a Mak'e kafad'a tayi tare da yin kasa da kai. Lek'o fuskanta yayi yace " zaki rakani ne ko kuma.....?" "Ehh....ehh zzzzan raka ka"ta amsa muryanta yana cracking Dariyan mugunta yayi cos ya san ya gama tsorata ta,sannan ya shige ya barta a tsaye. Kaman bazata je ba amma tasan in bata je bama zai iya zuwa ya tafi da ita yasa ta fara jan k'afa a hankali har zuwa bakin k'ofan bathroom d'in ta tsaya. Shahada tayi da ta gaji da tsayuwa ta bud'e ta shiga ciki,jikin k'ofan ta jingina ta tsaya kanta a kasa. Tana d'agowa sukayi 4eyes dashi yana k'wance cikin bathtube,da hannu ya mata alaman ta karaso. A ranta take mita ,wai mesa baya ganewa tana kunyan shine? "Oya come on babyna ke nake jira" ya katse mata zancen zuci da take. Bata da wani option daya wuce na zuwa. Da dabara ya rinka janta har tasaki jiki sosai dashi,sun kai 1gud hour suna wankan sannan suka fito. Shi ya zab'a mata night gown da zata saka,nan sukayi shirin k'wanciya suka k'wanta ya rungumeta sosai kaman wani zai kwace mishi ita sukayi baccinsu mai dad'i. Haka suka yi ta zuba love kaman su lashe juna dan yanda Al'meen yake nuna mata luv yasa itama ta sake sosai dashi suka ci amarcinsu har 7 days da zaiyi a d'akinta suka kare,kuma a yau ne zai koma d'akin Lateefa. [3/24, 6:47 AM] Ummee Yusuf: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA~* 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman yusuf) *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u no pain~* *part nineteen* Ameera tana zaune a palourn ta bayan tayi sallahn isha'i duk ta rasa me yake mata dad'i. Al'ameen yana dawowa daga masallaci direct part d'in Lateefa ya wuce,ya samu ta baje a palournta tana waya,tana ganinshi ta katse wayan tayi tare da K'irk'iro murmushi tanayi mishi barka da zuwa. Bai zauna ba yace ta fito main palour yana son magana dasu,ta amsa da toh sannan ya fita zuwa part d'in Ameera. Yana shiga parlourn yaganta ta zuba tagumi da hannu 2,tsayawa yayi yana kallonta yana jin ba dad'i a zuciyar shi dan yasan abinda yake ji a zuciyar shi itama shi take ji,gashi kuma ya sabar mata da abubuwa da yawa wanda yasan dole yanzu su dame ta. Cire mata tagumin yayi lokacin da yake zama kusa da ita. A d'an firgice ta juyo ganin shine yasa ta d'anyi dariya tace " yaushe ka shigo ne?" " tayaya zakiji shigowata while u re lost in ur thought,wai tunanin me kike ne haka?" " nothing just bana jin dad'ine".ta amsa mishi cikin dauriya. Jawota yayi jikinshi yayi huging d'inta sannan ya fara rad'a mata magana cikin kunnenta yace..." am sorry Babyna nasan abinda yake damunki but am asuring u bai kai rabin yanda nake ji ba cos i will miss u badly.sai dai ina so ki k'wantar da hankalinki dan after 2days zamu kasance tare kinji?" Gyad'a kai kawai take dan kukan da take ba zai barta tayi magana ba.hannu yasa yana share mata fuskanta,sannan ya d'ago fuskanta suka had'a ido,murmushi yayi mata itama ta mayar mishi. Kissing d'inta ya shiga yi sosai,bai barta ba saida yaga ta samu natsuwa sannan yace ta tashi su fita main palour zaiyi magana dasu. Yana rik'e da hannunta suka fito zuwa palour,nan suka tarar da Lateefa zaune tana jiransu. Ameera da Lateefa suna had'a ido kowacce zuciyarta saisa ya buga,bama kaman Lateefa dan k'yaun Ameera shi ya razanata,ashe rannan kallon tsoro tayi mata. Ita kuma Ameera ganin Lateefa goggayiyar mata kuma wayayyayiya shi ya bata tsoro,tayaya zata iya kishi da ita? Gyaran murya Al'ameen yayi bayan sun zauna sannan ya fara magana yace...Lateefa dake zan fara tunda kece gaba da ita muna tare dake yau 14years kenen dan haka kinfi kowa sanin gidanki dani kaina kuma wannan..."ya nuna Ameera dake zaune tana wasa da wani zoben gold dake d'an yatsanta yace.... " k'wanwarki ce kuma bak'uwa,ina son kija girmanki ki rik'eta da amana kuma kijata a jiki.ke kuma Ameera ina son ki bata girmanta ku zauna lafiya tunda kinga ni ba zamaunin gida bane,soo in kin bata had'in kai kuka zauna lafiya jin dad'inku ne dukkan ku,nima hankalina zai k'wanta". Gyara zamanta Lateefa tayi tana tab'e baki tace..."muna godiya my Ameen kuma ka taya mu da addu'a Allah ya had'a kanmu muma zamuyi iya k'okarinmu na ganin bamu baka kunya ba". Murmushi yake cikin jin dad'i dan wani irin nishad'i yake ji cos baiyi zaton haka daga Lateefa ba,kallon gefen da Ameera take yayi sannan yace" kina da magana ne babyna?" Girgiza kai tayi da sauri ba tare da ta d'ago kai ba. "Alhamdullilah naji dad'in haka wannan ya nuna min tun yanzu zaman lafiya ya samu a cikin gidan nan,now sai kuyi shawara k'wana nawa-nawa zaku yanke?" " ni a ganina k'wana 2 yayi koya kika ce Babyn angonta"Lateefa tace tana hararan Ameera cos tunda Al'ameen yace mata babyna ta kasa controling kanta. Ameera ko tunda ta shigo kanta a k'asa yake dan haka bata san ma tanayi ba. Yanzu ma da Al'ameen ya nemi ta fad'i ra'ayinta cewa tayi duk abinda sukayi dai-daine. " toh ni zan shiga in k'wanta sai da safenku "tashi tayi ta nufi part d'inta ba tare da ta tsaya taji amsan su ba. Da ido ya rakata har ta shige sannan ya dawo da duban shi kan Ameera da har yanzu kanta yana k'asa. Zuwa yayi ya tsugunawa a gabanta yace..."ya dai babyna?" Ajiyan zuciya ta sauk'e tana dubansa tare da k'ak'alo murmushi. Cike da damuwa yace..."bana son in ganki cikin damuwa pls idan ba ki saki ranki ba bazan iya tafiya in barki ba". Gefen fuskan shi ta shafa tace " ba damuwace a raina ba just ina tunanin yanda zanyi 2days without u,but dont worry ya wuce na daina"tace tana murmushi. "Tashi muje in rakaki d'aki". Tashi tayi suna tafiya kaman basa so har suka shigo palourn ta,rungumeta yayi tsam kaman Zai maida ta ciki yana shinshina wuyanta,daga nan kuma maganan ya sauya dan kissing d'inta yake tare da romancin d'inta da zafi-zafi. Ture shi tayi da taga yana shirin zarcewa.sake ta yayi suna maida numfashi dak'yar. Juyawa yayi da sauri ya fita ko sai da safe bai tsayayi mata ba dan yasan in ya cigaba da tsayuwa ba zai iya controling kanshi ba Yana fita ta zube a wajan tana kuka zuciyarta a cunkuse da kishi a ranta tana dole Lateefa ta musu hauka ranan da a kawota dan duk macen data d'and'ani zama da miji irin Al'ameen dole ta guji duk wani abinda zai rabasu koda na minti1 ne. Mikewa tayi ta hau kan gado ta k'wanta taji duk pillown da ta d'aura kanta akai baya mata dad'i dan rabonta da k'wanciya akan pillow tun tana gida,juyi ta rink'a yi akan gadon dak'yar ta samu bacci ya d'auketa. Al'ameen part d'inshi ya nufa yana tsammanin zai samu Lateefa a can amma yaga wayam bata nan dan haka bathroom ya fad'a da niyan wanka amma sai yaji ba dad'i saboda cikin k'wanaki da sukayi tare da Ameera ya saba da abubuwa dayawa wanda da bai san dasu ba a auren su da Lateefa. A daddafe yayi wankan ya fito still bata zo ba har ya shirya cikin white pyjames d'inshi ya fito ya nufi part d'in Lateefa amma ga mamakin shi yaji k'*ofan ta a bud'e . Bud'ewa yayi ya shiga sannan ya mayar da k'ofan ya rufe. Tana k'wance suna waya ita da Salees d'inta taji motsi a palourn ta dan haka cikin sauri ta katse wayan ta tura shi karkashin pillow ta runtse ido kaman me bacci. Ya dad'e tsaye a kanta yaga alama baccin take da gaske. Hawa gadon tare da shigewa cikin duvet da ta rufu dashi,rungumeta yace " har kinyi bacci?" Mik'a tayi (irin ita mai baccin nan). Bud'e ido tayi a hankali tace "my Ameen ka shigone,ina amarya?" "Kema kinsan yau Ameen nakine meye na pretending"yace yan k'ara rugumeta. " no ba pretending bane just kaima kasan yanda ciwon kaina yake in ya tashi but na sha magani,let me sleep for while i wiil b alright"tace tan yamutsa fuska tare da lumshe ido. Wani kululun bakinciki ne ya tokare mishi mak'ok'ora dan ya fara gajiya da wannan wanda halinta wanda bata tashi rashin lafiyanta sai taga yazo gare ta.ba dan ya kasance mai yaki da zuciyarshi ba da tuni ya fad'a halaka. Cike da jin haushin kanshi ya fice daga part d'inta yayi nashi tare da alkawarin ba zai k'ara waiwayanta ba tunda Allah ya mishi canji. Yana k'wance a kan lallausar gadon shi sai juyi yake ya kasa bacci Ameera kawai yake bukata a wannan lokacin. Kasa daurewa yayi ya jawo wayanshi dage side drower yayi dialing no Ameera. [3/24, 6:47 AM] Ummee Yusuf: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA~* 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman yusuf) ✍✍✍✍✍✍✍ *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION~* ✍✍✍✍✍✍✍ *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u no pain~*❄ *part twenty* Ameera tana cikin bacci ta rinka jin ringin d'in wayarta sama-sama,dak'yar take iya bud'e ido saboda nauyin da sukayi mata. A take ta nemi baccin ta rasa sakamakon sunan Al'ameen da tagani yana yawo akan screen d'in wayan. Sallama tayi mishi cikin muryan jan hankali bayan tayi recieving. Wani sanyi yaji yana ratsa zuciyar shi har ya nemi bacin ran da Lateefa ta sa mishi ya rasa. Tana jin shi ta cikin wayan ya sauke ajiyan zuciya sannan yace..." sorry Babyna kina bacci na tashe kiko?" " bakayi bacci ba har yanzu"ta tambaye shi cikin mamakin ya akayi Lateefa ta bar shi har ya kirata a waya a wannan lokaci? " tunaninki ne ya hana ni bacci,I'm really missing u Babyna wanda har nake jin ba zan iya controling d'in kaina ba.i'm coming to ur room right now".yace mata in a serious tone. Duk da taji dad'in kalaman shi amma hakan bai hana ta Saurin katse ba tace... " no Yayana kayi hak'uri kada kazo ka manta d'azu kai kake gaya min cewa inyi hak'uri zamu rink'a kasancewa bayan ko wani k'wana 2,kuma in kazo yanzu ita kuma kaga ai bamu k'yauta mata ba" a zuciyar shi yake cewa da kinsan wacece Lateefa da baki bakin kiba...... Muryarta ne ya sake katse shi a karo na 2 tace..." kuma bana son ka kasance cikin masu shanyayen jiki ranar gobe k'iyama". Jikin shine yayi mugun sanyi jin kalamanta kuma ya godewa Allah da ya bashi mace mai natsuwa kamarta cos he know Ameera is a blessing frm Allah.dan haka yace..." hakane Babyna nagode da kika tunatar dani gaskiya i will try my best wajan k'watanta adalci a tsakaninku insha Allah,nan suka kama hira kaman ba dare ba sun dad'e kamin suka hak'ura suka k'wanta bacci. Da washe gari ya kasance monday ne dan haka Al'ameen tun 8 na safe ya shirya fita zai office,ko kallon kayan breakfast dake jere akan table baiyi ba ya wuce part d'in Ameera a lokacin kuma Lateefa tana can tana baccin asara da ta saba. Yana shiga part d'int Ameera ya same ta fes taci k'walliya da wani material peach clour riga da skirt sun zauna das a jikinta saboda dinkin yabi jikinta tayi matuk'ar k'yau duk da ba wani k'waliya tayi ba. Tana ganin shi ta tashi ta tare shi da murnanta dan ba k'arya tayi missing d'in mijinta. Ajiye brief case d'in hannunshi yayi tare da bud'a mata bud'e hannayen shi,da gudu tazo ta fad'a kirjinshi suka rungume juna suna dariya.d'ago hab'anta yayi suna kallon juna yace.." i missed u so much Babyna..." K'wantar da kanta tayi akan kirjin tana shakan daddad'an kamshinsa tace..."ina k'wana my one". D'agota yayi tare da bata peck a goshi sannan yace..." kin tashi lafiya Babyna?" " lafiya lau,ya na ganka da jaka ko yau zaka fara fita aiki ne?" " yes yau zan fara kuma in na tafi sai 6:00pm" yace mata cikin tsokana. Shagwab'e fuska tayi kaman zatayi kuka tace..." wai gasikya yayi yawa ni dai ka rage time d'in ko in bika office d'in"tace cikin shagwab'a har da dire-diren k'afa. Shiko kallonta ya tsayayi cike da sha'awa dan yana matukar son mace mai shagwab'a.kasa jurewa yayi saida yayi kissing d'inta sosai sannan ya saketa ya juya zai fita ta tsayar dashi ta hanyan tambayan shi " kayi breakfast kuwa?" Tsayawa yayi ya dawo da baya yace...."dont worry in naje office zan sha tea acan". Bata bashi amsa ba ta kama hannun shi har zuwa kan table ta zaunar dashi,nan da nan ta zuba mishi chips da fried egg a plate sannan ta had'a mishi tea mai kauri tace .." bismilla". Tunda ta fara mishi hidima yake binta da wani irin kallo mai cike da zallan so,yaushe rabon da ya samu kulawa a wajan Lateefa haka ita da kullum tana bacci yake fita office ba ruwanta da yaci ko bai ci ba. Ameera bata barshi ba saida ya cika tumbinsa sannan ta rako shi har bakin k'ofan palourn ta tace..."Allah ya bada sa'a ya kare ka daga dukan abin k'i". Hancinta yaja yana murmushi yace" ameen Babyna Allah yayi miki albarka"zuciyar shi fari sol kuma cike da jin dad'in addu'ointa ya fita zuwa office,zai iya cewa tunda yake da Lateefa bata tab'a yi mishi irin wannan addu'an ba shiyasa yake jinta daban a cikin zuciyar shi gata dai yarinya ce k'arama amma abinda take wajan kula da miji tafi manyan mata dayawa. Lateefa duk ta fita hayyacinta saboda yanda taga Al'amern ya susuce akan Ameera,duk ta rame ji take kaman ta k'ona su kowa ya huta amma in ta tuna da maganan bokanta sai hankalinta ya d'an k'wanta saboda ta yarda da aikin shi. A daddafe tayi wata 1da boka ya basu,lokaci yanayi suka hanya ita da Aina'u sai gidan boka. " boka gamu nan mun dawo dai-dai lokacin da ka bamu"Aina'u ce takewa boka bayani yayin da Lateefa kuma tana zaune ta k'osa taji mai boka zaice. Boka saida yayi wasu tsurkullen shi sannan ya d'ago kai yana kallonsu yace..."aikinki na yau ba mai sauki ne bane kaman da saboda yariyan tana da ibada sosai ba wani aljani da zai iya tunkarar ta a halin yanzu". Gumi Lateefa ta goge zuciyarta na bugawa da karfi jin abinda boka yace,cikin matuk'ar tashin hankali tace...." na shiga uku boka da kai kad'ai na dogara yanzu ya zanyi?" (waiyazubillah) Dariya boka ya kece dashi sannan yace..." bukarar ki zata biya amma wannan karpn saida taimakon ki" Cikin sauri ta katse shi tare da cewa..." ka gaya min komenene zanyi boka". Wani bakin kulli ya mik'o mata yace..." ga wannan ki sa mata a abin sha tana sha bacci mai nauyi zai d'auketa,ke kuma a lokacin da take baccin sai kije d'akinta ki samo rigarta dana mijinku zan baki wasu layu da guraye saiki nannad'e su da kayan ki tura su a k'arkashin gadonta.in kikayi haka toh kin gama kama gidan dan ba abinda zasu iya aiwatarwa saida umarninki,zasu kasance cikin matuk'ar tsoronki da shakkarki yanda ba k'ya zato.kece zaki mulke su son ranki dafatan hakan yayi miki". Wani irin dariyan farinciki ta fashe dashi cikin tsananin murna tace..." yayi boka zan aiwatar da komai yanda kac,wallahi sai na sa sun bauta min dukkan su 2 sai sun gane basu da wayo" Makud'an kud'ad'e ta ajiye mushi wanda yafi na kullum sannan suka fito. A hanyarsu ta dawowa gida Aina'u ta dubi lateefa tace..." besty yanzu ya zakiyi ki bata wannan maganin tasha?" Harar Lateefa ta wurga mata tare da tab'e baki sannan tace..." sai kace baki san dawa kike magana ba?" "Toh ai gani nayi ko fitowa batayi kikace". "Ke dai zuba ido kisha kallo"tace cikin isa. " nasan zaki iya ba abinda zai baki wuya mata a gidan Ameenu"Aina'u tace tana k'ara zugata. Cike da k'warin guiwa ta iso gida. [3/24, 6:47 AM] Ummee Yusuf: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA~* 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman yusuf) *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~* *part twenty one* Bayan dawowarsu daga gidan boka Lateefa duk ta tashi hankalinta kullum cikin tunanin ya za'ayi ta zubawa Ameera magani take,k'watsam rannan suna zaune da kannen ta a palour suna kallo wata dabara ta fad'o mata. Cikin sauri ta juyo wajansu tace.... "ke fa'iza ina son kuje kifito min da 'yar iskan can da my Ameen ya ajiye a can part d'in yanzu amma fa cikin dabara ". ta k'arasa maganan tana duba lek'en part d'in Ameera. Shamsiya ta ajiye remote d'in hannunta sannan tace..."dats great Aunty dama ni kullum mamaki kike bani da kika k'yaleta ta samu k'wanciyar hankali a gidan nan,yanzu kuwa zakiga aiki da cikawa,taso muje Fa'iza". Shamsiya tayi gaba Fa'iza tana binta a baya har bak'in k'ofan palourn Ameera,knocking sukayi har su biyu sannan suka ji ta amsa da" da waye ne ? ina zuwa". Sanye take cikin wata black abaya tayi rolling da veil d'in kayan,sosai yayi mata k'yau kuma ya kara fito mata da haskenta. tana tunanin waye haka by dis time? tasan dai ba mijin ta bane dan shi yana da key a wajen shi ko yazo sai dai ya bud'e ya shigo. Har ta k'araso k'ofan bata daina zancen zucin ba. Bakin fuska ta gani bayan ta bud'e k'ofan. Fa'iza da Shamsiya baki da hanci suka sake suna kallonta dan basuyi especting zasu ganta haka ba. "Sanun ku da zuwa, tace ganin basu da niyan maga saina mujiya da suka zuba mata. Shamsiya ce tayi karfin halin cewa..." uhummm amarya dama mun zone dan mu gaishiki". Fara'anta fuskantata ne ya fad'ad'a, ta d'an matsa ta basu hanya, sannan tace " ku shigo mana ya kuka tsaya a waje". Shigowa sukayi suna k'arewa palourn ta kallo cos ba karya ya burge su. Saida suka zauna sanna Fa'iza tace.." nasan baki samu ba ko?" Murmushi tayi tana wasa da yatsin hannunta tace.." eh gaskiya ban gane ku ba". Tab'e baki Fa'iza tayi tana gyara zama sannan tace.." muna cikin gida 1 amma bamu san juna ba,toh mu k'annen Aunty Lateefa ne ganin har kinfi wata a gidan bamu sanki ba shiyasa muka zo dan mu gaisa". Shamsiyya ta karb'e da " ina zamu ganta kullum tana cikin part d'inta a kulle". Dariya Ameera tayi tana " wallahi ba haka bane,kinsan in kana bak'o sai a hankali". " eh hakane kam amma tunda mun biyo ki yanzu kin wuce bak'uwa,sai ki saki jiki damu mu saba ayi zaman tare kema zaki fi jin dad'in gidan". Cikin jin dad'i Ameera tace...hakane kuma nagoda da zumuncin,let me get u something to drink". Rik'eta Fa'iza tayi tana " noo da kin barshi kawai ". B'ata fuska Ameera tayi tace.." haba mana ya haka kuma,ku da kuka ce in saki jiki daku mun zama d'aya shine za kuce ba zaku ci abincina ba?"ta karasa cikin shagwab'a. Kallon sha'awa Fa'iza take binta dashi,can ta daure tace..." is ok ba sai kinyi mana kuka ba je ki kawo mana koma menene zamu ci kinji". Tana dariya tayi hanyan kitchen still idon Fa'iza na kanta. Mari Shamsiyya ta zuba mata a cinya sannan ta dawo hayyacinta,ta juyo tana kallon yayarta spechless. " come back to ur sence Fa'iza nd stop stairing at dat bitch"Shamsiyya tace tana hararnta cike da kishi. Yawu ta had'iye tana kallon Shamsiyya still bakinta ya kasa furta komai. " karki soma nagetive tinking akan yarinyan nan saboda dalili 2,first ina son ki tuna wacece ita nd 2 kuma zaki iya samu a wani hali bcos u re not sure she will accept u or not.pls Baby think twice b4 doing something" Shamsiyya tace mata tana shafa mata gefen fuska. Ajiyan zuciya ta sauke tare da kamo hannun Shamsiyya ta rike tace " tnx da kika tunatar dani if not i have done something rubbish" ta k'arasa da dariya but deep down her bata hak'ura ba kuma ta tabbatarwa kanta she will surely have her one day. Suna cikin dariyan Ameera ta iso d'auke da katon tray ta cika shi da kayan ciye-ciye da drinks kala-kala ta ajiye a gabansu. Sunfi 30 mins suna hira sannan suka ce mata zasu tafi. B'ata fuska Ameera tayi tana " har zaku tafi,pls ku zauna mana muyi hira". Da sauri Fa'iza ta d'auke kai cos in taga tana wannan shagwab'ar da ya zama al'adarta ji take kaman taje ta rungumeta. " a'a in kina so ki fito muje main palour muyhiran acan,kinga sai mu k'ara sabawa ". " ku bari zuwa gobe sai in fito muyi hiran acan" Ameera tace musu tana murmushi. Fizgo hannun Fa'iza Shamsiyya tayi sukayi hanyan fita tana mita " muyi tafiyar mu Fa'iza dama ba wani bak'unta dama kawai bata son alaka damune take wani fakewa da bakunta" Fa'iza dai binta kawai take dan sosai take nadaman shigowanta part d'in nan. Har sun kai bakin k'ofa tayi saurin dakatar dasu ta hanyan cewa " pls ku tsaya mu muje,dan Allah karkuyi fushi dani ba nufi na ba kenan". Tsayawa sukayi suna murmushi tare da cewa " ko kefa". Jerawa sukayi tare suka fito palourn suka zauna tare da cigaba da hiransu. Shamsiyya ce rike da phone d'inta tana rubatawa Auntynta short msg kan cewa gasu nan a palourn sun fito da ita. Cikin minti 1 reply d'in Lateefa ya shigo mata. Mikewa tayi bayan ta karanta massage d'in tace..." ammm ina zuwa pls" sannan tayi hanyan part d'in Auntynsu. A tsakiyan palournta ta same ta sai kaiwa da komowa take " gani Aunty" tace lokacin da iso gabanta ta tsaya. " take dis ku tabbata kunsa mata shi a drink ta sha,pls try ur best my lovely sisters".tace mata pleadlly. "Don't worry Aunty consider it done ".tace mata tana zuba maganin cikin wani drink dake cikin glass cup,ta zuba wasu glass 2 suka zama uku sai dai ta banbant zaman cups d'in sannan ta d'auki katon trayn ta fita zuwa palourn da ta barsu. Ameera da Fa'iza sunan zaune a inda ta barsu suna ta kwasan dariya. Dire trayn tayi akan center table na glass dake tsakiyan palourn sannan ta jawo shi gaban su. " wai hiran me kuke ne?naga kuna ta kwasar dariya haka?"tace lokacin da take zama. "Labarin k'wawarki Aisha nake bata,yanda tasha k'asa a gaban saurayinta"Fa'za tace tana dariya. Dariya Shamsiyya tayi sannan ta d'auko drink mai ta mikawa Ameeera tace " toh ya isa ga drink nan kowa ya ya sha dan muji dad'in hira". Ba tare da tunanin komai ba Ameera ta karba,suma suka d'auka suka fara sha suna hira. Sun gama sha kaman da minti 10 Ameera ta fara jin dizzness ko bud'e ido dak'yar take yi can kuma ta yanki jiki ta fad'i kan kujeran da take Zaune ta kama bacci kaman matatciya. [3/24, 6:47 AM] Ummee Yusuf: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA~* 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman yusuf) *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u no pain~* *part twenty two* Zuba mata ido sukayi dukan su 2 kowacce da abinda take tsak'awa a ranta. Dawo da dubanta Fa'iza tayi kan yayarta fuska d'auke da damuwa tace..." sis me kika bata ne a cikin drink d'in nan tasha har ya jefata cikin wannan halin?" Fuska cike da fara'a Shamsiyya ta amsa mata da cewa..." ni ba abinda na saka mata,hasalima Aunty ce ta bani tace mu bata tasha.i don't know her mission amma let me call her"ta k'arasa zancen tare da dannawa Lateefa k'ira nan da nan ta fad'a mata halin da Ameera take ciki,cike da zumud'i tace gata nan fitowa. Cinkin abinda baifi minti 2 ba sai gata ta fad'o cikin palourn kaman an jefota. Sauri- sauri gudu-gudu ta k'araso hannunta na dama rik'e da tsurkullen da boka ya bata hannunta na hagu kuma rik'e da rigan Al'ameen ta k'araso wajansu tana" ke Shamsiyya zo ki raka ni ke kuma Fa'iza ki zauna da ita kamin mu fito" Ta nufi part d'in Ameera ba tare da ta jira amsarsu ba Shamsiyya ta mara mata baya suka bar Fa'iza da taradaddin kar Allah ya basu sa'an cutar da ita dan yanzu ita tausayi take bata. Suna shiga part d'in direct bedroom d'inta suka wuce,wani riganta na atanfm Lateefa ta binciko a cikin sip d'inta ta had'a da rigan Al'ameen ta nannad'e kaya tsafin boka dasu, Shamsiyya ta taya ta suka d'aga gadon suka tura kayan karkashin gadon sannan suka gyara komai kaman ba abinda ya faru suka fito palour. Ameera saida ta k'washi gud 4 hrs tana bacci sannan ta farka.cikin baccin da tayi boka yayi nasaran yin aikin shi a kanta sannan ya turo wata aljana da zata zauna a jikinta ta hana ta addu'oin da take saboda kar aikinsu ya lalace. Da ido kawai take binsu d'aya bayan d'aya ta kasa tantance wani hali take ciki har idonta ya sauka kan Lateefa da itama idon ta zuba mata dan taga reaciton d'inta. Wani irin bugawa taji zuciyarta yayi kaman ya fad'o k'asa. A take taji wani irin tsoron Lateefa na ratsa duk jinin jikinta,a yanda take ji a yanzu komai ta saka ta źata iyayi. Tsawa Lateefa ta daka mata tana " wace irin mayya ce ke da zaki zo ki tsare mutane da ido kaman na mujiya?" Murya na rawa tace" Aunty kiyi hak'uri ba kallon ku nake ba". Wani malalacin murmushi tayi ganin tarkonta ya kama tsuntsu duk da dama ta yarda da aikin bokanta,yanzu saura Al'ameen take jira shima yazo taga yanda zaiyi. Hada rai tayi tace " oya tashi kije ki d'aura mana dinner" Sunkuyar da kai tayi k'asa zuciyarta na k'ara speed tace..." me zan dafa Aunty?" Tsawa ta k'ara daka mata cike da masifa tace..." ke dak'ik'iyar inace ina baki comand kina min tambayoyi...? Shamsiyya ce tayi caraf tace..." ai dole ta tambaya Aunty ba'a saba cin mai maik'o ba a gida,so gwara ki bata order kar aje ayi mana k'wamacala". Gyara zama tayi tana wani huhhura hanci a garance tace..." je kiyi mana tuwon shinkafa miyan taushe sannan kiyi peppe soup d'in d'anyan kifi da fruit salad...kuma saura ayi sallahn magrib baki gama ba kiga yanda zanci ubanki a gidan nan". Jiki na b'ari ta mik'e cikin sauri kaman zata kifa ta fara laluben babban kitchen d'in gidan kasancewar tunda aka kawota gidan bata tab'a fita daga part d'inta ba. Dariya Shamsiyya ta kwashe dashi tana " shikenan mun samu sabuwar 'yar aiki". "K'yale ni dasu sai sun gane shayi ruwane,dole ta bauta min daga yau zan dakatar da masu aikin cikin gidan nan". Fa'iza dai shiru tayi tana jin ba dad'i cikin zuciyarta saboda tausayinta. Murmushine ya k'wace mata da ta tuna cewa itama zata iya amfani da wannan daman ta cimma burinta akanta.cikin jin dad'i itama ta shiga cikin hiran da suke. Kujeran da ta gani guda d'aya a kitchen d'in Ameera ta zauna dafe da kirjinta da har yanzu bai bar bugawa ba,tana mamakin sudden change daya same ta. Tasan tabbas tun farko tana tsoron Lateefa amma na yanzu na musamman ne tunda ko ido bata iya had'awa da ita balle tayi mata musu, gata harda sakata girki. Cikin zuciyarta take cewa tasan Al'ameen yana zuwa zaiyi maganin abin yayi musu iyaka saboda ba zai yarda da wannan zaluncin ba. Pls kuyi mange da wannan dan yau sau 3 ina typing yana gogewa. [3/24, 6:47 AM] Ummee Yusuf: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA~* 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman yusuf) *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u no pain~* *part twenty three* Tashi tayi ta fara girkin da aka sata,saboda kar lokaci da aka bata ya kure gashi kuma tayi warning d'inta. Bata dad'e ba ta kammala girkin gaba d'aya gidan ya karad'e da kamshin girkinta. Wani had'dd'en set d'in warmers ta d'auka ta zuzzuba abincin a ciki sannan ta k'washe su ta kai kan dinning ta jera su. Dawowa tayi cikin kitchen ta zauna tana tunanin fita,ba dan komai take gudun fitan ba sai dan kar su had'u da Lateefa. Gajiya tsyi da zama a kitchen d'in kuma tana son yin wanka kamim Al'ameen ya dawo daga wurin aiki,dole ta mik'e ta fita tana jan k'afa. Suna nan zaune a inda ta barsu ga kayan ciye-ciye a gabansu suna ci suna hira,yawancin hiran akan samun nasararta akan Ameera ne. Daga can nesa dasu ta tsaya kanta a kasa tace..." Aunty na gama ". Juyowa sukayi suka zuba mata ido suna mamakin wai har ta gama girkin bayan har kala 2 ta bata dan kar ta gama da wuri ta samu abin ci mata mutunci,sai gashi harta gama.daga ita har k'annenta ba abinda suka iya a fannin kitchen kasancewar mamarsu ba ruwanta da sasu aiki in dai zasu fita su kawo mata kud'i toh bata da case da su. Kallon up nd down Lateefa take mata,cikin tsawa ta fara matq magana..." waye sa'an ki anan da zaki zo ki tsaya a kan mu kina magana without any respect ,daga yau in har zaki min magana ki tabbatar kin rage tsawonki ". A hankali ta kai guwowinta k'asa idonta tab da hawaye amma bata bari sun zubo ba. Murna fal cikin zuciyarta tace.." je ki gyara min bedroom da toilet d'ina yanzun nan kuma as from today kece mai gyaran duk bedrooms da toilets na gidan nan". Bata ce komai ba ta mik'e tayi hanyan part d'in Lateefa. Tana b'ace musu Fa'iza ta mik'e itama tana d'an soshe-soshen rashin gaskiya tace..." ummm Aunty na bari in d'auko system na a bedroom d'inki ". " ok kuma ki duba min ko wancan banzan tana min gyaran yanda ya kamata". Cike da murnan samun nasara tayi hanyan part d'in da saurinta,Shamsiyya ta bita da ido saboda tadan karya take komai na bukatansu yana part d'insu. Ameera tana tsakiya gyaran palour Fa'iza ta shigo da sauri ta kama hannun Ameera suka koma kan kujera suka zauna,ita dai Ameera zuciyarta sai dakan 3 yake dan bata san da wacce muguntar tazo mata ba. Cikin k'wantar da murya tace..." kiyi hak'uri Ameera ban san me yake damun Aunty ba take miki haka amma nayi miki alkawari duk lokacin da kike neman taimako kizo wajena zan miki koma menene....kinji?"tace tana shafa gefen fuskanta . Mik'ewa tayi tsaye kanta a k'asa tace " nagode da kulawarki Aunty bari in k'arasa sauran aikina". Bedroom d'in Lateefa ta shiga tana mamakin Fa'iza duk da kalamanta sunyi mata dad'i amma tana da kokonto a kai ga wani shafa mata jiki da take shiyasa ma ta shi ta bar mata palourn dan banbarak'wai abin yazo mata. Tsab ta gyara mata ko ina sannan ta fito palour zuciyarta na bugawa Tana shigowa da tsawa Lateefa wai me ya fito da ita bayan tasa ta aiki. " na gama Aunty shiyasa na fito"tace kanta a k'asa. " sauran toilets d'in gidan wa zai wanke miki ?" ta tambaya tana banko mata harara. Juyawa tayi ta koma ta hau sama zuwa part d'in Al'meen ta hau gyaran parlourn duk da dama ko ina a kintse yake,ta kama handle d'in kofan bedroom taji muryan Lateefa ta hayyako mata..... "Ubanwa ya baki izinn shigowa part d'in mijina?" Ameera duk ta rud'e murya na rawa tace...." kiyi hak'uri Aunty ke kika ce in wanke toilets na gidan man duka shiyasa na shigo amma dan Allah ki yafe min". " tashi ki bani guri munfuka,sai ana magana ta rink'a wani sunne kai k'asa kaman mutuniyar k'warai". Tsimi-tsimi ta fice zuwa nata part d'in ,direct bathroom ta wuce ta had'a ruwan zafi ta shiga ciki ta kwanta dan yanda take jin bayanta kaman zai balle saboda tunda tazo duniya bata tab'a aikatuwa irin na yau ba. Alwalan magrib ta d'auro bayan ta gama wankan sannan ta fito tayi sallah,tana addu'an Allah yasa lafiya ganin har anyi sallah Al'ameen bai dawo ba. Al'ameen driving yake a mota ya taso daga gidansu sakamakon amsa k'iran Alhajin shi da yayi bayan ya tashi a office, murmushi yake shi kad'ai saboda yana cike da farincikin zaiga sanyin idaniyan shi wato Ameera cos yayi missing d'inta sosai.dan haka duk ya k'osa yaga ya isa gida. Yana zuwa mai gadi ya bud'e mishi