"[10/1, 9:36 PM] Nanameera: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 1 Nimcyluv Bright pens. second batch *Marubuciyar. ❤🔥* *Mijin malama* *Munafukin miji* *Moon* *Idan ba ke* ..... E.t.c and now *MUTALLAB* "* for some reasons. Akwai copywrite kar a haɗa mini ducoment, banda YouTube a bar mini kayana" haƙƙina ne* "Jami'an tsaro ne ta ko'ina cikin kayan kaki ma bambanta, duk da cewa yammacin ranar lahadi ne a watan" Fabrairu bai hana ta gane fuskarsa ba. Cikin tashin hankali jikinta na rawa da kyarma ta nufe shi tare da "ƙoƙarin cakomo wuyan babbar rigarsa tana furta cewa ""Shi ne, wallahi shi ne, daman na ce zan gano shi""" a gigice mutumin dake ƙoƙarin shiga motarsa da aka buɗe masa ya yi baya yana mai ƙarewa matar kallo sosai sai dai ya kasa gano ko wace ita? Daga ina me kuma take buƙata. """Wace ita?"" Ya furta yana tambayar zuciyarsa tare da kallon gefe. ""Wallahi shi ne, mugu azzalumi sai ka" "yi kuka, ka wulaƙanta "" Jin furucinta ya saka ƴan'jarida dawowa kan ta, suka fara tambayar ""Kin san" "shine? Mene haɗinki da shi?"" Kafin ta yi magana wani ya ce ""Arrest her, ku kamata""" "A hankali ya jingina da jikin motar can ya numfasa yana kallon yaronsa ya ce ""Wace ce? Na santa ne? To" "me ya sa take abu kamar ta sanni?""" """Sir da gaske ta sanka bana jin ko mutuwa ta yi ta dawo zata manta fuskarka, kuma zamanta a raye yana" "nufin abubuwan da yawa dole a yi wa tufkar hanci, kar a bari ƴan'jarida su samu ganawa da ita, even your securites, wannan matsalar kai da kai ce kuma zata shafi kimarka"" cike da mamaki ya yi ta kallon yaron nasa na tsayin sacanni da ƙyar ya cije leɓe ya ce ""To ina na santa? Me ya sa zata zama" "damuwata?""" """Sir ita ce wacce ka saka aka kawo maka ita, wacce ka yi wa fyaɗe a lokacin ,""" """Ya isa!"" Ya ce yana jin jiri na neman ɗauke shi, ya dubi tarin jama'ar da suke wajan can ya yi murmushi" "yana ɗauke fuska sai kuma ya ƙurawa yaron idanu ya juya ya kalli matar ya gyatsine fuska ya ce ""kuma ta" "kasance a raye ya haka? To a yi hanzarin toshe wannan ɓarnar ya zama kamar ba a yi ba""" """Amma me ya kamata a yi mata?""" """A yi mata allurar hauka, wacce ake yi duk shekara da wata wata kana a kaita gidan yari, life in prison har" "ta mutu. Bayan haukan zata mance komai, su ƴanƴan talakawa wama ya damu da su mutu ko su yi rai bata da wani mai tsaya mata kai mutuwa ma za ta yi"" yana faɗin hakan ya shige mota. Tana takure a jikin ƙofar ɗakin da aka ajjiyeta idanunta ƙur a kan photonsa zuciyarta sai zafi take mata wani abu ya tsaya mata. Da sauri ta juya jin an buɗe ƙofa wani mutum ne sanye da farar riga ya rufe fuskarsa hannunsa riƙe da ƙaton sirinji iya ruwan allurar da ya yi ja abin tsoro ne, ta fara ja da baya amma a haka ya fincikota tare da yin cilli da ita,ta faɗi saman carpet bai tsaya jiran komai ba ya caka mata allurar a ƙashin" bayanta wajan spinal cord ihu ta fara da birgima idanunta ya shiga ƙaƙƙafewa jikinta na sandarewa ta dinga buga kanta da jikin bango tana buge-buge a hankali jini ya fara fitowa ta cikin hanci da bakinta tabbacin allurar ta amshe ta za kuma ta yi aikin da ake buƙata a jiki da ƙwaƙwalwarta. ****** Cikin sauri suke tafiya a wani ɗan dogon lungu mai duhun gaske tsarin wajan gabaɗaya a ƙuntacce yake kamar zunubin gidan yari. Magana suke ƙasa-ƙasa ɗaya daga cikin su kuma yana duba agogon dake hannunsa tare da duba cikar lokacin fuskarsa a haɗe take sosai. Sai da suka kawo ƙarshen ginin suka tsaya ya ɗaga kai a hankali ya dubi saman da kansa ke taɓowa ya ɗan rusuna sai kuma ya dubi jami'in "tsaron dake wajan ya yi masa nuni daya buɗe ƙofar. ""Yes sir!""" Bayan ya sara ya ƙame ya buɗe ƙaton kwaɗon yana toshe hanci saboda wari da zarnin wajan. SP Gali ya kalli team ɗin nasa cikin bada umarni ya ce """Ku jira nan, idan akwai damuwa zan muku alama na san dai he can't do anything, ba zai iya komai ba""" "gabaɗaya suka jinjina masa kai tare da zagaye ƙofar fuskar kowannen su manne da baƙin gilas. A hankali Sp Gali ya tura ƙofar ya shiga yana durƙosawa saboda rashin girman wajan. Tunda kafin su ƙarasu wajan ya san da zuwan nasu har aka buɗe ƙofar tare da shigowa, yana durƙushe inda yake ya kifa kansa a ƙasa hannunsa dunƙule ya damƙe abu wanda tun kafin a kawo shi gidan abu yake a hannunsa, yin duniya yaƙi" buɗe abun balle a san menene shi. """Hey you!"" Sp Gali ya ce yana saka ƙafa tare da buge ƙafarsa ganin yaƙi motsawa, tamkar gunki haka yaƙi" "motsi ya kuma ƙi ɗago kansa Sp Gali ya shiga kallon wajan ya rasa wanne irin hali ne da wannan yaron mai baƙar zuciya da taurin kai ya sauke numfashi cikin kwantar da murya ya ce ""Ni idan na ce maka ina da tausayi na yi maka ƙarya, amma ka saka zuciyata karaya kana bawa kanka wahala kana bawa jami'anmu wahala. Me zai hana ka sauƙaƙa mana wahalar nan ka faɗa mana gaskiyar abin da ya faru a wannan rana kuma a wannan daren? Me ya sa ka aika abin da ka aikata? Ka kashe matarka, ka kashe ta har lahira kuma kaƙi magana shekara uku kenan kana wajanmu ka rainawa hukuma hankali da kotu, kai baka da zuciya ne dame kake taƙama saboda kana da tsari a jikinka ƙarfe ba zai ratsa naman jikinka ba, muna da kalolin azaba nau'i-nau'i amma gaskiya muke buƙata, ka amsa cewa ka kashe matarka a zaman" "kotu na yau shikenan sai a yanke maka hukunci daidai da zaluncin da ka aikata""" "Har Sp Gali ya kammala maganarsa bai motsa ba, babu alamun zai ɗago kai balle ya tanka. Sp ya miƙa" hannu zuwa hannun mutumin dake dunƙule da abu zai amsa a firgice ya ɗago kansa yana buɗe dara- daran idanuwansa akan Sp Gali sai da zuciyarsa Sp ta motsa saboda wani mugun jaa da idanunsa ya yi. Fuska ɗaure ya yi wa Sp kallon warning har lokacin bai yi magana ba dukkan naman jikinsa rawa yake kamar zai kaiwa Sp damƙa fuskarsa baibaye da gashi kansa ma cunkus yake ba'a gane kamanninsa sosai saboda cikar gashi. "Sp ya duba lokaci sai kuma ya shafa kai ya ce ""SCORPIO"" nan ma ya sake ɗago kai da sauri ya zubawa Sp" "idanu ""Idan ka bari na gano cewa kai ne Scorpio """ "Ya cije baki yana miƙewa tsaye ya furta ""Zan addabi rayuwarka, gwara ka zauna a iya wanda ya kashe" "matarsa da dai ka kasance kai ne Scorpio. Mene asalin sunan naka?"" Ya tambaya yana juyawa kamar zai fita saukar gurnanin da ya ji ya saka ya yi saurin juyawa idanunsa ya sauka wanda ake zargi da kashe matar tasa yaga ya dafe kai da hannu bibbiyu yana jujjuyawa ya dinga haɗa kansa da bango cikin sauri Sp" Gali ya ce """Team"" a guje suka shigo hakan ya saka ɗan ƙaramin ɗakin cika fuskar Sp ba wasa ya ce ""Ku danne shi a" "karɓo abin hannunsa dole mu san mene babu mamaki zamu samu hujja a ciki"" yana cewa haka ya fita yana amsa kira. Ganin sunyo kansa ya yunƙura gabaɗaya ya fisu faɗin ƙirji da damtse amma suka rufar masa sanin cewa sarkin yawa ya fi sarkin ƙarfi ya saka shi damƙe hannunsa da kyau yana ɓoye abun da suka karɓa, kokawa suke da shi ya dinga haɗa su da bango ya kama hannun ɗayan ya karya bisa dole suka fice a wahale. Sp ya saka wasu manyan mutane fito da shi suka ɗaure shi da ankwa tare da sarƙa" tun daga ƙafa har zuwa kansa. A harabar Criminal Investigation department CID aka tsaya dashi domin tafiya zuwa kuto a rana ta "ƙarshe wanda ke nuna ko a sake shi, ko a kashe shi ko kuma ya tafi gidan ɗan'kande. Team guda ne masu matuƙar basira da ƙwarewa akan aikinsu team ɗin ya haɗa da wanda yake ɓangaren Legal section, Anti- human trafficking, Medical Staff, Legal services, NDLEA, FID Federal investigation department. Gabaɗaya idanunsu yana kansa kowanne yana karantar yanayinsa amma shi ko a jikinsa banda faratansa na hannu dana ƙafa da aka ciccire wajan gana masa azaba babu wani rauni a tattare da shi sai matsanancin baƙi da ya yi ya zama kamar mahaukaci saboda shekarun daya ɗauka a kulle daga kuto zuwa state cid zuwa Fid amma har tsayin shekarun bai buɗe baki ya yi magana da kowa ba, babu kuma wanda ya damu daya tsaya masa. Suna ta surutai ƙasa-ƙasa duk yana jinsu har sanda wani yake cewa ""Babu hanyar da za a" "tilasta shi ya yi magana ne? Muna buƙatar muryarsa""" "Sp Gali ya ce ""Ina zargin wani abu game da matarsa daya kashe""" """Wanne abu? A binciken da mukai a wajan iyayen yarinyar tun farko ita ta nuna tana son shi, shi da ita" "class mate ne kuma age mate, tun suna shekaru 15 a secondary school suke soyayya. Me ya sa ya zaɓi ya kashe ta? Sun ɗauki shekaru tare bai taɓa yunƙurin rabata da duniya ba sai ranar da aka ɗaura musu" "aure? This is complicated"" C.i.d Research ya jinjina kai ya ce" """Duk binciken da aka yi shine a ruwa, gwajin hannu, yatsun hannu da sahun tafin ƙafa da CCTV camera" "na kan titin unguwar da aka kai amaryar tasa duk bincika shine""" Shiru sukai suna tunanin gabaɗaya kansu ya ɗauki zafi. Yana da can inda yake ya ja idanunsa ya lumshe yana fesar da iska daga cikin hancin wacce hucinta ya sauka har saman fuskarsa “BESTIE” haka ya ji saukar muryarta a kunnensa kamar yanzu ne suke tare da ita. Ya sake lumshe idanunsa yana jin saukar dariyarta sosai ya tuna lokacin yana zaune shi kaɗai a cikin class ranar aka dawo hutun makaranta shi kaɗai ne zaune ciki yana sanye da farar riga sai wando blue black ya ɗora ƙafarsa ɗaya saman benci tare da yin baya. "A hankali ta shigo cikin class ɗin hannunta riƙe da lunchbox da textbook sai school bag data goya, hijab" ɗinta daidai da ƙirjinta ita ce ta fara shigowa da mamaki take kallonsa zuciyarta na bugawa ta je ga zauna "inda yake ta zuba masa idanu sai kuma ta ce ""Ka yi holiday assignment?""" "Ya buɗe manyan idanunsa bai ce komai ba ta sake ƙasa da murya ta ce ""Na san bama ka yi ba ka daina" "haɗe mini fuska, ka naso a yi ta faɗa da kai da teachers"" nan ma bai kula ta ba a hankali taci sautin da cikinsa yake yi sai ta jawo lunchbox ɗinta ta buɗe tare da tura masa gabansa ta ce ""Your breakfast, ka ci kafin a shigo na san baka karya ba"" sai a lokacin ya buɗe idanu ya juya gabaɗaya yana kallonta sosai ta yi" ƙasa da murya kamar zai yi faɗa sai kuma a hankali ya ce """Kuma ga mayunwaci ko?"" Ta yi murmushi ta ce ""Da ƙyar na jure ban biyoka gida ba, na yi kewar ka" "sosai bestie"" ya yi mata shiru sai kuma ya haɗe fuska sosai yana janyo abincin yaga dankali ne aka soya" da ƙwai ya yi ɗan tsaki ya ajjiye spoon ɗin ya damƙa ya kai bakinsa ta yi saurin kama hannunsa ta ce """Kai baka iya komai bane? Sai a yi maka dariya cin abinci da hannu"" ya ware idanu sai kuma ya murtuke" "fuska ya ture hannunta a hankali duk da muryarsa a kumbure take ya ce ""Ki daina kusanta kan ki dani, ni fa ba ɗan iska bane""" """Laaa Allah Ya baka haƙuri kai duk abin soyayya baka iya ba"" a taƙaice ya ce ""Ke kika santa"" ta ja baya" "tana ɗaga hannu ta ce ""Lalala to shikenan ni dai ƙaddararka ce, na faɗa a gida a yi mini aure, ka san me" "na ce?"" Ya girgiza mata kai kawai yana sake damƙo dankalin yana dannawa cikin bakinsa saboda yunwa" ko gani baya yi sosai ta buɗe gorar ruwa ta miƙa masa a hankali ta ce """Na ce su yi mini aure wallahi bana son karatun nan, na ji aure nake so kuma na faɗa musu kai nake so," "amma wai ban isa ba karatu ya zama dole kuma shekaruna sun yi kaɗan amma ai ma girma shekararmu 15 years fa, ko kai baka isa aure bane?"" Ya yi mata shiru sai ta fashe da kuka sosai ta ce ""I love you so much Bestie, don Allah ka aure ni zan zauna dakai a duk yadda kake ka taimakawa rayuwata"" ya zame hannunsa tas ta miƙa masa tissue ya goge ya ja baya yana lumshe idanunsa har yanzu students basu fara" "shigowa ba, ta ɗan yi gaba kamar za ta shige masa ya cikin tsawa ya ce ""Zan kwaɗe ki kuwa""" """But what if i told you i love bestie? You mean the world to me, wallahi aure nake so ba karatu ba"" ta" faɗa tana shassheƙar kuka sai a lokacin ya kalleta fuska babu walwala ya dubi yadda take kukan sosai ya ce """Ke, babanki ne ya mutu? Ko uwarki ce?"" Ta girgiza masa kai ya sake haɗe fuska yana rarraba idanu a" "cikin ajin kamar mai neman wani abu can ya ce ""To kece za ki mutu kenan?"" Ta girgiza kai sai kuma ta ce ""A'a""" """Kukan fa?""" """Na soyayyarka ne bestie taɓa ƙirjina ka ji wallahi ni ce ƙaddararka ba zaka gane hakan a yanzu ba, da ina" da ikon cire abin da nake ji a ƙirjina da na yi hakan ina jin dama na mutu na huta kuma idan ban aure ka "ba zuciyata zata iya bugawa""" """To gwara ta buga na huta da na ci, shekaruna 15 za ki lalata ni da batun aure, ke tashi ki ware daga nan" "ɗauki kwananki kar ki ƙara kawo mini abinci"" ta miƙe jiki a sanyaye zata bar wajan ya nuna mata" "lunchbox ɗin daya cinye komai ""Ko daɗi bai yi ba abincin""" "Sai a lokacin ta kyalkyale da dariya kamar ba ita ta yi kukan ba, dimples ɗinta na lomawa ta ajjiye masa" "500 ta yi waje tana cewa ""You're my darling jarumina, i love you Mai dawa da jeji"" ta faɗa tana sake yin dariya tare da yin waje......." Ya yi saurin dafe kansa jikinsa na rawa yana jin dariyar nata na yi masa amasa kuwwa a kunne kamar "yanzu ne take yi jikinsa ya ɗauki rawa sosai daidai lokacin aka tura shi cikin motar shiga babu biya, aka nufi kuto. Tun kafin a shigar da shi suka ci karo da wani saƙo daya basu mamaki ainun suka tsaya suna kallon juna sosai cike da tsoro da shakku musamman Sp Gali ya juya ya kalli wanda ake zargin a karo na" farko yaga ya yi wani irin murmushin kefen baki wanda ya bada sauti kamat na tsaki yana murza kai gefe. "Cikin sauri Sp Gali ya ce ""Amma wane ya yi hakan? Bayan ba a gama bincike an tabbatar da hakan ba," "mene matsayin ran yarinyar daya kashe ina matsayin iyayenta"" ""Sp Ghali ka yi abin da aka ce, kuto ta" "wanke shi daga zargin da ake yi masa ku sake shi ya tafi gida baku da ikon riƙe shi""" "Sp Gali ya girgiza kai cike da damuwa ya ce ""Sir kana nufin bashi ya kashe ta ba"" cikin tsawa ya ce ""Ko" "shine ya zaka yi? Ka yi abin da ya dace a matsayinka na jami'i Sp Ghali karka matsa"" jiki a matuƙar sanyaye Sp Ghali ya kunce shi tas ya ce ""Congratulations. Ka sani shari'a saɓanin hankali ce"" shi dai bai ce komai ba ya ciri biron gaban rigar Sp Gali ya fara yi masa rubutu a tafin hannunsa dam zuciyar Sp ta buga ganin ya rubuta kalmar SCORPIO kafin ya yi magana tuni ya juya ya fara tafiya cikin sauri duk da" rashin kuzarin da yake dashi yana jin inda iskar ƴanci ke ratsa jikinsa yana shaƙa tare da kaiwa hunhunsa. Kano/Birget Dambe suke yi a tsakiyar tsakar gidan mata wajan uku ne kowacce da ɗaurin ƙirji ga tukunyar abincin dake saman murhu. Banda sautin hayaniyarsu babu abin da ake ji hatta Malam dake waje da Almajirai yana jin yadda suke aibata juna da zagin juna hakan ya saka ya miƙe riƙe da bulala yana ajjiye allon hannunsu da yake rubutu ya yi cikin gidan. """Ke har kin isa ki ce za ki hana Mufeederh abinci a gidan nan? Wace ke?"" Cikin ɗagawa Inna Binta ta ce" """Ni Binta matar malam ki faɗa mini nawa Mufee ta bayar aka haɗa wajan yin abincin nan? Ke uban yaran nan bai bada kuɗin abinci ba, ba zai yiwuwa yara su haɗa kuɗi kuɗi a siyo dusar awara a yi dambun nan ki ce wai na zubawa Mufee ba ƴar banzar yarinyar da bata da kunya, kina kallo sauran ƴan'uwanta suka fita nemo kuɗi ita ta yi kwanciyarta tunda ƴar mai ce ai yanzu sai ta ci hantar ubanta Malam gashi can" "yana zaman banza ba fuss""" "Mama dake ƙoƙarin ganin ta wafcin dambun a kwano ta ce ""Daɗin abin dai ba yaranki kawai suka haɗa" "kuɗin ba, hadda Saudat ko Zaituna?""" """A'a ba ruwan Zaituna tun jiya nake ganin hazo-hazo a idanuna cikina banda salati ba abin da yake," "Saudat da ciwon ciki ta kwana Olser ta buge ta saboda yunwa ki yi ta kan ki kawai wannan rayuwa Allah dai ya fisshe mu, amma yunwa za ta yi ajalin rabin jama'a a wannan zamanin"" Mama Zaituna ta faɗa tana turo kwanan Saudat da nufin a zuba mata ta ɗan tsakura a ciki ta yafa a nata cikin. Inna Binta ta shammafe ce ta yi sama da tukunyar kasancewar ta sharifiya ta ce ""Wallahi sai Mufee ta ci abincin nan"" Mama Zaituna ta ce ""To Allah Ya isa daman kun saba cin kayan Allah Ya isa in sha Allah sai ta yi aman" "shi"" Inna Binta ta ji an cauɗa mata bulala a ɗuwawu ta yi saurin dire tukunyar ta ce" """Kan uba wanne mai tsautsayin ne haka?...,"" shiru ta yi ganin Malam ya ce ""Kina sake magana ina ƙara" "cauɗa muku shasha kawai mara kan gado""" "Ya juya wajansu ya ce ""Mayu marasa godiyar Ubangiji kawai akan abinci duk maƙota da unguwa sai" "anjiku"" Inna Binta ta ce ""Yaushe rabon da muga sisi taka banda masifar tsiya kana bamu za mu yi haka ne?"" Kan ta ya yi da bulala ta yi saurin waftar dambun a hannu ta yi ɗaki tana ""Ohho dai na ɗiba na mai" "da mugun miyau""" Haushin karnuka suka ji wanda rabon da su ji shekaru uku kenan gabaɗaya suka juya wani ihu Mama Zaituna ta yi tare da fatali da dambun da ake ta yin masifa akan shi har zaninta na kuncewa zuwa ƙasa ta yi saurin juyawa zata ɗakko ta zame da ɓawan albasa ta faɗi dif a ƙasa Kasancewar ƙatuwa ce sosai ta fasa ƙara da jan ɗuwawu ta shige ɗakinta hankali tashe. Shi kansa Malam sai da zuciyarsa ta motsa saboda tsoro ya dinga kallon karnukan da idanu yadda suke ɗaga jela tare da zaro harshe waje jibga- jibga dasu sai zagaye wanda ya shigo suke yi. Da ƙyar Malam ya ja numfashi ya ce """Muɗallabi Ɗanmalam nake gani haka? Ya suka sake ka basu kashe ka ba, ni na ɗauka ma tuni ka mutu" "wallahi, ikon Allah"" sosai kansa ke masa ciwo kamar zai rabe ga wani ciwo da jikinsa yake yana jin fatarsa" "na rawa, ya yi baƙi sosai amma manyan idanunsa na nan kayan jikinsa duk a yage ya zubawa Malam" idanu. """Kai Muɗallabi ba da kai nake magana ba? Yanzu da suka sake ka me suke nufi ka kashe ƴar mutane a" "banza kenan? Ba zan goyi bayan gaskiya ba dole na je wajan jami'an tsaron yanzu na bi ba'asi""" Cikin sauri Ammo ta fito daga ɗakinta jin sunan wanda aka kira zuciyarta har rawa take tana fitowa suka haɗa idanu dashi ya kafe jikin bango a hankali yaran gidan suka fara fitowa ya dinga bin guntattakin "yaran da kallo wasu duk bai san su ba. Ya nufi Ammo ta yi saurin ɗaga masa hannu ta ce. ""Ina jin tsoron" "kiran ka a matsayin ɗana na ji na yi dana sanin haihuwarka wallahi""" Ya buɗe manyan idanunsa sai kawai ya ja ya lumshe yana ƙara yunƙurin zuwa wajanta kenan ya ji ihu a waje kafin ya motsa Goje ya shigo da sauri yana cewa """Mai dawa ƴan unguwa ne ɗauke da makamai wai za su ɗauki fansar. "" Da sauri MOH ya ɗagawa Goje" "hannu baya son ma a kira sunanta a kusa da shi zuciyarsa buɗewa take sosai. Goje ya sake cewa ""Ba ƴan" "unguwa kaɗai ba har da gajoji da cinnakun layi"" kafin Goje ya ƙarasa sun ji ana cewa" """Ba iya Mai dawa ba har Malam da babarsa yau sai sun mutu da duka mutanen gidan sai mun ɗauki" "fansar yarinyar daka kashe tunda jami'ai sun sake shi a banza"" Mutallab ya kalli karnukansa ya musu inkiya Tiger ne ya fara zuwa ƙofar ɗakin Ammo ya tsaya Rainbow ya je ƙofar gidan ya tsaya, Spider kuma ya tsaya yana kewaye Malam. Goje ya ce ""Kai ƙarfe baya cinka tsine baya ratsa jikinka su Malam sune matsalar"" bai magana ba kai tsaye ya nufi waje gaban Ammo ya faɗi ganin ba makami a hannun Mutallab. Inna Binta ta fito tana zunduma ihu tana jama'a su kawo musu ɗauki tana leƙa ƴar ƙaramar katangar gidan ganin tarin matasan da suke waje ɗauke da makamai ya saka Inna Binta kurma ihu tana faɗin ""Ya gafilan zanbi waya kashifal gammi "" Bata gama ba aka raɗa mata gora aka ta faɗo ɗaga" saman katangar ta baje wanwar a ƙasa Mufee ta fasa ihu tana yin wajan Inna Binta ganin haka sauran mutanen gidan suka shige ɗaki banda Ammo da Malam. Moh na fita suka yi masa ƙawanya kasancewar akwai shafi a hannunsa duk wanda ya daka sai ya baje a "wajan, suna da yawa sosai cike da rashin sanin cewa tsarin jikinsa ya karye ya shiga tsakiyar su ɗaya ya ɗauki dutse ya buga masa aka nan take ya fashe, wani ya ɗaga wuƙa ya soka masa a ciki nan take wuƙar ta shige Goje ya zaro idanu ganin sun yi nasara ya saka suka zagaye Moh suna kai masa sarawa, baya faɗa da makami bai san kuma ya ake yi ba, kafin wani lokaci sun kai shi kasa ko'ina na jikinsa jini ke fitarwa daidai lokacin tawagar mafarauta suka ƙarasu wajan tare da zugar karnuka faɗan ya koma tsakanin ƴan unguwa da mafarauta cikin mawuyacin hali Moh ya ja jikinsa a hankali jin wani yana waya da ƴan'sanda ji ya yi dama layya zana na wajansa a yanzu haka? Ya dinga tafiya yana jan jiki har ya bar unguwar ya shiga cikin wani waje mai kama da gonaki kuma jeji-jeji. Tana zaune cikin bukkar hannunta" riƙe da ƙwaryar nono ta ji an faɗo cikin bukkar a gigice ta miƙe tsaye... "*To ga dai shi nan ban san ya zaku amshe shi ba, amma tabbas zai zama daidai da ra'ayinku musamman" iyayenmu mata da maza da suke wasa akan yaransu. MUTALLAB zai zo da sabon salo in sha Allah za a yi kuka sosai kuma za a yi dariya fatana kar ku yi mini zagin da kukai a MIJIN MALAMA ku amshi labarin da hannu bibbiyu ku tayani isar da saƙon zuwa ga manya ta hanyar yin sharing saboda Allah* 08164069385 WhatsApp only "[10/2, 8:40 PM] Nanameera: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 2 Nimcyluv Bright pens. Second batch * Warning... For criminal issues* "Cikin bukkar ya faɗa jikinsa jina-jina da jini sara ta ko'ina da ƙyar yake iya fidda numfashi, ya zube a" "gabanta idanuwansa a lumshe har yanzu yana jiyu sautin ihu da kukanta, ya kasa ceton ta, ta sake mutuwa, yaushe zata ci-gaba da rayuwa tana sake macewa akan idanuwansa? Ya cije jajayen laɓɓansa wanda jini ya ɓata sam bai damu da yadda yake shanye jinin yana koma masa ciki ba, a matuƙar fisge ya yi maganar mai sautin gurnani ya ce ""Na amince, da gaske na amince Abbasa, zan zama mata maza, ki mayar dani jinsin mace ina tunanin zama macen ya yi daidai da tafiyar ƙaddarata! Zan zama mata maza," "bana iya kwanaki ba, bana iya wa'adin sa'a ba, ba kuma iya na tafiyar sakwanni ba, ba kuma iya na" "gilmawar kwanaki ko shuɗewar watanni da nisan shekaru ba, a'a Abbasa, a'a Abbasa ina son zama mata" "maza ne na daidai da tafiyar agogo da adadin shekarun da zan yi a duniya""" "Yadda furucin ke fitar da kan su, da yadda yake magana idanuwansa na fiddowa waje duka jikinsa rawa" "yake da ɓari yana wani irin tsuma bakinsa har wani hayaƙi yake yi jijiyoyin kansa tamkar zasu ratsa fata bakwai su keto, ganin halin daya shiga ya saka Abbasa cewa. ""Iya zubin tunanin naka kenan? Iya jarumtar kenan? Mayar da suffarka zuwa abi mafi nakasu a rayuwarka? Ka zama mace shin ko ka mace" "da. """ """Abbasa!""" "Ya kira sunanta a karo na farko a tsawa ce, domin baya son tuna abinda take ƙoƙarin cewa ""Shikenan" "shikenan, zaka zama jinsi biyu, mai halitti biyu"" ya girgiza mata kai yana jin amo da sautin muryarta cikin wutar da suka babbaka ta ciki ""Kawai ki nakasta ni"" ""Tabbas zaka nakasa, zaka zama kamar jaririn da aka haifa yau, zaka zama riƙaƙƙe zaka gagara, ubanka zai alfaharin haihuwarka duk da tsinuwarsa na tattare da kai, zaka sake yi rashi, rashi irin wanda baka taɓa yin irinsa ba, zaka samu dukkan wata shahara da" "ɗaukaka da kake buƙata, amma zaka dauwama a matsayin mata maza""" Ihu ya fasa yana ƙoƙarin miƙewa tsaye da ya yunƙura gefen cikinsa yake sake buɗewa saboda shafcecen "saran da aka yi masa, jikinsa bashi da wani gurbin da babu sara.Abbasa ta miƙe ta ɗakko wani farin abu a hannunta tana zuwa kan shi ta danne shi da duka ƙarfin daya zo mata, ta ɗauki garin abun ta fara shaƙa masa a hanci yana shaƙa da ƙyar da sauri ya damƙi hannunta ya kifa fuskarsa da hancinsa gabaɗaya," "yana ihu da gurnani jikinsa na rawa ya fara sambatu, Abbasa ta ce ""A me ka zo waje na?""" """Taya"" ya bata amsa a raunace idanunsa na lumshewa. ""Wasu sun biyo ka ne?"" Ya girgiza kai can ya ce" """Cinnaku, Cinnaku na fi ƙarfin su"" ya dinga juyya kansa can ya ce ""Akwai Kimini a tattare dani, ya faɗawa ƙashi wani abu, sun nemi asawa da Tsohuwa. !"" Ya kasa cewa komai idanuwansa har yanzu na hango" yadda gangar jikinta take ci a wuta. "Ita dai Abbasa ta kasa cewa komai ta zuba masa idanu, ta dinga kallon yadda jikinsa je rawa a hankali" "kuma ya fara saki idanunsa ƙur a saman bukkar cikin fitar hayyaci da yanayi irin na maye yake sambatu tare da kiran sunayen da ita kanta mata sani ba. A hankali ta ce ""Mutallab"" bai amsa ba sai zuciyarsa kawai dake rawa ta hango hakan ne a yanayin yadda ƙirjinsa ke ɗagawa. Ganin ya zama kamar matacce" "tsoro ya kama Abbasa ta tuna ashe bai taɓa shaƙar abin da ta bashi ba a yanzu, maganin ƙarfe dana tauri" kawai yake sha gashi kuma zaman da ya yi na shekara uku a hannun jami'an tsaro ya sa tsarin ya karye. Ƙwarya ta ɗakko ta jiƙon wani magani tare da ruwa mai zafi ta fara danna goge masa jinin jikinsa sai a "lokacin ta lura da gabaɗaya farcen yatsun ƙafafuwansa dana hannu babu ga jikinsa duk alamar an jona masa shokin akan tilasta masa amsa laifin da babu wanda yake da masaniyar komai akai, sun yi masa haka ne da nufin ya amsa laifin kashe matarsa da ya yi. Ta sauke numfashi tare da kallon bakinsa a" hankali ta kara kunnenta a tausashe yake cewa. """Ina son ta, ina son ta zuciyata zata fito ita ce wajan ta uku me ya sa.... Ina jinta a ƙasan zuciyata"" Tunda" "suke bai taɓa yi mata zance ɗiya mace ba, haka bai taɓa magana mai tsayin da ya yi a yanzu ba, duk abin da ya saka Mutallab magantuwa ba ƙaramin abu bane ba. Miƙewa ta yi ganin kamar ya samu yin bacci ta fita waje zuciyarta cike da saƙe-saƙe." Unguwar ta yi shiru saboda zuwan ƴan'sanda wanda da ƙyar suka raba tsakanin mafarauta da jama'ar da "suka zo ɗaukar fansan wacce aka kashe zai ya zama kamar an saka kafiyo ne kasancewar babu wanda bai san labarin kisan rashin mutuncin da aka yi wa yarinyar ba. Tiger, spider, rainbow sune suke ta kai kawo a ƙofar gidan Malam saboda basu tsaro kamar yadda Moh ya saba musu ya raine su tamkar mutane hatta mara gaskiya suna ganewa. Da sauri suke tafiya hankali tashe gabaɗaya basa cikin nutsuwa ɗaya" "sai ɗaga hannu sama take ba'a jin maganarta sai sautin murya. ""Ki yi haƙuri""" Sa'adah ta ce tana shafa hannunta a ƙirji alamar ban haƙuri da yaran kuramen da zata gane ta girgiza kai "tare da sunkuyawa tana buga ƙasa ta ɗaga yatsa sama alamar rantsuwa. ""Allah Ya kyauta, da kin bari mun ƙarasa gani ai ya kori ji Bafullatana"" daidai nan suka ƙarasu ƙofar gidan ba kowa a rumfar Almajiran sai allonansu da rubar tadawa da ƴan rubobi na bara. Tiger ya ƙare musu kallo yana shinshina su sai" kuma ya ja da baya yana ɗaga ƙafa ya basu hanya suka shige cikin gidan. Da Inna Binta dake yashe a ƙasa suka fara cin karo jini na zuba a gefen goshinta ɗan tofinta a bankaɗe "Allah Ya sa ba yara a wajan cikin hanzari Sa'adah ta nufeta tana girgizata ta juya ta yi wa Bafullatana alama data bata ruwa bata fahimci komai sai kawai ta kinkimo ruwa bokici guda ta kwarawa Inna Binta ajjiyar zuwa ta sauke a firgice ta miƙe zaune tana furta ""Dambun Mufee, a kawo ɗauki jama'a dambun Mufee ƴan ta'adda za su kashe ni"" ta ƙanƙame hannunta jikinta ya jiƙe jagab amma har yanzu dambun na hannunta ta miƙe ganin Sa'adah da Bafullatana sai kuma ta ja tsaki ""Irin bala'i wallahi Ammo ta haifawa unguwar Birget masifa ɗai-ɗai da ɗai-ɗai zai dinga kashe mu yana zuƙe jininmu ku duba wannan" "yarinyar ma ya kashe ta kari na uku""" Idanun Sa'adah ya cika da hawaye amma ta ɗauke kai ba tare data tanka Inna Binta ba. Inna Binta ta "watsawa Bafullatana harara wacce ke ta ihu tana taɓo Sa'adah ta ja tsaki ""Kurman banza da wofi gayya masifar, daga haihuwar kurma sai ta ɗan jagaliya"" tana kaiwa nan ta shige daƙinta ta samu Mufee tana bacci ta yi maza ta tashe ta, tura mata ɗan guntun dambun ta yi a baki bayan ta cinye ta ce ""to sha ruwa kiji abin da kika samu sai kuma gobe, ki yi addu'a ki goge Allah ki gode Muhammadur Rasulullah. Banda ina buɗe ido a gidan nan kema mutuwa za ki yi saboda yunwa kamar taki ƴar'uwar"" sai kuma saka dariya" "sosai ""Inna mene?""" """Tukunyar dambu ta kife dan ubanki da tuni ba ki lasa ba kema"" Mufee dai ta buɗe manyan idanunta irin" na Mutallab tana kallon Inna Binta. "Ammo ta dinga bin Sa'adah da idanu ganin yadda take kuka kamar ranta zai fita, Bafullatana kuma ta" "haɗe rai sai girgiza kai take ""Ammo don Allah ina Mutallab yake? Da gaske ya dawo an sake shi? Sun wanke shi daga zargin da ake masa, yana ina?"" Ammo ta ɗauke idanunta zuwa can gefe tana kallon wani waje daban a ɗakin nata can ta ce ""Ki daina kira mini sunansa sallamamman yaron nan a kunnena" "Sa'adah, ki yi hankali watarana zai iya kashe ki""" """Ba zai taɓa kashe ni ba, duk lalacewar shi jinina ne ɗan'uwana ne a wannan halin da yake ciki na ɗauka" "za ki yi murna Ammo? Za ki ja yaronki jikinki ki nuna masa kulawa gudun kar ya sake lalacewa, kar ki ce za ki yi abin da kikai a baya duk lalacewar Mutallab kece wacce kika haife shi, tun yana ƙaramin kin san zuciyarsa yadda yake da zafin nama taurin kai. Kin san yadda yake da ƙulafucin uwa kodayaushe yana manne dake, me ya sa za ki yi haka?"" Miƙewa Ammo ta yi ta nunawa Sa'adah hanya ta ce ""Tashi ki tafi gidan mijinki, banga dalilin zuwanku ba ni bani da wani ɗa Mutallab kuma na sani kuskurena ya saka na haifeshi. Wallahi kika sake yi mini maganar tsinannen yaron nan sai na daina amsa gaisuwar ki har abada"" tana kaiwa nan ta fice ta bar musu ɗakin, fuuu Bafullatana ta fice daga ɗakin zuciyarta na yi mata zafi Sa'adah ta yi shiru ita dai tana mugun son ƙannin nata ai da ba haka yake ba, ya kamata su amshi" hakan matsayin ƙaddara! Washegari Malam na zaune a rumfa yana sauraren karatun wani sabon almajirin shi. Ɗanyaro ne zauna "gefe kusa da Malam yana lissafa sabbin kuɗin hannunsa ƴan dubu-dubu sai sheƙi yake ya duba yaga dubu biyar cif ya mayar aljihu ya zaro baƙar leda mai cike da gurasa da nama ya ya fara ci yana ajjiye lemo fanta a gefe. Ajjiye bulalar Malam ya yi ya ce ""Ɗanyaro ina ka samu kuɗi da nama haka?""" """Bani aka yi Malam"" kafin Malam ya sake magana Ɗanyaro ya miƙawa Malam baƙar leda guda mai" "ɗauke da gurasa a ciki da nama ya haɗa masa da dubu biyu ya ce ""A yiwa su Mufee girki Malam""" "Jiki na rawa ya amsa yana buɗe bakinsa ""Da kyau yaron arziƙi, ina ka samu kuɗi fal haka sana'ar me ka" "fara?"" Ɗanyaro ya girgiza kai kawai can kuma ya kalli Malam ya ce ""Bana yin sana'a, kyauta ake bani kullum, bani kaɗai ba har Muhajeed da Iro"" Malam ya yi sak tunani fal ransa ya sake kallon Ɗanyaro shekarunsa goma rak a duniya a hankali ya miƙe ya yi cikin gida." **** A kusan tare manyan motoci biyun suka tunkaro babban gate ɗin ganin ya rigata kai hancin motarsa ya "saka ta rage ta fiya, hannunta ɗaya a saman sitiyarin motar ɗayan kuma ta ɗan riƙe fuskarta a hankali ta lumshe idanunta gajiya ce a jikinta sosai da ƙyar take buɗe tuƙa motar don dai bata san wahalar driver ne." """Fiyya"" Ya kira sunanta a hankali cikin muryarsa mai cike da nutsuwa ta buɗe idanunta da sukai mata" "nauyi ta kalli wayarta ta manta video call suke yi ma suna haɗa idanu da shi ta ɗauke kan ta gefe tana ya motsa fuska ""Fiyya na miki wani laifi ne? Kin sauya""" """I am sorry ina driving we'll make a call later"" ya zuba mata idanu cike da so da ƙauna yana jin ina ma a" "janyo ranar aurensu da Fiyya a ce gobe ne? Ya sauke numfashi zuciyarsa na buɗe a hankali ya ce “I adore you Fiyya"" ta buɗe idanu ta kalli cikin idanunsa sai kuma ta murguɗa masa baki ya buɗe idanu sosai sai" "ya girgiza kai yana dariya ya matso da fuskarsa dab da camerar ""Na ji kamar ina shaƙar numfashinki """ "Ya yi shiru jin ana knocking ƙofar motar da take ciki, itama ta juya ganin wanda yake tsaye ya saka ta ɗan" "yi murmushi baya ganinta saboda duhun gilas ɗin motar amma murmushi mai kyau ne a fuskarsa. Ta cikin wayar ya ce ""Waye?"" Tana ɗaukar jakarta a taƙaice ta ce ""Yaya Junaid ne""" """Ok"" ya yi sai kuma ya ce ""Fiyya"" ta ɗago idanunta da sukai laushi ta kalle shi dasu can ƙasan maƙoshi ya" "ce “I love you Fiyya"" da sauri ta kashe call ɗin tana haɗe fuska ta ɗauki wayar ta fita daga motar." """Yaya J"" yana murmushi ya ce ""Manager"" ta ɗan yi murmushi kawai ya amshi jakar hannunta ""Me kika" "zo da shi""" """Ba kyau bincike J"" ya jinjina kai suka nufi shiga gate J ya kalli driver ya ce ""Ka shigo mata da motar, she" "left the key inside the car"" Fiyya ta marairai ce fuska tana mannewa jikin J ta ce ""Yaya J na gaji sosai""" """Sannu Manager, ko goyaki zan yi?"" Ta buɗe idanu sannu yake ta yi mata har suka shiga babban parlon" "gidan ƴan samari wajan biyar a zaune a parlon duk dawowar su daga aiki kenan. Wajan tare suka dinga cewa ""Sannu Manager"" ta shige tsakiyar su tana kwanciya a cinyar Marafa ta ce ""Thank you brothers, ku yi mini tausa akwai labari""" """Gulma dai ba labari ba, daka dawowa ko wanka ba ki yi ba kin zaunawa mutane a jiki ƙazamar banza""" "Shiru ta yi masa don basu fiye shiri ba sosai ta juya idanunta rufe, tana jin yadda Marafa ke ta danna mata farar ƙafarta. Yaya J kallonta kawai yake with different thinking running on his mind. Gabaɗaya suka juya jin tafiya cikin sauri ana sakkowa daga saman bene shiru duk sukai suna binsa da idanu domin basu san ya dawo gidan ba, hannunsa ɗaya zube cikin aljihu farar riga ce a jikinsa ta kakin sojoji a gaban" rigar wajan gefe an rubuta A.A MARAFA. """Kee!"" Ya faɗa a tsawace da sauri Fiyya ta buɗe idanunta lokaci ɗaya kanta ta sara sosai tsawar ta ratsa" "kanta, ta miƙe zaune fuskarsa babu walwala kamar yadda itama ta yi kicin kicin da rai ""Tashi a nan, stupid kawai"" ta miƙe tsaye tana murguɗa baki ko inda yake bata kalla ba ta nufi saman bene kai tsaye daƙinta ta nufa idanunta cike da bacci ta faɗa saman gado cikin ƙaramin lokaci bacci ya ɗauke ta. Firgigit ta farka jin sautin labaran ɗ da ake faɗa a gidan rediyo wacce take cikin ɗakin nata, ta miƙe tsaye ta ɗauki rediyon ta ƙanƙame a jikinta tare da lumshe idanunta wasu hawaye masu zafi suna shiga bin idanunta. Ta cikin idanunta take hango fuskarsa a lokacin da rigima ta haɗa su da ita sai take ganin" kamar yanzu ne komai yake faruwa. Students ne an cika sosai saboda class partyn da ake yi na kammala exam maza da mata babu teacher ko ɗaya tunda ta shigo hall ɗin makarantar tasu take duban inda zata ganshi. Cikin sa'a ta ganshi yana zaune saman window sanye da gajeren wando fari tas sai armless ɗin riga wacce duk aka yanke hannunta gashin kansa rabi a aske ya zubawa wani tafkeken gidan masu kuɗi idanu ta waje baya ko ƙiftawa kamar an ce ya juya ya ganta tsaye ta zuba masa idanu yaja tsaki kafin ta yi magana an shigo an "ce ""Mutallab, principal yana nemanka an kai ƙarar ka wai kana son Fiyya""" "Ya ware idanu abin da bai taɓa zuwa tunaninsa ba kenan sai kuma ya cije baki ""Shi principal ɗin ubana" "ne Malam Abdullahi kenan?"" Ya juya ya kalleta sosai ya ce ""Sai godiya, ni? Kuma ke hauka kenan""" """Kai ne mahaukaci"" furucin ya fita daga bakin Fiyya ""Kuma na yi maka nisa, kasan yadda nake da masoya" "a makarantar nan amma ni ubana ba soyayya ya kawo ni ba, karatu zan yi ina da buri mai faɗi da zan" "cimma"" Ya miƙe tsaye yana kallonta daga sama har ƙasa a ransa yana ƙissima abu ""Shi uban naki can ta" "matse masa, karatun banza kawai ka zama mai iko shine""" """Ba dai ubana sai dai "" Ya buɗe idanu sai kuma ya fasa abin da ya yi niyya ganin hawaye a idanunta" abin da bai taɓa gani ba. Da sauri ta fice daga hall ɗin ta zaga baya ta durƙushe a wajan tana fashewa da "wani irin kuka kamar zata haɗiye zuciya ""Daddy na shiga uku ina son Mutallab""" "Ƙanƙame redion ta yi tana sake fashewa da kuka jikinta har jijiiga yake ta ce ""Na shiga uku Daddy, ba zan" iya ba I can't do it ina son shi. "Kamar daga sama haka ya faɗo cikin gidan, jikinsa duk liƙe da bandeji jini na ɗiga kaɗan-kaɗan kwana" "biyu yana jinyar raunin bai san waye ya yi masa ɗinki ba. Idanunsa jajur har lokacin saboda bai gama dawowa daidai ba sai muzurai yake yi ya ja ya tsaya yana kallon murhun da aka sauke abinci akai ya juya ya kalli ɗanwaken dawar da Inna Binta ta yi ta shiga daƙi ɗakko magi ta barbaɗa ko arziƙin yaji bai samu ba, yaja kwanon da hurɗu-hurɗu yake tura ɗanwaken kafin wani lokaci ya kammala cinyewa tas ya zube a wajan ya kwanta ya rufe idanu, wata nutsuwa yake jin daya kwanta a tsakar gidan mahaifin nasa. Ya yi kamar bacci yake yana jin Inna Binta ta lailayo ashar ta ƙunduma ta ce ""Wanne ɗan abu takazar ne ya cinye mini abinci Mufee wanne mayunwacin ne mara godiyar Ubangiji"" tsit ta yi ganin Moh kwance hannunsa duk manja taja baki ta tsuke ta ɗauke kwanan tana suɗewa a zuciyarta tana jan Allah Ya isa. Har ya shiga ɗakin Ammo ta bankaɗa labule ta ce ""Wallahi abincin da ɗan ta'addar ɗanki ya cinye mini Allah Ya isa, kawai kin haifa mana jaraba ko ɗanɗana ɗanwaken ban yi bafa ya cinye"" ta dinga zagin Ammo ta uwa ta uba ta shige ɗaki tana sake suɗe kwanon da ƙyar ta samu rancen ɗari biyu ta yi cefane" da ledoji ta dafa. Tana shiga ɗaki ba jimawa ta ji an bankaɗo labule sai ta zuciyarta ta buga ganin shi tsaye hannunsa riƙe "da gora ya suke askara a gefen ƙugunsa ga gori a hannunsa, ya juya ya kalli Mufee da hannu ya yi mata alama data fita cikin sauri ta fice tana fita muryarsa a daƙushe kamar dole ya ce ""Tiger spider a yi mata aiki"" manyan karnukan suka faɗa cikin ɗakin Inna Binta ta fara ihu tana maƙale jikin sif ""Nafsi nafsi jama'a na shiga uku ya Allahu Ya Rahmanu, don Allah ka yi haƙuri Muɗallabi zan bawa Ammo haƙuri ka rufa mini asiri kar Mufee ta zama marainiyya"" Haushi kawai karnukan suke Tiger na kai mata cafka Inna" "Binta ta fashe da kuka fitsari na bin ƙafarta ta ce ""Hal'àtaka hadisul gashiya ni Binta na shiga uku""" "Moh ya ce ""Sai godiya"" gabaɗaya karnukan suka tsaya cak Inna Binta na haki ta jiƙe gabaɗaya da fitsari" "har lokacin tana maƙale jikin sif kamar ba zai magana ba ya ce ""Bani ƙudin nan"" jiki na rawa ta miƙa masa ɗari biyar ɗin hannunta ya amshe ya yi waje ta sake sif ɗin ta fashe da kuka tana faɗin ""Tsinannen yaro manta ganin yaron dake son uwarsa kamar mutuwa ba irin shi"" Moh na fita ya leƙa ɗakin Ammo ta ɗaga kai tana ganinsa ta ɗauke fuska ya yi ta kallonta ya jima tsage kafin ya sauke labulan ya juya. Yana fita wani babur na tsayawa a gabansa aka cillo masa takarda da gudu aka ja babur ɗin tare da barin" wajan. Ya ɗauki takardar ya buɗe rubutu ne bai fi layi biyu ba a hankali ya fara karantawa. _Mai dawa baka gajiya? Sau dubu zaka kula mace sau dubu zamu kashe ta. Karo na uku kenan ga misali akan matarka nan_ da jan biro akai rubutun ya juya da sauri amma tuni babur ɗin ya ɓace ɓat waye wannan? Su duka shi ne silar mutuwar su kenan? Waya ya amsa hannun wani Almajiri ya kira wata "number ana ɗaga aka ce ""Sai godiya"" Ya numfasha" """Duk inda ƴan daba suke ka haɗa mini su"" ta cikin wayar aka ce ""Mene haɗinka da daba ko dai ka fara" "shaye-shaye a state cid ɗin?"" Moh ya cije baki ya ce ""Zan fitini mutane, na ji daɗin zama can""" """To me za su yi maka?"" Wannan yaran da suka sare ni iyayensu za su ɗauki sabbin ciki yau, ƴan cikin gari" "ne a yi mini kan me uwa jawabi"" yana faɗin hakan ya kashe kiran ya goge number tas ya lumshe idanunsa ya buɗe sai kuma ya cije leɓe zuciyarsa zafi take sosai ji yake dama ya yi kuka, amma ba a haife shi don ya zubar da hawaye ba ya ɗaga idanu sama ya ce ""Da gaske ni na kashe ta amma ba zaku taɓa sani ba"" daidai lokacin mafarauta suka kawo kai suna busa ƙaho da buga gangaga suka zagaye Moh ana ""Sai Mai dawa ina uban wasu ga namu wuya a ina wuya a daji, kai ne mai Tiger kai ne mai gadon tawada"" Jikinsa ya hau ɓari da karkarwa tsumin shi ya motsa idanunsa na ƙaƙƙafewa ya yi kururuwa tare da ɗaga gora sama ya ja ya ƙame sai jikinsa dake rawa ya fara ""La'ilahaillahu, sai ni ɗan babana Malam Abdullahi ɗan malam ɗan gatan Ammo ƙanin Sa'adah ƙanin Bafullatana waye ce bani ba Muɗallabi sarki Mai dawa da jeji"" gabaɗaya suka zagaye shi suna sake zuga shi daidai lokacin kuma suka ganta kamar" daga sama..... *In sha Allah za ku ji abin da baku taɓa ji ba * 08164069385 WhatsApp only "[10/4, 9:17 PM] Nanameera: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 3 Nimcyluv Bright pens. Second batch "Da sauri ya nufe ta kamar zai kai mata cafka, ta yi saurin ja baya idanunta cikin nasa. Yana tangaɗi ya ja" "ya tsaya a gabanta tare da ƙura mata idanunsa da suke lumshewa, har yanzu jikinsa ɓari yake domin" basu daina buga ganga da ƙahon da suke busawa ba kamar masu yin gangi. "Hannunsa ya ɗaga musu cikin sauri suka daina abin da suke, cikin izza da gadara ya basu umarnin tafiya" "har lokacin idanunsa yana kanta ganin yadda take kallon shi kamar ya ta saba ganin halittarsa. ""Ban yi zaton a haka zan ganka ba, autan Ammo me ya sa?"" Ya ɗauke kansa yana haɗe fuska sosai ba wargi banda cewa ita ce ba zai taɓa tsayawa ba. Cikin raunin murya kamar za ta yi kuka ta ce ""Me za ka yi da wuƙa haka?"" Ya buɗe ido sosai sai bai magana ba, a hankali ma ya bi gefen ta zai huce ta yi saurin riƙe masa hannunsa tana faɗin ""Ni ɗin ma? Yau za a ji kan mu da kai, kar ka faɗa mini sauyin da ka yi ya" "zagayo har kai na?""" "Ya ɗago kai ya kalle ta ya kalli hannun data riƙe shi da shi, hannunta fari tas saɓanin