gate ya shigo cikin gidan. Ya dade a cikin motan sannan ya samu courage d'in fitwowa a ciki sakamakon yana shigowa haraban gidan yaji haka kawai gaban shi yana fad'uwa ga wata fargaba da mutuwar jiki da suka sauko mishi lokaci 1 wanda baisan dalili ba. Da k'yar da jan k'afa yayayi sallama ya shigo palourn farko, bakowa nan ya k'arasa main palour anan ya tarar da Lateefa zaune tana sanar da rabi cewa ta dakatar dasu daga aikin. A razane rabi ta d'ago da kai tana kallonta saboda tashin hankali ta rasa bakin magana cos tun Lateefa tana amarya suke tare har ya zamanto ta kasance leader. Dariya Lateefa tayi tana " k'wantar da hankalinki ba na sallame ku bane hutu na baku saboda nasamu sabuwar 'yar aiki,ina son ku bar mata aikin tayi ita kad'ai na d'sn wani lokaci saboda ta saba". Rabi zatayi magana taga shigowar Al'amee,ba shiri ta had'iye maganarta jiki na rawa tayi mishi sannu da zuwa ta fita ta basu waje. Kallon inda yake Lateefa tayi dan bata san da shigowar shi ba,suna had'a ido yaji duk duniya ba wanda yake tsoro da shakka sama da ita. Cike da dauriya yayi yak'e yace..." my Lateefa kina hutawa ne?" Harara ta galla mishi tace..." kai meye haka daga zuwa zaka wani cika ni da sututu,haba Ameeenu" ta k'arasa da jan gajeran tsaki. Sassauta murya yayi yace..."Allah huci zuciyarki my queen ". Tashi tayi tana murmushin nasara ta k'araso gabanshi tare da kama hannun shi tace..." muje kayi wanka sannan kaci abinci ko?" Bashida bakin magana bare musu,haka yabi bayanta kaman rak'umi da akala har cikin bedroom d'in shi. Fitowa tayi bayan shigarshi wanka ta shiga k'wakawa Ameera k'ira, wacce zamanta kenan a gaban dreesing mirrow danyiwa angonta k'walliya amma jin muryan Lateefa yasa ta tashi jiki na b'ari ta zumbula hijabi ta fito palour. Zubewa tayi a gaban Lateefa kai a k'asa tace..." gani Aunty". Al'ameen yana sauk'owa daga stairs idonshi ya sauka kan Ameera da take durkushe gaban Lateefa tana masifance ta nan yaji zuciyar shi tana bugawa da sauri-sauri har ya k'araso wajansu. [3/24, 6:47 AM] Ummee Yusuf: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA~* 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman yusuf) *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u no pain~* *part twenty five* Rufe k'ofan yayi da key ta ciki sanna cikin hanzari ya wuce bedroom d'inta. Tana k'wance daga ita sai kayan bacci a jikinta wanda gaba d'aya ya tattare yayi sama ga gashin kanta duk sun baje kan pillown da ta d'ora kanta tana ta baccin gajiya. Ya dad'e a tsaye a kanta yana kallonta dan ba k'aramin k'yau tayi mishi ba duk da ta rame tayi duhu cikin 'yan k'wanakin nan. A hankali ya lallab'a ya hau gadon ya k'wanta a gefenta yana gyara mata gashinta yana shafa ta a hankali. Motsi tayi ta juyo kaman zata bud'e ido amma baccin yafi karfinta. Matsota sosai yayi jikinshi ya rungumeta tsam yana mata rad'a a kunne yace..." wake up my sleepin beauty". Kaman a mafarki take jin kamshin turaren shi ga kuma d'umin jikin shi da taji yasa ta k'ara gyara k'wanciyarta a jikin shi tana shakan kamshim da tayi missing.amma jin muryan yasa ta bud'e ido a firgice. A rud'e ta fara k'okarin zare jikinta daga nashi tana " yayana dan Allah ka tafi kar Aunty tazo ta same wallahi zan shiga matsla babba". Rik'ota yayi da sauri yana shafa bayanta a hankali yace..." cool down mana ki k'wantar da hankalinki ba wanda zai shigo nan dan tana can tana bacci kinji.." Fashewa tayi da matsanacin kuka mai tsuma zuciya tare da k'ank'ame shi ta fara magana. "Yayana wai me yake faruwane?,ka taimake ni ka sanar dani me yake faruwa...? Bai samu bakin magana ba sai shafa bayanta da yake har yanzu alamun rarrashi,toh shi mema zaice mata saboda shi kanshi baisan me yake faruwan ba. Had'e bakin su yayi ya fara bata hot kiss yana aika mata da sak'onni cikin zafi-zafi saboda ba k'aramin missing d'inta yayi ba. Bai barta ba saida suka faranta ran juna sannan ya shiga lallashinta da kalamai masu dad'i da taushi sai gata nan tana k'yalkalan dariya kaman ba ita ba,nan suka shiga hiransu ta masoya kaman basu da wata matsala har zuwa 3am sannan yayi mata saida safe ya fita da k'yar dan ji suke kaman kada su rabu. Da fargaba ko zsi tarar Lateefa ta dawo d'akinshi,zuciyarshi sai bugawa yake kaman wanda yayiwa sarki babban laifi amma ga mamakinsa yana shiga d'akin yaga ba kowa kaman yanda ya tafi ya bari. Zuciyar shi fari kal ya haye gadonshi ya k'wanta cike da nishad'i. Ameera haka tacigaba da rayuwa a gidan Lateefa tana gana mata *UKUBA* iri-iri duk tayi bak'i ta rame ta fita hayyacinta,duk wanda ya ganta sai ya tausaya mata hatta masu aikin gidan suna tausaya mata dan ba yanda suka iyane amma wani lokaci suna fakan ido su tayata aiki bama kaman Rabi duk tafisu taimakonta. Al'ameen shima duk ranan da Lateefa ta koma d'akinta sai ya lallab'a yaje d'akin Ameera su sha love abinsu.har yau baisan dalilin da take guduwa cikin dare ta barshi ba,yafi alakanta hakan da kin bashi hakkin shi da take baisan cewa raba dare suke da Salees d'inta suna waya ba. Yau monday Ameera da k'yar ta fito daga part d'inta saboda k'wata-k'wata bata jin dad'in jikinta,kasala ce zallah yake damunta ga wani azababben ciwon kai da take ji tun cikin dare dan haka a daddafe ta gama aikinta na safe ta koma part d'inta tana neman magani bata samu ba dole ta hak'ura ta dawo ta cigaba da aikin saboda lokacin d'aura abincin rana yayi. Faten doya da yaji ice fish da kayan lambu tayi musu,ta jera musubakan table kaman yanda ta saba sannan ta k'arasa palour inda ta samu Lateefa sun baje itada k'annenta sun cika palourn suna kallo. Can nesa dasu ta durkusa dak'yar tace...Aunty na gama". Zuba mata ido sukayi a wulakance banda Fa'iza da take binta da murmushi. Cikin basarwa da gadara Lateefa tace..." naji ina sauran aikin kinyisu?" "Kainane yake ciwo Aunty banyi ba amma yanzu zanje...."a tsawace tace.." wat?,lallema yarinyan nan wuyanki yayi k'wari ya isa yanka har insaki aiki ki tsaya kina kawo min k'abli da ba'adi?,ba ciwon kai ba uban ciwon kai kike ba abinda ya dameni dan haka ki bace min da gani kamin in b'allaki banza kawai" ta k'arasa maganan tare da jan digon tsaki. Daurewa ta k'ara yi ta yunkura ta tashita koma aikinta. Shamsiyya tayi dariya tana jinjinawa Auntynta tace "Aunty kina wuta muna binki da fetir". Cike da ji da kai tace..." kad'an ma suka gani dan yanzu na fara bautar da ita". Ajiyan zuciya Fa'iza dake sauraransu tayi kana tace..." ni dai Aunty ina ganin da gaske take fa bata da lafiyat". "Ina ruwana da rashin lafiyarta kai ta mutuma mana ni meya dame ni?"tace tana wani tab'e baki. K'ara k'wantar da kai Fa'iza tayi tace.." ai shiyasa nake ganin ya kamata ta samu kulawa daga wajanki ko dan kiji dad'in bautar da ita". Murmushi Lateefa tayi tace..."ke Fa'iza in kin fara wannan nacin naki nasan ba bari zakiyi ba saboda haka kije ki d'auki paracetamol 2 cikin first aid box ki bata ta sha nd na bata hutun 10 mins kawai ta dawo kan aikinta". A kitchen Fa'iza ta taddata zaune rik'e da kanta da yake barazan fashewa. Dafa shouldernta Fa'iza tayi,a firgice ta mik'e tana " kiyi hak'uri Aunty yanzu zanyi wallahi". Rik'ota Fa'iza tayi da sauri tana mata murmushi tace.." k'wantar da hankalinki ba Aunty bace nice ". Hankalinta ya d'an k'wanta da ganin Fa'izan dan ba laifi ita tana k'yautata mata ba kaman sauran sisters d'inta ba. Da kanta ta bud'e fridge ta ta d'ebo mata ruwa tare da b'allo mata paracetamol 2 ta bata. Ba musu tasa hannu ta kab'a ta watsa a bakinta tare da kora ruwan. " kije d'aki ki k'wanta ki huta inji Aunty". Murmushi tayi tace " nagode Aunty Fa'iza Allah ya saka da alkhairi". [3/24, 6:47 AM] Ummee Yusuf: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA~* 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman yusuf) *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u no pain~* *part twenty four* Gadan-gadan ya nufo su zuciyar shi na bugawa,rai a matuk'ar b'ace ya iso gaban Lateefa ya tsaya da niyyan yi mata magana.amma suna had'a ido ya manta me ya kawo shi wajan saima wani murmushi da ya sake mata yace..." my Lateefa yunwa nake ji". Murmushin itama ta mayar mishi tare da kama hannun shi sukayi hanyan dinning tana" dont worry ur food is ready my Ameen". Ameera ta dade a durkushe a inda suka barta saboda ta rasa kuzarin tashi daga wajan,dama a tunaninta Al'ameen yana dawowa komai zai daidaita komai,sai gashi ko kallon inda take baiyi ba bare tasa ran zai kulata ko d'aukan mataki. Muryan Lateefa taji tana k'wala mata k'ira kaman tana wata duniyar. Amsawa tayi ta mik'e cikin sauri ta isa dinning d'in ta durkusa nesa dasu kanta a k'asa tace..." gani Aunty". " k'washe kayan nan kije ki wanke su tas kamin ki k'wanta dan bana sin k'azanta". Wani abu ya rink'a ji a k'asan zuciyarshi lokacin da yaga tana k'washe kayan,yana son kallon fuskanta amma ya kasa yana tsoron kar Lateefa ta ganshi. Ameera tana barin wajan Lateefa ta jashi zuwa parlour dan suyi hira amma shi ya kasa maida hankali kan hiran saboda rabin hankalin shi yana kan Ameera. Dube-dube take a kitchen d'in inda ta bar abincinta amma cikin ikon Allah ta neme shi sama da k'asa ta rasa,gata sosai take jin yunwa cos yau ko lunch batayi ba. Abinda bata sani ba Lateefa ce ta d'auke abincin nata ta bayar dashi dan mugunta.ganin yunwa na neman halakata yasa ta jawo sauran abincin dasu Lateefa suka rage ta cinye sannan tayi wanke-wankenta tare da gyara kitchen d'in tsab ta fito. Ba kowa a palourn ta wuce part d'inta zuciyarta a cunkushe kan sabon rayuwa da ta tsinci kanta a ciki,bata dad'e da kwanciya ba bacci mai nauyin gaske yayi gaba da ita sakamakon gajiya da take tattare da ita. Al'ameen zubawa Lateefa ido yayi wacce take bacinta cikin k'wanciyar hankali,yana son zuwa d'akin Ameera saboda yau k'wananta ne amma tsoron Lateefa ya hana shi koda yunkurin tashi ne bare yayi gigin fita a d'akin. Yanzu da yana wajan Ameera ne suna can suna tattalin juna amma ita saidai ma ta kara mishi damuwa Yasan kuma da gayya tazo ta k'wanta mishi a d'aki dan kar ya samu daman keb'ewa da Ameera.tunda sai suyi kusan sati 2 bai isheta kallo ba dama a wajan Ameeran shi yake samun kulawa. Juyi yake yana ta sak'e-sak'e a zuciyar shi da k'yar bacci yayi nasaran d'auke shi. Ameera data farka da asuba bayi mamakin rashin ganin Al'ameen ba saboda yanda taga jiya ya wofintar da ita. Tana idar da sallah asuba bata tsaya yin addu'a ko azkar ba tayi hanyar kitchen,hasalima mantawa tayi anayi saboda wannan shine amfanin aljanin da aka turo mata. Ruwan zafi daya sha kayan kamshi ta fara d'aurawa sannan ta d'ebo irish da take ganin zai ishi gidan ta fara aikin ferewa. Kamin tagama firan har ruwan tean ya tafasa yanata kamshi,juyewa tayi a wani babban tea flask sannan ta fara soya irish d'in. Tana gama soyawa ta samu wani babban bowl ta fasa eggs a ciki ta yayyanka mishi wadatattacen albasa ta soya shima,ta k'ara musu da kunun k'wak'wa sannan ta fito dasu kan dinning ta jerasu. Komawa kitchen d'in tayi ta gyara ko ina sannan ta fito palourn ta share tare da yin mopping,b4 8am harta gama aikinta tayi wanka taci k'walliyarta da wani less peach colour da white stones a jiki tayi bala'in k'yau. Zama tayi a bakin gadonta tana jira taji k'ira dan tasan basu tashi ba. Ba tafi 10mins da zama ba taji ana zabga mata k'ira,cikin azama ta fito. Kamshin turaren ta yasu d'ago kai suna kallonta. Al'ameen kam kasa d'auke idonshi daga kanta yayi saboda gaba d'aya ta rikita shi. Tsawan da Lateefa tayi yasa shi dawowa cikin hayyacin shi kuma ya nemo natsuwa cikin d'an k'ankanin lokaci ya sunkuyar da kai tare da wayancewa. Ameera itama tuni tasha jinin jikinta ta fara karkarwa. Lafiyayen marin da tajine ya sata mik'ewa ba shiri tare da dafe fuskanta inda Lateefa ta mara dan ga yatsunta nan tsab sun fito abinka da farar fata. Nunata take da yatsa cike da masifa take magana..." ke k'aramar 'yar iska wallahi zanyi maganin kine a gidan nan wato tsabar kinyi degree a karuwanci shine kikayi wannan k'waliyan harda saka ture kika zo gaban mijina ?" Kama 1 kunnenta tayi ta murd'e iya karfinta sannan tace..." zanyi miki last warning a gidan nan,duk ranan da naga kinyi k'walliya ko kika saka turare a gidan nan hmmmm....." murmushin mugunta tayi sannan ta cigaba" wallah sai na lahira ya fiki jin dad'i.dallah b'ace min daga nan bak'ar munafuka.." Da gudu ta koma part d'inta tana kuka kaman ranta ya fita. Lateefa ta juyo tana kallon Al'ameen daya sunkuyar da kai k'asa ba zaka tab'a tantance yanayin da yake ciki ba tace..." sorry my Ameen wannan munafukar tana son b'ata min rai da sassafen nan". Ajiyar zuciya yayi ya dago kai tare da kirkiro murmushin dole yace..." sorry my Lateefa kema kinsan bana son b'acin ranki". Jawo warmers d'in gabansu tayi ta fara serving d'insu cikin jin dad'i tace..." shikenan my Ameen na hak'ura". Abincin yayi mishi dad'i sosai tsakanin jiya da yau yasan an samu canji wajan girki a gidan dan ya lura Ameerarsa ce take girkin amma hakan baisa yaci ba sai jujjuya fork d'in hannun shi yake. Ganin irin kallon tuhuma da Lateefa take aika mishi yasa ya zage ya fara tutturawa. Suna gamawa ta rako shi har waitin palour abinda bata tab'a yiba wai dan kar ya samu daman branching a wajan Ameera. Tun kamin ta karaso cikin palourn ta fara k'iran Ameera. Fitowa tayi cikin wani jallabiya red fuskanta a kumbure babu make up d'in dazu sakamakon kukan da tasha. " wuce ki gyara kan table d'in sannan ki gyara min bedroom kuma ki wanke min toilet tas " tace mata a gadarance. "Toh Aunty " tace tana yunkurin mik'ewa domin taje ta aiwatar da abinda aka sakata. Yauma bata samu zama ba sai kusan tara na dare dan haka wanka kawai tayi tabi lafiyar gado,cikin minti 2 bacci mai nauyi yayi gaba da ita. Al'ameen yana k'wance amma duk a takure yake saboda yau k'wata-k'wata baisa Ameera a idonshi ba saboda Lateefa ta kara tsanta doka kan cewa in Al'ameen yana gida kar ta yarda ta fito ko tabi inda yake. Abinda Lateefa bata sani ba shine boka yayi nasaran dasa tsoronta a zukatansu amma soyayyar da suke ma juna yana nan daram. Bai saba k'wanciya tare da ita yasa yake jinsa a matse. Motsinta daya ji shiya shi saurin rufe ido kaman mai bacci,yana jinta tana sauk'owa a hankali har ta iso bakin k'ofa ba tayi wani babban motsi ba gudun kar ya farka. Yana ji ta bud'e k'ofan ta fita tare da maida k'ofan ta rufe duk a hankali tayi su. Bayan ta fita kaman da 5mins ya bud'e idonshi yaga tabbas bata d'akin,zama yayi a bakin gadon ya kai minti 10 zaune amma baiji motsinta ba. Tashi shima yayi cikin tsand'a kaman wani b'arawo ya iso main palourn yaga bata nan,rab'ewa ya dinga yi tsakanin cushins d'in palourn har ya isa hanyan part d'in Ameera cikin sa'a ya samu k'ofan a bud'e,ba wata wata ya bud'e k'ofan ya shiga. [3/24, 6:47 AM] Ummee Yusuf: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA~* 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman yusuf) *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u no pain~* *part twenty six* Sakamakon gajiya da take fama dashi kuma ya hadu da kasala tana k'wanciya bacci mai dad'i yayi awon gaba da ita. Baccinta take harda mafarkin su Umma da Fateema tana musu korafin sunk'i zuwa dubata daga nan suka bige da wasa da dariya ita da fateema wanda har yake fitowa a zahiri. Ruwa mai bala'in sanyi da aka shek'a mata shi sanadin katse mata baccinta mai dad'i. A gigice ta farka tana neman hanyan guduwa. Ficikota akayi taji tare da kifa mata wani wawan mari da ya k'ara gigita ta tare da k'ara mata ciwon kai. Muryan Lateefa da Shamsiyya suna zazzaga mata k'wandon rashin mutunci akan meyasa tayi bacci har lokaci ya k'ure gashi 5 ta gota batayi girkin rana ba har time d'in d'ora na dare yayi. Shamsiyya itace a gaba wajan neman nad'a mata na jaki ,Fa'iza ta shigo da k'yar ta k'waceta tana basu hak'uri. Hankad'a keyarta sukayi zuwa har cikin kitchen d'in sannan suka k'yaleta. Tana kici-kicin d'ora girki Fa'iza ta shigo ta same ta. Rik'ota Fa'iza tayi tana kallon yanda fuskanta ya kumbura yayi jah sai hawaye da take sharewa. Zaunar da ita tayi ta fita sai gata sun shigo da rabi,tacewa rabi ta cigaba da aikin ita kuma Ameera taje ta k'wanta ta huta. Har k'asa Ameera ta duka zatayi mata godiya tayi saurin rik'eta tana " bana son haka Ameera ni sonki nake shiyasa bana juran inganki cikin wahala yanzu jeki k'wanta ki huta sun fita ba zasu dawo da wuri ba. Fita tayi zuwa part d'inta zuciyarta cike da farinciki tare da bawa Fa'iza daraja na musamman a cikin zuciyarta. Rabi sai jinjina abin take a ranta saboda tana da shakku akan Fa'iza meye dalilinta na yin haka alhalin tasan Shamsyya rashin mutunci,koma menene tana mata addu'an neman tsari daga masifar Lateefa da k'annenta. Allah ya taimake ta har dare ba wanda yabi ta kanta,amma zazzabi da ciwon kai sun hanata bacci sai juyi take akan gado tana hawaye. 12:30 am Al'ameen ya lallab'o ya shigo part d'inta ya same ta a haka. Hankalin shi inyayi dubu to ya tashi jin zafin jikinta har yayi over ga fuskanta da ya kumbura suntum saboda maruka da tasha a wajan Lateefa. A rud'e ya d'agota yana jero mata tambayoyi..." Babyna meke damunki?,tun yaushe kike k'wance haka?" Da k'yar ta iya d'aga hannunta na dama ta nuna mishi kanta. K'wantar da ita yayi ya shiga cikin bathroom d'inta ya d'ebo ruwa a bowl da towel ya dawo kan gadon. Rage mata kayan jikinta yayi sannan ya fara goge mata jiki da ruwan sanyi,daga nan ya fita parlour zuwa inda suke ajiye first aid box ya had'o mata drugs harda na zazzab'i. K'ara d'agata yayi ya bata drugs d'in sannan ya k'wantar da ita yana ta mata sannu. Zuwa 30 mins bacci yayi awon gaba da ita,yana zaune ya zuba mata ido yana jin wani abu a zuciyarshi wanda baisan dame zai fassarata ba. Shi bai bar d'akin ba sai wajan karfe uku na asuba a lokacin jikin yayi sanyin sosai,haka ya wuce ba dan ranshi ya so ba. Koda ya dawo d'akin shi kaman yanda ya zata Lateefa bata nan,rannan dai bai wani samu baccin kirki ba. Kiran sallahn farko a kunnen Ameera,wanka ta farayi da ruwan zafi ko zataji dad'in jikinta .kuma ba laifi ta d'an ji dama-dama. Sallah tayi sannan ta zura doguwar riganta na atamfa ta zumbula hijab ta fito aiki. Haka kawai taji yau ranta ba abinda yake so kaman fresh milk,bata tsaya b'ata lokacinta wajan duba fridge d'in palourn ta ba saboda ya dade da zama empty rabonta dasu tun kamin Lateefa tayi nasara akansu. Tana zuwa main palourn ta bud'e fridge Allah ya taimake akwaisu aciki,guda 2 ta k'wasa ta wuce kitchen gudun kar wani ya ganta duk da tasan cewa yanzu ko sallah basuyi ba. Tana shiga kitchen kuwa ta kafa kai ta shanye k'wali d'aya sannannta fara aikinta cikin karfi hali dan har yanzu tana jin zazzab'in. Al'ameen shima da saboda rashin baccin da baiyi ba last night ya tashi da ciwon kai har da zazzab'i. Yana k'wance bayan yayi sallahn asuba basida niyan tashi bare yayi shirin office. D'ayan wayarshi da yake kusa dashi ya fara ringing d k'yar ya mik'a hannu ya jawo wayan. Sunan yayanshi Sa'ad ya gani yana yawo akan screen d'in dan haka ba b'ata lokaci yayi recieving call d'in yayi sallama. Amsa sallaman yaya Sa'ad yayi bayan yana ce masa ya biyo hospital d'inshi yana da magana dashi. " bros yau bazan fita office ba" ya bashi amsa. " why wat happend"ya buk'ata. Numfashi yaja yake cewa fever ce kawai yake d'an ji amma yanzu zai sha paracetamol. " don't u try dis kasan self madication ne nd u know i dont like it,just hold on gani nan zuwa" yana fad'an haka ya kashe wayan ba tare da ya jira amsan Al'ameen d'in ba. Duk da abinda yake ji a jikin shi amma bai hana shi murmusawa ba saboda yanda yayunshi suke ji dashi. Yana ajiye waya Lateefa ta shigo cikin k'walliyarta kaman mdi zuwa dinner sai baza kamshi take. Turus tayiganin Al'ameen still cikin bargo,k'arasowa tayi gaban gadon tana " my Ameen lafiya kuwa har yanzu baka tashi ba ?" " fever ce take son kamani "yace mata lokacin da take zama kusa dashi. Tashi tayi da sauri dan d'auko mishi magani ya dakatar da ita ta hanyan cewa "ya Sa'ad is on d way". Gaba d'aya ranta taji ya b'aci jin cewa Sa'ad zai shigo mata gida dan ita tun kamin auren su da taji ya kushe ta take jin haushin shi amma kuma koda wasa bata iya nunawa a gaban shi sabida duk rashin mututuncinta shakkan shi take. "Okay " kawai tace ta fice zuwa kasa ta sami Ameera tana goge-goge tana layi kaman zata fad'i. "Keee" ta daka mata tsawa,a razane Ameera ta juyo tare da durkusawa k'asa tace..." Aunty ina k'wana". A wulakance take dubanta tace" ke rik'e gaisuwarki kuma ki tattara ki wuce part d'inki nd kada ki kuskura ki fito sai na neme ki". Amsawa tayi da "toh" ta tashi ta wuce part d'inta tana godewa Allah cos atleast zata samu hutu koda kad'an ne kamin su nemetan. Wasu masu aiki ta kira suka cigaba da hidimomin gidan. Cikin 20mins Ya Sa'ad ya k'araso gidan hankali tashe. Sai da ya duba shi hankalin shi ya d'an k'wanta ganin cewa stress ne ya mishi yawa. Sama- sama suka gaisa da Lateefa,ya kama hanyan fita Lateefa har ajiyan zuciya ta saki na samun relief. Har ya kai bakin k'ofan fita ya dakata tare da juyowa yace..." bros ina amaryarka ne ban ganta ba? Ina ganin sau 1 na ganta lokacin da muka had'u da ku a gidan Hajiya har kamin alkawari zaku je mana yini muka ji shiru da alama rowanta kake" ya k'arasa cikin zolaya yana dariya. Lateefa ji tayi kaman ta shak'e shi ya mutu. Bata gama kulewa bama saida ta tsinci muryan shi yana ce mata " uwar gida kirawo min kanwar taki pls". Bata da bakin musu haka ta fita tana tsine mishi albarka. [3/24, 6:47 AM] Ummee Yusuf: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA~* 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman yusuf) *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u no pain~* *part twenty eight* A main palour suka yada zango anata hira da raha,Hajiya tasa 'yar aikinta ta gyarawa Ameera d'akin da zata zauna,cikin k'ank'anin lokaci ta gyara yayi fes. Nan Hajiya ta umarce ta shiga ta k'wanta ta huta. Bayan ta shiga Hajiya ta dube su tace..." ina son maganan nan a rufe shi anan ya zama tsakaninmu kad'ai zai tsaya,kaima Al'ameen ban yarda ka fad'awa matarka ba ka bari in lokaci yayi ta gani ina fatan kun fahimta ?" Duk amsawa sukayi da "eh sun fahimta kuma zasu kiyaye,a haka taro ya watse duk suka tafi gidajen su amma banda Al'ameen da ya mak'ale yaki tafiya. Yana ganin Hajiya ta shiga bedroom d'inta ya sulale yabi Ameera d'akinta. Yana shiga ya maida k'ofan ya rufe,a tsaye ya sameta fitowanta kenan daga wanka. Zuwa wajanta ya farayi idonshi akanta yana murmushi,yana k'arasowa ya jawota jikinshi ya rungume yana mata godiya. Had'e bakinsu yayi ya fara kissing d'inta har suka fad'a kan gado,sun dad'e a haka sannan ya sake ta ya d'ora kanta akan kirginshi yana shafata a hankali yace...",Babyna ranan da kika haifa min abinda yake cikinki bansan yanda zanyi ba dan farinciki da zanyi ba zai misaltu ba". Ita dai murmushi kawai take ta rasa bakin magana,saboda yanda taga duk sun rikice gaba d'aya saboda cikin dake jikinta toh ranan da d'an ya fito kuma fa? K'ara narkewa tayi a jikinshi cikin shagwab'a tace..." yayana yunwa nake ji amma fresh milk nake so mai sanyi" Kwatar da ita yayi akan gadon ya tashi yana " bari in dubo miki yanzu amma ya kamata kici wani abu saboda Ya Sa'ad yace kar a barki da yunwa". " ni dai koma menene ka had'o da fresh milk"tace tana gyara k'wanciyarta. Yana fita direct bedroom d'in Hajiya ya nufa lokacin tana shirin shiga wanka,ganin d'an autan nata yasa ta dakata tana dubansa. Yana shafa k'eya yace..."Hajiya me za'a samu ne a gidan?Ameera ce take jin yunwa". Fasa shiga wankan tayi ta dawo da baya tace..." yanzu nake shirin insa Altine ta kai mata abinci,ko akwai abinda tace tana son ci?" " komai ma zata iya ci sai dai wai a had'a mata da fresh milk" ya bata amsa. Girgiza kai Hajiya tayi tace..." banyi zaton akwai fresh milk a gidan nan ba,kayi maza kaje ka sayo mata ni kuma zan sama mata abinda zataci da kaina". "Toh" yace ya fita da saurinshi zuwa wani mall dake kusa da gidansu,caton 6 na fresh milk ya siyo ya dawo gida ya samu Hajiya tayi mata peppe soup na hanta da k'oda yaji kayan kamshi da yaji yanda mai ciki zata ji dad'in ci. Mai wankinsu Hajiya shi mallam tukur shi ya rink'a shigowa da kayan da Al'ameen ya sayo. Hajiya baki bud'e ta kallon catons na fresh milk d'in tace..." lalle Al'ameen d'aukin ne haka?ina mutum d'aya zai iya shanye wannan kayan duka?" Murmushi yayi yana sosa kai yace.."Hajiya aina zata tana bukatarsu dayawa ne". Dariya tayi tace..." hmmmm kai dai ka sani,yanzu ka bud'e 1 ka zuba a frdge daga nan kuma ga abincin can ka d'auka ka kai mata d'aki,kasan bata da lafiya kuma tunda cikin baiyi k'wari ba,bai kamata ace tana yawan zirga-zirga ba". Amsawa mata yayi sannan ya d'auki trayn abincn ya wuce d'akin ya sameta tana bacci abinta hankali k'wance. Ajiye kayan yayi a hankali ya fita zuwa masallaci dan gabatar da sallahn la'asar. Bayan ya idar da sallah ya dawo cikin gida tare da mahaifin shi,wajan frdge ya ya nufa ya bud'e ya d'auko k'wali 2 na fresh milk ya wuce d'akin Ameera dasu a hannu. Akan sallaya ya sameta ta tana sallah itama. K'arasawa yayi ya zauna a bakin gado yana jiran ta idar. Bayan ta sallame ta dube shi tace..." Yayana baka je office ba yau?" Jawota yayi ta fad'a jikinshi yace..." Babyna yau ba zancen zuwa office,ga babban office anan ". Murmushi tayi kawai ba tare da tace komai ba l. Saukowa yayi ya zuba mata peppe soup d'in a plate sannan yace..." Bismillah ga abinci harda fresh milk da kika bukata". Zamowa tayi itama ta zauna kusa dashi,sosai taci peppe soup d'in tana ta santi shi kuma yana zaune yana kallonta har saida ya tabbatar ta k'oshi sannan shima ya ci kad'an. Dariyarta yake yanda take shan fresh milk d'in har tana lumshe ido saboda santi. Tana k'wance a cinyanshi suna ta hira abinsu har 5pm. Knocking suka ji daga bakin k'ofa Ameera tayi saurin tashi daga jikin shi Al'ameen ya bada izinin shigowa. Hajiyace ta shigo ta dubi Al'ameen tace..." ka manta ne da tafiya gida yau?" "ban manta ba Hajiya" yace yana sosa kai. " tunda baka manta ba tashi ka tafi gida gashi har 5 ta gota". Agogon azurfa dake d'aure hannunshi yayi saurin dubawa yana cewa..." dama haka lokaci ya tafi ban sani ba?" " mu da bama son matarka ta gane in har kana zuwa ka dad'e haka zata iya sa zargin wani abu a ranta kuma bana so kazo ka takura min ita dan ta huta na dawo da ita gidan nan dan haka tashi ka wuce". [3/24, 6:47 AM] Ummee Yusuf: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA~* 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman yusuf) *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u no pain~* *part twenty seven* A parlour ta Tatar da Ameera a baje a k'asa har ta fara bacci wai dad'in sanyin tiles d'in take ji. K'afa tasa ta haure ta maimakon ta tashe ta,a firgice ta farka tana raba ido. K'ara rud'ewa tayi ganin Lateefa akanta tana aika mata da muguwar harara. Jiki na rawa ta durkusa ta fara bata hak'uri a zatonta tayi bacci mai nisa ne sosai har tayi laifi Dan bata manta maruka da tasha ba jiya. A wulakance ta d'aga mata hannu tace..." Keep quite idiot, me kika min da zaki ban hak'uri?ki wuce muje part d'in my Ameen Ku gaisa da yayan shi" Kamin Ameera ta samu bakin bata amsa taji an murd'e mata kunne da karfin tsiya sannan tace mata.." Saura kiyi misbehaving da zaki nuna halinki na jakuna a wajan,hmmmm kema kinsan sauran ba saina bata bakina ba". Tana fad'an haka ta dugure mata kai tayi gaba abinta. Da sauri ta mik'e tana gyara zaman hijabinta tabi bayanta tare da shafa kunnenta daya sha murd'a. Sun same su suna tsakiyar hira da dariya shida d'an uwan shi,Ameera tayi sallama ta durkusa daga bakin k'ofa tana gaishe shi.yayin da Lateefa ta wuce ba tare da sallama ba ta zauna a bakin gado tayi crossing legs d'in tana kad'asu. Ya Sa'ad Yana amsa gaisuwan tare observing d'in yanayinta a matsayin shi na doctor. Al'ameen yana daga k'wance yana kallonta ba bakin magana amma ji yake kaman yaje ya rungumeta ya tambaye ya jikinta. Suna gama gaisawa bata wani tsaya b'ata lokaci ba ta mik'e dan komawa part d'inta saboda ta kiyaye gargad'in da akayi mata. Tana tashi jiri ya kwashe ta sakamakon zafin zazzab'in dake dake jikinta ga cikinta tun jiya baiga k'wayar hatsi ba,saurin dafa bango da tayi shi ya hanata fad'uwa. "Subhanallah ba dai kema baki da lafiyan ba ya barki a gida?"ya Sa'ad ya tambsya Yana aikawa Al'ameen mugun kallo. Sadda kai k'asa yayi ganin Lateefa nayi mishi kallon warning ta k'asan ido. Ameera batace komai ba saima kokarin barin d'akin da tacigaba dayi. Dakatar da ita yayi da sauri ganin da gaske fitan zatayi.yace..." Wai meyasa kake Al'ameen? In kai Baka son hospital meyasa zaka bar iyalinka cikin irin wannan hali". Tsaki yaja yana mai mik'ewa yacewa Ameera da take tsaye waje 1 ta kasa gaba ta kasa baya " muje hospital in duba ki i can't tolarate dis". Yana fita Ameera bata tsaya bata lokaci ba ta mara masa saboda itama tana bukatar ganin doctorn. Yana zuwa bakin motan shi ya bud'e mata back seat ta shiga ta zauna ya rufe sannan ya zagayo ya bud'e driver seat ya zauna ya juya ya kalli k'ofan palourn yaga da gaske Al'ameen bashida niyan biyosu dan haka ya ciro wayarshi ya danna mishi k'ira a lokacin Lateefa tana zaune agefen shi tana mitan halin Ya Sa'ad kiran ya shigo wayarshi. Bai kulata ba ya d'aga wayan yasa a kunnen shi,kamin yayi magana yaji muryan yayanshi yana cewa.."fito muu tafi tare dan kaima ban gama da kaiba" yana gama fad'an haka ya katse k'iran tare da maida hankalin shi hanyan fitowa daga palourn. Ajiye wayan Al'ameen yayi tare da mik'ewa daga kan gadon,da ido Lateefa tabi shi har zuwa bakin closet d'inshi ya cire rigan baccin shi ya zura jallabiya milk colour akan wandon rigan baccin shi. Dawowa yayi bakin gado ya k'washe phones d'in shi yayi hanyar fita ba tare da yace mata cikanki ba. Da gudu Lateefa ta tari gabanshi tana aika mishi mugun kallo tace..." ina zuwa haka mallam?" " Ya Sa'ad ne yake k'irana" ya bata amsa yana murmushi saboda yasan ba yanda ta iya dashi. Wucewa yayi abinshi ya barta nan tsaye cike da tashin hankalin me zai faru in suka fita tare. Cike da farinciki Al'ameen ya fito kasancewar zuciyarshi ta k'wad'aitu da zuwa amma tsoro ya hana shi Allah ya kawo mishi hanya cikin sauki. Front seat ya bud'e ya shiga,Ya Sa'ad yaja mota suka bar gidan. Lateefa tana jin tashin motansu tayi bedroom d'inta cikin matukar tashin hankali ta k'ira Aina'u. Ringing 2 yayi ta d'aga tana " Hajiya a gidan Al'ameen ya akayine da sassafen nan?" "Aina'u ba lafiya wannan yayanshi mara mutuncin yana son rusa min aikina". Wani yayan shi kuma?" Aina'u ta tambaya. Nan Lateefa ta k'washe abinda ya faru ta fad'a mata sannan ta d'ora da cewa.." pls besty ina son yanzu kije gun boka ya rufe musu baki kar su iya furtawa kowa abinda yake faruwa,yanzu zan miki transfer ta acc d'inki". "Toh " tace tare da tabbatar mata da samun nasara sannan sukayi hanging. A hospital kuwa suna zuwa ya Sa'ad ya bata gado tare da jona mata drip wanda ya had'ata da alluran bacci a private room da yake duba familynsu kawai sannan ya fara dubata. Jininta ya d'eba ya bayar aje lab a g'wada yanzu-yanzu sannan ya fita a d'akin ya barsu. Al'ameen jawo kujeran roba dake gefe yayi zuwa gaban gadon ya zauna ya kallon yanda fuskarta tayi fayau ya k'ara haske tana bacci. Jikinshi yayi sanyi sosai ganin yanda Ya Sa'ad ya share shi tun a mota har zuwa yanzu,yasan fushi da yayi ba karami bane kasancewar shi baya fushi da wuri. Toh shi ya zaiyi ya fahimtar dashi ba laifinshi bane? Tsam ya mik'e da niyan zuwa office d'inshi dan ya gaya mishi halin da suka tsincin kansu shida Ameerar shi a ciki ko zasu samu mafita.a bakin k'ofa suka had'u dashi yana shigowa da wata peper a hannunshi fuskarshi kuwa kaman gonan auduga babu sauran fushin nan da ya fita dashi. Kallon mamaki Al'ameen ya bishi dashi har ya manta abinda yayi niyan gaya mishi. Hannunshi Ya Sa'ad ya rik'o suka dawo cikin d'akin har bakin gadon da Ameera take bacci,shi dai Al'ameen da ido yabishi yana neman karin bayani. Huggin d'inshi yayi yana furta " alhamdullilah!!!." Mik'awa Al'ameen papern yayi yana dariya wanda rabon Al'ameen da yaga yayi irinta har ya manta,kasancewar shi ba ma'abocin yin dariya bane sai dai murmushi. Karanta result d'in yayi amma kwata-kwata bai fahinci me yake nufi ba,idon shi inba gizo yake ba pregnany test ya gani kuma da sunan Ameera akai. D'agowa yayi yana kallon yayan nashi tare da neman karin bayani. "Yes bro ur wife is 2 months pregnant"ya kara tabbatar mishi. Wani yanayin da bai tab'a tsintan kanshi a ciki ba ba yau yake ji. Hawaye ne yake zuba a idonshi bakin shi yana motsi alamun yaña son yin magana amma ya kasa fidda sauti ko kad'an. Rungume Ya Sa'ad yayi yana hawayen farinciki,ashe shima yana da rabon ganin k'wanshi a duniya. Da k'yar Ya Sa'ad ya fitar dashi daga d'akin dan yana kokarin katsewa Ameera bacci wajan murna. Office d'inshi ya kaishi ya zaunar dashi sannan ya k'ira iyayensu yayi musu albishir na samun jika daga d'an autansu,daga nan kuma ya cigaba da kiran sauran 'yan uwansu suma ya sanar dasu duk cike farinciki suka ce gasu nan zuwa. Cikin k'ankanin lokaci suka cika hospital d'in anata taya juna murna kaman riga da anyi haihuwar. Ameera bata san wainar da ake toyawa tana ta baccinta,sai bayan sallahn azahar ta farka daga baccin. Har rige-rigen yi mata sannu suke duk sai taji kunya ya rufe ta ganin harda Hajiyar Al'ameen a ciki. Bayan tayi wanka tayi sallah,tea mai kauri Hajiya ta had'a mata tare da peppe soup na naman rago zallah sannan ta zo ta zauna a gefenta ta fara bata amma Ameera ta kasa sakewa taci abin kirki. Ganin haka yasa Hajiya tace duk su fita a barta ta samu taci abinci,ba musu duk suka fice tare da ja musu k'ofa. Al'ameen kaman jira yake suna fita ya taso da sassarfa ya rungumeta yana sauke ajiyan zuciya,ture shi Ameera ta fara tana cewa..." haba yayana ka bari mana kar wani ya shigo ya ganmu a haka". Ba tare da ya sake ta ba yace..." let me feel u Ameera yau ina cikin farinciki wanda ban tab'a tsintan kaina a ciki ba, bani kad'ai ba all my family re happy because of u". D'ago kanta tayi tana kallonshi taga idonshi duk yayi ja alamun hawaye zai iya saukowa at anytime. " ni kuma me nayi haka?"ta tambaya idonta itama yana cikowa da hawaye. Result d'in da yake rik'e dashi a hannu tun d'azu ya mik'o mata,karb'a tayi ta fara karantawa ai bata gama karantawa ba tayi jifa dashi ta rufe bakinta da hannunta na dama hannunta na hagu kuma tana yarfe shi tace..." na shiga 3 yanzu dukkansu sun sani?" Dariya ma ta bashi ganin yanda yarintarta ya fito a fili,maimakon yayi dariya yab'ata fuska yace..." kinga kuwa kowa ya sani har Hajiya saida tayi fad'a". Waro ido idonta tayi gaba d'aya tana kallonshi cikin tashin hankali can kuma ta fashe da kuka tana " wallahi ni ba zan zauna anan ba tafiyata zanyi". Kunshe dariyarshi yayi yace.." ki tafi ina? Ai kina tafiya kuma ace kinyi rashin kunya". Yarfe hannu ta cigaba dayi tana.." wayyo toh ya zanyi wai?" Haka ya rink'a zolayarta tana k'ara rud'ewa da k'yar ya. rarrasheta tayi shiru ,yace mata wasa yake mata tare suka ci abincin suna hirarsu cike da nishad'i. Bayan sun gama yana tattare wajan su Hajiya suka shigo suna k'ara mata ya jiki,ita kuma ji take kaman ta nutse k'asa saboda kunya. Ya Sa'ad ne yace..." Alhamdullilah jikinta kam yanzu da sauki zan sallame ta amma ba zan yarda Al'ameen ya tafi da ita gida ba saboda bashida kula zan kaita gidana incigaba da kula da ita har cikin yayi k'wari sannan zan yarda ta koma gidanta". Hajiya tayi caraf tace..." ban yarda da wannan idean ba, ni zan tafi da ita ta zauna a karkashin kulawata sai dai kullum ka rinka zuwa gida kana duba min ita". Nan yace "shikenan Hajiya ai duk 1ne". Al'ameen yana jinsu baisa baki ba amma zuciyarshi fari kal jin cewa ba zata koma cikin *UKUBAR* Lateefa ba kuma yana ganin k'ila su samu solution d'in matsalarsu kamin ta samu lafiya. Cikin 'yan mintina suka harhad'a kayansu sukayi gidansu Al'ameen. Alhamdullilah naji sauki sosai kuma ina mika gdy ta tare da jinjina ku my fans ,ina yinku irin sosai din na [3/24, 6:47 AM] Ummee Yusuf: 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA~* 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by ~UMMEE YUSUF~ (Maman Yusuf) *~GOLDEN PEN WRITER'S ASSOCIATION~*✨✨✨ https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~* *part thirty* Ameera suna shiga d'akin,d'an k'aramin fridge dake gefen gadon ta nufa ta bud'e ta d'auki fresh milk mai sanyi ta kafa kai bata d'aga ba sai da ta shanye shi tas. Al'ameen da yake zaune a kan kujera yana kallonta yace..."ke dai yanzu kina son wannan abin dayawa". Sai da ta sauke empty roban a bakinta sanna ta amsa mishi da..."wallahi yayana in bansha ba jina nake ba dai-dai nake ba kuma sai in rinka jina... "Turo k'ofan da akayi tare da sallama shiya dakatar da maganan da take. Altine ce ta shigo d'akin d'auke da katon tray da warmers akwai ta ajiye a kan rug dake tsakiyan d'akin tare da gaishe su,amsa mata sukayi fuska a sake. Fita ta k'arayi ta dawo da wani madaidaicin tray mai d'auke da tea flasks da plates da cups ta ajiye ta fice tare da rufo musu k'ofa. Kama hannunta yayi suka sauka k'asa inda Altine ta jera musu kayan breakfast. Al'ameen shi ya fara bubbud'e warmers d'in yana dubanta yace..." Me zaki ci in zuba miki?" "Zuba min pepper soup d'in saboda bakina yafi son Abu mai yaji". Zuba mata yayi a plate ta fara ci,shi kuma chips ya zuba suna ci suna hiransu. Al'ameen yace..." Babyna wai kin fad'awa su Umma rashin lafiyarki kuwa?" "Um-um " tace tana tura katon tsoka bakinta. "mesa baki fad'a ba?" Ya bukata. "Zan k'ira wayan Fateema anjima in fad'a mata sai ta gayawa Umma". " Fateema kenan sarkin rawan kai bansan meya hanata zuwa gidanmu ba"yace yana murmushi. Bata fuska tayi tace..." Hmmm tana son zuwa amma Abba ya hana dan ba abinda ya tsana kaman fita anguwa daga makaranta sai gida". Gyad'a kai yayi yana ajiye tea cup dake hannun shi yace..." Abba yana da gaskiya cos 'ya mace sai da kula". Bayan sun k'are cin abincin,k'wanciya yayi a cinyarta suka bud'e sabon shafin love. Ameera tana wasa da gashin kanshi tace..."yayana ka manta maganan Alhaji ne?" "Wanne magana kenan?" Ya tambaya yana b'ata fuska kaman mai tunani. Dariya tayi tana ture kanshi akan cinyarta tace..."kasan abinda nufi tashi ka tafi office ". Tashi yayi ya zauna suna facing juna ya rik'o fuskanta da hannayen shi yace..." Kora ta kike ko Babyna?" Zaro ido tayi tana kallon shi tace..." Na isa in kore ka....."bata samu daman k'arasa maganan ba sakamakon had'a bakinshi da nata da yayi. Sun jima a haka har yana k'okarin zarcewa Ameera ta k'wace kanta da k'yar tace..." Ka manta a gidanku muke?in Hajiya ta shigo ta same mu a haka fa?" Yana gyara riganshi yace..." Ni nasan ba wanda zai shigo nan koda k'wana zamuyi a cikin d'akin nan". Rau-rau tayi da ido cikin shagwab'a tace..." Yayana ka manta meya kawo mu nan ko sai kasa Hajiya ta koremu". " hmmm wai ke wayo ko?gashi daga zuwa gidan Hajiya kin warke". Ajiyan zuciya tayi tana kallon gefe tace..." Yayana ina su Aunty dash Fa'iza?" Had'a rai yayi kaman wanda aka gayawa sak'on mutuwa yace..." Muna zaune lafiya shine kike son b'ata min rai ko?" Matsowa tayi ta d'ora kanta akan kafad'an shi tace..."ba haka nake nufi ba kayi hak'uri dan Allah". Rungomota yayi ta gefe ya fara magana..."ki yafe min Ameera akan abubuwa da suke faruwa a gida bansan me yake faruwa dani ba musamman in a gaban Lateefa ne sai in rasa ina kaina yake ga kuma wani shakkarta da nake ji ko kallonki bazan iya yi aganta ba,wannan abu yana matuk'ar damuna.ina son in kika k'ira Umma tazo ki fad'a mata su taya mu da addu'a nima zan fad'awa su Hajiya". Hawaye na sauka a kan fuskarta tace..."abu d'aya muke fuskanta yayana Umma tana zuwa zan fad'a mata ta gayawa Abba ya taimaka mana da addu'oi". Suna cikin magana Ya Sa'ad ya shigo yana yiwa Al'ameen tsiya wai Baban twins. Shiko sai dariya yake yana amsawa da Allah yasa ya fad'a a bakin mala'iku. Bai jima ba ya duba Ameera tare kad'a kan Al'ameen suka fita tare. Bayan tafiyansu ne Ameera tayi dialling number Fateema,bai dad'e yana ringing ba ta d'aga tare da tambayan waye "Ke dallah Teema nice fa" Ameera ta amsa mata a d'ayan b'angaren. Ihu Fateema tayi cikin murna tace..." Sisto kece wayyo I missed u ina wayar ki take kika kirani da wannan?". Dariya Ameera tayi tace.." Ke kar ki cika min kunne,wayar Al'ameen ce. meya hanaki zuwa in kinyi missing d'ina da gaske?kuma ko a waya in ban kira ki ba,ba kya kirana". Marairaice murya Fateema tayi tana... " ya kike magana kaman baki san halin Abba ba?yanzu abin nashi ya kara gaba dan cewa yayi in muna yawan zuwa gidanki mutane zasu ce mun zuba k'afa a gidanki sabida k'wad'ayi munga mijiki mai kud'i,shiyasa baki ganni ba ". " toh shikenan ki bawa Umma wayan " . Fita tayi zuwa tsakar gida inda Umma take zaune tana gyara gyad'an miya,mik'a mata wayan tayi tace Ameera ce ta k'ira. Karb'a Umma tayi bayan sun gaisa Ameera take fad'a mata abinda ya faru, nan tayi mata Allah ya sauwake tare da alkawarin zasu zo gobe su dubata ita da Fateema. Cikin tsanin farincikin zata ga Ummarta ta tashi ta fito parlour wajan Hajiya kuma har tana aiyanawa a ranta matsalarta ya kusa karewa dan tasan Abba yana ji zaiyi wani abu akai. [3/24, 6:47 AM] Ummee Yusuf: 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA~* 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by ~UMMEE YUSUF~ (Maman Yusuf) *~GOLDEN PEN WRITER'S ASSOCIATION~*✨✨✨ https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~* *part twenty nine* Hajiya fita tayi ta barsu ganin Al'ameen ya tsaya nuku-nuku yaki fita. Tana fita ya kamo hannayenta duka 2 ya matse acikin nashi yana kallon cikin idonta yace..."Baby zan tafi sai kuma gobe in na dawo,ina son ki kula da kanki da kuma babyn mu". Gyad'a mishi kai tana murmushi ba tare da tace komai,kissing d'in goshinta yayi sannan yasa hannu ya shafa shafaffen cikinta a hankali ya mik'e ya fito parlour yayiwa iyayen shi sallama ya kama hanyan gida shida drivern Alhajin shi. Shida saura driver yayi parking a compound d'in gidan,Al'ameen cike da fargaban me zai cewa Latifa ya sauka ya nufi cikin gida. A main parlour ya tadda ta zaune tayi crossing legs d'inta tana kad'asu,cikin rawan murya yayi mata sallama wanda bakinshi ne kad'ai ya motsa amma babu sautin da ya fito balle mutum yaji,amma ga mamakinsa yaga ta taso da murnanta ta tare shi tanayi mishi ya jiki? Har cikin bedroom d'inshi ta raka shi ta had'a mishi ruwan wanka sannan tace ya shiga yayi wanka. Ba musu ya shiga wankan kuma sai a lokacin ya tuna ashe through out yau baiyi wanka ba farincikin cikin dake jiikin Ameera ya mantar dashi komai. Ita kuma Lateefa fitowa tayi ta barshi fuskarta d'auke da murmushin mugunta dan tunda rana Aina'u ta kirata ta fad'a mata sak'on boka,ya tabbatar mata da kulle bakinsu da yayi kuma yace ta kwantar da hankalinta kaman yanda suka zo suka tafi da ita haka zasu dawo da ita da kansu. Bayan sallah isha'i suka zauna yin dinner amma sai yaji abuncin ba dad'i Sam saboda yanzu ya saba da girkin Ameerarsa amma gudun masifar Lateefa yasa ya tuttura harda santin karya. Koda suka dawo parlour suka zauna hira nan ma Al'ameen sam hankalin shi baya jikinshi yana wajan Ameera har ta kai Lateefa ta fara tsarguwa tace..." My ameen lafiya kuwa na ganka yau wani iri ko dai jikin ne har yanzu?" Yak'e yayi mata wanda dashi g'wara babu yace..."eh jikin ne kuma gobe da sassafe muna important meeting shiyasa nake son k'wanciya da wuri ". " ya kamata kaje ka k'wanta tun yanzu Dan karka makara". Tun kamin ya mik'e ta riga shi dama kaman jira take tana Hamma tace..."nima dama baccin nake ji kuma ina son yin nafilan cikin dare,"tana fad'an haka tayi hanyan part d'inta. Da kallon takaici ya bita,baisan ranan da zata canza ba.gashi dai bashi da lafiya maimakon ta tsaya ta kula fashi shine tayi tafiyarta ta barshi. Bedroom d'inshi ya shiga shima ya hau makeken gadon shi ya k'wanta,wayarshi ya jawo ya dannawa Ameera k'ira,a lokacin ta fara bacci taji ringing d'in wayar shi da ya bar mata kafin ya tafi. Bata bukatan duba screen d'in wayan saboda tasan mai k'iran nata. A kasalance ta d'aga wayan tasa a kunnenta a shagwab'ance tace..." Assalamu alaikum". "Sorry Babyna kin fara bacci na tashe ki ko?" K'ara narkar da murya tace..."eh yayana kasan drugs da aka bani harda na bacci a ciki". Cikin muryan rarrashi yace..." Koma kiyi baccinki dama na k'ira ne inji lafiyarku keda Babynmu". Cikin jin dad'in yanda yake nuna kulawar shi a gare ta tace..." Lafiya lau muke tunda muna da kamar kai dole mu kasance natsuwa da k'wanciyar hankali". Murmushi ya sake kaman tana ganinshi kana ya d'ora da cewa" k'wanta kiyi bacci Babyna saina zo da safe" nan sukayi sallama ta koma baccinta mai dad'i cikin k'wanciyar hankali. Da washe gari da sassafe Al'ameen ya shirya ya fice daga gidan Lateefa ko tashi batayi ba balle tasan ya k'wana. Direct gidansu ya nufa ganin babban parlourn ba kowa ya tabbatar mishi masu gidan suna bacci. Bedroom d'in Ameera ya wuce kai tsaye ya murd'a handle d'in ya bud'e ya shiga ya mayar da k'ofan ya rufe a hankali harda murza key. Baccinta take cikn bargo ta kudundune kaman mai jin sanyi. " sleeping beauty " yace yana rage kayan jikinshi. Hulan kanshi ys fara cirewa sai kuma riganshi ta shadda d'inkin tazarce shima ya cire ya zama daga shi sai vest da dogon wandon shi,hayewa gadon ya k'wanta kusa da ita. Jawota yayi jikinshi ya gyara mata k'wanciya akan faffad'ar kirjinshi,yasa d'ayan hannunshi kuma ya rungumota sannan yaja musu bargo ya lullub'e su dashi.da yake shima baccin shi na jiya rabi da rabi ne,nan da nan bacci mai dad'i yayi awon gaba dashi. Tara saura k'wata Ameera ta farka daga bacci sakamakon wata azabbabiyar yunwa da ya addabeta. Ganinta tayi mak'ale akan kirjin mijinta,cike da so da k'auna take kallonshi kuma lokaci guda ta cika da mamaki da ta tuna cewa ba gida d'aya suka k'wana ba.yaushe yazo kuma? Ta tambayi kanta kuma ta rasa mai bata amsa. Bata son katse mishi bacci sakamakon ganin yanda yake jin dad'in baccinsa,maida kanta tayi a hankali ta k'wanta tana kallonshi har agogon d'akin ya buga karfe tara cif. A lokacin ne kuma dauriyarta ya k'are,ya kamata ta nemi wani abu tasa a bakinta dan yanzu a yanda take jin yunwan gani take in ta k'ara minti 5 zata iya halaka. A hankali ta fara raba jikinta da nashi ta yanda take ganin ba zai farka ba but tun kafin ta gama raba jikinta da nashi taga ya bud'e ido yana kallonta tare da murmushi akan fuskarshi yace..." Kin farka Babyna". Gyad'a kai tayi tana maida mishi martanin murmushi tace..."yaushe kazo ne Yayana,kodai anan muka k'wana tare?" 'Yar dariya ce ta subuce mishi yace..." Da safen nan nazo na tadda gidan duk kuna bacci sai masu aiki kawai Nagani suna aikinsu,nima dama da baccin nazo shiyasa kiga na kwanta.hala bakiyi sallahn asuba ba ko?" Shafa gefen fuskanshi tayi sanna tace.." Haba wani baccine da zai hani sallah asuba akan lokaci,amma kai me ya hanaka baccin?" Lakace mata hanci yayi yace..." Tunanin ki da Babyn mu shi ya hana ni bacci". Rau-rau tayi da ido kaman me shirin kuka tace..." Haba yayana ka rinka bacci mana bayan kasan muna lafiya karkashin kulawar Hajiya,kuma kaima kasan rashin bacci yana da illah ko?". "I know Babyna ayi min afuwa na daina " ya k'arasa maganan yana rik'e kunnuwansa duka 2. Fari tayi da ido tana kokarin mik'ewa ya rik'eta yace "ina zaki je?" " wanka zanyi" ta amsa a takaice. Mik'ewa yayi shima yana harararta da wasa yace..." Shine bazaki jira muyi tare ba? "Rabonmu da wanka tare tun yaushe?"tace a cikin zuciyarta amma a zahiri dariya tayi ta juya da niyan shiga bathroom d'in abinta. Taku 2 tayi kawai sai ji tayi an d'aga ta cak an nufi bathroom d'in da ita. Sai cikin bathroom ya direta,suka fara wanka tare da wasanni Bayan sun fito daga wanka ya tayata shafa mai ya shiryata cikin kaya na alfarma da Hajia tasa aka kawo mata su tun last night sannan suka fito babban parlour suka tafda iyayen nasu akan table sun gama break fast suna hira. Zubewa suka yi a k'asa suka k'washi gaisuwa,cikin jin dad'i da kulawa suke amsa musu. Wannan yana cikin abinda yasa suke k'ara sonta,akwai ta da natsuwa da bawa na gaba girma. Hajiya ce tace..." Wai kai yaushe ka shigo ne banga wucewarka ba?" Shafa suman kanshi da yasha gyara yayi yace..." Ai lokacin dana shigo baku fito ba shiyasa na wuce ". Alhaji ma cewa yayi..." Yau dai a daure a lek'a office d'in nan " "Eh zan tafi dama na tsaya ne Mu gaisa sai in wuce" yace yana mik'ewa kaman da gaske. Hajiya ce ta katse shi ta hanyan cewa..." Tsaya bari insa Altine ta kai muku break fast,tace dazu taje bata tashi ba k'ofan a rufe. Mik'ewa sukayi suka koma d'akin Ameera bayan sun amsa da "toh". Pls kuyi min afuwa kunjini shiru na kwana 2 saboda wasu dalilai da suka fi karfina,amma insha Allah daga yanzu zaku rinks ganin post kullum.tnx 4 ur luv and care. [3/22, 9:04 PM] 0mmer Farouk: 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA~* 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by ~UMMEE YUSUF~ (Maman Yusuf) *~GOLDEN PEN WRITER'S ASSOCIATION~*✨✨✨ https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~* *part thirty* Ameera suna shiga d'akin,d'an k'aramin fridge dake gefen gadon ta nufa ta bud'e ta d'auki fresh milk mai sanyi ta kafa kai bata d'aga ba sai da ta shanye shi tas. Al'ameen da yake zaune a kan kujera yana kallonta yace..."ke dai yanzu kina son wannan abin dayawa". Sai da ta sauke empty roban a bakinta sanna ta amsa mishi da..."wallahi yayana in bansha ba jina nake ba dai-dai nake ba kuma sai in rinka jina... "Turo k'ofan da akayi tare da sallama shiya dakatar da maganan da take. Altine ce ta shigo d'akin d'auke da katon tray da warmers akwai ta ajiye a kan rug dake tsakiyan d'akin tare da gaishe su,amsa mata sukayi fuska a sake. Fita ta k'arayi ta dawo da wani madaidaicin tray mai d'auke da tea flasks da plates da cups ta ajiye ta fice tare da rufo musu k'ofa. Kama hannunta yayi suka sauka k'asa inda Altine ta jera musu kayan breakfast. Al'ameen shi ya fara bubbud'e warmers d'in yana dubanta yace..." Me zaki ci in zuba miki?" "Zuba min pepper soup d'in saboda bakina yafi son Abu mai yaji". Zuba mata yayi a plate ta fara ci,shi kuma chips ya zuba suna ci suna hiransu. Al'ameen yace..." Babyna wai kin fad'awa su Umma rashin lafiyarki kuwa?" "Um-um " tace tana tura katon tsoka bakinta. "mesa baki fad'a ba?" Ya bukata. "Zan k'ira wayan Fateema anjima in fad'a mata sai ta gayawa Umma". " Fateema kenan sarkin rawan kai bansan meya hanata zuwa gidanmu ba"yace yana murmushi. Bata fuska tayi tace..." Hmmm tana son zuwa amma Abba ya hana dan ba abinda ya tsana kaman fita anguwa daga makaranta sai gida". Gyad'a kai yayi yana ajiye tea cup dake hannun shi yace..." Abba yana da gaskiya cos 'ya mace sai da kula". Bayan sun k'are cin abincin,k'wanciya yayi a cinyarta suka bud'e sabon shafin love. Ameera tana wasa da gashin kanshi tace..."yayana ka manta maganan Alhaji ne?" "Wanne magana kenan?" Ya tambaya yana b'ata fuska kaman mai tunani. Dariya tayi tana ture kanshi akan cinyarta tace..."kasan abinda nufi tashi ka tafi office ". Tashi yayi ya zauna suna facing juna ya rik'o fuskanta da hannayen shi yace..." Kora ta kike ko Babyna?" Zaro ido tayi tana kallon shi tace..." Na isa in kore ka....."bata samu daman k'arasa maganan ba sakamakon had'a bakinshi da nata da yayi. Sun jima a haka har yana k'okarin zarcewa Ameera ta k'wace kanta da k'yar tace..." Ka manta a gidanku muke?in Hajiya ta shigo ta same mu a haka fa?" Yana gyara riganshi yace..." Ni nasan ba wanda zai shigo nan koda k'wana zamuyi a cikin d'akin nan". Rau-rau tayi da ido cikin shagwab'a tace..." Yayana ka manta meya kawo mu nan ko sai kasa Hajiya ta koremu". " hmmm wai ke wayo ko?gashi daga zuwa gidan Hajiya kin warke". Ajiyan zuciya tayi tana kallon gefe tace..." Yayana ina su Aunty dash Fa'iza?" Had'a rai yayi kaman wanda aka gayawa sak'on mutuwa yace..." Muna zaune lafiya shine kike son b'ata min rai ko?" Matsowa tayi ta d'ora kanta akan kafad'an shi tace..."ba haka nake nufi ba kayi hak'uri dan Allah". Rungomota yayi ta gefe ya fara magana..."ki yafe min Ameera akan abubuwa da suke faruwa a gida bansan me yake faruwa dani ba musamman in a gaban Lateefa ne sai in rasa ina kaina yake ga kuma wani shakkarta da nake ji ko kallonki bazan iya yi aganta ba,wannan abu yana matuk'ar damuna.ina son in kika k'ira Umma tazo ki fad'a mata su taya mu da addu'a nima zan fad'awa su Hajiya". Hawaye na sauka a kan fuskarta tace..."abu d'aya muke fuskanta yayana Umma tana zuwa zan fad'a mata ta gayawa Abba ya taimaka mana da addu'oi". Suna cikin magana Ya Sa'ad ya shigo yana yiwa Al'ameen tsiya wai Baban twins. Shiko sai dariya yake yana amsawa da Allah yasa ya fad'a a bakin mala'iku. Bai jima ba ya duba Ameera tare kad'a kan Al'ameen suka fita tare. Bayan tafiyansu ne Ameera tayi dialling number Fateema,bai dad'e yana ringing ba ta d'aga tare da tambayan waye "Ke dallah Teema nice fa" Ameera ta amsa mata a d'ayan b'angaren. Ihu Fateema tayi cikin murna tace..." Sisto kece wayyo I missed u ina wayar ki take kika kirani da wannan?". Dariya Ameera tayi tace.." Ke kar ki cika min kunne,wayar Al'ameen ce. meya hanaki zuwa in kinyi missing d'ina da gaske?kuma ko a waya in ban kira ki ba,ba kya kirana". Marairaice murya Fateema tayi tana... " ya kike magana kaman baki san halin Abba ba?yanzu abin nashi ya kara gaba dan cewa yayi in muna yawan zuwa gidanki mutane zasu ce mun zuba k'afa a gidanki sabida k'wad'ayi munga mijiki mai kud'i,shiyasa baki ganni ba ". " toh shikenan ki bawa Umma wayan " . Fita tayi zuwa tsakar gida inda Umma take zaune tana gyara gyad'an miya,mik'a mata wayan tayi tace Ameera ce ta k'ira. Karb'a Umma tayi bayan sun gaisa Ameera take fad'a mata abinda ya faru, nan tayi mata Allah ya sauwake tare da alkawarin zasu zo gobe su dubata ita da Fateema. Cikin tsanin farincikin zata ga Ummarta ta tashi ta fito parlour wajan Hajiya kuma har tana aiyanawa a ranta matsalarta ya kusa karewa dan tasan Abba yana ji zaiyi wani abu akai. [3/24, 4:15 PM] Ummee Yusuf: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman Yusuf) *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u no pain~* *part thirty one* A parlour ta iske Hajiya da wata bak'uwarta suna hira,durkusawa tayi har k'asa ta gaida bak'uwar sannan ta samu waje a kasa ta zauna. Hajiya ta b'ata fuska tana dubanta tace..."ya zaki zauna a k'asa ki hau kan kujera ki zauna". Batayi gardama ba ta hau ta zauna, ganin yanda Hajiya ta b'ata fuska. Bak'uwar tana murmushi tace..." Hajiya bak'uwa kikayi ne bangane ta ba". " asama'u kenan amaryar d'an auta nane baki gane ba?"Hajiya tace itama tana murmushin. Wacce aka k'ira da Asma'un ta k'ara fad'ad'a fara'ar fuskanta tace..."Allah sarki itace wacce mukayi bikin k'wanakin baya ko?" Kamin Hajiya ta bata amsa ta cigaba..." Ke yanzu kinga laifina ya za'ayi in gane ta tunda shi Al'ameen d'in kanshi rabon shida gidana sai ince yafi shekara goma bare matansa". " kada ki damu zai kai miki su ku yini insha Allah " Hajiya tayi assurance d'inta. Ameera dai tana jinsu bata ce komai ba saida Hajiya ta gabatar mata da matan a matsayin k'awarta ce tun suna secondary school. Kasa sakewa tayi tare dasu dan haka bata dad'e da zama ba ta tashi ta koma d'akinta ta k'wanta. Sai bayan shiganta ne Hajiya takewa Asma'u bayani game da Ameera,nan ta taya su murna tare da addu'an Allah ya raba lafiya. Bayan sallahn azahar misalin biyu da rabi saiga Al'ameen ya kasa zaman office ya dawo gida. Koda Hajiya ta fara mishi fad'an meyasa ya dawo lokacin tashi baiyi ba,marairaice fuska yayi yace zazzabine yake son rufe shi shiyasa ya dawo. Sannu ta shiga jera mishi tace..." Ya sha paracetamol ya k'wanta ya huta. Karb'an maganin yayi yana Jan k'afa shi a dole ga mara lafiya ya wuce d'akin Ameera. Dariya Hajiya tayi tana girgiza kai tace..." Wai ni zaiyiwa dabara". Sallama yayi ya tura k'ofan ya shiga,baki bud'e Ameera take kallon shi har ya maida k'ofan ya rufe. Ajiye brief case d'inshi akan kujera yayi ya juyo yana kallon yanda ta sake baki tana kallon shi ga abinci a gabanta ta bud'e da niyan zubawa amma ta kasa. Gabanta yazo ya tsuguna yasa hannun shi ya rufe mata bakin yace..." Rufe bakin mana 'yan matana". D'an had'a rai tayi tare da kawar da kanta gefe tace..." Haba Yayana yaushe ka bar gidan nan da zaka k'ara dawowa,na lura so kake Hajiya ta kore mu a gidanta mu huta". Rungumota yayi ta baya tare da kissing d'in wuyanta yace..."haka ake taran miji Babyna tunda baki saba gani a gida by dis time ba ai kamata yayi ki tambaye ni ko lafiya,ko kin manta tare muka fara laulayin ne in tuna miki?" Kunya maganar shi ta karshe ya bata ta rufe idonta da hannu tana dariya,cakulkuli ya fara mata shima yana taya ta dariyan. Saida suka gama wasannin su,sannan ta zuba musu abincin suka fara ci.sai zuba yajin daddawa da Hajiya ta aiko mata take tana ci har tana lumshe ido. "Kasa yajin kaji yafi dad'i wallahi" tace tana k'ara zubawa a gabanta. Girgiza kai yayi yana..." Um-um ci kayanki da alamu me kada'i Hajiya ta aikowa". A ranan ma ba bai bar gidan ba saida Hajiya ta kora sannan ya tafi gida badan ranshi yaso ba. Da washe gari misalin sha biyun rana Umma da Fateema suka iso gidansu Al'ameen duba Ameera. Albarkacin hutu na k'wana 2 da tasamu a gidan Hajiya yasa tayi d'an dama-dama,raman da tayi shi kuma sun danganta shi da zazzabin da take.dan haka Umma bata kawo komai a ranta ba. Hannu bibbiyu Hajiya ta sauke su,nan da nan Altine ta cika gabansu da kayan sanyi dana marmari. Ameera dad'i kaman ya kashe ta yau taga Ummarta. Bayan sun gaisa Ameera taja hannun Fatima zuwa d'akinta dan su d'an taba hira,suka bar Umma tare da Hajiya suna hira Haka baje suna yi can Fateema tace.." Naji jiya kina complain akan zuwa gidanki Wallahi Ameera kullum ina son zuwa amma Umma da Abba suke hanani wai gaki da abokiyar zama kuma mutane zasu ce Dan kin auri mai kud'i shiyasa muka zuba k'afa gidanki tunda muna jinki a ways aiya wadatar". "Ni dai tunda ita Umma tunda ita ba zuwa take ba ai ya kamata ke kina zuwa koda sau 1 a wata ne,amma zanyiwa Umma magana ana barinki". Cikin jin dad'i Fateema tace..." Good sister". Ameera tunda suka shigo d'akin take yunkurin fad'awa Fateema abinda yake cinta a rai amma ta kasa daga tayi niyya sai taji bakinta yayi nauyi,hak'ura tayi suka cigaba da hiransu. Bayan sallahn azahar Umma ta shigo d'akin Ameera su d'an zanta kamin su tafi,nan ma Ameera tayi-tayi ta kasa fad'awa Ummanta komai tana ji tana gani sukayi mata sallama suka tafi. Kuka tayi sosai bayan tafiyansu har saida taji kanta yana ciwo kaman ya rabe 2 sannan ta rarrashi kanta tayi shiru. Tana magana cinkin ranta.. Wannan wani irin rayuwa ce ace ke da gidan mijinki ki koma tamkar baiwa?ita da za'a shawarceta sai tayi zamanta an an yafi mata zama a can,nan Hajiya tana kula da ita kaman k'wai ga uwa uba samun kulawan mijinta da take samu a koda yaushe sab'anin gidanta da ko ganinahi batayi sai dai ya saci k'afa yazo ya dubata tsakiyar dare. K'iran sallahn la'asar da taji anayi yasa ta mik'e ta fad'a bathroom tayi wanka tare da d'auro alwala. Saida ta tsaya ta d'an tsara make up dan bata son Al'ameen ya fahimci halin da take ciki. Ta idar da sallahn la'asar amma bata tashi akan pray mat d'in ba tana zaune tana tunani Al'ameen yayi sallama ya shigo. Suna had'a ido suka sakarwa juna murmushi. " ya jikin Babyna?"ya tambaya a lokacin da yake zama a bakin gadon yana facing d'inta. "Alhamdullilah da sauki " ta amsa