nasa da yake mai" "kauri kuma baƙi irin na majiya ƙarfin nan wanda suke tashe akan shekarunsu. ""Don Allah ka tsaya mu yi magana, ni ko gidan ba zan shiga ba wajanka na zo"" ya cije bakinsa ya mai da kai gefe cikin muryar mai kauri ya ce ""Kin ci darajar Ɗan Amina, mene sakin?"" Ta girgiza kai kawai tana duban gefe dakalin dake wajan ta gani ta je ta zauna akai, ta yi masa alama ya zauna amma ko motsi bai yi ba, ta san cewa yana jinta amma hankalinsa na kan hanya sai waige-waige ""Mutallab ka kalle ni bafa wani zai kawo maka farmaki ba"" ta nisa idanunta cike da ƙwalla ta ce ""Don Allah kai ne ka kashe ta? Ba zargin ka nake ba Autan Ammo ni me iya rufa maka asiri ce idan ya zama kana da laifi ka faɗa mini gaskiya na maka" "alƙawarin ko Ammo ba zan faɗawa ba, ka kashe matarka ko ba kai bane?""" "Ya juya da wani irin sauri yana kallon fuskarta da take kallon shi cike da damuwa, idanunsa ya yi jajur" "naman jikinsa na motsawa ya kasa furta komai. Miƙewa Anty Hameeda ta yi tana girgiza kai kuka na cin ƙarfinta ""Ko minti ashirin ba mu yi da kai maka matarka ba, sai labarin mutuwar ta muka ji da kisan wulaƙancin da aka yi mata. Mutallab kai ne fa muka gani tsaye akan gawarta, kai ne fa riƙe da wuƙar da aka kashe ta da ita jikinka duk jinin matarka innalillahi wa'inna ilaihirraji'un na kasa yadda ka kashe ta, daman soyayyar da ka nuna mata na iya fatar baki ne?"" Wani irin ihu Anty Hameeda ta yi tana kaiwa jikin bango ganin ya ɗaga hannunsa ya yo kanta sai kuma ya tsaya cak, a hankali da baya da baya ya dinga ja yana ƙare mata kallo sai kuma ya taune bakinsa idanunsa kamar zasu zazzago don girma kallo ɗaya idan ya yi dasu sai an razana da ƙyar ya iya ware laɓɓansa biyu da sukai masa nauyi sosai ƙasan" zuciyarsa na ta fasa banda cewa Anty Hameeda ce tabbas da sai ya karya ta gida huɗu. """Ni na kashe ta, ta cancanci haka ne"" ya juya da sauri Tiger da spider da rainbow suka bi bayansa kamar" "zai tashi sama haka ya sha kwana. Zubewa Anty Hameeda ta yi a wajan tana rushewa da kukan baƙin ciki, su waye suke da saka hannu wajan lalacewar Mutallab? Ba komai ta sani ba ita ba ma'abociyar zaman garin bace ita da mijinta ta dinga kuka da ƙyar ta rarrashi kan ta, ta miƙe tsaye kamar zata shiga gidan nasu sai kuma ta fasa tana ƙoƙarin barin wajan ta ji Malam ya ce ""Hameedatu me kike anan ina mijin da yaran naki?"" Kanta a ƙasa ta ce ""Suna gida, ina yini Malam?"" Ya jujjuya yana kallon hannunta ganin babu komai ya ce ""Ba za ki shiga bane?"" Ta girgiza masa ""Zan juya wajan Mutallab na zo"" ya jinjina kai domin" ba wannan ne a gabansa ba. """Ba wata mutalla da zan iya samu a wajanki na siyo wainar rogo?"" Ta buɗe jakarta ta zaro kuɗi tana" "irgawa ya yi maza ya fisge ya ce ""Mene na lissafi? Maza jeki wajan yaranki kuma na ja kunnenki babu ke babu yaron nan idan ba su kike watarana ya ja miki masifar da za ki ƙare rayuwarki a gidan ɗan kande ba"" bata ce komai ba sai data juya zata tafi ta ce ""Duk lalacewar Mutallab kai ne ka haife shi, jininka na wanzuwa a nasa"" tana kaiwa nan ta yi gaba abinta saboda ɓacin rai da damuwa ko gabanta bata gani" sosai. Moh na kwance a saman wani dutse idanunsa a rufe tun bayan barin shi wajan Anty Hameeda ya zo "wajan ya kwanta, zuciyarsa a cunkushe take babu gurbin samun sauƙi a cikinta duk yadda ya ke son tuna waye shi me ya sa ya zama haka sai ƙwaƙwalwarsa ta yi hooking, ya ɗauki zafi sosai ta yi ta processing ya ji Ammo ɗinsa kawai yake son kasancewa da ita yanzu. Ya motsa kaɗan zazzaɓi ne sosai a jikinsa saboda saran da aka yi masa bai gama warkewa ba, baya kuma shan magani wacce zata iya kula da shi baya jin zai iya zuwa wajanta. Ya ƙanƙame jikinsa sosai abubuwa da yawa baya son tunawa sai ya cimma muradin zuciyarsa sai ya ɗauki fansa na abin da aka aika, sai ya bayyana abubuwa da dama tunda har suka bari ya shiga cikin gidan yari ya kuma yi shekaru uku a Cid ya rayuwa cikin masu aikata manyan laifuka. A sama" ya ji an kira sunansa """Mai dawa, sarki mai jeji"" bai buɗe idanunsa ba, bai kuma ɗauki murya ba haka baya buƙatar sanin waye" "don hakan babu abin da zai ƙare shi da shi. Ya nemi waje ya zauna yana furta ""Ka saɓe Mai dawa ka basar, fansa kake buƙata ba raunin zuciya ba, ka ajjiye tunanin baya ka fuskanci burinka ka zama abin da kake muradi kafin aga bayanka"" har lokacin bai buɗe idanu ba, ko inuwarsa bata motsa ba. Mangal ya ɗaga kai yana busawa samaniya hayaƙin sigari ""Idan kana son yin bacci cikin nutsuwa ka manta komai ya kamata ka sha wannan"" ya zaro abu a aljihu yana kalle-kalle sai a lokacin Mai dawa ya buɗe rinannun idanunsa ya juya ya kalli mai maganar irin kallon waye kai? Mangal ya ce ""Ka dake musulmi akul" "musulmu, zuwa na yi na taimaka maka""" """Riƙe wannan tiramol ce, ko doki ya sha sai ya gane barno gabas take kana afawa za ka ji zam-zam komai" "ya zama labari"" Mai dawa zubawa ƙwayar idanu shi bai taɓa shan ta ba, bai taɓa shaye-shaye ba ya juya ya kalli Mangal ""Da gaske zan yi bacci?"" ""Darr ne ai aikin wannan kamar yankan wuƙa ne, mai ƙirin ce da ƙyar aka bani ita ina karɓa na doƙu nan"" jikin Mai dawa na rawa ya amshi ƙwayar guda ɗaya ya cilla cikin bakinsa, yana runtse idanu ya yi shiru. Mangal ya zubawa Moh idanu a ransa yana jin wani daɗi da kuma farinciki bai taɓa yin aikin da za a bashi kuɗi masu yawan da aka ce ba irin na yau, gashi ya yi nasara Moh ya sha ƙwayar. Jikin Moh ya ɗauki rawar zafin zazzaɓi duk da irin dariyar da yake da ita, gashi duk inda ya motsa ciwon shi jini yake babu wani wanda zai iya duba lamarinsa sannu a hankali ya fara dafe kan shi da wani irin gurnani yaga sama na jujjuya masa ya ɗaga hannu da niyyar ya tare sama ya faɗo daga saman dutsen sai saka hannu yake yana tare sama a hankali kuma jikinsa ya fara saki yana jin wani shuu a tsakiyar kansa yana game jikinsa gabaɗaya zuciyarsa da tunaninsa suka dinga kissima masa kawai ya" kashe kansa ko ya cinnawa gidansu huta gabaɗaya kowa ya mutu har shi. Ganin laɓɓansa na motsawa alamar yana magana ba'a ji sosai ya saka Mangal matsawa tare da kafa "kunnensa a bakin Mai dawa cikin mawuyacin hali yake furta ""Safiyyerh... Safiyyerh...Safiyyerh"" Mangal ya maimaita sunan a fili “Safiyya?” wace haka? Ko ita ce wacce ta mutun wacce aka kashe? Ya miƙe" tsaye ya ɗauki wayarsa wata number daya haddace ya saka ya kira ana ɗagawa Mangal ya ce """Sakin nan ya kammalu, yanzu zan zo a taya na amshi fararen"" shiru ya yi yana sauraren mai maganar" "kafin ya ce ""Jira jira jira nifa cikin uwata aka haifan ba ɗan zina ba, na maka al'ƙawarin dole zan bawa Mai dawa ƙwayar kuma da sannu zai zama namu. Sai dai na ji yana kiran sunan wata ɗawa wai Safinu ko Safiya?"" Ya ƙara yin shiru ya numfasa ya kalli Moh dake kwance a wajan ya ce ""A'a Oga ni bana sabga da masu ɗan kwalin nan. Da ƙirin ka oga kanka baya kullewa a fice kake sai na doƙu yanzu"" Kashe wayar" Mangal ya yi kuma ya goge kiran cikin sauri kuma ya bar wajan. "Baya tantance halin da yake ciki, sai dai yanayin na yi masa daɗi sosai shi ba'a sama ba shi ba'a ƙasa yana" fatan ya dauwama har ƙarshen rayuwarsa. Duk da a cikin giyar maye yake bai hana shi gano fararen "kyawawan idanunta masu matuƙar ɗaukan hankali ba, a lokacin da take masa wannan duban ji yake" kamar ba zai taɓa aikata abu makamancin haka ba amma ƙuruciya da wawta ya saka komai ya wakana a lokacin da duk su biyun basu ankara ba. Gani ranar yake kamar yanzu a cikin idanunsa ya juya da ƙyar yana buɗe idanu zuwa gefe guda sai fara hango kansu su biyun a shekarun da suka huce suna tsaye tana jifansa da wani irin kallo. "Suna tsaye za su shiga practical a lokacin, ya jingina da jikin bango ƙafarsa ɗaya a jikin bangon ɗaya a" "ƙasa ya harɗe hannayensa duka biyun a ƙirji students ɗin yake kallo yana mamakin abin da ya saka ƴan mata ke burge wasu mazan, as a man kuma good man kawai ka nemi kuɗi ka yi arziƙi ka shahara a duniya shi ya fi, ka zama mai iƙo da faɗa a ji, ka zama wanda zai iya samun abincin da zai ci da safe kuma ya ci da rana ya ci kuma da dare ya bawa ƴan'uwasa da duk mai jin yunwa ya zamana kuma ka kasance mutumin da ake shakka duniya ta san da zamansa bawai kana namiji ka ƙare a wajan wata yarinya ba." Yana cikin wannan tunanin ya ji an ja mugun tsaki ya buɗe idanu ya ganta sosai ya buɗe idanunsa da suke a rufe kodayaushe cike da gashin idanu masu tsayi. """Kai ai babu macen da zata soka a school ɗin nan, sai dai kaga ana soyayya"" bai taɓa tsayawa ya tanka ta" "ba sai lokacin har zai mata shiru sai ya ce ""Ok"" ta haɗe fuska ""Saboda macen abinci ce ko iskar shaƙa daya zama dole Mutallab ya amfana dasu?"" Ta yi masa sheƙeƙe tana nuna masa ɗaliban makarantar da kana ganinsu zaka san iyayensu nada arziƙi sosai kowanne a students ƙuruciya da tashen balaga na ɗawainiyya da su. Ta ce ""Mata ai sune jin daɗin maza, kai fa mace ko kiss bata taɓa yi maka ba a school ɗin nan"" Mutallab ya yi ta kallonta daga sama har ƙasa ""Matar Moh zata zama mai irin halin MOH"" har ya juya sai yaga bata ci bulus ba ya tako har inda take ya zuba idanunsa cikin nata kamar yadda take kallon tsakiyar nasa idanun yana sake matso da fuskarta ""About the kiss, ƙilan Moh ya ji ƙan ki ya yi miki" "don naga shi kike buƙata""" Tsoro ya kamata amma ta dake ta fara ja baya ya yi saurin saka ƙata ya falleta kamar zata kita ya saka "hannu ya cafko gaban wandon uniform ɗinta ya dawo da ita dab dashi yana sauke mata numfashi a hankali kuma ya ɗora fuskarsa. ""Mai dawa"" kiran da aka yi masa ya saka bidiyon abin da ya faru a baya" "saurin gogewa a idanunsa har lokacin idanunsa na kafe waje guda sosai yake son sake tuna abin da ya faru a lokacin ya gagara. Goje ya ce ""Nan ka auno kenan, na samo sha ɗayan gayen nan. Ya naga kamar a buge kake?"" Goje ya faɗa yana tattaɓa jikin Moh ya ji zafi sosai idanunsa kuma ya kaɗa ya yi ja ya san babu abin da zai fahimta koda ya yi masa bayani ""Mene haɗin mafarauci da shaye-shaye?"" Shi dai ya yi shiru kawai zumbur kuma ya miƙe tsaye kamar wanda ya tuna wani abu ya juya idanu wuƙar da ya gani a jikin Goge ya fusga duk yadda Goje ya yi da shi amma ya kasa amsar wuƙar cikin sauri kuma ya mara" masa domin ganin me zai aikata? Tafiya suka dinga yi har suka kawo titi ya tsayar da mai napep ya faɗa shima Goje ya faɗa ciki. Shi kansa "bai san ina za a kaisa ba. Tafiya suka sosai har suka ƙarasu daidai wajan wani ƙaton kamfani wanda kaf Kano babu wanda bai san zaman wannan kamfanin ba. Iya haɗuwa ya haɗu ginin kamfanin ma abin sha'awa ne ga masu tsaro ta ko'ina. Ya tsayar da mai napep ɗin ya sauka ""Kuɗi na?"" Ya buɗe ido sai ya" "share ""Malam haƙƙina na daƙƙoka daka waje mai nisa ina da wajan zuwa"" Goje ya ce ""An cinye""" """Kut, ni da haƙƙina daman tunda na daƙƙo ku na ji kuna warin wiwi na san cewa ɓarayi ne ku, cikakken" "ɗan zamani ne nima ku bani kuɗina yanzu ku na daki kuɗin"" Goje ya ce ""dan babarka zo ka daka idan ka haifu"" mai napep ɗin ya share shi, ganin Mai dawa ya yi shiru yana kallo kamfanin ya nufi inda yake ya damƙi wuyansa ya ce ""Kai ka tsare ni ai ,"" kafin ya ƙarasa maganar Mai dawa ya damƙi hannunsa ya" "matse ya bada sauti ƙass har lokacin ya kafe kamfanin da idanu. Mai napep ɗin na ihu yana neman ɗauki Goje ya zaro wuƙa yana bubbuɗe jajayen idanu hakan ya saka ba wanda ya zo wajan kowa saurin barin hanyar yake gudun kar tsautsayi ya faɗa masa. Mai dawa ya saki karyayyen hannun mai napep ɗin ya ƙara damƙar ɗayan zuciyarsa na tafasa har yanzu ba komai yake ganewa ba, ya sake karya hannun" daman ba tare daya sake shi ba ya ce """Goje""" """Mai dawa sarki mai jeji, sai godiya""" """Kamfanin meye wannan? Na waye kuma?"" Goje ya kalli tafkeken kamfanin da manyan motoci ke ya" "shiga da fita kafin ya ce ""Sai godiya, ciki ne a kan sabgar nan bani da ilimi akan wannan massarafar""" Mai dawa ya saki mai napep ɗin da ya karya masa duka hannunsa biyu yana ja da baya a hankali ya ce """Ina son shi, ina son ya zama mallakina"" cikin sauri Goje ya ce ""Me kake so?""" """Kamfanin""" "Tana zaune akan kujerar dake haɗɗan office ɗin, cikin nutsuwa dake danna system ɗin gabanta files da" yawa cike saman table ɗin hankalinta na kan aiki sosai kana kallon fuskarta zaka san serious ce ita akan aikinta bata da wasa ko kaɗan. Brown suit ce a jikinta mai riga da wando ta yi rolling kanta da mayafi zagayayyiyar fuskar ta fito sosai ta saka wani shade a idanunta baƙi. Wayarta ta fara ƙara alamar kiran ta "san tunda ya fara ba zai daina ba, cikin nutsuwa ta murja kujerar ta yi ba, suu kuma ta kujerar zuwa inda wayar take ta ɗaga kiran tana sawa a hands free" """My manager"" ta ɗan buɗe idanu ta cikin glasses ɗin ta yi shiru tana ta danna system a hankali ya ce" """Maamah"" ya kira ta kamar yadda suka ce mata ta sake yin shiru domin bama ta jinsa sosai ""Fiyya ina miki magana?""" """Yaya J yaushe zaka fara ɗaukan aikinka very serious, ina kan aiki fa"" ya yi murmushi mai kyau tana jin" "sautin shi a kunnenta ""Sanda kika so na zama Mamaa""" """Uhm kiran fa?""" """Kin ci abinci, nina manta Captain ya saka na kira na tambaye ki"" cak Fiyya ta tsaya da abin da take ko dai" "bata ji daidai ba ""what?"" Ya ce ""Kin ji ai"" a taƙaice ta ce ""Na ci"" ya ce ""Good, ƙarfe nawa za ki tashi?""" """Ina da meeting Yaya J ka biyo ka ɗauke ni i can't drive cikina ciwo"" cikin sauri ya ce ""Subuhanallahi! Bari" "na zo na duba ki ko kawai mu tafi gida"" kashe wayar ta yi domin ba wani ciwon ciki da take so take ta saka kanta busy sosai ko zata manta da wasu abubuwan. Knocking aka fara tana ji ta yi shiru can ta ce ""In"" ya buɗe ya shigo idanunsa ya sauka a jikin sunanta dake manne a table ɗin “SAFIYYERH A. MARAFA”" "ya ɗauke idanunsa yana rusunawa ya ce ""Good day Maa""" "Da hannu ta yi masa nuni ya zauna bayan ya zauna, still idanunta akan system tana danna keyboard ta" "miƙo masa file ya ɗauka ya ce ""Wannan fa?"" A nutse ta ce ""I have to ask, daga ina file ɗin nan? Wanne kaya aka fitar aka samu ruɓanyar kuɗi kashi wajan goma cikin awa guda Accounter?"" Ya ɗan shafa kai ya" "ce ""Maa ni ma haka na gani, kawai aka ce na kawo ki saka hannu""" """To ba zan ba"" ta ce a taƙaice. ""Maa ya zama dole fa""" A hankali ta ɗago idanunta sai kuma ta cire glasses ɗin idanunta manyan fararen idanunta tas a kan shi "ya yi saurin ɗauke nasa idanun saboda kwarjin da ta yi masa ""Ni ce Manager, ka faɗawa duk wanda ya" "turo ka cewa ba zan ba, ina buƙatar explanation me aka siyar a kamfanina nan har aka samu shigowar" "kuɗi kimanin 5.1B cikin awa guda, ba details na abin da aka siya sai file na zuwan kuɗin kuma yanzu ana buƙatar fitar dasu daka account ɗin kamfani? This is complicated"" zai yi magana cikin tsawa ta ce ""Out of my office accouter"" cikin saurin ya miƙe tsaye yana ficewa daga officer ɗin. Numfashi Fiyya ta sauke ta rufe idanunta da sauri kuma ta buɗe jin an shigo ba tare data bada umarnin a shigo mata officer ba." Cikin sauri ta miƙe tsaye tana ɗan ja baya ta shiga ƙare masa kallo daga sama har ƙasa ta yi mamaki to babu security a ƙofar office ɗin nata ne? Da ƙyar ta ja numfashi tana saukewa ta ce. """Who are you? Waye kai." For more information 08164069385 "WhatsApp only.[10/6, 9:07 AM] Nanameera: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 4 Nimcyluv *Bright pens. Second batch* Ƙarewa office ɗin kallo ya yi yana buɗe idanunsa akan Fiyya wacce ta ɗan ja da baya tana ɗauke kanta "gefe. ""Ya Allah i really missed her, Safiyya A. Marafa"" ya furta yana kallon makaken photon Fiyya dake cikin office ɗin kafin ya ƙarasa ciki murya a hankali ya ce" """Wa kike tunanin zai zo banda mijinki Fiyya? You're enjoying teasing me"" sai a lokacin ta sauke ajjiyar" "zuciya a ɓoye tare da ɗan yin murmushi mai kyau wanda ya saka shi lumshe idanunsa ya buɗe ""Like this. I missed you completely Fiyya ba shiri na dawo gida fa""" """Ina yini ya hanya?"" Ashraf na kallon files ɗin gabanta ya ce ""Allahamdulilah. Ya naki aikin Manager?"" Ta" "ce ""Lafiya, me ka zo yi a kamfanin ko kana da business damu ne?""" """Eh, babban business ma"" tana kallon system ba yabo babu fallasa ta ce ""Ohh"" kallon ta ya dinga yi" "yadda take operating system ɗin cike da nutsuwa fuskarta a kame ba wargi hakan bai hana kyan fuskarta bayyana ba ya ja numfashi ya sauke yana jin wani abu sosai na fuskarsa a kan Fiyya ya kalli agogon hannunsa ya ce ""Ko gida ban je ba, ina son na samu nutsuwa da kallon fuskarki dear"" kamar baza ta ce komai ba sai kuma ta ce ""Ok"" mamakin halinta na ko ina kula yana damunsa cikin damuwa yana sassauta" "murya ya ce ""Fiyya"" ta ɗago ta kalle shi sai kuma ta zame idanunta." """Na kasa fahimtar me kike nufi dani Fiyya anya kina so na kamar yadda nima nake son ki? I told you na" "dawo saboda ke amma ki ce mini wani ok? To hell with the ok ɗin na tsani irin wannan ɗabi'un naki, da na yi miki uzurin rashin sabo ne amma for good 5years muna abu ɗaya dake? Idan customers ne kya musu fara'a ki yi welcoming nasu, amma ni da zan zama mijinki kwana kwana nan kike ma haka, ko wanne gardi ya zo office naki kin zama wata kamar jerry abar kallon kowa"" ya girgiza kai cikin damuwa" da ƙunci yana zare gilas ɗin idanunsa tare da buga table ɗin gabanta ya ce """A cikin abu biyu dole ne a yi guda""" Kallon Ashraf kawai take ta tabbatar yana da anger issues tama rasa me za ta ce masa don takaici ya zo "har office ɗin ta kuma yana yi mata hayaniya, yana ƙoƙarin tara mata jama'a. Ko motsi ba ta yi ba, tana" "juya kujerar da take kai a hankali idanunta zube a kansa. ""Ina ji Ashraf"" bata taɓa kiran sunansa ba sai" yau hakan ya saka ya kalleta da sauri ransa ya ƙara ɓaci. """Aure ko aiki, ya zama dole ki zaɓi guda ɗaya a ciki""" """Ok"" ta sake cewa tana miƙewa tsaye tare da ɗaukar jakarta da wayarta da makullin mota ta zaga a" hankali zata shige shi ya yi saurin saka hannu ya riƙo nata hannun cikin sauri ta kalle shi tare da jefa masa wata iriyar harara sakinta ya yi ya matsa dab da ita yana sauke mata hucin numfashin ɓacin ransa dake fitowa tun daga ƙasan zuciyarsa. """Ki bani amsar abin da na buƙata kafin ki fita, aikin ki ko aure""" Ta taune leɓenta tana ware masa manyan idanunta sai kuma ta kalli wayarta tare da buɗewa ta shiga "wajan photos pictures ɗinsa ta nemo wanda ya yi kyau sosai ya saka ƙananun kaya lokacin bashi da lafiya ta je duba shi ya fito harabar gidan tana murmushi ta ce ""My patient, bari na ɗauki photo as evidence karka mutu bani photon nunawa yarana masoyin da ya tafi ya bar Fiyya"" a lokacin juyawa ya yi ya kalleta daga kwancan da yake ya wurga mata harara sai kuma ya miƙe tsaye yana nufar inda take ta yi saurin yin" baya tana masa wani irin murmushi ya tsaya yana kallon ta sai kuma ya ce """To make you clear, ba ki da wasu yara sai na Ashraf, ba ki da wani miji sai Ashraf ba wanda za ki yi wa" "takaba sai Ashraf. Ashraf na Fiyya ne Fiyya kuma ta Ashraf ce in sha Allah"" murmushi kawai ta yi bata" ce komai ba ta ɗauke shi photon yana langwaɓe kai gefe. Fiyya ta shafa screen ɗin wayarta tana kallon photon kamar yanzu ta ɗauka cikin muryar mara hayaniya "idan tasu ta ce ""Ya ce wai na zaɓa aiki ko shi, kar ya buƙaci jin amsar daga bakin Fiyya"" fisge wayar ya yi ""Dole ki bani amsa yanzu ba sai anjima ba"" ta gyara tsaiwa tana fuskantar shi da kyau a hankali ta matsa dab da shi ta ce ""Allah Ya baka wacce ta fi Fiyya"" Ashraf ya yi sak can ya ce ""Me kike nufi?""" """Ina nufin na haƙura da auren, na zaɓi aikin"" tana kaiwa nan ta fisge wayarta cikin sauri ta yi waje ya bita" "da kallo zuciyarsa na ta fasa. Tana fita ta kalli security ta ce ""Idan ya fito a rufe mini office"" waje ta yi ko Elevator bata tsaya shiga ba ta sakko ta bene dake a wajan 5 floor office ɗin nata yake. Sai gaisheta ake yi amma ba wanda ta saurara idanunta har dishi-dishi yake saboda ɓacin rai." Misalin 1:43 dare ya nutsa ana samawa zuciya nutsuwa ya yinda kowa yake bacci a lokacin ne safiyarsa "ta waye. Ya tsaya a ƙofar gidan yana kallon gate sosai ya jima a wajan kafin ya juya ya kalli Goge da Darma cikin hanzari Goje ya shiga buga gate ɗin gidan kamar zai cire shi, sun jima kafin daga bakin ƙofar suji an ce ""Waye?"" ""Buɗe"" Goje ya ce yana zare wuƙa tare da matsawa jikin ƙofar mai gadin a ruɗe yake" "sosai ya ce ""Kamarya na buɗe a wannan zamanin da muke cikin insecurity na sani ma ko ƴan fashi ne?""" """Sune"" Darma ya ce yana yin muzurai shi kaɗai ne a cikin su yake a buge shi Moh abin da Mangal ya" "bashi har yanzu bai gama sakin shi ba, shi ya sa ba komai yake ganewa ba. ""Wallahi ba zan buɗe ba, babu mamaki kun ji Alhaji Wada ya dawo gari shine za ku yi masa fashi""" """Ko ka buɗe gidan nan na rantse da Ɗan Amina na shigo sai na yi maka ɓalli-ɓalli"" ai kowa mai gadin ya" "ce ""Ka yi mini ɗari-ɗari ma amma babu abin da zai saka na buɗe daman ƙasa babu lafiya ga yaron can daya dawo abin tsoro ana ta surutu a unguwa ya kashe matarsa kuma ya shigo cikin al'umma zai lalata jama'a..."" Kafin ya ƙarasa faɗa Moh ya saka ƙafa ya daki ƙaramar ƙofar nan take ta ɓalle ya faɗa cikin gidan, da sauri mai gadi ya ja baya ba wani sanin Moh ya yi ba kawai zancen ya dawo kunnensa da labarin kisan daya game ko'ina a shekaru uku da suka shige. Goje ya daƙo mai gadin ya falle shi ya faɗi" """Kai har ana cewa ka buɗe ƙofa kana ƙi?""" """Goje""" """Sai godiya"" Moh ya numfasa yana durƙosawa daidai fuskar mai gadin ""Me ya ce a yi masa?"" ""Sai godiya" "ɗari-ɗari ya ce yana buƙatar tsini"" ihu mai gadin ya saka ya ce ""Wallahi tallahi ƙarya nake""" """Zaɓi ɗaya"" cewar Moh yana fito da askira ya ajjiye gefe ya sake fito da wata wuƙar ya ajjiye ya jima a" "duƙe kamar mai tunani sai ya ce ""Ko ɓalli-ɓalli ko ƴan uku ko na jaki""" """Ɓalli-ɓalli"" mai gadin ya ce da sauri ya ɗauka wani abun za a ɓalle da idanu ya kalli Goje da Darma suka" "riƙe mai gadin tare da juya shi yana ihu da komai Moh ya ɗauki ankarar ya dinga tsaga masa a baya jini na fitowa shi kansa zuciyarsa ce kawai ke ingiza shi ya yi hakan kuma daidai gani yake yanzu daidai yake da tsarar kowanne mutum haka ƙwaƙwalwarsa ke karantar da zuciyarsa. Tun mai gadin na kuka har ya yi laƙwas sai nishi yake fitarwa, suka yar da shi a wajan cike da tafiyar taƙama yana taku ɗaiɗai jikinsa na buɗewa cikakken namiji a tsaye matashi dake kan lokacinsa. Cikin sa'a ya samu ƙofar shiga babban parlon gidan a buɗe ya kutsa kai yana kallon tangamemen parlon ya dinga kallon komai, iya haɗuwa ya haɗu sai ƙarar a.c ya lumshe idanunsa ya buɗe ya jima kafin ya ƙara shiga cikin ɗaya parlon su Goje na" biye dashi. Alhaji Wada na zaune shi da iyalansa basu da jima da sauka daga ƙasar ba. Yana saman kujera matarsa "na gefe sai yaransa guda biyu mace da namiji kayan ciye-ciye fal a gabansu bama su damu da cin abincin ba sai ice-cream dake hannunsu suna sha. Da sauri Alhaji Wada ya miƙe tsaye yana kallon matasan da suka shigo ya juya ya kalli matarsa da yaran ya ce ""Su waye ku? Me kuka zo yi mini a gidana a irin" "wannan lokacin?""" Moh bai ce komai ya zaga ya zauna saman kujera ya jingina ya ɗora ƙafarsa a saman table ɗin yana kallon abincin Goje da Darma na tsaye sai muzurai suke yi cikin sauri Alhaji Wada ya ɗauki wayarsa zai "kira ƴan'sanda ""Ba wani abu da zai bani tsoro, yadda aka fara dakai dole a ƙare da kai Alhaji Wada""" """Waye kai? Me aka fara dani"" fuskar Moh a rufe ya saka hannu ya zame abin da ya rufe fuskar da shi" """Idan maye ya ci ya manta ai uwa ba zata manta ba, idan kare na yawo zabo na yawo za a haɗe ya ranar""" "ƙirjin Alhaji Wada ya buga ya yi baya da sauri ya ce ""Kai ne? Me na yi maka""" """Ba labari na zo baka ba, ba fansa na zo ɗauka ba na zo ka ganni kasan ina raye ina numfashi ka san cewa" "na cika ɗan babata Ammo Mai dawa nake sarki mai jeji, na gode Ɗan Amina da ka zama kai ne silar da ya saka na gano wasu abubuwan"" Alhaji Wada jikinsa rawa kawai yake ya ce ""Don Allah kar ka yi mini komai kar ka taɓa yarana basu san abin da ya faru ba"" ""Idan zan yi mana jira, idan na yi sai ta ɓaci. Ina je store ɗin gidan nan?"" Da hannu Alhaji Wada ya nuna masa hanya ita kam matar ta kasa motsi saboda tashin hankali bata taɓa ganin fuska mai ban tsoro irin wannan ba, yaran sai takurewa waje guda suke yi ko haɗa idanu da Moh basa son yi"" ganin har lokacin Moh bai tashi ba ya saka Alhaji Wada cewa ""kar ka ce zaka mini komai"" shi dai Moh kallon Alhaji Wada kawai yake zuciyarsa na tuna masa irin zaluncin da ya yi masa da hannu ya nuna masa yaran cikin kakkausar murya ya ce ""Ko dan waɗan nan, ba zan so su zama abin da na zama ba"" ya juya ya kalli Goje ya yi masa fito da inkiya suka nufi store ɗin kayan abinci kamar hauka haka suka dinga fito da buhun shinkafa katon na taliya da maroni su magi da galan na mai suka" jide waje guda. "Yana bada faɗi ya miƙe tsaye ya nuna kayan abincin ""Ka raba a masallaci ka haɗawa mutane da haushin" "kare guda goma-goma, ka kai har gidanmu"" Ya juya zai fita sai ya tsaya ya saka hannu a aljihu ya zaro kunama ƙatuwa baƙa ƙirin da ita ta ɗaga ƙari sama ya damƙi hannun Alhaji Wada ba tare da yaran sun gani ba, ya cilla kunamar ciki ya damƙe hannun. Azaɓa ta saka Alhaji Wada zubar da hawaye zufa na yanko masa sosai da sosai a hankali cikin ƙasa da murya ya ce ""Ka kira cinnaku ƴan'sanda kenan ka faɗa musu an yi maka fashi, idan sun tambayi waye karka yadda ka ce Mai dawa, ka ce SCORPIO"" yana kaiwa" "nan ya kashe kunamar ya soke jikin bango da sauri ya fice kamar walƙiya, su Goje suka mara masa baya." "Fiyya na durƙushe a gabansa kanta a ƙasa ji take dama tana da ƙarfin yin kuka a yanzu, ta kasa fahimtar" sai yaushe ne komai zai daidaita ya tafi daidai? Tana haɗiye abubuwa da dama ba tare da kowa ya sani ba bata bari a san rauninta amma yau ita aka saka gaba akan abin da sam bai kai ya kawo ba? Ita zaiwa haka?. """Safiyyerh A. Marafa""" Ya kira sunanta a karo na uku sai a lokacin ta ɗago kai ta kalli Daddy dake zaune saman kujera hannunsa riƙe da carɓi fuska ba wasa ya lura sai ya dage sosai akan Safiyyerh. """Ya kuka yi da Ashraf me neman auren ki?"" A hankali ta ce ""Ba komai Daddy""" """Ba komai Daddy, na gaji da jin wannan daga bakin ki Safiyyerh ke kina nuna mini ke mai wayo ce kuma" "kin girma kin isa ki yi handling dukkan wasu matsalolinki ko? Ke jaruma mai experience akan aikinta Managern FS WORLD INVESTMENT COMPANY? na yarda kina da wayo tunda na kasa sanin damuwarki tsayin shekaru na yarda kina da experience hakan ya sa cikin ƙaramin lokaci kika zama Manager but amma.."" ya yi shiru yana kallon ta sai kuma ya ce" """Safiyyerh kina buƙatar aure shine cika da ƙimar kowacce mace, me kike buƙata a rayuwa da ba a yi miki" "ba, wanne gata ban yi miki ba da kika ce kin fasa auren Ashraf?""" """Daddy ya ce na zaɓi aiki ko aure""" """Sai kika zaɓi me?""" """Aiki"" Daddy ya dinga kallon ƴar tasa shi ya rasa gane wani mataki zai ɗauka a kanta." """Ba za ki yi auren ba kenan, baƙin cikin jikoki kike mimi Maama? Sai na faɗi na mutu za ki yi auren me ya" "sa kika kasance stubborn ne, ko don kinga ina biye miki?"" Fashewa ta yi da kuka sosai ita kanta bata san" "kukan ya ƙwace ba, kalmar mutuwar da Daddy ya faɗa ya firgitar da ita sosai idan Daddy ya mutu ta shiga uku." """Daddy gasu Yaya J, su Marafa, su Captain Daddy me ya sa sai ni za a yi aure ne? Ni ce ƙarama fa nawa" nake gabaɗaya ko aure za ka mini ka ƙara mini lokaci Ashraf zafin zuciya ne dashi baya fahimta ta a "kodayaushe""" """Maama kuma taurin kai, ji da kai while zafin zuciya, Safiyyerh dole za ki yi aure"" runtse idanunta sosai" kenan duk abin da take ya tashi a banza? Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un me ya sa Ashraf zai yi mata haka me ya sa zai haɗata da mahaifinta? Ta kasa cigaba da kukan abu ya tsaya mata a wuya sosai. Har Daddy ya je bakin ƙofar shiga sashinsa ya tsaya ba tare daya juya ba ya ce """Cikin satin nan zan ɗaura miki aure da Ashraf in sha Allah""" "Dum! Haka ta ji zuciyarta ta buga da ƙarfi har tsakiyar kanta kuma ta ji hakan, ta runtse idanunta sosai" "take ƙoƙarin jan numfashi ta kasa ta yi saurin riƙe wuyanta da take jin kamar an soka mata abu a ciki saboda zafin da yake. Cikin sauri J ya ƙarasu parlon daman ya shigo da nufin yiwa Daddy sai da safe ya nufeta yana riƙo hannunta ya ce ""Manager lafiya? Mene?"" Kafin ta bashi amsa Marafa shima ya shigo ya nufe ta, haka Dr Hash gabaɗaya suka zagaye ta suna tambayarta lafiya kasancewar suna mugun son ƙanwar tasu kamar rai. Hannun J ta riƙe gam tana nishi hawaye na zubu mata sosai ta kasa magana hakan ya saka Dr Hash miƙewa ya ɗakko ruwa mai sanyi ya yiwa J alamar ya ɗago ta, a hankali ya dinga" bata ruwan tana sha ya zame rubar ruwan. """Junaid kwantar da ita saman kujera ko ka kai ta ɗaki""" """Bari ta ƙara jin dama dama a dai ƙaro gudun acn ta fi shaƙar iska da kyau"" cikin sauri Marafa ya nufi" wajan ƙaro a.c a hankali suka ji an ce """Kar ka ƙaro"" ya juya ya kalli Captain dake zaune kan kujera abin shi yana dannawa, yana zaune Daddy" "ya kira Fiyya duk maganganun da sukai yana zaune har halin data shiga. ""Captain daman kana ciki kana kallo Maama ba lafiya?""" """Ni na ɗora mata?""" """Amma baka ce mata sannu ba, she's our little sis our favourite"" kallon da Captain ya yi wa Marafa ya" "saka dole ya yi shiru dukkan su ba wanda ya iya cewa Captain komai domin sun san hali basa shiri da Fiyya bai shiga sabgarta ba, duk abin da ya shafe ta babu ruwansa da shi. Ko magana bai fiya yi ba ana" ganinsa kowa ke nutsuwa domin shine babba a cikin su Fiyya kuma Auta. Fiyya ta yi lamo jikin J tana sauke numfashi Dr Hash na riƙe da hannunta jin jikinta ya fara ɗaukan zafi sosai. Da ƙyar ta lallaɓa J na riƙe da ita suka haura sama duka sauran mazan suka bi bayansu banda Captain da yake harkar gabansa. Wajejen 2:30 Daddy ya sauke numfashi yana kallon yadda take sauke numfashi a hankali ko a baccin "bata da walwala ya juya ya kalli Captain dake tsaye hannunsa zube cikin aljihu ""Aliyu me na ragi Maama da shi a duniya dana kasa fahimtar meke damunta? Ita ɗaya ce mace ƴata laifi ne don na so ta yi aure?""" Captain dai ya yi shiru idanunsa a saman fuskar Fiyya Daddy ya miƙa hannu ya taɓa goshinta ya ji har "lokacin da zafi daman ya fi ƙarfin awa guda zaune a wajan, yana cikin Captain ya buɗe ƙofa ya shigo da" "tunanin babu kowa cikin ganin Daddy ya saka dole ya tsaya. ""Maama ki yi mini alfama ki yi auren nan, shi" "ne abin da za ki yi ki faranta rai na"" ya gyara mata hannunta daya lanƙwashe kana ya miƙe tsaye zai fita" """Aliyu mu je""" """After you daddy""" Daddy ya jinjina kai ya fita yana janyo ƙofar. A hankali Captain ya nemi waje ya zauna a gefen gadon ya "zuba mata idanu sosai, a nutse a kamo hannunta ya riƙe cikin nasa jin jikinta zafi sosai ya saka ya saki hannun ya ɗakko towel da ruwa ya dinga goga mata a goshi har lokacin yana riƙe da hannunta har sai da zafin ya ragu, bai tashi ba yana zaune aka fara kiran sallar farko cikin sauri saki hannunta ya miƙe tsaye yana haɗe fuska J ne ya shigo a hankali ya bi Captain da idanu har ya fice daga cikin bedroom ɗin na" Fiyya. ***** Cikin gidan ya faɗo babu ko sallama Inna Binta na zaune har za ta yi magana ganinsa tsaye ya saka ta yi shiru da bakinta. Yau ranta fari tas an yi musu rabon abinci Malam ya basu ya ɓoye sauran. Ɗakin Ammo ya nufa yana ɗaga labulan ɗakin ya ganta zaune tana ɗaura kuɓewa tun kan ya shigo jikinta ya bata yana hanya saboda gabanta daya tsananta faɗuwa. "Ya shiga ɗakin ya zauna ita dai bata kalle shi ba, sai kallon ta ya ke yi can ƙasa da murya kamar ba shi ba" "ya ce ""Ina yini Ammo?""" "Miƙewa ta yi maimakon ta amsa masa, ya cije bakinsa yana rufe idanu kwanon abinci ya jenyo ya buɗe" yaga taliya ce jallof ta ji albasa nan da nan yawunsa ya tsinke ya tuna rabon shi da abinci har ya manta. """Alhaji Wada ya bawa Malam, idan da zuciya ai ba za ka ci abincin daya bamu ba"" cak ya tsaya yana" "kallon abincin kamar zai tashi sai kuma ya nutsa hannunsa ciki ya ɗebo lauma zai kai bakinsa cikin sauri aka ce ""Allah Ya isa ban baka ba ida ka ci abincin nan"" Malam ya kalli Ammo ya ce" """Bana ce kar ki yarda ya shigo gidan nan ba? Wato har abinci kika bashi ko?"" Ta girgiza kai ta ce ""Ɗauka" "ya yi""" Jiki a sanyaye Moh ya miƙe ya fice daga cikin ɗakin yana saka ƙafa ya banko ƙofar da ƙarfin gaske yana "zuwa daidai inda Inna Binta ke gyara shinkafa ya saka ƙafa ya yi fatali da farantin shinkafar ta tarwatse ya yi waje kamar zai tashi sama. Ta dafe ƙirji tana rafka salati ""Ƴar gwamnati ce fa Allah ya isa wallahi""." "Goje ya dubu Mangal ya ce ""Me ka bashi wai? Yake wannan sambatu da mimmiƙar haka?""" """Sha fara kaga aljan ce, ita za ta yi aiki a jikinsa, daga sama aka bani ita"" Goje ya juya ya kalli Mai dawa" "ya sauke numfashi cikin damuwa ya ce ""Dole sai ka koya masa shan waɗannan abubuwan ne?""" """A'a ina zaune ya zo mini kamar an koro shi yana huci ya ce na bashi irin abin da na bashi kwanaki" "saboda damuwar zuciyarsa ta kau ya manta da komai ni kuma na bashi sha fara kaga aljan""" """To gashi nan yana ganin aljanin ai"" da ƙyar ya samu ya yi bacci a wajan. Bayan ya farka Mangal ya bashi" "abinci ya girgiza kai ""Mai dawa idan kuɗi kake so ina da hanyar da zan yi maka ka dinga samun kuɗi sosai cikin sauƙi har ma ka taimaki wasu"" tunda ya farka sai lokacin ya ɗaga kai ya kalli Mangal alamar ina ne? ""Bangar siyasa kasan yanzu muna gab da fara shiga sabgogin siyasa uban gidana cikakken ɗan siyasa ne," "shima yana da uban gida kuɗi zaka samu sosai a sabgar nan ina faɗa maka""" """Kai ni"" kawai ya iya cewa yana miƙewa tsaye." Suna zaune a wani haɗaɗɗan parlo inda suke karɓe wa su yi meeting na sirri. Gabaɗaya suka kalli MUTALLAB TAHHB SCORPIO ɗaya daga cikin su ne ya ce. """Mene sunanka""" """Mai dawa""" """Kai mafarauci ne?"" Ba tare daya kalli mutumin ba ya ce ""Darr"" babban mutumin ya jinjina kai sosai ya" "zaro wani photo a aljihu ya ce ""Kafin mu yi maka bayanin su waye mu, me muke buƙata da kai, fara ganin wannan ka saka dai a ranka mu ƴan siyasa ne""" "Shi dai Mai dawa bai ce komai ba, aka ajjiye masa photon a gabansa ""Ɗauki ka buɗe ka gani mana""" "Wani daga cikin mutanen ya ce ""Manager ce a FS WORLD INVESTMENT COMPANY aiki za ka yi mana a" "kanta kafin mu faɗa maka aikin mene ka fara ɗaukan photon kaga wacece"" a sanyaye ya ɗauki photon kafin ya kai idanunsa kai...." 08164069385 For more information WhatsApp only "[10/8, 7:59 AM] null: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 5 """Safiyyerh Abdu Marafa Manager ce a Kamfanin FS WORLD INVESTMENT COMPANY kuma ƴa a wajan" "tsohon leccara, muna buƙatar ka yi mana kidnaping ɗin ta"" Moh Kallo ɗaya ya yi wa photon da suka bashi ya ɗauke kai" """Ka santa?"" Shi dai bai ce komai ba." "Eng Ali wali ya dinga kallon Moh yana tunanin abubuwa da yawa a ransa kafin ya ce ""baka gama ganin" "photon bane, ko da yake yana da kyau da ƙare mata kallo maybe ka zama silar mutuwar ta ko ka kashe" "ta da hannunka, ka ya zama dole ka gane kamamminta""" "Goje ne ya ɗago kai da sauri yana kallon Eng Ali wali kafin ""Sai da kai mai gida wannan aikin ai ko ni zan" "iya yin shi ba sai Mai dawa ba, ka huta ka sarara mai gida""" Eng Ali wali ya yi murmushi yana jingina da kujera ya ɗauki ƙafarsa ya ɗora akan ɗaya ya kalli Mai dawa "wanda ko motsi bai yi ba sai jujjuya photon da aka bashi yake. ""Ko Mangal ba zai iya aikin nan ba da ya fika wayo a sabgar balle kai da na sani yanzu, shi wannan Mai dawan idanunsa na kalla na san zuciyarsa za ta iya aikata komai""" "Ya yi shiru sai kuma ya ce ""Ni ɗan siyasa ne babu mamaki ka taɓa ganin poster na ko bana, shekaruna" "takwas ina riƙe muƙamin Ɗan majalisa na tarayya a jam'iyyar da nake ta kara, bani da ra'ayin haƙura da kujerata kamar yadda ake yi mini kirarin idan na yi na gama na karya kujerar. Siyasa jinina ce Mai dawa, bana jin akwai wani dalili da zai zo ya saka na haƙura da kujerar na amma wannan karon na yi karo da muruci wanda yake shirin yi mini wahalar dafawa ko ta halin yaya ne dole na sake hawa kujerar nan a karo na huɗu. Hon Maɗatai yana tare da manya wanda suka san kan siyasa ciki da bai dole mu fito da salo na musamman wanda zai kai su ƙasa. Hon Maɗatai shine ɗan takarar jam'iyyar hamayya kuma yana da ƙarfi har yanzu ba'a san mene rauni ko aibun shi ba amma akwai jita-jitar data zo kunne na domin" "tabbatar da gaskiyar al'amari ya saka na kawowa cikin jama'ata""" Sai a lokacin Mai dawa ya ɗago kansa ya ɗan kalli Eng Ali wali kamar ba zai ce komai ba sai ya cije baki yana karkatar da kai gefe ya haɗa hannayensa biyu suka bada sauti mai ƙara cikin wata murya ta izza ya ce """Mene haɗin ta da maganar yawar ku?""" "Eng Ali wali ya ce ""Wa kake magana""" """Ita ɗawar mai ɗan kwalin?""" "Cikin rashin fahimta Eng Ali wali ya ce ""Meye ɗawa da ɗan kwali kuma?"" Mangal ya yi murmushi yana" """Ka fice Mai gida, ɗawa da mai ɗan kwali mace kenan ake kwafa maka zancen"" Ya ce ""Yaran naku sai ku""" Miƙewa Mai dawa ya yi tsaye yana ɗora ƙafarsa a saman farar kujerar dake parlon kallonsa kawai Eng Ali "wali ya yi bai ce komai ba. Sai wani ya ce ""Mai dawa farar kujera ce fa?"" ""Ko takaddar jikinka zan ɗora ƙafa akai"" wanda ya yi maganar ya yi saurin kallon farar shaddar dake jikinsa fara tas da ita sai ya ja bakinsa ya yi shiru. Moh ya kalli gefe yana furzar da iska daga bakinsa ya ce" """Me ya sa ka neman, bayan kana da gajojinka?""" """Saboda kai ne baƙuwar fuska a cikin wannan sabgar tamu, ba wanda zai gano cewa a tsagina kake za ka" "yi aiki mai kyau hankalina ya kwanta da kai Mutallab"" wani irin kallo Mutallab ya jefa masa idanunsa sun sauya kala ya yi murmushi ya ce" """Oh Mai dawa da jeji, ya batun yarinyar ka santa ne ko ka taɓa ganin fuskarta?""" """Na santa ko ban santa ba ina jin bashi kake buƙata ba. Yaushe kake so a kawo maka ita?"" Girgiza kai Eng" "Ali wali ya yi ya ɗauki ruwa ya kurɓa ya ajjiye kana ya miƙe tsaye yana zagaye parlon hannunsa a baya ""Ka jira umarni na, kawai ka zama cikin shiri a koyaushe zaka iya jin kira. Akwai gidan dana samu a bayan gari zan baka makullin ko ka ɗakko ta can zaka ajjiyeta kai ne zaka dinga kula da ita har yanzu lokacin da muka shirya abin da mukai niya, a cikin gidan akwai kayan aiki irin naku wanda za su sama muku" "nutsuwa""" "Goje ya jinjina kai cike da jin daɗi kafin ya ce ""Mai gida za a siya mana mota mai iska kamar yadda muke" "ƴaƴan iska?""" """Za a yi muku komai, ku riƙe amana. Sai dai kawai sharaɗi ko da wasa kar ku nuna kun sanni idan ina" "buƙatar ganin ku a wannan gidan zamu dinga haɗuwa, ku buɗewa kowa idanu kar ku ji tsoro da shakkar komai ni zan tsaya muku har zuwa ci zaɓe"" Moh ya ce ""Bayan cin zaɓan fa?""" """Kamarya?""" "Ya buɗe manyan idanunsa sosai a kan Eng Ali wali a karo na farko ya ƙare masa kallo ""Mene farashin" "aikina?"" ""Nawa kake so?"" Ya yi shiru yana tunani can ya ce ""Zan sanar""" "Eng Ali wali ya ɗakko ƙatuwar bana da fastoci ya bawa Goje da yawa ya ce ""Kuje ku fara da aikin liƙawa" "wannan a unguwanni da saƙo da lungu ya zamana babu wanda ake ganin sai Eng Ali wali, bayan wannan akwai wani dattijo da yake zuwa gidan rediyo yana yi sojan baka kuma duk ni yake kushewa yana son jiƙa mini aiki a tabbatar an saka shi yin shiru da baki da kowacce hanya"" kuɗi ya ciro daga cikin Aljihu ya miƙawa Goje ya ce ""Aje a yi caji a huta"" har Moh zai juya sai kuma ya tsaya ya cake waje guda kamar" "saƙago ya ce ""Me ya sa kuke son a kamata?""" """Aiki ne kawai naka wani abu ba sai ka sani ba, mune shuwagabanni ku dai a baku kuɗi da kayan" "sararawa shine"" kai tsaye Moh ya ce ""To nemi wani"" Eng Ali wali ya ce ""Me ya sa? Bayan kai ka cancanta?""" """Ba zan ba""" """Shikenan na gane, Safiyya Abdu Marafa na faɗa maka ƴa ce wajan tsohon leccara, yana kawo mini" "barazana a sabgar siyasa tare da nuna rashin cancanta a fili. Matasa na jin maganarsa abin da ya zaɓa kuma da shi suke yin aiki a yau ɗin da muke ciki matasa sune siyasa ina so a sa shi yin mubaya'a dole. Kasan da yawan lokaci Malamai suna kawo mana cikas"" Mai dawa ya jinjina kansa alamar ya ji sai dai bai" "yi magana ba a hankali ya duƙa yana buɗe hannu ya ce ""Sai godiya""" """Sai godiya"" Mangal da Goje suka faɗa suna zagaye shi. Cikin sauri kuma ya fice daga cikin parlon suna" mara mishi baya. "Eng Ali wali ya dubi wanda ke zaune sai kuma ya yi dariya sosai ya ce ""Amfanin su kenan fa babu wani" "aiki da ɗan daba zai iya yi maka banda bangar siyasa kashe kashe da sare-sare mu kuma sai mu jefe su da abin da sukewa""" Fiyya na tsaye gaban madubu tana gyara rolling mayafin kanta yau ma suit ce a jikinta ta mata riga da "wando blue black ta amshe ta sosai ta kalli kanta a madubin she missed the old Safiyyerh komai nata sabo take jin shi, ta ji kamar ta rasa wani abu mai amfani a tattare da ita amma mene? Shi ne abin da sam ta gaza fahimta ko a cikin bacci. Ta sauke numfashi tare da ɗaukan wayarta da jakarta tana ƙoƙarin buɗe ƙofa ta fita Ummi na shigowa cikin ɗakin Fiyya ta yi baya tana bata hanya kafin ta ce ""Good morning Ummi"" daga sama har ƙasa Ummi ta kalle ta sai kuma ta je can bakin gado ta zauna tana sake" "kallon Fiyya ""Ina za ki?"" ""Ummi Company""" """Junaid told me ba ki da lafiya, na yi bacci da wuri"" a hankali ta ce ""Lafiya lou nake Ummi ga alama kin" "gani zani aiki""" """Fiyya bana son irin wannan shigar taki, kuma ki haƙura da aikin nan yau za a kawo kayan auren ki"" da" "sauri ta ce ""Aure kuma Ummi? Ba sai nan da watanni ba?""" """To Daddynku ya ce cikin satin nan""" """Shikenan zan je aiki""" """A'a ki haƙura yau"" marairai ce fuska ta yi sosai kamar za ta yi kuka ta ce ""Ummi akwai buƙatar na je, ina" "da meeting da ma'aikata ba zan jima ba"" Ummi bata san damuwar Fiyya dole a hankali ta ce ""Allah Ya tsare ki dinga kula ke dai macace ba namiji ba, kina lura da abubuwa da kike yi"" Fiyya ta yi dariya tana yin waje ta ce ""Kuma ki saka tsoron Allah a ran ki Fiyya ban da wulaƙanta jama'a, al'umma ta Annabi ce""" "Ummi ta girgiza kai kawai ta ce ""Wato kin haddace kenan""" """Dole na Ummi""" "Cak ta tsaya tana riƙe kan ta Ummi ta ce ""Subuhanallahi Fiyya kina lafiya? Ba za ki haƙura da zuwa aikin" "nan ba?"" Ta ɗan ya tsuna fuska da nuna alamar ba komai ta ce ""Kawai na ji kaina kamar an saka mini shocking"" gaban Ummi ya faɗi sosai sai bata nuna ba ta kama hannun Fiyya suka sakko ƙasa." "Dr Hash ne ya fito shima sanye da farar riga ta likitoci Fiyya na kallonta ta ce ""Likita bokan ture, kuma" "fiɗe ku ɗinke""" """Kamar wasu mahauta"" ta yi murmushinta mai kyau tana lumshe idanu ""Barka da safiya Dr"" ya yi mata" "murmushi ""The whole Manager in the world"" Ta buɗe ido shima ya buɗe kafin su ce komai J ya fito shima yana cewa ""In the world mana, wannan kamfanin nan ku ina ne basu da reshe ni dai watarana zan zauna ki bani labarin kamfanin sosai na ji ai na yin wanda yake da shi"" ""Kai Yaya J nima ban san ko na" "waye"" ya buɗe ido ya ce ""Ban gane ba?""" """Da gaske nake Yaya ban san asalin me shi ba, kawai dai na san ni Manager ce""" """Ji nake Ashraf's father is the owner of the company""" "Ta tura baki gama tana harar shi ""Kuma ka sani kake tambayata"" ya ɗaga mata gira ya ce ""Zan zo ki nema" "mini alfarma wajan surukin naki nima ya bani ko messenger ne"" bata kula shi ba. Ɗago kai ta yi suka" "haɗa idanu da shi yana zaune ya watsa mata harara yana ɗauke kan shi gefe ""Aliyu ba yau zaka tafi bane"" ya yi shiru a hankali kuma ba tare daya ɗago kai ba ya ce ""A'a""" """Ok na ɗauka yau ne, ni wallahi duk firgitar dani kake mutum ba walwala kamar a filin yaƙi nan fa gida ne," "amma kodayaushe kamar an yi maka dariya ko yaya ne ka dinga murmushi""" """Ban iya ba Ummi""" """Murmushin ne baka iya ba Aliyu? Ka gwada zaka iya"" ya miƙe tsaye yana yin waje ""Ban san yadda zan" "ba"" ""Ina kwana Captain?"" Fiyya ta faɗa tana haɗe fuska ko inda take bai kalla ba ya yi waje abin shi. Shi dai J murmushi kawai yake yi halin Captain na bashi malam sosai suka jera shi da Fiyya suka fita. Mota ta shiga yana ɗaga mata hannu shima ya shiga tasa motar kowa ya kama hanyar wajan aikin shi. Fiyya na driving a nutse ta hangi wata mota na bin duk inda ta yi sai ta taɓe fuska ko a jikinta a fili ta ce ""Ɗan" "wahala ko waye""" "Daddy dake zaune bayan shigowar Ummi cikin parlon sama ya kalleta ya ce ""Me kike cewa Ummi?"" Ta" "damuwa ta ce ""Kwana biyu ba a amshi maganin Fiyya ba, kuma kamar ciwon zai tashi"" ya ajjiye littafin hannunsu yana saka glasses ya ce ""Wani abin ya faru?"" Ta numfasa yana faɗin ""Irin abin da ya faru kwana ki tana jin kamar ana mata shocking a kanta, ni wallahi bana son ma ta dawo daidai bana fatan ubangiji ya ƙara gwada mini tashin hankali dana gani shekarun baya"" Daddy ya jinjina kai ""Nima addu'ar da nake a raina shi ya sa ma na matsu kawai a yi ai maganar auren nan, wallahi bana son Maama ta" "dawo old Safiyyerh""" """In sha Allah hakan ba zai kasance ba""" Meeting hall ɗin ya yi shiru sai muryarta dake tashi cikin faɗa tana ɗan buɗe hannayenta tare da yin "baya ta ce ""Wanne irin rainin wayo da hankali ne, file ɗin dana ajjiye shi a office ɗina ina jiran a kawo mini proof hujjar abin da aka fitar aka samu shigowar kuɗi zuwa asusun kamfani kamar yadda Accounter ya faɗa mini shine za a ce wai na yi signature a file aljana ce ni da zan taso da gida na zo kamfani na saka hannu, idan zan saka me ya sa ban yi ba tun da file ɗin ya zo table ɗina?"" Ta miƙe tsaye tana kallon su gabaɗaya duka maza ne ita kaɗai ce mace ta koma ta zauna tana juyi a kan kujerar ""I need to find out the truth, meke faruwa a wannan kanfanin. Md da kai da secretary za ku kai ni na duba ko'ina a wannan kamfanin yau ɗin nan, kai kuma Director ka kawo mini record ɗin komai daga watan daya shige zuwa yau ɗin nan, ina buƙatar statement yanzu a office nawa"" ta sauke numfashi fuska a haɗe sosai ""An" "gama"" secretary ne ya kalleta kamar a tsora ce yake ya ce ""Manager akwai baƙi da suke jiran ki""" File ta ɗauka ta miƙe tare da ficewa daga cikin meeting hall ɗin. Bata nufi office ɗin ta ba inda suke "ganawa da baƙi ta nufa ta tura office ɗin a hankali a hankali ta yi sallama ta shiga. Manyan mutane ta gani su biyu zaune a kan kujera kana ganin su ba sai an yi magana ba ta zauna kan kujera mai cin mutum biyu a ladabce ta ce ""Ina kwanan ku? Welcome to FS WORLD INVESTMENT COMPANY i am Safiyya A. Marafa how can i help you?"" Wani rushehen mutum ne daya Hakim ce a kan kujera ya dinga kallon ta kamar zai haɗiye ta idanunta dai na kan system tana ta dannawa da aikin tura saƙo can ta ɗago kai suka" "haɗa idanu ta sake kame fuska ta ce ""How can I you? Ta ya ya zan iya taimaka muku""" """Ba ki gane ni ba""" "Sarai ta gane ko waye ta ce ""Yau na taɓa ganinka""" """To ma sha Allah. Sunana Hon Maɗatai zan saka hannun jari ne a cikin wannan Company""" """Ok, me kake buƙata?""" "Ya gyara zama sosai ya ce ""Za a dinga bani shinkafa, suger, wake a kan farashin yadda Company yake" "siyarwa ni kuma zan ɗora kaso 50 domin cin riba amma daga lokacin Company ba zai sake siyarwa da kowa kaya ba sai ni"" Fiyya ta dinga kallon shi sosai a ranta tana mamakin son zuciyar wasu ya suke so talakawa su yi da ran su ne? Burin shuwagabanni talaka ya faɗi ya mutu saboda yunwa? Ta yi jim sai" kuma ta ce """Da wata ce matsayin Manager ba Safiyya A. Marafa ba do wataƙila ka samu wannan damar a yanzu ina" "maka murna da cewar we're not interesting anymore, da wannan zai fi kyau ka buɗe naka masana'antar ka nemi matasa marasa aikin yi wanda suke lalacewa ka basu abin yi"" ya dinga kallon ta can ya ce ""Kin" "san waye ni? Ƴan'mata ki bi a hankali fa""" """Ai ba a yi wa Fiyya maimaici Hon Maɗatai ba zamu baka hannun jari ba You can leave"" ya miƙe tsaye" "yana jin ba'a taɓa yi masa wulaƙancin da yarinyar ta yi masa ba ""Safiyyerh ko? Ki bi a hankali haɗuwar farko ce wannan, zan tafi amma zan dawo""" Ficewa ya yi rai ɓace zuciyarsa na zafi. Fiyya ta ɗauki kayanta ta nufi office. A hankali take bin bayan Md "da Secretary ɓangaren kayan abinci aka kaita kana da mai daga can baya wajan shara inda ake ajjiye bukar kamfanin ta dinga jiyo wari da sauri ta nufi wajan Md ya ce ""Manager sharar kamfani ce nan"" bata kula shi ta nufi wajan sharar tana rufe hanci da f facemask kamar an ce ta juya idanunta ya sauka akan" yatsun hannu guda huɗu da suke a leda ƙuda na bin su. Tunda ya nufu layin su tiger na biye masa baya hannunsa riƙe da gora yara suke watsewa sai waje ake "bashi hatta almajirin Malam sai da wasu suka bar wajan banda Ɗanyaro dake zaune yana danna sabuwar wayar daya siya sosai Malam yake ji da shi yanzu lokaci zuwa lokaci yake yi malam alheri na kuɗi ga nama da yake kawo masa, sai dai cikin dare Ɗanyaro zai lallaɓa ya gudu ba zai dawo ba sai safiya. Moh na ƙoƙarin shiga gidan Malam ya tare ƙofar ya ce ""Na haifi yaro sunan shi Muɗallabi amma yanzu bani da wannan yaron na bar wa ƴan iska shi da ƴaƴan banza tunda ya zama shaiɗani ba zaka ja mini masifar da zan mutu a gidan ɗan kande ba"" Moh zuciyarsa ta fara tafasa har wani hayaƙi ke fita ta cikin bakinsa ya dinga kallon asawan nasa ya kasa cewa komai ya leƙa surar gidan ko zai ga Ammo amma sai Inna Binta" "dake suɗe tukunya tana faɗin ""Matsalata ɗaya a duniyar nan abinci idan na ci na ƙoshi Mufee ta ci ni fa" "ko a jikina"" Juyawa Moh ya yi kamar zai yafi sai kuma ya nufi saman katanga ya kama ya dire ta cikin" "gidan Inna Binta ta zabura tana faɗin ""ƙulna naru ƙulni bar dan wasalamun Allah Ibrahim, auzubillahi"" jikinta sai rawa yake masifar tsoron Mai dawa take kamar ran ta sauran jama'ar gidan duk suka shige ɗaki banda Mufee da ta yi tsaye tana kallon shi sosai idanunsu yake iri shi bai san wace ita a gidan ba, bai" damu daya sani ba yara ne kamar yaƙi wasu iyayensu basa cikin gidan. Labulan ɗakin Ammo ya ɗaga ya ganta zaune tana ninke kaya ya fi minti goma tsaye kamar zai juya sai "kuma ya shiga cikin ɗakin idanunsa akan kwanon abinci sosai yake jin yunwa idanunsa na rufewa ya miƙa hannu zai ɗauki abincin Malam ya ce ""Kana ci zan maka Allah Ya isa ka tashi ka bar mini gida tsinannen yaro"" da sauri Ammo ta kalli Malam sai kuma ta ɗauke kai." Jikin Moh ya fara rawa jijiyoyin kansa na mimmiƙewa jin uban daya kawo shi duniya na yi masa Allah Ya "isa ya yi ƙasa da kansa idanunsa kamar za su fito waje ya ji babu abin da yake buƙata sai ƙwayar da Mangal ya bashi ya sha, ita kawai zata sauke masa abin da yake ji ya manta da komai, yaushe ne zai zama daidai kamar kowanne mai rai an ci zalin shi an lalata masa rayuwa. Ya miƙe da sauri yana banko" "ƙofar ya yi waje ""Sallamammen yaro Allah dai ya rabani da ƙaddara na huta""" "Kai tsaye Moh dabarsu ya nufa yana zuwa suka mimmiƙe Darma na faɗin ""sai godiya Mai dawa sarki mai" "jeji, wani ya ce ba kai ba yanzu mu fito mu yi farfesun hanjinsa""" Yanayin fuskar Mai dawa a bar tsoro ce ya takure waje guda yana jin kamar zuciyata zata fito waje don "baƙin ciki. ""A sama yake ku bashi sha fara kaga aljan"" cewar Darma Mangal ya girgiza kai ya ce ""Ba za ta" "yi masa ba, kawai a yi masa allurar fenta""" """A'a ta yi masa girma yaushe ya faɗo sabgar kar ka luda masa ya yi mana na jakuna yanzu"" zaro sirinjin" "ya yi Moh ya ƙurawa siririn idanu ganin yadda Mangal ke zuƙo ruwan ciki ya fara girgiza kai da ƙyar ya ce ""Kar ka yi mini Ka bar ni da tunanin bana son mantawa"" kokawa suka fara yi da shi ya ɗauki Darma ya buga da ƙasa Mangal ya faki idanunsa ya caka masa allurar a gadon baya. Jinjiga ya fara sosai cikin ƙaramin lokaci ya yi shiru yana jin shi kamar a samaniya yana yawo yanayin ya yi masa daɗi sosai ya ji zuciyarsa wasai a wannan yanayin bacci ya ɗauke shi. Can cikin dare ya farka kam shi ya yi masa nauyi har yanzu bai dawo daidai ba, babu komai a cikinsa ya miƙe tsaye yana layi kamar zai faɗi Mangal ya ce" """Mai dawa""" "Ya yi masa shiru yana ɗaukar wuƙa ya soke ya ɗauki fitila ya riƙe ""Dare ya yi ba, kana fita waɗancan" "ɗankokin za su iya kama ka gashi babu da goge a hannu ka zauna, kasan kuma ƴan cikin gari sun shigo sun samu labarin mun yage musu poster bama wannan ba ɗazo an ga gawar wani to ana tunanin mu ne kuma yaron ɗan cikin garin ne fansa suka zo ɗauka,na bibiyi abun shi yaron ƙwacan abar magana ya yi" jama'a kuma sun fara ɗaukan doka a hannunsu suka rufe yaron da duka har ya mutu. Su Cokali kuma ba "za su haƙura ba kar muna zaune su ci mu da yaƙi""" """Sai godiya""" "Ya furta da ƙyar daga nan sake yin shiru yana shirin barin wajan kamar zai kifa ""Ina zaka ne? Ka dawo ka" "kwanta""" """Kai fa ba Malam zan haɗaka da Rainbow""" """Shikenan ina zaka yanzu"" ya cije leɓe zuciyarsa na ayyana masa abin da zai yi shi ne daidai allurar sai" "gaibu take faɗa masa a hankali ya ce ""Zan kashe Malam ya baza lahira""" For more information 08164069385 WhatsApp only "[10/9, 5:16 PM] Nanameera: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 6 *Bright pens... 2nd batch* * for the adults and criminal side please just take it as a lessons* "Goje daya farka daga bacci ya yi saurin miƙewa yana furta ""Malam ɗin zaka kashe mahaifin naka?"" Ya yi" "shiru bai yi magana ba, yana sake riƙe wuƙar a hannunsa da kyau duk jikinsa rawa yake, ga wani irin ciwo da kansa yake yi masa sosai, idan ya tuna abubuwan da aka aikata masa sai ya ji zuciyarsa ta bushe ta kuma ƙeƙashewa. Ya saka ƙafa ya banga je Mangal dake tsaye zai shige Goje ya yi saurin shan gabansa yana ɗaure fuska sosai ya ce ""Saboda kana jin kanka a sama ta bakwai kake jin komai za ka iya yi? Me ya sa ba zaka yarda sarki sammai ke yin komai ba, mu fa ba haihuwar ta zubar bane ko yaya ne mun san abin da ya dace kashe mahaifinka ba shi ne mafita ba Mai dawa"" ya ɗaga jajayen idanunsa kamar zai ci babu yadda ƙwaƙwalwarsa take faɗa masa ba daidai haka komai na duniyar yake yi masa babu daɗi" maƙoshinsa na yi masa zafi da raɗaɗi wani abu ya tsaya masa da ƙyar ya iya buɗe bakinsa ya ce """Ya zan yi?""" "Kai tsaye Goje ya ce ""haƙuri, ka bi komai a sannu mai dawa ita gaggawa aikin ƴan annaru ce. Kashe" "Malam a yanzu ba zai rage maka kashi goma a cikin ɗari na damuwar da kake ciki ba, iya wuya iyaye ne su""" """Ba iyaye na bane, ka bari ko ɓalli-ɓalli na yi masa"" ganin da gaske shirin tafiya ya ke yi ya ce ""Idan kaga" "ka bar wajan nan sai dai ni za ka fara kashewa"" Ya ƙuri da idanu yana kallon Goje har wani hayaƙi ke fita ta cikin bakinsa ya wani cije gefen baki yana karkatar da kai gefe. Kamar wasa Goje ya ga Moh ya nufe shi da wuƙar shima yaƙi matsawa yana ganin kamar wasa ne yana ƙoƙarin kawai Goje sara su kaga mutane kamar daga sama sun zagaye su. Moh yaƙi motsawa sai Goje da ya yi baya ya cake yana zazzaro idanu tare da ɗaga gora sama. A kallon farko Mai dawa ya gane cinnaku ne ƴan'sanda sai ya ɗauke kai" shi Goje bai faɗa da labarin ba saboda shigar fararen kaya suka yi. """Eng Ali wali ya aiko mu wajan ku kawo muku kaya"" sai a lokacin Mangal ya ƙarasu yana tale ƙafa ya ce" """Kaya sun sauka da zafin su kenan yallaɓai, amma eh kun razana mu shigowa ba notice sai mu ɗauka dire aka yi mana"" ɗan'sandan ya yi murmushi kawai ya ce ""Kuna da kamar Ali wali za ku ji tsoro? Kune matasan da yake ji daku a yanzu musamman wannan da naga ko kallo bamu ishe shi ba"" Goje ya juya ya kalli Mai dawa da yake kallon wani sashi daban alamar baya ma jin me suke cewa ""Mai dawa sarki me" "jeji wajanka aka aiko mu domin aikin bana yara bane""" """Faɗi""" Moh ya ce yana bada faɗi ba tare daya kalli da ɗan'sandan ba. Abu ya fito da shi a jaka ya miƙawa "Mangal ya amsa ya ce ""Ka a dana kada a je a yi ta sha ana ɓarna, Eng Ali wali ya ce akwai fita ta musamman kuma ƙauyen da za shi basu da kirki dole tafiyar sai daku a ranar zaku cake ku bawa samaniya yazo ta yi hadari"" Mangal ya buɗa ya ce ""Dar hakan ya yi mana, sai Eng Ali wali ko ana su ko ba'a su ya zama dole don uwatar"" Police ɗin ya juya kan Mai dawa a hankali cikin magana mai muƙamin" ya ce """Ka taɓa jin mai suna Scorpio?""" """Wa?"" Goje ya ce da sauri yana kallon Mai dawa da sai a lokacin ya juyo ya kalli Jafar shima Jafar ya kalle" shi da kyau ya ce """Akwai matsala ne babba, Scorpio yana yi wa Eng Ali wali barazana, yana da babbar hujjar da zai iya" "kawo masa matsala a mulkinsa kuma babu shakka ko waye Scorpio akwai alamar ya shirya fito na fito da Eng Ali wali, to muna jami'ai ba zamu bari ba tunda a jikin shugabannin da ƴan dabarun mu muke samun namu rabon. Ali wali yana buƙatar ka taya shi gano waye wannan Scorpio da sunan shi kawai ake ji ba" "kamanni""" """Kamarya kenan?""" Mai dawa ya tambaya a taƙaice yana jin ƙirjinsa na buɗewa saƙo ya fara isa kenan a fili kuma ya sha kunu "sosai. Jafar ya dafa kafaɗar Mai dawa ya ce ""Kamar kai yanzu kowa ya san sunanka Mutallab inkiya Mai dawa saɓanin shi da sunan Scorpio kawai muka sani, babu wanda Eng Ali wali ya yarda da shi sai jami'an Dss ka baza jama'arka su tayaka binciko asalin waye Scorpio akwai kyauta mai yawa idan hakan ya" "tabbata, kuma ya ce ka faɗi kome kake so zai baka""" "Wani irin kallo Moh ya dinga yi wa Jafar na kan kaga biri, biri ya ganka kifi na ganinka mai jar koma sai" "kuma ya ɗaga kai sama yana kallo sama cikin kumburarriyar murya ya ce ""Bayan Dss da shi uban gidan naku waye ka ji yana neman SCORPIO?"" Jafar ya ce ""Me ya sa kake tambaya?""" """To kuje ku yi aikin da kan ku"" ya faɗa yana juyawa cikin sauri Jafar ya riƙo shi ya ce ""ka dinga" "sassautawa zuciyarka da fushi. Bayan Dss akwai jami'ai mafi hatsari da suke neman shi idanu rufe FID Federal investigation department, basu da imani wannan mutanen jami'ai ne da ba zaka taɓa tunanin ta" "ina zasu cimmaka ba, suna iya zuwa a suffar mahaukata ma ko mai neman taimako, su kakkarya mutum" "ko su kashe shi ko haukata shi ba wani abu bane a wajan su""" """Suka kasa kama Scorpio?"" Jafar ya watsa hannu ya ce ""Sannu sannu da zarar sun gane kamanmin su," "babu mamaki su ɓullo ta wata hanyar kafin hakan ta fara ka ruga su kai hari,mun gama magana da kai" "Mai jeji"" ya yi shiru bai ƙara cewa komai ba ""Ka yi shiru?""" """Ka bada sha ɗayanka, zamu jauwalo ka idan akwai sagi"" cewar Goje Jafar ya girgiza kai ""Ka bar shi ya yi" "magana"" Moh ya sake kame fuska babu wasa kuma yaƙi cewa komai sai ma fito daya fara yi yana kallon bindigar dake hannun ɗaya ɗan'sandan. Bisa dole suka juya suka tafi ba tare daya tanka su ba,daman Goje ya san ba maganar zai yi ba. Goje ya juya ya kalli Mangal da yake zuƙar wiwi a hankali ya ce ""Ka" "raina musu hankali waye Mai dawa waye Scorpio""" """Ni ne, MUTALLAB TAHHB SCORPIO""" Mai dawa ya ce yana zare idanu waje manya gwanin tsoro da razani har sai da Goje ya ja da baya don bai taɓa ganin halittar idanu kamar ta Moh ba ƙwayar ta juye kamar bata mutane ba kuma sai ƙara ware manyan idanun yake yi. """Akwai matsala Moh idan suka gano cewa kai ne Scorpio, za su yi maka illa gwara ka ɓace kawai daga" "yankin kafin komai ya sarara"" ""Gawata za su iya gani su haƙura da nema na"" Ya furzar da iska daga cikin" bakinsa kansa ya yi masa nauyi """Goje an yi sake tunda aka bari na je state cid,ba san komai ba amma a fitar dani. Zan iya haƙura da" "komai banda abin da yake damuna a zuciya ni da kai na zan bayyana cewa nine Mutallab Tahhb Scorpio da zarar na cika muradina na abin da na yi niyya""" """Mai dawa""" """Sai godiya""" """Ina tunanin ka haƙura ka bar wa Allah komai duk zamu baza mu je gare shi ya yi mana eh hisabi"" Moh" "ya taune harshe yana kaɗa leɓe tare da saka harshe ya kashe wuƙar dake hannunsa ""Zafin nake ji a" "zuciyata zan yi ɓarna, zan sha jini""" """Kamar wani maye? Shi Ali wali ɗin me ka yi masa ne?""" "Mai dawa ya ja idanunsa ya lumshe ko yaya idan ya yi shiru sautin kuka biyu yaje ji a kunnen shi, tare da" "jiyo ƙarar wutar dake cinye jikin nata hakan ya saka baya iya runtsawa idan ba wani abu ya afa ba haukwata shi ake son yi. ""Na yarda da kai Goje, ka ci amanata askira zan saka maka a maƙoshi"" ""Ni ɗan halak ne. Yanzu ya batun Manager ɗin? Ka santa ne na ji baka bashi amsa ba"" jin ya yi shiru ya saka shi" cewa """Ko dai ka san Managern kamfanin?""" """Karka ka daman""" ***** Fiyya na zaune a saman gadonta tunda ta dawo take kwace tunani ne fal a cikin zuriyarta ga wani irin "tsoro da bata taɓa jin shi ba, a karo na farko ta ji tana son sanin komai da komai na Kamfanin FS WORLD INVESTMENT COMPANY, da duk mutanen da suka saka hannun jari a ciki data rufe idanunta yatsun hannun take ganin da aka yanka aka zuba cikin leda sosai taga rubutu jikin ledar amma ta manta bata duba ba. Ta juya a hankali tana kallon wayarta kamar mai tunanin wani abu kuma sai ta ɗauki wayar tana dannawa numbersa ta kira aka danna line busy. Har zata ajjiye wayar sai ta ji an kira ta zubawa" sunan idanun kafin ta ce. """Ashraf...""" Kiran ta ɗaga ta kara a kunne ta yi shiru ta cikin wayar ya sauke numfashi da ƙyar muryarsa a hankali. """Na ji tsoro Fiyya"" ta ɗan tura bakinta gaba kamar yana kallonta muryarta mai daɗi ta ce ""He said he was" "scared"" ya ƙara fidda numfashi kamar tana gabansa ""Maama kina wahalar dani da kika zaɓi aikin nan na kusa mutuwa, na ji ba zan iya barin ki ba kuma ke ce dai wacce nake so Fiyyar nan tawa""" """Ba na ce ka daina ce mini Maama, why not Fiyya kawai?"" Kamar mai raɗa a hankali Ashraf ya ce ""I am" "sorry bestie me""" Dum! Haka ta ji kan ta ya yi masifar sarawa da sauri ta dafe kan nata tana jin kamar wani abu na janta a "gigice cikin faɗa ta ce ""Karka sake kira na da wannan sunan"" ta cikin wayar ya ce ""Ba zan sake ba amma lafiya kike? Yanzu kike mini magana cikin soyayya Fiyya me ya sa sometimes kike abu kamar bake ba?" "Are You okay?""" """Kai na ke ciwo""" Tana cewa haka ta kashe kiran ta cillar da wayar nata zuwa gefe guda. Da sauri ta miƙe babu ko hula a "kan gashinta yana tashi sama tana dafe da kanta bata ganin ko gabanta duhu ne a cikin idanunta haka ta dinga sauka akan matattakalar benen. Karo ta yi da mutum cikin sauri ta kama hannunsa tana ɗorawa a kanta ""Yaya J kai na zai cire wani abu nake ji, ciwo yake mini kamar ana jana"" gabaɗaya ta rikice ta" ƙanƙame shi har zufa ke tsattsafo mata. Kama hannunta ya yi ya jata saman kujera taƙi sakin shi ya zauna a hankali tare da zaunar da ita ta yi saurin ɗora kanta a cinyarsa ya riƙe mata kan yana murza goshinta nata very careful kar ta ji zafi. Sun jima kana ta shiga sauke ajjiyar zuciya numfashinta na sauka ya ɗan leƙa fuskantarta yaga bacci take ya saka hannu ya juyo da fuskarsa yana zuba mata idanu ya riƙe hannunta har lokacin bai ce komai ba. """Aliyu""" "Da sauri ya saki hannun nata yana zame ta ya miƙe tsaye Ummi ta kalli Fiyya ta kalle shi ta ce ""Ita kuma" "lafiya take bacci a nan? Yaushe ta shigo gidan ai lokacin tashi bai ba?"" Captain dai ya yi shiru ta juya ta kalle shi sosai ta ce" """Lafiya take?""" """Ban sani ba""" """To ya naga kana haɗe rai duka zaka kawo mini me kai komai naka babu walwala Aliyu ka dubi girman" "Allah ka dinga murmushi shifa yin murmushi sunna ne ta ma'aiki"" ya shafa kan shi yana zuba hannu a aljihu cikin gaskiyarsa ya ce ""Ban iya ba wallahi Ummi ki koyan""" """Shi murmushin? Allah ya rufa asiri to wannan matarka ta shiga uku"" yana dai tsaye bai ce komai ba." """Maama?""" """Ummi""" """Maama ta shi yammaci za ki yi ƙunci ko ciwon kai idan kikai bacci"" ta buɗe fararen idanunta suka haɗa" idanu ta sha kunu sosai tana tura baki ya zabga mata uwar harara ta yi baya zata koma baccin. """Kee"" ya kira sunanta ta buɗe idanu ""Tashi kafin na yi balle da wannan silar ƙafafuwan"" miƙewa tsaye ta" yi ta murguɗa masa baki bata ce komai ba shi kuma ya yi kamar zai juya ya damƙo hannunta ta ƙwalla ihu daidai nan Daddy ya shigo parlon cikin sauri ya sake ta. """Da kyau Soja gwara ka nuna ƙarfinka akan ɗiyata, yanzu zaka tattara ka koma inda ka fito""" Captain ya juya ya bar parlon gabaɗaya yarinyar haushi take bashi har zuciyarsa. Daddy ya kalli Fiyya ya "ce ""Maama, yaushe za ki girma ina ganin wawtar wanda ya ɗauki muƙa min Manager ya ba ki wallahi""" """Daddy kune kuke raina ni wallahi, na girma am matured enough"" ya girgiza kai kawai kasancewar t.v. na" "kunne aka fara karato taƙaitattun labarai. Sunan Scorpio aka fara ambata matsayin wanda jami'an tsaro na hukumar FID Federal investigation department suke nema idanu rufe. Dake t.v a hankali ta juya ta kalli mai karanto labaran matashin ɗan jarida dake aiki a gidan t.v na VOA juyawa ta yi ta ce ""Daddy ɗan" "bani aron wayarka""" """Ki yi me da ita?""" """Wayata zan kira, ina son fita ne wajan Kinal"" ya miƙa mata wayar ta ɗan jim tana ɗaga hannunta tare da" "copy na wasu numbersa sai kuma ta miƙa masa bayan ta yi deleting tana murmushi ""La la la na tuna inda" "na sata""" "Ya kalli t.v ya kalleta ya kuma kalli wayarsa, ya dai amsa a ransa yana mai jin tsoro da mamakin kaifin" "tunanin Maama. Ummi kuma ta ce ""Ayi ta neman mutum kamar kiyashi shi kuma ya rasa sunan da zai" "sawa kan shi sai kunama?"" Daddy bai yi magana ba Ummi da abin ke ta cinta ta kalli Fiyya dake shirin" "haurawa sama ta ce ""Maama ta shi me ya yi ne?""" """Ummi ina zan sani, idan kika ɗauke yadda ake juya biyar ta zama goma ba abin da Fiyya ta sani"" tana" "cewa haka ta haura cikin sauri tana nanata numbersa dake kanta cikin sauri ta yi wanka ta shirya cikin abaya ta yi rolling tare da fesa turare sauri-sauri take a haka ta sakko hannunta riƙe da waya ko jaka bata ɗauka ba. Daddy ya dube ta ya kalli lokaci ""Wai zuwa wajan Kinal baya tashi sai yamma? Ita Kinal ɗin nan" "ta dinga zuwa mana zai fi""" """Daddy ba jimawa zan yi ba, na jima ban je ba mun gaisa ba""" """Maama bani da nutsuwa haka kawai idan kika fita gari ya hargitse bani number Kinal ɗin nan na kira ta""" "kafin ta yi magana J ya yi saurin ƙwace wayar Fiyya ya ce ""Bari na kira maka ita Daddy"" babu sunan Kinal a jerin wanda ta yi waya dasu yau cikin sauri ta amsa ta ce ""Number Kinal a kashe yaje fa J wai ni yarinya ce na san yadda zan kare kai na no body can come and hit me"" Ta kalli Daddy da Ummi ta juya ta kalli J" "ta ce ""To tsoran na mene ni Safiyya A Marafa?""" """Allah Ya tsare Maama jeki"" amsawa ta yi da amin ta raɗawa J kunne ""J akwai gulma yau bari na je na" "dawo"" tana fita harabar gidan mota ta shiga ta yi mata key cikin nutsuwa dake driving har ta fita ganin ta" hau kan titi ta dubi bayan motarta ta cikin gilas wata ajjiyar ta sauke mau nauyi ta rufe idanunta ta buɗe sai kuma ta ɗauke hanyar ta nufi wani titin daban a zuciyarta addu'a take yi sosai. ***** Eng Ali wali na zaune a parlo cikin wani gidansa da yake ganawa da ƴan siyasa masu mara masa baya a "kujerar shi. Ya dubi CSP chief Superintendent of Police ya ce ""Ina son ku ɗauke idanunku akan yarana, ko me kuke buƙata zan baku idan ɓarna sukai zan ji da komai"" Csp ya ce ""Hon yaushe za mu cigaba da zuba idanu ƴan dabarka suna yin yadda su kaga dama a garin nan musamman a unguwar Birget gashi lamarin na shirin haddasa faɗa tsakanin ƴan cikin gari da su ƴan Birget, mu jami'ai ne mun san gaskiya muke take" "ta""" """Ku cigaba da takewar su wannan yaran suna da wa'adi dana samu na ci zaɓe ko inuwata babu mai gani" "a cikin su. Don haka ku rufe idanunku a toshe kunnuwa, zuwa gaba har matsayi zan saka a ƙara maka mu yi ƴan dabaru"" CSP ya jinjina kai Eng Ali wali ya ɗakko kuɗi mai yawa ya miƙa masa yana cewa ""Idan kun" kama masu dilar ƙwayoyi da kayan maye na san ana miƙa su hannun NDLEA ko? Ka tabbatar ƙwayoyin "na zuwa wajan Jafar shi kuma zai bawa yarana, kar ka sake sunana ya fito daman ai ƴaƴan asara ne ko an" "kama su ba za su taɓa furta ni suke yi wa aiki ba, lastly magana akan Scorpio ɗin nan yana neman bani ciwon kai bana son ya zama damuwata, idan F.i.d suka riga ku kama shi akwai matsala""" """Karka damu hon mun zuba yaran mu ta ko'ina""" "Eng Ali wali ya ce ""Lallai Scorpio ya zo hannu kafin zaɓe""" Cikin sauri Fiyya ta fito daga cikin motarta tana shiga cikin wajan data zo a reception ta tsaya na wasu "mintina tana zaune ta fito tana murmushi ta ce ""Ikon Allah kamar tare kuke?"" Fiyya ta buɗe idanunta sosai ta ce" """Wa?""" """Captain yayanki""" "Gabanta ya faɗi ta kasa cewa komai Kinal ta zauna ta ce ""Wallahi zuwan shi biyu fa, nima dai na yi" mamaki amma ya ce aiki yake dubawa shi ne ya leƙo mu gaisa har ma na tambaye shi ke sai bai bani "amsa. Amarya ya kike ya sabgogi""" """Good. Yanzu lokacin ku ne Kinal siyasa ta matso ana ta fama da habaice-habaice""" """Kamarya habaici?""" "Fiyya ta cire gilas ɗin idanunta ta ce ""babu abin da mawaƙa suka iya sai habaici wallahi ku zagi wanda" "kuke so kuma ku yabi wanda ku kaga dama"" Kinal ta yi murmushi ta ce ""A'a ni ba ruwana idan an kira ni" "dai waƙa ina yi amma ai ni ta soyayya nake yi tunda a nan na fi kauri, ina nan ina shirya miki ke da" "Ashraf"" Fiyya ta sauke numfashi ta ce" """Ina cikin matsala Kinal ban so faɗawa kowa ba wallahi""" """Subuhanallahi matsala wacce kuma? A kamfanin ko gida ko wani wajan?""" """Kema kin san a gida ba wanda zai mini komai sai mai baƙin halin nan, tunda ya dawo ya uzzura mini ko" "parlo bana fitowa mutum sai baƙar zuciya ɗan wahala kawai aikin kawai"" Kinal dai ta zuba mata idanu kafin ta ce ""Mene damuwar?""" """Kwana biyu da suka shige ana bibiyata kullum idan na fita, harta nan wajan da na zo sai da aka biyo ni," "ni ba damuwata kai na ina tsoron su Daddy su sani kin san abu idan ya same ni tashin hankali suke shiga. Kinal ban san su waye ba me kuma suke buƙata saboda bani da issues akan kowa wallahi na ji kawai ina son sanin wanda ke following nawa duk inda na je gwara mu yi fito na fito da shi, da na ce ko na yi hayar ƴan daba nima suna take mini baya?"" Kinal ta buɗe idanunta sosai ta ce ""Daman na fara zargin kina da taɓin hankali Fiyya, ke yanzu ina kika san inda ƴan daba suke bare ki je? Bakya tsoro ko shakka ai matsalarki police ne wannan ina ganin a gayawa Captain kawai"" tsaki Fiyya ta yi tana miƙewa tsaye ""gwara duk abin da zai same ni ya zaman da dai na faɗawa Captain ni ina da abin yi"" ""Ƴan daban za ki yi" "haya yanzu kenan?""" """E"" sai kuma ta koma ta zauna cikin nutsuwa ta kalli Kinal ta ce ""Akwai abubuwan da bana ganewa" "kwana biyu kamfaninmu ina son na yi bincike duk abin da na samu ba daidai ba wallahi sai na kaiwa hukuma Kinal yatsun hannun mutum na gani a cikin kamfanin fa?"" Kinal ta zare idanu waje ta ce ""A'a ki fara samun mai kamfanin ku yi magana dashi tunda ke ce Manager"" ""Sai yanzu na fara tunani, i wonder aka bani Manager a kamfanina bayan akwai maza da yawa sosai da na yi tunanin ko experience ɗina ne" "yanzu kawai na ji ina zargi""" """Zargin me?""" "Ta ɗaga kafaɗa ta ce ""I don't know, na fara bincike dole zan gano gaskiya"" Kinal ta ce ""To ki bi a hankali" "Please Fiyya we care about you ni ma zani anniversary na makarantarmu FGC dana shigo Kamfanin gobe," "har waƙa na yi mana yanzu haka wani Eng Ali wali na yi wa waƙar da aka saka ni"" shiru Fiyya ta yi tana" "nanata sunan FGC a ranta ""Na ji kamar na san makarantar nan fa""" """Ke da ba ita kika yi ba ina za ki sami, ni a can na yi secondary school kinga""" """Haka ne bari na je""" """To ki kula Please kar ki saka kan ki cikin matsala don Allah Fiyya"" murmushi kawai Fiyya ta yi tana ficewa" daga cikin studio ɗin. ***** Kamar an cillo shi haka yaga Mai dawa ya faɗo masa cikin office ɗin nasa da yake tare da manyan "mutane sosai tun kafin ya yi magana ya ce ""Kowa zai iya tafiya"" duk suka fice ya ɗaga kai ya kalli Mai dawa ya ce" """Ka daina zuwa ina nake ni zan dinga neman ka""" """Ka yi ƙarya""" """Ni nake maka ƙarya Mai dawa?"" Ya wani haɗe fuska tamau fuskarsa ɗauke da sabon yankan da aka yi" "masa jiya har yanzu ba'a gyara ba. ""Kai ai ba Malam Abdullahi bane da ba zan ce kana ƙarya ba""" "Eng Ali wali ya jinjina kai ya ce ""Me ya kawo ka yanzu? Har cikin office nawa""" """Ka saka ni aiki har biyu, da kamo maka ɗawar can da nemo Scorpio"" ya shagiɗar da baki gefe ya yi fito" "wanda ya cika office ɗin sosai ""Na je gidan asawanta jiya""" """Kana nufin gidan Abdu Marafa?"" Ali wali ya ce yana miƙewa tsaye cike da tsoro Mai dawa ya ɗaga ƙafa" "ya ɗora a saman table ɗin gaban Ali wali ""sharaɗin kawo maka ita barewar shi ne mallaka mini kamfanin FS WORLD INVESTMENT COMPANY, aikin Scorpio kuma ka saka cinnakunka cire hannu daga sabgar ka bar mini ni zan nemo maka shi, bana haɗa aiki da wasu""" "Ali wali ya ce ""Mene haɗina da kamfanin nan? Karka saka ni rigimar da tafi ƙarfina da ka san ma'anar" "abin da FS WORLD INVESTMENT COMPANY yake nufi ba zaka haɗa kan da shi ba, wannan Kamfanin ciwon idanu ne"" Mai dawa ya ce ""Ni Mutallab Tahhb ɗan babana Abdullahi da inkiya Mai dawa bana harin abu na haƙura, wannan kamfanin shi ne burina"" Ali wali ya goge zufa ya ce ""baka san kamfanin ba shi ya sa a ba ki yake maka wahalar faɗa ni Ali wali sabgar siyasa na sani na saka gaba, ka bar ni a haka" "ba zaka saka ni a masifa ba""" """Waye mai kamfanin?""" """Sannin hakan daidai yake da tunuwar asirin manyan mutane da dama, ka bar komai yadda ka sani""" "jinjina kai Mai dawa ya yi ya ce ""Zan maka jahilanci ne, ka riƙe amana ka bi sharuɗan da na ce zan maka komai ni ɗan daba ne kai mai neman iko da muƙa mi ni na sare na kashe mu bauta maka shi ne. Batun kamfanin zan yi bincike da kai na, kar ka zama butu don wallahi sai na yi maka daƙiƙanci""" """In sha Allah, daga nan har bayan zan yi maka komai""" """Dar zan doƙa yanzu sai godiya""" "Yana fita Eng Ali wali ya ɗauki waya ya kira Csp ya ce ""Waye Mutallab yaron da ya fito daga wajan state" "cid kwanan nan bayan ya yi shekaru uku a wajan su"" ta cikin wayar Csp ya ce ""Sunan shi dai Mutallab ya kashe matarsa aka aka kama shi, daga baya kotu ta sake shi a zama na ƙarshe ba wanda ya san dalili"" Ali wali ya kashe wayar yana sauke numfashi a fili ya ce ""waye MUTALLAB?""" For more information 08164069385 "WhatsApp only.[10/11, 9:21 PM] Nanameera: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 7 *Bright pens... 2nd batch * The door is open... Ga masu buƙatar ayi musu tallah. Na hango wasu ƙwailaye a conversation group da Mikiya writers Maman Sayed ta ce a faɗa muku akwai maganin gargajiya cikin sati guda komai zai kankama haɗaɗɗan maganin da Fiyyar Ashraf ke amfani da su ta ce a baku numberta ba... 08063114606 "Washegari da safe Fiyya na ƙoƙarin buɗe ƙofa ta fito da nufin zuwa office ya rigata buɗe ƙofar, kallo ɗaya" "ta yi masa ta ɗauke kan ta zuwa gefe a hankali kuma can ta ce ""Ina kwana?"" bai amsa ba sai cewa da ya yi ""You told Abba za ki wajan wata, amma kin yi ƙarya ina kika je?"" Manyan idanunta ta ɗago ta kalle shi ta ce ""Ƙarya kuma?"" Ya rufe ƙofar ya tsaya ""Idan kina yi mini kamar ba ki gane ba, kwaɗa miki mari zan yi maybe it will help you to understand it very well"" ita mamakin shi take yi ""Ni fa Manager ce business zai iya fitar dani ko'ina"" ya buɗe mata manyan idanunsa sosai sai kuma ya ce ""ina kika je"" ta tura baki gaba sosai ta yi gefensa za ta shige ya saka hannu ya fisgota kafin ta yi motsi ya ɗago fuskarta ya wanka mata mari ƙwayar idanunsa tamkar zata fito waje yana ihu a saman kan ta ya ce ""Idan na sake maimaita miki" "tambayar sai na tabbatar yatsun hannuna sun kwanta fuskarki""" """Sai dai ka kashe ni"" ta yi maganar ko gezau gefen fuskarta ya yi jajur dakakkiyar zuciyarta kuma ya saka" "ta nuna ko a jikin ta, ƙasan zuciyarta kuma wani zafi da raɗaɗi take ji ""ni kike cewa na kashe ki?"" Hannu ta saka zata ƙwace nata hannu idanunta cikin nasa ba tsoro ta ce ""Me kake so na yi maka? Ka shigo kana tambayata abin da ban sani ba, ka saka hannu ka mari fuskar da kullum nake shafa mata mayuka masu tsada, ni ka mara ban maka komai ba, tunda ka tsane ni ka kashe ni kawai"" da ƙyar ta iya ƙare maganar saboda muryarta dake rawa Captain ya saka hannu ya sake ɗauke fuskar Fiyya da mari yana huci ya ƙara ɗaga hannu zai mare ta cikin sauri ya tsayar da hannun nasa ganin hancinta na fitar da jini sosai kuma" yaƙi tsayawa. "Ta yi masa ƙuri da idanunta da ruwa ya kwanta a ciki, jinin kuma bai fasa zuba ba daidai nan aka buɗe" ƙofar tare da shigowa ciki da sauri Fiyya ta nufi wajan Daddy ta riƙe shi tana fashewa da kukan dake cin "ran ta jikinta har wani irin rawa yake yi da ɓari jinin dake fita a hancinta kuma ya shiga ɓata masa farar rigar jikinsa. Daddy ya juya ya kalli Captain daya haɗe fuskarsa ""Aliyu me ka yi mata?""" """Ni kuma?"" Ya tambayi daddy irin bai ma san me ya faru ba ""To ita da waye haka ji bi yadda take kuka" "hancinta na jini kuma kai na gani a ɗakin, dole kasan mene ya faru"" cikin damuwa daddy ya yi maganar wacce sai da ta bayyana saman fuskarsa ya ɗago Fiyya yana duban ta sosai ya ƙara kallon Captain" """Maama wannan jinin fa? Daman kina yin haɓo ne wani abun Aliyu ya yi miki?"" Ita dai Fiyya taƙi cewa" "komai sai shassheƙar kuka take yi numfashinta na yin sama, Daddy duk ya rikice baya wasa da al'amarin daya shafi Maama ko kaɗan a ƙasan zuciyarsa yake jin soyayyarta ya kuma tabbatar ita ce rauninsa Fiyya kawai za a taɓa a iya nakasta rayuwarsa. ""Ya isa daina kukan haka nan, Allah Ya nuna mini sati mai kamawa ki tafi gidan mijinki ni ma zan fi samun nutsuwa da hakan zan fi samu nutsuwa idan kikai auren" "nan Safiyyerh""" """I love you daddy"" Fiyya ta ce a hankali tana rungume daddy ya shafa kan ta cike da soyayya ""daddy love" "Safiyyerh"" tuni Captain ya fice daga cikin parlon. Anty Turai da zuwan ta gidan kenan ta ce ""Ikon Allah. Yaya kai ne kake ɗaurewar yarinyar nan gindi wallahi ka lalata da soyayya take yin abin data ga dama, ko" "Aliyu baka tambaya abin da ta yi masa ba ta wannan figaggiyar yarinyar kake""" """Fita daga ɗakin nan Turai"" rai ɓace Anty Turai ta fice tana zabgawa Fiyya harara ranta duk a ɓace." "Daddy ya kalli Fiyya sosai kamar zai yi magana sai kuma ya ce ""jeki wanke fuskarki I'll drop you""" """Daddy daman i missed your drive wallahi"" murmushi ya yi mata a duk santa zai kalli Fiyya sai gabansa" "ya faɗi ya juya a hankali ya dubi picture ɗinta dake gaban madubi sanye da kayan graduation ta yi wani kyakkyawan murmushi ta rungume hannunta tana kallon gefe guda. Ya ƙarasa ya ɗauki photon ya shafa a hankali ""Maama na ni kamar na yi ba daidai ba, bani da wani zaɓi ne i am sorry Safiyyerh Abdu Marafa"" ya lumshe idanu ya buɗe a kan photon ""kina tunanin kin yi girman da za ki iya kula da kan ki, ki" "kuma yankewa kan ki hukunci? Maama ba kin san komai ba a rayuwa you're nothing but a stubborn girl""" Ya ajjiya photon ya ɗauki wayarta babu wani password a kai dudduba abu ya fara a nutse yana yi yana "kallon ƙofar banɗaki can ya sauke ajjiyar zuciya ya ajjiyar wayar daidai nan ta fito. Ya yi waje yana ""Ki" "same ni a ƙasa""" "Suna tafe a hanya daddy na driving a nutse ta ce ""Daddy"" bai kalleta ba yana dai sauraren ta domin" "program ɗin da ake yi da Eng Ali wali a redio shi ne ya ɗauke masa hankali. ""Zan raka Kinal FGC""" "Wani burki ya ja a kusan tsakiyar titin Fiyya ta dafe kai tana ""Subuhanallahi""" """Mene haɗin ki da FGC Maama?""" """Daddy Kinal zan raka suna yin taro na makarantar zan bita idan na tashi aiki"" zufa har fitowa daddy take" "a saman goshi sunan FGC ba ƙaramin gigita masa lissafi ya yi ba. ""ba za ki ba"" shagwaɓe fuska ta yi ""don Allah daddy wallahi na ji ina son zuwa""" """Wallahi mistakenly kika je shegiyar makarantar nan sai ranki ya ɓaci kuma sai kin daina fita hatta aikin" sai kin ajjiye. Wallahi Safiyyerh Abdu Marafa idan kika je za ki san waye Abdu sai na zane miki jiki da "carbi ko bulala"" ta yi ƙasa da kanta zuciyarta duk babu daɗi idanunta na cika da hawaye tun tana ƙarama take yin biyaya a komai akan abin da ya yi crossing da buƙatar daddy." "Hannunta riƙe da jakarta ɗaya hannun wayarta data kara a kunne suna magana da Kinal, duguwa ce" "hakan yasa bata fiya saka takalmi mai tsayi ba suit ce jikinta as always fara tas mai riga da wando ta yi rolling da black ɗin mayafi idanunta sanye cikin wani shade glasses mai kyau a hankali take tafiya tana ɗan jinjinawa mutanen kamfanin kai with so much respect tana da girmama mutane kawai rainin hankali ne bata ɗauka ""Kinal ki je kawai idan na koma gida za mu yi magana, daddy ya hana"" yadda ta yi furucin" ya bayyana ainihin abin da take jin a zuciyarta. """To shikenan nima na zo studio ne zan yi waƙa idan na koma gida zan shirya za mu yi video call na nuna" "miki cikin FGC ɗin"" Fiyya ta ɗan taɓe baki daidai lokacin da take isa bakin ƙofar office nata security ya" "matsa ta buɗe ta shiga ta buɗe idanu ganin Ashraf zaune a office ɗin ""Kinal mu yi magana anjima"" ta cire" wayar tana kallon Ashraf daya miƙe tsaye yana mata murmushi """Kuma da permission ɗin wa ka shigo?""" """Wake neman permission idan ana batun ganin mata, na zo ganin matata ne"" ta ajjiye jakar hannunta" "tana zama saman duguwar kujera ""Sannu mai mata"" ya miƙe ya dawo kan kujerar yana leƙa fuskarta" """Miji ɗaya gare ki a duniya kuma nine"" cikin wasa ta ce ""Ai kowa ba zan aure ka don ka ji""" """Funny Fiyya"" a yanayinta na rashin damuwa da soyayyar ta ce ""How are you?"" Yana kallonta yana ji" "wani abu sosai game da ita ""Fiyya na yi kuskure wallahi bana sanin ina shige limit ɗina sai na yi wani abu. Ni na san ba wani sona kike ba amma idan kika yi haƙuri watarana za ki ji son nan ko yaya ne kullum kina ƙara nesanta kan ki dani yayinta zuciyata ke ƙara kusanto kanta gare ki. Komai da lokacin shi idan mukai aure muka rayuwa inuwa guda I'll definitely be honest to you, ina jin kishin ki a ƙirjina ne a nan nake ji" "kina mini motsi Fiyya"" ya nuna ƙirjinsa saitin zuciyarsa sai ya ɗan juya gwanin tausayi" """Amma bakya so na""" """Who told you that?""" "Ashraf ya buɗe idanunsa ""When are you gonna tell me you love me?"" Tana kallon shi tana murmushi ita" "tana son shi sosai kawai bata san