mishi lokacin da take zama kusa dashi," ya aiki zance koya office zance?" " huuh all d same ba sauki dan yanzuma gudowa nayi saboda aiki ya min yawa". Haka rayuwar Ameera tayi ta gudana a gidan Hajiya dan yau satin ta d'aya da zuwa taji sauki sosai kuma ta murmure kaman ba ita ba . Bayan sallahn la'asar as usual Al'ameen ya dawo daga office suna zaune suna hiransu Hajiya ta aiko tana k'iransu. Ba b'ata lokaci suka iske ta a parlour tana zaman jiransu,waje suka samu suka zauna. Hajiya ta tattaro hankalinta gare su kana tace..." Ameenu ina son yau d'in nan Ameera ta koma gida tunda taji sauki saboda bana son Lateefa ta fahimci abinda yake faruwa". Kirjin Ameera ne ya buga da karfin gaske jin furucin Hajiya, ta saci kallon Al'ameen taga yayi k'asa da yana son sanar mata halin da suke ciki shima ya kasa cewa komai. Hajiya ta juyo ga Ameera tace..." Ina son ki kula da kanki sosai in kin koma gida,kada ki kuskura kiyi sakacin da zata gane cewa juna 2 gare ki,ina son ki yawaita saka Mayan hijabai saboda wasu dalilai.kin fahimce ni ko? " Kasa motsa labb'anta tayi saboda nauyin da suka mata dan haka da kai ta amsa mata. Al'ameen shima kasa magana yayi,tace..." Kai ka tafi yanzu anjima da daddare zan kawo ta da kaina". Amsawa yayi ya tashi jiki a mace ya koma d'akin Ameera dan d'auko hulan da car keyn shi. Ameera bata motsa daga inda take ba Hajiya tace..." Tashi kije ki fara had'a kayanki kamin lokaci yayi". Mik'ewa tayi sum-sum kaman wacce k'wai ya fashewa a ciki tabi bayan shi. Hajiya taso ta fahimci wani abu amma ganin basuyi mata bayanin komai ba yasa ta kawar da zargin da yake ranta. Pls masu korafi kuyi hakuri kubi novel din a sannu zaku gane wani sako name son isarwa. [3/26, 7:05 PM] Nabeelah Shu'aib: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman Yusuf) *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u no pain~* *part thirty two* Yana zaune a bakin gado yasa hannayen shi duka biyu ya rike kanshi dasu yana kallon k'asa. Bud'e k'ofan da Ameera tayi shiya dawo dashi hayyacin shi daga duniyar tunani da ya fad'a,suna had'a ido kowannensu ya kakalo murmushi yake na son kawar da damuwa ga junansu. Tsayawa tayi a bakin k'ofa ta hard'e hannayenta a kirji tace..." Ya naga ka zauna bayan kuma tafiya ya kamata kayi?" Da hannu ya mata alama tazo,zuwa tayi a hankali ta zauna a gefen shi,kamo hannayenta tayi duka 2 ya rike cikin nashi yana kallonta da idanuwansa da suka rine da fari zuwa ja yace..." Ameera bana son komawarki gidan can nafi son ki zauna a nan ko in saya miki gidanki daban yanda zaki zauna cikin k'wanciyar hankali har Allah ya sauke ki lafiya,I tried to tell Hajiya amma bansan meyasa ba na kasa fad'a mata komai " ya karasa maganan cikin matukar damuwa. Murmushi kwance a kan fuskanta take dubanshi tace..." Karka damu yayana tunda Hajiya tace in koma zan koma mu zauna nasan nan da d'an lokaci komai zai daidaita". Har yanzu fuska ba fara'a yake kallonta ya fara magana..."gaskiya na riga na yanke hukunci baza ki koma gidan nan ba ". Cikin muryan rarrashi da k'wantar da murya tace..." Kayi hak'uri in koma saboda kada Hajiya taga kaman mun tsaba umarninta,beside na fad'awa Umma na tabbatar zata taya mu da addu'a "haka tacigaba da tausan da kalamai da tasan zai k'wantar mishi da hankali har saida taga ta sama mishi natsuwa tare da danne nata damuwan, ko kad'an bata yarda yaga wani abu a fuskan ta ba illah murmushi dake tashi a kyakkyawar fuskarta Bayan fitarsa ta kama hada kayanta tana mai zubar da hawaye saboda tausayin kanta da Kanta take ji, dama ya ta kare kuma bare ace lateefa taji labarin juna biyu gareta? girgiza kai tayi ta cigaba da had'a duk wani abu nata. Bayan sallahn isha'i Hajiya tasa ta a gaba suka kama hanyan gidanta zuciyarta sai dukan 3-3 yaje,a mota Hajiya sai k'ara jaddada mata ta kula da kanta har suka isa gidan . A parlour suka iske Al'ameen da Lateefa suna kallo,hannu 2-2 Lateefa ta karbe su harda rungume Ameera a gaban Hajiya wai tayi missing d'inta. Hajiya bata bar gidan ba saida ta had'asu tayi musu nasiha mai ratsa jiki wanda Lateefa yake shiga 1 kunne ya fita ta 1. Bata wani dad'e ba a gidan ta mik'e dan ta koma gida, suma duk suka mik'e dan yi mata rakiya " koma ki huta Ameera keda baki gama warwarewa ba" Hajiya tace mata. Ba tayi gardama ba ta koma ciki dama tana tsoron zama cikinsu bata san wani rashin mutuncin zasuyi mata ba bayan tafiyan Hajiyan. Lateefa kuma ta k'asa take hararar Hajiya a zuciyarta tana zanyi maganinku duka. Direct part d'inta ta wuce cikin sauri ta bud'e k'ofa ta shiga ta mayar ta rufe tare da jingina a jikin k'ofan,wasu zafafan hawaye ne suka gangaro mata data tuna yanzu wani hali zata shiga. A nan ta zube tasha kukanta na tausayin kanta da kanta ta more da kyar ta rarrashi kanta ta mik'e zuwa cikin bedroom d'inta. Wanka kawai tayi ta haye gadonta ta kwanta zuciyarta a cunkuse. Da washe gari da sassafe ta tashi ta nufi kitchen kaman yanda ta saba,dama Lateefa tun cikin dare ta sanar da masu aiki dawowar Ameera kuma ta umarce su da su sakar mata aiyukan gidan. Duk da Lateefa ta hana su bai hana Rabi fitowa dan taya taba saboda har cikin zuciyarsu suna tausaya mata sosai. A zaune ta same ta a cikin kitchen d'in tana firen dankali, Ameera da saurinta ta karaso cikin kitchen d'in tana cewa "haba Rabi ba kya gudun laifina ya shafe ki?" D'an tsagaita firan Rabi tayi ta d'ago tana kallonta fuskarta cike da fara'a tace..." nasan suna bacci a wannan lokacin balle inji tsorin zasu fito su same ni anan,dan haka ki k'wantar da hankali ki ba abinda zai faru sai alkhairi". K'arasa shigowa ciki tayi tana jin hawaye na taruwa a idonta,kusa da ita tazo ta durkusa tace..." Nagode Rabi da taimakon da kike min a gidan nan,dame zan taimaka miki yanzu dan mugama da wuri?" " d'auko d'anyan kifi a friji ki wanke min kamin in gama firan"tace tana cigaba da aikinta. Murmushi kawai Ameera tayi ta juya zuwa deep freezer ta bud'e ta d'ebo su yanda tasan zasu ishi gidan . Wanke su ta farayi a sink d'in cikin kitchen,k'arnin kifin ne ya fara damunta sosai har ya haddasa mata tashin zuciya lokaci d'aya,duk dauriyanta amma saida amai ya kwace mata ba shiri. Rabi dake firan dankali bata san lokacin da tayi cilli da wukan hannunta ba tazo da gudu ta riketa tana yi mata sannu. Da'kyar ta samu ya tsaya,wanke fuskanta tayi tare da kuskure bakinta tana maida numfashin wahala. Akan kujera Rabi ta zaunar da ita tace..." Zauna anan bari ni zan karasa aikin". Jingina tayi da kujeran ta lumshe ido saboda yanda take jin cikin ta yana wani irin murd'a. Lemun tsami Rabi ta d'auko mata a frdge ta bata tace..."ki sha wannan zaki ji saukin tashin zuciyan. Bata musa ba tasa hannu ta karba ta fara shan lemun. Rabi kuwa duk Rabin hankakinta yana kanta,tana aikinta kuma ta na juyowa tana kallonta fuskarta d'auke da murmushi sakamakon ta riga ta gane cutar Ameera. Dan Rabi ba karamar mace bace a kalla zatayi 37 years a duniya. Cikin ikon Allah Ameera taji saukin tashin zuciyan amma hakan baisa ta daina shan lemun ba saboda dad'i yayi mata sosai dan kwata-kwata bata jin tsamin saima wani zaki-zaki da taji lemun yana yi mata. Suna aikinsu suna hira sai gashi sun gama cikin k'ank'anin lokaci. Bayan sun zuzzuba a warmers Rabi tace..." Toh bari in tafi kar su shigo". Godiya Ameera tayi mata sannan ta kama hanyan fita, har ta kai bakin k'ofa ta juyo fuskanta d'auke da fara'a tace..." Hajiya ina taya ki Murna ". Da wuri Ameera ta waigo tana dubanta cike da fargaban me zata ce mata ta tako a hankali zuwa gabanta tace..." Murnan meye Rabi kike tayani dashi?" Rabi bata daina murmushi ba tace..." Hajiya ga dukan alamu juna 2gareki". Zuciyarta ne ya buga da karfi,ashe dai ana ganewa da ake cewa ta boye? Baki na rawa tace..."yanzu kowa ya gani zai gane?" Rabi ta fahimci damuwar da take ciki dan tace... " ki k'wantar da hankali ki ba mai ganewa a gidan nan tunda ba wacce ta tab'a haihuwa a cikin su balle su lura da canzawarki,ni kaina amai da kika yi a gabana shiya tabbatar min da hakan sai dai ina baki shawaran ki guji Inda suke ki nisance su sosai dukda dama ba wata alaka bace tsakaninku kinji?Allah zai kare ki daga sharrinsu kuma Allah ya sauke ki lafiya". Nauyayyen ajiyan zuciya ta sauke tare da sakin fuskarta tace..."nagode Rabi Allah ya saka da alkhairi". Komawa tayi cikin kitchen dan k'arasa sauran aikin ita kuma Rabi cikin sauri ta koma part d'insu na masu aiki. https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman Yusuf) *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u no pain~* *part thirty three* Kan dinning ta shirya musu kayan breakfast d'in sannan ta koma d'aki duk abin duniya ya isheta saboda yau tun tashinta bata sha mutumin taba wato fresh milk. Duk da tasan fridge d'inta babu komai a ciki amma hakan bai hanata bud'ewa ba ko zata samu wani abun,ga mamakinta fridge d'in cike yake da fresh milk harda ice cream. "Allah sarki Yayana" tace lokacin da ta d'auki roba 1 ta koma kan kujera ta zauna tana sha,tana jinjina mishi tasan shine kad'ai da wannan aikin kila dare yabi ya tanada mata abinda yasan tana matuk'ar bukata. Tana gama sha ta d'auko burmemen hijabinta dogo har k'asa amma mai hannu ta saka ta fito parlour. Suna kan table suna breakfast ta same su,durkusawa tayi har k'asa ta gaishe su. A wulakance Lateefa ta amsa,Al'ameen ko d'agowa baiyi ya kalleta ba balle tasa ran zai amsa. A tsawace Lateefa tace..." Ke dan ubanki ban hanaki zuwa inda mijina yake ba?sai ana magana ki kama sunkuyar da kai sai kace wata mutuniyar arziki"ta karasa maganan tana harararta. Tsum- tsum Ameera ta mik'e tayi hanyan part d'inta. Wata tsawar ta kuma daka mata..."ke ina zaki tafi kuma bayan ban gama dake ba?ki wuce part d'insu Fa'iza ki gyara musu kamin su dawo daga sch". Al'ameen yana jinsu amma ko d'ago da kanshi ya kasa balle yayi yunkurin hanawa. Part d'insu Fa'izan ta wuce ta bud'e parlour ta shiga, gani tayi duk sunyi kaca-kaca da parlourn komai a warwatse. Cikin k'ank'anin lokaci ta kimtsa ko ina ya zama fes. Cikin bedroom ta nufa shima da nufin kimtsata,tana bud'e k'ofan bata san lokacin da ta k'wala wata irin razanannen kara ba sakamakon abinda idonta ya gane mata. Ihun da tayi shi ya dawo dasu cikin hayyacinsu ,a razane suka rabu da juna suka juyo suna kallonta. Jikinta gaba 1b'ari yake,Fa'iza,Shamsiyya da wata sabuwar k'awarsu mai suna Binta ta gani tsirara akan gado suna murkususu. Shamsiyya ta wawuro towel ta d'aura a lokacin da take saukowa daga kan gadon,ta nufo Ameera da ta kasa motsi ta sandare waje 1. Wani gigitacen mari ta fara d'auketa dashi tana nunata da yatsa tana huci ta fara surfa mata ruwan bala'i. Kan kace me sauran ma sunyi joining,nan suka taru suka nad'a mata na jaki. Haniyarsu ce ta cika gidan har Lateefa taji ta iso wajan tana tambayan ko lafiya? Shamsiyya tayi caraf tace..."Aunty ace karuwancin yarinyan nan yayi nisa kuma ta rasa inda zatayi sai gidan nan?" "Ni Ku gaya min me yake faruwa nace?" Lateefa ta k'ara tambaya cike da k'osawa. Binta ta matso gaba tace..."Aunty wanka fa muke yarinyan nan tazo tana lekamu". Salati Lateefa tasa tana tafa hannu ta juyo ga Ameera tasa k'afa ta hamb'areta ta fad'i k'asa. Bata tsaya yin tunani ko la'akari da me zaisa su many an 'yan mata shiga wanka tare ba. Ta cigaba da bala'i..."dama kana ganin idonta zaka san tayi nisa a harkan lesbian, toh wallahi ba a gidan nan ba sai dai kije can ki nemi abokan shashancinki".tana magana bugunta sai da sukayi mai isarsu sannan suka k'yale ta dan Kansu. Da k'yar ta iya jan jikinta dake mata ciwo ga uwa uba mararta daya kulle ji take kaman zai balle saboda azaba. K'wanciya tayi cikin azaba da rad'ad'i tana ta juyo kuma tana tunanin alak'arta da Fa'iza da irin abubuwa da take mata,sai yanzu ta fahimci manufarta. Godiya ta shiga yiwa Allah da bai bata nasara a kan ta ba har tasan wacece ita,ta gwammace ta dauwama a *UKUBAR* Lateefa da ta kasance a irin wannan halin. Haka ta cigaba zancen zuci har baccin wahala ya d'auketa. Har bayan 12pm Lateefa bata ga gilmawar Ameera ba yasa ta k'walawa Rabi k'ira tazo gabanta ta durkusa,nan take tambayarta ko Ameera tana kitchen? Amsa mata tayi da... " a'a ban ganta ba Hajiya". Wata k'atuwar ashar Lateefa ta lailayo sannan tace..." Tab lalle yarinyan nan ta rainani in har ban gyara mata zama ba,wata rana sai taci tuwo akaina". Tana gama fad'an haka ta mik'e a fusace tayi part d'in Ameera, Rabi tabi ta da ido tana girgiza Kai cike da jimami. A kan tiles ta same ta zube tana baccin wahala,ga fiskan nan ya kumbura suntum. Ba imani balle tausayi Lateefa tasa hannu ta wanka mata lafiyyar mari kan kumburaren fuskanta. A razane ta mik'e tana muzurai,suna had'a da Lateefa ta zube a wajan tana bata hak'uri amma hakan bai hana Lateefa zazzaga mata bala'in data k'waso ba. Tasa kyarta tayi har kitchen d'in tana balbale ta da masifa kuma tace maza ta d'aura musu abincin rana. Ko d'ago da kai ba tayi ta kalleta ba har ta gama ta fice. Goge hawayen fuskarta tayi,ta fara kiniyan d'aura girgin. Rice and stew tayi niyan girkawa dan haka duka 2 ta d'aura su lokacin d'aya,tana soya kayan miyanta da tasa kayan kamshi harda curry a ciki. Ka min ta gama soya miyan saida tayi amai har sau 2 saboda yanda take jin curryn yana hawa mata kai. D'an k'walin kanta ta cire ta rufe hancinta dashi,d'ayan hannunta kuma rik'e da lemun tsami tana tsotsa. A haka ta gama musu girkin ta jera musu akan dinning sannan ta wuce part d'inta dan yin wanka. Ruwan d'umi ta had'a ta gasa jikinta dashi,k'wanciya tayi lamo cikin ruwan tana jin dad'inshi ga mararta ma har yanzu bai daina ciwo ba. Tana fitowa daga wankan mai kawai ta shafa tasa wata jallabiyar ta ash colour babu zancen k'walliya saboda an haramta mata shi a gidan. Hijabi ta d'aura akan jallabiyan tayi sallahn azahar. Tana idarwa tayi hanyan kitchen saboda wata zababbiyar yunwa da take ji,tana addu'an Allah yasa sun rage mata. Allah ya taimake ta dan ta samu sun rage dayawa. Sai dai kuma ba zata iya cin miyar ba saboda warin curry. A plate ta d'ebi white rice tasa man gyad'a tare da marmasa maggi kad'an akai,albasa da attargu tasa a turmi ta d'an jajjagasu shima ta juyesu akan white rice d'inta ta zauna ci. Sosai abincin tayi mata dad'i sakamakon sunfi shiri da abinci mai yaji yanzu dan haka taci dayawa. Tana gamawa kuwa ta kama kiciniyar d'aura na dare,saboda tasan tana k'wanciya bacci zatayi azo ana masgarta a banza. Bayan dawowarta daga gidan Hajiya kaman da wata 2 Fateema da ya kumbonsu suka zo mata yini kuma Allah ya taimake ta ranan Lateefa bata nan sun fita watsewarsu ita da Salees d'inta su Fa'iza ma basa nan dan haka lafiya lau suka wuni suna tafi. A k'wana a tashi ba wuya dan yau cikin Ameera ya shiga wata na 7 kenan,amma duk gidan ba wanda ya sani in ka cire Al'ameen da Rabi. Cikin ikon Allah cikin yabi jikinta da yake Allah ya mata baiwan diri da na Fulani dan haka su suka rike mata cikin . Wata safiyar Wednesday Ameera tanan goge-goge a parlour,Mamarsu Lateefa tayi sallama ta shigo. Lateefa cike da murna ta tare ta. Ameera dak'yar ta kai k'asa ta gaisheta. Fuska ba yabo ba fallasa ta amsa suka wuce part d'in Lateefa . Ameera ajiye dustern hannunta tayi ta shiga kitchen dan had'owa Mamar Lateefa ruwa da abin motsa baki. Cikin dauriya take komai sakamakon nauyi da cikin tayi mata. Katon tray ta cika shi da drinks da snacks ta nufi part d'in Lateefa dashi. Hirarsu suke suna k'wasan dariya kaman wasu k'awaye,Ameera tayi sallama ta shigo. Tafiya take a hankali harta k'ataso tsakiyan parlour ta ajiye tray akan center table dake tsakiyan parlourn. Tsiyaya juice d'in tayi a glass cup tazo gaban Maman Lateefan ta mik'a mata tare da k'ara mata sannu da zuwa. Mik'ewa tayi da k'yar ta fice, duk akan idon Maman Lateefa ta k'asa cewa komai. Bayan fitan Ameera ta juyo ga 'yarta tace..."wacece wannan ko sabuwar 'yar aiki kika samu?" Dariya Lateefa tayi har rana rik'e ciki tace..." Mama kenan wannan Ai itace amaryar Al'ameen amma kinga yanda na maidta mai aikin gidana duk wani aikin gidan nan ita take yinsu na hana masu aiki...." " me dallah dakata shasha"ta katse ta cikin tsawa. Lateefa sororo tayi ta na kallon Mamanta ita kuma ta cigaba ..."Ai kuwa kece mai aikinta nata dan kina gab da zama 'far kallo a cikin gidan nan,ke da nake ganin ba wacce ta tako k'afana cikin 'yan matan da Allah ya bani sai me Ashe kuwa ba haka bane". Turo bani Lateefa tayi tace... "Haba Mama keda na d'auka zaki tayani farincikin ina jiya kishiyata amma sai ki hau yi min fad'a akanta?" Tsaki Mama tayi tace..." Baki da idone Lateefa, ba k'ya ganin abinda yake jikinta wannan kishiyar taking?" Zaro ido tayi ta na kallon Mama tace..." Bangane ba,Mama me kika gani a jikinta?" "Bud'e kunnenki kiji duk yanda akayi yarinyan nan ciki ne da ita". [3/31, 3:03 PM] Ummee Yusuf: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman Yusuf) *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u no pain~* *part thirty four* Wata irin zabura Lateefa tayi ta mik'e tsaye tare da d'aura hannayenta duka akai tace..." Na shiga 3,dan Allah Mama da gaske kinga ciki a jikinta?" " k'irata ki gani da idonki"Mama ta bata tabbaci. K'wala mata k'ira ta farayi da dukkan karfinta. A tsorace Ameera ta shigo ta zube a k'asa tace..." Gani Aun..." Katse ta tayi cike da karaji tace..." Mik'e daga tsugunen nan munafuka". Yunkura tayi ta mik'e tsaye da k'yarta tana kallon yanda duk ta hargitse. Wawuro hijabinta Lateefa tayi zata cire mata,Ameera tayi saurin rik'ewa tana..." Aunty ki hak'uri,me nayi ne?" Lateefa bata ma jin me take cewa babban burinta ta cire wannan hijabin da bata rabuwa dashi dan ta tabbatar da maganan Mamanta. Da karfin tsiya ta samu nasaran cire hijabin, ai kuwa cikin tagani ya d'an fito kaman an kifa k'warya. Lateefa bata san lokacin da hijabin ya sub'uce ya fad'i a hannunta ba. Mama tace..." Yanzu kinga zahiri ko?" Wani mahaukacin mari ta d'auketa dashi wanda yasa har ta kifa a k'asa. Binta tayi ta cigaba da dukanta tana taka cikin da k'afa tana sumbatu kala-kala kaman wata sabuwar kamu kana ganinta kasan bata cikin hayyacinta. Mama da k'yar ta samu nasaran janye ta gefe tare da zaunar da ita akan kujera tana ta haki. Ameera kuwa tuni ta fice daga parlour da rarrafe dan tsira da ranta. Mama ta dubeta taga har yanzu bata dawo hayyacinta ba sai huci take,kamo hannunta tayi ta girgizata tace..."ke ki nutsu ki dawo hayyacinki kiji abinda zance miki,ba haka ake yi ba in kin kashe 'yar mutane fa?da sannu ake bin komai duk da kema kinyi sake sosai a zamanta a gidan nan da haka bata faru ba.karki damu tunda kina dani yanzu zan baki shawaran yanda cikin zai bare cikin sauki". Sai a lokacin ta samu daman sauk'e nauyayyen ajiyar zuciya tare da gyara zama tace..."ina jinki Mamana ya za'ayi?" "Aiki zaki k'ara mata yafi na yanzu,dan 'yan aikin nan da take ba masu wuya bane.abinda nake so sake shine duk kayan ku na wanki da guga ita zaku tarawa,ke harda sharan wannan tafkeken gidan naku ciki da wake karki tausaya mata kiyi haka zuwa sati 1,in baki ga wani cigaba ba kimin waya balle nasan za'ayi nasara saboda da alamu cikin k'arami ne". Rungumeta Lateefa tayi tana murna da godiya mama tace..." Haba sai kace baki sanni ba?ba zamuyi sake gidan hutun ya sub'uce mana ba". Nan suka cigaba da hirarsu wanda kusan gaba d'aya akan yanda zata Lateefa zata musgunawa Ameera ne. Sai bayan a zahar tayi shirin komawa gida bayan Lateefa tayi mata goma na arziki ta rakota har parking lot.nan take fad'an har zata koma bataga su Fa'iza ba. Nan Lateefa take shaida mata sun tafi rabon katin auren k'warsu Binta wanda za'ayi nan da 2weeks. Sak'on a gaishe su ta bari wajan Lateefa tashiga mota driver ya maidata Gida . Komawa cikin gida tayi tana ayyana sabon rashin mutuncin da zatayiwa Ameera. Kayan sawanta dana Al'ameen sun kai kusan set 30 ta fito dasu tana kwalla mata k'ira. Tana jan k'afa ta fito daga part d'inta zuwa cikin parlour inda Lateefa take jiranta ,tana shirin tsunguna taji an watso mata fuska. "K'washe kayan nan kije ki wanke minsu tas sannan ki jira su bushe ki goge su duka a yau and bana son machine wash dan yana b'ata min kaya dan haka use ur hands and wash them" tace tana watson matso mugun kallo dan bata ki ace ta shak'eta su mutu ita abinda yake cikinta ba. Tsungunawa tayi da k'yar tana tattara kayan saboda tunda Lateefa ta tattaka mata ciki take cin mararta yana mata wani irin zogi. Haka ta fita dasu can compound d'in gidan zuwa bakin tap dan wanke su. Mai wankin gidan yana ganinta ya taso da gudunshi da niyan karb'a amma ta dakatar dashi tace ya barsu ita zata wanke su da kanta. Jikin shine yayi matuk'ar sanyi dan haka ya rasa bakin magana yaja gefe yana kallonta harta kai bakin tap tana shirin fara wankin da hannu kaman yanda aka umarceta . Wajen maigadi yaje yana maida mishi zancen. Girgiza kai yayi cike da jimami yace... "Yarinya 'yar k'arama da ita amma matan ba d'igon imani bata dashi take azabtar da 'yar mutane". Driver yace..." Nifa laifin maigaidan nake gani tunda shi ya kamata ya tsawatar mata amma ya kasa". Mai gadi ya girgiza kai yace..." Kai dai bari wannan lamari sai Allah tunda yasha sayo mata abubuwa yana bani ajiyarsu sai can cikin dare zai dawo ya karba". "Hakane kam wannan abu sai Allah" inji mai wankin. Ameera tana can tana tikan wankin tana zubar da hawaye tana kuma nadaman kin amicewa da shawaran Al'ameen na bata da yace zai saya mata gidanta daban taki gashi tunda ta dawo abin k'ara gaba yake. Dan mugunta irin na Lateefa wasu kayan ma a wanke suke ta had'a dasu. Haka ta gama ta shanyasu gaba d'aya akan igiyan shanya,sannan ta koma cikin gidan tace tagama. Harara tabita dashi idon nan kaman zasu fad'o k'asa tace..."wallahi inna Cuba kayan nan naga jik'a-jik'a kika min,hmmm.." Yatsunta 2 ta had'a ta Mirza sukayi k'ara kana tacigaba" kema kinsan sauran ba said na fad'a miki ba tashi ki bani waje". Harta ta tashi zata tafi tace..."yauwa sak'wara nake son ki mana duka gidan hard a masu aikin gidan nan". Kasa magana tayi kawai kitchen d'in ta wuce kai tsaye ta d'auko manyan doya guda 3 ta kama fira, bayanta mararta duk sun rike sai azaba take ji,ga yunwa da take ji dan rabonta da abinci tun safe. A haka ta had'a musu lafiyayyar miyan egusi da yaji ganyan ogu da cry fish ga naman rago,gidan sai kamshi yake. Bari d'aya kuma doyanta data d'aura da d'an gishiri ya nuna. Turmi da tab'aryata ta d'auko ta fara kirb'awa,tanayi tana tsayawa sakamakon azaba da cikinta da bayanta ke mata. Haka Rabi ta shigo ta sameta ta Mike sharkaf da gumi. Da sauri Rabi ta k'arasa tana..." Hajiya kawo in kib'a miki amma wannan rashin imanin yayi yawa ,Allah ya saka miki Hajiya wallahi koba dad'e koba jima Allah ba zai barta ba karshenta ba zai tab'a k'yau ba". Zubewa tayi a k'asa tana juyi akan tiles d'in kitchen, Rabi tana kirb'awa amma hankalinta gaba d'aya yana kan Ameera sai hawaye take tana mata sannu . Cikin ikon Allah kamin Rabi ta gama taji ciwon ya lafa,dan haka tazo tasa hannu ta fara tayata yin malmala suna zubawa a warmers. Rabi tana hanata amma taki tace taji sauki shiysa. Bayan sun kammala ta koma wajan kayan dan gogesu ta tatar da mai wankinsu yana aikin gogr mata su. Nan ta nemi ya bar mata ta k'arasa yace bakomai taje bakomai zai k'arasa mata. Bata koma cikin gida ba gudun kada Lateefa ta ganta ta shiga 3,dan haka can garden d'in gidan ta wuce ta samu waje ta zauna. Sai bayan 9 ya gama gugan ta k'waso kayan ta shigo cikin gida, bakowa a parlor,wucewa tayi dasu d'akinta ta ajiye da safe ta bata. Wanka ta farayi sannan tayi sallahn isha'i,da rarrafe ta k'arasa kan gadonta ta k'wanta tana maida numfashi. Ko 30 mins batayi da k'wanciya ba taji cikinta ya fara wani irin murdawa na yunwa. Ba shiri ta tashi ta nufi kitchen dan samawa cikinta wani abu. Duk dube-dubenta bata samu komai ba a kitchen d'in,tana son d'aura ko indomie ne amma tana tsoron a kamata a kitchen a nad'a mata na jaki saboda tasan wannan shirin Lateefa ne dan in bata son taci abinci a gidan Sai tasa a k'washe abincin akai can layi ko kan soak away azubar. Dawowa tayi d'akinta ta k'wanta,bata jima da k'wanciya ba taji motsin mutum a parlour ta. Bata motsa ba daga kwacenta saboda tasan mutum 1 ne mai shigo mata d'aki a irin wannan lokaci. Yanda ya ganta ya matuk'ar razana shi,da sauri ya k'araso ya hau kan gadon tare da sa hannu ya d'agota yana tambayarta meya sameta. Da hannu ta nuna mishi cikinta da bayanta. Kwantar da ita yayi ya fita da sauri zuwa parlour,ya samo mata ibomol cikin first aid box ya dawo ya same ta kaman yanda ya barta. Tambayanta yayi ko taci abinci?ta amsa mishi da bata ci ba. Fita ya k'arayi zuwa kaman 15mins Sai gashi ya dawo da plate a hannun shi cike da indomie sai tururi yake da alamu yanzu ya dafa shi,d'ayan hannunshi kuma rik'e da wani k'aton shopping bag ya ajiye a k'asa ya hau gadon. D'agota ya jinginar da ita a jikinshi sannan ya fara bata abincin abaki,nan da nan ko ta cinye shi tas.. Ledan da ya shigo dashi ya b'ude,cake ne da sauran snacks zallah a ciki,shima ta hau ci hannu baka hannu k'warya,kallonta yake cike da tausayi saboda mutum yana ganin yanda take abinci zaka san yunwa ya gama cinye ta.saida taci mai isarta sannan ya bata maganin tasha. K'wantar da ita yayi yana lapping d'inta kaman 'yar jinjira har baccin mai dad'i ya k'washeta. Shi bai bar d'akin ba saida yaga baccinta yayi nisa sannan ya fita ba dan yaso ba ya ayyana abubuwa a ranshi. [3/31, 11:33 PM] Ummee Yusuf: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA~* 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman Yusuf) *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~* *part thirty five* Washe gari bata farka ba sai wajan karfe shida da rabi na safe. Garau ta tashi ba ciwon mara dana bayan da take ji jiya,wanka tayi tare da alwala tayi sallah sannan ta fito aika-aikacenta da yanzu ya zame mata jiki. Rabi ta iske a kitchen tana girki harta kusa kammalawa. Da murmushinta ta k'araso tana mata sannu da aiki. Bayan sun gsisa Rabi take tambayarta ya jikinta? "Da sauki wallahi dan yau na tashi bana jin ciwon komai" tace tana murmushi. "Alhamdulillah Allah ya k'ara lafiya ya raba Ku lafiya" inji Rabi. Ta amsa da "Ameen". Hannu tasa suka k'arasa aikin tare suna hira abinsu,dan yanzu Rabi ita zame mata tamkar k'awa. Da ita kad'ai zata zauna tayi hira cikin k'wanciyar hankali. Yau sati 1 kenan Lateefa take gallazawa Ameera dan cikin jikinta ya b'are amma shiru ba labari,sai ciwon mara da baya da kusan suka zame mata jiki amma tana shan ibomol da Al'ameen ya ajiye mata su a d'aki harda paracetamol sai taji sauki. Ganin ba canji yasa Lateefa tayi shawaran k'iran Mama dan su canza shawara. Can cikin bedroom d'inta ta shiga sannan ta k'irata,bayan sun gaisa take fad'a mata cikin yana nan bai zub'e ba. " kada ki tada hankalinki ki turo min d'aya daga cikin k'annenki tazo in bata wani magani dana tanadar miki, da zarar ta sha cikin nan ba zai k'wana a jikinta ba"Mama tace mata cikin rarrashi. Dariya tayi na jin dad'i tana jin ba wanda ya kaita sa'an uwa na gari. "Yanzu zan turo Shamsiyya tazo ta karb'a". Mama ta katse ta da ..." Yau zata zo bazaki bari sai gobe ba? Naga yanzu yamma tayi". "Hak'urina ya kare Mama na k'osa inga babu cikin nan ajikinta dan haka zan iya jurewa zuwa gobe ba"tace tana huci kaman wata macijiya. Suna gama wayan tayi dialling number Shamsiyya tace tazo bedroom d'inta ta sameta. Cikin minti biyar ta shigo tace..."gani Aunty". " zariya zan aike ki akwai sak'ona a wajan Mama ki karb'o min kuma pls karki k'wana duk yanda zakiyi ki dawo yau". Shamsiyya tace... " toh ba zan k'wana ba saboda muma muna nan muna shiye-shiryen auren Binta". Lateefa tace..."oh ashe auren ya matso ko?" "Eh saura 5 days, bari inyiwa driver magana muje mu dawo da wuri" tace tana mik'ewa. Dakatar da ita Lateefa tayi tace..." Kije ke kad'ai ba tare da driver ba saboda sirri ne ". " shikenan Aunty saina dawo".tace tare da ficewa daga bedroom d'in. Wani maganin gargajiya Mama ta bata cikin goran faro ta kawo. Cikin tsananin murna Lateefa tasa hannu ta karb'a ta ajiye a gefenta sannan ta fara k'walawa Ameera k'ira. Ameera tana jan k'afa ta shigo parlour saboda yanda cikin nata kullum yake k'ara girma da nauyi. Maganin ta mik'o mata tace..." Gashi maganine shanye ki bani roban". "Magani kuma Aunty? Lafiyata k'alau fa" tace tana shirin mik'ewa ta bar wajan. Murmushin mugunta tayi tace..."wato bazaki sha girma da arziki ba ko?Ku rik'e min ita in bata". Kamin ta rufe baki Fa'iza har ta iso inda take tana janta cike da mugunta dama yanzu ba wanda ya kaita jin haushin Ameera tunda ta kasa cimma burinta akanta. Shamsiyya tazo tayi joining suka rirriketa,Lateefa ta taso da roban maganin a hannunta. Cikin tashin hankali Ameera ta fara mata magiya kan taji kanta ta k'yaleta amma Lateefa ko d'igon imani babu a ranta balle tausayi burinta kawai shine taga ta b'atar da abinda yake cikinta ko hankalinta zai k'wanta. Murmushine shimfid'e a fuskanta harta k'araso gaban Ameera tace..." Kada ki damu 'yar k'anwata,wannan magani da kike gani zai taimaka miku sosai wajan haihuwa kinsan ina ji dake bana son ki sha wuya shiyasa kika na nemo miki maganin da kaina". Tana gama fad'an haka ta matse mata baki ta fara d'ura mata maganin su Fa'iza suna tayata suna dariya. Basu k'yaleta saida taga goran ya zama empty sannan suka k'yaleta. Gaba d'aya Ameera ta galabaita ta fita haiyacinta ido jawur take kallonsu,har yanzu basu bar mata dariyan ba. Daddafa kujeru tayi ta mik'e da kyar tayi hanyan part d'inta tana layi,a ranta kuwa tana ayyana karshenta yazo bata cire d'aya cikin biyu maganin mutuwa ta d'ura mata. Ba yanda zatayi sai dai taje ta jira mutuwarta. Tana shigowa parlournta taji mskoshinta yacika da wani irin bauri da d'aci wanda ya haddasa mata tashin zuciya lokaci d'aya. Da gudu