ya zata nuna bane sometimes rigimarsa ke sawa ta bijire itama ta miƙe tsaye tana danna kiran number messenger bayan ya ɗaga ta ce ""Call Md for me, ka kira mini Md da Secretary hadda accouter"" ta ajjiye ta ce ta haɗa shayi a cup guda biyu ta saka cokali tana miƙawa Ashraf" "ɗaya idanunta cikin nasa ta ce ""San da aka kai ni gidanka matsayin mata"" ya lumshe idanu ya buɗe" """I'll wait as far as you're with me. Abin da kawai nake buƙata shine ki so ni. Ki so ni ko da kaɗan cikin" "yadda nake sonki ne""" ***** Anty Hameeda na sunkuye a madaidaicin parlon gidanta tana duba jarkokin lemon ginger ɗin da take "siyarwa ta ji hucin mutum da sauri ta miƙe sai kuma ta yi baya a razane ganinsa tsaye a gabanta yana waige-waige kamar wanda aka biyo ga wani irin yanka a ƙarƙashin wuyansa da alama yanzu akai masa jini ja zuba, ya yi zuru-zuru sai huci yake yi naman jikinsa musamman na ƙirjinsa na motsawa ""Ɗan autan Ammo wannan hucin fa kamar an biyoka wani abun ka yi? Wane ya yanke ka haka me ka yi masa?"" Bai kula ta ba ya juya ta bi bayan shi kitchen taga ya nufa ba jimawa ya fito da kwanon abinci daidai nan" wata mata ta fito tana ganin Mai dawa ta yi saurin sakin butar hannunta ta ce """Wannan tantirin ƙanin naki uban ne ya zo yi mana a gida? Yaushe ma aka sake shi innalillahi wa'inna" ilaihirraji'un mugun ji da mugun gani Ubangiji ya kare Allah wadaran ƴan daba ya tsine musu albarka ya "saka su fita a cikin ajalin su"" matar ta faɗa hawaye ya cika idanun Anty Hameeda ta ce ""Baba ina laifin ki" "ce Allah ya shirya ɗa fa na kowa ne bawa kuma sai me shi, ciki ne mai haife-haife baka san me Ubangiji" "ya ɓoye ba suma fa ƙaddara ce ba wanda ya zaɓi yadda rayuwarsa zata kasance""" """Ai duk wani ɗan daba ƙarshe wulaƙantacciyar mutuwa ce ko idan sun sha ta faɗa musu babu daɗi su" "kashe kan su, ko kuma su haukace garin shaye-shaye ko garin faɗan daban su a kashe su. Allah wadai"" Moh dai bai yi magana ba abinci kawai yake ci hannunsa ko wankewa bai ba duk jini Anty Hameeda ta shige ɗaki bayan ta share hawayen idanunta lemo ta ɗakko masa da ruwa ta ajjiye tana kallon yadda kusan rabin fuskarsa ya yi tabo da yanka yaro ba ya kalle shi ihu zai yi ba annuri a fuskar nan. Duk yawan abincin ya cinye ta sha ruwa ya shanye lemon tas ""Na Ammo yanzu kana jin abin da ka zaɓawa rayuwarka shine daidai ka ji tausayin mu don girman Allah. Wallahi daka kasance cikin wannan rayuwar gwara ka dinga aikata abubuwan da kake a baya, jibi yadda ka yi muni ka zama ƙazami sai warin dauɗa kake yi. Na je gida sun ce sun fi sati uku ko gilmawar ka basa gani wai malam aure zai ƙara kuma da ƙyar idan ba Ammo zai saka ba, na rasa wake bashi kuɗi ya fi son ya yi ta auri saki ana haifa masa yara yana" "kasa kulawa da tarbiyyar su""" Tamkar bada shi take ba haka ya yi ko gezau can ya miƙe tsaye ta ciro kuɗi dubu ɗaya ta bashi ya kalle ta ya kalli kuɗin idanun nasa a rine kamar gauta yaƙi amsar kuɗi ganin inda ya nufa hannunsa riƙe da wuƙa ya saka Anty Hameeda ihu ta ce """Me za ka yi ka rufa mini asiri kar ka kashe mini aure na shiga uku"" ko kallon ta bai yi ba, ya ɗaga labulan" "ɗakin Baba tana sujjada ya same ta. Tsartuwa ya yi ya fito da kunama ya cilla mata a cikin hijabi kafin ta ankare ta ɗago jin abu na bin bayanta kamar kunamar tsafi ta shige mata riga ya zaro askira ya daidaici ɗuwawunta ya lafta mana wani uban yanka, baba ta saki ihu tana ta shiga uku ya yi saurin fita askirar na" zubar da jini da. Yana fita su spider suka rufa masa baya. A cikin wani kango ya kwanta ya yi shiru cikinsa zafi saboda faɗan da sukai da ƴan cikin gari akan fita wajan kamfel da sukai kilashin. Ya rufe idanu zuciyarsa na buɗewa wani irin ɗaci yake ji a cikin maƙoshinsa wani a ya tokare masa kamar yanzu komai ke faruwa haka yaga magic ɗin idanunsa ke hasko masa bidiyon komai ta ciki inda take tsaye. Yana zaune a gida a lokacin yana jin yadda karatun Almajirai ya cika masa kunne ya yi kicin-kicin da fuska. "Ammo ta kalle shi ta ce ""Yau kuma waya taɓa jarumin Ammo?"" Ya yi mata shiru don bai fiya cewa komai ba idan ran shi ya ɓaci kafin ta sake magana wani yaro ya yi sallama ya ce ""Wai bestie ya zo in ji bestie""" """Waye bestie? Injiwa jeka tambayo""" "Mutallab a lokacin bai motsa ba ya hakimce kamar sarki kansa a ƙasa yaron ya dawo ya ce ""Wai in ji" "Safiyyerh matar Mutallab bestie""" "Baki buɗe Ammo ke kallon Mutallab ta ce ""Na Ammo yaushe ka yi aure bani da labari yau naga abin da" "ya fi ƙarfina, yara ƙananu daku wacece Safiyya"" ya miƙe tsaye daga shi sai gajeren wando ta wata riga ƙarama ""ban san ta ba""" """Ikon Allah""" Fita ya yi yana shan kunu ganinta tsaye suna haɗa idanu ta yi ƙasa da kan ta. Ya dinga kallon ta yana jiran "ya ji mene ""meye ne?"" Ya tambaya." "Hawaye ya gani a idanunta fal ""Ni a gidanku zan kwana"" tar ya gama buɗe shanyayyun idanunsa a kanta" """wanne gidan?"" Ta nuna masa gidan ""sai ki ce ke wa?"" Tana masa shagwaɓa wacce daman ya san hali" """Matar Mutallab, baka zo makaranta ba yau ba kyau fashi"" da wani irin ƙarfi ya ce ""Safiyyerh!"" Gani an yi" kanta. *** “Safiyyerh” ya ƙwalla kiran sunanta yana zabura kamar yanzu ne abin ke faruwa jikinsa duk rawa "yake ganinsa shi kaɗai a kangon ya saka ya kifa kansa zuciyarsa na wani irin tsalle tana huci jijiyin kansa sun fito sun yi kwance saman kan shi. Ƙwayar Rohypnol ya ɓalle ya haɗiye har huɗu ya yi shiru jikinsa ya yi weak yana ganin kangon na jujjuya masa lokacin gudu yadda idanunsa suka gane masa cikin jini kwance saman gado ya sake faɗo masa, ya dinga jujjuya kansa ƙwaƙwalwarsa ta tsaya cak kamar wacce ta yi hooking da sauri ya zaro takardar daga cikin aljihu tsoron ƙara kalla yake ya yi saurin damƙe ta cikin hannunsa sai kuma Ammo ta faɗo masa a rai bai damu da jinin dake fita a wuyansa ba ya yi kwance a" ƙasa shi kaɗai kamar maraya. "Yammaci liƙis yana zaune gaban ta, ya kalleta a karo na farko ya ce ""Me ya sa kika buƙaci na ce ina son" "company?"" Abbasa ta ajjiye abin hannunta ta kalli cikin bukkar ta ce ""Sanda ka faɗa mini waye Mutallab," ka bani labarinka zan faɗa maka hujjata tare da dalilin cewa ka cewa Ali wali kana son kamfanin FS "WORLD INVESTMENT COMPANY""" """Bakya tsoro na kashe ki?"" Ta dube shi ta saka hannu tana goge masa wajan ciwon ""ba zaka iya kashe ni" "ba babu abin da zaka iya yi wa Abbasa. Ya batun zama mata mazan? Mene dalilin daya saka kake so ka zama?""" """Bana son haɗa danganta da kowacce kurciyya, ba idan aka yi baru aure kenan ana wani abu ba, to bana" "so ba wacce za ta yi sha'awar zama dani mata uku kenan babu su saboda ni ki mayar dani mata mazan""" """baka watarana zaka iya buƙatar lafiya ko kasancewa da mace""" """Sai godiya kafin lokacin na cika muradaina na baza ƙiyama ki mayar dani"" ta dinga kallon shi ta ce ""Ka" "tabbata ka yi tunani""" """Ki aikata kawai""" """An gama, riƙe wannan"" abu ta bashi ya amsa ya sha ba jimawa bacci ya ɗauke shi. Bai san lokacin daya" shafe ba sai farkawa ya yi ya gan shi an wanke masa ciwon an saka audiga ya yi shiru yana jin he just missed something very important. Message ɗin Eng Ali wali ya gani kan yana son ganinsa da gaggawa ya tura masa address ɗin wajan. Mai "dawa na tsaye yana kallon Eng Ali wali da ya yi badda kama ya zame facemask ɗin fuskarsa yana kallon Mai dawa ya ce ""Mai dawa"" bai magana ba sai fito yake yi." """Abdu Marafa ya shiga gidan rediyo yau da safe ya sake jaddada ra'ayinsa akan ƙin takara ta yana kuma" "janyo hankalin matasa da su farka a daina amfani da su, domin yanzu matasa sunw siyasar wannan mazanin. Gwara youth su haɗa ƙungiya suna fitar da wanda suke ganin ya cancanta ya zana shugaba ba irina ni Eng Ali wali ba. Mutallab a fara shirin ɗakko yarinyar nan yadda zamu saka harshen Abdu Marafa" "ya yi laushi dole zai kawo kasa ya yi mubaya'a a gare ni Eng Ali wali"" Mutallab dai ya yi shiru abin shi." """Mutallab ina magana ka yi shiru?""" """Yau kake so a kawo ta ko gobe? Kai yanzu tukun mene ra'ayin naka akan matasa?""" """Bangane ba""" """Ka gane mana, ka zama ɗan halak cikin gyatuma idan ka ƙi cika mini alƙawari bayan cin zaɓe zan maka" jahilci. Jinin malam Abdullahi ke guna a jikina idan na so dole na janyo maka farinjini amma na daina wannan sabgar yanzu. Na rantse da ɗan Amina ka yi mini ba daidai ba za kaga ba daidai ba ɗan malam "nake ka daina ganina haka"" Ali wali yace" """Ai kai ƙanina ne, amma waye kai? Zan so jin tarihinka ka faɗa mini waye kai Mutallab?"" Nan da nan" "Mutallab ya sake haɗe fuska tamau ya yi shiru. ""Shikenan zan maka komai ka tabbatar ka sato mini" "yarinyar nan babu lokaci ban san me Hon Maɗatai yake shiryawar ba amma shirun da ya yi yana nufin komai. Sai batun nemo Scorpion""" """Zan tafi zan aiko Mangal anjima"" yana faɗin hakan ya fice kamar walƙiya." "Kwana biyu da faruwar abin da Captain ya yi bata ta ɗauke walwala daga gidan kodayaushe tana sama," "tun lokacin bata sake jin motsin shi ba. Abubuwa da yawa ke damunta yadda ciwon kai ke damunta tana jin kamar ana jona mata wani abu, bata iya bacci. Ga matsalar kamfani da kullum manyan kuɗaɗe ke shigowa cikin asoson kamfanin an rasa daga ina? Ta yi duk binciken daya kamata ta kasa gano bakin zare masu gadi sun tabbatar mata da cikin dare manyan motoci na zarya a kamfanin hakan ya saka ta ɗauki niyyar dole yau zata saci hanya ko wajan ƙarfe ɗaya na dare ta fita tana jin hakƙin kula da kamfanin yana kanta ne. Ta ƙara adding number cikin jerin numbersa ɗin abubuwan da take buƙatar sanin abu kai ma'ana hadda hujjar daddy na hanata yin wasu abubuwan. Miƙewa ta yi tare da yin wanka ta tare da alwala ta gabatar da sallar issha ta yi addu'a sosai da azkar wanda ke sanya mata nutsuwa tare da kusantata ga Ubangiji. Fiyya ta dinga kallon kanta cikin madubi sometimes tana jin kamar ba ita ba, she" missed the old Safiyyerh. Buɗe ƙofar akai tare da shigowa """Zaman ɗaki manager ta fara kenan?"" Murmushi kawai ta yi tana juyawa ta saka hijabi" """Yaya J, how are you?"" Ya yi murmushi" """Nothing without manager, ki fito daddy na kira an kawo invitation card"" ta haɗe fuska ya yi baya yana" "ɗaga hannu ya ce ""cut me out Fiyya da kan shi ya saka akai yi komai"" ""wai dole sai an yi mini aure ko me daddy ke tsoro?""" "Shiru J ya yi sukai waje ta samu Dr Hash zaune ta ce ""Dr good day, ina gefen kan mutum na ciwo yana" "ganin reflection na wasu abubuwa what was the problem?""" Dr Hash ya ɗago kai haka J da kuma Marafa Ummi ma kallo Safiyyerh take daddy na zaune yana ji bai "ɗago ba. Ta buɗe musu manyan idanunta Dr Hash ya ce ""Me kike gani?"" Kawai ta haɗe fuska ta ce ""babu"" wajan daddy ta ƙarasa ta durƙusa har ƙasa ta kashe shi ya miƙo mata waya Ummi ta ce ""Ki zaɓi furnitures ɗin da kike so"" ta yi sak tana kallon su dai daddy ya Aman wayar ya ce ""Babu buƙata, zuciyata ta kasa nutsuwa zan yi requesting da an ɗaura auren kawai Ashraf ya bar ƙasar dake"" da sauri ta kalli daddy ""Daddy aikina fa?"" ""Za ki bar aikin"" ta girgiza kai ta ce ""ba zan maka musu ba daddy kai mahaifina ne ina yin biyayya a komai, amma don girman Allah ka bar ni daddy akwai binciken da nake yi a kamfani da zarar na kammala zan je duk ƙasar da kake so idan ma ƙare rayuwata ne a can zan yi"" daddy bai kulata ba ya miƙe ya bar wajan J yana jin babu daɗi Ummi ma ta yi shiru babu yadda za ta yi da daddy idan abu akan Maama ne sai dai a kalle shi ta jawo Fiyya jikinta ta dinga bata haƙuri tana kwantar mata da hankali, Fiyya ta rungume Ummi tana kuka. Kamar kullum J Kalla ne yake sanar da an samu gawar wani babban mutum mai suna Alhaji Haladu da aka shiga aka kashe har gidan shi ana kuma zargin Scorpion ne saboda shaidar daya bari na sunan Scorpion a jikin bango. Ta dinga kallon screen ɗin t.v sai" "kuma ta miƙe ""kin ci abinci?"" Ta girgiza kai ""na ƙoshi an yi mini formatted folder a wayata Yaya J""" """Formatted kuma ko dai kin shiga wani wajan ne"" ta ɗaga masa kafaɗa ranta duk a ɓaci. Kwanciya ta yi" sukai waya da Ashraf yana ta mata maganganun masu daɗi har ta yi bacci. "**** Idanunta ya kalla muryarsa a hankali ya ce ""There's something about you that make me feel like" "you actually use magic about me, many things I do because you, many things I don't even know or remembered when I started doing them. The love I have for you is so real baby. Yet, ban san me ya sa zuciyata take yawan bijiromin da kokwanton yiwuwar samunki a rayuwata ba. I love you Safiyyerh""" “I love you Safiyyerh” A gigice ta farka daga baccin tana ihu da ƙanƙame pillow jikinta na rawa sosai da ɓari da sauri Daddy ya "buɗe ƙofa ya shigo haka Ummi da Yaya J wajan karfe biyu na dare ""Fiyya mene? Maama mene?"" Ta" sakko daga kan gadon a gigice ta nufi wajan daddy bakinta na rawa ta kama hannun daddy ta ce """Mutallab daddy, Mutallab who is Mutallab?""" For more information akan littafin MUTALLAB. Via 08164069385 WhatsApp only Na'ima Sulaiman Sarauta Assalama alaikum Hajiya muna da ingantaccen maganin gyaran nono wadda ya amsa sunansa magani Maganinmu ingantaccen maganine da yake tada jijiyon nonon da suka saki y'ar uwa breast dinki ko yakai silifas saboda kwanciya kikai amfani dashi in sha Allah zakiga amfaninshi acikin 1week maganinmu powder ne yana ciko da breast y gyarasu bashi da illa ajikin mutum munyi amfani da saiwoyi da magunguna gargajiya domin gyaran breast 08063114606 ina garin kano karki sanya y'ar uwa nono yana karawa mace martaba a gurin mai gida maganinmu kowa zai iya sha wadda zatai yaye ko gyara budurwa duk zasu iya sha breast dinki ya ciko yayi bull -bull "[10/13, 10:53 PM] Nanameera: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 8 *Bright pens... 2nd batch* """Daddy na ji kamar gangar jikina ta wanzu da wannan mai sunan, na ji ƙirjina ya mini nauyi numfashina" "ya taɓa gauraya da nashi daddy ina jina kamar bani ba, daddy who is Safiyyerh? Daddy tell me something about me, don Allah wallahi zuciyata bugawa take i missed something very important..." "Daddy!""" "Ganin duk sun yi mata shiru ya saka ta girgiza daddy da hannunta biyu ""waye Mutallab daddy?"" Duk" "suka sake yi mata shiru kamar basu fahimci me take nufi ba Dr Hash da bai jima da shigowa gidan ba saboda aikin kwana ya yi a asibiti ya nufi inda Fiyya take tsaye yana leƙa fuskarta ya ce ""Mutallab kuma?"" Ta kasa magana sai bin su take da idanu daddy ya yi namijin ƙoƙarin wajan kama kafaɗun Fiyya ya ce ""Maama waye haka? Kinga irin abin da nake faɗa miki akan muhimmanci da ƙarfin addu'a kina sake da" "gaske kina wasa da azkar""" "Sakin daddy ta yi ta nufi wajan Ummi ta ce ""daddy na san ke za ki faɗa mini"" nan ma Ummi ta kama" "hannun Fiyya ta ce ""Mamaa ban san me kike nufi kowa kike magana akai ba, kamar mai iskokai ki farka kina surutai mene haka kike safiyyerh?"" Da sauri ta saki Ummi ta nufi wajan Yaya J ganin ta nufu shi ya yi saurin juyawa ya fita da sauri yana dafe kan shi. Fiyya ta sake juyawa wajan daddy jikinta duka rawa yake da ɓari kamar mazari ta kama hannun daddy ta ɗora a saitin ƙirjinta idanunta na cika da hawaye bakinta" na rawa da ƙyar ta ce """Ni ban buƙaci sanin wani abu bayan hakan ba, ban ce dole na san wani abu ba ka yi mini alfarma ka" "faɗa mini waye shi waye Mutallab? Daddy please...!""" Kasa magana ta yi jin an tsira mata sirijin allura ta runtse idanunta ta saki daddy ta juya a hankali ta kalli "Dr Hash ta sake nutsa ganinta cikin idanunsa ta kalli allurar hannunsa sai kuma ta yi murmushi ta sake juyawa ta kalli photon daddy dake gefen gadonta ""why? Me ya sa ake mini allura daddy i love you"" sai kuma ta lumshe idanunta jikinta ya saki ta ji kanta ya mata nauyi tunaninta na ruɓanya gudun zuciyarta na ƙaruwa, kamar wacce ake yi wa updating haka take jin ƙwaƙwalwarta ganinta zata faɗi ya saka daddy ya riƙota ya jima bai ji tausayin abu ko wata halitta a duniya irin Fiyyarsa ya dinga kallon fuskarsa cike da so da ƙauna a hankali ya kwantar da ita saman gado ya ɗora kan ta a saman cinyarsa ya dubi Dr Hash ya" ce """Hashim ya zan yi da Fiyya ta fahimta me zan yi Hashim, Awais ya ya zan yi da Maama?"" Ya faɗa yana" kallon Marafa duk suka kasa magana Ummi idanunta ya yi jajur baccin da basu koma ba kenan sukai spending sauran lokacin wajan Fiyya sai addu'a yake yi mata. Dab da asuba ya miƙe ya fice daman shi ya yi saura ya kulle ƙofar. Duk da nauyin da kanta ke mata bai hana ta motsa ba saboda kiran sallah wanda hakan alama ce ta "cewa kai musulmi ne da zarar lokacin asuba ya yi dukkan wani rai a duniya daya kasance musulmi sai ya motsa, bakinta ɗauke da addu'a ta ce" ” لاَ ْ ُ هلل لاِ ي أْ َ انا َ ْ ُ َ ا أَ اَ َ ا إول َ ه "لاَ ُ رو""" "muryarta da ƙyar take fita a hankali ta ji an ɗan matsa hannunta, ta motsa yatsun hannun ta ji shi sarƙe" "dana wani ta rufe ido ta san cewa Yaya J ""ni ka cika mini hannu""" Ya buɗe ido ganin yadda ta murguɗa masa baki bai motsa ba a hankali ya zare yatsun shi ganin tana ƙoƙarin juyo da fuska zuwa ina yake ya miƙa hannu da sauri ya kashe hasken ɗaki the same time ya miƙe ya fice yana rufe ƙofa ta bi door way ɗin da kallo. **** Ammo na zaune a cikin ɗaki kamar yadda ta saba kodayaushe Malam ya ɗaga labule yana daga tsaye ya "kalli Ammo ya ce ""Ba dai tunanin wancan gantalallan kike ba? Kamar wacce aka ce na mutu kike takama ki yi ni ɗaki kwana ɗaki, to idan ma shine ki sawa zuciyarki ruwan sanyi da salama ki sallama shi, yanzu ke ba kifi samun nutsuwa ba da bakya ganin gilmawarsa yana saka miki faɗuwar gaba"" ita dai bata tanka shi" ba ta cigaba da aikin da take yi. Ya sake duban ta da kyau yana furta """Aure zan ƙara na hango wata ƴar duma-dumar bazawara fara tas sakin wawa ku yanke shawara a cikin" "ku wa zan saka"" a sanyaye ta ce ""Allah ya sanya alheri, duk wacce ka saka babu komai ko ni ɗin ce""" Malam ya juya zai fita Anty Hameeda ta shigo idanunta zuru-zuru alamar ta yi kuka gaban malam ya faɗi "ya ce ""mene kuma Hameeda?""" """Malam wajanka na zo da Ammo don Allah ku saurare ni"" ya yi jim sai kuma ya yi ɗakin Ammo ta bi" "bayansa gaishe su ta yi kafin cikin sanyin murya ta ce ""Ammo ke uwa ce kin ɗauki cikin Mutallab watanni wajan 11 ɗaya yake zaune kafin ki haishe shi, kin ji zafi da raɗaɗin naƙida wajan haihuwarsa, kin shayar da shi kin goya shi a bayanki, kin bashi abinci, kin ƙaunaci Mutallab sai dai ƙaunar da yake miki kamar har ta ninka wacce kike masa, idan bashi da lafiya baya yadda kowa ya taɓa shi sai ke ban san yaushe ne ko yaya ne ya zama haka ba, labarin da nake da shi akan Mutallab ba cikakke bane, zamana a Lagos ya saka ban san wasu abubuwan ba, kin ƙi faɗa mini yadda ya zama haka kin hana a faɗa mini, shin bakya jin rauni irin na uwa? Ƙauna irin ta uwa da ɗanta, duka bakya jin hakan kike barranta kan ki da autanki Ammo, hannunka baya taɓa ruɓewa ka yanke ka yar kar ki manta kalmar da ake cewa idan ka ƙi naka duniya ta so shi, idan ka so naka duniya ta ƙi shi, Ammo ga duniya da bakin jama'a na rige-rige kai" "Mutallab kabari idan kyautata zaton watarana za a kashe shi ko ya je inda ba zai taɓa fitowa ba..,""" """Allahamdulilah da zai mutum ai da ya sawwaƙa mini da ƴan'sanda Mutallab masifa ya zame mini ni na" "gode Allah da bana ganinsa cikin idanuna"" kallo malam kawai Anty Hameeda ke yi da ƙyar tana haɗiye abu mai ɗaci a maƙoshi ta ce" """Dukkan iyaye suna saka hannu cikin abin da ya fi gaban sanin mutane.Kowannen su yana ba da kaɗan" "daga jikinsa. Ta haka, abin da ya yi girma a cikin uwa ya zama mutum. Saboda haka, ba abin mamaki ba" "ne, sa’adda da aka haifi jariri, mutane sukan ce _mu’ujizar haihuwa_ , haƙiƙa, haihuwar yara ita ce" "hakƙin iyaye na farko. Da farko, jarirai suna dogara ƙwarai ga iyayensu, amma sa’adda da suke girma," suna buƙatar fiye da a mai da hankali ga abincinsu kawai. Suna bukatar taimako domin su yi girma a "tunaninsu, a motsin rai, a ɗabi’a, da kuma a ruhaniya." "Domin su yi girma da kyau, yara musamman suna bukatar iyayensu su yi ƙaunarsu. Ko da yake yana da" "muhimmanci a furta kalami na ƙauna, ya kamata ayyuka su tokara hakan. Haƙiƙa, yara suna bukatar misali mai kyau daga iyayensu. Suna bukatar ja-gora a ɗabi’a, mizanai da za su bi a rayuwa. Kuma suna bukatar wannan tun suna ƙanƙanana zuwa gaba. Abubuwa masu ɓata rai suna iya faruwa kuma suna" "faruwa sa’adda da ba a taimaki yara ba har sai da ya makara"" kukan da take dannewa ya ci ƙarfinta" """Ammo idan Malam bai fuskanta ba ki daure ki gane don girman Allah, shi kaɗai autanki ɗanki tilo ɗaya" "namiji da Allah Ya ba ki idan babu ranku shi ne zamu kira da sunan uba, zai mana walicci a ko'ina bai kyautu don ƙaddarar Ubangiji ta kitta a rayuwarsa ku ce za ku juya masa baya ko wofitar da rayuwarsa har haka ba, akwai hakƙin iyaye akan yara haka akwai hakƙin yara akan iyaye shin kina buƙatar Ubangiji ya tuhume ki da hakƙin Mutallab? Allah da kan shi cikin hadisi mai girma ya ce; ƴaƴanku amana ce kuma kiwo ne a gare ku, lallai za mu tambaye ku wannan amanar da kiwon idan an ce ki faɗi inda yake a yanzu ba za ki faɗa ba wannan abun da kuke kun bashi dama da lasisin ƙara lalacewa ne idan yaro ya ɗaƙko" "hanyar kangara jawo shi aje jiki a nuna masa ƙauna da soyayya""" "Miƙewa ta yi tsaye tana share idanunta ""ya zo mini jikinsa duk sara kamar korarre mara iyaye a duniyar" "nan har na yi na gama magana bai tanka wani kuskuren iyaye ke haddasa shi""" Tana kaiwa nan ta fice abin ta inda ta shige Inna Binta da Mama Zaituna na kokawa akan wani ƙanzon "tuwon da aka baza ya bushe sai ya yi gwanin sha'awa tana ɓantara da kaiwa baki ta ce ""eh, kya yi kya gama wannan ƙanzon sai na bawa Mufee ke ni fa akan abinci ba wani kirki gare ni ba, ba zan zauna yunwa ta yi ajalina a gidan nan ba, tunda mai gidan zuciyarsa a mace take bai san fus na hakƙin iyali ba sai auri saki da tare yara kamar ƴaƴan ɓeraye kowanne kana kallonsa yunwa zata fara maka sallama a jikinsa haba me ake da hali na..."" Da sauri ta yi shiru ganin malam tsaye ta yi mamaki da bai tanka mata" ba ya shige. Safiyyerh ta sakko daga saman bene tana yi tana duba wayarta ganin saƙon da Ashraf ya tura mata cewa ya ɗan yi tafiya ba ta yi reply ba ta riƙe wayar. Yaya J ta gani zaune ta juya masa manyan idanunta da suka sake fitowa farare tas ta ce """Office ɗin kenan?""" """Ina ni ina zuwa office banga yadda little sis ta farka daddy's favourite"" ta girgiza kai tana ɗan murmushi" "iya leɓe ta ce ""Yaya J kenan, good morning""" """Kin tashi lafiya sai ina?""" """Office, ina da meeting kuma Yaya J ka yi mini addu'a Please da wannan kyakkyawan harshen naka, zan" "baka labari mai daɗi"" ya ware hannunsa ya ce" """To ina jira ko na kai ki office ɗin?"" Ta girgiza kai ta juya tana nufar sashin daddy dake ƙasa. Fiyya tuni ta" "manta abin da ya faru ta manta wani Mutallab fresh take jin kan ta, tana ƴar waƙarta ta turanci tama" manta ta shigo parlon daddy dake zaune ya zuba mata idanu ta yi saurin rufe ba ki ta ce """Ka yi haƙuri daddy i enjoying when i sing a song, don Allah ka yafe wa Maama""" """Sai an yi magana idan kin yi laifi kina buɗe manyan idanunki kinawa jama'a turancin yaran zamani ke ba" "kowa naki da yake bature""" """To babana babban laccara ne wanda ake alfahari da shi dukkan matasa ke son shi saboda ƙoƙari da" "iyawar shi"" Fiyya ta ce tana zaman ƙasan ƙafafun daddy ""Tiger"" sak ta yi jin sunan da ya kira ta da shi," lallai an taɓa donganta ta sa wannan sunan na Tiger ta share kana ta gai da daddy. Ya amsa cikin kulawa duk motsin da take akan idanunsa Fiyya na da mugun wayo dana da wani "experience da Qualities bata yin abun da za a iya following footsteps ɗin ta, she is a clever girl faɗanta har tsoro yake bashi ga taurin kai da miskilanci har addu'a yake Allah ya sassauta mata sai gashi Ubangiji" ya gyara komai a lokacin da bai zato ba. Ya ɗauke kai yana kallon wani gefen """Aliyu yaushe ka dawo?"" Idanunsa a kan waya yana dannawa, wandon uniform na sojoji ne jikinsa sai" fara t.shirt tas wacce ta kama damtsen hannunsa ya saka p.cap ta sojoji fuskarsa kamar ya ce ya shiga uku can ya ce """Da daddare""" """Dare da yaushe? Aliyu kai kana son shigowar dare kamar mara gaskiya?"" Captain ya ɗan kalli daddy ya" "ce ""Tun 12""" """Kuma baka shigo ba me ya sa?""" """Kawai daddy"" ficewa ya yi yana cilla wayar a aljihu yana jin Fiyya na gaishe shi ko inda take bai kalla ba." """daddy ni ba zan iya ɗaukan wannan halin ba wallahi bai ishe ni kallo ba zan daina ko gaishe shi ina dalili, Safiyyerh Abdu Marafa na da class babu mai ɗaga mini shoulder, duk wannan abun da ya yi aure a waje ne yake soja"" Ranta duk a ɓace ta miƙe tana cewa daddy ta tafi ya ce ""Allah Ya tsare Manager ya shirya safiyyerh Abdu Marafa"". Kasancewar sauri take yi ta saka ta yi driving kamar zata tashi saman bata wasa idan tana kan titi, tana isa ta buɗe office ta shiga fahimtar da sabuwar envelope a table ɗin ya saka ta sa hannu ta ɗauka tare da buɗewa taƙaitaccen rubutu ne mai ɗauke da jan biro wanda ke nuna rayuwarta" na cikin matsala. A hankali ta fara duba consent ɗin da takardar ke ɗauke da shi tana ajjiye waya. "“Jarumtarki bai kai ki tsaya bincike akan FS WORLD INVESTMENT COMPANY ba, kina iya ɗaukan rubutun" matsayin wasa amma gargaɗi ne da jan kunne ga yara masu rawar kai irin ki. Ki tsaya da binciken da kike you're nothing but a manager” Ta dinga juya takardar a hannu tana jin confidence nata na ƙara hakan kamar wata dama ce aka haska "mata na nuna cewa lallai akwai ƙullalliyya a wannan kamfanin, kuma ta shirya buɗe faifai ko da za su yi zubaibai ƙwarya ne, ko da gaskiyar da take ƙoƙarin bayyanawa zai yi silar barin ta numfashinta daga ƙirjinta. Ta yi Addison na cikin abubuwan da take ƙarawa a binciken za ta yi komai ko hakan na nufin fito na fito da surukinta ne. Zama ta yi ta fara duba files na sabbin kayan da aka kawo can ta saka aka kira" mata accouter bayan ya shigo ba tare data kalle shi ba ta ce """Accouter kana buƙatar wani abu ne?""" """Allah Ya taimaki manager kamarya fa?"" Still bata kalle shi ba ta yi baya tana duba maganar da aka turo" "mata yanzu a waya ta ce ""kawai kuɗi idan kana so na buƙatun rayuwa""" """Ina jiran lokacin albashi ya yi ai nasan za a sallame mu da wuri"" ta ɗago idanunta masu sanyi ta zuba a" "kan shi sai ta cillo masa ƙaramin file ta ce ""na saka hannu ka yi signature as a accouter ka cire 1m a" "asusun kamfani na baka"" da mamaki ya ce" """Ni kika bawa kuɗin?""" """E, ko baka so?""" """To na ga ban yi wani aikin da na cancanci 1m ba kin sa na fara jin tsoro ba zan iya cin abin da ba haƙƙina" "ba"" ta ɗan yi murmushi ta janyo files ɗin ta yaga ta ce ""meye cikakken sunanka ma?"" Rainin hankalin" "Manager mamaki yake bashi sai kawai ya ce Wazeer"" da hannu ta ce ya je yana fita ta saka aka kira mata MD abin da ta yi wa Accouter shi ta yi wa Md cikin sauri ya ce" """Yanzu kika ɗakko hanya manager da za ki haƙa ramin da za ki iya binne kan ki ciki ai duk sai na raina" "wayonki wallahi da ajin nan naki ko mene a ƙasa ba ruwanki mind your own business rayuwar nan kana kallon wasu abubuwan kake yi kamar baka sani ba, to a haka cibiya ta rai ne mu kuma yanzu hankalin jama'a da yawa na kan siyasa, matasa na neman hanyar karatu, wasu na can suna bautawa ƴan siyasa, wasu sojan baka wasu rayuwar social media wasu bangar siyasa wasu kasuwanci. Safiyyerh da yawa ana yin abin da ya samu ne ko yazo hannu ba wanda kake ganin cancnatar shi ba, ba a duba capacity na abu ko a siyasa kana ji kana ganin wanda ya dace amma kake rufe idanu ka ɗauki baragurbi saboda yana watsa maka hatsi mu ɗin kamar ka ji suka ɗauke mu, think big Fiyya ke macace babu mai ce miki don me," "akwai kuɗin da shi kan shi Alhaji Baihaƙi bai sani""" """Kana son siyasa""" "Md ya yi murmushi ya ce ""Safiyyerh siyasa yanzu ai kusan a jinin kowanne matashi take, kinga muna da" "jam'iyyu uku ɗaya ce mai ƙarfi saboda ita ke riƙe da muƙami ma'ana ƙasar a nan Hon Maɗatai yake neman takarar kujera, sai jam'iyyar su Eng Ali wali sai last jam'iyya wacce mutumin cikin ta ya fi kowanne" "nagarta kuɗi masu dame shi ba, da ƙyar aka taushi zuciyarsa yake muƙamin kusan matashi ne matasa na" son shi amma kasancewar yana cikin jam'iyya ƙarama kusan sabuwa ya sa ba a yin maganar shi ma kuma "da ba musulmi bane"" Safiyyerh ta jinjina masa kai ta ce ""Ka bawa accouter ya yi signature a baka 2m, enjoy yourself MD, but sunan wanda kake bani bayani yanzu?""" "Ya washe bakinsa ba ƙaramin jin daɗi ya yi ba ya ce ""Abraham Denial David, shine ɗan takarar""" """Yana da hannun jari a nan ne?""" """A'a, i don't think zai saka hannun jari a nan gaskiya"" a hankali ta ce ""Me ya sa?""" """Kar ki zurfafa a bar maganar, za mu yi aiki tare"" sallamar shi ta yi tana jin zata yi amfani da Md da" accouter Md zai taimaka wajan sanyawa ta san sirrin kamfanin cikin sauƙi accouter zai taimaka wajan bayyana komai. A gefe guda tana jin kamar ta shiga batun siyasar Abraham ɗin kawai ta ji ya yi mata she just want to help him. **** "Su da kan su sun kwana biyu basu saka shi a idanunsu ba, ba kuma su samu labarin inda yake ba sai" "yanzu da suka ganshi kamar walƙiya kwance a ƙasa idanunsa buɗe yana kallon sama Darma ya ce ""Sai godiya wanda ya ce zai bi sawunka ya wahala, ɗan malam yaƙi halin malam dafinka ƙarinka masifa ne" "idan ka taɓa mutum da shi""" """Darma""" """Ka dake Mai dawa ka jima ka yi lastin irin na dabino, wa kake so a taka a kashe ko a yi masa fiɗa"" Darma" ya ce yana buɗe hannu sama tare da karkatar da baki hannunsa riƙe da ledar pure water ya nannaɗe a "hannu yana kaiwa baki tare da zuƙa. Mutallab ya sake buɗe idanu a sama ya kasa cewa komai tunaninsa ya tafi wani wajan. Goje ya ce ""Sai godiya matsalar goge ce ko wato ka kayan lantarki""" """Zaman gidan yari ba daɗi,amma na ji daɗi""" """Ka ce ka tuna na jakuna nan cinnaku tsakaninmu da su sai ƙarfe ba ma'ana ka tuna na jakin da suka" "haɗa maka kenan""" """Ina jin zafi a ƙirjina farcuna na da suka cire mini sun ƙi fitowa, zan ɗauki fansa Goje""" Kafin su yi magana an yi sallama an ƙarasu cikin sauri Mutallab ya rufe idanunsa jin muryar zabuwa. Goje "ya dinga kallon wacce take tsaye ""Bayin Allah sallama nake muku fa"" Mangal ne ya kalleta sosai ya ce ""Yi batu"" ta ɗan rausayar da kai gefe ta ce ""Amma dai ku musulmai ne amsa sallama wajibi ce""" """To alaiki, mene sagin aiki kike so a yi miki?""" "Kinal ta fito da littafi da biro ta ce ""Sunana Kinal ni mawaƙiya ce, har zan shige na hango ku na ji ina son" tambayarku na ji ina son na yi waƙa akan ku kasan mu da mu da marubuta kusan aikin mu ɗaya muna da "son bin ƙwaƙƙwafi"" Goje ya ce ""To ina ruwan mu? Fece kafin na yi miki lahani""" """Ku ba ƴan shaye-shaye bane? To akan shaye-shayen zan muku tambaya ina yin waƙar zan kawo muku" "ku ji, idan kun yi shaye-shayen me kuke ji mene dalilin daya saka kuka fara shaye-shaye kuma kuke harkar daba""" "Moh na jin su ya juya musu baya zaka ɗauka bacci yake, ransa duk a ɓace saboda jin muryar mace da ya" ji ya san daya juyo zai iya kashe ta tsaf don bashi da wani business da mata. Darma ya ce """Yanzu yadda muke ji za mu faɗa miki kenan?"" Kinal ta yi saurin cewa ""E, wallahi na iya waƙa ina da" "murya sosai babu mamaki idan na yi waƙar na saka a YouTube ta je viral na saka a tiktok ta yi trending"" Darma ya ce ""To ni dai tun daga sanda a gida na yi...,""Da sauri Goje ya tsayar da shi yana cewa ""Kai amma ɗan tsinanniya ne kai, ba haka ake bayani ba""" "Miƙewa ya yi ya ce ""bari na faɗa miki"" wuƙa ya zaro a ƙugunsa Kinal ta zare idanu tana yin baya cikin" "sauri Mangal ya tare bayan jikinta na rawa ta fasa ihu jin yadda Goje ya yanke ta da wuƙa a fuska,ya" danna mata ledan wiwin a baki ta fara zare ido tana ihu. Sai a lokacin Moh ya juyo yana kallon yarinyar ya cije bakinsa tare da juyawa exactly irin ihun da Safiyya ta yi lokacin zata mutu. """Gani ya kore ji, idan kin rero waƙar muna dakon ki a nan sata ƴar munafuka""" "Darma ya dinga tuntsira dariya sosai yana riƙe ciki ""Amma Goje baka da imani kamar fa fitsari ta yi a" "wando gaskiyar kurciyar nan akwai jan ido ga bayani nan kin gani ganin idanunki ai"" ya juya ya kalli Moh ya leƙa ga wata cukurkuɗaɗdiyya takarda yake karantawa shi ba wani karatu ya yi ba ""Wai wannan takardar mece kamar ta asiri kodayaushe tana wajanka, kamar numfashin shaƙa ka faɗa mana ta mece""" cikin sauri ya ɓoye yana damƙe ta a hannu Goje ya ce """Nima sai fakon farar nake na mata karatun makarantar allo, na rasa wacce tsiyar ce a ciki""" """Goje""" """Sai godiya""" """Zan saka maka tsini idan ka taɓa takardar nan ko na saka su tiger cinye ka ɗanye, wallahi zan iya kashe" "ka akan takardar nan""" "Kafin su yi magana an zo da babur an cillo wata takarda da sauri mai babur ɗin ya juya, Mangal ya miƙe" "tsaye ya ɗakko ya buɗe cikin sauri ya kalli Mai dawa dai kuma ya miƙa masa amsa ya yi ya duba, photo" "na gudu biyu ne ɗaya zanen fuskar wata kamar dai mahaukaciya sai kuma photo jira-jirai, photo me mai magana ga wanda yake da cikakken lissafi a gefe an rubuta FS WORLD INVESTMENT COMPANY." **** "Kwana biyu Safiyyerh ta yi busy duk wani family sun zo saboda gobe ne ake ɗaura auren, kamar auren" munafurci ba wata gayya ko shagali ɗaurin aure ne kawai ana yi kuma Ashraf zai ɗauki matarsa su tafi. A daren ranar Safiyyerh ta riga data gama accepting auren Ashraf ta yarda bata da wani miji sai shi zata sawa zuciyarta yadda zata zauna da shi tunda tana son shi ko ba can ba. Waya suka yi da Ashraf ya dinga "tsokanarta ""Har na hango idanun Maama a ɗakin miji, mijin na kuma Ashraf ta yi nasarar samun" "kyakkyawan saurayi"" ta murguɗa masa baki ta ce ""Zan fasa"" ya yi saurin cewa ""Idan ki kaga ba ki auri" "Ashraf to mutuwa na yi ko ke kika mutu, da gaske Fiyya ina son ki Allah shine shaida duk da ina dalilin auren ki ko saka ni akai na yi hakan amma na yi you're my life partner har janna in sha Allah""" """Kamarya? Mene dalilin auren?""" """Ke ba ki da wani favourite words ne sai kamarya, zan faɗa miki komai a daren ranar da kika zama" "halaliyyar Ashraf zan faɗa miki, zan sauƙaƙa miki binciken da kike akan Company"" a ruɗe ta ce ""Ta ya ya kasan ina bincike akan Company""" """Safiyyerh kenan, that's is the difference between man and woman, ina da baƙi sai goben idan na zo" "ganin matata a wannan lokacin dole na rungume ki halal runguma zan miki Safiyyerh"" hankalinta duk a tashe waye Ashraf ne me ya sa daddy ya amince da auren shi? Ta kasa magana har ya kashe kiran sai ya ƙara kiranta video call ƙura mata idanu ya yi taga yana shiri cikin sauri ta ce ""Kuma sai ina?"" ""Inda kika" "aike ni"" ta buɗe idanu" """Kamarya?""" """I miss you Fiyya shine abin da na manta na ce miki, a nan nake jin motsin ki"" ya nuna mata saitin ƙirjinsa," "daga nan ya kashe wayar. Daga ƙarshe ta yi zamanta cikin bedroom Awais har bedroom ya shigo ya dinga mata shira ""Yaya Aiwas ka ɗan yanke mini farce"" ""to ban taɓa ganin amarya irin ba tunda nake a duniya"" ya jawo ƙafar ya fara yanke mata farce ta rufe idanu." "Washegari da sassafe Fiyya na bacci daddy da kan shi ya tashe ta, ta farka da ƙyar saboda kan ta dake" "ciwo mamaki ta yi ganin kusan family a ɗakin ya kalleta ya ce ""Kin dai yi sallah ko?"" Ta ɗaga masa kai ""Daddy lafiya?"" Ya yi shiru ya ce ""Junaid je ku fara yin gaba, Captain an kira shi yanzu daga can headquarter, Ummi ɗakko mini hijabin Maama"" Hijab ya karɓa ya saka mata ya riƙe hannunta Anty Turai ta yi gaba tana zabgawa Fiyya harara har harabar gidan suka je, abin mamaki gidan shiru ta rasa meke faruwa a motar daddy suka shiga yana baya riƙe da ita Awais na jan motar da Ummi. Motar Fiyya kuma da ita Captain ya yi using wajan fita saboda shi bai Fiyya ɗaukan tashi ba. Fiyya ta yi shiru kan ta a ƙasa,har suka ƙarasu cikin babban gidan mai tarin jama'a daidai lokacin aka fito da shi daddy na riƙe da" "hannunta ya ce ""Mamana je ki masa addu'a""" """Addu'a? Daddy waye?"" Ta furta muryarta na rawa ta juya ta kalli makarar da aka ajjiye gabanta ɗauke" "da gawa, ya sake riƙe hannunta da kyau ya jata zuwa gaban makarar ya duƙa tare da yin namijin ƙoƙarin buɗewa. Fiyya numfashinta ta ji ya ɗauke lokacin da idanunta ya yi arba da gawar Ashraf dake kwance cikin makara, jira ya fara ɗaukar gangar jikinta da gaske Ashraf ne kwance ba yau aka ce za a ɗaura musu aure ba shine zai mutu anya gawar Ashraf ce numfashinta ya tsaya cak tana daga tsayen suka ji ta yi" "wani irin ajjiyar zuciya tare da yin baya cikin sauri a tare daddy da J suka tare ta, ta ƙarasa suma a jikinsu." Bayan sallatar gawar Ashraf da binne shi duk ana zaune ana addu'a daddy ya ce yana neman alfarma "don Allah suka ce tame ""Kar a tambayan hujja ko dalili a yanzu ina son a ɗaura auren Safiyyerh da Aliyu""." "*฀for now na san a ranku za ku yi ta wasu wasu, wasu ma su ce ba su gane inda labarin ya nufa ba ku" "dai nutsu tafiyar kura ce mai tsarƙaƙƙiyya har nishaɗi kuke bani idan ana comment tafiyar da hasashe ku lissafi ba zai taɓa kawowa tunanin mutum ba, kar ku ji kun karaya domin na san dole a gaba zaku buƙaci" "labarin, har yanzu shimfiɗa muke yi iya shafi 8 mukai*" Littafin MUTALLAB na kuɗi ne kuma za a ke yin posting kullum. An fara biya yau domin shiga paid group na MUTALLAB. MUTALLAB. "Book 1, 2 &3" 500 Naira 0116886423 Union Bank Na'ima Sulaiman S. A tura shaidar biya ta nan 08164069385 ku yi ku biya a sati uku mu kammala ฀ Domin gyaran nono ❤🔥🔥💃 Assalama alaikum Hajiya muna da ingantaccen maganin gyaran nono wadda ya amsa sunansa magani Maganinmu ingantaccen maganine da yake tada jijiyon nonon da suka saki y'ar uwa breast dinki ko yakai silifas saboda kwanciya kikai amfani dashi in sha Allah zakiga amfaninshi acikin 1week maganinmu powder ne yana ciko da breast y gyarasu bashi da illa ajikin mutum munyi amfani da saiwoyi da magunguna gargajiya domin gyaran breast 08063114606 ina garin kano karki sanya y'ar uwa nono yana karawa mace martaba a gurin mai gida maganinmu kowa zai iya sha wadda zatai yaye ko gyara budurwa duk zasu iya sha breast dinki ya ciko yayi bull -bull "[10/15, 2:30 PM] Nanameera: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 9 *Bright pens..2nd batch* """Bani da wani zaɓi sai na hakan, haɗa auren Aliyu da Safiyyerh kar ku tambayan dalili kar a tambayan" "cikin Safiyyerh da Aliyu waye ba ƙwayar halittata bace ta yi sanadin zuwan shi duniya, hankalina zai fi kwanciya kafin Ashraf ya kwana cikin kabari ya zamana Safiyyerh nada igiyar aure a kan ta"" ajjiyar zuciya Sharfaɗi ya yi idanunsa a kan Prof Abdu Marafa ya ce ""Me kake jin tsoro da kake so dole ka aurar da ita, Allah Ya gani amintar mu ya saka muka yanke hukuncin haɗa yaran nan aure saboda ƙarfafa zumunci, to kana taka Ubangijin talikai na tashi nasa kuma shine gaskiya, Ashraf ya rasu baya duniya ina tunanin ka bar yarinyar nan ta samu nutsuwa ta duba wanda take so yake son ta sai a yi mata aure, kar a ƙuntata" "rayuwar yarinya""" """Sharfaɗi ba zaka fahimta ba, ka yi mini wannan alfarma ka wakilci Aliyu ni zan wakilci Safiyyerh ga" "jama'a su shaida Please sai a haɗa a yi addu'a har ta Ashraf"" J zufa har yanko masa take yi na tsananin mamaki mene haɗin Captain da Safiyyerh da za a yi musu aure? Baya son zuciyarsa ta gasgata abin da yake jin tsoro ko wassafo shi cikin kan shi, Safiyyerh fa and Aliyu? Ya Allah! Shi dai Awais kan shi a ƙasa" Dr Hash daman baya wajan yana can duba Fiyya tunda ta faɗi wajan ya yi shiru can daddy ya ce """Kawai alfarma nake nema zan ji daɗin hakan idan ka yi mini""" """To shikenan, waye maɗaurin auren?""" "Daddy ya nuna wani abokinsa, Sharfaɗi ya ciro kuɗi mai yawa a cikin aljihu ya dire ya ce ""Ni Sharfaɗi ina" "nemawa ɗana Aliyu Abdu Marafa auren Safiyyerh Abdu Marafa a wajan waliyi na wannan yarinya"" daddy ya saka hannu ya ɗauki kuɗin ya ce ""Ni Abdu Marafa uba a wajan Safiyyerh Abdu Marafa na bawa Aliyu Abdu Marafa auren yarinyar wajena Allah Ya sanya musu albarka"" addu'a aka yi nan take kuma aka" ɗaura auren a gaban shaidu ma ɗaurin ya ce """Aure ya ɗauro a kan sadakin da Sharfaɗi ya bawa dubu ɗari biyu, Allah Ya sanya albarka tsakanin Aliyu" "da Safiyyerh ya kuma kaɗe fitinar da kan iya wanzuwa a tsakaninsu"" duk aka amsa da amin. Daddy ya" "lumshe idanunsa yana sauke ɓoyayyiyar ajiyar zuciya nutsuwar ta saukar masa, bashi da sauran fargaba a yanzu Safiyyerh ta zama matar wani." "Kasancewar rasuwar ɗan babban mutum ce kamar Sharfaɗi ya saka manyan mutane zuwa gaisuwa, ƴan" "kasuwa da ƴan siyasa da wanda dai suke jin kansu wasu ne a garin. Kallo kallo aka shiga yi tsakanin Hon Maɗatai da Eng Ali wali dukkan su cikin shiga ta alfarma, ga mutane da take musu baya kowanne da tarin ƴan jagaliya da ƴan daba gudun kota kwana. Hon Maɗatai ya yi murmushi yana miƙawa Ali wali" hannu ya ce """Kwana da yawa Ali wali?"" Ali wali ya ɗauke hannu sai kuma ya juya ya ce" """Ba yanzu ba ka jira na wani lokaci komai zai haska, za a yi tsawa walƙiya ta bayyana munafukan da suke" "ɓoye cikin duhun