tayi bathroom kamin ta k'arasa ta kece da amai mai tsanani kaman zata amayar da kayan cikinta. Aman bai tsaya ba saida ta komai na cikinta ya fita sannan ya tsaya. Shower ta sakarwa kanta sannan ta fito ta k'wanta akan gadonta tana kuka tana mik'awa Allah lamarinta a haka har baccin wahala yayi gaba da ita. Pls manage dis.kuma masu complain akan Ameera Ku kara hakuri. [4/1, 8:34 PM] Ummee Yusuf: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA 😭😭😭😭😭😭 *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~* *part thirty six* Lateefa tana k'wance a parlournta ajan 3 seater cike da nishad'i take danne-danne a wayarta,kana ganinta zaka san tana cikin farinciki. Number Aina'u tayi dialling tasa a kunnenta,fuskarta cike da annuri take cira ta d'aga wayan. "B'atan hanyan kikayi ko kuma ince sai yau kika tuna dani?" Aina'u tace bayan ta d'aga wayan. Dariya mai cike da farinciki ta k'washe dashi tace..."Besty yau ina cikin farinciki shiyasa na kiraki ki tayani farinciki " " a haba! Meya faru ?bani insha mu taya juna murna" "Hmmm Aina'u wai ashe wannan yarinyan munafurta ta take". Cikin sauri Aina'u ta katseta tace..." Wace yarinya kuma?" Lateefa saida taja numafashi tace..." Wannan tsinannaiyar Ameeran nan mana ashe ciki ne da ita". Zumbur Aina'u ta mik'e daga zaune dafe da kirji tace..." Me kika ce Lateefa,ya akayi kikayi wannan saken har hakan ta faru?" K'ara gyara k'wanciyarta Lateefa tayi sannan ta bata amsa..." Bar shegiyar yariyan nan b'oye cikin tayi ban tashi sani ba saida Mama tazo gidan nan ta ganta,dan munafurci kullum hijabi take jurmuk'awa..." Da sauri Aina'u ta katseta..."yanzu wani mataki kika d'auka ko shine abin farinciki da kika k'ira ki gaya min?" " ke dad'ina dake gajan hak'uri"Lateefa tace mata tana dariya. "Uhum ina jinki,zuciyata ce take tafasa shiyasa kika ga na kasa hak'uri" Aina'u tace mata. Lateefa saida ta k'ara dariya sannan tace..." Bazan iya k'watanta miki tashin hankali dana shiga ba a wannan lokacin,idona rufewa yayi na hauta da duka ta ko ina.da k'yar Mama ta k'wace ta,tace min ba haka make ba ta bani shawaran kara mata aiki masu wuya zuwa sati,nayi ta d'aura mata amma ba nasara shine yanzu ta aiko min da wani jiko muka d'ura mata wanda Mama ta tabbatar min ba zata k'wana dashi a jikinta ba.farinciki ne ya cika ni shiyasa na kiraki ki tayani murna". Dariya mai kama da shewa Aina'u tayi tace..." An gaishe da Maman Mu,sai yanzu naji hankaluna ya k'wanta,yanzu tana ina?" "Tana can d'akinta tana fama da kanta"Lateefa ta bata amsa. Aina'u tace..." Bari in k'ara miki wata idea nima,ki kula da takunta da zarar kinga ta fara labour sai kiyi amfani da wannan chance d'in ki k'arasata kowa ya huta.kuma ba wanda zaiyi doubting d'inki dan kowa cewa zaiyi ta mutu a wajan haihuwa". K'yalk'yalewa tayi da dariyan jin dad'i tace..." Gaskiya yayu Besty shiyasa nake ji dake". Sallama sukayi ta ajiye wayan bayan Aina'u ta k'ara mata evil ideas . Fa'iza da Shamsiyya sun saka Binta a gaba suna ta kuka wiwi wai a dole sunyi rashin masoyiya. Binta tazo ta rungumesu tana rarrashinsu tace"haba Ku daina bata hawayenku kusan auran nan zanyi ne Kawai ba dan ina so ba kawai saboda matsayinshi yasa zan aure shi ku tuna fa major general ne fa? kunga akwai naira da zamuyi abinda muka ga dama bayan haka kuma alakarmu tana nan ba abinda zai canza kunsan nima ba zan iya rayuwa ba ku ba dan kun zama jinin jikina". "Shamsiyya tace..." Are u sure?" " off course yes"ta tabbatar musu. Cike da farinciki suna shiga shasshafata tare da sauran abinda ba zan iya tsaya in gani ba balle in d'auko muku. Ameera bata tashi a baccin wahala da take ba sai wahan 8:39pm. Tana farkawa tajita jakam a jik'e. Cike da tashin hankali tayi yunkurin mik'ewa amma ta kasa,ji tayi kaman an kulle mata mara. Komawa tayi ta k'wanta. A tsorace tasa hannunta a hankali karkashinta inda take jin danshin. Hannunta har rawa yake saboda tsaban fargaban me zata gani. Wani ruwa mai yauk'i ta gani had'e da jini yana bin k'afanta. Kuma ne mai karfi k'wace Mata mata,ta rasa wani irin tunani zatayi. A duke tana bin bango har ta shiga cikin bathroom zama tayi dirshan akasa tana kallon ikon Allah,jinin dai ya tsaya amma ruwan bulbulowa yake kaman an bud'e famfo. Bata san ma ta ina zata fara ba shiyasa tayi zamanta,sai kusan 9:45 ta samu ya tsagaita zuba,da k'yar ta mik'e tayi wanka ta fito tare da canza kayanta ta k'wanta tana jiran hukuncin Allah. Azaba take ji kota ina ga abin cikinta nata da yake k'ara damunta da motsi. Juyi take tana hawaye ba mai taimakonta,sai bayan karfe biyu da rabi na dare sannan ta samu wani wahalallen bacci ya d'auke ta. Tana ta zuba ido ko Al'ameen zai shigo amma har tayi bacci ba labarinshi. Koda same da ta tashi ciwon da take ji ya d',an lafa saidai ruwan ne bai tsaya ba... Zamanta tayi cikin bedroom d'inta ko parlournta bata lek'a ba balle tayi gigin fita aiki. Tana nan zaune ta fara jin motsi a parlournta,zuba ido tayi tana jiran taga ko wayene saboda tasan Al'ameen ko kallonta bai isa yayi ba balle har ya kaiga shigowa part d'inta. Zuru tayi tana kallon k'ofan shigowa bedroom d'inta. Turo k'ofan akayi aka shigo. Lateefa ta gani tsaye a bakin k'ofan da murmushi akan fuskarta. Tsoro k'arara ya baiyana akan fuskan Ameera ganin Lateefa yau har cikin bedroom d'inta, ta san dai alkhairi ba zai tab'a shigowa da ita ba sai dai akasinta . K'arasowa tayi gabanta tana kallon ta har yanzu da murmushinta. "Ya jikin 'year k'anwata?" Tace lokacin da take tsugunawa a gabanta . Da k'yar bakinta ya iya cewa "da sauki". " ina da ina ke miki ciwo"ta tambaya still wit her smiling face. Da hannu ta nuna mata cikinta da bayanta. Matsowa ta k'arayi gabanta taxa hannu ta danna mata mara da iya karfinta har saida tayi k'aran azaba tace..." Nan ko?" "Sannu kinji,ina son in kika ji ciwon ya k'aru ki min magana mu tafi hospital ko?" Gyad'a kai tayi kawai dan batada bakin magana. Mik'ewa tayi tare da nufan hanyan fita. D'an dakatawa tayi ta waigo tace..."ina parlour in kina nema na". Tana fad'an haka tasa kai ta fice. Wayarta ta lalubu da yake gefenta da niyan k'iran Ummanta ko Al'ameen dan su san halin da take ciki sai dai Nash ashe wayar ba kota flashing. Cilli tayi da wayan a tsakar d'akin har komai na wayan ya tarwatse saboda haushi wayar ma ya bata. Daga bata kuma taga in wayar tana kunne kila Al'ameen ko Fateema wani ya neme ta a cikinsu. Yunkura tayi da niyan d'auko wayarta dan ta had'a amma ta kasa motsa koda kafartane . Hak'ura tayi ta kwanta tana jiran mutuwarta . Motsi ta kara ji a parlournta kuma yanzu cikin sand'a. Hakan ba k'aramin taxa mata hankali yayi ba,kar dai Lateefa ce ta k'ara dawowa dan ta k'arasata. Zubawa kofa ido tayi tana jiran taga mai shigowa. https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA 😭😭😭😭😭😭 *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~* *part thirty seven* K'ofan taga an turo a hankali wanda ya k'ara mata tsoro da fargaba da take ciki. Rabi taga ta lek'o da kanta itama a tsorace. K'arasowa tayi da sauri ganin Ameera a yashe a tsakar d'akin tana..." Subhanallahi 'yar nan jikin ne haka?ni dama tunda safe da ban ganki ba hankalina yaki k'wanciya.ina son shigowa in dubaki amma tsoron Hajiya ya hanani shigowa,yanzuma wannan mutumin nan da suke yawan fita tare shiya zo suka fita shiyasa nayi amfani da wannan daman na shigo dan duba lafiyarki.ashe haka jikin ya k'ara tsanani?" Ameera kawai sauraronta take dan bakinta ya kasa furta komai. Rabi tace..." Yanzu ina yake miki ciwo?" Da k'yar ta bud'i baki tace..." Rabi cikina bayana zai karye,Rabi zan mutu ki k'ira min Ummata" "Ba zaki mutu ba Hajiya alamun nak'uda nake gani a tare dake, Sai dai kaman lokacin haihuwar da saura.ko kuma jirani ina zuwa" tana fad'an haka ta fice da saurinta. Bata tsaya a ko ina ba sai wajan Baba mai gadi,tana zuwa bata b'ata lokaci ba ta sanar dashi halin da Ameera take ciki. Nan da nan yacewa Rabi ta kawo ruwa ya mata addu'a in dai haihuwa ce toh da izinin Allah ba zata dad'e ba zata haihu,in kuma wani abinne daban shima da izinin Allah zai zo mata da sauki. Da gudu Rabi tayi cikin gida tazo da ruwa a cup ta mik'a mishi. Shima kamin ya tazo yayi Alwala yana jiranta. Tana bashi ruwan ya zauna ya fara addu'oi yana tofawa a cikin ruwan. Ya d'auki lokaci mai d'an tsawo kamin ya gama ya bata yace... "Gashi in kinje ki zaka k'ankara a ciki yayi sosai a bata tasha da bismillah. Godiya Rabi tayi mishi sannan ta koma cikin gida da saurinta,saida ta saka k'ankara yayi sanyin sannan ta kaiwa Ameera tasha. Abinci ta kawo mata ta tilasta mata taci kad'an. Zama tayi kusa da ita tana mata hira samama,zuwa kaman 40 mins Ameera harta manta da wani da take ji,suka kama hira sosai harda dariya. Rabi taji dad'in yanda taga ta watsake haka tace.." Uhum Hajiya hiran ba zata k'are ba kuma tunda naga ciwon ya d'an lafa bari inje in d'ora girki". Sai a lokacin Ameera ta tuna ashe fa bata da lafiya..." Rabi wallahi na daina jin komai wani irin magani kika bani nasha?" Baba Bello ne ya miki addu'a a cikin ruwa na kawo miki,ko a kauye mutane suna tururuwa wajan karb'an ruwan addu'a a wajanshi kasancewar k'auyenmu d'aya dashi shiyasa na sanshi". Ameera tace..."Allah sarki Baba,Rabi dan Allah ki fara mik'a mishi sak'on godiyata kamin inje da kaina". Yunkura Rabi tayi ta tashi tana.." zaiji insha Allah". Tana fita Ameera itama taja jiki ta tashi ta fad'a bathroom tayi wanka dan ta k'ara jin dad'in jikinta. Rama salloli da ake binta ta farayi sannan ta kimtsa ta fito kitchen wajan Rabi wacce harta kusa gama aikinta. Kallonta Rabi ta tsayayi saboda mamaki can tace.." Haba Hajiya ya zaki fito?aida zamanki kikayi saboda na kusa kammalawa". Murmushi Ameera tayi tace.."aiko da wanke-wanke zan taya ki". "Barshi ki koma d'aki kada tazo ta iske ki anan, kuma karki bari tasan kin samu sauki kiyi k'wanciyarki ki na k'wana 2.ina tsamanin matsalar da ya sameki yana da nasaba da aikin wahala da kikeyi". Ameera bata musa mata ba ta amsa da " toh " ta koma part d'inta. Rabi tana gama girki ta zubawa Ameera a warmer ta kai mata har bedroom. Bata fita a d'akin ba saida ta tabbatar da Ameera taci ta koshi sannan ta k'washe kayan ta fita tana k'ara jaddadawa Ameera tayi k'wanciyarta kuma tayi yanda tace mata dan tasan yanzu duk yanda akayi Lateefa tana kan hanyar dawowa,sabida duk tsiyarta bata yarda Al'ameen ya rigata dawowa. Rabi tana fita idonta ya kai kan wayarta da yake tarwatse a tsakiyar d'akin. Da sauri ta d'auka ta had'a shi ta kunna tana Allah sarki Yayana nasan ya neme in bai samu ba. Kunna wayar tayi ta ajiye a gefenta tana kallon yanda a in cikinta ya isheta da motsi,hannu ta kai tana shafawa da murmushi a fuskarta. Wayanta ne ya katse mata abinda take,wayar ta jawo tarw da receiving call din. Sallama tayi tana murmushi kaman yana ganinta. Lumshe ido Al'ameen yayi tare da ajiyan zuciya tace..." Haba Babyna kin kusa zautar dani yau,kinsan zan kiraki Dan inji lafiyarku shine kika kashe min Waya?kodai wani laifin nayiakayi min irin wannan horon mai tsanani a haka?" Bata katse shi ba harya kai aya sannan ta bashi amsa da..." Ko d'aya Yayana ai kai haka laifi a wajanmu just dai na manta ne ban kunna way an ba". Nan suka cigaba da hiransu kaman basu da wata matsala a rayuwa. Lateefa cikin sauri take driving cos a yanzu babban burinta shine taje taga wani hali Ameera take ciki. Yau kwata-kwata bata so ta motsa ko nan da can ba saboda tana son yin amfani da shawaran Aina'u tana fara haihuwan ta karasata kowa ya huta. Sales shiya hura mata wuta a Waya kan dole taje su had'u wai yayi missing d'inta,da taso yi mishi gardama amma ganin ranshi ya back yasa ta hak'ura tabi shi badan komai ba sai dan bata son bacin ranshi. Tana shigowa cikin gidan direct part d'in Ameera ta nufa tana aiyana abu iri-iri a ranta. Da d'an fargaba ta tura k'ofan ta shiga. Ameera suna cikin waya da Al'ameen taji motsin mutum a parlournta. Kashe wayan tayi gaba d'aya ta tura shi can kan gado sannan ta rungume cikinta da hannu 2 tare da runtsr ido ta fara murkususu. Lateefa saida taji zuciyarta ta bada *DUM* ganin har yanzu da sauran ranta kuma nataccen cikin nata yana nan bai b'are ba. Sai dai ta wani side d'in taji sanyi a ranta tunda da alamu bata ciki. hayyacinta. D'an dariya Lateefa tayi na jin dad'i sannan tasa kai ta fice. Ameera bata juyi da murkushe-murkusen ba said a ta tabbatar da Lattefa ta sannan ta mik'e zaune Rana murmushi saboda taji dadin shawaran Rabi. Lateefa tana fita part d'inta ta wuce. Bayan ta rage kayan jikinta ta zauna a bakin gado tare da kitan Mamanta. Bayan sun gaisa Lateefa ta bata abinda ya faru tunda daga ranan da suka mata maganin har zuwa yanzu da ta fito a d'akinta. "Ba wacce maganin nan ciki ya zauna a jikinta,ba dai kince bata cikin hayyacinta ba?" Mama ta tambaya. Lateefa ta bata amsa da "eh" Mama tace..."ki bata kwana 2zai zube ". Cikin jin dad'e Lateefa tace " shiken nan Mama nagode" " INA k'anenki ne yau kusan kwana 4ban jisu a Waya ba" "Suna can wajan shiye-shirye bikin kawarsu" https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) *Story by* *UMMEE YUSUF* (Maman Yusuf) *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~* *part thirty eight* Suna gama waya da Mama ta fad'a bathroom hankali k'wance tayi wankanta tare da tsantsara make up ta zauna jiran Al'ameen ranta fari sol. Al'ameen bai samu daman shiga part d'in Ameera ba sai wajan karfe 2 na dare. Tana tsakiyan baccinta ya shigo. Yaye bargon yayi shima ya shiga ya k'wanta tare da k'ara lullube su. Jawota yayi jikin sosai ya rungume ,sai faman shinshinata yake kaman wani sabon maye. Bud'e ido tayi ta ganshi mak'ale da ita,kara shigewa jikin shi tayi dan sunyi missing d'in juna. Al'ameen dama kaman jira yake ya shiga aika mata da sak'oni,shi bai barta ba sai suka farantawa juna rai. Daga nan suka shiga hirarsu cikin k'wanciyar hankali, bai bar d'akin ba sai da ya tabbatar da ta koma bacci sanna ya koma part nashi. Haka Ameera tacigaba da zamanta a cikin d'aki ko parlourta bata fitowa sai dai taci tayi wanka ta kwanta. Lateefa bata daina mata sintiri a d'aki ba,wai ko zata ga tana labor ta k'arasatan. Ameera itama tana jin motsinta zata fara murkususun k'arya,ba zata daina ba har sai ta fita. Wannan abu yana yiwa Lateefa ciwo ace yau kusan sati da bata maganin amma ciki yaki ya zube,kuma da zarar tayiwa Mama complain sai tace ta k'ara hakuri zuwa k'wana 2n da Lateefa bata son ji dan haka tayi niyyan d'aukan mataki da kanta. Yau Saturday yazo dai-dai da ranan d'aurin auren Binta da mijinta Major General Ibrahim Hassan. Su Fa'iza sun kai sati da tarewa a gidansu Binta kasancewarsu manyan k'awaye. Lateefa tayi shirinta tsab na zuwa bikin,tasha ky'au cikin purple shaddanta with purple veil in short komai purple tayi amfani da shi. Sai dai Kasan zuciyarta ba bikin bane dalilin fitanta,so take daga can ta wuce su had'u da bestynta ta bata shawara akan Ameera da d'an cikinta dan yanzu ta gaji da ganinta haka gara ayita ta kare. Ameera tana jin fitanta ta fito main parlour tayi zamanta dan rabonta da fitowa tun ranan da Lateefa da kannenta suka d'ura mata magani. Lateefa bata wani jima a gidan bikin ba ta wuce Neman Aina'u. Numbernta tayi dialling kusan 3 missed call ta bata kamin ta samu ta daga wayan tana magana da k'yar tace" Besty ya akayine?". A zuciye Lateefa tace.." Wai a ina kika ajiye wayan ina ta kira baki d'aga ba?" Hak'uri Aina'u ta bata tace tana tare da Alhajinta ne yanzun amma ta bata nan da 15 mins zata fito Sai su had'u a at home restaurant. Ba b'ata lokaci Lateefa taja motantan sai can,sai dai bata fito ba ta zauna a cikin motorn tana jiran isowarta. Kaman yanda ta fad'a ba tafi 15 mins tana jiranta ba ta iso wajan cikin adaidaita sahu. Fitowa itama tayi suka shiga ciki tare da samun wuri suka zauna. Suna zama Aina'u tace.." Kinga ni yunwa nake ji,kiyi mana order abinci". Tabe baki Lateefa tayi tace..."ke kike ta abinci saboda dani matsalata daban ta kawo ni nan amma kiyi order duk abinda kike so akawo miki". Abinci mai rai da lafiya tasa aka kawo mata ta fara ci. Aina'u ba tayi magana ba sai da tayi kusan rabin abincin sannan ta d'ago da kai tana kallon Lateefa data zuba mata na mujiya tana kallonta. "Menene matsalar taki Hajiya?" Sauke tagumi tayi tare da sauke ajiyar zaciya tace..." Kema kinsan baya wuce maganan yarinyan nan cos ita kad'aice matsalata a yanzu". Aina'u batayi magana ba sai da ta gama shanye juice d'in da ta d'ora a bakinta sanna ta fara maganan. "But I think mun gama da chapternta tun last week,ko wani abine ya bullo bayan shi?" "Shi d'inne Aina'u,taki haihuwan balle in samu daman aikata abinda nayi niyya.ga cikin shima yaki lalacewa sai dai kullum tana d'aki tana murkususu".tace cike da damuwa. Tunda ta fara Aina'u take kallonta,bata katse ta ba sai da ta kai aya sannan tace.." Wallahi kina bani mamaki yanzu ,Lateefa kaman ba kece mai bani shawara ba da komin saukin abu yanzu sai ki kasa samun bakin zar....." Katse ta Lateefa tayi da..." Ke ni dan Allah ki bar surutun nan ki bani shawara insan abinyi dan ni kaina ya kulle na rasa wani irin tunani zanyi". Aina'u saida ta numfasa tace..." Abune mai sauki Besty tunda kina da kudi,abinda zakiyi gobe ki samu private hospital mai k'yau ki kaita a matsayin kin kaita haihuwa daga nan ki samu babban doctor ki lallab'ashi ya mata alluran da zata shek'a kowa ya huta". Zaro ido Lateefa tayi tana kallonta tace..."Aina'u so like asirina ya tonu?wani doctor zaka kaiwa wannan babban al'amari ya saurare ka?" Aina'u cikin k'wanciyar hankali take cin naman kaza dake gabanta tace..." Dad'ina dake saurin karaya,a duniyan nan wa zaik'i kud'i?millions zaki bashi nasan tabbas da gudu zai share miki hawaye nima zan shigo goben sai mu kaita tare,kada kiji wani abu saboda inaji a jikina matsarki tazo karshe". Haka tayi ta bata shawara tare da karfafa mata guiwa harta amince sannan suka rabu akan sai gobe ta iso. Sai bayan 5:39 Lateefa ta dawo gida, ko ta kan Ameera ba tabi ba tana jiran wayewar gari su aikata barza'u. Ameera cikin baccinta ta fara mafarkin tana jin wani azaba a mararta tun tana daurewa har ta fara juyi na azaba. Wani irin juyi taji cikinta yayi wanda yayi sanadiyar farkawanta ba shiri,kuma sai a lokacin ta tabbatar ashe ba mafarki bane a zahiri take ji ga jikinta duk ya b'aci kaman na lokacin da Lateefa suka d'ura mata magani. Addu'a ta farayi tana hawaye tana cewa a ranta inama ace rana ne da Baba mai gadi yayi mata tofi ta sha ko zata daina jin wannan azaban. D'ago kai tayi tana kallon wall clock dake manne a d'akinta taga 1:30 na dare. Tun tana hawaye tana add'uoi har hawayen suka kafe bakin ma ya mutu murus saina zuci da take. K'ara kallon agogon tayi taga 2:00 ne kawai. Cikin wani wahalalen murya tace " wayyo Ummata ki yafe min nasan yau mutuwa zanyi. Gumi duk ya wanke mata jiki kaman ba a.c a d'akin. Ita kanta ta tabbatar ciwon yau da take ji ya nika wanda da take ji da nikin ba nikin. Har karfe uku da rabi tana nan zaune ko k'wanciya ta kasayi balle wani abu wai shi bacci gashi yau Al'ameen bai shigo ba da ya taimaka mata. A lokacin ne kuma taji fitsari ya cika mata Mara. Yunk'ura tayi da niyan tashi amma ta gagara da haka da rarrafe ta k'arasa bathroom danyin fitsarin amma abin mamaki ta kasa tsugunawa. Zamanta tayi dirshan a cikin bathroom d'in tare da mimmike k'afa. Yunkura tayi da niyan fitsarin amma taji wani abu daban da bata san dame zata k'watanta shi ba yazo ya danne ta ga wani azaba da tunda tazo duniya ko labarin shi bata tab'a jiba take ji. Fasa fitsarin tayi tana yarfe hannu ta rasa ina zata saka ranta taji sanyi. Sau uku tana gwadawa amma sai ta kasa na hud'une taji wani nishi mai karfi yazo mata wanda saida ta toshe baki da hannu dan ji take kaman ta k'wala ihu saboda zaba. Maimakon taji tayi fitsari sai jin wani abu daban tayi ya fad'o harda kuka. A firgice ta kalli wuri yaro ta gani fari sol dashi. Mamaki da tsoro ya hanata tab'a yaron. A wautarta bata San cewa labor take ba ta d'auka irin ciwon nan me da take yi yana lafawa. Zuba mishi ido tayi tana kallon yanda yake tsotsan hannu tare da bin bulb light dake bathroom d'in. Sababbin azaba ta fara ji tana juye-juye,ba'a d'auki lokaci ba ta sankato da baby girl. Cikin ikon Allah tare da mabiyan suka fad'o ta fara cancara kuka. Motsi mutum taji a cikin d'akinta wanda ya haddasa mata tsoro da fargaba. Motsin na kara kusanto bathroom d'in yayin da zuciyarta me kara lugude. Ba kowa take tsoro ba illa Lateefa,cikin daren nan ta same ta da yaran nan komai zai iya faruwa. https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman Yusuf) *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u no pain~* *part thirty nine* Knocking k'ofan bathroom d'in taji anyi wanda saida hanjin cikinta ya kad'a saboda tsoro. Murya k'asa-k'asa taji yace..."Babyna are u alright? " Ajiyar zuciya ta sauke mai nauyi sannan ta saita muryanta da ya dashe tace..."Yayana kaine a wannan lokacin?" "Mafarkai nake tayi akanki shiyasa na kasa daurewa nazo in duba lafiyarki". Murmushi tayi jin furucin shi tace..." Ka shigo mana". "Me kike yine a cikin bathroom at this time har kike cewa in..." Maganan ce ta mak'ale mishi a mak'ok'oro ganin Ameera zaune da 'ya'ya 2 a tsakanin k'afanta. Da sassarfa ya shigo ciki jikinshi har b'ari yake. Idon shi cike da kwalla ya tsuguna kusa da ita. Hannun shi yana karkarwa ya kai yana shafasu cike da so. Juyowa yayi yana kallon Ameera da hawaye shame-shame a fuska dan yama kasa magana. Girgiza mishi kai tayi tana murmushi,kasa daurewa yayi ya jawota jikinshi ya rungume yana kukan farincikin k'yautar da Allah ya bashi,yau shekara goma sha hudu da wani abu da yin aure bai samu haihuwa sai yau. Wani sabon k'aunarta yake jin yana ratsa ko ina na jikinshi. Da k'yar Ameera ta k'wace kanta tace.." Yayana ya isa haka,kaji ana kiran an k'ira sallah tashi ka tafi massalaci". Girgiza mata kai kawai yake yana k'ara matse ta a jikinshi. "Pls ka tafi zaka makara a jam'i don't worry we will be fine". Da k'yar ta samu ya sake ta ya nufi hanya fita,har ya kai bakin k'ofa ya dawo yace..." Kin iya yanda ake yankan cibi?" "Ban iya komai ba amma ka bani Waya in k'ira Umma dan ta iya har gida ake zuwa ana kiranta tana taimakawa masu haihuwa". Bata gama rufe baki ba ya fita da gudu ya d'auko mata wayan ya bata. Wajan da yaran yaje India suke k'wance suna tsoson hannu. Shafa gashin Kansu dake k'wance har wuya ya shiga yi,dariya ce ta tsubuce mishi wanda baisan lokacin da yazo mishi ba ji yake kaman ya maida su ciki yake jin. Dawowa yayi ya k'ara k'amk'ame Ameera yana mata godiya tare da kissing d'inta ko ta ina. Da sud'in goshi Ameera ta samu ta kora shi massalaci dan har an tada iqama lokacin. Number Fateema tayi dialling,a lokacin Umma ta shigo tashinta yin sallah. Ido ta zaro tana kallon Umma tace..." Umma Ameera ce fa". "Ameera kuma da asuban nan,lafiya kuwa?"Umma ta tambaya da damuwa k'arara akan fuskarta. " wallahi bansani ba nima"ta amsa itama cikin damuwa. "Yi maza ki d'auka inji ko lafiya ". Fateema tana d'agawa tace..." Aunty lafiya kuwa?" "Lafiya lau" Ameera ta bata amsa sannan ta cigaba ..."ina Umma?" "Gata nan,ko in bata wayan?"ta tambaya. Amsawa tayi da a bata d'in. Mik'awa Umma tayi tace" ke take nema". Karb'a Umma tayi tasa a kunnenta tace..." Ameera lafiya kira da asuban nan?" Gaisheta ta farayi,Umma ta amsa cikin kotsawa dan ita ba gaisuwarce a gabanta dalilin k'iran take son ji. "Umma in kinyi sallah Ku taho yanzu". A rikice Umma tace..." Inzo yanzu lafiya?" A kunyace tace... " Umma ban iya yanke cibi bane kuma....kuma..."sai tayi shiru. A take damuwar kan fuskarta ya koma fara'a tace..." Masha Allah!! tun yaushe kika haihu?" Murmushi kawai tayi ba tare da tace komai ba . Umma tace.." Toh gamu nan zuwa amma kamin zuwan Mu ki samu towel ko zani ki lullub'e su saboda iska". "To Umma sai kun iso" nan sukayi sallama ta ajiye wayan. Umma ta juyo tana kallon Fateema da take dariya alamun taji zancen ba sai an mata k'arin bayani ba. Had'a rai Umma tayi tace..."ba washe baki zaki tsaya yiba,yi maza ki yi sallah Mu tafi". Da gudu Fateema ta d'auki buta tayi bayi. Al'ameen yana idar da sallah ya dawo wajan 'ya'yanshi ya saka su a gaba yana kallo. Saida tace mishi Umma da Fateema suna hanyan sannan ya hak'ura ya tafi part d'inshi. Ya fita bai jima ba su Umma suka iso. Umma ganin jikoki har 2 a lokaci 1 yasa ta kasa rufe baki sai sannu take ta hero mata. Yanke musu cibi Umma tayi tare da musu wanka ta nannad'esu cikin d'an k'walin Ameera kasancewar ko wando ba'a saya ba. Itama mai jego Umma ta had'a mata ruwa mai zafi sosai tayi mata wanka tayi fes da ita kaman ba ita ta haiho yara 2 nan ba. Fateema kasa ajiye su tayi, tana rungume dasu saii jijjigasu take. Suna zaune suna hira Rabi ta shigo dan dubata. Turus tayi tana kallon su cike da al'ajabi tace..." Ikon Allah mu da muke cikin gidan ma bamu san anyi haihuwa ba,har kuda kuke nesa kunji kun iso?" Umma ta dubi Ameera tace..." Dama 'yan gidan naku basu san kin haihu ba?" Girgiza kai tayi tare da sadda kai k'asa tana murmushi. Ladi tana k'arasowa ciki tace.." Da mun sani ai anan zaki same mu Hajiya". Hannu tasa ta karb'i d'an dake hannun Fateema tana kokarin zama ta hango wani jaririn akan gado. Fara'arta ne ya k'aru tace..." Dama wai 'yan biyu ne?" Dariya Umma tayi tace..." Wancan kishiya ce shiyasa kika ganta a yashe". Dariya suka k'washe dashi dukkansu,Rabi tace.." Ungo mai gidanki dan ni k'awata zan d'auka" Nan ma dariyan suka saka. Saida suka tab'a hira mai cike da bark'wanci sannan Rabi ta fita zuwa kitchen dan had'owa mai jego da bakinta abin kari ta kawo musu sannan ta fara had'a na masu gidan Al'ameen tunda ya koma part d'inshi ya kasa zaune balle tsaye sai zagaye d'akin yake yana ta buga waya yana fad'awa 'yan uwa da abokan arziki. Jinshi yake kaman anyi mishi albishir da gidan aljanna. Sallahn nafila ya rinka jerowa yana mik'a godiyarshi ga Allah na nuna mishi wannan babban rana a rayuwarshi. Wanka yayi ya shirya dan tafiya office. Lateefa yau bata samu baccin safe ba dan ta k'wana da maganan da sukayi da Aina'u a ranta. Tana zuwa parlour taga kan dinning wayan ba komai. Bud'e murya tayi ta fara k'walawa Rabi k'ira. Da sauri Rabi ta iso gabanta ta zube a k'asa tace..." Gani Hajiya". "Wani irin rashin mutunci ne yasa har yanzu baki gama breakfast ba?" Ta tambaya tana harararta. Rabi kai na kasa tace..." Kiyi hak'uri Hajiya gidan ne da baki shiyasa". "Baki,wani irin baki kuma ya ban gansu ba?" "Suna can sashin Amarya" ta bata amsa. Zuciyarta ne ya buga da karfi can kuma wata zuciyar tace..."ko Allah ya takaita mata wahala ta shek'a cikin dare. Atake taji wani dad'i ya ziyarci zuciyarta,tana murmushi tace..."meye ya faru a part d'in nata?" " *HAIHUWA* tayi Hajiya"Rabi ta bata amsa. https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀🙆‍♀ *~UKUBAR KISHIYATA 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman Yusuf) *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u no pain~* *part forty* Wani abu mai kama da mashi Lateefa taji ya soke ta a kirji,ga wani d'aci daya taso mata Wanda bata san ta ina yazo ba saiji tayi ya cika mata mak'ok'oro. Da k'yar ta saita kanta gudun kada Rabi ta fahimci halin da take ciki tace..."naji tashi ki tafi ki k'arasa aikinki" Mik'ewa Rabi tayi tana dariya a cikin ranta tace..."duk *UKUBAR* da zaki gana mata baki isa ki canza abinda Allah ya tsara ba. Rabi tana b'ace mata ta fad'a kan kujera ta baya dab'as ta zauna dan dama jiri take gani daurewa kawai take.. Ta rasa wani irin tunani zatayi,wani sashi na zuciyarta yace kije ki gani da idonki kamin ki yanke hukunci. A zabure ta mik'e kaman wacce aka tsikarawa allura tayi part d'in Ameera. Tana shiga ta samesu sun saka kayan breakfast da Rabi ta kawo musu a gaba Umma tana yiwa Ameera fad'an ta shanye tea d'in da ta had'a mata. Zama tayi kusa da Ameera tana dariya wanda yayi kama da mai nishin kashi. Gaida Umma ta farayi sannan ta juyo tana duban Ameera tace... "Haba k'anwata muna cikin gidan nan amma ki haihu ke kad'ai ba k'ya tsoron wani abu ya faru dake?" "Yanzu na gama yi mata fad'a kada ta sake irin wannan koda a gaba ne"Umma tace mata. Lateefa ji yayi kaman an watsa mata tafashasshen ruwa ajiki. Tana yiwa Umma wani irin kallo ta k'asan ido kuma tana magana a zucoyarta tace kaji min munafukar tsohuwar nan har wani haihuwa 'yar taki zata k'arayi a gidan nan wannan ma sakaci nane but zan baku mamaki a gaba. K'ara had'iye damuwarta tayi tace..." Ina jinjiran ko jinjiri muka samu?" Umma ce ta bata amsa da.."gasu can kan gadi" Cike da fargaban me Umma take nufi gasu can ta juyo ta dubi kan gadon. Idanunta kusan zazzagowa suka yi ganin twins a kan gado,zuciyarta kuma kaman ya fashe take ji. Da k'yar ta daure ta rarrashi kanta ta mik'e ta iso bakin gadon tana lek'ensu. Wannan karan da k'yar ta hana bakin ta kurma ihun da yazo mata ba shiri. Umma da Fateema suna cin abinci basu lura da yanayinta ba amma Ameera tana kallonta ta k'asan ido. Ko d'aukansu batayi ba tace..." Ina zuwa ta fice cikin sauri saboda ta tabbata tana k'ara minti 2 a gaban yaran nan zata iya aikata abinda bashine ba a gaban mutane. Tana fita yayi daidai da sauk'owar Al'ameen daga part d'inshi. Ya lura da yanda ta birkice amma ya basar yace.." Ya naga kan table bakomai ko masu aikin basa nan ne?" Da gudu Lateefa tayi kanshi tare cin k'walan rigan shi tana jijiga shi ta fara bala'i.."Al'ameen wallahi kayi kad'an ka wulakantani a gidan nan daga kai har ita baku isa komai a wajena ba,munafuki kawai in banda munafurci kaida nayi maka iyaka da wannan yarinyan ta yaya ka ka tsallake kaje kayi mata ciki? Iye tambayarka nakeyi" Murmushi kawai Al'ameen yake yana kallonta,a haka Aina'u ta shigo ta same su. Da k'yar Aina'u taja ta zuwa part d'inta. Gyara zaman rigan shi yayi ya shige part d'in Ameera hankalin shi k'wance. A parkour ya iske Umma da Fateema suna kintsa mata. Durk'usawa yayi har k'asa ya gaida Umma,Fateema ma ta gaishe shi sannan ya wuce ciki bedroom inada Ameera da twins d'inta suke. Ameera tasa twins a gaba tana ta kallo tana mamakin wai a jikinta suka fito. A haka Al'ameen ya shigo ya same ta. Zama yayi a bakin gado suka sakarwa juna murumushi ya shafa gefen fuskarta yace..." Maman twins kinyi kokari ya jiki ?" "Da sauki" ta bashi ansa. D'aukan Baby boy d'in yayi yayi mishi hud'uba yayi pecking goshi shi sannan ya rungume shi yana k'ara jin k'aunar yaron yana ratsa ko'ina a jikin shi. Da k'yar ya ajiye shi sannan ya d'auko Baby girl itama yayi mata d same thing ya ajiye ta. Yana juyowa yaga Ameera ta zuba musu ido tana murmushi,gira d'aya ya d'aga mata yace..." Ya dai?" "Bakomai kallo nake" ta bashi amsa tana murmushi. Dungure mata kai yayi yana dariya yace ..." 