ciyayi"" murmushi Hon Maɗatai ya yi kawai yana furta ""Allah Ya nuna mana"" gaisuwa duk sukai sai dai daddy tsakaninsu kawai addu'a ya miƙewa daga wajan. Bayan yin ta'aziyya Hon Maɗatai ya ce ""Allah Ya yi wa Ashraf Rahama, ya taƙaita iya kan shi"" Sharfaɗi ya juya ya kalli Hon Maɗatai kana ya kalli Eng Ali wali sai kuma ya ce ""Amin, yanzu ba gashi ba gwanin sha'awa a dinga siyasa bada gaba ba sai an fi samun nutsuwar zuciya data ƙwaƙwalwa duk wanda zai samu wannan kujerar Ubangiji ya gama rubutawa kawai dai lalube ake yi cikin duhu ku haɗa kai da hannu kowa ya yi kamfel nasa babban jin" "daɗin ba jam'iyyarku ɗaya ba""" Cikin jinjina kai Hon Maɗatai ya yi murmushi daman shi bashi da wata matsala da Eng Ali wali shi yake "haukan shi hankalinsa na kan wanda ya yi shiru, shirun nasa kuma yana nufin babbar barazana a gare shi ""Siyasa ai ba zata haɗa musulmi irina faɗa da wani ba, munga jiya mun ga yau muna da tabbacin za muga gobe mai kyau, ni fatana na samu gurbin saka hannun jari a kamfaninka idan aka bani dama an yi" "mini komai Sharfaɗi"" daddy na jin su can aka kira shi waya da sauri ya miƙe tsaye yana neman uzurin" tafiya Eng Ali wali ya bisa da idanu. "Cikin dare Fiyya ta farka da wani irin ciwon kai na ɓari guda, ta kasa buɗe idanunta a hankali ta saka" "hannu ta dafe kan ta duk da halin cewa bai hanata yin addu'a ya yi tashi a baccin ba domin tabbatarwa da kanta ba a cikin kabari ta farka ba. ""Sannu Maama"" shine abin da Ummi ta iya cewa tana hamdala a ranta domin shirun ya yi yawa ta damƙe hannunta sosai" """Ummi kai na ciwo, ciwo nake ji a gefen kaina"" jikinta har rawa yake na tsananin ciwo Ummi ta ce" """Maama zai daina in sha Allah, bari a kira likita""" """Ummi daddy fa?""" """Yanzu ya fita, ki yi ta addu'a komai ya yi farko yana da ƙarshe, wannan ciwon kan zai daina miki" "watarana buɗe idon ki kalle ni"" a hankali ta buɗe idanun ganin yadda idanun ya yi jajir ya saka Ummi cewa ""Subuhanallahi wannan jan kuma na magani da mene?""" """Ummi jimawar da ta yi a kwance da ciwon kan shine ya saka idanun ja yanzu daddy zai shigo Fiyya zata" "ji sauƙi ki kwantar da hankali"" daidai nan daddy ya buɗe ƙofa ya shigo J na bin shi a baya da Dr Hash, ganinsu kuma ya saka komai ya dawo tunanin Fiyya ta runtse idanunta tana jin fargaba na saukar mata. ""Da gaske Ashraf ya mutu daddy? Da gaske an binne Ashraf babu Ashraf ya mutu yanzu haka yana kwance cikin kabari mijin da zan aura ranar ɗaurin aurena ya mutu daddy na shiga uku"" daddy ya kama" hannun Fiyya cikin nutsuwa ya ce """Laa, sam ba ki shiga uku ba tana iya yiyuwa ya shige iyakar shi ne, kuma mutuwa a hannun Ubangiji" "take idan lokacin ya yi kota wacce siga ce dole wannan rai ya koma wajan wanda ya samar dashi, Maama da gaske mijin da za ki aura mutu ki sawa ranki haƙuri ki yi masa addu'a ki saka salama ki ɗauka bashi ne zaɓinki ko alheri gare ki ba, Ubangiji na yin komai a lokacin ya yi niyya babu mai tuhumarsa hujjar hakan domin shi ishasshe ne ki yi addu'a Safiyyerh Ashraf is no longer alive pray for him"" juyawa Fiyya ta yi ta zubawa daddy manyan idanunta wanda yake cike da hawaye da ƙyar ta ce ""Ashraf ya mutu ya bar ni cikin zullumi daddy, inama tuntuni aka ɗaura mini aure da shi, innalillahi wa'inna ilaihirraji'un wayyo ni" "Safiyyerh""" """Zullumi na me kuma Safiyyerh kin ga abubuwa da yawa a rayuwa sai mutuwar Ashraf zai tsaya miki? Ba" "za ki yi addu'a ki sawa zuciyarki sallama, kuma wani hanin ga Allah baiwa ne kamar yadda aka sanar yau ɗaurin auren ki da Ashraf Allah bai yi ba, haka kuma alƙawarin Allah gaskiya ne igiyar auren wani ta hau kan ki Maama"" ta yi shiru don ta tabbatar daddy ba zai fahimce ta ba, ba zai gane me take nufi ba, ta yi missed Ashraf tun ba'a je ko'ina ba ta ji inama ita Ubangiji ya ɗauki rayuwarta ya bar Ashraf ko da bai aure ta ba, babu mamaki ta dalilinsa wani ya san abin da yake ɓoye gashi ta mutu ya barta da wani irin" damuwa ba tare daya bar mata ƙofa ko ɗaya da zata gane ba komai ba. """Daddy me ya sa ka haɗa aure na da Ashraf tun fari?"" Daddy ya kalli Fiyya cikin kwantar da hankali" """Saboda ya cancanta kuma ya dace Maama ki yi shiru da wannan maganganun duk zafin ciwo ne yake sawa kike furta su kamar saukar ruwan sama ki yi addu'a"" ta jinjina masa kai a hankali ta zare hannunta daga cikin nasa idanunta rufe sai sauke numfashi take yi ba tare da ta ce komai ba ta juya ta kwanta maganganun Ashraf na dawo ba, a ranta ta dinga masa addu'a ita bata taɓa sanin bashi da lafiya ba, he" never told her he was sick innalillahi. Dr ne ya shigo zai yi magana daddy ya yi saurin girgiza masa kai alamar kada ya ce wani abu serious Dr "ɗin ya zubawa Safiyyerh idanu ya ce ""za'a sallame ta yau kamar yadda ka buƙaci baka son kwana zan" "mata allura amma before""" """Thank you Dr""" "Dr Hash ya miƙe ya ce ""daddy zan je asibiti ina da aikin dare Awais zai yi dropping nawa bana jin daɗi""" "Ummi ta ce ""Kuma baka jin daɗin zaka tafi kamar dole ka yi kwanan tsaye ba'a ɗaukan uzuri ne"" ya ɗan yi murmushi kawai ya ce ""Ummi ai ba zai yiwu na amshi kuɗi na ƙi aiki ba, sai Ubangiji ya kama ni da" "wannan hakƙin ki yi addu'a zan iya"" ta ce ""To Allah ya sauwaƙe ya bada sa'a ya kuma kare""" """Amin Ummi""" "Dr ɗin ya yi wa Fiyya allura ta samu bacci mai nauyi, Ummi dai kallon daddy take jin ya kira Aliyu ya zo ya" "ɗauki Fiyya nan da 20 minutes shi zai tafi tare da Ummi har lokacin Aliyu bai san da batun auren ba kamar yadda Fiyya bata ɗauki maganar daddy serious ba. Ya gyara mata kwanciya ya miƙe Ummi ta miƙe tana shafa kan Safiyyerh a haka suka fita. Har wajan ƙarfe 1:30 Fiyya na kwance tana bacci lokaci zuwa lokaci wata nurse ke shigowa duba ta. Yana tsaye hannunsa biyu zube cikin aljihu ba zai ce ga abin da yake tunani ba, amma fuskarta kawai yake kallo ganin yadda a bacci ma take ɓata rai ta sauke ajjiyar" "zuciya, ƙofa aka buɗe ya yi saurin yin baya yana kame fuska sosai." "Dr ya kalli Captain ya ce ""Sai yanzu na ɗauka ma ko a nan zata kwana"" Aliyu dai ya yi shiru ya zaro waya" "ya fara dannawa ""ga maganganun nata wannan za a yi amfani da shi lokacin...,"" ""Ka kira su, sai ka musu bayani"" shi daya tsaya tunanin yadda zai tashe ta yake ga daddy sai kiran shi yake banda haka da ba zai zo bama, ya saka ƙafa ya fara zungurun gadon dr ya ce ""Allurar da aka yi mata nada ƙarfi sai dai ka ɗauke ta"" siririn tsaki ya yi ""to ɗauke ta kai"" ganin fuskar Aliyu cikin serious ya sa dr ya nufi Fiyya zai ɗauke ta zuwa waje kafin ya ƙarasa kawai yaga Captain ya saka hannu da drip ɗin da mayafin nata ya ɗaga sama ta zabura ta yi saurin riƙe shi Idan ba kuskuren ji ya yi ba ya ji kamar ta ce ""TAHHB"" ya sata gaban mota" ya kwantar da kujera kamar wanda ake bi haka yake jan motar. **** Yana durƙushe ya tsattsare mutumin da jajayen idanunsa wanda suka shige ciki alamar a buge hannunsa riƙe da askira gefe kuma jibgegen karan shi Tiger ne da duk a cikin karnukan ya fi son shi. Ya saka askira ɗin a cinyar mutumin ya nutsa jini ya fara fita sosai yana ihu da kururuwa cikin tsakiyar daren ga duhu ko'ina ya ce """Wai me ya sa baka da imani ne, zaka raba mini cinya biyu""" "Duk da cewa a buge yake amma tar ya buɗe idanunsa, cikin muryarsa da kana ji ka san shi ba ma'abocin" magana bane da wani kalar sautin mai kama da gurnanin zaki ya ce """Ka gane ni yanzu?"" Ya jinjina kai yana wani irin nishi da kakari kamar na mutuwa ya ce ""Na gane na" "gane, wallahi na gane ka""" """Good"" ya sake nutsa askirar ya yi feshi kunama ta faɗo ta shige cikin wandon birnin ya ce ""Sanda aka yi" "mini baru ma'ana aure, da nazo kai na ganin bakin ƙofar gidana, haka ne?"" Ya sake faɗa yana ƙara cilla masa wata kunamar baƙa ƙirin ta sake shigewa cikin wandon mutumin, Darma da Goje sun tale shi" kowanne ya take hannu ɗaya mutumin ya yi shiru hakan kuma ya sake fusata Moh ainun """Idan aka bani ciwon kai hauka nake yi ba zaka ka ji daɗi ba, a yunwa ce nake, yi batu"" kamar zai mutu" "cikin kakarin mutuwa ya ce ""Zan yi, zan yi magana"" suka sake shi suna kallon shi." """Mutane kala biyu ne suka shigo a wannan daren da aka kawo ta, na farko sun bani kuɗi fuskar su a rufe" "take na biyun ma sun sake bani kuɗi suma fuskar su a rufe take amma sun bani saƙo na baka tun a wannan lokacin, bayan an kama ka na rasa wa zan bawa na dinga bulayi kawai na haƙura, daga baya kuma aka zo aka sake cewa na bada wannan saƙon na ce a'a sai sukai mini tagoma shi da kuɗi har miliyan ɗaya kawai na basu ai kan ƙasar nan yadda muke fama da babu da yunwa ga iyalai ina dasu" "kawai na amsa na bashi""" "Darma ya ce ""ka ji kimini ƴan yankin nan ba za ku gama da duniya lafiya ba, da ƙyar kusha ruwan" "alkausara"" Moh ya zubawa mutumin jajayen idanunsa sai kuma ya miƙe tsaye magana yake son yi amma ta maƙale a harshen shi da ƙyar ya ce ""Ku yi masa ɓalli-ɓalli"" yana cewa haka ya juya." """Baka ji ba, ai na haddace abin da aka rubuta harafi uku ne a jiki. A.M.A, sai wani suna nada ban kamar" "sunan asibiti kamar sunan unguwa idan na tuna zan zo na faɗa maka amma don Allah kar ku yi mini komai a tausaya mini sabuwar amarya ce dani""" """Ni tawa matar ko kwana ban yi ɗakinta ba, duk irin gwagwarmayar dana sha, uhmmm"" ya yi shiru a" lokacin sautin muryarta yake ji na kakarin mutuwa a kunnensa can ya miƙe kawai ya yi gaba. Goje ya ce """Zan dinga zuwa lokaci lokaci domin kana cikin taskar Moh""" "Da sauri suka bi bayansa ganin har ya yi nisa sosai ""Mai dawa daman ka iya yaran nasara na ji ka ce" "Good""" """Na yi kala da wanda iya turanci ko mota ko amfani da waya ne?"" Kallon tsaf sukai masa Darma ya ce" """Ciki ne kai yasin sai fama kake da kan ka ba wannan maganar a basar kawai ya maganar ɗawan nan?""" "Kamar zai yi shiru sai ya ce ""Bana son sabga da mace zan iya kashe ta kamar yadda itama ɗayar na kashe ta""" "Darma ya fashe da dariya sosai yana kaɗa kan shi ya ce ""ba wannan ba wallahi wata figigiya da ita, suma" "dai basu da man kai wai ita ce manja"" Goje ya ce ""matsalar kai daƙiƙi ne ajawo sam ciki ne kai, manager ake cewa dake mayen garau garau ne kai wai manja ai uwar manja gaja kawai"" Darma dai bai kuma Goje ba ya ce ""Maganar gaskiya wannan za a iya karya mata ƙugu a wajan ɗakko ta ma sille kenan, Mai dawa ko kai baka ganta bane"" Ya yi musu shiru yana jinsu dai ""Sai godiya, ina magana baka ganta ba wata ƴar" "shila da ita?""" """Ita wa?""" """Manja ɗin""" """Idan ka ƙara ce mana manja a wajan nan za kaga manja ganin idanunka, ɗan wahalar yaro kawai""" "Mutallab dai idanunsa a lumshe tunanin da yake yi daban, kalmomin da mutumin ya faɗa masa nata yawo a cikin kan shi. A.M.A Ya kasa fahimtar kowanne harafi me yake nufi sai kawai ya taune bakinsa ƙirjinsa na buɗewa duk jikinsa tsami yake masa ya buɗe idanunsa ya kalli sama yana ganin yadda" gajimare ke gudu yana haɗewa tare da warewa muryarsa bata wani fito sosai can ƙasa ya furta kalmar. """her eyes look alike, tiger""." Washegari misalin 12 na rana Safiyyerh na saman bene cikin ɗakinta ta dinga kallon Kinal bata da "nutsuwa sosai da babu abin da zai hanata yin dariya. Kinal ta share hawayenta tana ɓata fuska cikin sanyin murya ta ce ""Kalli yadda sukai mini da fuska daga tambaya na ɗauka za su faɗa mini ashe ƴan" "wahala, ni bada wata munufar na je wajan su ba wallahi kawai su bani amsa na ƙara gaba""" """To ga amsar nan ai""" """Maama fuska ita ce kyan mace fa, yanzu idan tawa ta lalace waye zai aure ni haka? Sun kusa tsaga mini" "baki gashi yanzu ina da aiki a ƙasa sosai har Hon Maɗatai zan yi wa waƙa"" Safiyyerh ta yi shiru tana tunani so take ta fice daga cikin gidan secretly amma no way ""wai ina magana kina ji ba zan shariyar nan naki damuna yake, na zo ɗebe miki damuwa da kewa na rashin Ashraf kamar yadda Ummi ta buƙata duk" "da ciwon da bakina yake mini ina da zuba ke kina ignoring nawa for God sake""" """Idan ba ƙi auro ba sai ki auri ɗan daban kawai"" Kinal ta yi tsaki ta ce ""Kuma zan iya, mene a ciki""" """Shi auren ɗan daban?"" Fiyya ta buƙaci amsa tana kallon Kinal. Kinal ta ce ""Deal, nama yi miki alƙawarin" "in dai ina da numfashi wallahi wallahi sai na auri ɗaya daga cikin ƴan daban nan, kamar ni mawaƙiya za" "su yi wa haka? Uhm"" Fiyya ta lumshe idanu ta buɗe deep down ƙirjinta na bugawa sai ta ce" """You most like them ma, ƴan daban ai sun iya soyayya""" """Ke ta ya kika san sun iya?"" Shoulders kawai Fiyya ta ɗaga ba tare da ta ce komai can ta sauke numfashi" tana kallon Kinal ta ce """Kinal Ashraf ya rasu, mijin da zan aura ya bar ni Kinal ina cikin damuwa ina jin da old Safiyyerh ce ba zan" "ce ina cikin damuwa ba, gwara ta kashe ni haka nake ji"" Kinal ta jinjina kai ""Fiyya something is over doesn't mean your life is over, ki yi haƙuri mu ɗauki ƙaddara ki yi wa Ashraf addu'a Please kar ki saka damuwa wani abun ya zo yana damun ki daman ke idan kika birki ce kamar mai ƴar mero a ka, ƙaddararmu zata zama mai kyau muna tare da addu'ar iyaye ai"" sun jima tare da Kinal har yamma kana" ta tafi gida tana jin dole ta sake komawa wajan ƴan kodin ɗin nan. "Da ƙyar da daddare Fiyya ta sakko ƙasa bayan tayi sallar issha tana sanye da hijabi har ƙasa, fuskarsa" looking ok ba yabo ba fallasa sai dai ta faɗa idanunta ya fito akwai damuwa a tattare da ita. Inda ta yangi "su J ta nufa ta shiga tsakiyar ƴan mazan ta zauna a nutse ta ce ""Sannun ku"" Awais ya ɗago ya kalleta ya" "ce ""Yawwa Manager ya ƙarin haƙuri?"" Idanunta ya juya ta cije baki ta ce" """Allahamdulilah,thank you"" daddy dake kallon ta cike da tausayi ya ce ""tashi a nan wajan Safiyyerh""" """Daddy me ya sa?""" """Ki dai tashi na ce ko?""" "A sanyaye ta miƙe sai kawai ta yi sama ya bita da idanu a hankali ta ce ""Sai yaushe zaka faɗa mata batun" "auren?"" Daddy ya ce ""Da sai an kammala Visa ɗin ta, na san wacce take da ita a baya ta yi expired, to Safiyyerh stubborn girl ce da na yi maganar visa zata kalli cikin idanuna ta fara mini turanci wayonta tsoro yake bani, kuma yanzu i feel very comfortable da Aliyu matsayin mijinta duk da basa shiri amma ba" "zai ɗaga mata ƙafa bana son dai ta yi rayuwa a wajan shi kamar Prisoner, za ta yi shakkar yi masa abu""" """Kana ganin zata amince da auren?"" Ya miƙe tsaye yana haurawa sama ya ce ""In sha Allah"" daman daga" sallah ya dawo shine ya zauna. J dai baya uhm baya uhm'uhm abubuwa da yawa ke yawo a ƙasa wanda baya rasa nasaba da tunanin wace Safiyyerh waye Aliyu? "Ummi ta kalli yadda ya shigo ba wanda ya kula kamar bai ga kowa ba ta ce ""Aliyu tun safe ina ka je ne?""" "Ya buɗe ido ya yi shiru ta ce ""Kuma ka ci abinci ne? Kodayake ba'a tambayar soja ko ya ci abu da za'a buɗe cikin ka duk ganye ne"" kallon Ummi kawai yake kuma ya yi shiru" """Yaushe zaka tafi goben?""" """A'a, night Ummi"" ya ce yana shigewa cikin ɗakin shi dake part ɗin mazan." Fiyya ta ci kuka a ɗaki kamar rai da sauri ta buɗe system ɗinta taga saƙo a e-mail nata tun sanda sukai last called da Ashraf bayan hakan ta minti ashirin da wajan biyar. Maganar daya tura mata ya saka ta buɗe idanu sosai. "_Safiyyerh daddy ya zo ya fita yanzu, ko ma dai menene ki tabbatar ba ki bawa wani damar mallakar FS" "WORLD INVESTMENT COMPANY ba Fiyya mutane biyar sune mamallakan wannan kamfanin mutane masu haɗari ko ni ban san su ba, da ina da yadda zan yi a yanzu zan faɗa miki komai domin sauƙaƙa miki," "ki fara nemo ma'anar FS shine key ɗin binciken, don't cry when you miss me i love you""_" "Safiyyerh was shocked, thinking me ya saka Ashraf ya yi mentioned sunan daddy a lokacin, meke shirin" "faruwa ne gabaɗaya kan ta ya ɗauki zafi da gaske ta yi rashin Ashraf sai yanzu ne take jin gudun zuciyarta na ruɓanya aikinta a kan Ashraf ɗin. Ta kwanta tana rufe idanunta ƙarar notification na wayarta ta saka ta buɗe idanu tana janyo wayar a hankali, rubutu a taƙaice mai ɗauke da azanci da ɓoye manufar abin" da ake so a bayyana. _“laifi akan laifi again? Kodayake shi laifi tudu ne Safiyyerh ke inuwar wani ce ki yi ƙoƙari kar a saka ki shiga wuta”_ "A gigice ta ce ""Na shiga uku ni Safiyyerh""" **** Cikin dare ne wajan biyu da arba'in motarsa na gefen titi cikin duhun daren ya saka facemask ya rufe "fuskarsa tsoro da fargaba ya gaba gitta masa zuciya a hankali ya zuge glasses ɗin motar babu mai cewa shine a ciki, yana buɗewa ya faɗo cikin motar ya ce ""Kira cikin dare? Ban fiya son ina tsaka da wani aikin" "kuma ana kira na wani ba, ya akai?""" Photo ya fito masa da shi na wani kyakkyawan yaro fari tas da shi idanunsa buɗe ya shagwaɓe fuska tare "da miƙa hannu alamar a bashi wani abu, yana sanye cikin wasu ƙananun kaya baƙaƙe. ""Na gani photon" "waye? Wannan yaron fa?""" """Ɗan gidan Safiyyerh ne"" ya furta yana lumshe idanu tare da yin baya ya jingina da kujerar zuciyarsa na" "buɗewa sosai tsoro da fargaba na cika shi ""What! Safiyyerh yaronta kuma?""" """E, idan kaga Safiyyerh ka gan shi kamar an yi kaki ban san ko ta san da yaron ba a tabbatar an gano mini" "inda sa Safiyyerh take""" "Kwanakin wajan biyar da rasuwar Ashraf daddy bai faɗawa Fiyya batun auren ba, haka ma Aliyu Fiyya" "kullum sai ta fita wajan aiki ba kuma ta dawowa da wuri. Yamma wajan magariba take driving a gajiye take sosai fahimtar ana bin bayanta ya saka ta ƙarawa motar giyar da sauri ta ɗakko waya number J ta fara kira amma bai ɗauka ba, ta shiga kiran ta daddy amma a kashe duk wanda take tunanin kiran" "number shi a gidan ta kira bata samu ba," "ta kalli madubin taga har yanzu motar na biye da ita, tare da wasu babura biyu bata iya hango fuskar" "mutanen amma kallo guda ta yi musu ta san ƴan daba ne, ko dai masu satar mota ne ko satar waya ta shiga uku. Baburan guda biyu suka cimma ta ɗaya ya saka hannu ya daki glasses motar nata, ta yi gefe tare da ƙarawa motar gudu suma suka take mata baya a lokacin tsoron da ya yi mata yawa ya saka ta fara gani dishi dishi kan motar na neman kwace mata, cikin sauri tana ƙanƙame steering ta shiga lalubar numbersa bata da tabbacin ko tana da ita cikin sa'a ta gani ta danna kiran sai da ta yi kiran biyar bai" "ɗauka ba, gashi hanya babu mutane a kira na shida ya ɗaga cikin ɗaga murya da fitar hayyaci ta ce" """Yaya na shiga uku Captain wasu ne""" "Ya yi mata shiru can ya ce ""Who are you?""" """Yaya Safiyyerh ce wasu ƴan daba suka biyo ni gashi titi babu kowa, Captain suna da yawa wasu a babur" wasu a mota na kira number kowa a gida basu ɗauka ba gashi ciwon kaina kamar zai tashi bana ganin "hanya sosai kan motar ƙwace mini yake"" ta cikin wayar Captain ya yin siririn tsaki can ya ce" """Ina ruwana?""" """Captain kashe ni fa za su yi innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!""" """Allah Ya ji ƙan ki""" littafin MUTALLAB Na kuɗi ne we're still on free pages. Ka biya a yi adding naka a paid book before mu yi cutting free pages ɗin. MUTALLAB. "Book 1, 2 &3" 500 Naira "0116886423 Union Bank Na'ima Sulaiman S. A tura shaidar biya ta nan 08164069385[10/17, 8:12 PM]" Nanameera: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥* Page 10 *Bright pens..2nd batch* """Kamarya Allah Ya ji ƙai na, Captain ina faɗa maka biyo ni ake yi za'a kashe ni, kana cewa Allah Ya ji ƙai" "na, i called you saboda na rasa wanda zan kira Please help me"" ta cikin wayar Captain ya yi tsaki ya ce" """Kee, ina ruwana idan sun kashe ki who cares about your life, zan kira daddy a ɗauki gawarki ok"" kashe" wayar ya yi. Safiyyerh wani irin zafi ta ji a zuciyarta da raɗaɗi bata san ma wanne gurbi zata saka Aliyu ciki ba idanunta ya kawo hawaye baƙin cikin kiran da ta yi masa tana zargin kanta da laifinta ne. Ta cikin madubin motar take sake kallon motar dake bib bayanta da kuma sauran baburan ta runtse idanunta a "fili ta ce ""Ya Allahu Ya Rahmanu ka dubi Safiyyerh ka kawo mata ɗauki..Daddy!""" Ta kira sunan daddy a gigice tana sakin steering motar bata sake sanin abin da ya faru bayan nan ba. Yana tsaye fitowar shi daga motar kenan ya dubi yadda ta yi flat kwance a ƙasa gefen kanta da jini ya "kalli sauran jami'an tsaron da suke wajan ""Is she ok? Tana numfashi?""" """She is, buguwa ne kuma Allah Ya rufa asiri motar ta tsaya da kanta, ba'a yi nasarar kama ko mutum" "ɗaya ba, yarinyar ce dai bamu san wace ita ba za mu duba id card nata sai a kira iyayenta a shaida musu ko asibiti ne a tafi da ita"" ya yi maganar cikin girmama kan shi a ƙasa, wanda ke tambayar ko Fiyya na raye ya yi baya rungume da hannunsa can ya duba a gogo sai bai ce komai ba ""Sir meeting ɗin naka? Ina tunanin ka je kawai za mu kula da komai tunda shugaban jam'iyya da secretary na jam'iyya na jiran zuwan naka"" kafin ya yi magana cikin sauri wata mota ta ƙarasu wajan kamar zata tashi sama ko gama daidaita tsaiwar motar bai yi ba ya fito idanunsa a kan Safiyyerh, mutumin ya dubi fuskarta shima a" hankali kuma ya ce. """Easy Captain, ka kira ni sanda muke kan titin da take ta kuɓuta Allahamdulilah"" jinjina kai Aliyu ya yi" "cikin girmamawa ya ce ""thank you""" """Anything for you Aliyu, amma ku kula tana da harshe zuciyar nan tata irin take ce, Allah Ya bata lafiya""" "Aliyu dai na tsaye idanunsa akan fuskarta ya kasa magana har mutumin ya shiga motarsa driver ya ja, jami'an tsaron suma suka shiga motar suka marasa masa baya cikin tafiyar sirri. Ya jima yana kallon ta hannunsa riƙe da wayarsa tunanin yadda zai yi da ita, ƴar mitsitsiyar yarinya ta fito da shi, banda darajar daddy da babu abin da ya yi masa zafi sanin cewa idan Fiyya ta mutu hakan na nufin tsayawar numfashi daddy ya saka ya lallashi zuciyarsa. Cak ya ɗauke ta ya saka ta a gaban mota yana yin baya da kujerar a" "ransa ya ji ba zai zama drivernta ba, ya ɗauki wayarta ya rufe motar yana shiga ya tare da zama ya sake" juyawa ya kalle ta da kyau sosai jinin ke fita a goshin nata ya taɓe bakinsa kawai a hankali kuma yana ɗora mata tissue ya furta “Fitinanniyya... Safiii” "Farar safiya ce gari ya yi shiru amma shi idanunsa biyu, yadda ya ga dare haka ya ga rana idanunsa tarwai" "a sararin subuhana yana kallon sama da abubuwan da Ubangiji ya wanzar a cikinta, a hankali ya juya ya kalli Darma da Goje sai kuma Mangal dake can gefe guda ya sha ta gaya masa babu daɗi sai lilo yake da ƙafarsa a sama. Mangal ne ya buɗe idanunsa da sauri ya miƙe zaune yana murza idanunsa alamar bai" gama wastsakewa ba. """Jeji naka dawa taka ka huta mai dawa, ba dai gaba da gaba ko ta baya ƙaryar mutum dan uwatar ya aka" "yi ba ka yi kasa bane ka raya daren da gadin mu?"" Moh ya yi shiru ƙirjinsa sai ɗagawa yake. ""Ina tsoron shirun nan naka don ba zai haifar da ɗa mai ido ba, ka tara dafi a cikinka jira kake ka samu inda zaka sauke ƙarin dake damun jikinka ka sarara a kaiwa mai duka lillahi kukan kawai"" sai a lokacin ya juyo da gajiyayyun idanunsa da suka shige ciki duk girman da suke da shi, sun yi wani bala'in ja ya zubawa" Mangal ido """Talk da turanci kenan da hausa na goga maka yi magana sarkin jeji""" """Mangal""" """Yes inji masu jajayen kunnuwa bi ma'ana na'am"" muryar Moh bata fita sosai a lokacin duk wanda ya" "nutsu zai hango wani irin sanyin murya da yake da shi da sauti maraya hayaniya. ""Wacce cuta aka taɓa yi maka a rayuwa wacce ba zaka iya yafewa ba?""" """Kan uban nan, ni ai ka sani a kusurwa kaina ya kulle wanda sukai mini kuma tuni sun girbe abin da suka" "shuka bana yafiya bana cuta bana bari a cutan"" cije baki kawai Moh ya yi yana lumshe idanunsa da sauri ya buɗe su tar saboda yadda yake jin kakari da numfashin fitar ranta yana yi masa amo a kunne, ya mirgina kaɗan ya ɗauki ƙafarsa ɗaya ya ɗora akan ɗaya yana girgiza wa ya zubawa zara-zaran yatsun" ƙafarsa idanu tare da rungume hannayensa a ƙirji. """Wai what happened Mai dawa?""" """Ka dai na yi mini turanci don uwarka""" """Ɗan tsinanniya ba, ba uban da ya iya kuma ya san ai duk bama ji shima a Legas ya koya"" cewar Goje" "yana farkawa tare da zama dukkan su babu wanda yake da niyyar miƙewa domin yin sallah. Goje ya kalli Mutallab ya ce ""Yaushe za a kwalo berewar nan ne? Ka yi shiru karfa ka jiƙa masa aiki""" Da sauri Mutallab ya kalli Goje jin sunan daya kira na barewa ya lumshe idanu ya buɗe zuciyarsa na "bugawa sosai sai bai ce komai ba can dai ya miƙe zaune a hankali kuma ya tashi tsaye ya zaga bayan katanga ya daɗe kafin ya dawo wajan Darma ya kalli hannun Mai dawa ya buɗe idanu ya ce ""Bura... Wannan ƙwayar ka shanye to kwarankwasa ka shirya zama mahaukaci, ƙwayar doki ce fa? Wai kashe kanka za ka yi akan wasu ƴanƴan jakuna ka fito musu gaba da gaba mana, a yi komai duk abin da zai faru" "ya jima bai faru ba, ƙarshe dai gidan ɗan kande ne kuma mu ba wai baƙin ta bane""" Mutallab ya tsaya cak a tsakiyar wajan naman jikinsa na motsawa musamman kakkauran ƙirjinsa mai "faɗi sai kawai ya shagiɗe bakinsa gefe kamar zai yi murmushi da sauri ya tsuke fuska zuciyarsa na tuna masa shekarun da suka shige a fusge ya furta ""Sai godiya"" gabaɗaya suka miƙe tsaye suna maimaita" """Sai godiya""" Basu fargaba sai ganin tarin wasu ƴan daba suka gani suna fitowa daga wasu lunguna a ƙalla sun fi su "ashirin ɗauke da gorori wasu wuƙaƙe. ""Dara ta ci gida lallai an raina mu, mu wasu daƙiƙai zasu kawowa" "farmaki har lukanmu?"" Cewar Darma Mangal ya kalle su ya ce ""Kuma suwaye ku yara?""" "Wani daga cikin su ya fito ya tsaya a gaba ya ce ""Sanin sunana ko waye ni bashi da wata fa'ida a gare ka," "da zaka tambayi wanne kalar kisa zan maka zai fi maka, amma saboda gudun tilawa ko tafiya ƙiyama da tunanin wanda ya kashe ka lallai zan goga maka sunan nawa"". Ya zaro wuƙa daga cikin ƙugunsa idanunsa akan Moh da bai ma kalle su ba sama kawai yake kallo yana jin yanayin na yi masa daɗi ya ɗora da ""Uban ƴan daba nake maganin ƙananun yara masu ɓoyewa a saƙo, to cut you short sunana Lauje, ban duƙo dan na saka muku makami ba, na zo na tafi da uban gidan naku salin alin akasin hakan wajan bijire mini zai" "saka an samu kwacewar lissafi dar kenan"" wanda ke kusa da Lauje mai suna Modara ya ce" """Ka saɓo shi a wuya mana sai ka tsaya ɓata yawun da Ubangiji ya halitta a bakinka Oga?""" """Ban zo don rigima ba, bisa umarnin Hon na zo wannan shine""" "Darma ya matsa gefe yana nuna musu Mai dawa Moh kenan ya ce ""Bisimillah gashi nan kuje da shi kuna" "da hannu na san"" Moh ya sake juya musu baya maganganunsu da gaske ciwon kai da zafin zuciya suke" ƙara masa hannunsa kawai yake dunƙulewa yana hura iska sama ko yaushe ya zama sa'annin yara irin su Lauje? """Ji mana""" "Mutallab ya juyo yana gyara tsaiwa idanunsa a birkice Lauje ya dinga kallon Mai dawa, shi bai ya yi" tunanin haka yake ba yaji ana Mai dawa da Mutallab sai ya ji sunan Mutallab kamar na ƙananun yaran "ganin Mutallab cikakken namiji a tsaye mai kakkauran hannu da buɗaɗɗan ƙirji gabaɗaya jikinsa a murɗe yake musamman damtsen hannun ya basar ya ce ""Shige muje""" "Da hannu Mutallab ya yi masa alama da ya zo ya tafi dashi, Lauje ya nufi wajan Mutallab ba tare da sanin" "cewa akwai shafin hannu a jikinsa ba ganin ba wani makamani hannunsa ya saka ya nufe shi. Yana miƙa hannu da sunan kama shi Mutallab ya yi masa wani naushi a gefen ƙirji, nan take Lauje ya fara fari da idanu ƙashin gefen ƙirjinsa ya yi ƙara ya sulale a wajan ba numfashi. Ganin hakan ya saka su Modara ja" baya a tsora ce ya ce """Kut ya bazar dashi ba, wannan mahaukaci ne""" """Bai mutu ba tafiyar zango ƙalilan ya yi kawai ya samu karaya a ƙirji, kar dai ku manta da Mai dawa kuke" "magana masu jeji da namomin jejin da kansu matsalar gajanci kenan kun tari mutumin dake da shafi a hannunsa duka ɗaya ka sume gwara ya saka maka kaifi daya saka hannu, ya zame muku hadda. Yi batu" "waye ya aiko ku?""" """Hon Maɗatai""" """Wani abu ne haka? Me za a yi masa?""" "Modara ya ce ""Bamu sani ba, ya ce yana buƙatar ganinsa shi kaɗai kuma a sirrince""" """To ba zan zo ba""" "Cewar Moh yana cije bakinsa hannunsa har yanzu rawa yake baya son yin kisa, idan ya riƙe wuƙa bai san" "me zai iya yi ba kuma sam. Da mamaki Modara ya ce ""Kasan waye hon Maɗatai kowa? Wallahi taimako" "zai baka shine kawai yake jin tausayin ƴan daba irin mu""" """Ɗan daba irin ka dai, shi Malam Abdullahi ne balle ya yi mini baki, ko Malam Abdullahi can ta matse" "masa"" Modara ya buɗe baki da nufin sake magana ""Kana kira mini sunansa sai na yi maka sabuwar kaciya"" ba shiri ya tsuke bakinsa suka ja Lauje tare da barin wajan cike da takaici." "Safiyyerh na kwance tana bacci tun bayan sallar asuba da ta yi, Dr Hash ya sake ɗaura mata ruwa a" "hankali kuma ya ji tana surutai ƙasa-ƙasa ya kasa kunne da kyau ko zai ji mene take cewa ""Ashraf ka taimaka ka dawo ka faɗa mini ma'anar FS, ka faɗa mini suwaye mutane biyar ɗin da kake magana akai, Ashraf the company is belong to your father,ko a mafarki ne ka faɗa mini ko a fatalwa ne ka zo mini bazan ji tsoro ba, Ashraf i really really need your help, don ka dawo"" Dr Hash ya juya ya kalli daddy da ya" yi ƙasa da kan shi """Daddy akwai damuwa fa, meke faruwa da Fiyya ne? Me take buƙata wajan matacce ne Ashraf zai fito" "daga kabarinsa kuma ya yi mata, daddy Ashraf ya rasu fa ranar da za a ɗaura musu aure da Fiyya me ya sa ba za ta yi tawakakkali ba, me ya sa wai?""" """She loves him so much, tana son Ashraf ne shi ne dalili"" cewar daddy yana sake matsawa tare da zama" "a bakin gadon ya kama hannun Fiyya ya riƙe cikin nasa da kyau ""wannan zafin hannun fa? Her temperature is too high, bana son zazzaɓi a jikin Maama ka yi wani abu Dr Hashim"" Dr Hash ya ce ""Ciwon kanta da bugawar ne ya saka mata zazzaɓi, na yi mata allura zuwa anjima zai sauka ai""" "Maimakon Fiyya ta yi shiru sai ta cigaba da surutan sosai tana furta ""Ni ba Tiger ba ce Tahhb, why are" "you decided to call me Tiger?"" Kamar a gaske kamar kuma yanzu ne ta ji saukar muryarsa a tsakiyar kanta, sautin ya sauka a ƙirjinta ""Saboda ke matar Moh ce Tiger, zama matar Moh is not easy we most fight together halinki irin na tiger ne, matar Moh"" tar da buɗe idanunta a gigice a kuma sauti na ruɗani" "ta ce ""Motar Moh""" Daddy da Dr Hash suka kalli juna jin abin da ta furta kafin su yi magana Safiyyerh ta juyo ta kalli daddy sai "ta yi murmushi mai kyau wanda suka jima basu gani a saman fuskarta ba, ainahin murmushi da kyawun Safiyyerh daya shuɗe ya dawo fil ta riƙe hannun daddy a nutse ta ce ""His voice daddy, muryarsa ce""" """Shi wa?""" """Tahhb"" daddy ya yi murmushi yana shafa sumar kanta ya ce ""ai kuwa na ji nima, ki yi bacci Maama za ki" "samu sauƙi in sha Allah"" ta jinjina masa kai tana riƙe da hannunsa har lokacin ta ce ""In sha Allah daddy," "in sha Allah daddy"" jikinta ya saki ta koma bacci daddy ya sauke numfashi ko samun sukunin karyawa bai yi ba, ya dubi Dr Hash ya sake duban Fiyya ya ce ""Ka yi mata allura kafin ta farka""" """Daddy ka duba Maama tana cikin damuwa ba, baka jin allurar zai saka ta dawo da ɗabi'unta na baya" "daddy yin allurar ba mafita ba musamman ga lafiyarta, tsayin shekaru na daddy har yaushe ne ka duba Safiyyerh don Allah"" miƙewa tsaye daddy ya yi ya ce ""Ka yi hakan Dr Hashim Abdu Marafa, completely tsayin rayuwa haka nake son ganin Safiyyerh"" jinjina kai Dr Hash ya yi sai ya haɗa allurar har guda biyu ya juya bayanta ya caka mata cikin sauri ta ƙanƙame jikinta wani irin azaba da raɗaɗi take ji a duk sanda aka yi mata allurar. Yana yi mata ya fice ba tare daya sake kallon daddy ba. Ya zubawa photonta idanu" yana juya mata baya a hankali ya ce """Ki yafe mini Safiyyerh ki fahimce ni ki fahimci mahaifinki, i am sorry Safiyyerh"" fita ya yi ya rufo ƙofar ya" nufi parlonsa a zaune ya tarar da Ummi tana kallon shi ta ce """Ya jikin nata? Ta farka ne?"" Ya zauna yana numfasawa ""Ta sake yin bacci, ina Aliyu?"" ""Kasan sai ya yi" "niyya yake shigowa"" daddy ya ɗauki wayarsa ya kira number Aliyu yana ɗagawa ya ce Aliyu zo mana ya ajjiye ya kalli Ummi cikin kulawa ya ce" """Ina jin kamar haɗa auren Aliyu da Safiyyerh na yi kuskure ina jin kuma hakan shine mafita, ina jin tsoron" "tambayar da dukkan su za su yi mini wacce bani da amsar su, da gaske bani da wannan amsar tasu Ummi," ba komai Safiyyerh take ganewa tana jin ta isa ta yankewa kanta hukunci ita ba kowa face yarinya mai "wayon gaske da tunani Safiyyerh bata san komai ba ita kawai yarinya ce""" """Ka san dole zaka jira amsar wannan tambayar da kake tsoro, amma sanar dasu auren shine zai fi maka a" "raina ina jin Maama ba zata yi maka gardama ba"" kafin ya ce wani abu Aliyu ya buɗe ƙofar ya shigo da izinin daddy kamar kodayaushe wandon sojoji ne a jijinsa da farar riga tas ya ɗora hula p.cap a kan shi ya zauna kansa a ƙasa yana furta ""barkan ku da safiya""" """Aliyu ya aiki, baka san Maama ba lafiya bane naga baka shigo ba?""" """Na sani"" ya ce kawai a taƙaice yana danna wayarsa ""Ka sani kuma? Shine ba ka yi mata sannu ba me ya" "sa kake haka ne Gadanga, me ya sa kai zuciyarka bata motsawa sai akan Maama meke damun tunaninka baka ɗaukan responsibility ɗinka as a brother""" """Idan bai ɗauki responsibility nasa matsayin yaya ba, yanzu zan ɗauki responsibility Safiyyerh a matsayin" "mijinta"" da wani irin yanayi Aliyu ya juya ya kalli daddy yana son sake tabbatar da abin da ya faɗa masa a" "zuciyarsa wani irin fargaba ne ya wanzu ciki a fili kuma ko gezau ya dai zubawa daddy idanu can ya ce ""kamarya?""" """Da kai da Safiyyerh baku da wata kalma da za ku replying mutum ko responding maganarsa sai kamarya?" "To kamarya dai yadda ka ji ai aikin da ka yi na soja bai saka ka daina jin Hausa ba, har gwara Safiyyerh" "ma"" daddy ya gyara zama Aliyu dai kallon mahaifin nasa kawai yake da wani irin yanayi mai ɗauke da zallar mamaki." """Aliyu ni ban isa na saka dole ba, ban kuma isa na tilasta rayuwarka yin abin da ka yi niyya ko baka so ba," "Aliyu ni dai mahaifinka ne ka saka hakan a zuciyarka. Bani da wanda zai mini wannan rufin asirin kaf family, ka manta da batun Junaid da Awais da kuma Dr, kar ka tambayi mai ya saka na zaɓe ka na ji a raina zaka kula da Safiyyerh ko bayan bana numfashi ko bayan ƙasa ta rufe mini idanu na zaɓi aura maka ita saboda dalili mai ƙarfi, na yarda da ingancinka"" Ya yi shiru Ummi kuma Aliyun take kallo shi kuma yana kallon daddy da duk nutsuwarsa. ""Ranar da Ashraf ya rasu a ranar aka ɗaura maka aure da Safiyyerh, don Allah don girman Allah karka tambayan tsakaninka da Safiyyerh waye ba jinina ba, wannan tambayar shine abu mafi girman laifi a gare ni, ka taimaka ka yi mini alfarma ka riƙe Maama ka" "amshe ta matsayin matarka""" "Captain ya kasa motsi balle magana bai ma san mene zai ce ba. Daddy ya matsa hannunsa ""Don Allah" "Aliyu""" """Ita ta sani?""" """A'a, kai na fara sanarwa Safiyyerh bata da wata matsala ga umarni na"" Aliyu ya sake yin shiru idanunsa" "a ƙasa har ya juya baya ya sake juyawa ya kalli daddy a hankali ya ce ""tell her first, ko bana son ta zan yi ƙoƙarin ganin na fara son Safii in sha Allah""" """Ba zan tambaye ka ni ne ba ɗanka ba ko ita, zan bar tambayar a raina har sanda ka shirya faɗa mana" "gaskiya ni da ita, zan rayuwa da fargabar sanin amsa, da gaske daddy zan so Safii iya tsayin numfashi tunda kai ka zaɓa mini ita""" Daga Ummi har daddy kallon Aliyu suke musamman daddy bai yi tunanin jin wannan amsar ba ya dinga "kallon Aliyu ba ko ƙiftawa ""da gaske zaka so Safiyyerh? Ka san Safiyyan da nake nufi Aliyu?"" Aliyu ya" buɗe idanunsa wanda hula ta ɗan rufe masa su """Safiyyerh Abdu Marafa ko ba ita ba?""" """Ita, zaka so ta ka ce?"" Daddy ya sake faɗa da mamaki" """Bata da Qualities ɗin da za a sota ne?""" """Haka ne tana da shi, na shirya tafiyar ku za ku bar ƙasar nan nan da kwana biyu bana buƙatar ku" "gabaɗaya a yanzu domin nutsuwar zuciya"" Aliyu ya sake duban daddy ya ce" """Kuma? Ka bar tafiyar nan daddy"" sai kuma ya juya gabaɗaya ya kalli Ummi da daddy" """Aliyu soja ne, so i will be with her always""" Yana cewa haka ya fita da ƙyar ya yi jarumtar kai kansa ɗaki ya cire p.cap ɗin kansa ya shiru ba auran ke "damun shi ba, tunani ya fara wa daddy ya haifa tsakanin shi da Safii?" Da yamma Safiyyerh ta ɗakko ƙasa bayan tafiyar Kinal daga ita sai duguwar rigar bacci kanta ba hula "sosai ƙuruciyar nan tata ya bayyana, ta zauna saman kujera ta lumshe idanunta ta zama wata ira tun bayan tashin ta daga bacci jikinta ba ƙwari. I dake kallonta ya ce ""Sannu Manager, ya jikin yanzu?""" """Bayana ke mini ciwo Yaya J, ina jin Dr Hash ya mini allura, bana son allurar nan Yaya J bana jin daɗin ta" "watarana zata kashe ni don Allah ka cewa daddy ya daina sawa Dr ya yi mini"" idanunta ya shiga kawo" "ruwa ta yi lamo da kanta saman hannun kujera. Daman yana bakin ƙofa jin abin da take cewa sai kawai ya juya shi kuma Yaya J ya ce ""Ki yi haƙuri Maama za a daina miki in sha Allah"" ta yi shiru kawai." Dr Hash na zaune a lambun gidan yana waya kasancewar baya da wani aiki a asibiti hutawa yake kashe "wayar ya yi ganin Captain tsaye a kan shi. ""Babban yaya barka da fitowa"" kamar ba zai zauna ba sai kuma" "ya nemi waje ya zauna fuskarsa kamar kodayaushe babu walwala ya jima a haka kana ya ɗaga kai ya kalli Dr Hash ""Akwai wani abu da kake son faɗa ne Captain?""" """Ka daina yi mata allurar da kake mata""" """Me ya sa?""" """Haka dai na ce, idan kuma ka yi zaka sha mamaki"" Dr Hash ya ce ""Wannan kam ai daddy zaka faɗawa" "shine ke bada umarni""" """Wa kake da suna, ka da ka sake ka kuma yi mata idan ba haka ba kuma wallahi zaka kwana ɗakin duhu""" yana cewa haka ya miƙe tare da barin wajan. ***** Hon Maɗatai na zaune gabansa zube da fastocinsa yana magana da wani yaronsa wajan keɓantacce ne kamar lambu haka yake bai san da zuwan mutum ba sai huci da ya ji ta bayansa ya juya da sauri sau kuma ya buɗe idanu waje kafin ya ce """Ya zaka faɗo mini kamar ɓarawo?""" """Da ɗan siyasa da ɓarawo uwa ɗaya ta haife su, waye kai?""" """Baka san waye ni ba a garin kake nufi?""" """Ba'a haife ni da na sanka ba, ka aika akawo ni ina fatan saƙona ya iske ka?""" "Hon Maɗatai ya kalli mutumin gabansa da wani ya ce ""Waƙa ta yi, da ita za'a fara fita yawon kamfel a" "biya a dinga sawa a gidajen rediyo"" ya ciro kuɗi miliyan biyu ya bawa mawaƙin ya ce ""Ga sadakin ka, ina fatan waƙar gaba tafi wannan akwai wata zabiya wai ita Kinal A Awaya"" cikin jin daɗi mawaƙin ya amshi kuɗin ya ce ""Na san Kinal ai ta iya waƙa, ba dai ta shahara sosai bane""" """To sai mu saka ta shahara na ji ta yi Ali wali waƙa, ta yi sosai ta zuba kalamai na fikira harshen nata" "akwai zaƙi dani kuma kawai ya dace a nemo mini ita"" ""zan kawo ta in sha Allah hon, ka yi ka gama ka karya kujerar dambu mai hawa uku Allah Ya kare ka ɗan Majilisa kai ne da nasara Hon"" ""zaka iya tafiya sai na jika""" """Akwai taliya da atamfa da su Omo suger, a tabbata duk local government ɗin da aka je kamfel an basu," "a kuma ɗauki photo da bidiyo za a bawa ƴan social media su baza shi ko'ina. Sai sauran magana na siyan ƙuri'u za ku yi da p.a you can leave Musbah"" Musbah ya miƙe tsaye ya fice sai a lokacin ya juya ya kalli" Moh dake tsaye fuskarsa duk rauni """Nan ai ba jeji bane, ni kuma ba naman jeji bane ba have a seat""" """Bana zama""" """Saboda me?""" """Tsaro, yi magana""" """Shi wanda kakewa aikin baya kula da lafiyarka ne dubi fuskarka Mutallab""" """Ka kira ni da Moh ko Mai dawa sai mu yi magana"" Hon Maɗatai ya jinjina kai ya ce ""Ina son sanar maka" "na haɗa hannu da Dr Abraham, ta yiyuwa ya janye muƙamin da yake nema ƙarƙashin jam'iyyarsa idan haka ta gaske zamu kai Ali wali ƙasa ne, ka haɗa hannu dani lallai za ka ji daɗi""" """Me ka shirya yi wa matasa idan kaci zaɓen?"" Hon Maɗatai ya ɗaga kai ya kalli Moh sai kuma ya yi" murmushi ya ce """Inganta ilimin su, rage musu kuɗin makaranta samar musu da ayyukan yi cusa musu ra'ayin noma da" "muhimmanci yinta""" """Su kuma ƴan daba fa? Wanda kuke anfani da su wajan cimma burikan ku, bayan yaran ku na keɓe kuna" "tattalin tarbiyar su ba ruwansu da sabgar siyasa sai mu ƴaƴan talakawa ƴan wahala kuma ƴan daba mashaya mune ƴan bangar siyasar ku a yau, a gobe a manta damu jibi kuma a neme mu shine ko?"" Hon Maɗatai ya yi murmushi ya ce ""Mutallab kenan, duk wata nasara da muka samu ai daku zamu rabata ni mulki da siyasa tamkar don su ne aka haifan, ina da kyakkyawan tanadi akan ku ba za a bar rayuwarku" "haka ba""" """Me kake buƙata""" """An saka ka kamo Manager ta kamfanin FS WORLD INVESTMENT COMPANY ko?""" """Wanne kiminin ya faɗa maka?"" Hon Maɗatai ya miƙe tsaye yana zagayawa ya ɗauki fasta ɗinsa ya dinga" "kallon kansa ta ciki can ya ce ""kai yin aikin ne a gabanka, mu ƴan siyasa da idanu ɗaya muke bacci mun" "raba kunnuwanmu ko'ina, ka dai sani a siyasa babu masoyi na dindin haka ma maƙiyi, iya ruwa je fidda kai kowa ya iya allonsa ya ce wanke kuma ni da Ali wali ai sahun qiwa ne ya take na raƙumi kowa da abin" "da yake buƙata, idan ka yi kidnaping yarinyar ka tilasata maka ta saka mini hannu domin na saka hannun" "jari a wannan kamfanin shine abin da nake buƙata"" Jin Mutallab ya yi shiru ya saka ya ce ""Ko baka