'Yar sa ido kawai". Dariya itama tayi batayi magana ba. Nan yake tambayarta abinda ya kamata ya sayo musu. Cewa tayi ya tambayi Umma ta gaya mishi. "OK ke bazaki gaya min ba?"ya tambayeta. Amsa mishi tayi da..."kasan tafini sanin abinda ya dace". " hakane,na tafi saina dawo"yace tare bata Peck sannan ya fito parlour wajansu Umma. Dukawa yayi ya tambayi Umma abinda ya dace ya sayo,nan tayi mishi bayanin abubuwan da ya dace ya sayo irinsu madaran da zasu sha towels,kayan sawa,kayan sanyi da sauransu. Ya mik'e da niyan fita Hajiyar shi tayi sallama ta shigo. Komawa yayi ya zauna suka gaisa ya mata jagora zuwa d'akin mai jego sannan ya fita siyan abinda aka lissafa mishi. Lateefa tana zaune sai cika take tana batsewa tana ciccize leb'e. Aina'u tace" wai meya faru na ganki haka,ki tashi tunda ya fita mu kai shegiya ayi mata alluran mu huta". "Komai ya lalace Aina'u komai ya wargaje" Cikun rashin fahimta Aina'u take kollonta tace..."bangane komai ya lalace ya wargace ba". Murmushin takaici Lateefa tayi tana kallonta k'awarta tace.."ta haihu,ta haifi 'ya'ya har 2". D'ora hannayenta duka 2 Aina'u tayi tana salati tace..."2? Lateefa bama d'aya ba?" "Saima kin gansu zuciyarki zata iya bugawa" Lateefa tace tana goge hawayen daya zubo mata. "Haba dole in ganki cikin tashin hankali,kuttt ya akayi kika bari ta haihu baki kashe shegiya ba?" Aina'u ta tambaya cikin tashin hankali. "Cikin dare ta haihu kawai ganinta nayi yara da safen nan,ita kuma munafukar uwarta harda cewa nayi mata fad'a haihuwa ita kad'ai koda gaba ta nemi mutum kusa da ita" ta karasa maganan cikin k'waikwayon muryan Umma. "Kaji 'yar abu kazan uba,kinsan abinda zamuyi wajan boka zamu koma ya kashe yaran shima munafikin mijin naki muyi maganin shi ya kasance naki ke kad'ai". Ajiyar zuciya Lateefa tayi tace..." King Aina'u na fara tsinkewa da al'amarin nan kuma...." Pls kuyi manage da wannan. 🙆🙆🙆🙆🙆🙆 *UKUBAR KISHIYATA* 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman Yusuf) *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION~*💫💫💫 ❄ *~we bearer's of golden writer's assiduously percieven No pain so Magical our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u no pain~*❄ https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ *Part forty one* "Ke dallah dakata" Aina'u ta katse ta tana huci. "Karki bani kunya mana sai kace ba Lateefa 'yar k'walisa ba,ta yaya zaki basu chance suyi winning akanki.just ki bani wuka da nama kiga abinda zai faru but for now dole ki daure zuciyarki karki sake ki nuna musu ba k'ya farinciki da haihuwan nan yanda koda daga baya wani abu ya faru ba wanda zai zarge ki.bayan suna sai mu koma wajan boka".... Lafuza da shawarwarin Aina'u sunyi tasiri wajan k'wantarwa Lateefa hankali tare da d'aukan alkawari zata daure ayi komai da ita. Al'ameen yana fita wani babban shopping mall da ake saida kayan babies suka je shida driver. Kaya Al'ameen yake ta k'wasa kaman ba gobe,yawanci bala ke nuna mishi abinda ya dace ya saya kasancewar shi yana da yara har 3. Saida suka cika trolley 3 da kayan babies sannan suka dawo gida. A lokacin gidan a cike yake tap da 'yan barka,kama daga matan brother's d'in Al'ameen da 'yan uwan Ameera duk sun iso gani. Haka gidan ya kasance kullum cike da 'yan barka. Lateefa ta daure zuciyarta akayi ta hidima da ita mutane sai yabon k'yan halinta suke. Ranan suna yara suka cika sunan parents d'insu wato Mudassir mai sunan Alhajin Al'ameen sai Hadiza wacce taci sunan Umma Ameera. Anyi shagali kaman ba gobe an bawa naira kashi sosai kowa da yazo sunan sai ya tafi da katuwar jaka cike da gifts. Ameera da twins suma sun samu gifts daga 'yan uwa kala-kala.tun daga kan uban gayya wato Al'ameen,iyayen shi da 'yan uwanshi wanda ya kara hura wutan tsana su a zuciyar Lateefa.. Bayan suna da k'wana 2 Umma tace zata tafi da Ameera gida wanka. Bori Sosai Lateefa ta tayar wai za'a rabata da 'ya'yanta harda kukan munafurci. Ganin yanda ta dage yasa Umma tace toh su zauna ita da Fateema kuma zata turo da Gwaggonsu ta cigaba da yi nata wanka. Lateefa ba haka taso ba,taso ace ita kad'ai aka barwa Ameera da yaranta yanda zataji dad'in b'atar dasu ba tare da wani ya ankara ba. Ta wani side kuma taji dad'i tunda komai zasuyi a gabanta za'ayi. Kusan kullum a part d'in Ameera take wuni ana hira da kula da twins tare da ita. Sosai Gwaggo take jin dad'in zama da ita kuma take yabonta harta kai tana yiwa Ameera fad'a tabi ta su zauna lafiya dan a wannan zamani kamin ka samu mace kamar Lateefa sai an tona. Shiru kawai Ameera take in taji Gwaggo tana irin wannan magana saboda ko tayi niyyan fad'awa Gwaggo halin da take ciki a sanadin Lateefa sai taji kaman ansa super glue an like mata baki. Satin ta 2 da haihuwa babban jikan Gwaggo ya rasu ta tattara zata tafi zaman makoki Fateema ta rakata suka tafi tare. Gida Fateema ta wuce daga gidan rasuwan wai tayi missing Ummanta. Wuni tayi a gida suna hira da Umma sai bayan 5 tayi shirin komawa gidan Ameera nan Umma ta had'a mata kayan gyara tare da jadddawa Fateema ta fad'awa Ameera ta kula da kanta. Da zata tafi Abba ya kawo ruwan Addu'a ya bata yace ta kaiwa Ameera su sha ita da yaranta kullum da safe kamin taci komai kuma in zasu k'wanta su shafa jikinsu dashi harna tsawon k'wana 7. Fateema tana zuwa tayi mata bayanin kayan da Umma ta bata dalla-dalla sanna tayi mata bayanin ruwan addu'an. A ranan suka fara amfani dashi har zuwa k'wana 7 kaman yanda aka umarce ta. Kuma a ranan Fateema ta had'a kayanta zata koma gida soboda zasuyi resuming school. Da daddare Al'ameen ya maida ta gida bayan sun cika ta da sha tara na arziki harda Lateefa wacce farinciki ya cika mata ciki sun watse sun bar Ameera zata cika burinta cikin sauki. Da washe gari da safe Ameera tana shirin yiwa Fadeel da Fadeela wanka( sunan da Fateema ta zab'awa twins a rinka kiransu dashi kenan)su Fa'iza da Shamsiyya sukayi sallama suka shigo. Amsawa tayi tana mamakin wai yau ita su Fa'iza kewa sallama. Gaisheta sukayi ta amsa still a mamakince. Fa'iza ta tambaya "ina twins ne?" "Gasu can a cikin gadonsu yanzu nake shirin yi musu wanka". Shamsiyya tace ..." Dama Aunty ce tace ki kawo su tayi musu wanka". "Wanka kuma" ta tambaye su. "Eh saboda ta tayaki ne yau taga bakowa Fateema ta tafi". Fa'iza ta amsa mata. Kaman zata kara cewa wani abu kuma sai tayi shiru. Wani k'aramin basket d'insu ta d'auko tasa kayansu kala 2-2 dasu diapper,su mai,powder da sauran kayan amfaninsu ta mik'a musu . Shamsiyya ta d'auki Fadeel,Fa'iza kuma ta d'auki Fadeela suka fita. Suna fita direct part d'in Lateefa suka wuce dasu,dama tana zaune tana jiransu. Da sananin murna ta karb'i yaran tayi ciki, su kuma suka fita zasu tafi gidan binta tare da mamakin canzawar Auntyn nasu. Ruwan sanyi Lateefa ta tara a bathtub sannan ta saka yaran aciki ta barsu suna ta tsala kuka kaman ransu ya fita. Tana dariya ta fito parlour ta kira Aina'u tace..." Gasu can na saka su a cikin ruwan sanyin kaman yanda kika ce". Dariya Aina'u tayi tace..." Kai Besty baki da wasa wallahi yanzu kukan sune nake ji haka?" Dariyan itama ta shek'e dashi tana..." Ta ina zanyi wasa da wannan babban dama da na samu". " gaskiyane yanzu saura step 2" inji Aina'u,suka sa dariya a tare. Tana gama wayan ta koma wajansu duk sun galabaita ba bakin kukan sai idonsu da yake a lumshe. Fito dasu tayi a cikin ruwan ta dawo d'aki ta k'wantar dasu a kan tiles babu kaya a jikinsu balle ta lullub'e su da towel. Kara karfin a.c d'akin tayi ta fito parlour ta k'wanta bayan ta kulle k'ofan harda murza key. Ameera tunda aka fita da yaranta taji sam hankalinta bai k'wanta ba. Bayan tayi wanka ta shirya ta d'an kishingid'a akan 3 seater tace bari ta bada 10 to 15 mis in basu dawo dasu ba zuwa zatayi ta karb'o kayanta. Tana k'wanciya wani bacci mai nauyi yayi gaba da ita sakamakon jiya daddare Al'ameen ya hanata bacci da wuri da fitinan shi dama kaman jira yake Fateema ta tafi. Bayan good 2 hrs Lateefa ta tashi cike da d'aukin ganin halin da suke ciki ta bud'e k'ofan ta shigo. Farinciki fal zuciyar Lateefa ganin basa motsi. Turus tayi tana kallon yanda suke fitar da numfashi a hankali da alama baccin su yayi nisa. Cike da takaici take tsaye akansu tana tunanin abinyi wata zuciyar tana bata shawaran ta shake su kawai su mutu ta huta amma wata zuciyar ta hanata. Basket d'in kayan su ta jawo tasa musu diaper da kaya ko mai bata shafa musu ba ta fito tana k'walawa Ameera kira. A nan parlour sukayi clashing da Ameera da farkawarta kenan kuma ta fito neman yaranta . Mik'a mata su tayi tace ..."wuce kije ki basu nono yunwa suke ji". Ameera tana karb'ansu taji jikinsu sanyi kalau kaman kankara. A razane ta d'ago tana kallon Lateefa wanda har saida itama Lateefan ta firgita jin tambayar da Ameera tayi mata. " meye ya faru dasu naji jikinsu sanyi kalau haka"Ameera ta tambaya tana kallonta. Wani yawu Lateefa ta hadiye na mamaki had'e da tsoron me yake shirin faruwa a gidanta. Cikin inda-inda tace..." Ke ni kikewa tambayan rainin wayon nan?" Murmushi Ameera tayi tace..." Ki sani ni Ameera ba zan tab'a zuba miki ido ki cutar min da yara ba,amma in kina ganin zaki ita toh bismillah kuma ina tabbatar miki in har wani abu ya samu yarana hmmm" tana gama fad'an haka ta juya tayi part d'in ta da yaranta ko d'ar babu a zuciyarta bata san dalilin da yasa ta rage tsoron Lateefa ba Dan cikin 100℅ 70℅ ya ragu. Lateefa kam daskarewa tayi a wajan ko yatsanta ta kasa motsawa dan bata gama yarda wai Ameera ce ta gaya mata wa'yan nan magagganun ba. 🙆🙆🙆🙆🙆🙆 *UKUBAR KISHIYATA* 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman Yusuf) *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION~*💫💫💫 ❄~*we bearer's of golden writer's assiduously percieven No pain so Magical our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u no pain~* https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ *forty two* Lateefa da k'yar ta dawo hayyacinta tana tambayar kanta meke faruwa ne? Juyawa tayi cikin sauri ta koma part d'inta tare da dannawa Aina'u k'ira. Bai dad'e yana ringing ba ta d'aga tana cewa..." Nasan kin kira ne dan bani good news,yah sun shek'a?" Lateefa a hasale tace..." Ke yi min shiru wani good news zan baki yara da shegen taurin rai,ba abinda ya same su lafiyarsu k'alau.ni ba wannan ba yarinyan nan wai yau har ita take kallon tsakiyan idona ta gaya min magana". " wacce yarinya kuma kika samu?"Aina'u ta tambaya. A zuciye Lateefa ta amsa mata da..." Wace yarinya kuwa banda wannan 'yar iskan gidan nan,akan way'an nan b'erayen nata ta dubi cikin idona tace in wani abu ya same su in kuka da kaina". " wai Ameeran ce tace miki haka?"Aina'u tace cike da mamaki. Kwafa kawai Lateefa tayi ba tare da tace komai ba. Aina'u ta cigaba cewa..."lalle akwai matsala dole mu koma wajan boka but before then ya kamata ki koyawa shegiya hankali kamin in dawo muje dan yanzu haka ina hanyan zuwa Kano nida Alhaji nura amma k'wana 2 kawai zanyi,ki nuna mata ko ba boka kinfi karfinta". Cike da k'warin guiwa Lateefa tace..." Off course wallahi ubanta zanci a gidan nan dole tasan ni Lateefa nafi karfin uwarta bare ita useless da ita". Shawara sosai Aina'u ta bawa Lateefa wanda yasa mata natsuwa da courage akan gallazawa Ameera sannan suka rabu akan sai tazo jibin. Ameera tana shiga part d'inta ta hada ruwa mai zafi sosai tayi musu wanka dashi tare da shafa musu baby oil jikin su sosai sannan ta saka musu kayan sanyinsu,ta had'a musu madara ta basu suka sha suka koma bacci. Saka su tayi agaba tana kallon yanda suke had'a gumi a goshinsu,sai a lokacin hankalinta ya k'wanta. Tana zaune tana accusing kanta meye dalilinta na basu yaranta bayan tasan ba k'aunarta suke ba bare abinda ta haifa. A yanda take jin yaranta a cikin ranta zata iya yin komai kuma da kowa da yayi niyar cutar mata dasu. Har dare basu had'u da Lateefa ba ko wacce tana part d'inta. Al'ameen yauma ya shigo da daddare duk suka isheta da fitina da shida twins,bata samu bacci ba sai kusan asuba. Koda tayi sallahn asuba komawa baccinta tayi tare da tura Fadeel da Fadeela wajan Rabi dan tayi musu wanka. Tana tsakiyan baccinta kaman daga sama taji saukan ruwan sanyi a jikinta Wanda yayi sanadin farkawarta agigice. Lateefa ta gani tsaye a kanta rik'e da k'ugu tana girgiza cike da masifa. Tashi Ameera tayi tana gyara zaman Rigan bacci ta. Lateefa ta fara zuba mata ruwa bala'i. "Samun guri da k'wanciyar hankali,iyyeh har baccin safe kika samu yanzu Dan kinga k'wana 2 ina d'aga miki k'afa kina jin kanki kamar wata toh bari in gaya miki as from now hutun da na baki ya kara daga yau zaki dawo bakin aikin kamar yanda kike da.ki wuce yanzu ki had'a min breakfast kuma 5 mins na baki just 5mins ko minti d'aya kika k'ara akai kema kinsan sauran". Tunda ta fara magana Ameera take kallonta tana mamaki . Ganin ta ida masifarta yasa itama ta shanye nata mamakin ta fara maida mata martani. " na farko ke wacece wama ya baki izinin shigo min har bedroom saboda rashin tarbiya,maganan ina d'aukan kaina ni wata ce kinyi kuskure anan ni ba wata bace amma ina da matsayin da wasu suna nema da milliyoyin kudi amma basu samu ba,ni UWACE nayi miki gya..." Lateefa al'ajabi ya gama daskar da ita ta NASA cewa komai sai ido da ta zuba mata amma kalamanta na karshe su suka harzuk'ata har ta d'aga hannu da niyan marinta amma Ameera tayi caraf ta rik'e hannun. Tana murmushi tare da girgiza mata kai tace..." Don't ever make this mistake in ur life saboda in har baki rik'e girmanki ba ni kuwa zansa k'afa in taka ta"tana gama fad'an haka tayi jifa da hannun abinka da mai kib'a tayi tangal-tangal ta fad'a kan stool din gaban mirror Ameera har ta na buge goshinta. Ameera ko kallonta bata k'arayi ba ta fad'a bathroom tare da bango mata k'ofa da karfi. Lateefa jiki duk jiki yayi yayi tsami more especially goshinta har ya taso haka taja jiki ta fice mata a daki. Al'ameen mamaki fal a ranshi wai Ameera ce tayiwa Lateefa haka,tayaya hakan ta faru?amma can k'asan zuciyar shi kuma dad'ine fal. Basarwa yayi yana wani yamutsa fuska yace.."wacece haka sabuwar 'yar aiki kika samu?" Farinciki ne ya lullub'eta ganin har yanzu asirin bai bar jikin shi ba. " ka kirata yanzu ka korata gidansu dan nagaji da ganinta cikin gidan nan".ta fad'a in a commanding way. Mik'ewa yayi ya nufi hanyan part d'inshi yace..."tunda a karkashin ki take ke ya kamata ki Kore ta bani ba dama me kike d'ebo 'yan aikinki". Takaici duk ya cikata ta rasa ya zatayi can wata zuciyar yace ta k'ira k'annenta su dawo mana tasan su zasu iya maganinta. Nan take ta k'ira Shamsiyya tana d'auka ta fara sauke mata bala'i da take dannewa a ranta. "Bansan wani irin hankali gare Ku ba,in banda shashanci daga yiwa k'awarku aure sai kuje Ku tare mata a gida haka akeyi?toh ina gaya muku duk abinda kuke Ku bari Ku dawo gobe ina nemanku kuzo Ku min maganin k'aramar 'yar iskan gidan nan". " Aunty wa kike nufi wai kuma meya faru?" Nan ta basu labarin abinda ya faru tsakaninta da Ameera. Fa'iza sai huci take har ji take kaman ta faso ta cikin wayan . Hakuri suka bata suka ce gobe da sassafe zasu shigo su gyara mata zama. Al'ameen daya sauk'o k'asa yaga Lateefa ta tashi bata parlour,bai tsaya bata lokaci ba ya fad'a part Ameera ya same ta tanawa babies d'inta wasa hankali k'wance . K'arasowa yayi ya zauna tare da sa hannu ya d'auki Fadeela ya fara mata wasa yace...."Maman twins kin ganki kuwa kullum k'afa k'yau kike meye sirrin ne?" Ajiye Fadeel tayi ta juyo gare shi haba d'aya tana fuskantan shi..." Kaine sirrin Yayana". Kanne mata ido d'aya yayi yace..."kin tabbata?" Dariya tayi tana gyad'a mishi kai. Zama yayi sunsa yaransu a tsakiya suna ta hira,anan yaci abincin shi na dare. Shi bai koma part d'inshi ba sai bayan sallahn asuba. Wanka yayi ya shirya ya fita office. Ameera zama cikin d'aki ita kad'ai ya isheta,yau suka fito ita da yaranta main parlour dan shan iska. Canza channel tayi daga MBC Bollywood zuwa saudi2 tana sauraron karatun alqur'ani. Bata dad'e da zama ba Lateefa ta fito tana yamutsa fuska. Daram zuciyarta ya buga da karfin gaske ganin Ameera ta baje tana kallo. Tana son tanka mata amma wata zuciyar ta hana ta ,kar ta gama zubar da ajinta bari ta hira zuwan su Fa'iza. Kan dinning ta wuce ta fara breakfast tanayi tana satan kallon Ameera da take harkokinta ta d'auke kai kaman bata san da ita ba a parlour. Tana mamakin yanda abin ya juye lokaci 1 haka kaman ba Ameerar da bata iya mata magana sai a duke ba kamar ba Ameerar da in ba cewa tayi tashi anan ba bata isa ta motsa ba kaman ba Ameerar da...shigiwar su Shamsiyya shi ya katse mata zancen zuci da take. Suka wuce Ameera suna mata kallon banza ita ko ta bawa banza ajiyarsu. Bayan kus-kus da sukayi da Auntynsu suka nufo ta gadan-gadan dai-dai lokacin kuma Fateema tayi sallama ta shigo. 🙆🙆🙆🙆🙆🙆 *UKUBAR KISHIYATA* 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman Yusuf) *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION~*💫💫💫 https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *_~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~_* *part forty three* Shigowan Fateema bai hana su Fa'iza k'arasowa gaban Ameera ba kowacce tana k'okarin kai mata bugu. Da gudu Fateema tazo ta shiga tsakaninsu tana..."me zan gani haka wani irin dabbobi ne ku?" Ameera ko k'ala bata ce musu ba saida ta k'washe yaranta ta kaisu safe place sannan ta dawo ta samu har sun fara gabazawa da Fateema,Lateefa tana gefe tana suyi kasa-kasa da ita sannan su bi Ameera data gudu. Ameera tana zuwa batayi wata-wata ba ta finciko Fa'iza ta gashin kanta da yasha Brazil. Ihu Fa'iza tasa tana neman k'watan kanta amma ta kasa ga bakinta yaki mutuwa sai zagi take aikawa Ameera. Buge bakin zagin Ameera tayi da iya karfinta sai ga bakin yana tsiyayan jini,wancalar da ita gefe ta fad'a kan glass center table. Kasa tashi Fa'iza tayi illa dafe goshinta tayi da yake ta zubar da jini tana kula. Tana juyowa d'ayan side sai ganin Fateema tayi ta haye ruwan cikin Shamsiyya sai bugu take kai mata kota ina. Murmushi Ameera tayi ta juyo arean dining inda Lateefa take zaune. Suna had'a ido Lateefa ta mik'e jiki na b'ari tayi hanyan part d'inta dama a tsorace take tana mamakin wani irin karfine dasu duk sun raunata mata k'anne. "Ina zaki je?ki tsaya ki nuna min jarumtar ki,ki tsaya nace".Ameera ce ke fad'an haka lokacacin da ta bin bayan Lateefa da gudu. Tsantsin tiles ne ya k'washi Lateefa sai gata tayi zaman 'yan bori a kasa. Dakewa tayi ta juyo ga Ameera duk da a tsorace take hakan bai hana ta fara cika baki ba harda zagi..."Dan ubanki karki ga ina kyale ki ina nan a Lateefa ta da kika sani ba zan tab'a canzawa ba Kuma dole ki kasance a karkashin iko na in mulke Ki dan Abu Kazan ubanki.." Ameera batayi niyyana tab'ata ba amma jin zagin da take antayo mata yasa ta jawo wire receiver da yake gefen kayan kallonsu ta shiga lafta mata ta ko ina. Lateefa duk iya kokarinta na ganin ta kare kanta kasawa tayi. Ganin in batyi da gaske ba zata sha wiya,hankad'a Ameera tayi da duka karfinta tayi hanyan part d'inta da gudu. Tsayawa Ameera tayi tana dariya har da fad'uwa kan kujera ganin yanda Lateefa take k'wasan gudu jiki na rawa. Da k'yar ta d'aga Fateema akan Shamsiyya da tasha mazga. Zama Fateema tayi tana huci tace..." Wallahi Aunty ke kike sake musu har suke k'okarin tab'a lafiyarki,wallahi kun ci sa'a yau ina cikin mutunci if not hmmm mayu duk kunsa min 'yar uwa a gaba ganin ba abinda 'yar uwarku ta iya sai katon kashi." Ameera dai dariya take tayi mata tace..." Haba Fateema duk suburbud'an da kika yi mata kike cewa haka?" Fa'iza da Shamsiyya da k'yar suka ja jikinsu suka fece daga gidan gaba d'aya ba tare da kowa ya lura dasu ba. Lateefa tana cikin d'aki sai kaiwa da komowa take ta rasa me yake mata dad'i a rayuwa jikinta duk yayi rud'u-rud'u da shatin wire. Waya ta d'aga ta k'ira Aina'u tasa mata kuka. Hankali tashe Aina'u take take tambayar ta me yake faruwa? Da'kayar ta tsagaita kukan ta bata labarin abinda ya faru dasu yanzu. Ashar Aina'u ta fara d'urawa tana kunfan baki tace yau d'in nan zata taso wallahi sai sun koya mata hankali sannan su koma wajan boka yayi maganinta. Da washe gari da sassafe Lateefa ta fita sannan ta k'ira Aina'u tace ta fito tazo su wuce. Bata wani dad'e ba tazo ta same ta suka tafi. ****************** Dariya boka ya bushe da ita yana kallon yanda Lateefa da Aina'u sukayi tsuru-suru suna sauraron shi. " dukansu 2 kike son akashe?" Da sauri ta amsa da..."eh boka dan rayuwar yaran nan tashin hankaline a gare ni". "Za'a kashe su duka amma ba yanzu ba sai mun tura bak'ak'en aljanu suyi ta azabtar dasu zuwa shekara d'aya sai a kashe su,kin amince da wannan shawaran?" Cikin jin dad'i ta amsa.." Na amince boka dan ni hakan ya min dad'i sosai kuma boka ina son a mantar da Al'ameen yaran nan da ita uwarsu gaba d'aya". Wani d'an k'aramin sanda da aka laulaye shi da guraye ya mik'o mata yace...bansan ya akayi kikayi sake har tasha abinda ya karya kusan duka sihirin da yake jikinta ba kuma a halin yanzu ba wani aljani da zai iya tunkarta saboda haka ki samu dama ki ajiye mata wannan sandan a karkashin gadonta kuma ki tabbatar a k'wance kika ajiye shi". D'an dakatawa yayi sannan ya cigaba..."ina gaya miki koda yayi satan k'afa ya shiga d'akinta toh ba abinda zai iya tsinana mata balle harta k'ara haihuwa a gidan". Farinciki mara misali ne ya lullub'e Lateefa jin abinda boka yace mata. Godiya suka mishi tare da tula mishi mak'udan kud'i suka fito. Lateefa bata samu tangard'a wajan aiwatar da duk wani sharad'i da boka ya bata ba komai ya tafi dai-dai yanda take so. Aikin boka yayi k'yau as usual dan yanzu Al'ameen ya manta hanyan part d'in Ameera balle ita da yaranta.. Haka Ameera take rayuwarta da yaranta duk da rashin kula da Al'ameen yake musu yana damunta amma ta daure tana sha'aninta. Lateefa tunda tasha suburbud'a a hannun Ameera bata k'ara shiga harkanta ba,hankali k'wance take jiran time d'in da boka ya bata yayi taje a gama mata dasu. Fadeel da Fadeela yau kusan suna da 6 months amma in ka gansu zasu baka tsoro saboda kamanninsu gaba d'aya ya canza ko zama basu iya ba sai mugun cin abinci. Ranan wata talata Fateema ta kawo musu ziyara tare da fad'a mata auren 'yar k'anwar Umma da za'ayi nan da 3 weeks. Fateema tunda ta shigo take kallon yaran da damuwa a fuskanta tace..." Ameera ya nake ganin kaman abin nasu gaba yake dan last time da nazo kaman bai kai haka ba". Sauke ajiyar zuciya Ameera tayi da matuk'ar damuwa akan fusksnta tace.." Bansan ya zanyi ba Fateema hakan ma da kike gani da sauki dan d'azu nayi musu addu'a na shafa musu ajiki". "In na je gida zan fad'awa Umma ta fad'awa Abba yayi musu addu'a". Fateema tace haka tana d'aukan Fadeela. Girgiza kai Ameera tayi tace..." Karki fad'a musu ki tayar musu da hankali nafi son inje da kaina ya gansu". " shikenan ba zan fad'a ba Allah ya kaimu lokacin kije da kanji"inji Fateema. Haka Fateema ta wuni mata sai yamma lis ta koma gida. Ameera tana son fita zuwa bikin amma ta rasa ya zatayi taga Al'ameen ta tambaye izinin fita. Ana gobe zata je bikin ta fito ta zauna a main parlor ko zata gan shi. Tana nan zaune har bayan sallahn isha'i sannan tagan shi ya shigo dawowar shi daga masallaci kenan. Suna had'a ido dukkansu saida zuciyar su ya buga a tare. Ameera ganin duk ya lalace ya rame yayi baki kaman bashi ba shiyasa zuciyarta bugawa tana tunanin me yake damun shi ya lalace haka?. Shi kuma ganinta da yayi yau shiya tuna mishi da ita a rayuwar shi. Yana son sake kallonta amma yaji wani haushinta yake ji dan haka ya d'auke kai yayi hanyan part d'in shi. Da sauri tace..." Yayana..." Tsayawa yayi can ba tare da ya juyo ba. Ganin ya tsaya yasa ta taso da sauri tazo ta tsaya a bayan shi tace..."yayana meya faru ko ince me nayi maka ne ka yanke yi mana wannan babban hukuncin nida yaranka?" Tafiyan shi ya cigaba dayi ba tare da ya tanka mata ba. Hawayen idonta ta share tace.." Ina Neman izininka zanje gida gobe saboda muna da biki zanyi k'wana 2 kamin in dawo". Ware hannayen shi yayi irin who cares d'in nan ya k'arasa bakin stairs inda Lateefa take jiran shi da murmushin farnciki a fuskanta tace..." My Ameen meya had'aka da wannan idiot d'in?" "Pls ki daina b'ata bakin ki akan useless thing my Lateefa". Dariya tayi suka haura sama suka barta nan tsaye tana hawaye. Ranta bai tab'a b'aci akan halin ko in kula da Al'ameen yake musu kaman yau ba,toh me yake nufi da ita? In har ya daina sonta ne ya sauwaka mata ta koma gidan iyayenta ko zataji sauki. Saida tasha kuka sosqi a wannan daren da k'yar ta samu bacci ya d'auke . Da washe gari da sassafe ta tashi ta had'a musu kayansu a d'an k'aramin trolley. 9am sun gama shiri tafiya tsab. d'aukin yau zata je gidansu yasa ko breakfast bata tsaya yiba su Rabi suka rakota da kayanta har wajan mota. Bala driver yana ganinsu ya taso da sauri ya fito da mota sannan ya karb'i trolley a hannun Rabi ya saka a boot sanna yaja mota suka fita su Rabi suna ta d'aga mata hannu cike da kewanta. Bala yana parking a k'ofar gidansu ta fito tana mamakin yaushe aka gyara musu gidan ya koma haka. Kota kan kayansu bata bi ba ta Shiga gida da matuk'ar sauri kaman ta kifa tare da k'walawa Umma k'ira. Fateema ce ta fito da gudu suka rungume juna a zaure tasa hannu ta karb'i Fadeel suka karasa shigowa cikin gida. Umma ta fito cikin farinciki daga kitchen inda take aikinta tana musu lalle marhabin. Tabarma Fateema ta shinfid'a musu a bakin sabon parloursu suka zauna ana gaisawa. Bala yayi sallama ya shigo da trolley su tare da gaishe da Umma sannan yayi musu sallama ya tafi. Nan Ameera take tambaya ina Abbanta?Umma ta amsa mata daya tafi duba wani abokin shi da bashida lafiya. Ajiye mata yaran sukayi suka shige d'akin Fateema data sha gyara tana bata labarin Ai Al'ameen ne yayi musu gyra nan. Tunda suka shiga Umma take kallon yanda yaran suka canza kaman basu ba,ga Ameera itama duk ta canza kana ganinta zaka San tana cikin matsala ba sai an fad'a maka ba. Cike da damuwa Umma ta k'wantar dasu ta koma kitchen ta cigaba da aikinta zuciyarta a cunkushe. Ameera suna d'aki Umma ta gama jefa d'an waken da take ta k'ira Fateema ta kai musu d'aki suka faraci. Sun kusa gamawa suka ji muryan Abba yayi sallama ya shigo. Da matukar Murna Ameera ta fito da gudu tana yi mishi sannu da zuwa baki har kunne.. Abba cike da farinciki yake amsawa yana tambayarta yaranta. Fateema ta shigo dasu tana "Abba ga takwaran Umma nan ita zaka fara d'auka". Suna had'a ido Fadeela ta callara ihu,yariyan da ko zama bata yi yau sai gata tana rarrafe tana Neman hanyan fita daga parlour. Tsoro,figici da mamaki ya hana kowa tab'a ta illa zuba mata ido da sukayi. Murmushi Abba yayi yana kallon Ameera da take hawaye yace..."mesa yaran nan basu da lafiya baki kawo min su ba?" Cike da rashin fahimta Umma tace" wani irin rashin lafiya kuma Mallam?" 