ji ba?""" """Na ji""" """Mene alaƙar ka da makarantar FGC?""" """Ban sani ba, maganar kuɗin aikinka sai na yi aikin zai sanar. Sai godiya"" yana cewa haka ya bar wajan." Kasancewar Monday ce Safiyyerh ta shirya da wuri zuwa office har yanzu jikinta bai warware ba dole "amma ya zama sai taje. Ba jimawa Md ya shigo bayan sun gaisa fuskarta dai a kame ya shafa kai ya ce ""Manager gari ya ci wuta fa"" idanunta akan wani ducoment tana juya kujera a hankali kamar ba za ta yi magana ba sai kuma ta ce ""Nawa kake buƙata Md?""" """Ko dubu ɗari biyar ne zan yi maleji""" """Zan saka accouter ya baka miliyan ɗaya"" ya dinga mata godiya sosai ta yi murmushi kawai ta ce ""Mene" "ma'anar FS ni kam Md?"" Tsam ya yi da ransa sai kuma ya ce ""Ba zan iya ba ki wannan amsar ba Safiyyerh, zan dai faɗa miki abin da ba ki sani ba"" ta sake juya kujerar hannunta a haɓarta tana murmushi mai kyau" """Ina ji Md""" """Yatsun da kika gani kwanaki gaskiya ne, ana siyar da ƙodar mutane a wannan kanfanin tare da jarirai," "ana kuma dillacin ƙwayoyi, sauran abun ki yi bincike da kan ki za ki iya dacewa"" yana cewa haka ya fita. Kasa motsi Safiyyerh ta yi numfashinta ya tsaya cak da ƙyar ta miƙe ta ɗauki ruwa ta sha ta dawo saman duguwar kujera ta zauna zufa ta dinga yanko mata a hankali ta ware rolling na kanta ta rufe idanu tana" "kiran sunan Allah. Knocking aka yi da ƙyar ta ce ""In""" "Ta buɗe idanu da mamakin ganin wanda ya shigo, ya ƙarasu cikin office ɗin ""Ba dole ki buɗe idanu ba" "Safiyyerh, idanunki kenan?"" Ta yi murmushi tana gyara zamanta" """I. Qasim kai ne""" """Ni ne Safiyyerh""" "Ya nemi waje ya gaisa ta ce ""Yaushe gari kuma?"" Ya yi murmushi ya ce ""Zama likita a garin nan is not" "easy Fiyya, ya batun ciwon kan ki kowa?"" Ta ce" """Yana nan""" """Ayya sorry, akwai maganganu da zan ba ki in sha Allah da allura, gudun kar ki dinga sha ba daidai ba zan" "dinga zuwa dasu kina sha a gabana na yi miki allurar, za ki samu sauƙi in sha Allah""" """Thank you I. Qasim na gode sosai"" wayarsa aka kira ya kalleta sai kuma ya miƙe tsaye tare da yi mata" alama da yana zuwa. Ta bishi da idanu har ya fita. ***** "Safiyyerh ta dinga kallon daddy kamar mahaukaciya saboda rashin fahimta ta ce ""Daddy, aure da Yaya" "Aliyu ka ce dani kuma Safiyyerh, mu duka ƴaƴanka ne fa"" hawaye ya fara suntiri a saman fuskarta ta saka hannunta ta toshe kunnuwata tana girgiza kanta gabaɗaya ta jiƙa hijabin da ta yi sallah da shi da hawaye ""ruɗanin da kake sani a kullum yana shirin haukatar dani daddy, ba auren ne ban yi na'am da shi ba na" "kasa fahimta ne dani da Captain waye wanda ka haifa waye ba ɗanka ba""" """Ku duka yarana ne Maama, idan har kin yarda ni uba ne a gare ki kuma kina so na da ƙaunar farincikina" "ki amince da auren Maama, ba zan taɓa cutar dake ba ni ubana ne, uban ƙwarai kuma yana zaɓawa yaransa abun ƙwarai ne ki yi mini biyayya Safiyyerh, kin ji ko?""" """Na amince daddy zan amince da abin da ya fi wannan ma, Allah Ya sa shine mafi alheri a gare ni"" ta faɗa" "tana rushewa da kuka da sauri kuma ta yi waje ta nufi ɗakinta ta faɗa saman gado ta dinga wani irin kunjin kukan kamar ranta zai fita wai wanne irin abu ne haka? Ta shiga uku meke faruwa aure fa, auren ma da Captain innalillahi wa'inna ilaihirraji'un addu'a take Allah ya yafe mata komai ta fahimta da ƙyar" bacci ya ɗauke ta ko abinci bata ci ba. Cikin dare ta farka ganinta ta yi rufe da bargo ta yi saurin buɗe ido don bata san kwanciya a duhu gashi an kashe mata hasken ɗakin babu mamaki Yaya J ne. Gani ta yi "wajan ɗaya da rabi ta miƙe ta ɗauki ɗan makullin mota da wayarta ta saka hijabi har ƙasa, ƙofa ta buɗe ta sauka downstairs ba kowa ta buɗe ƙofa ta fita mota ta shiga mai gadi ya buɗe mata cikin sauri ta nufi kamfani gari shiru sai hasken fitilo na titi ta dinga duban hanya ba wanda ke biye da ita a haka ta isa kamfanin ta ajjiye motar a waje, ciki ta shiga wajan mai gadi sun jima suna magana ya ce ""Ana shigo da mata cikin dare ana kuma fita da su, na yi bincike abin da ya saka ke iya ɓangaren abinci kika sani to" "akwai asibiti a cikin wannan kamfanin"" ta ce ""Ka ɗauki number motar ko haddacewa?""" """A'a ranki ya daɗe""" """To shikenan na gode Baba, ga wannan"" ta ɗauki kuɗi ta bashi a cikin aljihun rigarta. Tana ƙoƙarin buɗe" "gate ɗin kamfanin ta fita kawai ta ji ƙarar dingowar mutane, ta juya da sauri suka haɗa idanu da Darma" da kuma Goje da Mangal wani irin mummunan faduwar gaba ne ya sameta lokacin da idanunta ya shige cikin nasa shi bai kai ga dingowar ba yana zaune saman katangar shima ɗin ita yake kallo babu ƙiftawa... MUTALLAB PAID BOOK ne a jerin littafan bright pens. We're still on free pages kar ki bari a yi bake. MUTALLAB. "Book 1, 2 &3" 500 Naira 0116886423 Union Bank Na'ima Sulaiman S a tura shaidar biya ta nan 08164069385 via WhatsApp only. DOMIN INGANTA NONO Assalama alaikum Hajiya muna da ingantaccen maganin gyaran nono wadda ya amsa sunansa magani Maganinmu ingantaccen maganine da yake tada jijiyon nonon da suka saki y'ar uwa breast dinki ko yakai silifas saboda kwanciya kikai amfani dashi in sha Allah zakiga amfaninshi acikin 1week maganinmu powder ne yana ciko da breast y gyarasu bashi da illa ajikin mutum munyi amfani da saiwoyi da magunguna gargajiya domin gyaran breast 08063114606 ina garin kano karki sanya y'ar uwa nono yana karawa mace martaba a gurin mai gida maganinmu kowa zai iya sha wadda zatai yaye ko gyara budurwa duk zasu iya sha breast dinki ya ciko yayi bull -bull "[10/18, 9:23 PM] Nanameera: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 11 *Bright pens.. 2nd batch* "Ya ƙura mata idanu yana daga zaune saman katangar a hankali yake girgiza ƙafarsa, fuskarsa rufe da" "baƙin ƙyalle a lokacin duniyar ya ji tana masa daɗi yana jinsa kamar a cikin jirgi ana juyawa dashi, shi ya sa yaƙi sakkowa ƙasa daga katangar, shi kansa bai san wacce irin ƙwaya Mangal ya kawo masa ba. Fiyya ma shi take kallo ganin shi kaɗai ne ya rufe fuskarsa Goje da Darma da Mangal suka zagaye ta, ta juya ta" kalli securityn da yake on duty ranar ta nuna masa Goje """Su kuma waɗannan fa security?"" Kai tsaye ya bata amsa da ""Ban san su ba, amma Hajiya akwai hatsari" "bamu san me suka zo nema ba"" Goje ya matsa kusa da ita yana kallon ta" """Mai dawa wannan ce ƙuruciyar? A hotun kamar bata kai haka girma ba, ƴar firit da ita kamar benu, nan" "kuma an ci kuɗin jama'a an sha madara da milo an yi ɓulɓul"" sai ƙarewa Fiyya kallo yake ita kuma ta yi tsaye tana jin yadda warin wiwi ke dukan hancinta kamar za ta yi amai amma taƙi matasa saboda taurin kai irin na Safiyyerh Abdu Marafa da rashin tsoro. Tsaki ta yi kawai ƙasan zuciyarta kuma tsoro ne fal ga" ƙirjinta dake bugawa kamar zai fito waje sai buɗe manyan idanu waje take yi. """And what is my business with you? Me kuke nema a wannan kamfanin kun zo sai warin ganye kuke" "mini"" Mutallab ya sake buɗe manyan idanunsa jin sautin muryarta zaƙwai a cikin kansa ya kalli bakinta dake motsawa cike da masifa duhun dare ne amma kamfanin haske tar tar ko'ina. Mangal ya lailayo ashar ya dannawa Safiyyerh ""ke dan ƙaniyarki mune muke warin ganyen, su waye sila idan baku ba, ƴar" "wahalar yarinya idan ban bawa tiger namanki ɗanye ya cinye ba""" "Safiyyerh ta juya ta kalli tiger daya hauro ya zauna kusa da Moh, yana zaro harshe waje ta nuna karan da" "hannu ta ce ""abin da ya fi namana ɗanye, banda rainin hankali jikin nawa zaka ɗauka ka bawa shegen karan naku, idan kuɗi kuke buƙata na baku don nasa na yin caji kuke nema, stupid"" Goje ya juya ya kalli" "Mai dawa ya ce ""ba zamu rage wa yarinyar nan tsayin harshe ba kuwa? Kauɗinta ya yi over, ka je ka" "zauna matsalar idan ka sha wannan ƙwayar baka gane komai yanzu babu mamaki jinka kake a saudia""" Moh ya lumshe idanunsa ya sake buɗe su a kan Fiyya duk motsin da take yi a kan idanunsa sai dai ba "wani fahimta yake ba muryarsa a cunkushe mai ban tsoro ya shafa kan tiger ya ce ""shiit""" Tiger ya diro shima ya diro ya tsaya a kan ƙafafuwansa hannunsa ɗaya yana murza gashin kansa wanda ya zama wani iri ba kyan gani na shegun shahararrun ƴan daba ɗin nan. """Mai jeji ƙirit ka ankare ba lokaci ka ɗaƙkota a kafaɗa mu fece kafin kwalawa su kawo kai dan akwai" "kimini a nan wancan mai fararen kayan"" ya nuna securityn wajan wanda shi kaɗai ne kawai ya rage. Safiyyerh ta ja baya tana juya idanunta ta ce ""ban gane ya saɓo ni kafaɗa ba kamar wata ƴar iska ko mara gata, kai naga alamar kai ne shugabansu ko? To wallahi ba wuƙa ba ko bindiga ce bana tsoro kana taɓa ni sai na raba ai an ce ba wani ƙwari ne daku ba"" ta ƙare maganar tana kallon cikin idanun Mutallab" wanda tun ɗazo shi take kallo shi kuma yaƙi furta komai. """Ki iya harshenki ƴar kanzagi ko na fitar miki da jini yanzu na shata miki bille a wannan fuskar kamar" "gwada"" juyawa ta yi ta ce ""Baba wai where are the securities? Where are the rest ka kira su yanzu"" kafin" "baban ya motsa Mangal ya saka ƙafa ya kwarfe shi zuwa ƙasa, ya sake saka ƙafa ya danne masa baki. Darma ya zaro wuƙa ya ce ""Ke fitsararriya ce ko? Ba wata uwar muke nema ba ke muka zo ɗauka, don ke muka cikin wannan kamfanin ke za mu yi kidnaping yanzu kin fahimta kin gane ko, ki shige salin alin ko" "na ɗauke ki yanzu na haura dake wallahi""" Fiyya ta buɗe idanu tana kallon wuƙar dashi kansa Darma ɗin ta yi murmushi zuciyarta kuma bugawa "tsoro ya shige ta, ƙoƙarin danna recoding take a wayarta hannunta ya shiga rawa ta dake a ƙasan zuciyarta tana kiran sunan Allah da ƙyar ta furta ""kidnaping kuma ni, ni Safiyyerh Abdu Marafa za ku sace," "ni Safiyyerh matar soja guda kuna hauka ne ko kuna tunanin mijina zai bari hakan ta kasance?""" "Jin furucin Safiyyerh ya saka Moh sake kallonta da sauri yana hana zuciyarsa abin da yake ji, haka kawai" "ya dinga jin tafasar zuciya ya nufi wajan Safiyyerh jikinsa na rawa idanunsa suka fito waje kamar zasu faɗo da muryar mai ban tsoro mafi muni ba muryar ba ita kanta fuskarsa abar tsoro ce tsaf mutum zai dinga mafarkin ta. Hannunsa riƙe da wuƙa yana kallon cikin idanunta da kyau dab da ita ya ce ""Ba mijinki ba ko ubanki Abdu Marafa aka bani umarnin daƙƙowa ko kashewa sai na yi balle ke"" ya cije bakinsa ya feshi ya cilla mata ƙatuwar baƙar kunama ta shige ƙirjinta kai tsaye, zufa ta dinga yanko mata saboda" "tsananin azaba ta kasa ihu ko kuka ga warin da yake yi yana neman kashe ta, idanunta ya juye ya yi ja ta" "zuba masa idanu tana kallon fuskarsa data yaye,ta miƙa hannu da nufin shafo fuskarsa ta ji ya caka mata" "wuƙar a gefen cikinta ta yi wata ƙara tana buɗe idanu duk yadda jikinta ke rawa ga jini na zuba mai hanata sake kai hannunta ta shafo fuskarsa ba, daidai nan ya yunƙura zai saɓata a kafaɗa suka ji shigowar motoci na jami'an tsaro, bai niyyar barinta ba yadda Goje ke jan shi da ƙarfi ya saka kawai ya" sake ta a wajan yana furta “Mutallab” Ɗaya bayan ɗaya suka kama katangar suka haure daman kuma kaf kamfanin ita ce ƙaramar katanga wacce babu kwalabe jikinta. Securities kala biyu ne dana fararen kaya da masu uniform sai shi da yake sanye da wando three qauter "da farin takalmi da riga baƙa ko p.cap ɗin kansa babu, ya nufe ta sauran suka nufi wajan baba suka fara ɗaukan statement ""Baba kwantar da hankalinka babu abin da zai sameka in sha Allah, bayan waɗannan ƴan daban da suka zo, an bamu tabbacin a daidai yanzu Scorpion ma yana wajan nan ko kuma ya zo"" a hankali Aliyu ya juya ya kalli baban jin tambayar da ake masa, sai kuma ya ɗauke kai ya saka hannu ya ɗauki Fiyya zuwa cikin mota bayan ya kwantar da ita ya tsaya yana kallon wanda ke ɗaya motar a tsaye" "da yake ce masa ""Ya akai kuka barta ta fito cikin dare haka? Macace ita fa""" """Sir ƙuruciya, thanks for the call""" """Anything for you Captain Aliyu"" suka shiga mota duk suka bar wajan ya rage sai jami'an F.i.d kawai da" suke tambayar baba. "Su Goje cikin kwalabati suka shige suka ɓoye suna zare idanu da muzurai a hankali ya ce ""Akwai matsala" "jami'an tsaro ne fal yasin, baka dai bar sheda ba kuma me ya saka ka caka mata wuƙa idan ta mutu fa?""" Moh ya yi shiru can ya ce """Ba zata mutu ba""" """A ciki ka soka mata wuƙar fa? Baka kalli yadda jini ke zuba bane da zaka ce wai ba zata mutu ba?"" Kai" "tsaye Moh ya ce ""ba zata mutu ba""" """A buge kake shi ya sa, askira ka caka mata fa na ɗauka tsoratar da ita kawai za ta yi""" "A firgice ya kalli Goje idanunsa kamar za su faɗo ""Goje, idan ka sake maimaita mini cewa na saka mata" "wuƙa zan maka jahilci yanzu wallahi zan iya kashe ka""" """Kashe ni mana daman ai daba babu wata amana a ciki dole na faɗa, ɗaƙkota aka ce kawai ka yi ba kashe" "ta ba"" Mutallab ya wani juya cikin zafin nama ya damƙo wuyan Goje cikin sauri Darma ya shiga tsakiya ya ce ""Sai godiya kar a yi haka akwai amana, kai Goje ka iya bakinka idan ba farkawa kake so ka yi ka ganka a ƙiyama ba"" Moh ya cije bakinsa kansa na wani irin sara masa yana girgiza kansa ya kalli sama ""duk sanda na sake ganinta sai na kashe ta don uwarka"" duk sukai masa shiru sun daɗe a wajan kafin jami'an tsaron su bar wajan suka fito tare da barin wajan suma kallo ɗaya za ka yi wa Moh ka ɗauke kai saboda" yadda yake huci ya fiddo da ƙarin jikinsa neman inda zai sauke kawai yake. The following days. "I. Qasim ya ce ""Tunda ta bar I.c.u ai Allahamdulilah, she will soon recovering""" """Dr Qasim ba dai abin ku kuke mana na likitoci ba, ya jikin Maama don Allah ita ce kawai last hope ɗina""" "Dr Qasim ya yi murmushi ya ce ""Safiyyerh zata ji sauƙi in sha Allah, ba'a caka mata wuƙar inda za ta yi" "mata illa ba ta zubar da jini sosai ne sai kuma zuriyarta data ninka gudun da take yi, ka yi mata addu'a""" """Shikenan Allah Ya bawa Maama lafiya,zan iya shiga ai kwana biyu ba'a barin mu shiga sai na ji kamar" "har yanzu bata dawo hayyacinta ba"" I. Qasim ya girgiza kai ya ce ""Daddy kana son Safiyyerh da yawa, shiga ka ganta"" har bakin room ɗin da take ciki ya shiga ya shiga sanye da kayan daya dace a shiga aga mara lafiya. I. Qasim ya juya ya fita daddy ya zubawa Safiyyerh idanu tana ƙwace ta sake yin fari a barka da farar mace ta ɗan faɗa an ja mata rigar marasa lafiya zuwa saman ƙirjinta duk da baya kaya a jikin sai iya rigar an buɗe wajan ciwon da akai mata aiki a wajan ya zuba mata idanu ya matsa a hankali yana kama hannunta addu'a ya shiga yi mata sosai ta samu sauƙi zuciyarsa duk babu daɗi idan ya rasa Maama" bai san yaya zai yi ba kuma. """Allah Ya baki lafiya Maama, don Allah ki rage wa kan ki fitina da zaƙewa cikin wasu al'amuran kalli" "yadda za ki saka rayuwarki ta lalace, Safiyyerh ban shirya ba ban shirya ba Safiyyerh"" ya damƙe hannunta" yaga bakinta na motsawa amma sam baya jin me take cewa. Ta shi ya yi ya fita yana sake yi mata addu'a a ransa na samun sauƙi da rangwame. "Bayan ya fito waya ya saka ya kira Aliyu yana ɗagawa ya ce ""Aliyu kana ina ne, an fito ita daga i.c.u amma" "babu kai a wajan bana son haka fa, da baya da yanzu ba ɗaya bane matsayin Safiyyerh ya jima da sauyawa""" """Allah Ya sauwaƙe""" Kawai Aliyu ya furta ta cikin wayar daga nan ya yi shiru ran daddy ya sake ɓaci yana jin kamar ya yi "kuskure na aurawa Aliyu Safiyyerh na damƙa masa dukkan ragamar rayuwarta da tunanin zai kula da lamarin Safiyyerh amma ba lallai hakan ta kasance ba, sosai abubuwa da yawa ke damun zuciyarsa yana hana shi sukuni tare da rashin isasshen bacci, idan Safiyyerh ta tare a gidan mijinta dole ne ya amshi" responsibility da Ubangiji ya ɗora masa na mijinta. "Ummi na kallon daddy da jajayen idanunta ta ce ""Ina ta zuba idanu rayuwar yarinyarta na neman" "lalacewa, ka yi abubuwa da yawa Professor na ja baki na yi shiru da tunanin duk abin da ka yi daidai ne, zuciyata ba zata ɗauka ba Safiyyerh gabaɗaya nawa take ni kawai ta haƙura da aikin wannan Companyn da bana gane masa ai shekarunta bai kai ya kawo ba, ban shirya rasata ba"" daddy ya yi shiru yana kallon" yadda Ummi ke kuka. """Ki tashi muje dare na yi"" da sauri ta kalle shi tana share hawaye ta ce" """Kuma ban gane muje ba zuwa ina?""" """Ai kin san majinyata basa kwana a wannan hospital ɗin, patient ne kawai yake da alhakin kwana"" tun" "kafin ya kammala magana take girgiza masa kai ""i don't think zan iya barin wannan asibitin da Safiyyerh ita kaɗai, ni bana ma ganewa irin haka ka yi musu magana ko a nan zan iya kwana I'll manage"" Daddy ya" "yi gaba yana furta ""Kar na sake maimaita miki"" dole ta miƙe bayan ta sake leƙa Fiyya ta yi waje." "Kafin a rufe shigowar masu ziyara Yaya J ya daɗe zaune gaban Fiyya yana kallon fuskarta, da kwanakin" "baya ne zai riƙe hannunta cikin nasa yana ta mata sannu da addu'a yanzu kallon ta kawai ya kasa koda yin addu'ar ma, can ya miƙe ya fice haka Awais da Dr Hash duk suka shigo basu da tabbacin bacci take ko farkowa ne ba ta yi ba. Wajajen 2 na dare ya buɗe ƙofar ya shigo bayan I. Qasim ya bashi damar hakan daman aikin kwana zai yi idanunsa a kanta har ya shigo ya rufe ƙofar a hankali ya tsaya gabanta" hannunsa biyun zube cikin aljihu ya ɗauki minti a ƙalla ashirin kafin ya ƙarasa ya zauna bakin gadon har yanzu bacci take ya dubi hannun da ruwa yake shiga ya dubi ɗaya hannun da jini ke shiga a hankali ya kama hannun drip ɗin da yake ɗan mitsi-mitsi ya riƙe cikin nasa a hankali yake murza yatsunta can ya ji ta riƙe hannunsa ya ɗaga kai yaga tana jujjuya kanta sai a lokacin ya lura da sauyin ƙarar da na'urar ke yi. Safiyyerh tana buɗe idanu ta rufe saboda wani fau ɗin haske daya shige mata ciki sai kuma hawaye ya "fara bin idanunta ya ɗan sunkuya yana kallon fuskarta. Ta sake buɗe ido ta kalle shi ta dudduba taga ba kowa ta rufe idon still ta buɗe har lokacin jujjuya kanta take yi ""Yaya"" ya yi mata shiru ya sake cewa" """Me na yi musu?"" Still shiru ya yi mata ta buɗe idanu ta kalle sai ta fashe da kuka sosai ƙirjinta na" ɗagawa ya damƙe hannunta """Yaya""" """Safii..."" Ya kira sunanta a hankali ta ce ""Kai na zai cire ƙirjina ciwo cikina ciwo yaya mutuwa zan yi""" """Allah Ya yi miki Rahma"" sai kuma ya matsa dab da kan nata ta saka hannu ta riƙe nashi ta yi shiru a" "hankali ta sake cewa ""Captain""" """Manager""" """Na ce musu mijina soja ne, wai ko sojan zasu kashe balle ni"" ta yi shiru ta sake cewa ""Ka riƙe mini kai na" "ciwo yake mini sosai na shiga uku daddy wayyo"" maimakon ya riƙe kan nata sai ya ɗora goshinsa saman" "nata, ta buɗe idanu ta kalli fuskar Captain kamar zau haɗe da data a nutse ya ce ""sun kashe kin?"" Ta girgiza kai" """Me ya sa?""" """Ban sani ba"" ya ɗan murza mata goshinsa yana kallon cikin idanunta ya ce" """Saboda ke matar soja ce"" ta yi shiru kawai tana kallon shi can ya matsa yana sauka ya zauna saman" kujera. "Washegari da sassafe ƴan sanda suka shigo room ɗin lokacin tana zaune ta ɗan jingina da jikin gado," statement na abin da ya faru suke tambaya. Sp Ghali ya kalli Safiyyerh data sunkuyar da kanta ƙasa ya ce """Da suka zo sun faɗa miki abin da suke buƙata?"" Ta girgiza musu kai." """Za ki iya gane wani daga cikin su? Suna ko kammani?"" Ta ɗago ta kalli Sp Ghali dake tsaye ta ce ""Idan na" "gane kamannin sai me za'a yi to?"" ""Zamu kira a zana mana fuskar wanda kika gane ne""" """To ban gane ba""" "Duk suka tsora mata idanu musamman daddy ta buɗe idanunta itama ta ce ""Kamarya? To na gane ne?""" "Daddy ya ce ""Maama wa kija ji ya ce wani abu?""" Sp Ghali ya dinga kallon Safiyyerh yana jin wani irin abu a ransa na motsa masa sai ya yi murmushi ya ce """dear kin ce basu nemi komai ba, ba wanda kika gane ba suna amma haka kawai sai su caka miki wuƙa" "think Safiyyerh"" sarai Safiyyerh ta tuna sunan da ta ji ya ambata na Mutallab sai ta yi shiru a hankali kuma ta ce" """Sp kasan matsalar da ƙasar nan take ciki musamman Jiharmu akan ƙwacan waya, wayata zasu ƙwace ni" "kuma na hana saboda ina da abubuwa a ciki shine sukai mini haka"" ya jinjina kai ya ce ""Haka ne dear za mu yi bincike zan gano kowaye za mu hukunta shi ƙarƙashin hukuma bisa kundin da aka wanzar, get well soon dear"" ya sake faɗa yana murmushi kan ta dai a ƙasa yake. Sallama sukai dasu daddy suka tafi." Captain na zaune ko tari bai yi ba wayarsa kawai yake dannawa can ya miƙe ya fita daddy ya bisa da kallo haka Yaya J ganin ko sannu bai yi Fiyya ba daman bai jima da zuwa ba. Eng Ali wali ya dinga kaiwa yana kawowa ransa duka a ɓace ya kalli Mai dawa ya ce """Yanzu daka kashe ta fa? Wai me kake nufi da wannan abin da ka yi ne Mutallab?""" """Ka dai na yi mini ihu kamar Malam Abdullahi"" Ali wali ya jinjina kai kawai ya ce ""Kasan ka raina ya ɓaci" "kake cewa haka? Ya zan aike ka ka yi sato yarinya kuma ka caka mata wuƙa salon ka ɓata mini aiki da sanyin safe ake kama fara ba mai dawa""" """To na fasa""" "Ali wali ya buɗe idanu ya ce ""Meka fasa ɗin? Ba dai ɗakko yarinyar ba kake nufi?"" A taƙaice ya ce ""Shi""" """Haba uban mafarauta, kai baka san wasa ba kai kamar ɗa kake a wajena fa"" sai a lokacin Moh ya buɗe" "idanu ya kalli Ali wali yanzu dai normal yake ba'a buge ba ""baka haifan ba, san da aka haifan baka da labari"" ya yi fito yana miƙar da ƙafa ya ce ""To ka kira ɗan naka ya yi maka aikin, mu fa kuke sawa a wahala har a yi zaɓe aci a cinye ka hau kujerar ba lallai yaranka suna ƙasar ba, ba'a rainawa Moh hankali" "ka bar mu matsayin ƴan daban kawai"" Ali wali ya ce" """Ya batun yarinyar?""" """Na ji"" ya ce yana miƙewa tsaye har zai shige ya dawo ya ɗauki bandir ɗin kuɗi ƴan dubu-dubu ya watsa" "cikin aljihu. Sautin daya ji kamar gurnani kamar kuka kuma ya sa ya nufi ƙofar da yaje jin hakan ya murɗa handle zai buɗe cikin sauri Eng Ali wali ya riga shi ya ce ""Haba Mutallab idan iyalina ne a ciki fa?"" Moh ya zubawa Ali wali ido ya kalli ƙofar sai kawai ya fice yabar wajan. ""Ɗan wahalar yaro ɗan jaraba Allah Ya" "nufa na lashe kujerar ganina sai ya yi maka wahala""" "Hon Maɗatai yana zaune ya kalli Sp Ghali ya ce ""Ka lemo record ɗin nasa?""" """Na samu Hon amma cin dai amana ne irin namu na jami'an tsaro amma fidda record ɗin wani criminal" "ya saɓawa kudin tsarin ƙasa"" Hon Maɗatai ya ce ""Waye Mutallab?"" Sp Ghali ya ce ""Nothing serious about him hon, shekaru uku da suka shige an kama shi da laifin kashe matarsa ranar da aka kai masa ita matsayin amarya, kafin nan yana da record na zama gidan yari na watanni sai kuma taɓa guduwa Legas," "a baya kuma kafin hakan shi mafarauci ne ma'abocin shiga jeji ya yi farauta""" """Hon akwai matsala ne? Na ga ka yi shiru?""" """Batun Scorpion ba, case ɗin yarinyar nan Manager a ranar ance shima Scorpion ya je wajan"" Sp Ghali ya" "ce ""Hon Scorpion da ƴan siyasa irin ku yake da matsala fa, ko mutumin daya kashe last yana da za hujjar kisan mune dai bamu sani ba, waye Scorpion ba wanda ya sani jami'an mu na neman shi haka F.i.d Federal investigation department wallahi suna kama shi wannan kisa ne nan take ko su yi masa allurar hauka"" ""Al'amarin Scorpion ya yi kama da ɗaukan fansa fa, za mu zuba ido ya kashe mu ne? Ku hanzarta" "nemo ko waye Sp Ghali""" """In sha Allah Hon""" "Aliyu na zaune saman kujera daddy ya ce ""Kaji ai ko?"" Ya jinjina kai kawai ""Zuwa dare sai ka ɗauke ta ku" "tafi can part ɗin dake gidan daman tuni an zuba komai empty dai yake to ɗazo an kaiwa Safiyyerh kayanta, Aliyu Safiyyerh amana ce idan ka ci amana ba zan yafe maka ba, na yi haƙuri na rabu da kai amma na so kun bar ƙasar gabaɗaya"" addu'a daddy ya yi musu sosai duk da Fiyya bata wajan. Aliyu ya tashi ya fita. A daren ranar ƴan jarida suka shigo saboda hirar da za su da daddy. Sosai aka yi hirar inda yake cewa. ""har kullum ni Professor Abdu Marafa bana goyan mutumin da bashi da wata nagarta wanda baya duba rayuwar yaranmu matsa wanda kuma zuwa gaba sune zasu gaje mu, duk wanda ya buƙaci ku zaɓe shi ku fara duba nagartar shi waye shi, bane background na rayuwarsa waye shi tun farko? kar a yi amfani da talauci da rashin iliminku a saka ku yi zaɓan tumun dare a wannan lokacin matasa yana da kyau ku yi gangami ku magana da murya ku saka iyaye na gida ƙanne da yan'uwa su zaɓi cancanta, wannan masu gamu taliya gishiri ko masu siyan ƙuri'ar mu basu ne wanda suka dace ba, ƙuri'armu ita ce ƴa'cinmu kana siyarwa baka da damar yin zaɓe ku kalli yadda ake mayar da ƙananan yaran ƴan daba masu bangar siyasa ana basu ƙwaya suna aikata zunubi suna kai kansu inda za'a kashe su, ku faɗa mini ko sau kun taɓa ganin ɗan wani daga cikin ƴan takarkarun nan? no! Sai yaran talakawa wanda basu da ilimi ko basu da sana'a sai a yi amfani da wannan damar a janyo su a kurɓata musu rayuwa a ƙarshe kuma ko gidan yari yaro ya tafi wallahi sai dai iyayensa su yi fafutuka duk da cewa har da laifin wasu iyayen a lalacewar yaran, matasa ku haɗa ƙungiya da za ku dinga taimakon juna kar ku yadda da mulkin" "kama karya kuna kallon shekaru huɗu da suka shige yadda zaɓe ya kasance""" """Professor Abdu Marafa kenan a yayin da yake bawa matasa shawara akan su miƙe tsaye domin" "ƙwatuwa jiha ƴan'cinta. Professor mai ya sa duk maganar da zaka yi akan matasa ne? Da batun shaye- shaye ko daba?"" Daddy ya rantse idanunsa yana jin zuciyarsa na yi masa zafi can ya ce" """Ɗan jarida kenan baki abin magana, saboda matasa sune yau, sune gobe haka jibi matasa sune cigaban" "ƙasan idan har aka tsaya musu aka fitar da iri mai kyau, shaye-shaye kuma. ,"" sai kawai ya yi shiru." "Yakasai ya ce ""Gabaɗaya abin da zamu iya naɗa kenan a wannan satin, zamu cigaba da bibiyar professor" Abdu Marafa domin ganin haƙar tasa zata cimma ruwa ko yaya ne? Ni Khalid A Yakasai nake cewa a huta "lafiya""" **** Numfashi Mutallab ke fitarwa a hankali jikinsa duk yanka saboda faɗan da suka yi da ƴan cikin gari bai "san adadin mutanen daya sara ya fitarwa da jini ba, bashi da tabbacin ko bai yi kisa bama rabin fuskarsa duk yanka ne wani wajan har ya zame masa tabo. Goje shima cikinsa rauni ne da ƙyar yake fidda numfashi a hankali ya ce ""Sun kashe Darma fa, ni ban ɗauka haka zuwa kamfel ɗin yake ba, wallahi sun" "kashe Darma na yi ƙoƙarin kai masa ɗauki amma ta kai nake""" """Goje""" """Na'am, Sarki""" """Nemi maɓoya"" ya ce ""Idan na ɓoye kai fa? Naga ba zaka iya tashi ba gwara ni ma kai ma da tuni sun kai" "ka kushewa, gashi wannan ɗan jakar Mangal ban san inda yake ba, balle a jira Ali wali a faɗa masa koda taimakon da zai mana""" """Wai baka jina idan ba ƙiyama kake shirin zuwa ba ka tashi ka face Goje"" da sauri Goje ya miƙe ya yi" "kwana saboda ƙarar motar kwalawa da ya ji, Moh ya saka hannunsa a aljihu ya danna laya tuni ya ɓace a wajan." Abbasa ta dinga kallon Mutallab kamar baya numfashi ta girgiza kawai ta kalli mai yi masa treatment ɗin "bayan ya gama ya miƙe ta ce ""Sannu da ƙoƙari"" ya jinjina mata kai ya fice kawai. Ta yi shiru tana sake kallon Ɗan'malam." "Kamar yadda daddy ya buƙata Safiyyerh ta tare cikin part guda da yake gidan daga can baya, ita dai da to" "kawai take binsa sai kuma idanu ta yarda ba zai zaɓa mata abin da bai dace da rayuwarta ba, ta amince zata zauna da Captain Aliyu zata koyi son shi. Cikin sauri yake gudanar da komai kamar mai tsoran wani abu. A harabar gidan Aliyu na tsaye yana kallon Awais da yake cewa ""Yaya ban gane tambayar da kake" "mini ba""" """Ya sunanka ma?""" "Da mamaki Awais ya ce ""Ikon Allah Yaya ni fa ƙaninka ne tsayin shekaru baka san sunana ba?"" Aliyu ya" "haɗe fuska ba wasa ya ce ""Kuma dole akai na haddace, seriously bana iya tunawa""" """To kai ne Baba captain Aliyu sai Junaid sai Dr Hash sai ni Awais sai Maama"" ""Ok, shi likitan wanne allura" "ya ke yi mata ban damu na san ba a baya yanzu ina so""" """Wai Dr Hash da ya kewa Fiyya? Ban sani ba gaskiya Yaya why not ka tambaye shi?"" Wata tsawa ya" "dakawa Awais yana cewa ""Get lost mumu"" fita ya yi daga cikin gidan gabaɗaya." Har ɗaya saura Safiyyerh na kwance a bedroom ta yi shiru tana jin ciwon na yi mata zafi ta yi kuka sosai "na rashin sanin dalili har bacci ya ɗauke ta. Cikin bacci ta ji an buɗe ƙofar an shigo ta yi saurin rufe idanu yana sanye da kayan bacci farare ya ƙarasu ya duba magungunan yaga ko ɗaya bata sha ba, ya ƙarasa bakin gadon ya zauna shi gabadaya ya manta cikakken sunanta na gaskiya rashin sanin ne zai ce kawai ya saka hannu ya janyo ƙafafuwanta zuwa ƙasa ta matso dab da shi da sauri ta buɗe idanu, suna haɗa idanu" ta tura baki tana juya fuska """Zan saka bindiga na harbe ki a iska kina juyawa"" ta kalle shi ta ce ""To yaya ciwona ka fama mini"" kallon" "da yake mata ya saka ta miƙe zaune ""kin accepting auren?"" Ta jinjina kai ta ce ""Na yi kamar yadda ka yi na san daddy yana da nasa dalilin damuwata ɗaya na rashin sanin gaskiyar ni ce ƴar daddy ko kai, amma aure tun kafin na zo duniya Allah Ya rubuta wanda zai zamo miji gare ni ina da sani daidai gwargwado" "zan zauna ƙarƙashinka duk da baka so na, ko kana so na?"" Ya girgiza mata kai alamar" """A'a""" """Ni ma,sai mu koyi son juna"" ya kalleta kawai sai ya ce ""Muga ciwon"" ""Yaya a wajan ƙirjina ciwon yake" "fa"" da rashin fahimta ya kalli ƙirjin ya kalleta kuma ya nisa ya ce ""Kuma mene a ƙirjin?"" Ya faɗa yana yaye rigar." WE'LL SOON END OF THE FREE PAGES. Ku hanzarta biyan 500 domin karanta Mutallab posting za mu "babu ɓata lokacin ba lallai ku fahimta a yanzu wanda suka shiga paid group sune da batu ko rabin book 1 babu shiga ba. Tsakiyar labarin akwai muke, mene ya faru a farko me zai faru tsakiya ba zaku taɓa sani" ba ko a sashe. MUTALLAB. "Book 1, 2 &3" 500 Naira 0116886423 Union Bank Na'ima Sulaiman S a tura shaidar biya ta nan 08164069385 "[10/21, 2:10 PM] Nanameera: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 12 *Bright pens..2nd batch* "Hannunsa ta cire da sauri ta ce ""ciwon fa a wajan ƙirjin yake yaya"" da mamaki Captain ya kalleta ya kalli" "ƙirjin, da gaske bai san mene matsalarta da hakan ba. Ya ɗauki lokaci kafin ya ce ""kuma mene special a" "ƙirjin?""" """Baka sani ba?"" Fiyya ta buƙaci jin amsa ganin har lokacin kallon ta yake da alama processing" "ƙwaƙwalwarsa take yi shi dai ya san wajan da aka caka mata wuƙar kawai zai gani. Bai sake cewa komai ya miƙe tsaye ya nufi fita, Fiyya ta bisa da idanu tana jinjina rainin wayon Captain yana abu kamar baya fahimta. Ta yi shiru bayan fitar tasa, ta ɗan jingina da jikin gadon thinking me ya sa abubuwa suke juyawa tare da faruwa ne? Ba wani tsanar Captain ne a zuciyarta sosai ba, kawai yadda yake abubuwansa ke ƙular da ita amma kaf yayyanta tana matuƙar so da ƙaunar su. Damuwar bai shige dalilin" "daddy na aura mata Captain ba, bayan shi blood brother ɗinta ne. Yanzu ita ce ba jinin daddy ba ko Aliyu?" Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un! "Da sauri ta riƙe ƙirjinta jin zuciyarta na harbawa, duk yadda take ƙoƙarin ko a cikin bacci ta sake ganin" "gilmar reflection ɗin shi ta gagara, ko sautin muryar tasa ma ta mata sai kuma tunanin mahaukacin daya" caka mata wuƙa ya faɗo cikin ranta wai shi Mutallab? Who is he? """Who is he?""" "Muryarta ta sauka a tsakar kanta tana nanata mata tambayar da zuciyarta ta yi mata a fili. ""To ya ɗauke" "ni ya yi mini me? Safiyyerh Abdu Marafa ai ba sa'ar yara bace, bata zama teddy ba, the whole manager anya ya san me yake ce mini? Ba sai ya sake ganin ko inuwar fiyya ba balle ya aiwatar da abin da ya yi niyya a kaina, aikin banza aikin wofi don ma dai ban san ya zaro wuƙar bane zuwa gaba Captain zan" "lallaɓa ya ara mini bindigarsa problem solved""" Ita kaɗai take ta yin mita ta zubawa madubi idanu bayan ta miƙe tsaye. Wanka ta yi tare da alwala bayan "ta idar da sallah ta ɗauki skin products mai kyau dake sa fatarta laushi ta yi ta ƙyalli, tana son amfani da kayan Aisha s bayero skin care nd herbal medice, ta ɗauki riga mara nauyi saboda ciwon jikin nata. Kasa bacci ta yi ta ɗauki system ɗinta ta fara dannawa hannunta riƙe da ruwan zafi ta jima suna tattaunawa da Md da Secretary ta email kafin ta rufe system ta yi addu'ar bacci ta kwanta sai dai ciwon ya dameta" da zafi har zazzaɓi ya saka ta. "Washegari da ƙyar ta yi sallar asuba don bata yarda ta shige ta, ta rufe jikinta da duvet ta girgiza kai da" "ƙyar baccin ya sake ɗauke ta. Har 12 bata fito ba, sanin abin da ya faru da ita ya saka ba'a nemi ba'asin rashin zuwan nata kamfani ba." "Wajejen ƙarfe biyu ta buɗe idanunta dalilin ƙamshin da ta ji da kuma goshinta da ake murzawa a hankali," ta juya ta kalle shi taga waya ya ke yi muryarsa ƙasa tana jin yadda yake magana one by one jin ana "kallon shi cikin sauri ya ce ""i will call you later""" "Ya juya suka haɗa ido a hankali ta ce ""Ina yini?"" Ya yi mata shiru yana kallon kanta da sauri itama ta kalla" "sai yanzu ta lura kan nata yana cinyarsa ne shi kuma hannunsa na gefen fuskarta ""ɗaga ni""" """Yaya bani lafiya fa"" ya harareta kawai ya yi shiru shima ya ji zazzaɓin ta juya masa baya tana sauke" kanta idanunta rufe zafin zazzaɓin na ƙaruwa ji tayi ya ɗago ta zaune kamar wacce zai zaunar a cinyarsa "ya faki idanunta ya damƙe gefen cikinta ta yi ƙara tana riƙe shi ""Ki dai na yi mini sauti haka, za ki je" "zaman barrack lazy"" ta haɗe fuska tana ji yana taɓa cikinta yaga wajan ciwon na jini ya saka hannu ya" shafi ciwon ya taɓo jinin da hannu can ya miƙe yana juyawa. """Captain jini wajan yake yi ka fama mini na shiga uku"" idan ba kuskuren ji ta yi ba, muryarsa ta ji ya furta" """Allah Ya ƙara""" Cikin dare ne yana tsaye ya fito daga cikin motarsa sanye da manyan kaya na alfarma da fuskarsa rufe da "facemask ya dubi yaran da suke gabansa ya ce ""Ina buƙatar aiki cikin gaggawa bana son wani mistake" "idan aka samu akasi ina cikin taraddi, kuna kallo abu ya taho lokacin na neman cimmana"" Ya buɗe idanu yana sake dudduba inda yake tsaye gani yake kamar ana ganinsa za kuma a iya gane wanene shi." """Mai gida wanne kalar aiki ne ya fito da kai cikin duhuwar nan, faɗa taka cikawa tamu sai da kai iya wuya" "ba wani shege a baya wallahi"" ya ɗan yi murmushin jin daɗi yana kallon mai maganar da kana ganin shi zaka san a buge yake cikin maye kamar kullum" """Idanun mutane nake so, maza uku mata uku"" ya ce yana kallon wanda yake faɗawa maganar ganin" "yadda ya yi shiru kamar dai ban fahimta ba. ""Aiki ja idanun bama na mutum ɗaya ba? Akwai kuskure fa""" """Yanzu akwai wani aiki da zan iya sakawa ka yi mini da zai fi ƙarfinka? Kai ɗin amintacce nane na kuma" "yarda da ƙwarewarka ina jin daɗin business da kai wallahi"" ya zaro kuɗi masu yawan gaske ya miƙa masa, ya sake zaro wata ƙwaya kala daban-daban masu kyan gaske da tsada kana gani kasan manya ne ke shan irin ta. ""Ka fara riƙe wannan kuɗin nasan kana buƙatar caji a kanka kafi yin aiki yadda ya kamata, idan ka kammala ka sanar mini zan faɗa maka inda zaka ajjiye ko?"". ""Ka yi ƙarko irin na dabino sai da kai wallahi yau zam dani, ko kan mutum ka ce na kawo maka a yadda ƙwayar nan ke buɗe mini tunani kawowa zan, ba ƙaramin ilimi ne dani ba da tuni fa ni zan yi ministan kuɗi nace na fasa, kaf ƙasar waye bai sanni ba don uwar mutum"" sambatu kawai yake na maye ya bugu ƙarshen buguwa, shi mutumin dariya kawai yake basa hakan kuma na yi masa daɗi ainun. Mota ya shiga ya bar wajan shi kuma ya gangara ya shiga lungun titin da suke. Tunda ya tafi ya zauna cikin yan'uwansa mashaya yake tunanin ta ina zai fara? Ina zai samu mutane har ya ƙwaƙwule idanunsu hankali kwance? Ya yi shiru yana kallon sama yana ta furzar" da iska mai ɗauke da warin sholi dana bakin gabaɗaya. ***** Mutallab ya tanƙwashe ƙafafuwansa kamar wani sarki ya kuma ɗora hannunsa saman cinyarsa cikin "kowacce ƙafa, kallon Abbasa yake tun ɗazo take magana yaƙi cewa komai ko tari kuma bai yi ba, raunukan jikinsa ya kame sai saura, ido biyu za ka yi da shi ba zaka ƙara marmarin kallon nasa ba, babu rahama a fuskarsa nan zaka ɗauka tunda Ammo ta kawo shi duniya bai taɓa yin murmushi ba, ko haɗa" hanya da inda fara'a take. """Kalli nan""" "Ya dubi abin da take nuna masa, zanen kamfanin ne da photon jariran sai kuma kalmar A.M.A ""Da fari" "mu fara gano ma'anar kalmar A.M.A, photon jariran kuma mai sauƙi ne ana nuna maka har jarirai da aka haifa yau ana siyar da shi a kamfanin FS WORLD INVESTMENT COMPANY, abu biyu ne wanda dole za ka yi ko kusan ukun, da fari sato ita wannan yarinyar ta yiwu a samu wani haske tattare da ita, na biyu kasan yadda duk ka yi ka mallake wannan kamfanin cikin sauƙi, na uku. ,"" sai kuma ta yi shiru ta dinga" kallon Moh ciki da bai """Waye Mutallab, waye kai, dole ka faɗa mini asalin waye kai kana ji na?""" """To na haƙura""" "Ya miƙe tsaye a hankali a lokacin ras yake sai abubuwan da sukai masa tsaye a zuciya da maƙoshi ""Dole" "na san waye kai, ko ka faɗa mini ko ba ka faɗa ba, abu na uku sai ranar da asalin naka ya zo kunnuwana zan furta maka shi"" bai dai yi magana ba, hannunsa zube cikin alijun kayan da Abbasa ta basa ya sauya da ƙyar yafi ƙarfin minti ashirin a tsayen yana harhaɗa kalmomin abin da zai ce mata ransa duk a jagole." """Lalacewar Moh bai kai ya sato yarinya ba""" """Kuma dole a yi hakan fa""" "Ya yi waje abinsa yana yana ƙoƙarin ficewa daga cikin bukkar ta ce ""Baka da lokaci fa Mutallab, kuma" "baka da ikon taɓa ta a waje idan ba kana shirin komawa gidan yari bane, kasan yadda za ka yi dai wish you all the Mutallab""" "Bai ƙara bi ta kanta ba, ya dinga ɗora ƙafafuwansa a ƙasa kamar mai tsoron taka ƙasa sai haɗe fuska yake" "yana kwaɓewa duniyar ya ji ta yi maza zafi ta ko'ina, ya rasa ina zai je me kuma zai yi sai ɗaga yatsun ƙafarsa yake wanda suke zara-zara matar nan Abbasa ta fara takura masa ko waye ya ce ta yi masa gyaran farce? Yama a ka yi ta samu mai yin aski ya wani kwashe masa suma? Bakin bishiya ya samu ya zauna ya sunkuyar da kansa ƙasa, zufa ta shiga tsattsafo masa ta tsakiyar goshi ya sa yatsa ɗaya yana gogewa ya shafa jikinsa ba kayan garawa ko ɗaya yana buƙatar fita daga yanayin da yake ciki, baya son" tunawa ko da wasa. "_“One day i will leave you, duk son nan da nake maka”_" "Ya ji saukar muryarta a kansa ta sauka har ƙasan zuciyarsa a ɗan lumshe idanunsa da ya yi, ya juya zuwa" "gefe sai yake ganin bidiyon abin da ya faru bayan kammala assembly, at that time yana can baya zaune ya yi shiru yana kallon students bai san da zuwanta ba sai ganinta ya yi ta baya kamar zata shige jikinsa ya fiddo manyan idanunsa waje yana miƙewa tsaye hannunsa ɗaya zube a aljihu ya dinga kallon ta da" "ƙyar ya furta ""And what is this Safiyyerh?""" """Bestie shi ake cewa love mana"" ta langwaɓar da kai gefe yana sake kallon yaluwar fuskarta kamar" "zabiya. ""To iskanci za ki mini?""" """Iskanci kuma bestie? Me ya sa kake haka ne, son ka kawai nake yi fa why are you doing this to me? Kai" "ba'a gane maka sam? Ko murmushin masoya ne ka dinga yi mini mana, bafa ni na ɗorawa kai na son ka ba"" idanunta ya cika da waye tana jin zuciyarta na yi mata zafi bata ganin komai a idanunta sai fuskar Mutallab." """A love? Shine za a yi wa mutum fyaɗe a soyayyar??"" Ta buɗe idanu tana rufe baki jikinta har rawa yake" "tana jin kamar ta idda abin da zuriyarta ke umartar ta ""To ka yi haƙuri idan dai na mutu ka huta, kuma idan baka zo gidanmu yau ba Allah a wajan Ammo zan kwana"" fuskar nan a ɗaure ya ja sirirn tsaki ya shige cikin class kafin ya ƙarasa ya ƙara jiyo ta a bayansa tana sake yunƙurin riƙe shi da sauri ta juya sai" kuma ta ɗauki school bag ɗinta ta fice daga makarantar tana kuka. "*** ""i missed the hug"" ya furta ƙasan zuciyarsa lokacin da bidiyon abin ya ɗauke daga kusa da shi, ya yi" shiru yana tunani har yamma ta yi lis bashi da niyyar tashi daga wajan baya son shiga cikin jama'a yana jin nan ɗin shine daidai da ina ya kamata ya ɓoyewa kwalawa. He feels uncomfortable a cikin jama'a haka nan. Safiyyerh na zaune bayan ta dawo daga kamfani ko ɗaki bata shiga ba idan ta tuna yadda Hon Maɗatai "ya sake matsa mata akan hannun jarin da yake son sawa a FS WORLD INVESTMENT COMPANY sai ranta ya sake ɓaci, duk dukiyar da Ubangiji Ya bashi bai gode Allah ba, mutane nawa ne a wannan duniyar da basa ci, idan anci na safe ana fargabar na rana, idan na rana ya samu dare kuma sai dai a yi salatin Annabi a sha ruwa a kwanta, masifar rayuwa ta yi wa talaka dirar mikiya, yunwa na neman illata su ga lalura ga rashin aikin yi? Amma hon Maɗatai shi dukiya yake nema idanu rufe ƴan siyasa da yawa kansu kawai suka sani suke ginawa, mene amfanin talaka ya je ya yi zaɓen? Gabaɗaya sabgogin dimokuraɗiyya ya lalace son zuciya kowa yake bi. Ta yi tsaki tana jin ko zata rasa kujerar Manager ɗin ba zata taɓa bari" Hon Maɗatai ya saka hannu a kamfanin ba. "Miƙewa ta yi ta nufi bedroom bata ɗauki wani lokaci ba ta fito sanye da wando da riga,wandon iya cinya" "kanta ko ɗan kwali babu da mamaki take kallon Captain ganin ya ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya yana danna mata system ga wayarta a hannunsa kafin ta ƙarasu ya kashe system ɗin ya ajjiye har wayar. ""Yaya me kake nema a system ɗita kuma?"" Ya yi mata shiru ta zauna kawai tana buɗewa bata sake kallon shi ba, ta shiga duba dukkan ayyukan da aka fitar yau da sauri ta kira accouter da number da take amfani da shi na" kamfanin tana girgiza ƙafa a hankali cikin faɗa ta ce """Accouter me nake gani a haka? Kuɗi fa kimanin miliyan 500m yanzu sun shigo account na kamfani dana" "gani a bayanai, bayan tafiyata me aka fitar ne shinkafa ko me?"" Faɗa take sosai domin ta iya faɗa ajin" ƙarshe ce a fannin. """Manager nifa kina tunawa accouter ne kawai, bani ke da alhakin saka hannu a fitar kaya ko shigowar su" "ba, kawai ni ke saka hannu a duk wani kuɗi da zai shigo ya fita, i am nothing but a Accounter""" "Miƙewa tsaye ta yi tana riƙe ƙugu ta ce ""Rubbish; ka tura mini ducoment na PDF via email na abin da aka" "siya har miliyan 500m yanzu yanzu accouter""" """Ki yi magana da Md ni kawai kuɗin naga shigowar su babu wani file daya zo officer nawa, trust me" "manager ba zan ɓoye miki, na san dai bayan tafiyarki Professor Abdu Marafa ya shigo kamfanin"" ""daddy!""" "Ta furta da ƙarfi ""E, mahaifinki shi""" """Kamarya to?""" """Shine ban sani ba"" sai kawai ta kashe wayar ta ajjiye waje guda, ta sauke numfashi da ƙyar ta shiga uku" "meke shirin faruwa ya ake ƙoƙarin amfani da ita ba tare data sani ba?""" """Yaya"" bai amsa ba idanunsa a ƙafarta ta ce ""Yaya bacci nake ji"" ""to ina ruwana""" Sai kawai yaga ta ɗora kanta a cinyarsa maimakon ta juya masa baya sai ta juyo wajan cikinsa ta yi shiru "tana kallon ƙirjinsa dake buɗe. Ta yi shiru tana sauke numfashi shi dai bai yi magana ba, bai ɗauka haka take da masifa ba yana jin ƙirjinta na ɗagawa a hankali kuma bacci ya ɗauke ta. Cikin baccin ta ji hucin numfashi ta buɗe idanu kallonsa ta dinga yi yadda ya kifa fuskarsa a tata hannunsa ɗaya tamƙe cikin nata ""Captain"" da sauri ya buɗe idanun ya ƙurawa cikin idanunta ido sai kuma ya ɗauke fuska yana haɗe rai. Fiyya bata ce komai ba ta miƙe zaune shi kuma ya shige cikin part ɗinsa yana taku da sauri sai shafa" kai yake yi. Notification ta gani kamar wancan lokacin saƙo ne ta dm nata. Ta buɗe ba wani magana mai tsayi bane sai dai maganar dab take da rusa tunaninta ta bi saƙon da kallo inda ake cewa. "_“bai ci a ce kin yi mantuwa mai nisan haka ba, ki tuna akwai hakƙin wani kan ki Allah Yana kallon ki" TIGER“_ ta dafe kan ta to hakƙin waye a kanta waye mai wannan saƙon kuma? Tsaki ta yi ta miƙe ta bar parlon. Bata sake ganin Captain ba har dare ta yi kwanciyarta. **** Cikin sauri take tafiya tana yi tana juyawa sauri take ta isa chemist amsar maganin ga dare ya raba mijin "nata ya fita. Kamar daga sama taga mutane sun tsaya gabanta fuska rufe ""Su waye ku? Don Allah ku rufa mini asiri magani zan siyo"" muryarta na rawa ta yi maganar. Haɗa idanu sukai sai suka ɗaga ta sama tare da danna ta cikin napep ɗin basu tsaya ko'ina ba sai wani kango a nan taga wasu mutanen kwance kamar basu da rai, kuka take tana duk addu'ar data zo bakinta ""Don Allah kar ku cutar dani don Allah ku" "rufa mini asiri da yarana da rayuwarsu""" Tana ji tana gani suka danneta tun tana ihu har ta kasa jini kamar an yanka rago babu imani suka cire ƙwayar idanunta duk biyun tare da watsa su cikin aliju da gudu suka fice daga kangon. "Bayan ta dawo daga wajan aiki ta shige gidan Anty Turai saboda kiran da ta yi mata, a parlo ta samu Anty" "Turai da yaranta da kuma wasu ƴan mata zaune. ""Ina yini Anty?""" """Sannu matar Captain Aliyu Marafa?"" Cewar Anty Turai ita dai Safiyyerh idanunta akan waya bata ce" "komai ba Waheeda ta ce ""Mama wai shi Uncle captain ɗin son ta yake yi ne? Ni banga abin so a jikin wannan zabiyar ba sam sam wallahi"" Zahiderh ta yi saurin cewa ""Ina fa? Captain ne zai ce yana son Fiyya" "never wallahi, kawai dai auren dole aka yi masa, wannan fari ko na lalura""" "Safiyyerh dai jinsu take Anty Turai ta ce ""Sannu Safiyyerh, ya kamfanin yanzu ai Aliyun ya bar nan wajan" "Zahiderh ya zo ki dinga haƙuri da shi ya jaddada mini baya buƙatar ki cikin rayuwarsa bai san me zai yi da zabiya ba"" miƙewa Safiyyerh ta yi ta ce ""To Anty a ɗaura masa aure da Zahiderh ni bani da wata matsala, zabiya kuma ina jira ku halitto irin kalar idan da sauƙi, so kuma ba abin da ya yi mini zafi da shi zan zauna da mijina haka tunda zaɓin daddy ne, wallahi babu wanda ya kai level ɗin ɗagawa Fiyya hankali"" Anty Turai ta miƙe tana nuna Fiyya idanunta ya rufe sam bata kula da shigowar shi ba, balle ankarar da ita da" su Waheeda suke ta ɗaga hannu zata mari Fiyya dake tsaye tana juya idanunta ta ji an riƙe hannun. "Tun zuwan shi ta ji ƙamshin turaren nasa, ya tsaya a bayanta Anty Turai ta kalli Aliyu ta kasa cewa komai" "ya saki hannunta yana matsawa bayan Fiyya ya zagaye hannunsa a ƙugunta ya jata jikinsa daga baya yana sake kallon Anty Turai ""Shekararki nawa Anty yaushe na zo gidan naki kuma? And who told you bana son ta?"" Duk a dagule yake maganar yana sake haɗe Fiyya da ƙirjinsa kasancewarta duguwa sosai" "so ma sha Allah. ""Aliyu ni zaka shigo gida ka faɗawa haka?""" Bai kalleta ba sai Fiyya daya kalla wacce take shirin juyawa idanunta cike da hawaye ya yi saurin riƙo "hannunta yana ""Wait"" sai kawai ta kifa kanta a ƙirjinsa tana shassheƙar kukan da bata shirya saboda" "ganin idanunsa ""Anty karki sake mini haka""" """Idan na sake me za ka yi Aliyu na ce me za ka yi?"" Ya girgiza kai ya rungume Fiyya tsam a jikinsa ya ce" """Ban san me zan iya yi ba, kawai dai na faɗa miki, kuma i love my wife"" Fiyya ta yi saurin ɗago kai ta kalle shi ya ɗage mata gira ""Yes, I Iove You Safii"" yana cewa haka ya kama hannunta suka fice." *** Suna zaune a dabarsu ya yi sauri ya miƙe tsaye Goje ya ce """Sai godiya, ina aka nufa don shirwa kake baka jewar banza, ɓauna mai tafiyar ɗaukan rai jeji naka" "dabbobi naka, a lafiya mai dawa"" jikinsa ya ji ya fara kakkarwa tsohon tsuminsa na neman tashi ya yi ƙasa da kansa yana ƙoƙarin hana kansa yin kirari da amsar saƙon Goje, ya bar wannan layin tuni. Da ƙyar yana girgiza kai ya ce" """Goje""" """Sai godiya, wuya a ina wuya a daji kai ne mai dawa da jeji na Malam Abdu shalelen Ammo, ƙanin" "Sa'adah da Bafullatana a lafiya aminin Hamida, ɓauna taka mesa taka ba wani bayanka jan biro maganin daƙiƙin yaro Allah Ya ja da ran mai dawa"" gabaɗaya jikin Mai dawa ɓari yake yana damƙe hannunsa wajan ganin mai ɗaga su sama ba har can cikin kansa yake jin kirarin. Kawai ya juya ya bar wajan ""Wai" "ina zaka ne kasan yanayin da ake ciki fa akwai cinnaku""" """Baka haifan ba balle ka tambayan karka biyo ni"" yana cewa haka ya bar wajan ya jima yana tafiya kafin" ya ƙarasu gidan sai ya saka maƙulli ya buɗe ya shiga. A ɓangaren su Safiyyerh tunda suka bar gidan Anty Turai suka shiga mota basu ce komai ba ya kuma "haɗe fuska itama bata ce komai ba, daidai wani gida a bakin titi taga ya tsaya ya kalle ta ""Kar ki fito jira ni nan"" ta jinjina masa kai. Fita ya yi ta jingina tana ɗaukan waya, abin da ta fara cin karo da shi a X picture ɗin wani kyakkyawan yaro yana murmushi ya rufe idanunsa saboda hasken da ya yi masa yawa kamar ka" "taɓa shi jini ya fito, ta dinga kallon picture ɗin sai kawai ta yi skipping zuwa next tweet." "A hankali ya buɗe ƙofar ya shiga idanunsa zube a saman tafkeken screen ɗin computer dake jikin bango," "gabaɗaya wajan nau'in kayan computer ne kala-kala. Ya ɗan dafa kafaɗar wanda yake zaune akan kujera yana juyawa a hankali, kallo ɗaya zaka yi masa kasan mayen computer ne masanin hakin da duk wani surƙulle. Captain ya ce ""Where are you hiding?"" Ya ɗaga idanunsa a hankali ya kalli Captain bai ce komai ba kuma ya cigaba da danna wayar, Captain ya saka hannu ya dungure masa kai ya nemi waje ya zauna yana taɓa computer shima. Da sauri ya miƙe kuma jin sautin muryarta da yadda take ƙoƙarin buɗe ƙofar ya yi saurin miƙewa ya nufi ƙofar daidai nan Fiyya ta shigo ""Yaya gaskiya yunwa nake ji akwai hadari" "sosai a gari ina tsoron ruwa""" """Muje""" Ya yi saurin faɗa yana kama hannunta tare da rufe ta da jikinsa leƙawa take son yi ya saka hannu ya juyar "da fuskarta ya jata waje, shima ɗin dake zaune ya juyo a nutse ganin sun fita ya saka ya cigaba da abin da yake yi." "Cikin dare Fiyya na bacci ta ji ana buga ƙofar parlon kamar za a cire ta, ta miƙe da sauri riga da wando ne" "jikinta na bacci wandon iya cinya ta saka slipper ta fito, tana mamakin mai ya sa Captain ya kai dare har haka? Ta buɗe ƙofar ""Yaya ka tashe ni daga musulmin bacci da nake..."" Shiru ta yi tana yin baya ganin shi tsaye a bakin ƙofa su Goje da Mangal a bayansa ""Kai ne me ka zo yi mini har gidan mijina, matar aure ce" "ni fa"" banko ƙofar Moh ya yi ya shiga yana ƙarewa parlon kallo" """Mai dawa ɗauke ta mu shige kar a yi ta kwanaki"" ta gudu Fiyya ta juya zuwa part ɗin Captain tana kirin" "sunansa a tsora ce kafin ta ƙarasa Moh ya saka ƙafa ya falleta ta faɗi ƙasan tayal idanunsa ya yi jajur domin ba haka ya zo da su ba, jin ana shirin buɗe ƙofar ɗakin Captain Moh ya kalli Goje da sauri Goje ya laɓe a baya kafin Captain ya fito, cikin sauri ya rufe fuskarsa da ƙyalle." """Safii are you ok? Peanut ihun nan fa wife?"" Yana fitowa Goje ya saka gora ya maka masa a ka" kasancewar Captain bai shirya ba ya faɗi a wajan da sauri kuma Moh ya ce Goje ya ɗauki Fiyya ko me ya tuna sai ya saka hannu ɗaya ya sunkuceta a kafaɗa yana ɗaga wuƙa sama suka fice daga gidan... MUTALLAB. "Book 1, 2 &3" 500 Naira 0116886423 Union Bank Na'ima Sulaiman S a tura shaidar biya ta nan 08164069385 Zan yi cutting free a shafi na 15 in sha Allah. Wannan shafin ku hanzarta yin payment "kafin wannan lokacin yanzu kuma na labarin a rufe yake zuwa gaba za ku ce kun shiga uku ashe haka abin yake ina ƙara tuna muku ba fa farkon labarin muke a tsakiya muke waya san mene ya faru a farkon? Me kuma zai faru a gaba? Just pay 500 naira only.[10/23, 5:43 PM] Nanameera: *❤🔥" MUTALLAB ❤🔥* Page 13 *Bright pens..2nd batch* "Safiyyerh na durƙushe a ɗan ƙaramin ɗakin da suka ajjiye ta ciki, warin sigari ya cika ɗakin sai yunƙurin" "amai take yi ta kasa, ta shiga tashin hankali da tunanin suwaye waɗannan da suka je har gidan mijinta suka dake shi tare da yin kidnapped ɗinta? Me suke buƙata a wajanta waya saka su yin hakan? Da alama ba kuɗi suke nema ba wani muradi ne a ran su da suke son cikawa manufar da bata san ta mece ce ba. Ta ɗago kanta da ƙyar tana buɗe kumburarrun idanunta saboda kukan da ta yi da hanzari ta fara buga" ƙofar da hannunta tana girgizawa tare da faɗin. """Wai baku da imani ne me na yi muku idan kuɗi kuke buƙata ku bani waya na kira daddyna zai biya duk" "abin da kuka buƙata na fansa ta, macace ni fa a gidan mijina kuka je har gabansa kuka sato ni, don Allah ku buɗe mini wallahi wari zai kashe ni babu iska a ɗakin ku tausaya mini"" abin da take faɗa tana dukan ƙofar da hannu, amma ko tari ba ta ji sun yi ba, kuma tana da tabbacin suna jinta ta sake ɗaga murya ta" ce """For the sake of Allah, da girman iyayenku ku mayar dani gida gaban iyayena me na yi da za a yi garkuwa" "dani,ku barni da raina kar ku kashe ni zan muku kwatancen gidanmu ku je wajan daddyna a baku dukkan kuɗin da kuke buƙata, idan ba ku yarda ba ku a cikin kuɗina zan baku wallahi mahaifina ya ji abin da ya same ni mutuwa zai yi, innalillahi wa'inna ilaihirraji'un me na yi muku ne kukai garkuwa dani na shiga uku ni Safiyyerh Allah ka kawo mini ɗauki"" ta sake durƙushewa a bakin ƙofar ta tura kanta cikin cinyoyinta saboda warin sholi daya gama hautsina mata ciki kamar kayan cikinta zai fito haka Safiyyerh ke ji, duk girman idanunta sai da ya yi mitsi-mitsi abin ka da zabiya da ƙyar take buɗe idanun nan, ba sunan wanda bata kira ba hadda Anty Turai akan su kawo mata ɗauki Yaya J ya sha kira. Ta sauke ajjiyar zuciya tana karanta addu'ar neman tsari da kuɓuta daga magauta ta yi zumbur ta miƙe saboda fitsarin" dake mintsinin mararta. "A can wajan ɗakin a cikin gidan da su Goje basu san da shi ba, duk suna zaune suna busa kayan shaye-" "shayensu hayaƙi ya cika wajan, wani na shan sigari wani na shan sholi wani wiwi sun hautsina sai surutai suke yi. Moh na gefe ɗaya ƙwance ƙafarsa ya ɗora akan ɗaya idan yana acting ka ɗauka jinin sarauta ne ko wanda yake da aljanu sarakai a kansa, duk ihun da Fiyya take yi da surutai yana jinta. Goje ya kalle shi" "ya ce ""Wannan yarinyar tafa dame mu wallahi, ka kira ka faɗa masa tunjiya mun ɗakko ta ya san abin yi""" Shiru ya yi yana sake kaɗa ƙafarsa a hankali har lokacin idanunsa a rufe yake. Goje ya kalli ƙofar ɗakin da "Fiyya ke ciki ya sake kallon Moh kafin ya miƙe tsaye ya ce ""Ina da matsala da jin kuka gaskiya, ko dai a" "rufe mata bakin ko a ɓara bakin biyu yanzu da askira""" """Mangal""" "Da sauri Mangal ya kalli Moh jin ya kira shi domin tunjiya da suka ɗakko Fiyya ko tari bai sake yi ba, bai" "runtsa ba har gari ya hawaye ba wanda kuma ya kula a cikin su. ""Ankar sarki, faɗa taka cikawa tamu" "akwai wani sagi a ƙasa ne?""" """Bana son hayaƙin nan"" lokaci guda suka kalle shi a take suka cillar da sigarin tare da saka ƙafa suka" "murje ""Angama sai mene na gaba?"" Bai magana ba ya juya musu baya a hankali ya buɗe idanunsa ya zaro takardar da yake faman ajjiya kamar rai, kusan kullum yana karantawa sama da sau wajan biyar a rana abu ɗaya ne amma sai ya ji baya fahimta,baya kuma ganewa, ya zubawa rubutun idanu Goje shima ya leƙo kai yana kallo ganin ya ninke ya ɓoye ya saka ya yi siririn tsaki ""Na ji takaicin rashin makarantar" "da ban, shi ilimi ko yaya yana da rana""" """Ina zargin wannan takardar bata tsafi bace, kamar ita ce ransa ko iskar dake shaƙa ya manta da komai" "amma banda ita, watarana sai na sace ta yasin"" dariya Goje kawai ya yi ya san Mangal faɗa kawai yake yi. ""Mai dawa kasan a yankinmu an sace mutane har biyu, yau da sakaliya anga gawar ɗaya ba idanu"" ya juyo a hankali ya zubawa Goje idanu kamar mai tunani sai kawai ya miƙe yana taku ɗaiɗai ya fice daga" "cikin gidan, suka bisa da idanu ganin yau ya zama wani so silence kamar ba Moh ba." "Safiyyerh ta ji an turo ƙofar da sauri ta miƙe tsaye tare da ja baya, mutum biyu take gani Goje da Mangal" "shi kuwa tunda ya cillar da ita a ɗakin bata ƙara ganin shi ba. Abincin hannunsa ya cilla mata da ledar ruwa pure water ta kalli takeaway ɗin da ruwan, ta ɗauke kai a hankali tana sake ja baya ""Saura ki ƙi ci kamar na ɗazo, idan kuma kika sake yi mana amai a nan sai kin lashe abin ki tas"" ta ƙurawa wajan ido ta ce ""Ba zan iya cin abinci a nan ba, ni bana shan ruwan leda abincin ma ba irin wannan nake so ba, ko" "nama babu akai""" """Kuma a ina kike tunanin ganin nama? Don ma kin samu an kawo miki dar yarinya saboda kina Manager" "kun saba cin mai kyau a sha mai kyau, a saka suttura a shiga mota a kwana cikin a.c ga naru a gida 24/7, a ci shinkafa basmati da ruwan gora dole ki ce haka, ɗiyar ƙaruna""" "Girgiza masa kai ta yi muryarta na rawa ta ce ""Da gaske nake maka, ni kawai a bani ruwan jakar da lemo" "ko snacks"" Goje ya dinga kallon ta ganin she is serious juyawa ya yi zai bar wajan ta yi saurin cewa ""Don" Allah ku bani waya na kira daddy na maka alƙawarin yanzu za a kawo kuɗin da kuke buƙata wajan nan "akwai sauro headache da fever zai kamani"" ta langwaɓar da kai gefe alamar neman alfama." """Ki jira Mai dawa ya zo, sai ki tambaya bani da ikon haka. Da kike maganar kuɗi kin ji mun ce muna" "buƙata ne? Ba kidnapped ɗin ki mukai domin a bamu kuɗin fansa ba, mun sato ki saboda a koyawa asawa hankali a rage masa tsayin harshensa da yake da kauɗi kin gane? Daga yanzu ki cire rai da samun" "ƴanci""" """Daddy?""" "Safiyyerh ta faɗa a gigice tana dafe kan ta idanunta ya cika da hawaye, tausayin kanta dana daddy ya" "cika mata zuciya babu wani wanda take so a duniya sama da daddy da Ummi me za su yi masa rayuwarta suke son kassarawa tabbas idan suka taɓa kimar mahaifinta. ""Me daddy ya yi muki, mene alaƙae sato ni da kukai da mahaifina me kuke nema a wajansa na roƙe ka da girman Allah kar ku cutar da mahaifinsa kar ku illata rayuwarsa, shi ne jin daɗi da farincikin zuciyata, ku duka kuna da iyaye na tabbata ba za ku" "so rasa su a rayuwarku ba ka ji tausayina Please brother""" """Ni ba brother naki bane ni ɗan daba ne sunana Goje kin gane, idan kina buƙatar wani abu kina iya" "bubbuga ƙofar"" kafin Safiyyerh ta yi magana ya yi sauri rufo ƙofar ya fita. Ya je ya samu Moh a wajen gidan zaune ya sake tanƙwashe ƙafafuwansa ya kalle shi sosai kana ya ce" """Scorpion""" """Kana son faɗar sunan, zan manna maka hauka Goje zan ja maka ruwa"". ""Me ya sa baka son na dinga" "faɗa ne? Ai dafinka ma ya fi na kunama ni ina son sunan"" Moh ya yi shiru yana sake harɗe hannayensa duka biyun ya zubawa samaniyya idanu. ""Idan zan nuna maka asalin kalata a Scorpion ba zaka ɗauka ba," "za ka daina haɗa idanuwa dani sauƙin sunan na wajan faɗa ne, ka kalle ni a Moh ko Mai dawa ok""" """Yadda ka ce haka za a yi, ya zamu yi da yarinyar nan yanzu? Kwananta ɗaya da wuni fa, kuma bata cin" "abinci""" Cikin rashin fahimta Moh ke kallon Goje su yake ya tambaye shi wacce yarinyar bakinsa kuma ya yi masa "nauyi ya dinga juya idanunsa akan fuskar Goje, fahimtar hakan ya saka shima Goje cewa" """Manager wacce Ali wali ya saka mu ɗakko yarinyar da muka je gidansu jiya"" haɗe fuska sosai Mai dawa" ya yi idanunsa ya shige ciki haka kawai ɓacin ransa ya sake ninkuwa ya yi shiru ya datse laɓɓansa kamar "zai raba su gida biyu ya yunƙura zai tashi Goje ya ce ""Wannan sauyin na yanzu na mene? Na fara jin daɗi" "a raina kwana biyu baka sha ƙwaya ba, lafiya dai?""" """Mutallab"" still ya yi shiru Goje ya sake kiran sunansa yana leƙa fuskarsa ganin babu alamar zai kula shi" kawai ya miƙe ya fice ya bar wajan. "***Gabaɗaya suna zaune a cikin parlon banda shi dake tsaye, zuwan nasan ake jira amma tunda ya shigo" "bai kalli kowa ba balle ya yi magana, fuskar nan a murtuke kamar kodayaushe. Yaya J, Awais Dr Hash, Anty Turai Waheeda sai Ummi dake zan gefe bata cewa komai sai goge hawayen da yaƙi tsaya mata take yi. Daddy baya uhm baya uhm'uhm kansa a ƙasa zuciyarsa ta bugawa da ƙarfi yama kasa yarda da abin da ake faɗa har lokacin gani yake wasa ake yi masa da hankali da kuma wahalar da zuciyarsa da ake" saboda anga yana ƙaunar Safiyyerh ƙauna mai tarin yawa an fahimci ita ce rauninsa. """Captain Aliyu Abdu Marafa shiru ba naka bane, ba muzo nan da a shiru ba a matsalar kidnapping ba a yi" "mana wasa"" cewar Sp Ghali daya ƙara amsar case ɗin Safiyyerh a karo na biyu ya ɗaga kai ya kalli masu gadin asalin gidan da kuma na part ɗin su Captain sai kuma ya ce ""Heyy you man, mene sunanka da aikin" "da kake yi?"" Cikin rawar murya ya ce ""Sunana Isma'il ni mai gadi ne Yallaɓai""" """Isma'il sanda abin ya faru ƙarfe nawa ne? A daidai lokacin kana ina kuma?"" ""Ban san ƙarfe nawa bane a" "lokacin don ban duba a gogo ba, sanda abin ya faru kuma ina bakin gate ne amma kafin nan na miƙe na" "shiga banɗaki kama ruwa wallahi gaskiya nake faɗa maka Yallaɓai""" """To na ƙaryata ka ne? Kenan Isma'il bashi da sani akan waɗanda suka shigo gidan ko? Da ɗauke" "Safiyyerh?"". ""Duk abin da na ce maka na yi ƙarya abu ɗaya na sani fitowar su ɗauke da ita, hannunsu riƙe" "da makamai ɗaya ya ce na buɗe ko ya ɓola mini ciki na ji tsoro haƙiƙa sai na buɗe ashe sun yi parking mota wata ɓaka mai kyau daga can gefe""" "Murmushi kawai Sp Ghali ya yi yana duban ɗaya ma'aikacin ya ce ""Kai kuma fa? Mene information?"" Shi" "wannan jikinsa har ɓari yake don tsoro ya ce ""Yadda na gansu Allah Ya sa naga Annabin Rahama, misalin biyu da arba'in ne ina zaune na ji ana dirowa ta katanga kafin na yi magana ɗaya ya make ni yana nuna yatsarsa a baki alamun na yi shiru, ni kuwa na yi shirun don wallahi a lokacin na ɗauka mai gida shi sojan kenan daman shi ke kai wa dare a waje saboda yanayin aikin nasa, suka ɗaure ni ina hango sanda suka nufi part ɗin tunda can babu masu gadi daga nan ban san mene ya faru ciki ba sai gani mukai sun fito da" "ita a kafaɗa kamar ma a sume take yadda ta langwaɓar da kai""" "Daddy da Captain suka runtse idanunsu lokaci ɗaya, kowanne tunanin da yake daban a ransa, is he a" "loser? Captain ke tambayar kansa or he is falled as a husband maybe da yana kwana ɗaki ɗaya da Safii da hakan bai faru ba, idanunsa ya ƙara sauya kala. Daddy ma nasa tunanin dabanne, ko dai ya yi gaggawa ne ba yanzu ya dace ba? Ko mistake ya yi daya aurawa Aliyu Safiyyernsa ne? Is he a loser? Daya" kasa tsare rayuwar yarinyarsa mace ɗaya tilo a duniya ko dai da gaske he is falled as a father? "Kafin kowa ya yi magana ta shigo cikin gidan a gigice duk da nutsuwar da take da ita, da sauri kuma" Daddy ya miƙe tsaye cike da tsoro da mamaki hatta Captain sai da ya ji wani abu mai kama da faɗuwar "gaba, who told her? Tun kafin ta yi magana daddy ya yi saurin matsawa kusa da ita ganin yadda take ta zare idanu fararen idanunta fuskar nan nata ya ɗakko rana kamar ta yage don fari ""Zahiyerh""" "Girgizawa daddy kai ta yi a daburce ta ce ""Ina Maama?"" Ya yi shiru yana ƙoƙarin riƙe hannunta ta ƙwace" ta yi baya da ƙarfi kuma ta ce """Ina Maama? Ka bani ita na tafi da ita where is Safiyyerh""" """Safiyyerh has been kidnapped""" """Kidnapped?"" Ta maimaita tana juyawa ta kalli Sp Ghali anya ya san wacece ita da yake furta mata" "maganar anyi garkuwa da Safiyyerh kai tsaye bai tauna harshe ko ya lissafa maganar ba, Safiyyerh fa? Sp Ghali zai yi magana daddy ya girgiza masa kai yana sake kallon Zahiyerh wacce zuciyarsa ke buɗewa a duk sanda ya kalle ta. ""Ummimi please ki kwantar da hankali ki samu nutsuwa tafiyar nesa kikai jirgi kika" "hau""" """To na ji, ka faɗa mini meke faruwa da Safiyyerh?"" Daddy ya sauke numfashi a hankali kuma ya nuna Sp" "Ghali ya ce ""As he said, he told you already Safiyyerh has been kidnapped""" """Uhm""" """Komai zai daidaita Ummimi"" ita dai bata sake magana ba can ta ɗaga kai ta kalli Aliyu da sauri ya zame" "idanunsa ƙasa ta harɗe hannayenta a ƙirji ta tsaya jikin hawa steps ɗin bene. ""Afuwa Sp muje ko?""" """Next question ɗin mu akan Captain ne""" """Ok ka yi mana"" in ji Anty Turai." """Aliyu kafa yi haƙuri kalar aikin ku na sojoji daban, namu daban kowa da nasa iyawa da ƙwarewar a nasa" "ɓangaren ok. Aliyu kai ne zaka faɗa mana abin da ya faru a cikin gidan su waye suka sace maka mata har cikin gidanka a matsayinka na soja wanda kodayaushe zaka iya samun ƙarin matsayi na aiki, ya akai haka ta faru? Su waye?""" """Ban sani ba""" "Kai tsaye Captain ya bada amsa ""Baka sani ba? Har kuma suka ji maka ciwo kada ka saka na fara zarginka" "na yi tunanin sace Safiyyerh set up ne kuma ne ka yi plans ɗin hakan, ka sace matarka?""" "Aliyu ya dinga kallon Sp Ghali a hankali kuma ya ce ""E"". ""kana nufin ka sace matarka Safiyyerh?""" """E"" ya sake cewa" """Aliyu!!"" Daddy ya kira Aliyu da ƙarfi ya miƙe ya ce ""Da gaske ka sace Safiyyerh?"" Kamar idanun Captain" "za su faɗo ƙasa saboda yadda suka fito waje sai kawai ya lumshe ido ya buɗe ya ce ""E, na sace ta daddy""" "yana cewa ya fita daga parlon yana banko ƙofar da ƙarfi kamar ya cire ta. ""Innalillahi wa'inna" "ilaihirraji'un!"" Muryar Ummi ta karaɗe parlon ƴan mazan dai sukai shiru." """Karya yake yi"" Ummimi ta ce har yanzu taƙi zama lokaci zuwa lokaci kuma tana duba wayarta kawai sai" tabi bayan Aliyu. Daddy har jiri yake gani baya so a fitar da maganar ya fiso a yi komai secretly har Safiyyerh ta dawo gare su amma sai yaushe ne?. Only God knows. ****Ammo na zaune ta yi shiru a ɗakinta kamar kodayaushe ta yi nisa a tunaninta bata ma san Malam "ya shigo ba sai muryar Inna Binta da ta ji a sama wajan ƙofar ɗakin tana faɗin ""Yanzu don Allah Ammo da rana ma ba za ki daina kwantar miji kina satar kwana ba, wacce irin jaraba da masifa ce haka ni Bintalo jaraba kala-kala Malam ɗin duk da basir ya cinye shi da rana ma ba za a bar mana miji mu dinga ganinsa duk da ba wata tsiyar yake yi mana ba"" Ammo ta cira kai ta kalli Inna Binta ta juya ta kalli gefe har yanzu" ba taga Malam ba cikin rashin fahimta ta ce """Kamarya?""" """Ohho shafa ki ji mace an girma amma sai shegen munafurci da kissa wato kafin ki gama sallama ɗan" naki wa duniya kafin ya gama zama ɗan ta'adda ya miki aikin mallake malam ko? Shi ya sa kaf gidan nan "kin fi kowa yawan yara"" Ammo ta kasa cewa komai da ƙyar ta buɗe baki ta ce" """To ina Malam ɗin yake yaushe ya shigo mini?"" Ta banka mata harara ta nuna mata malam dake zaune" "ya yi shiru a hankali ta furta ""Ikon Allah ki yi haƙuri ban san ya shigo ba"" Malam ya yi gyaran murya ko" "kallon Inna Binta bai yi ba cikin damuwa ya ce ""Ammo ki nutsu ki ji me zan ce miki babu tabbacin abin" "dai har yanzu, ki yi haƙuri idan har hakan ya kasance gaskiya""" Jin haka ya saka Inna Binta neman waje ta zauna a bakin dakalin ɗakin Ammo ita dai wacce ake maganar "domin ta shiru ta yi tana bin Malam da kallo gabanta na faɗuwa ba wai yanzu ta saba da faɗuwar gaba ba, ta ji wannan ta musamman ce. ""Gawa aka tsinta. ,"" ""Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un! Na Ammo?""" "Malam ya ƙura mata idanu bai taɓa zaton tunanin wancan gantalallan yaron mara amfani a duniya zai zo ranta bq, ya girgiza kai kana ya yi shiru caraf Inna Binta ta ce ""Idan shine ai gwara ka faɗa ko kuwa? Kai aka cire masa ko wuƙa ce harsashi ne ko rayata ko babbake shi aka yi kasan haka ake yi wa ƴan daba, wallahi wani da aka rutsa shi ƴan unguwar jahilin duka sukai masa, ashe shima dai irin tsinannen yaron naka ne wuƙa bata huda shi, suka dinga rutsa masa dutse aka ina sai da kan ya ya yi dugu-dugu a nan cikin gari akai abin, da iyayen nasa suka je wajan ƴan sanda cewa sukai su yi haƙuri gawar ba zata ɗakko ba ta yi muni yaron nan dai da yake bashi da rabon rahama ko sallah ba a yi masa ba, yana can za a yi" "gwaje-gwaje da gawar ƴan makaranta daman ƙarshen duk wani ɗan daba kenan""" "Malam ya yi shiru bai yi zaton haka Inna Binta take ba, Ammo rasa kalmar da za ta yi amfani da ita ta yi" "wajan yi wa Inna Binta, ta yi shiru tana sunkuyar da kai." """Malam ka faɗa mata kawai sai ta ɗauki don gana""" """Wallahi tallahi ko""" Mama ta yi caraf ta faɗa ashe itama tana laɓe a jikin taga daga waje. Ya girgiza kai kawai cike da takaici "kana ya ce ""Gawa aka tsinta ta mace an cire mata idanu biyu kuma an cillar da ita bakin hanya, aka kira" "ana tunanin kamar gawar"" haka kawai ya ji yana jin tsoron kalmar da abin da zai biyo baya Ammo ta ƙura" "masa idanu a sanyaye ta ce ""Sa'adah ce ko Bafullatana ko Hameeda?""" """Hameeda""" """Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un! Astagafirulla Allah mun tuba jama'a an cire idanun Hameeda gatan na" "ammo ta shige jama'ar gida Hameeda ta mutu a kawo mana ɗauki"" a gigice Inna Binta ta zari mayafi tana ficewa zuwa maƙota. Mama kuma ta yi shiru idan haka ne ba ƙaramin gigita mutuwar Hameeda ya saka ta ba. Ammo bata ce komai ba a ranta tana nanata kalmar Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un! Ita kawai ta yi mata saura a cikin baki ""Ba a tabbatar bata, saboda haka ki taso muje a gani ƙila ki fini ganewa sosai"" kafin Ammo ta yi magana Baba uwar mijin Anty Hameeda ta shigo tare da mijin idanunta ya yi ja" cikin sauri Mama ta ce """Yaya lafiya dai Baba?""" """Ina lafiya, Hameeda ce daga fita siyo magani da daddare mun neme ta mun rasa kwana biyu kenan" "wallahi"". ""Shikenan ta tabbata an kashe Hameeda"" kafin ka ce me cikin gidan ya cika Inna Binta sai rusa ihu take yi tana sun shiga uku an kashe musu yarinya. Koda aka kawo gawar Hameeda ba kowa ya iya gani ba kamar dodo har ta fara wari an cire kyakkyawan idanun nan nata. Ammo ta dinga tuna nasihar Hameeda ta ƙarshe da ta yi musu,daga nan bata sake dawowa gidan ba wani abu ya tokare wuyan" Ammo ta kasa magana balle kuka sai kallon gawar take cike da sarewa. ****Kamar kullum yau na Goje ya buɗe ƙofar tana durƙushe duk ta fita daga cikin hayyacinta idanunta ya faɗa ba zaka taɓa cewa Safiyyerh bace. Ya dire mata abincin yau dai pure water ɗin hadda sanyin shi """Kar ki sake buga mana ƙofa domin ba wanda zai buɗe miki""" """Ka ɗauke bana ci""" """Dar kin yi kyan kai ƴar kurciya"" ya juya baya ta faki idanunsa ta zare ƙaramar wayar data gani a jikin" aljihunsa ta yi saurin ɓoyewa. Goje kuma ya dawo cikin harabar gidan Moh ya gani zaune yana sake karanta takardar sai ya yi murmushi yana dafa kafaɗar Moh ya ce """Ni dai na fara gajiya da siyo abinci gaskiya"" banza Moh ya yi yana ninke takardar tun daren da aka kawo" "Safiyyerh bai sake ganin kamarta ba sai sautin kukanta da yake ji kullum yanzu ma kukan take tana buga musu ƙofa da ƙarfi a fusace ya miƙe tsaye ya nufi ƙofar ɗakin Goje ya bisa da kallo can ya miƙe ya bi bayansa. Da ƙafa ya daki ƙofar ta buɗe da sauri Safiyyerh ta miƙe cak kukan nata ya tsaya a maƙoshi ta tattare ta haɗiye ta mayar zuwa cikinta, fitsarin dake mintsinin mararta ya saki kansa ya fara zuba a gefen ƙafarta, dukkan wata gaɓa ta jikinta ɓari take yi. Ashe da bata san waye ba, bata san waye ya yi kidnapping nata ba sai yanzu cikakkiyar siffarsa ta bayyana zubi da tsarin da halittar da Ubangiji ya yi masa mai firgitarwa bata san waye mafi muni a cikin ƴan daba amma ta san wannan tantirin ne ko daga tsaiwar da ya yi, cikakken namiji a tsaye majiyin ƙarfi matashi kuma mai jini a jika da cikakkiyar lafiya shine matsayin ɗan daba tsaye a gabanta gefen fuskarsa wani zabcecen yanka wanda akai masa ɗinki har ya zama tabo. Salati take ƙoƙarin yi ta kasa ta gama jiƙa wajan da fitsari ƙiris ne babu numfashinta ya" yi ƙaura daga ƙirjinta ta yi saurin ƙasa da idanunta. """Ka yi haƙuri kar ka mini komai, don Allah ko nan waje ne ku bar ni na fito kalli skin ɗina zai lalace akwai" "ants a nan waje"" ta tattare hannun rigarta tana nuna masa farar fatarta da ta yi wani irin tabo ritsi-ritsi kamar kwanciyar ji fuskarsa ta kumbura ta yi jaa sai susa take yi saboda ƙaiƙayi. Ta langwaɓar da kai ta ce ""Ka gani ko na sake nuna maka har bayana"" ta juya bayan tana ƙoƙarin ɗaga rigar ta ji ya daki ƙofar da" mahaukacin ƙarfi kafin ta juyo ya bar wajan. Ta sauke ajjiyar zuciya feeling reliver ganin ƙofar a buɗe. "Tana fitowa suka haɗa idanu da shi da sauri ta juya kanta na bugewa da jikin bango, anya tana da hankali" da lissafi kuwa? Fitsari fa a wando sai ya tsuke fuska. Suna zaune Mangal ya shigo yana hakki da sauri Goje ya zare wuƙa sama tiger ya yi zumbur ya miƙe tsaye yana gurnani Moh kuma kallon Mangal yake yana jiran ya ji suwaye suka biyo shi don yana da yaƙinin ba wanda ya san gidan da suke. """Kai ɗan wahala mene su waye suka biyo ka?""" """Daga layin su Mai jeji naje an yi rasuwa kuma a gidansu Moh aka anyata lahira wallahi"" duk suka juya" suka kalli Moh shima ɗin kallon nasu yake fuskarsa ba wani sauyi kawai ƙarashen maganar yake jiran ji. """Sai aka ce waye ya baza? Iyayen Moh dai akwai sauran rai wannan dar in sha Allah""" """Wai ko Hamida ko Hamda, idanu aka ƙwaƙule mata ashe tana cikin mutanen da aka sace ta"" Moh" "tunani yake yi ina ma ya san mai sunan Hameeda tasa Hameedan ba zata taɓa mutuwa a irin wannan halin ba, sam ba zata mutu ba duk da yanzu ba ruwansa da ita. Bayan wasu shuɗewar daƙiƙo zumbur ya" "miƙe tsaye kansa na sarawa a dagule ya furta ""Amini?""" Da sauri kuma ya yi wani ɗaki suna shiga suka same shi yana cakawa kasan wata sabuwar allura da Ali "wali ya basu da maye, bayan ya zuƙe ruwan a jikinsa ya ƙara ɗakko wata ya sake cakawa kansa sirinjin ana ukun Goje ya yi saurin matsawa ya ce ""Easy Mutallab,zaka haukata kanka a banza kasan wacce irin" "allura ce ko dan baka jin turanci muma bama ji, haukatar da mutane take yi fa?""" "Sakar masa allurar ya yi ya sake ɗakko wata Goje ya sake riƙe wa ya ce ""Wallahi in dai ina nan ba zaka" "sake yi ba"" ya ƙara sakar masa ya ɗakko fenta zai yi Goje ya ƙara riƙe, Moh ya shammaci Goje ya ɗauke shi ya damfara shi da ƙasa ya saka ƙafa ya take hannunsa hannun ya yi ƙara, ganin yana shirin kashe shi ya sa Mangal ya ɗakko abu ya makawa Moh aka, ya ɗauke ƙafarsa ya juya yana kallon Mangal da sauri" Mangal ya zare Goje ya fito da shi daga ɗakin da gudu suka fice daga cikin gidan. **The following days. Buɗe ƙofa Captain ya yi ya shiga ɗakin a hankali wanda ya yi wa Aliyu mugun sani shi zai lura da ramewar da ya yi. Idanunsa akan Ummimi dake zaune gefen gado hannunta tsakanin cinyoyinta ta sunkuyar da kanta ƙasa ya ƙarasa ya duƙa gabanta ya ɗora hannunsa a cinyarta a hankali kuma ya leƙa kansa ta ƙasa ya kalli fuskarta suka haɗa idanu ta zabga masa harara lallausan murmushi ya yi mata a hankali ya ce """Love""" """Aliyu fita""" "Ya girgiza mata kai ya yi shiru sai lokacin ta yi shiru tana ƙare masa kallo ""Ciwo ka yi ne Gadanga?""" """A'a love""" """Kuma yaushe ka damu da Maama har haka ka dame?""" """Love, Safii is my wife"" ta wani buɗe idanunta na rashin fahimta ""Waye Safii?""" """Safiyyerh, your Maama"" da sauri ta miƙe tsaye tana girgiza kai ""Yaushe aka yi haka? Tunanin waye" "hakan decision ɗin waye wannan professor ko?"" Gani take sauri take yi amma sai ta cire ƙafa ɗaya take mayar da ɗaya ta fice daga ɗakin a parlo taga duka mutanen gidan hadda police da team na musamman da suka fara bincike akan sace Safiyyerh Abdu Marafa. ""Ashe daman baka yarda ba professor za ka iya mini haka? Bana baƙin ciki da auren da ka yi musu amma ina da hakƙi na sanin ka haɗa Safiyyerh da Aliyu aure, Professor burinka ya cika ƙudirinka ya tabbata ka aurawa Safiyyerh Aliyu"" masifa Zahiyerh take yi tai Hausa tai turanci ta koma larabci ba wanda ya tanka ta, kan Abba a ƙasa. Da ƙyar Aliyu ya janye ta a ransa ya gode Allah da bata ce a raba auren ba tsaf zata iya. Ta nemi kujira ta zauna sai nishi" take yi na rashin lafiya. """Zo Aliyu"" ya ƙarasa wajanta ta nuna masa kusa da ita ya zauna, sai kawai ta rufe idanu ta kwanta ta yi" shiru a hankali ya fara danna mata kanta Dr Hash shima ya ɗauki ƙafarta data kumbura ya fara danna mata sai a lokacin Daddy ya buɗe idanu ya kalleta ya girgiza kai fatansa kafin ta farka Safiyyerh ta dawo gida. """Sp har yanzu ba wani kira da muka samu akan batun sace Safiyyerh, ina zargin anya issues na" "kidnapping ne?"". ""Za su kira ai sun sauya salo ina mai tabbatar maka cewa za a kira Safiyyerh zata dawo gida"" daddy ya jinjina kai ya yi shiru." Wayar Aliyu ce ta fara ƙara yana dubawa yaga kamar private number har sai share sai ya yi tunanin ko masu sace Safiyyerh ne? Da sauri ya amsa kiran was the first abin da ya ji daya nemi buɗe masa zuciya "sautin kukan Safiyyerh ƙasa ƙasa ya runtse idanu can ya ji ya ce ""Yaya Please help ants za su cinye mini" "fata Yaya za su kashe ni""" """Safiyyerh listen""" "Karo na farko daya kira sunanta ""Take a heart peanut, ke matar soja zama jaruma"". ""Yaya am scared" "wuƙaƙe"" ya buɗe idanu ya ga duk kallonsa suke yi hadda daddy Sp Ghali ya yi masa alama ya saka speaker. ""Kina ji na?"" Kamar tana gabansa ta ɗaga kai ""Be strong Maama, daddy is here for you, Ummi kowa ma hadda ni am here for you ƴan mata, hadda Ummimi"" da wani irin sauri ta ce ""Ummimi?" "Ummimita Yaya?""" """Sure, ki nutsu wanne waje suka kai ki, za ki iya tuna suna ko wanne abu da zai bamu haske?""" """Yaya sun rufe mini idanu ban san komai ba, don Allah ka taimaka mini daddy help me please"" idanun" daddy ya yi jajur already anyi connecting na wayar an fara bincke da ƙoƙarin tracking daga ina wayar ke zuwa. Shima kuma daga can haɗaɗɗan ɗakinsa da suke zube da kayan na'ura kamar hauka ya saka abu a kunne ya ɗora ƙafa yana girgiza kai a hankali yana jin conversation ɗin Safiyyerh da Aliyu yana yi yana duba time da cije leɓe. Abin da Aliyu bai taɓa yi ba kenan ƙoƙarin jan Safiyyerh da hira da ya ji Ummimi zata motsa zai yi saurin "girgiza ƙafarsa ""In sha Allah i will save you Safii, ki yi ƙoƙarin gane wani abu ki yi addu'a"" tana ƙoƙarin sake magana suka ji ihunta da ƙarar buga wayar da ƙasa ""Safiyyerh kina nan kina kan kayi baby?"" Aliyu ya jere tambayar. Kafin sun an kare daddy ya sulale a wajan babu numfashi." "****Tunda su Goje suka fita yake abu ɗaya kamar wanda za'a zarewa rai, sai buge buge yake yana fasa" "komai na gidan kumfa na fita a bakinsa ihun da ya yi da gurnani shi ya saka Safiyyerh sakin ihu tana yin cilli da wayar a gigice ta miƙe har lokacin kayan bacci ne a jikinta, tana fita ta ganshi a tsakar gidan ya yi tumu-tumu wani irin mahaukacin tausayinsa ya ratsa zuciyarta ta duba babu kowa a gidan sai ta yi tunanin wannan opportunity ne da zata bar gidan hankali kwance, bata damu da kayan jikinta ba sai kawai ta nufi ƙofa da gudu tana ƙoƙarin fita ta ji muryarsa cikin mawuyacin hali kamar ana fisgar ransa abin da ta ji ya saka ta tsaya ta yi jim itama kanta na sarawa tana gani bibbiyu ta sake yunƙurin buɗe ƙofar ta ji ya ce ""Safiyyerh. !"" Ya faɗa da ƙarfi a gigice ta juya taga ita yake kallo yana ƙoƙarin tashi ya" kasa yana miƙo mata hannu... *MUTALLAB IS NOT FREE* We'll soon end the free pages. ka yi payment a yi naka a paid group. MUTALLAB. "Book 1, 2 &3" 500 Naira 0116886423 Union Bank Na'ima Sulaiman S a tura shaidar biya ta nan 08164069385 Ƴan Niger kuma ya gadda tsarin yake. 'Yan Nijar ku turo carte airtel ta 300fcfa saman wannan layin 84506476 "[10/25, 11:14 AM] Nanameera: *This is not a love story,but a love that builds a story, and a love that" destroys the story.