🙆🙆🙆🙆🙆🙆 *UKUBAR KISHIYATA* 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman Yusuf) *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION~*💫💫💫 https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *_~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~_* *part forty four* "K'warai kuwa amma ba haka aka haife su ba ko?" Abba ya tambaya yana kallon Ameera da take kuka. Umma ce ta mishi bayanin yanda suke lokacin da aka haife su,nan Abba ya bukaci a shigo da Fadeel da yake bacci a waje. Fateema ce ta shigo da shi a hannu,aiko shima suna had'a ido da Abba ya fara ihu amma shi baiyi yunkunrin guduwa ba. Gyara zama Abba yace..."duk yanda akayi yaran nan da aljanu a jikinsu. Jin haka duk suka kid'ime musamman Ameera da tasa kuka da karfi. " Ku k'wantar da hankalinku zanyi musu ruquyya ba abinda yafi karfin ayar Allah". Cirko-cirko sukayi suna sauraron Abba. "Fateema ki shiga d'akina ki d'auko min ruwan zam-zam,man zaitun dana habba ki kawo min". Fateema har tuntub'e take saboda sauri, cikin lokaci sai gata ta dawo dasu a hannun. Abba cewa yayi duk su fita su bashi waje su jira zai fara. Mik'ewa sukayi suka fita dukansu suna ta waiwayen su. Suna fita Abba ya shafe su da man zaitun dana habba sannan ya fara karanto ayoyin alqur'ani mai tsarki da ake ruquyya dasu. Wanda yake jikin Fadeela shiya fara wani irin ihu da murya mai rikitarwa yana rokon Abba da yayi hak'uri ya barshi ba laifin shi bane boka ne ya turo su. Abba yace..." Akan wani dalili bokan ya turo ku kuke wahalar da jinjiraye?" " Hajiya Lateefa matar babansu ita tasa aka turo mu muyi ta azabtar dasu har zuwa shekara 1 sannan mu kashe su". Abba ya jinjina kai ya kara tambayan shi yace...."iya abinda aka saka ku kenan koda saura?" Murya a galabaice ya bawa Abba labarin irin tuggu da Lateefa ta shirya shekara da shekaru har zuwa yau,sannan ya roki Abba da ya yafe mishi karya kona shi zai fita kuma yayi alkawari ba zai sake zuwa ba. Atishawa Fadeela tayi ta jerawa har 3 sannan ta bingire da baccin wuya. Abba ganin Fadeela ta samu lafiya yasa ya maida hankalin shi gabaki 1 zuwa kan Fadeel daya zuba mishi ido ya mishi wani kallo kaman ya shake shi. Irin kallon da yake mishi yasa Abba sanin cewa wannan yana da taurin kai,dan haka ruwan zam-zam daya sha addu'oi ya d'auko yana watsa mishi a jiki yana cigaba da karatu. A tsawace yaji wacce take jikin Fadeel d'in tace..." Wai kai wani irin mutum ne mai nacin tsiya?gara ka rabu dani saboda ni duk nacinka sai dai kayi ka gama dan bazan fita ba sai na aiwatar da abinda aka sakani". Abba yace..."shikenan kada ki fita ni kuma zan kona ki da ayoyin Allah". Wani dariyan rainin hankali tayi irin na kayi kad'an d'in nan. Karatu Abba yake yana zuba mishi ruwn zam-zam d'in,tun tana ganin Abba yayi kad'an ya k'ona shi har ta fara k'onewan. Nan itama ta shiga magiyan Abba ya daina k'ona ta zata fita amma Abba yace shi bai yarda ba dan zata iya dawowa. Alkawari tayi mishi in ta tafi ta tafi har abada kenan sannan Abba ya tsagaita da karatun da yake. Atishawa masu karfi shima yayi ta jerawa sannan ya kama bacci kaman na 'yar uwar shi. "Alhamdulillah!!" Abba yake ta jerawa. D'aga murya yayi yace suna iya shigowa. Fuska shame-shame da hawaye suka shigo dama suna tsaye sun kasa zama suna jira. Umma ta d'auki tak'warta tana share hawayen fuskanta da gefen zaninta tace..." Wannan mata me zamuyi mata ne muji sauki a cikin ranmu?" " kul kar in kara jin haka daga bakin ki,mutum duk abinda zaiyi maka ka barshi da Allah dan baki ji sauran abubuwa da tayi bama". A hargitse Umma ta d'ago tana kallonshi tace..." Me kuma tayi bayan wannan?" Nan Abba ya maimaita mata abinda d'ayan ya fad'a. Kuma wiwi Umma take tana"Ashe wannan faram-faram da take mana na munafurcine? Oh mutum abin tsoro amma wannan mata Allah ya isa tsakanin mu da ita". Fateema ita ta fad'i abinda ta sani ciki harda dambe da sukayi Ameera ta hana ta fad'a. Umma ta jawota jikinta ta rungume tana rarrashinta tace..." Ki yafe mana Ameera duk laifin mu da bama ziyartan ki kuma muka hana kowa namu zuwa gudun kada mutane suce an zuba k'afa a gidanki dan k'wad'ayi ashe kanmu muka cuta da matar nan batayi nasaran wukanta min ke haka ba." Abba ya katse ta yace..."ya isa haka nan komai da kuke gani muk'addarine na ubangiji,in Allah ya hukunta faruwan abu to dole ne sai ya faru.yanzu abinda nake so ku tashi ke Ameera ku koma gidanki keda Fateema ku rusa kayan d'akin duk abinda kuka gani kada ku tab'a ku Kira ni awaya". "Toh " suka ce tare da mik'ewa nan Umma ma ta mik'e tace lalle tare zasu tafi kar wani abu ya samu 'yan matan ta. Abba yace ta zauna ba abinda zai faru tunda su aljanun da aka turo su dan aikin ma sun gudu toh komai ya k'are tayi hak'uri suje. Haka Umma ta hak'ura ta zauna ba dan taso ba,Ameera ta goyi Fadeel Fateema kuma ta goyi Fadeela suka fita. Har sun kusa bakin titi Ameera tace..." Dame zamu tafi dan ni ko naira banida shi". Fateema batayi magana ba ta juya ta koma gida can sai gata ta fito da d'ari 5 a hannunta suka karasa bakin titi tare da tsaida mai adaidaita suka shiga suka tafi. Pls kuyi manage da wannan. 🙆🙆🙆🙆🙆🙆 *UKUBAR KISHIYATA* 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman Yusuf) *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION~*💫💫💫 ❄~*we bearer's of golden writer's assiduously percieven No pain so Magical our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u no pain~* https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ *part forty five* A bakin gate mai a daidaita ya sauke su,Fateema ta bashi kud'i ya karb'a tare da maida mata change sannan suka nufi cikin gidan. Bala driver suna zaune da Baba mai gqdi suna hira suka shigo. Da sauri Bala ya mik'e ya tare su yana.." Haba Hajiya da kinyi waya naje na dawo dake,in Alhaji yaji ba zaiji dad'i ba". Murmushi kawai tayi tace mishi..."bakomai Bala". Cikin suka shiga ba kowa a main parlour hakan ya basu daman shigewa part d'in Ameerar ba tare da kowa ya gansu ba. A parlour Ameera suka k'wantar da Fadeel da Fadeela sannan suka wuce bedroom. Cikin abinda baifi 20 mins ba suka warware gadon. Mamaki da tsoro su suka daskar dasu waje d'aya ba wacce ta iya motsi cikinsu. Can Fateema tayi karfin hali tace..." Bani wayarki in kira Abba in fad'a mishi abinda muka gani" "Ba kud'i a wayan Fateema". " nima babu a nawa amma bari in fita in sayo yanzu ina zuwa" Fateema tans fad'an haka ta d'auki change da mai a daidaita ya basu ta fita. Bata jima ba kuwa ta dawo da recharge card na m.t.n. Ameera tana nan tsaye a inda ta barta bata matsa ba. K'iran Abba tayi bayan ta loda katin a wayarta. Wayar tana shiga Abba ya d'aga da sauri dama yana zaune shida Umma ya kasa fita ko bakin k'ofa suna jiran k'iran daga gare su. " Fateema kun samu me kuka gani?"Abba yake jerowa Fateema tambayar nan. "Eh Abba abubuwa da yawa muka ga..." "Kaman su me? Gaya min inaji" Abba ya katse ta. Nan ta shiga lissafo mishi abinda suka gani tace..." Akwai layu guraye sanda harda rigar Ameera dana mijinta da wasu k'ulle-k'ullen magani". Abba yace..."kada ku tab'a komai ku fara yin alwala sannan ku karanta suratul Iklas,Falaq,Nasi da Ayatul qursiyyu ku shafe jikinku dashi,kusa tsintsiya da abin k'washe shara ku k'washe da shi ku fitar waje". Kashe wayan Fateema tayi ta ajiye a gefe bayan ta amsa mishi. Parker da dustbin suka d'auko suka fara k'washewa kenan wayar Fateema ya fara ringing. Tsaida aiki sukayi Fateema ta amsa wayan taji muryan Abba yana cewa..." Ku kona duk abinda kuka fitar Fateema karku bar komai". "Insha Allah Abba " tace sannan suka cigaba aikinsu. Ta bayan gidan suka fita da kayan can arean su Rabi,wuta suka cinnawa dustbin d'in ba tare da sun juye surkullen a k'asa ba. Wuta ya kama yana ci bal-bal ga wani irin hayaki bak'i kirin na tashi wanda ya k'ara firgita su Fateema da suka koma gefe d'aya suna kallo. Wutan yana k'asa Ameera ta yanki jiki ta fad'i a wajan. A rud'e Fateema tayi wajan Rabi tana cewa tazo ta taimaka mata. Rabi tana tambayarta me ya faru amma Fateema bata tsaya bata amsa ba ta fita da gudu,ganin haka Rabi bata tsaya b'ata lokaci ba ta rufa mata baya. Salati Rabi ta fara har tana tafa hannu tare da tambayar meya same ta amma ba amsa. Haka suka ciccib'e ta sai cikin bedroom d'inta suka k'wantar da ita suna aikin fifita. Ruwan sanyi Rabi ta shafa mata a fuska. Ajiyar zuciya tayi ta bud'e ido a hankali tana binsu da kallo suna yi mata sannu. Tashi tayi ta zauna tana tambayar Fateema meya faru? "Bakomai just tiles ne ya k'washe ki kika fad'i" Fateema ta bata amsa tana b'oye hawayenta. Kukansu Fadeela suka ji a parlour Fateema ta tashi ta d'auko su ta shigo dasu. Ameera wasu abubuwa take ji kaman sun faru amma sai take gani kaman a mafarki ya faru. K'iran Abba ne ya kara shigowa wayar Fateema,parlour ta fita sannan ta d'aga yake tambayar ta ya sukayi. Abinda ya faru tun daga kan k'ona kayan tsafin harda fad'uwar Ameera duk ta bashi labari. Godiya ga Allah Abba ya fara yi na Allah ya bawa 'yar shi lafiya,nan yace mata ta kaiwa Ameera wayan zaiyi magana da ita. Komawa cikin d'akin tayi ta bata wayan tace Abba ne zaiyi magana da ita. Karb'a tayi taxa a kunne bayan tayi mishi sallama ya amsa ya shiga yi mata nasiha da fada akan rike addu'a da yin azkar saboda addu'a itace makamin mumini sai mutum yayi sake da azkar Sannan duk wani mugun abu zai iya shafar shi amma da mutum zai kiyaye kaman yanda manzon Allah (s.a.w) ya umarta toh bi izininllahi ya tsira sai sai wani ikon Allah. Ameera sai amsawa take da toh sabida ita tasan bata wasa da azkar bata san tunda tasha juice d'in da su Fa'iza suka bata ta daina duk wani Abu mai suna addu'a ba. Bayan sun gama waya da Abba ta dubi Fateema tace..." Fati Dan Allah ki gaya min me yake faruwa kaina ya kulle". Tiriyan-tiriyan Fateema ta maimaita mata iya abinda ta sani. Rungume twins d'inta tayi tana kuka sai yanzu take gani ashe abinda take gani kaman a mafarki da gaske ya faru da ita. Rabi ta dafa kafad'arta tace... " Hajiya yanzu ba lokacin kuka bane godiya ya kamata kiyiwa Allah da ya warware wannan kulle mai wuyar warwara". Bayan sun natsu suka had'a gadon yanda yake suna hira da 'yar uwarta tana jinta kaman wata sabuwar halitta. Kitchen ta fito tana cewa Fateema ta kula dasu Fadeel zata sama musu abinda zasu ci. Abinci mai sauki ta girka musu tayi musu pepper soup na kaza ta shirya a d'an madai-daicin tray ta d'auka zata fita Rabi ta shigo tana..."haba Hajiya ai da kinyi min magana zan girka muku duk abinda kuke so". Murmushi Ameera tayi tace..." Bakomai Rabi taimakon da kike min a baya ba abinda zance sai sai ince Allah ya saka mini da alkhairi". Tana gama fad'an haka ta d'auki trayn ta fita daga kitchen d'in Rabi ta rakata da murmushi. ****************** Al'ameen yana zaune a office aiki yasha mishi kai,Shu'aib sectaryn shi yana nuna mishi files yana signing. Wani matsanacin ciwon kai had'e da jiri yaji ya ziyarce shi lokaci d'aya har wani duhu-duhu yake gani. Dafe kan shi yayi da hannun dama har pen d'in hannun shi yana fad'uwa. Tambayar shi Shu'aib ya farayi ko lafiya,maimakon ya bashi amsa sai gani yayi ya yanki jiki ya zube a wajan. A rud'e ya fara k'walawa Massinger kira Wanda yayi sanadin Jan hankalin sauran mutane dake kusa da office d'in. Mota suka saka shi suka nufi hospital d'in Yayan shi. A hanyan su ta tafiya Shu'aib ya kira sauran 'yan uwan da iyayen shi ya sanar dasu halin da ake ciki. Innalillahi wa inna ilahi rajiun Alhaji yake ta maimaitawa yana sharce gumin da suka tsastsafo mishi a goshi. Hajiya ce ta fito daga kitchen hannunta rik'e da ludayin miya tace..." Alhaji lafiya kuwa,me yake faruwa?" "Al'ameen ne wai ya yanki jiki ya fad'i a office yanzu haka suna kan hanyan zuwa hospital dashi".Alhaji yace yana saka hula alamun fita zaiyi. Nan Hajiya ta bukaci ya jira ta su tafi, bai ki ba ya tsaya jiranta. Ita kuma ta kira Altine tace ta karasa mata aiki ta d'auki hijabi tabi bayan mijinta cike da tashin hankali. Su Shu'aib suna isa hospital suka Tatar da Ya Sa'ad da wasu doctors 3 suna jiran zuwan su. Nan da nan aka d'ora shi a wheel bed suka tura shi emergency. Basu dad'e da shiga ba iyayen shi suka karaso cikin tashin hankali. Ganin doctors basu fito ba,ba wanda zai basu gamshashiyat bayani dan haka waje suka samu suka zauna suna jiran fitowarsu. Sun kai good 1 hr a kanshi amma sun kasa gane me yake faruwa,gashi baya numfashi sai zuciyar shi da take bugawa kad'an-kad'an. Fitowa sukayi jiki a sanyaye. Wani doctor da ake kira da Abubakar shi yayi karfin halin yi musu bayanin abinda suka gani dan Ya Sa'ad kuka yake wiwi. " Alhaji kuyi hak'uri ba abinda Al'ameen yake bukata daga gare Ku kaman addu'a saboda a yanayin binciken da mukayi in numfashin shi bai dai-daita ba cikin 30 mins masu zuwa ba toh gaskiya ba abinda zamu iya yi sai hak'uri"yana fad'an haka shima ya wuce office d'in shi. Hajiya kuka take kaman ranta ya fita Alhaji yana bata baki duk da shima ta maza yake. Haka sauran yaransu suma sun taru ana rarrashin Hajiya. Da'kyar suka samu tayi shiru kowa ya nemi wake ya zauna da add'ua a bakinsu sunayi suna kallon agogo wanda ko wani mint da zai buga da zuciyarsu yake bugawa. Zaman forty mins sukayi suna add'ua amma shiru ba labari hakan yasa Alhaji yace su tashi su yafi dashi ayi mishi wanka akai shi gidan shi na gaskiya. Dole kowanne su ya daure zuciya tare da rungumar kaddara suka shiga d'akin da aka k'wantar dashi. Sun shigo suna kokarin d'aga shi su d'aura kan wheel bed Kaman daga sama suka ga yayi mik'a tare da salati a bakin shi ya bud'e ido. Nasan wasu sun kusan samun heart attack saboda sun dauka Al'ameen ya sheka😜😜😜 🙆🙆🙆🙆🙆🙆 *UKUBAR KISHIYATA* 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman Yusuf) https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *_~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~_* *part forty six* Da ido yake bin mutane da suke zagaye dashi suna mishi sannu. Mik'ewa yayi cikin hanzari ya zauna tare da tambayan meya faru,me suke yi a asibiti? Amsa mishi suke da bakomai ya k'wantar da hankalin shi,Ya Sa'ad yazo ya k'ara duba shi ya tabbatar musu komai normal yanzu. Tashi yayi yana cewa shi zai wuce gida dan a lokacin ba abinda yake bukata kaman ya saka Ameera a idon shi. Alhajin shi yace ba inda zaije sai dai driver ya kaishi. Dagewa yayi shi zai iya driving da kanshi saboda baya jin komai a jikin shi,nan Alhaji yace toh suje Shu'aib ya ajiye shi a gida dan ba zai yarda yaja mota da kanshi ba. A mota Al'ameen ya tsare sectaryn shi Shu'aib akan ya fad'a mishi meya faru dashi har aka kawo shi asibiti? Dolen shi ya bashi labarin abinda ya faru tun daga lokacin da ya yanki jiki ya fad'i har zuwa bayanin da doctors sukayi musu. Mamaki ya hana shi cewa komai haka Shu'aib ya sauke shi ya wuce office dan kimtsawa saboda a wargaje suka bar komai. Cike da nishad'i ya nufi cikin gidan yana jin shi kaman wani sabon halitta. Ameera suna main parlour ita Fateema harda Rabi suna hirar su hankali k'wance ga twins suna zaune a gefe da kayan wasan su . Rabi tana basu labarin wani yaro mara ji a kauyen su suna k'yalk'yalar dariya Al'ameen yayi sallama ya shigo. Dukkan su suka amsa mishi amma banda Ameera da ta tsura mishi ido ko kiftawa batayi. Shima idon ya zuba mata dukkan su ji suke kaman sun d'ebi shekaru basu ga juna ba. Rabi ta mik'e da sauri tare da kama hannun Fateema sukayi ciki suka basu waje. Karasowa yayi gabanta ya durkusa ba tare da sun d'auke idon su a cikin na juna ba. Kamo hannayen ta yayi ya sumbata yace..." Babyna ina kika shiga kika bar zuciyata cikin kuncin rashin ki? Kece farincikin rayuwata I can't live without u". Kasa magana tayi ta sunkuyar da kanta k'asa tana kuka mara sauti. Hannu yasa ya d'ago da fuskarta suna kallon juna,girgiza mata kai yake alamun baya son kukan da take.yasa hannu yana share mata hawaye. Fad'awa tayi jikin shi ta k'ank'ame shi tana kuka sosai. Shafa bayanta yake a hankali yana aikin rarrashi. Kaman daga sama suka ji muryan Lateefa ta danno wata muguwar ashar. A razane suka juyo suna kallonta ba tare da sun rabu ba. "Al'ameen me zan gani haka,kana cikin hankalin ka kuwa?meya had'a ka da wannan k'azamar karuwar da..." Lafiyayyar mari da taji a kuncinta shiya katse mata bala'in da take. A rud'e ta juyo tana kallon shi rike da kuncinta tace..." Al'ameen ni ka mara?" Ido a rine yana huci yace..."u re lucky marin ki kad'ai nayi a yau,but am warning u in kika k'ara attempting k'iran mata ta uwar 'ya'yana da mugayen suna makamancin wannan wallahi zan baki mamaki shasha kawai". Kasa gaskanta abinda yake faruwa tayi ta tsaya tana binsu da ido kaman wata doluwa,sai da ta d'auki some seconds sannan ta dawo hayyacinta. Hannayenta duka 2 ta d'aura a kai tare da fasa wani ihun da sauran mutanen gidan suka fito. " na shiga 3 na lalace ni Lateefa". Da gudu tayi kan Ameera tana..." Wallahi baki isa ba yau zan nuna miki kinyi kad'an kija dani". Ameera tana tsaye tana kallonta ko motsi batayi daga inda take ba har Lateefa ta kusan karasowa gabanta wanda takun da yake tsakanin su baifi 3 ta goce gefe Lateefa kuma ta taho da karfinta hakan yasa ta fad'a kan center table ta fasa goshi. Ko zugin da goshinta yake bata ji ta mik'e da gudu tayi kan Al'ameen taci k'walar shi tana... "Wallahi baka isa ba duk nafi karfinku wallahi karya ne..." Ameera ce tazo a zuciye ganin abinda take kuma Al'ameen yayi shiru yana kallonta ba tare da ya d'auki mataki ba. Finciko Lateefa tayi ta jefata kan kujera tana nuna ta da yatsa tace..."wani irin dabbanci kike mana a cikin gida haka?ki sani komai kika min zan d'auka amma ba zan tab'a zuba miki ido kina abinda kika dama akan mijina ba ". Mik'ewa tayi bakin nan nata bai mutu ba sai zage-zage da tsine-tsine take ta wuce part d'inta. Ameera kamo su Fadeel tayi tana rarashi saboda razana da suka yi. Al'ameen shima yazo joining yana tayata rarrashinsu. Lateefa tana shiga d'akinta sabon kuka ta saka tana..." Shiken nan asirina ya tonu komai ya lalace min". Wayarta ta d'auka ta nemi number Aina'u ,ringin 2 yayi ta d'aga tana..." Sarauniya a gida Al'ameen ya aka yine?" "Aina'u na shiga 3 duk asirin da mukayi duk sun warware yau ni Al'ameen ya mara a gaban tsinanniyar matarshi" tace cikin tashin hankali da matsacin kuka. Aina'u cikin tashin hankali tace..." Ya akayi haka ta faru ko dai kinyi kuskure wajan aiwatar da abinda boka ya saka ki?" "Ba tambayoyi nake nema ba Aina'u mafita nake nema". Lateefa ta amsa mata tana face hanci. Nan Aina'u tace mata mafita 1 ce shine su koma wajan boka. Babu musu Lateefa ta yarda kan gobe da safe zata same ta sai su wuce. Tana gama waya da Aina'u ta kira number Maman ta taji switch off,ta gwada nasu Fa'iza suma still a kashe. Haka ta k'wana a cikin part d'inta ita kad'ai dan koda wasa bata yi yunkurin fitowa ba kuma suma 'yan gidan babu wanda ya lek'a ta. Da washe gari da sassafe Lateefa ta tashi ta shirya tare da tattara 'yan kud'ad'e da suka rage mata ta fito dan tafiya wajan boka. A parlour ta had'u da Ameera tana shirya kan table ta d'ago suka had'a ido,harara ta Watso mata tare da cewa..." Kiyi abinda kike so in just 2 hrs dan kika bar wannan precious time d'in ya wuce it means a lot,dafatan kin gane"tana gama fad'an haka tasa kai ta fice daga gidan. Murmushi Ameera tayi tana girgiza kai a zuciyarta tana cewa ba abinda zan gani sai alkhairi saboda da Allah na dogara. ****************** Suna saka kai d'akin boka ya daka musu tsawa tare da dakatar dasu yace...." Ku tsaya daga nan kada Ku kuskura Ku shigo min cikin dan abinda kuka zo dashi ba mai yiwuwa bane saboda mutanen nan yanzu sunfi karfina gashi kinsa tsiburitu da manaru sunyi matukar fushi dani sakamakon k'ona musu 'yar auta da sukayi.Ku fita nace kamin kusa in huce a kan Ku". Lateefa dama tun jiya ranta yake a jagule kuma boka ya k'ara mata da nashi saboda ta gama imanin tana zuwa wajan shi zata samu solution amma ya kore ta,nan da nan taji zuciyarta ya mugun b'aci bata San lokacin da itama ta daka mishi tsawa ba tace... "Dallah dakata Mallam in ka kasane kawai kace mana ka kasa ba wai ka samu a gaba kana mana ihu kaman wasu 'ya'yanka ba kuma wallahi..." Bata samu daman k'arasa maganan ba sakamakon rufe mata baki da Aina'u tayi tana wuri-wuri da ido tace..." Lateefa bakida hankaline kike musu da boka,ko kin manta abinda na gaya mini a baya ne?" "Ke dallah sake min baki " tace tana ture hannun Aina'u a kan bakinta ta cigaba da magana..." Anyi mishi musun sai me?yayi duk abinda zaiyi in ya isa".tace tana huci. Aina'u zubewa tayi a kasa tana tuba a gaban boka . Wata mahaukaciyar dariya ya kece dashi yana nuna Aina'u yace..." Ke tashi kiyi tafiyarki,ke kuma kije zaki ga abinda zanyi da wanda ba zanyi ba" ya karasa yana zarowa Lateefa manyan idanun shi kaman na 'ya'yan boris. Tsaki Lateefa taja ta fice abinta ko d'ar bata ji a zuciyar ta ba. Suna shiga mota Aina'u tace..."gaskiya Lateefa kinyi kuskure ko ince kinyi ganganci but dont worry akwai wani shahararren boka da yafi wannan in kina so yanzu zan je wajan shi ya gama mana dasu dan shi ba abinda yake gagaran shi,shiyasa ake mishi lak'abi da boka gagara badau.amma yana da matsala 1 bata karban kudi kad'an kaman wannan bokan sai masu yawa". Ba tare da ta kalle ta ba Lateefa tace..." Har nawa yake karb'a?" "Millions of naira ake bashi" Aina'u ta bata amsa. Wani mugun kallo Lateefa ta watso mata tare da cewa..."wat millions of naira kika ce?amma daga ke har shi baku da hankali". "Da hankali na mana Besty ganin situation da kike ciki shi yasa nace muje wajan shi and am assuring u zai miki aikin da nan da wani lokaci kad'an ba mai yawa ba zaki maida abinda yafi wanda kika kashe,ko ya kika gani?" Aina'u tace haka tana kallon fuskan Lateefa. Ajiyar zuciya Lateefa tayi tace..." Na yarda dake Ainau,bud'e hand bag na ki d'auko min check book inyi miki singing duka abinda ya bukata just ki cire ki bashi". Da haka suka iso inda zata sauke Aina'u ta sauke ta da sharad'in kada ta koma gidan har sai ta k'ira ta sanar da ita aiki yayi k'yau. Direct hotel da take permanent room ta wuce akan a can zata zauna ta saurari k'iran Aina'u,dan baza ta iya jure ganin Ameera da 'ya'yanta cikin walwala ba. Salees ta k'ira a waya kan yazo suyi zaman su tare amma yace mata yana Dubai yaje saro musu kaya sai nan da sati maybe zai shigo. Haka ta cigaba da zama a hotel ita kad'ai ba abinda take sai shan wine sai bacci. A ranan da ta cika 3days ne da daddare har ta fara bacci ta fara jin motsi cikin baccin. A d'an tsorace ta bud'e idonta. Tsoron ta ne ya k'aru ganin d'akin duhu ya mamaye alhalin bata kashe wutane d'akin ba. Kamin tayi yunkurin yin wani abu taga haske a tsakiyan d'akin kaman an kunna candle. Boka ta gani yana mata dariya d'akin yana amsawa,hannayenta tasa ta toshe kunnuwanta da shi sakamakon Dodon kunnen ta da taji suna barazanan fashewa. Ganin shi tayi akan gadon da take tsirara da wata k'warya a hannun shi ga warin da yake fitowa daga cikin kwarayan shima yana yana barazanan sata amai. Hannu yasa ya ciro abin ya d'aura mata a kan cikinta tare da karanto wasu kalamai da shi kad'ai ya san ma'anar su. Tun da Ya fara Lateefa ta kasa motsa koda yatsanta balle tayi yunkurin guduwa. Saida ya shafe minti 2 yana yi sannan abinda ya d'aura mata a kan cikin ya b'ace bat. Abin yana b'acewa boka ma ya b'ace kuma wutan d'akin ya dawo, kuma sai a lokacin taji zata iya motsi. 🙆🙆🙆🙆🙆🙆 *UKUBAR KISHIYATA* 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman Yusuf) https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *_~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~_* *part forty seven* A razane ta tashi zaune tana dube-dube ko zata ga wani Abu amma bata ga kowa ba. Barin gadon tayi ta koma kan kujera ta takure cike da matukar tsoro. Kamin wayewar gari duk kamannin ta sun canza,baya ga haka ga cikinta inda boka ya d'aura mata abu ya zama gyambo yana fitar da wani irin ruwa mai warin gaske da ita kanta tana cutuwa da wsrin balle kuma ta kaiga mutum ya zauna kusa da ita. Gari yana wayewa ta k'ira Aina'u amma wayarta a kashe. Wuni tayi tana trying but amsa d'aya take samu shine is switch off. Ganin yamma ta karato yasa tsoro ya karu a zuciyarta tana ganin in ta sake k'wana a d'akin nan maybe abinda zai same ta sai yafi na jiya worst. Had'a 'yan kayanta tayi ta fito da niyan komawa gidanta. Tana fitowa reception,duk mutanen da suke wajan suka fara toshe hanci suna mata kallon kyama wasu har guduwa suke daga wajan. Sauri-sauri gudu-ggudu ta fice daga reception d'in ta fad'a motan ta. Direct gida ta nufa,ta shigo bugum- buzugum kaman wata mahaukaciya. Ameera ta gani k'wance a kan cinyar Al'ameen ta d'aura Fadeel kan cikinta,Al'ameen yana rik'e da Fadeela yana sai ta sauk'e Fadeel ta d'auki Fadeela da take kuka ita kuma tana bata so. Tsayawa tayi a bakin k'ofan parlour tana kallon yanda suka kaure da kokuwan wasa suna ta dariya. Lokaci d'aya suka ji wani irin wari mai kama da mushen jaki ya cika musu parlour. Lokaci d'aya suka toshe hanci tare da dubu-dube ko zasu ga me yake musu wari haka. Lateefa suka gani tsaye a bakin k'ofa fuska duk hawaye ga kamannin ta da yanayin ta duk sun canza. Ganin duk sun zuba mata ido yasa tayi hanyan part d'inta ba tare da tace musu komai ba,suma ba Wanda ya iya ce mata komai illa rakata da ido suka harta shige. Tafi 5 mins da wucewa sannan suka samu daman sake hancin su. Ameera turaren wuta ta saka a parlour harda room fresher sannan warin yayi dama-dama. Tsaki Al'ameen yaja yana cewa ..." Gaskiyan Hajiya da tace zata dawo da kanta ni ko shekara zata yi a gidan nasu ba zan tab'a binta ,ji yanda ta dawowa mutane kaman wata mahaukaciy".saboda Al'ameen duk a tunanun shi yaji tayi dan ya mare ta akan ta zagi Ameera. Ameera ta rasa bakin magana jin abinda Al'ameen yace,saboda tabbas tasan ba yaji tayi ba bisa la'akari da magananun da ta fad'a mata kafin ta fita. Allah ya musu tsari daga sharrinta tace a zuciyarta dan Al'ameen baisan komai game da zaman da suka yi a baya ba. Lateefa taci kuka a d'aki kaman ranta zai fita ta rasa tudun dafawa ga number Aina'u tayi ta gwadawa harta gaji. Alert da tagani ya shigo mata waya shiyasa ta tsayar da kukanta ba shiri ganin an k'washe mata kud'in da suke account d'inta dama 12.5 Millon ne a ciki. Tunawa tayi da Aina'u da kuma blank check da ta bata. Sumbatu ta fara tana zagaye d'akin ita kad'ai kamar wata zararriya,ya za'ayi Aina'u ta k'washe mata kud'i tas kuma ta kashe waya me take nufi da hakan? Kaman wacce ta tuna wani abu a zabure tayi wajan wani drower da take ajiye muhimman abubuwanta ciki harda documents na Al'ameen da ta k'washe a wajanshi. Tana bud'e drowern shima wayam tagani ba ko d'aya duk ya k'wshe kayan shi sai 'yan kud'ad'e a cikin. Ta baya-baya ta fara tafiya tana girgiza kai harta kai jikin bango. Zaman 'yan bori tayi a wajan ta rasa wani irin tunani zatayi dan hawayen ma kafewa suka yi. Lokaci d'aya komai na rayuwa ya tsaya mata Iowa ya juya mata baya ga wannan gyambon k'ara girma yake yana mata ciwon da ba zata ya misalta shi dana ciwon ajali. Wayarta ta d'auka ta k'ara gwada number Aina'un hoping zai ko shia but still a kashe. Number su Shamsiyya ta gwada suma a kashe dan haka sai ta k'ira na Mama bugu 2 ta d'auka tana..."Lateefa 'yar k'walisa ". Da ba sunan da take jin dad'in shi kaman shi amma yau wani bakin ciki taji ya rufe ta. Daurewa tayi tace..." Mama su Fa'iza sun zo gida wajanki?" "Yaushe rabona dasu,sun dad'e basu zo.basa gidan ne?" "Nima rabo na dasu yafi sati 2 bansan ina suka je ba" Lateefa ta amsa mata. Mama tace..." Kin san su da zuwa gidan k'awaye kila yanzu suna gidan wata k'awar su". Amsawa tayi da haka ne,suka yi sallama suka ajiye waya. Yini tayi a d'aki ko parlourn ta bata leka ba har zuwa dare. Karfe goma da rabi na dare tana kwance ta kasa bacci saboda azababben yunwa da yake k'wakularta tun tana daurewa har dauriyan nata ya kare taga ba zata iya jurewa ba. Cikin tsand'a ta fito dan nemawa cikinta wani abu, Allah ya bata sa'a babu kowa a main parlour bata tsaya b'ata lokaci ba ta fad'a kitchen. Warmers da akayi dinner dasu ta fara bubbud'ewa ko zata samu amma duk babu komai a ciki. Wata daban tagani a can kusa da sink tana bud'e shi taga guntun tuwon shinkafa ce da akaci aka rage ga pepper soup na kifi da akaci sauran shima aka zuba akai. Jiki na rawa ta jawo shi tare da zama dirshan akan tiles ta ciccire k'ayan ciki sannnan ta fara sambad'a loma hannu baka hannu k'warya. Cikin abinda baifi kiftawar ido ba harta cinye abincin tas . Bata tashi a wajan ba saida ta sid'e cooler tas kaman an wanke ta sannan ta hakura ta koma d'akinta ta kwanta da niyan gobe da sassafe zata tafi hospital taga doc ko zata samu maganin wannan bala'in da boka ya had'ata da shi. Da washe gari da sassfe ta saka kai ta fice daga gidan dan zuwa hospital ba tare da kowa ya ganta ba. Wani private hospital taje cikin sauki ta samu ganin doctor saboda warin jikinta duk inda taje bata hanya ake. Tana yi mishi bayanin matsalarta amma ji yake kaman ya fita ya bar mata office d'in. Daurewa yayi ya nuna mata gado da yake cikin office d'in yace ta hau ta k'wanta ya duba ciwon. Hand gloves ya saka tare da rufe hancin shi da abin rufe hanci sannan yaje kanta ya tsaya a k'yamace ya mata nuni da ta d'aga rigarta ya gani. Da gudu doctor ya fita a office d'in yana kwara amai kaman ranshi ya fita sakamakon ganin ciwon Lateefa da yayi. Da ido tabi shi zuciyarta na suya lalle boka ya gama cutarta yasa ta zama dodo a cikin mutane. A sanyaye ta tashi zaune tana gyara rigarta wasu securities 3 suka shigo suka tasa keyarta gaba har bakin motarta.. Shiga tayi ta tayar da motarta ta fita a asibitin ga hawaye sai tsere suke a idonta. Tunani take a zuciyarta na ta tafi wani asibitin ne kota ta fita abroad? Zuciyarta yafi amincewa da ta fita abroad d'in dan haka ta juya kan Motan ta tayi hanyan gida. Tana tafe tana zancen zuci,tana gwara da tayi dabara ta bawa Salees kud'inta yana juya mata su gashi yanzu sai ta karb'i abinta taje ayi mata maganin fitinan da boka ya had'ata dashi. Tsaki taja ganin yanda hold up yayi yawa yawanci 'yan zuwa aiki da makaranta sunfi yawa. Juyawar da zatayi kaman daga sama taga Aina'u cikin wata luxurious car sabo dal sai sheki take. Murza idonta tayi Dan tabbatar da gaskiya idonta yake nuna mata ko dai Aina'un da ta sani ne? Sauke glass na window motarta tayi tana k'wala mata amma bata jiba saboda ita glasses nata a rufe suke. Har tana shirin bud'e kofar mota ta fita taga taja motarta tayi gaba. Da sauri ta fad'a nata tabi bayanta. Tana bin bayanta taga Aina'u ta tsaya a wata lafiyyar gida madaidaici mai d'an karan k'yau. Tun kamin tayi horn mai gadi ya bud'e mata gate ta shiga ciki. Tana shiga ya mayar da gate ya rufe. Da gudu Lateefa ta fito a nata mota ko kashewa bata tsaya yi ba tabi bayan Aina'u ta shiga ta karamin k'ofa tana kwala mata kira. Juyowa kawai tayi tana kallonta fuska a had'e kaman an aiko mata da sakon mutuwa,ba tare da ta amsa ba har ta karaso kusa da ita tana haki da fara'a akan fuskarta. Hanci Aina'u ta toshe tana komawa baya tana mata kallon wulakanci da kyama tace..." Lafiya kike kwala min kira haka?" Hawaye ta fara tana..."Aina'u kin ga abinda boka ya min kin ga yanda ya maida ni na zama abin kyama a cikin mutane kowa ya ganni sai ya toshe hanci,kema kulum ina ta trying number ki bata shiga. Nayi ta jiran kiranki kaman yanda kikayi alkawari shiru sai daima alert d'in kwashe min kud'in account da kikayi gaba d'aya". Tunda ta fara magana take binta da kallon wulakanci harta karasa kana tace..." Maganan boka ke kika jawowa kanki dama na gargad'e ki tun farko ba'a mishi musu kikayi harda cacan baki,maganar kud'i kuma nice na kwashe su kuma banje wajan wani boka ba face rabona dana kwada dan bazan tashi a tutar babu ba,saboda haka fita ki bar min gida tun kafin ranking ya b'aci ko insa yanzu ayi min waje dake". Da gudu Lateefa tayi kanta tana..." Wallahi baki isa ba ni zaki yiwa haka?na rantse da Allah sai kin fito min da kud'i na". Hankad'ata Aina'u tayi sai gata ta zube a kasa kaman kayan wanki. "Isa isa!!" Aina'u ke kwalawa masu gadinta k'ira tun karfinta. Da gudu suka zo gabanta suka zube. Cike da masifa tace..."Ku fitar min da matan nan a gidana kuma wallahi in kuka k'ara barin irin wa'yan nan suna shiga min gida a bakin aikin Ku"tana gama fad'an haka tayi cikin gida abinta. Ciccib'ar Lateefa da take ta faman zage-zage da tsine-tsine harda fizge-fizge amma hakan baisa sun sarara mata ba saida suka fito da ita da karfin tsiya suka jefar tare da maida gate suka rufe. Ta dad'e zaune a bakin gate d'in gidan tana cigaba da masifa har tana bubbuga gate ba wanda ya kulata saima jama'a da suka fara taruwa suna mata kallon sabuwar mahaukaciya. Gajiya tayi da masifar ga zafin rana da ya ishe ta yasa taja tsuman jikinta ta shiga motarta ta bar anguwan. 🙆🙆🙆🙆🙆🙆 *UKUBAR KISHIYATA* 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman Yusuf) https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *_~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~_* *part forty eight* Kuka take kaman ranta ya fita wai yau ita Aina'u zata yiwa haka?duk abinda tayi mata a baya bata gani ba? Cak kukan nata ya tsaya kaman d'aukewar ruwan sama sakamakon abinda idonta ya gane mata. Fa'iza da Shamsiyya ta gani a bayan moton sojoji fuska duk a kumbure. Bata san lokacin da ta juya kan motan ta ba ta fara binsu a baya har zuwa jaji. Zata shiga wasu manyan sojoji masu kama da samudawa suka dakatar da ita. Rokonsu ta farayi kan suyi hak'uri su barta ta wuce kannenta ta gani an shiga dasu ciki. D'ayan yace.." wa'yan nan ne k'annenki?" Amsawa tayi tana k'ara kusanto su. Tsawa suka daka mata kan ta tsaya inda take. Duk baya sukayi suna toshe hanci tare dayi mata kallon k'yama. D'ayan cikin su yace... "Hey chidimma make u call oga and tell him". Wani k'aramin d'aki ya shiga ya d'auki waya irin lane line d'in nan yayi k'ira. Bayan sun gama magana ya fito yace..." Joseph escort her in". Mota ta shiga tace shima ya shigo su tafi. Kallon banza ya fara aika mata sannan yace..." Ban shirya mutuwa ba ji yanda kike wari kaman mushe in na shiga motarki suna na marigayi". Bata ce k'ala ba ta fara Jan motanta a hankali take bin bayan shi har zuwa wani area mai ban tsoro wajan tsit baka jin motsin komai sai wani k'aton soja mai manyan idanu gasu jawur dasu kaman barkono da suka gani a wajan da alamu shi yake tsoron wajan. Tambayar Joseph yayi daga ina? Nan Joseph yayi mishi bayanin komai. Ido ya tsura mata na wani lokaci sannan ya tambaya..." K'annin ka ne? "Eh dan Allah kuyi hak'uri ku sake su" tace tana mai zubda hawaye. Girgiza kai yayi yace..." Kasan menene sunyi kana cewa a sake su? " Da sauri ta girgiza kai dan gaba d'aya ta gama tsurewa ganin wasu d'ika-d'ikan sojoji sun zo wajan da manyan bindigogi a hannun su. "Those bloody bitches an kama su a gidan oga kuma a cikin bedroom na oga wit his wife suna yin iskanci,or I think u re among them abi?" Yace yana zaro mata manyan idanu shi. Jiki na karkarwa ta fara basu hak'uri tace..." Wallahi ban san suna aikata irin wannan mummunar d'abi'a ba dan Allah ku rufa min asiri ku bar ni in tafi". "Then get out before oga come and sees u here" yace mata cikin tsawa. Da gudu ta fad'a motarta ta fita daga barack d'in tana kukan bakin ciki na ba yanda zata yi ta fita dasu daga wannan bala'in,koda yake su suka jefa kansu a ciki. Toh ya akayi suna cikin irin mutanen nan amma bata tab'a sani ba . Sai yanzu idonta yake hasko mata yanda suke rayuwarsu su 2 kaman wasu masoya ta d'auka zallan shak'uwa ce ashe su abinda suke aikatawa kenan. Da haka ta k'araso gida cikin tashin hankali. Addu'a take Allah yasa ba kowa a parlour. Cikin sa'a kuwa babu kowa ta samu parlour sai t.v da yake ta aiki shi kad'ai. Ba b'ata lokaci ta fad'a part d'inta tare da murza key. Zama tayi dirshan a k'asa ta rushe da kukan nadama,wai yau su duniya ta juyawa baya haka? Daga ita har k'annenta suna cikin *UKUBAR* rayuwa. *UKUBAR* da suka jefa wasu a ciki yau gashi suna cikin wanda yafi karfin tunaninsu. Ga wacce suke wulakanwa a baya yau gata cikin k'wanciyar hankali. Dama haka duniya take?. Har karfe 2 tana zaune a wajan ta kasa tashi. Dama ba damuwa tayi da sallah ba,amma yau ganin azabar rayuwa yasa ta tashi tayi sallahn azahar. Komawa tayi ta zauna kuma a lokacin ne ta tuna ashe ba taci komai ba tun safe. Tunanin ya zatayi ta fita ta samu abinda zata ci take,can ta tuna ashe tana ajiye kayan tea a cikin d'aki. Jiki na rawa na nufi drower ta bud'e taga kayan tean suna nan harda su snacks. Bata damu da ta nemi ruwan zafi ba. Bathroom ta shiga ta taro ruwa a cup tazo ta had'a tea tasha da snacks ta koshi. Gado ta hau ta k'wanta tana tariyo tarihin rayuwarta. Ta dad'e a k'wance sannan ta tashi ta d'auki wayarta ta k'ira number Salees. Saida ya kusan tsinkewa ya d'aga yace..."yah ne Babyna?" "Ba lafiya Salees i na cikin wani yanayi na tashin hankali ga rashin lafiya ya sani gaba" tace muryanta na shaking alamun tana kuka. "Subhanallah!! Babyna meya faru,meke damunki?" Salees ya tambaya cikin tashin hankali. Saida ta face hanci sannan tace ..." Labari ne mai tsawo honey amma ina bukatan kud'ad'ena na wajanka saboda in samu daman fita abroad neman lafiya". Cike da tashin hankali yace.."abun har ya kai haka Baby na?kada ki damu gobe mu had'u a hotel sai in zo miki dasu ko?" Wani sanyi taji ya ratsa ta na jin ya rik'e mata alkawari tace..."nagode Salees daz y I love u". " I love u 2 my Lateefa".yace mata tare da katse wayan. Tana k'wance a part d'inta taji Al'ameen yazo yana knocking amma tayi biris dashi kaman bata jiba. Shima bai damu ba ya juya yayi kowan shi dama Ameera ce ta takura mishi lalle sai yazo ya duba lafiyarta duk da abinda Lateefa tayi mata bata rik'e ta a zuciya ba illa damuwa da tayi da ita. Gari na wayewa tayi sammakon ficewa daga gidan ta tafi hotel inda sukayi alkawari da Salees kan zai kawo mata kud'i. Anan tayi ordern kayan breakfast tayi ta zauna har zuwa 9am sannan tayi mishi waya. Shi kuma ya tabbatar mata da ba matsala yana nan zuwa. Zuwa thirty minutes sai gashi nan ya shigo jaye da wata katuwar trolly da wata madaidaiciyar jaka a kafada. Tana ganin shi ta mik'e cike da murna dan ta tare shi. Warin daya ji ya tare shi,shiya hana shi shigowa ya tsaya a bakin k'ofa yana yatsina fuska. Ganin haka yasa itama tayi turus ta tsaya ba tare da ta k'arasa wajan shi ba. "Kaga babban dalilin da yasa nake neman kud'in kenan Salees"ta fad'i haka tana duban shi tare da marairaicewa. Ta cigaba da cewa..." Banyi zaton kaima kana cikin masu guduna ba,saboda kai kad'aine hope d'ina Salees". "No don't say so Lateefa" ya fad'i haka yana k'arasowa ciki. Sannan ya cigaba..."kema kinsan bazan tab'a gudunki ba no matter how, saima in k'ara tausaya miki". Sauke jakunan da yazo dasu yayi tare da zuge zip d'insu duka. Dollars ne tab a cikin babban trollyn,sai k'aramar kuma dubu Dubu ne a ciki. D'ago kai yayi yana murmushi yace..."ga dukiyar ki nan na dawo miki dasu kaman yanda kika bani amana". Durkushewa tayi a wajan tana hawaye tace..."da za'a samu irinka a duniyan nan da duniya bata lalace haka ba dan rik'on amana yayi k'aranci a wannan zamanin .ban san da wani baki zan gode maka ba Salees sai dai ince Allah ya barmu tare.insha Allah in na sami lafiya na dawo zan baka sharen ka". Murmushi yayi yace..."don't worry Baby just buri na ki samu lafiya.let's go in kinsan nayi missing d'inki sosai". Cikin murmushi tayi ciki yana binta a baya ta hau gado ta k'wanta. "Oh gosh " yace yana dafa goshin shi sannan ya cigaba ..."na manta ban rufe kofa ba ,bari in rufe in dawo kuma nazo miki da surprise sai dai ina so ki rufe idonki har sai nace ki bud'e sannan ki bud'e kinji Babyna?" Cikin zumud'i ta saka tafin hannayenta ta rufe fuskanta. Tana ji ya fita zuwa parlour har ya rufe k'ofan ya dawo ya tarar har yanzu fuskarta a rufe yake. "Babyna bud'e idonki...." Yace cikin romantic voice. A hankali ta bud'e idonta tana murmushi. A zabure ta mik'e tana nuna su da yatsa bakinta yana motsi amma sauti yaki fitowa saboda kid'ima. Salees ya k'ara rugumo Aina'u suna mata dariya yace... " haba Babyna meye na kid'imewa haka?wannan shine first surprise saura na 2 kenan". Kukan kura tayi tayo Kansu da gudu. Tun kamin ta k'araso Salees yasa mata k'afa ta fad'i. Kamota sukayi suka fito parlour da ita Salees ya zaunar da ita akan kujera, Aina'u ta bud'e hand bag da tazo dashi ta fito da igiya ta bashi. Karb'a yayi tare da d'aure ta a jikin kujeran. Hannu yasa a aljihun wandon shi ya fito da gum ya manne mata baki dashi. Durkusawa yayi daidai fuskarta yana murmushi yace..."ni bawan ki ne da zaki ce kin bani ajiyar irin wannan kud'in kuma kice in dawo miki dasu?harda wai sai kin dawo zaki bani rabona?hmmmm gaskiya kin raina min wayo ke da baki kare amanan mijinki ba har kike zaton wani zai kare miki amana?kinyi kuskure babba Lateefa cos tunda muke dake ban taba sonki ba koda na second 1 ba.look at this"yace yana nuna mata kud'in da ido. Ya cigaba..."sune dalilin da yasa muke tare,na da kuma sabida Kore sha'awata nake tare dake.but I regret every second I spent with u"ya k'arasa yana huci. Dariya Aina'u ta sheke dashi harda rike ciki tace..."kasan me?wai ni ta bawa blank check akan in cire kud'i,dakikiya kawai saboda duk zaman da mukayi dake Lateefa ban tab'a sonki da alkhairi ba ,wajan boka da shawarwari da nake taimaka mini dasu Salees ne yake tilasta min inyi dan Mu cimma burin mu,but Lateefa i terribly hate u". Tayi kaki ta tofa mata a fuska. Rintse idonta tayi da karfi saboda wani rad'adi da take ji a k'asan zuciyarta da take ji kaman ya fashe. Meye zata iya yi musu balle taji sauki a ranta? Babu shine amsar da ta bawa kan ta sabida tasan sun gama cutarta a rayuwa kuma gata a d'aure. Saukar lafiyayyar mari taji shiya dawo da ita hayyacinta. Salees tagani yana nunata da yatsa yace...ni zaki rainawa hankali INA magana kina jina?" K'aramar jakan ya jawo gabanta yace..."ga rabonki sweetheart sai dai nake ganin kaman d'aukan zaizo miki da matsala,let me call wanda zai taya ki d'auka kin san bana son inga kina wahala". Wayar ta ya dauka ya fara scrolling yana neman Wanda zai kira. Yana zuwa kan sunan da yake nema ya kece da dariyar mugunta tare da nuna mata screen d'in wayar. Sunan da ta gani ne ya k'ara jefata cikin tashin hankali da ya d'ara na yanzu. Kai ta fara girgiza mishi hawayenta na k'ara k'aruwa. Shafa gefen fuskanta yayi yana murmushi yace..." Haba Babyna kar ki d'aga hankalinki just dakon kud'inki zai mini kin gane?" Tana gani ya danna k'iran number. Fizge-fizge ta fara ko zata iya kunce d'aurin da yayi mata amma ko motsin kirki ta kasa yi. 🙆🙆🙆🙆🙆🙆 *UKUBAR KISHIYATA* 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman Yusuf) https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *_~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~_* *part forty nine* Al'ameen yana rik'e da Ameera da take ta k'wara amai kaman ranta ya fita. Sannu yake ta jero mata kuma at d same time yana ta masifan shi..." Dama saida na hana ki zuwa d'akin nan amma kika nace ke sai kin kai mata breakfast, ita yarinya ce da sai an kai mata?gashi kin jawowa kanki aman dole.wannan warin jikinta dana d'akin nata zai iya kisa,kinyi sa'a da kika tsaya a amai". Ameera dai tana jinshi ba tace komai ba saboda aman yaci karfinta . Da k'yar ta samu ya tsaya ta kuskure bakinta tare da wanke fuskarta ta dawo kan kujera ta zauna tana maida numfashi. Shima zama yayi a kusa da ita yana yi mata sannu. Ringing d'in wayar shi da yaji yasa ya tashi zuwa kan center table inda ya ajiye wayoyin shi. Sunan Lateefa da ya gani yana yawo akan screen d'in wayan yasa yaji kamar kar yayi receiving saboda yanzu babu wanda ya tsana kaman ita ga sabon al'ada da ta samu na fita da shiga a duk lokacin da taga dama ba tare da izinin shi ba. Saida k'iran ya kusan tsinkewa sannan ya daure ya d'aga. Maimakon yaji muryarta sai yaji murya wani namiji yace.... "Alhaji Al'ameen mudassir mijin Lateefa ko?" Da k'yar ya bud'i baki ya amsa da..."eh nine meye ya kawo wayar mata ta hannunka?" Dariya ya kece dashi sai da yayi mai isar sa sannan yace....matarka ko matar mu?" Tsawa Al'ameen ya daka mishi wanda yaja hankalin Ameera gare shi yace..."bana son zancen banza waye ne kai?" Salees yace..." Easy man stop shouting yanzu zaka ce baka sanni ba?sau nawa kake zuwa ka same ni a gidanka koda yake raina maka hankali take tace maka no d'an uwanta ne,ga files da kake saka hannu ana kawo min.no need of explanation tunda kasan wannan wayar matar kace yanzu haka tana (prince hotel)room number 35 wannan d'akin matarka tana rik'e da shi fiye da 15years.u can come and see for urself saboda ka tabbatar da abinda na fad'a maka in kaki kuma kayi zamanka,maybe zakayi mamakin dalilin da yasa nake fad'a maka haka ko?ta gama yi min amfani shiyasa".yana gama fad'an abinda yayi niyya ya katse wayan yana kallon Lateefa fuskar shi d'auke da murmushi yace.... " mijinki yana nan zuwa ya d'auke ki,mu zamu tafi sai wata rana. Juyowa yayi wajan Aina'u yace mik'o min abin muyi mata suprice na 3. Wata sharb'eb'iyar wuk'a Aina'u ta ciro a cikin hand bag d'inta ta mik'awa salees. Karb'a yayi yana jujjuyawa daidai fuskan Lateefa wacce tuni tayi suman zaune dan hawayen ma bata san lokacin da suka kafe ba. Kan wuyanta ya d'ora yana dariya yace..."am sorry Babyna". Rude idonta tayi tana jiran mutuwarta . Hannunta na dama ya kama daidai wajan yatsunta 5 yace..."bazan kashe ki ba amma zan miki abinda zaki rinka tunawa dani always ". Sare hannun yaji wanda nan da nan hannun ya guntule ya fara tsalle a cikin parlour ga jini yana ta tarwatsuwa a parlour. Kafa yasa ya danne gutun hannun daya guntule har ran ya fita. Ya juya yana kallon Aina'u yace..." muje sweetheart". K'wasan duka tarkacen su sukayi gaba suka bar mata k'aramar jakan kud'in. Ita kuwa Lateefa tun daga nan bata san inda take ba sakaman yawan jini dake ta zuba a jikinta. Ameera ce durkushe a gaban mijinta tana kallon da ya rine yayi ja kamar gauta.. Hankalinta ne ya tashi saboda bata tab'a ganin shi cikin irin wannan yanayin ba. Cikin Sanyin murya ta fara tambayan shi meya faru? Ya dafe goshin shi da hannayen shi duka 2 yana kallon kasa. Ya d'ago yana kallonta,itama idonta taf da hawaye yace..."wani ne ya k'irani yake min maganan banza akan Lateefa har yake cewa in ban yarda ba inje in gani da idona". "Maganan banza?wani irin maganan ne haka?" Ameera ta tambaya da alamun tsoro akan fuskarta. Mik'ewa yayi zumbur ba tare da ya bata amsan tambayarta ba yasa kai ya fita da saurinsa. Da kallo ta bishi tana addu'an Allah yasa lafiya. Yana fitowa compound gidan Bala driver ya taso yana mishi magana ko kallan shi baiyi ba balle ya tanka. Mota ya shiga ya fige ta da karfin tsiya ya fita a gidan. Driving yake kaman zai tashi sama zuciyar shi kuwa a cunkushe take duk da yana shakkar abinda yaji a Waya amma wani bangare na zuciyar shi kuma ta yarda bisa la'akari da rashin kulawa da yake samu daga gare ta. Cikin lokaci k'ankani ya iso hotel d'in ya fito a motan bayan yayi parking a parking space na hotel d'in. Bugun zuciyar shi sai k'aruwa take a lokacin da yake duba numbers na d'akunan har ya kawo room number 35. Cak ya tsaya yana fargaban bud'ewa dan bai San abinda idon shi zai gane mishi ba. Haka ya daure ya kai hannu kan murfin k'ofan ya murd'a ya jiya a bud'e. Turawa yayi ya shiga ciki tare da dube-dube. Lateefa ya gani d'aure kan kujera cikin jini male-male bata cikin haiyacin ta. Da gudu ya k'arasa wajanta yana ambaton sunanta tare da girgiza ta amma bata san ma yanayi ba. Waya ya fito dashi ya k'ira Ya Sa'ad da shi,shi kuma yace ya fara k'iran police tukunna suna zuwa. yana nan tsaye cikin tashin hankali dan ya rasa dame zai fasaara wannan al'anari. Within 15 mins ambulance da police suka zo at d same time. Bayan 'yan geaje-gwaje da bincike da police suka yi aka saka ta a ambulance akayi Hospital da ita. Al'ameen shima motan shi ya fad'a ya bisu a baya. Suna isa asibitin aka wuce da ita emergency,doctors kusan su hud'u harda Ya Sa'ad suka taru a kanta wanda a dole suke aikin saboda warin da jikinta yake fitarwa. Mamanta ya k'ira ya sanar da ita abinda yake faruwa. Cikin rud'u da gigita tace gata nan zuwa. Iyayen shi ya k'ira suma ya sanar dasu,nan suka taya shi jimami tare da cewa suna zuwa . Haka yayi ta sanar da duk wanda ya dace ya sanar,bayan ya gama wayar doctors suka fito da nasaran cewa an samu dakatar da jinin kuma anyi sa'a blood group d'inta A ne dan haka har an k'ara mata zuwa nan da 1 hr zata iya farkawa. Godiya ya musu sannan yace zai je gida ya dawo. Ameera tana zaune ita kad'ai a parlour ta rafka tagumi da hannayenta duka 2 . Tana ganin shi ta mik'e da sauri ganin ya dawo kaman ba yanda ya fita ba. A tare suka zauna akan kujera 2 seater yace ..." Ki shirya muje hospital " "Hospital kuma meya faru waye ba lafiya?"Ameera ta katse shi da tambaya. " Lateefa ce"ya bata amsa a gajarce tare da bata labarin abinda ya gani . Salati ta rinka maimaitawa tare da mamakin waye yayi mata wannan aikin. A gurguje ta gama shiryawa harda twins d'inta cikin kaya masu k'yau suka nufi hospital gaba d'ayansu. A can suka tarar dasu Alhaji da sauran 'yan uwa duk sunyi jugum dasu . Bayan sun samu waje sun zauna Hajiyar shi take tambayar shi ya akayi hakan ta faru? Nan itama ya maimaita musu abinda ya gani.kowa ya rink'a tofa albarkacin bakin shi,sun d'an jima zaune suka hango Maman Lateefa wujiga-wujiga tana tahowa. Idonta ya riga da ya rufe dan haka bata ma lura dasu ba har zata wuce Al'ameen yayi mata magana ta tsaya ta dawo wajansu . Hajiyar Al'ameen ta sauke Fadeela dake kan cinyarta ta kamo hannunta suka zauna tare da tambsyar ya jikin'yarta? Hajiya tace..."gamu nan dai muna jiran farfad'owarta dan sunce nan da awa 1 zata farka amma gashi har awa 2 ta wuce". Kuka tasa tana..."dan Allah ku gaya min ko ta mutu ne?" Hajiya ta bud'i baki da niyan bata amsa wata nurse tazo tana tambayar INA Al'ameen da Ameera? A tare suka mi'ke suna kallonta. "Ta farka kuma tace tana son ganin ku" Gaba d'ayan su suka d'uru cikin d'akin. A take sauran suka koma baya suna toshe hanci sakamakon warin da suka ji ya tare su. Kuka take kaman ranta ya fita tana duban su d'aya bayan d'aya . Cikin kuka tace..."Al'ameen,Ameera ku yafe min nasan alhakin kune yake bibiyata na cuci kaina na cutar daku a bata ta fanni da yawa". Nan ta fara zaiyane musu abubuwan da ta shuka tun kamin auren ta da Al'ameen har zuwa yanda Al'ameen yazo ya same ta a hotel. Tunda ta fara jawabin Al'ameen yake ji kaman ba shi ba kuma sai a lokacin ya fara tuno abubuwan da suka faru wanda da yake ganin kaman a mafarki ya faru ashe da gaske ne. Wani irin tsanan ta ya rinka ji wanda baya tsammanin akwai wani halitta da ya tab'a tsanan abu kaman yanda ya tsani Lateefa ba a yanzu. Rokonsu ta farayi tana magiya harda hawaye kan su yafe mata wanda Al'ameen yake ji kaman ruwan dalma take zuba mishi. A zuciye Al'ameen yayi kanta ya shake mata wuya yanda ko numfashi bata iya shak'a nan da nan idonta suka firfito waje tare da firfitowa. 🙆🙆🙆🙆🙆🙆 *UKUBAR KISHIYATA* 😭😭😭😭😭😭 (Its all about love and betrayal) Story by *~UMMEE YUSUF~* (Maman Yusuf) https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ *~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~* *_~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~_* *part fiffty* *last page* Da gudu yayun shi sukayi kanshi suna kokarin b'anbare hannun shi daga wuyanta amma suka kasa. Alhaji ne yazo ya k'washe shi da mari tare da hankad'a shi gefe. Bango ya nausa da duka karfin shi na haushin bai samu nasaran halakata ba inama ace Alhaji baya wajan da sai ya raba ta da duniyan inyaso duk abinda zai faru ya faru. Lateefa sai tari take Mamarta tana rik'e da ita gaba d'aya ta fita haiyyacinta. Ameera tana gefe sarkin tausayi sai sharar hawaye take tace...Anty kiyi shiru ni kam na yafe m....". Tsawan da Al'ameen ya daka mata yasa ta katse maganarta tana kallon shi a tsoro ce saboda a iya zamansu hakan bai tab'a faruwa ba. "Baki da hankali ne?kina jin abinda tace ta aikata miki harda yaran mu da bakinta amma ki wani ce zaki yafe mata?" Ya k'arasa maganan cike da takaici yana huci. Ta bud'i baki da niyar magana kenan police duka shigoda hakan kud'in da Sslees ya bar mata. Gaishe da mutanen d'akin sukayi sannan d.p.o ya fara bayani kan cewa basu samu evidence d'in komai ba,da alama mutanen sunyi da gloves amma dai zasu cigaba da bincike har sai sun gano wanda yayi wannan d'anyen aikin. Juyowa Al'ameen yayi wanda tunda suka shigo ya juya musu baya yace..."kaga d.p.kuyi tafiyarku ba sai kun wahala ba na yafe binciken Ku bar shi kawai". "Amma yallabai aiko kace mu bari ba zaiyu ba saboda dole hukuma ta nemo mai laifi a duk inda yake a hukunta shi and ga kud'in da muka samu a d'akin" ya k'arasa gaban Al'ameen ya ajiye jakan. "Ku d'auka bana bukata " yace Yana juya musu baya. Matsowa d.o.p yayi yana..." A gaskiya yallabai ba zamu iya d'auka ba saboda...." A harzuke ya juyo yace...." Nace ku d'auka in bakwa so ku jefar a hanya is not my problem but pls leave me alone ". Alhaji ne yasa baki yace su tafi kawai tunda yace baya so. D.p.o yace..." Shikenan Alhaji mun gode zamu tafi mu cigaba da bincike".nan suka juya suka fice,constable sai murna suke kaman suyi tsalle ganin makud'an kud'in nan ance ya zama nasu. Suna fita Al'ameen ya dawo da duban shi kan Lateefa da ta gama shan jinin jikinta yace..." Kina wani cewa kin cuce mu toh ki sani bamu kika cuta ba face kanki kuma ba wajan Mu zaki nemi gafara ba sai wajan mahaliccinki Dan shi sab'awa ba wani ba,anan kuma a gaban kowa zan fad'a in Al'ameen na saki Lateefa saki 3...." "Kai!!! Haka da hankali ne" Alhaji ya katse shi a tsawace. Hajiya ce tayi saurin cewa..."haba ya zaka hana shi?wannan shine dai-dai da ita sai taje can ta samu irinta ta aura ba dai d'ana ba wallahi kuma tsakanin Mu dake Allah ya isa macuciya kawai". Tana gama fad'anta ta fice a zuciye,alokacin ita da Alhaji ne kawai suka saura Dan Al'ameen da yayun shi sun dad'e da barin d'akin. Alhaji ma fita yayi ba tare da yace komai ba saboda shima hukuncin yayi mishi dai-dai ya dai yi magana ne kawai a matsayin shi na babba a wajan. Mama kanta a k'asa tayi shiru ba tace komai ba har suka gama ficewa a d'akin suka bata daga ita sai 'yar ta. Ita kanta abin ya bata mamaki da takaici dan duo shekarun nan bata tab'a sanin wannan mummunan halin 'yarta ba,ta d'auka tunda tayi aure ta watsar da komai a titi ashe abin ba haka yake ba. Jiki a mace Mama tace..."ina su Fa'iza ban gansu ko basu san abinda ya faru dake ba?" Murmushin takaici tayi sannan ta bawa Mama labarin abinda ya faru dasu. Kuka Mama take sosai irin kukan nadama nan. Lateefa tana kallonta tace..."lokacin kuka ya wuce Mama tunda kece sila na duk wani rayuwa da muka tsinci kan mu a ciki,run farko me kika lalata mana rayuwa Dan muddin zamu kawo miki kud'i ba ruwanki komai ma muyi gashi yau wa gari ya wayewa? 'Yan Mayan ki 2 sun halaka ni da nake rayen ma gwara mutuwata kan rayuwar da zanyi a gaba". Mama kass cewa komai tayi sai kuka da take rizga saboda ita tasanmaganar da Lateefa ta fad'a gaskiya ce da hannunta ta watsar da yaran ta gashi yau duniya da rayuwar sun juya musu baya. ****************** Driving yake cike da nishad'i sun taso daga night club ya d'an kalli inda take yace..." Swthrt yau jina nake wani fresh dani". Dariya tayi tare da k'wantar da kan ta akan kafad'an shi tace..." Nima haka nake ji my love yanzu said Mu bud'e sabon rayuwa da zunzurutun kud'i naira million 150". Dariyan mugunta ya k'washe da ita yace..."kuma a banza muka same ta ba?" Hirar su suke sosai cikin jin dad'e har suka zo gidan su. Masu gadi har 2 sukayi rige-rigen bud'e musu gate suka wuce ciki. Wanka suka fara yi sannan Aina'u ta jera musu abinci akan table. Bayan tayi serving d'in shi yace..." Me ba zaki ci ba?" Girgiza kai tayi tace..." Zuciyar ta tashi take ba zata iya cin abinci ba ruwan Lipton zata sha tasa ruwa a kettle. Salees ya fara cin abinci suna hira yanda gobe zasu kai kud'ad'en su bank. Aina'u tace..." My love dole Mu raba k'afa in ba haka ba akwai matsala. D'an dariya Salees yayi sannan ya d'auki ruwan dake gaban shi ya shanye tare da ture gutun abincin da yake gaban shi ya dube ta yace..." Me meye tabbacinki na zan sure ki da har kikayi saurin amincewa haka?Ku mata k'wak'walwan Kifi ne daku,ita da taci amanar mijikin ta ta fifitani akanshi bai hana ni ci mata mutunci da wulakanta ta ba sai ke?kema kin San banida mutunci ko kad'an more especially akan money" Murmushi Aina'u tayi tana kallon shi ko d'ar babu azuciyar ta tace..." Na sani ba sai ka tuna min ba kai kare ne mara mutuncti how can I trust u? But tunda kaci abincin nan plan na ya taxi dai-dai saboda ko 10mins ba zakayi a raye ba balle evil plans d'inka suyi aiki a kaina" ta k'arasa tana yi mishi dariyan mugunta. Dariyan shima ya cigaba da taya ta dashi yace...." Wow!!! Kin birge ni sosai but u re too late ". Had'e rai yayi kaman ba shine yake dariya yanzu ba Pistol ya zaro daga aljihun wandon shi kamin Aina'u ta ankara ya d'auke goshin ta dashi. Nan Aina'u ta fad'i ko shurawa ba tayi ba. Tashi yayi yazo gaban trolleyn kud'in ya bud'e ya durkusa a gaban yana dariya yana shafa kud'in yana aiyana yanda plan d'in shi ya tafi kaman yanda ya tsara saboda yayi imanin Aina'u a yanda take matukar son shi ba zata iya Sa mishi wani abu a abinci ba. Tari ya fara yi babu kakkautawa jini ya fara fitowa daga baki da hancin shi. Nan ya fad'i yana shure-shure mutuwa ko minti 2bayi ba ya sandare a wajan . Parlour ne ya fara tururin hayaki ,ruwan zafin da Aina'u ta saka a kettle ya kone adalilin haka wuta ya kama gadan.-gadan. Kamin masu gadi su ankara had wutan yaci karfin gidan. Fire fighters sunyi nasaran kasbe wutan amma Aina'u da Salees sun zama toka. Lateefa da Mamar ta sun koma zariya sakamakon Koran kre da akayi musu daga asbitin Ya Sa'ad. Lateefa taga rayuwa kasancewar ta zama mai larura ga rashin hannu ga gyabonta da kullum k'ara gaba yake dan haka a waje tske k'wana Mama taki yarda su k'wana d'aki 1a Cesar ta zata iya mutuwa in suka zauna wake 1. Ko tana nema taimako ba mai taimaka mata duk sanyi da iska hard a damina akan ta suke k'arewa,in mutum ya ganta sai ya rantse da Allah ba Lateefa bace 'yar k'walisa tayi kuka har ta saddakar. Yanzu sosai abin nata yayi gaba saboda har kayan cikinta ya tab'a bata iya ci balle sha. Tana jefe a cikin gidan sauro ba mai kula ta had tsutsosi saida suka fara cinyeta. Kwana 2Mama bata ji motsinta ba tazo ta duba ta taga ashe rai yayi halin shi da dad'ewa dan harta fara kumburi.sakamakon in da gyambon ta yake fitarwa shiyasa basu lura da mutuwar ta balle suji warin gawa. Allahu Akbar!!! Shiyasa ake so mutum ya shuka khairi in kayi akasinta kuma tun a duniya zaka fara gani kamin muje kiyama.duk abunda mutum zaiyi ya tuna akwai Allah yana ganin mu kuma mu kuma mutuwa dole zata riske Mu ko kana so kp baka so.Dan haka Mu koyi rungumar kaddara a rayuwa mai dad'i ko akasinta Mu kai zuciya nesa.*ALLAH KA SHIRYA MANA ZUKATAN MU AMEEN. Al'ameen sabuwar rayuwa mai tsabta suke shida Ameerar shi da k'yawawan twins d'in su hankali k'wance. Duk Wanda ya gan shi zai San ya canza daga Al'ameen d'in baya. Iyayen shi sunfi kowa farinciki saboda kullum said yaje ya gaishe su ga 'yan uwan shisuna zumunci sosai bakaman da sai sunyi kusan shekara basu ganshi a gidajen su ba. Katafaren Gida Nagani na fad'a ya ginawa iyayen Ameera suka koma, aciki akayi auren Fateema,ta samu miji na gari a can garin gombe ba laifi shima yana da rufin asiri rayuwar suke gwanin sha'awa. Matan Yayun Al'ameen su duka 3 suka kawo musu ziyara da yaransu suka wuni har dare mazajen su suka zo d'aukansu . Nan ma suka dasa Sabon hira sannan suka raka su har bakin mota,basu bar wajan ba har saida suka ga tafiyarsu. Shigowa parlour sukayi tare da twins d'insu da suka k'ara girma da wayo nan suka zube kan kujera Ameera tace..."wash na gaji". Hararan wasa ya aika mata yana..."gaya min aikin da kikayi harna gajiya"? Cike da shagwab'a tace" haba Yayana ai wayan nan ma sun isa su gajiyar da mutum" ta k'arasa rana nuna twins da hannu. "Kuma fa hakane amma kin san me? Ya kamata ace suna dak'ani". Yace yana d'aga mata gira 1. " kani!!! Haba wallahi saina huta". "Wani Hutu kuma yara sun kai 3 years?" Yace yana tsare ta da ido. Cunno baki tayi ta juya mishi bata tana..." Ni kam ban shirya ba". Dariya yayi yana.." zaki ga shiryawa yarinya". K'iran twins yayi yace suje wajan Rabi ta basu ice cream su sha. Da gudu sukayipart d'in masu aiki suna tsallen murna. Tana ganin haka tasan nufin shi dan haka da gudu ta tashi tayi hanyan part d'inta tana dariya Shima mara mata bata yayi yana dariya yana "baki isa ba yarinya" kamin ta kai har ya kamo ta ya daga ta sama yana juyi da da ita suna dariya. *tammat bi hamdullilah* Alhamdulillah INA mika godiya ga rabbi da ya nuna min karshen novel d'ina lafiya kaman yanda na fara shi lafiya. Ina godiya gare Ku my fans na yanda kuka rinka bibiyar novel nan tun daga farko har karshen ta.INA mai Baku hakuri akan masu msg both fb and watsapp in kuka ga banyi reply ba toh abinne yafi karfina amma ina son Ku Sani INA kaunar Ku sosai fiye da tunanin saboda in babu Ku babu ni luv u all. My special thanks goes to big brother *UMAR DALHA* Godiya da jinjina zuwa ga *SIS NABEELERT* golden pen tana matukar alfahari daku without u guys things seems to b difficult.. Ban manta daku ba yan *GOLDEN PEN* kun amsa sunan Ku golden saboda yanda kuke haskawa a ko INA kun fita daban Allah ya kara baseera da karfin ido. At d end INA rokon Allah daya nuna mana azumi lafiya tare da wadata Ameeen.