* *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥* Page 14 *Bright pens...2nd batch* *Author's books* Munafukin miji Moon Mijin malama Tsintacciya Idan ba ke Sirrinmu E.t.c Follow on Arewabooks Follow on telegram Remain 1 free page Jikinta rawa yake ganin ya kafe ta da idanunsa har lokacin kuma kakkarwa nasa jikin yake yana fesar da numfashi. Ina ya san sunanta? Take tambayar kanta. A hankali Moh ya lumshe idanunsa bayan ya janye su daga gare ta yana ɗan ciccije bakinsa. "Safiyyerh ta kasa fita, idan ta bar shi ya mutu alhalin zata iya taimaka masa Ubangiji zai kamata da laifin" "rashin tausayi da imani, ta salwantar da rai ta hanyar ganganci da son zuciyarta." """Safiyyerh taki rayuwar fa? Kashe ki za su suma fa, ya kamata ki bar wajan nan tunda kin samu dama, shi" "kinga kamar mahaukaci ne maybe"" zuciyarta ta bata shawara cike da gamsuwa ta jinjina kai tare da kama handle ɗin zata fice." Haɗa idanu suka sake sanda ta juyo ya dinga kallon ta rinannun idanunsa sai ta saki hannun ƙofar tana ɗaga ƙafa zata nufe shi. """Run Safiyyerh, run away run Safiyyerh""" Ta sautin muryar zuciyarta a cikin kunnenta ta sauka har tsakiyar kanta ƙirjinta ya dinga ɗagawa tana son tafiya bata kuma san meke janta zuwa gare shi ba. Ta girgiza kai """Save him frist"" ta furta a iya harshenta. Yana ganin ta nufo inda yake ya rufe idanu kafin ta ƙaraso ya" juya baya yadda ba zata ga fuskarsa ba. Jikinta a sanyaye ta durƙusa cike da tsoro ta kasa magana can ta yi ƙarfin halin furta """Ina ke maka ciwo?""" "Ya mata shiru ba bacci yake ba, domin tana hango yadda ƙirjinsa ke ɗagawa sosai yana ƙoƙarin ganin ya" "hana kansa yin abin da ƙwaƙwalwarsa ke umarta shi. ""To faɗa mini inda maganin yake na ɗakko maka""" Jin shirun ya yi yawa ta matsa tana leƙa fuskarsa suka haɗa ido ya zaro mata manyan jajeyen ƙwayar "idanun ta yi saurin ɗauke nata idon ""Tab kalli idanunka fa, ko asibiti zaka je?"" Ta yi maganar tana ƙoƙarin kai hannu zata taɓa shi ya mirgina gefe yana haɗe fuska kamar ya ce ya shiga uku, da zata gane to tabbas ita ɗin ce baya son gani ko jin muryarta ta kura masa hakan" yake yi sosai ya tsuke fuska yana rufe idanu Safiyyerh ta miƙe gabaɗaya hopefully ya buɗe ido ko ya bata "amsa ba sarewa ta sake miƙa hannu dukan da ta ji ya kaiwa jikin bango ne ya saka ta yi baya tana zaman ƴan bori,shima ya tashi zaune yana zazzaro idanu daidai lokacin su Goje suka shigo ya kalli Safiyyerh da" take yarfe hannu saboda bugewar da ta yi ya dubi Moh daya miƙe tsaye yana tangaɗi ya shige ɗaki yana "rufo kansa a ciki. ""Ke me kikai masa?""" """Ƙato da shi me zan masa?""" """Abu a duhu na san matan yanzu ba kunya ce da su ba, idanu rufe suke afkawa maza"" da mamaki" "Safiyyerh take kallon Goje zuciyarta babu daɗi ga takaicin rashin guduwa gana wancan da ko inda take bai kalla ba duk maganar da ta yi masa, ta matsa tana takure jikinta waje guda sai yanzu ma take jin kunyar shigar jikinta sosai, ita Safiyyerh yau ita ce take rayuwa a wajan ƴan daba mashaya kuma ƴan ta'adda hawaye ya cika idanunta sosai mutanen da sam basu suwaye su ba, basu san kansu ba basu da" wani amfani a wajan al'umma. """Ke kina ji ko?""" """Safiyyerh sunana""" """Mene ya daman kuma warning zan miki kar ki kuskure ki sake zuwa wajan shi idan kina son tsira da" "ranki ba, ba kema ko Abdu Marafa bane a nan wallahi zai iya ganin bayansa, ki yi abin da ya shafe ki kawai ki tsaya iya matsayin ki na wacce akai garkuwa da ita kuma ɓarayin gwamnati"". ""Shi wa?""" "Ya nuna mata ƙofa ""kin gane ai""" """A'a"" wuƙa ya zaro yana gwalo idanu waje ya ce ""Idan na cire miki yatsa ɗaya za ki gane ai""" """Ni mu yi magana ta fahimta daku, me kuke buƙata zan baku koma mene amma ku rabu dani don Allah" "ina kyakkyawan fata da muradan da nake son cimma a rayuwa naga ku babu inda kuka saka gaba rayukan ku ma sam baku damu dasu, wallahi ina buƙatar rayuwa mai tsayi da zan bar baya mai kyau ba zaku ɓata mini rayuwata ba, kuma warin sigarin nan juya mini kai yake da ƙyar nake shaƙar numfashi, ni macace mai hankali da ilimi wacce iyayena suka bawa tarbiyya daidai gwargwado in da ilimin addini" "saɓanin ku da ba lallai ko ummul kitahhb kun iya ba, ƴan daba ne ko masu laifi rayuwarku a gurɓace take" "ba a yi muku tarbiyya ba"" hatta Moh dake cikin ɗaki idanunsa a sama yana kallon rufin kwano sai da ya" "waro ido yana sauraren maganganun da take cewa, Mangal ya yi mata ƙuri da nasa idanun haka Goje" """Wuyanki ya isa yanka ba laifinki bane za mu yi maganinki""" """To me na ce na ba daidai ba, don Allah ku ba ƴan daba bane ƴan ta'adda kuma ga tantirin can shine" "shugaban naku da alama asalin daƙiƙi ne ajin ƙarshe sai wari dauɗa dana rana ga na shaye-shaye wallahi...,"" saurin haɗiye maganar ta yi ganin shi tsaye a kanta yana huci ta miƙe tsaye hannu ya ɗaga kamar zai kwaɗa mata mari ta kurma ihu tana ƙanƙame jikinta ""Don Allah ka yi haƙuri ƙarya nake yi wayyo daddy wayyo captain"" sai idanunsa suka sake jirkicewa ta buɗe idanu taga ya zuba mata nasa idanun fuskarsa dab da nata sai juya ƙwayar idonsa yake a saman fuskarta kamar mai son tantancewa" wani abu. "Ta tura baki cike da tsiwa ta ce ""Kana kwaɗa mini mari zan rama tunaninka rabuwa zan yi dakai ka ci" "bulus? Bayan an ce duk wani ɗan shaye-shaye bashi da wani ƙarfi hayaƙi ya cinye shi"" Goje ya ce" """Wannan yarinyar ƴar wasa ce bayan kuɗi data iya sarrafawa har rashin kunya ta iya Allah kar ka rabu da" "ita"" Shi dai Moh na tsaye yana kallon ta ita kuma ta kasa jure ganin ƙwayar idanunsa ta yi ƙasa da kanta tana murguɗa masa baki, bata ankara ba ta ji ya cilla mata baƙar kunawa cikin riga ta zumduma ihu a gigice ta yi kansa zata riƙe shi ya yi saurin baya yana ficewa daga gidan Goje yana ta dariya da buga ƙafa" """Kinga aikin Mai jeji gana Scorpion nan""" ****Eng Ali wali yana zaune a gidan wutawarsa yana zantawa da wasu manyan mutane masu taimaka "masa a harkar kamfel ya dubi P.a ya ce ""P.A ina tunanin iya abin da ake buƙata kenan kuma na bada, ka" "sani ba kuɗi yanzu a ƙasa kamfen ya cinye komai, you can manage ko?""" """Ba damuwa amma muna da raguwar list na local government wajan biyar da bamu je ba yanzu haka, ga" "ƴan media sun matsa kasan mutane babu amana gwara a fara watsa musu hatsi tun yanzu fa a yi maganin yunwar data addaba musu"" Ali wali ya yi murmushi yana juya kai kafin ya ce ""Ku je za mu yi" "magana zuwa dare ina da hira da ƴan zuwa dare we'll talk"" P.A ya kalli mutanen ya ce" """Don't make any mistakes idan kun shiga gidan rediyon ku tabbatar kun yi abin da ya dace, kar kuma ku" "nuna wata alaƙa tsakaninmu da ku yadda na faɗa muku haka zaku faɗa"" ""In sha Allah, ai harma da abin" "da baku buƙata ba mu indai za a biya mu ai buƙatar maje hajji sallah zamu farfaɗi ayyukan bogi da ya yi kuma ya yi mana""" """Nice to hear this, you can leave ku je""" Tafiya suka yi suna murnar ƴar dubu biyar biyar ɗin da za a basu akan faɗar abin da ba haka bane. Ali "wali na shirin miƙewa ya ji numfashi a bayansa ya juya da sauri, tsaye ya ga Moh fuskarsa rufe sai ƙwayar" "idanunsa da take a fili ya cake yana muzurai. ""ka bani tsoro amma""" """Mara gaskiya ko a ruwa zufa yake""" """Me na yi na rashin gaskiya?"" Ya yi masa shiru yana wani irin fito ya ɗauki ƙafarsa ɗaya ya ɗora saman" "kujera yana zaro kunama ya ajjiye saman kujerar wajan ta fara yawo tana ɗaga ƙari sama ta kumbura sosai. ""Yaushe ka shigo? Na ce ni zan dinga nemanka bawai ka dinga biyo ni duk inda nake ba, bana so a san ina mu'amala da kai""" """Saboda annoba ne ni? Tunda ka jawo ni haka zaka shanye duk abin da na dama, na kwalo yarinyar" "mene next?"" Murmushi Ali wali ya yi ya ce ""Ai na san kun ɗakko ta, tunda CSP ya yi mini magana akan case ɗin kidnaping sannu namijin duniya""" """Zan kawo ta nan""" """Ina? A'a ka bar ta nan wajanku zan baka key ɗin wani gida sai ku tafi can kwafi sararawa ni bani da" "gaske koda zaka dinga huta gajiyarka a wajanta kana rage zafi"" Moh ya ɗaga kai ya kalli Ali wali da kyau." """Wacce gajiyar, sanyi ne a jikinta?""" """Kana abu kamar ba wayayye ba, mu bar maganar ka yi mini aiki na farko and i appreciate it. Sai batun" "Scorpion"" daidai nan kunamar dake yawo a wajan ta shige hannun Moh ya matse ta ya yar waje guda Ali wali ya cigaba da cewa ""Scorpion ba zai bar mu ba, Hon Maɗatai yake hari a yanzu nasan kuma bayan nan ni ne a list, yana neman zame mana masifa yana kawo mana barazana a akan siyasarmu gwara Hon Maɗatai ya samu dukkan abin da yake nema a mulki ya samu nasa rabon ni yaushe na fara? I will never" "let that happen ba zan bari ya yi galaba akai na ba""" """Me za ka yi?""" """Zan tabbatar an nemo shi an ɓatar da shi, don ba haka kawai yake yin abin da yake ba akwai abin da ya" "taka yake taƙama da gadara dashi, ka yi ƙoƙarin nemo mini shi kafin hukumar FID su kama shi zan" "ruɓanya maka abin da duk na yi niyya""" """To kuna da case da shi?"" Ali wali yace ""Pardon? Kamarya kenan""" """Basar""" "Key ɗin gidan ya basa, hadda na mota Moh yaƙi amsa wai he don't know how to drive ya basa kuɗin" abincin Fiyya mai kyau da duk abin da take so. """Kaƙi faɗa mini waye kai dai ban san komai dangane da kai ba Moh, sunanka kawai na sani Mutallab" "without surname and middle name, whatever shikenan dai"" Moh ya ƙara ɗaga ƙafa zai fita Eng Ali wali" yace """One more think Mutallab""" """Ali wali ka kira ni da ɗan daba ko ɗan ta'adda sai mu yi magana"" Ali wali ya yi murmushi ya ce ""Sai" "godiya"" ya tsuke fuska Moh." """Professor Abdu Marafa ya mini mummunan tabo a zuciyar matasan jihar nan,ya ɓata mini suna na ji ina" "son ɗanɗana masa kwatankwacin abin da ya yi mini ta hanyar ramuwar gayya wacce ake cewa tafi ta gayya daɗi, kamar yadda ya ɓata ni shima haka nake so a ɓata tarihin tarbiyyar gidansa da sunan da yake taƙama da shi, a dinga masa kallo a matsayin wanda ya gaza"" Ya yi shiru yana sauke numfashi yana duba" wayarsa ganin shugaban jam'iyya na kiran shi ya miƙe tsaye. """Bayan sato budurwar ƴarsa da kuka yi har gida, ina son ka yi Safiyyerh Abdu Marafa fyaɗe, ina son ka yi" "wa Safiyyerh Abdu Marafa ciki kaga tana da auren wani, wani kuma daban ya yi mata ciki wanin ma ɗan daba, ɗan daban da basu san waye shi ba, kaga Safiyyerh zata haifi ɗan zina ko""" """Ɗan zina?""" "Moh ya maimaita a fili Ali wali ya ce ""To ɗan mene? Yayinda da wani wanda ba mijin yarinyar ba ya keɓe" "da yarinya har ta samu ciki wannan cikin ya sunan shi? Cikin shege ba haka lissafin yake, idan na ce wani" "zan bawa wani aikin lissafin Eng Ali wali bai gama cika ɗari over ɗari ba, dole kai zaka aikata haka Mutallab dole kai zaka yi wa Safiyyerh ciki domin dauɗar gora ciki kan shata""" """Wanne zunubi ita yarinyar ta aikata, gyatuminta ne kamar batun nan ba zan ba, shi kuma daman cikin" "yinsa ake yi? Ba kawai girma yake ba?"" ""Au baka san yin ciki ake ba? Shekarar nawa?""" """Koma mene ba za a yi ba"" Ali wali ya yi murmushi ya ce ""Dole zaka yi, ka rubuta kuma ka ajjiye sanda za" "ka yi baka sani ba jeka"" bai wani ɗauki maganar Eng Ali wali da muhimmanci ba ya fice daga gidan." "***Safiyyerh ta rufo ƙofar bayan ta gama dubawa ta kalli Goje ta ce ""Kawai ku siyo mini kayan abincin na" "dinga dafawa sai ina san muku?""" """Kin iya wato ne?""" """Mene wato?"" Ya ce ""Shi girkin nake batu"" ta jinjina masa kai ya miƙe tsaye ya ce ""Da kin yi dabara" daman ba ki da wani amfani. Ita mamaki ta yi ganin kitchen hadda tukunya plates da spoons ga risho da sauran tarkace. Babu jimawa Goje ya dawo hannunsa riƙe da Indomie guda biyar da ƙwai guda goma hadda kayan miya da magi ya bata ya ce """Ta yi musulmin daɗi kin ji Manager""" Ta samu kanta da yin murmushi a ranta kuwa dabara take yi ta samu hanyar guduwa. Suna tsaye ya faɗo "cikin gidan sai ya yi turus yana kallon Goje yaƙi yadda ya kalle ta, ta ƙasan idanu ita kuma take binsa da" "idanu mamakin yadda jikinsa yake a murɗe take har ƙasan zuciyarta ta ji tana shakkarsa. ""Barka da antayowa mai jeji ya ƙarin haƙuri"" banza ya yi masa ya shige ciki Safiyyerh ta ce" """Au rashi ma aka yi masa?""" """Yayarsa aka sace sai jiya aka kanta an ƙwaƙwale mata idanu"" Safiyyerh ta zare idanu tana dafe ƙirji sai" "tausayinsa ya kamata a raunace ta ce ""Kuma bai je gida ba? Anya yana son yayar tasa kuma kun tabbatar wannan ba mahaukaci bane?"" Shi dai tuni Goje ya bar wajan. Ta gama dafa Indomie wacce ta ji azabar Attahiru rabon da ta shiga kitchen a rayuwa ta manta fuskarta ta yi jajir da wani irin roɗi-roɗi idanun" sukai micin-micin ta dinga mata ƙaiƙayi fuskar saboda zafin wuta ta nemi kaɗan ta juye musu a faranti. Moh yana kallon yadda ruga lauma kamar mayunwata sai jan yaji suke yi ya kalli Indomien ya kalle su "can ya miƙe ta ce ""Kai baza ka ci ba? Ni ina son yin sallah fa"" duk suka share ta, suna gama ci suka fice tare da rufo ƙofar ya rage sai ita kaɗai ta haɗe kai da qwwia ta dinga kuka kamar ranta zai fita har bacci ya ɗauke ta a wajan." Cikin bacci ta ji an cillo mata abu ta miƙe da buɗe idanu tsaye ta ganshi ya juya baya leda ce ya cillo ta buɗe taga duguwar riga guda biyu da hijabi da takalmi ta yi ta mamakin yadda ya san size ɗinta ta miƙe tsaye yana jin zata zo wajansa ya nufi hanyar fita ta sha gabansa ya yi turus ta dinga kallonsa shima yana kallonta """Wai kai baka yin magana ne, ko ƴar dariya babu kafin na tafi mu ƙulla mu zama abokai"" ta miƙo masa" "hannu ya kalli hannunta mai ɗauke da siririn zobe sai yatsunta zara zara da su ""Am Safiyyerh Abdu Marafa You?"" Ya sake yin shiru ta langwaɓar da kanta gefe guda ta ce ""Ina son zama ƙawarka fa, zan maka labarin daddyna da yadda yake so na, da labarin kamfanin da nake aiki hadda labarin Ashraf wanda zan aura ya mutu aka aura mini captain labarin Ummimi da Kinal ƙawata i will tell you everything," "abota Frist?"" Ta sake miƙa masa hannun a karo na uku. Gefenta ya bi ya shige yana rufe ƙofar gidan ya" bar ta tsaye da hannu a ƙaƙe takaici ya ishe ta shi wannan yana ɗan ta'adda yana jin kansa kamar ɗan gidan ƙaruna saboda faɗin rai ga miskilancin masifa the manager ita Safiyyerh take magana ake sharewa bai san cewa akan dole take yin maganar ba? Ta lumshe idanunta hawaye na cika cikinsu da ƙyar ta yi alwala ta fara jero salloli. Goje ne ya shigo da sauri ya ce """Ke kina ina fito maza taso"" ta miƙe za ta yi masa gaddama kawar Moh ya shigo ya damƙi hannunta ta" kalli baƙin hannunsa da ɗan mitsitsin nata farin hannun ya jata sukai waje mota ta gani bai tsaya jiran komai ba ya dannata a gaba Goje ya shiga baya Mangal dake tsaye ya ce """Waye zai ja motar yanzu? Ni ban iya ba kuma haka?""" Moh dake shirin shiga mazaunin driver ko me ya tuna ya kalli Safiyyerh a karo na farko ta ji muryarsa a "sake ya ce ""Dawo nan"" tsoran shi take ji ta fito ta koma wajan driver ya dawo ita ta tashi, ya cilla mata" "key ɗin motar ""Muje"" bisimillah ta yi ta fara driving ta juya ta kalle shi ta ce ""Ina?"" Ya bata wayar hannunsa wacce yanzu ya shigo da ita ta duba location da ya fara driving cikin sauri har suka bar wajan." Mintuna kaɗan da barin su motoci suka tsaya a ƙofar gidan Captain ya fito jikinsa danye da uniform na "sojoji da suka amshe shi sosai ga ƙatuwar bindiga sauran yaransa suka fito a hankali ya dinga bin wajan da kallo har ya shiga cikin gidan abin da ya fara cin karo da shi ya sanya zuciyarsa bugawa ganin rigar baccin Fiyya yashe a ƙasa ya ɗuka ya ɗauki rigar idanunsa ya sauka akan wani busasshen jini ya dinga kallon gidan a nan ya kalli ƙwayoyi kala-kala da wuƙaƙe da gorori ya lumshe idanunsa ""Where are you" "Wife? Ina suka kai mini mata?""" """Captain kuma ka tabbatar tracking ɗin nan ya nuna?"" Ya jinjina kai don baya jin zai iya magana. ""Sun" "gudu, amma ya akai sukai san an yi tracking location nasu har suka gudu da wuri haka?""" "Captain ya girgiza kai irin bai sani ba ""Ka kwantar da hankalinka matarka zata kuɓuta ko kana tunanin" "sun yi mata wani abu ne?"" Captain ya nuna masa rigar baccin Safiyyerh da jinin dake wajan mutumin ya dafe kai ya ce" """Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, in sha Allah ba abin da muke zato bane muje"" fita sukai Captain ya ji a" ransa ba zai bar abin haka nan ba. Mutallab wani gida ya kai su madaidaici mai kyau da tsari da yake can bayan gari duk suna zaune "Safiyyerh kanta na ƙasa tana mamakin yawan shiriun bawan Allan nan, idan ya yi shiru shi kaɗai sai ya" saki ajjiyar zuciya ko ya ƙurawa waje guda ido. ***Wajan sati guda babu labari akan batun sace Safiyyerh ba kiran waya babu komai Daddy ya hana a faɗi maganar ko a social media ko a gidan rediyo ya ce a bar ta tsakaninsu. Yana ƙwace hannunsa maƙale "da ruwa muryarsa a hankali ya ce ""Aliyu waye ya saka?""" """She is my wife daddy""" """And? Ɗan sanda ne kai ko soja?""" """Zan iya amfani da uniform ɗina ko babu haka ai she is my responsibilities yanzu na kula da haƙƙina zan" "ji na zama lusari idan ban nemo Safii ba, kar ka dakatar dani daddy police su yi nasu aikin ni na yi nawa""" """Ka cire hannunka a ciki Aliyu""" """Ok zan jire akan wanne dalili?""" """Aliyu yanzu baka tunanin dalilin hakan su yi mata wani abu ne? Baka san su waye mutanen nan ba, duk" "abin da zaka ji a bayan nawa dana Zahiyerh yake kar ka yi kuskuren da za su salwantar da rayuwar Maama na roƙe ka, mutanen ba mutunci ne da su ba kamar komai hannun Sp Ghali"" Aliyu ya miƙe ya nufi ƙofa ""I am sorry daddy idan kaga na tsaya to na mutu ne, idan da numfashi a ƙirjina ba zan gusa ba" "sai na dawo da Safiyyerh cikin rayuwata i am sorry"" yana cewa haka ya bar ɗakin." "Daddy ya rufe idanunsa daya cika da ƙwalla ya wani irin ramewa ko abinci baya ci Ummi ta ce ""Ka san" "halin Aliyu da baka fito masa ta haka ba, gwara ka saka Ummimi yi masa magana"" daddy yaƙi cewa komai. Wayarsa ta fara ƙara number ya gani sai ya yi sauri ya ɗaga yana kaiwa kunne aka ce." """Barka, ina magana da Professor Abdu Marafa na sani ko baka amsa, zan fara da yi maka ya jiki don ina" "da yaƙinin kana nan zuciyarka na ciwo bari na ɗora maka da wata maganar ban sani ba ko zaka iya jure jin abin da zan faɗa. Yarinyar da kake ji da ita ni na saka a sato mini ita Safiyyerh kenan ina son ka lashe aman da ka yi da kanka. Professor ni ɗan siyasa ne lissafin ɗan siyasa daban yake dana Malami, bana barin kota kwana daman mun saba saka jama'a a uku, wallahi ka shiga komata yanzu nine da wasan ka" "fara lissafa ranakun mutuwar yarinyarka daga yanzu"" da sauri Daddy ya ce" """Waye kai?""" """Sarai ka ɗauki ne muryarta professor, kana magana da Eng Ali wali mai neman takarar ɗan majalisa, ka" "hanani bacci yanzu lokaci ne da zaka ji abin da nake ji"". ""Ali wali me kake buƙata me Safiyyerh ta yi maka" "karka cutar mini da yarinyar don girman Allah kar ka taɓa ta""" """E, ba zan taɓa ta ba muddin ka yi abin da nake so""" """Me kake so?""" """Ka dawo jam'iyyata kuma tsagina ka lashe aman da ka yi ka kuma gyara ɓarnar da ka mini na rusa mini" "dukkan shirina, yadda ka ɓata sunana a wajan matasa da al'umma a gidan rediyo da kai da ɗan jaridar da" "yake mara maka baya ku sake sabon lale wajan wanke ni inma kana buƙatar kuɗi zan bayar hakan ba laifi bane ba""" """Uhm Ali wali kenan tun yanzu har ya yi sauri haka? Ni kake cewa idan ina buƙatar kuɗi kaga na yi maka" "kala da mabuƙaci? Kamar dai ka manta waye Professor kana buƙatar tuni na, laaa la la dama sauran lokaci ai. And da kake batun Safiyyerh tunaninka ita ce raunina ko?"" Daddy ya tsige ruwan hannunsa da ake ƙara masa ya sakko daga saman gadonsa daman tuni ya nunawa Ummi ƙofar fita tun kafin ma ya" ɗaga kiran. """Ka yi kuskure sosai, Safiyyerh is nothing to me kuma she never be my headache idan ka so ka saka wuƙa" "ka yankata a yanzu is doesn't matter for me, idan akan Safiyyerh ka kira ka mini warning ka makara Ali wali tunda Safiyyerh ta bar gidan nan ko da dai da rana ban taɓa tunaninta ba siyasa ce kai kuma yaro ne" "mu zuba mu gani""" "A ɓangaren Ali wali dariya shima ya yi ya ce ""Lallai prof ka cika ɗan siyasa, to wallahi ka shirya ganin" "gawar Safiyyerh a wannan daren ku tara ƴan jana'izarta"". ""Idan ka haifo kuma kai cikakken ɗan iska ne idan har ba zina akai ka haifeka ba na roƙeƙa Ali wali don Allah ka kashe Safiyyerh nima fa wani aikin ka rage mini..,"" ƙit Ali wali ya kashe wayar daddy ya saki dariya yana wani irin murmushi wata number ya kira ana ɗagawa ya shige toilet yana saka key, ya jima ciki kafin ya fito ya zauna saman gado Dr Hash ya shigo da Yaya J ganin daddy zaune ya saka dr cewa ""Daddy ya jikin naka?"" Hawaye ya cika idanun daddy ya ce ""ba abin da zai tafi daidai babu Safiyyerh zuciyata zafi take my innocent Fiyya, Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un ina tsoran halin da Ummimi zata shiga"" ganin hawaye a idon mahaifin nasu ya saka Junaid" ficewa dr ya zauna ya dinga lallaɓa daddy da bashi bakin za a ga Safiyyerh in sha Allah. Aliyu yana zaune a ɗakinsa aka buɗe ƙofa tare da shigowa ya ɗaga kai ya kalleta ya miƙe da sauri duk da "babu fara'a a fuskarsa amma sai da ya saki ajjiyar zuciya. Ta juya idanunta ""Nan ka ɓoye?"" Ya girgiza mata kai" """Ka cigaba da binciken inda Safiyyerh take Aliyu kar ka saurari mahaifinka ka ji ko?"" ""in sha Allah" "Ummimi"" ta zuba masa ido sai ta juya ya ce ""Tafiya za ki yi?""" """Me zan maka?""" """Love, ganin ki nake son yi"" ta haɗe rai tana cewa ""To ɗakko zani na goyaka"" ya buɗe idanunsa ya yi" "wajanta yana rungume ta ya saki ajjiyar zuciya ""I love you Ummimi, and I love Safii too""" "Kan shi ta shafa ta ce ""Kawai ka zaɓa ni ko ita"" ya lumshe idanunsa ya yi mata shiru, rungume shi ta yi a" "jikinta ta yi shiru tunani daban daban a ranta sai kuma ta sake shi ta ce ""Fito waje"" saƙo Aliyu ya samu cikin gaggawa sunansa ya fito a jerin sojojin da za a yi posting nasu wajan aiki ya dinga kallon saƙon yaushe ma ya dawo da za a sake tura shi wani wajan bayan babu shi a sojojin da aka yi list? Sai kawai ya fita da nufin zuwa kiran da ya samu domin bata uzurin yana da wani muhimmin aiki akan nasa iyalin ya" manta da batun a tsarin aikin sojoji babu sauyi idan har a zaɓe ka. ****Mafarki ta yi mai ban tsoro ta farka a gigice tana kiran sunan TAHHB sai haki take yi fitila taga an "kunna an hasko ta ya zuba mata idanu a ransa yana ƙara mamakin wannan hasken nata gefensa zabtareriyar addace saboda tsaro ya miƙe a hankali ya kunna hasken parlon sai a lokacin Fiyya ta lura da Goje dake cikin kwance cikin jini haka Mangal ga wuƙaƙe a gefen su sai numfarfashi suke yi. Ya taka ya je gabanta ya tsaya can ya duƙa dab da ita baki ta buɗe za ta yi ihu ya saka yatsarsa a bakinsa ""Shhhh"" ta yi" tsit ya cake addar """Mene?""" """Ban kira ka ba wallahi"" ya zuba mata idanunsa masu kaifi ta janye nata ""sunan wa kika kira to?""" """Tahhb""" """Sunanki ne? Ko na Abdu Marafa?"" Ta girgiza kai ""Mafarki na yi a mafarkin na ji sunan, amma ban sani" "ba ni na manta komai na mafarkin ma kai na ciwo yake i have a headache""" "Ya ɗaga addar ya cake ta tsakanin ƙafafuwanta sai sheƙi take yi ya ce ""Ko dai ki faɗa mini waye Tahhb ɗin" "da kika dame ni da kiran sunansa yanzu ki na ɓula miki cinya""" """Don Allah ka yi haƙuri wallahi ban san shi ba""" """Ke wace?"" Moh ya tambaya ""Safiyyerh sunana"" ya cije bakinsa sosai ya ce ""Matar soja ko?"" Ta jinjina" masa kai """To ni waye? Kuma ya nake a wajanki?""" """Wallahi ban san ka ba, kai ba kuwa bane a wajane"" idanunsa har ruwa yake ya daka mata tsawa a gigice" "ya ce ""Waye ni? Waye ni waye tell me...." "❤🔥🔥💃1 page remain ba zan taɓa buɗe komai ba shafi 15 is nothing nothing ku biya you'll never regret sai mun yi nutsu za ku fahimci labarin MUTALLAB bai haɗa hanya da kowanne kalar labari ba, idan za ka yi kuka ka fara tun yanzu ba kuma zan taɓa sauya labarina a yadda nake ba, you better shut" up... MUTALLAB. "Book 1, 2 &3" 500 Naira 0116886423 Union Bank Na'ima Sulaiman S a tura shaidar biya ta nan 08164069385 'Yan Nijar ku turo carte airtel ta 300fcfa saman wannan layin 84506476 "[10/27, 4:07 PM] Nanameera: *The story of a thug husband MUTALLAB, as a good parents za ku bada" "auren yarinyarki ga ɗan daba ɗan ta'adda? Ban ce ku fara kuka tun yanzu ba,ban ce ku ji soyayyar ciki" kamar a ƙirjinku ake wanzar da ita ba.* *The story of TIGER and MOH The destiny of CAPTAIN and FIYYA. Finally the eternal love* *between..The love that separate them and back them together❤🔥😭* *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥* Page 15 last free episode *Bright pens.. 2nd batch* For more updates follow Mutallab on Arewabooks in sha Allah ❤🔥 "Page 15 shine last free pages na labarin, kar ka yi tunanin ganin wani page ɗin a waje ka yi payment a yi" "naka into paid group akan 500 kacal, love ɗin da kuke showing yanzu ne zai yi aiki฀MUTALLAB." "Book 1, 2 &3" 500 Naira 0116886423 Union Bank Na'ima Sulaiman S a tura shaidar biya ta nan 08164069385 'Yan Nijar tsarin biyan zai kasance ta *Stock na airtel*. Ku yi wa wannan layin 84506476 magana sai ta ba ku lambar da za ku turo mata stock ɗin. Kafin ɗorawa da inda muka tsaya zamu ɗauki hutun zango na sati ɗaya tal maybe har a yi albashi ko masu mining ta fashe musu. Godiya ga Hajja Aisha Abubakar Khadhfsum data biyawa mutane 8 ga masu business zaku iya badawa a tallata muku idan kun ɗauki nauyin page in sha Allah. Ba zan manta da BESTIE ba I so much love her wish you all the best Aunty Nazeefah Sabo Nashe ta ce HADARIN GABAS yana hanya. Ina son ta sosai Gaisuwa ga haƙarƙarina uwar gidan Viper tunda mun amince Nabila ce amarya Ayushercool masoyiya. My beb Zee kumurya sai tallafe ƙirji muke muna sata a addu'a gashi zata fara yi mana ZAYTOON a watan Nuwamba i love them sosai "Conversation bana ce kuci kanku ba, saboda ina ƙaunarku Sarautar's library Mutallab fans, Nimcy paid" group my ArewaBooks people. Mikiya writers Association Mikiya fans AUTAR MANYA❤🔥 Ubangiji Ya bar ƙauna. Page 15 Last free pages "*What if I tell you, I love you?*" """kar ki ce ba ki sanni ba, kar ki ce haka dole ma tarihin rayuwarki ba zai taɓa cika ba sai da sunana, dole a" "same ni a cikin rayuwarki sai dai idan za ki cire wani sashi na cikin tarihin"" ya furta yana huci da gwame numfashi Safiyyerh was shocked and speechless at the same time ta kasa kallon shi wani irin tsoro shi" take ji mai girma ya ratsa zuciyarta. A hankali ta ɗago kanta zuwa gare shi hawaye na taruwa cikinsu yana sauka akan fuskarta "Ta ƙura masa ido da sauri kuma ta girgiza kai ta ce ""Wallahi da gaske ban san ka ba, ban taɓa ganin ka ba" "sai kwanakin nan, i don't even know your name balle kai,me ya sa zan sanka to?"" za ta sakar masa kuka ya ɗora yatsarsa a baki ya ce" """Shhhh"" ba shiri ta yi shiru tana sauke ajjiyar zuciya shi dai har lokacin fuskarta yake kallo yana murza" "tsinin wuƙar a ƙasa. ""To kai ka sanni ne? Ni ka cire mini wuƙar nan ka ji ɗan baƙi"" ta furta tana juya idanu" ta langwaɓar da kanta gefe guda. """Ki daina kiran sunana daga yau""" """Sai na dinga ce maka me to? Ka faɗa mini ban ma san sunan ba ai"" ƙoƙarin biye mata yake wajan ganin" ya samu abin da yake buƙata amma a duk kalma ɗaya daya furta ko kafin ya furta sai ya fama hautsina kan shi kafin ya san me zai furta mata. Wuƙar ya ɗauke ya cilar gefe guda ya juya ya kalli Goje jira ya ke yi safiya ta yi ya fara tunanin yadda zai samu likita ya ji ta ce """Kai ne ka yanke su ko? Ba kyau wallahi ka mutu a haka wuta zaka tafi babu fashi kana kallo za mu shige" "aljanna muna jiyo ihunka a cikin lazza ko saƙara tunda baka da wani aiki a rayuwarka sai daba da bushe- bushe cikinka ba komai sai ƙwaya da hayaƙi, gabaɗaya gudanawa kake daka zaɓi wannan rayuwar ne ɗan baƙi? Bayan rayuwa akwai mutuwa fa karka bari ka mutu cikin wannan halin ba zaka ji da kyau" "wajan Mala'iku ba""" """Kina da ɗan'uwa mala'ika ne?""" """Subuhanallahi, kai ko wa'azin baka so kamar jinin fir'auna ni tausayinka kawai nake ji tunda baka gani" "shikenan"" ta haɗe fuska irin ta ji haushin nan har ƙasan zuciyarta ita ƙyamar shi take yi rayuwarsa a gurɓace take babu wani abu na birgewa ko ban sha'awa a ciki deep down kuma tausayin rayuwar tasu take ji tana jin da tana da iko tabbas ba zata taɓa gazawa ba wajan ganin ta taimaka musu. Ya rufe idanunsa yana daga zaunen saman kujera ya ɗauki ƙafa ɗaya ya ɗora akan ɗaya ya fara yin fito wanda ya" cika ɗakin a hankali kuma ya zaro sigari zai kunna ta yi saurin cewa. """Matsalar daƙiƙi kenan a rayuwa, shi da kansa bature ya ce tana lalata lafiya dake babu arabi ba boko" "ba'a gane komai ai shikenan, goodness Safiyyerh what exactly wrong with you, that's not your business"" ta faɗa lokaci guda kuma tana miƙewa tsaye sai dai bata kai ga zuwa inda ta yi niyya ba ta gan shi tsaye a gabanta hannunsa riƙe da sigarin yana zuƙa da fesarwa, ta saka zata rufe hancinta ya sa hannu ya tukare jikin bango ya sata a tsakiya sigarin a bakinsa yana binta da jajayen idanu bakinta na rawa ta girgiza kai" "ta ce ""Mene haka wai?"" Ya yi shiru yana duƙawa fuskarsa dab da nata har lokacin ita ɗin da yake kallo" """Iskanci ne wannan matar aure ce ni fa, saboda ƙwaƙwalwarka bata faɗa maka daidai ko? Idan ka sato ni" "a gidan mijina shine yake nufin me? Zan barka ka yi yadda ka so ko ƙazamin jikinka ya taɓa fatar Safiyyerh ba zan taɓa yafewa kai na ba, da babbar murya ina faɗa maka ni Safiyyerh matar aure ce ka ji ko? Kana jin Hausa ai?""" "Ya zare sigari hayaƙin daya zuƙa ta cikin bakinsa ya dinga fesa mata a fuska ta fara tari tana ɗauke kai, ya" "ƙara zuƙar sigarin a baki ya matsa dab da fuskar tata ya sake fesa mata lokacin ta buɗe baki za ta yi magana gabaɗaya ta haɗiye hayaƙin, a gigice ta fara tari tare da kakarin amai ganin da gaske aman za ta yi,ya matsa a wajan tare da shigewa wani ɗakin. Safiyyerh ta durƙusa tana riƙe ciki saboda wani irin ciwo da yake yi mata ga amai dake ƙara hautsina mata kayan ciki ta rasa yadda za ta yi ta kwanta tana riƙe cikin da dinga rusa kuka. Duk abin da ya fara Goje na jinsu kawai yana cikin wani hali ne tsautsayi ya saka su fita a daren sukai karo da ƴan daban cikin gari sun shigo ɗaukar fansar wani faɗa da aka yi can kwanaki shine suka rufar musu, a cikin ƴan daban cikin garin wanda yake jagorantar su me suna Bakin wuta shine ya sare su shi kuma Moh sai da ya sari wajan mutum goma a yaran Bakin wuta wanda kuma shine faɗan su na farko a rayuwa ba wanda ya san wani, a cikin yaran ba sai da aka buɗewa wani ciki" kuma duka aikin Moh ne yana da tabbacin kuma Bakin wuta ba zai bari haka nan a ci bulus akan shi ba. Goje ya juya kaɗan ya kalli Safiyyerh dake kuka sosai kamar ranta zai fita itama yarinyar naci gare ta ga "bakin tsiwa da Moh na taɓa mace da tuni Safiyyerh bata duniya ya san ba zai iya kashe ta ba amma zuwa gaba zata gane bata da wayo idan ta cigaba da kai shi bango. Tana kukan a haka bacci ya ɗauke ta bata ji kiran sallah ba amma tunda ta motsa bakinta ɗauke da addu'a ta san asuba ta yi ta miƙe da ƙyar ta nufi banɗaki ta yi alwala ta jima tana azkar kafin ta yi raka'atul fijr kana ta yi sallar asuba. A hankali ta dinga leƙa shi abin da ya bata mamaki bai shige ganinsa durƙushe a kan qwiwinsa ba yana kallon gabas ba kuma sallah ya yi ba, kan shi a ƙasa ya yi shiru kamar zata shiga sai kuma ta fasa ta tsaya cak ta samu" kanta da yi masa addu'a samun sauƙi da mafita a rayuwarsa da shiriya idan yana da rabo. """Allah Ya shiryarka idan kana da rabo""" "Ya ɗago kan shi ya juya kaɗan suka haɗa ido, ba ƙaramin gigita ta yi da ganin idanunsa a haka ba, ya ƙura" "mata ido a ransa girman nacinta yake ƙara jinjinawa duk da bai yi mamaki bai kuma zama sabon abu ba," "bai fiya son takura ba wani lokacin. Safiyyerh ta harɗe hannayenta a ƙirji ta ce ""Ko yunwa kake ji na daba" "maka abinci? Ko shayi?""" """To na zo na yi maka shira? Ko waƙa?""" """Get out...""" "Ya ce a hankali muryarsa ƙasa ta buɗe ido jin ya yi turanci ta ce ""Wow ashe a ɗan san wani abu, nifa ba" "zan fita ba bakina ciwo yake na rashin magana gaskiya"" kafin ya yi magana ta shiga cikin ɗakin ya yi saurin tashi da ƙyar ya nufi kujera ya kwanta ƙafarsa ɗaya a armchair ɗaya a can saman kujera hannayensa ya harɗe a ƙirji idanunsa rufe. Safiyyerh ta zauna a ƙasa ita kanta bata san me ya sa take son yin magana da shi ba, ta ji kuma tana barin wajansu zata haɗa Kinal da shi ita take son auren ɗan daba a hankali muryarta a nutse ta ce ""Sunana Safiyyerh Abdu Marafa, ni ce auta a gidanmu..."" Ta ɗan yi shiru bata ga alamar yana ma jinta ba kamar bacci yake yi haka yanayinsa ya nuna bata karaya ba ta sake" matsawa ta ɗora da faɗin. """Mahaifina professor ne ya koyar a jami'o'i da yawa a wannan ƙasar cikakken lakcara ne matasa na son" "shi sosai saboda yana taimaka musu da shawarwari. Ina da yayyi huɗu babban yayenmu sunansa Aliyu muna ce masa Captain shi soja ne, bashi da kirki gabaɗaya baya dariya kamar kai ɗin nan amma shi ba baƙi bane fari tas, yana da ilimi he is educated, sai mai bi masa Dr Hash likita shi a ɓangaren kwakwalwa Neurologist, shi rayuwarsa ba sawa ba hanawa sai my favourite Yaya J sunansa Junaid shi aiki biyu yake yi aikin banki da business, ina son shi sosai kamar yadda yake so na, rayuwarsa abar sha'awa ce wallahi. The last one Awais Shi kuma ɓangaren siyasa yake so amma daddy baya so yanzu dai ya ce yana son zama shahararren ɗan kasuwa ne, sai kuma ni Safiyyerh nima na yi karatu ina aiki yanzu matsayin Manager a FS WORLD INVESTMENT COMPANY, ina da saurayina da nake so kuma yake so na Ashraf sunansa ɗan mai kamfanin da nake aiki ne, akwai wasu abubuwa da bana ganewa a kamfanin..."" Shiru ta" yi da sauri kuma ta kalle shi taga har yanzu idanunsa rufe yake bai motsa ba """Kodayake shikenan, saura kwana ɗaya auren mu da Ashraf ya rasu, Ashraf died ya mutu ya bar ni cikin" "tsoro da fargaba, a ranar daya rasu a ranar ne aka aura mini yayana Aliyu, da dai bana jituwa da shi sam" "amma ƙaddara ta haɗa kuma Ubangiji kaɗai ya san dalilin hakan, wannan shine labarin Safiyyerh Abdu" "Marafa""" "Ta leƙa fuskarsa taga idonsa still a rufe ta tura bakinta gaba ""Nima sai ka bani labarinka ai muna zaune" "waje guda bai kamata bamu san juna ba"" miƙewa taga ya yi ya nufi ƙofa kafin ta bi bayansa har ya fice" daga cikin gidan. "****Eng Ali wali ya dinga kallon Moh da yake tsaye kafin ya ce ""Ina wayar daka amsa wajena? Mene" "amfaninta ina kira baka ɗauka wai?""" """Ba gani gabanka ba?"" Moh ya ce yana kame fuskarsa kamar kodayaushe." """Yarinyar nan tana wajanka ko Mutallab?"" Moh ya yi tsaki a fili da ƙarfi kuma ya ce ""Ni a tarihina sau" "ɗaya ake faɗa mini magana na haddace ka yi batu kawai"" ya ƙarasa maganar yana jawo flask ɗin shayi ya tsiyayi ruwan zafi ya saka madara da su milo ya nemi waje ya zauna ya janyo biredi da plate ɗin ƙwai ya" fara ci duk zafinsa da taurin kan shi a nutse yake cin abinci sai dai baya laumar wasa """Daman kai aka kawowa abincin karin Mutallab? Ai shikenan magana nake so mu yi very important akan" "yarinyar nan daka ɗakko"" ya yi shiru can ya ce ""magana nake maka fa ka yi shiru""" """Kunne ke ji""" """Professor ya raina mini hankali wai ko kashe yarinyar nan zan yi ko a jikinsa yana nufin bai damu da ita" "bane ko mene? To wallahi ni Ali wali zan bashi mamaki, yarinyar nan kafin ya ganta sai ikon Allah don haka ka yi yadda na ce a kanta, ka yi mata fyaɗe ka yi yadda ka so da ita har ta samu ciki yadda zamu watsa labaran yarinyar professor Abdu Marafa ta yi cikin shege ya kore ta daga gida ni kuma na ɗauke ta na kula da ita har zuwa haihuwa,kaga daga nan hankalin jama'a zai yi kan Professor Abdu a bar batuna ni kuma na yi amfani da wannan opportunity wajan cin nasara a zaɓen da yake gabatuwa, don this time ba zan taɓa barin Hon Maɗatai ya yi nasara a zaɓe ba zan yi duk abin da zai tabbatar dani ne na ci zaɓe ko a can hukumar zaɓan inec na shirya tsaf ba gudu ba jada baya siyasa sai ɗan siyasa, harkar siyasa da zama wani a harkar ƙasar nan sai ka nuna ba wani shege ka cire tausayi da imani, ba ri ka ji Mutallab duk wani" "ɗan siyasa kan shi kawai ya sani"" ya numfasa yana ɗaukar ruwa ya sha." "Moh dai har lokacin shayin yake sha hankali kwance abin shi. Ali wali ya duƙa ya ce ""Dole ka yi wa" "Safiyyerh fyaɗe dole ne ka yi wa yarinyar nan ciki, samun cikinta shine plan ɗina na farko da zai kai ni matakin hawa kujerar ɗan majalisa""" """To ya ake cikin?""" """Baka san yadda ake yin ciki ba, ciki na haihu fa?""" """E, ban sani ba""" """Mutallab, da ake cewa ka yi aure a ranar an kashe maka matarka da me za ka yi da auren da ka yi""" """Bayan a yi wa mutum girki ya ci ya yi bacci akwai wani abu ne? To ni ban iya yin ciki ba, sara da soka" "kawai na sani a rayuwa da shiga jeji, ka bar batun hakan bani ba ko waye ba za a yi mata wani abu ba""" """Moh""" """Ali wali"" Mutallab ya ce yana yin kyatsa yana miƙewa tsaye kuma. ""Mutallab yadda aka fara aikin nan" "da kai, to da kai za a ɗora kuma a ƙarashe dole zaka yi wa Safiyyerh fyaɗe i am telling you this, za ka ce na faɗa maka""" """To ka fara bani matarka na yi mata ai kana da ita, sai kace Professor ɗinne ya yi mata"" Ali wali ya dinga" "kallon Moh ganin how serious he is da maganar kuma da gaske yake. ""Ni zan shige zan na ji kira idan ka" "shirya bani matar taka tunda yarinyarka Noor bata ƙasar""" """Ina kasan ina da yarinyar Noor?""" """Ali wali kenan""" Hanyar fita ya yi kamar wancan karan ya ƙara jin sauti mai kama da ihu ya dinga kallon ƙofar kafin Ali wali ya ƙarasu har Moh ya buɗe ƙofar ya shiga cak ya tsaya ganin wata mahaukaciya zaune sai ihu take "ita kaɗai gashinta ya rufe mata fuska ya juya ya kalli Ali wali ya ƙara kallon matar bai yi magana ba ya saki ƙofar zai fita Ali wali ya ce ""Ka manta kaga wannan, sirrina ne""" Ko magana Mutallab bai yi ba ya kwashi kuɗi ya yi waje abinsa yana rufe fuskarsa. Bayan ya fita Ali wali "ya ɗauki waya ya yi kira ana ɗauka ya ce ""an samu matsala P.A yau wani yaga ajjiyata, fitar maganar nan daidai yake da zuwana gidan yari"" ta cikin wayar P.A ya ce" """Kafin ka je gidan yarin ka fara tura wanda yaga ajjiyar taka can""" """Mutallab ne""" """Tab, matsala kenan ina ruwan ciwon idanu wannan yana matsala kuna samun akasi za kaga ba daidai" "ba"" Ali wali ya yi murmushi ya ce ""Ina da tsari P.A idan na tabbatar na ci wannan kujerar zan yi tuggun da za a yi wa Mai dawa ɗaurin rai da rai a gidan yari, ka zo mu yi magana wai kasan har batun ƴa ta Noor ya" "sani, uhm sai ka zo dai""" Yana gama wayar ya duba interview ɗin da za a yi da dukkan wani ɗan takarar ɗan majalisa daka mabanbanta jam'iyyu wanda BBC ke shiryawa hakan yana nufin za su haɗu waje guda da Hon Maɗatai da Dr Abraham Denial David yana da buƙatar ya zauna ya rubuta dukkan abin da zai faɗa a wajan. ***Yana zaune ya zubawa yaron idanu gabaɗaya ba zai shige shekaru biyu da watanni ba a duniya ya yi "wayo gwanin sha'awa duk wanda yaga yaron sai ya burge shi akwai shiga rai da ƙyar yake buɗe idanu saboda farin da yake da shi ya sauke ajjiyar zuciya yaushe zai rabu da damuwar ran shi sai yaushe zai ga Safiyyerh ya nuna mata abin da Ubangiji ya bata, daga samun cikin har haihuwar ba wanda ta sani. A fili ya ce ""Come back please Safiyyerh, where are you ina kika shiga haka me ya sa hakan? Jininki fa" "Safiyyerh haba my innocent Mahmah""" """Ka dinga yin addu'a komai zai daidaita ya zama tarihi Ubangiji yana gani kuma yana kallo ba zai bar" "addu'ar ta tashi a banza ba, zata dawo ta damu ɗan ta, zata dawo a faɗa mata gaskiya, mu ma muna da namu laifin""" """I missed Safiyyerh dear, ki bar ni na koka"" ya ƙarasa ya ɗauki babyn ya rungume a jikinsa hatta farinsa" "irin na uwarsa ne sak yaushe zai ga Safiyyerh ne? Wayarsa ya ɗauka ya yi kira ana ɗauka ya ce ""Har yanzu ba wani information akai ko?"" Ya yi shiru can ya ƙara cewa ""Ka san komai ba, ka san yadda na samu na tsira da raina bana sha'awar komawa kuma ni da aikin lauya har abada, komai namu a can muka baro bani da picture ɗin Safiyyerh ko guda wallahi zan yi ƙoƙarin neman ƙwararren mai zane na" "gani ko za a dace thank you""" "Kashe kiran ya yi ya ajjiye wayar yana sake rungume yaron da ko ɗomin jikin uwa bai sani ba, balle ya sha" nono kamar yadda kowacce uwa ke shayar da nata ɗan. "***Safiyyerh na zaune bayan ta gama musu girki Goje yana ci da sauri yana ƙona harshe ta ce ""Kaci a" "hankali mana akwai zafi"" ya yi murmushi ya ce ""Allah dai ya ba ki kada Manager""" """Amin""" "Suka yi shiru can ta ce ""Wai ba ka ce yayar wannan babban naku ce ta mutu ba? Me ya sa yake zaune a" "nan wai, ina yayenku suke"" Goje ya ce ""Babata ta mutu ni haka baba, shi kuma iyayensa suna nan cikin" "Birget Scorpion ai baya son zuwa gida ko unguwarsu baya son zuwa, tun bayan daya dawo daga gidan yari wajan state cid""" """Kai me ya yi haka to? Kwanansa nawa a wajansu""" """Shekara uku""" "Safiyyerh ta jinjina kai har ranta ta ji tana son cin labarinsa waye shi a hankali ta ce ""Ai daman naga baya" "ji shikenan da wuƙa a hannu ya sari wani wacce kalar rayuwa ce haka?""" "Goje ya ce ""Manager kenan, ai yanayi ne ke sanyawa a zama haka babu wanda ke son zama mutumin" "banza fa, ki gane hakan"". ""Son zuciya dai, Ubangiji daya halicci bayinsa an ce baya ɗora musu abin da ba za su iya ba, a tsaftace halicci kowa tun daga cikin uwa mahaifiya, a nan son zuciya ne da rashin" "wadataccen imani a zuciya da kuma yana da ilimi ai ba zai yi hakan ba"" Goje ya ce" """Ko? Kin san shi ne kin san waye shi? To ki maye masa gurbin abin da ya rasa sai kiga ya dawo daidai idan" "an yi sa'a""" """Me ya rasa shi ɗin?""" """Soyayya, ta uwa, ta mahaifi, ta mata""" """Ok nan wai a haka yana da mata?""" """Ta rasu"" Goje ya ce a taƙaice ta yi shiru ""Ki gwada cewa kina son kiga ki ce za ki aure shi"" da sauri" "Safiyyerh ta kalli Goje ta ce ""Kasan me kake cewa ne? Ina da aure fa ai zunubi ne haka""" """Zance kenan, ba ki da wani aure yarinya haka kalar masu auren take kenan?"" Safiyyerh ta yi shiru ita dai" "ko bata aure shi ba kawai za ta yi using opportunityn ɗin nan ya bata labarinsa, ko a lissafin ƙaddarorinta babu batun zama da ɗan daba balle soyayya har ace aure amma idan har zai bata labarinsa lallai za ta yi wani abu. Ta yi murmushi ta ce" """Kana da gaskiya ka gano ni, ai kaf ƙawayena ni ce bani da aure to bana son gori shine fa nake cewa ina" "da aure shi Captain ɗin ai yayana ne don ka ji, amma kana ganin zai so ni? He is such a arrogant, boring person yana da matsala""" """Ki gwada mana""" """Zan ƙoƙarta, ya sunan shi ok ka ce Scorpion ko?""" """Mutallab sunan shi, mantawa na yi""" """Wow a nice name, sunan shi ya fi shi kyau shine kuje ce masa mai jeji? Kai ya sunanka?"" Ya yi mata" shiru kawai sai ta miƙe ta shige ɗaki. "***A karo na biyu Aliyu ya kalli Commander ya ce ""Sir ka yi replacing nawa da wani mana""" """Aliyu me ya sa kake yin haka, na lura kamar aikin soja ya fara fita daga ranka ko? Ka je ka yi tunanin tun" "farko wahalar daka sha kafin zama abin da ka zama, ƙiriƙiri an ƙara maka muƙami amma ka nuna baka son ana kiranka da sunan muƙamin sai Captain? Why?""" """Sir to a ɗan bani sati guda ok?""" """Ba zai yiwu ba, ka je ka fara shiri cikin daren nan da kwana biyu za a poster ku"" rai ɓace Aliyu ya miƙe" "ya fita bai taɓa Jin takaici da kuma dana sanin zama soja ba a rayuwarsa sai wannan lokacin, shekarunsa nawa a duniya sai yaushe zai cigaba da jurewa yaushe zai ta yin haƙuri baya son shiga cikin ko barrack ne balle a nisanta shi da garin, ya samu sauƙi daga matsalar mata ga kuma wannan matsalar he need his" "wife, seriously he need his Safii yana buƙatar Safiyyerh a gefensa." "Daddy ya dinga kallon Aliyu kafin ya ce ""Aliyu mene plan ɗinka akan case ɗin nan wai? Sp Ghali yana" "neman information ka ja baki ka yi shiru na ce ka cire hannunka a wannan matsalar ko, ka san me hakan yake nufi?""" """Daddy Safiyyerh fa matata ce hakƙin kare ta yana wajena so allow me to do daddy ka rabu dani""" """Allow me to do daddy"" daddy ya maimaita ya juya ya kalli Ummimi dake zaune tana kallon Aliyu ya ce" """Kin gani ko Zahiyerh idan Aliyu ya saka na rasa Maama zai yi mamakina"" murmushi kawai ta yi ta ce ""Matarsa ce fa, ta ya ya zai yi wasa da ranta bayan yana buƙatar ta cikin tasa rayuwar, bana son wani magana mai tsayi da bayane babu mai yi wa Safiyyerh kutse a rayuwarta ka sani, su yi nasu binciken" "shima ya yi""" """Aliyu bar wajan nan""" "Fita ya yi rama rasa wanne kalar tunani zai yi, daddy ya lumshe idanunsa a fili ake ganin bugawar" "zuciyarsa bai shirya ba sam, baya jin kuma akwai abin da zai iya kawo masa cikas bai yi maganinsa ba." Daddy ya gargaɗi kowa akan kar a fitar da maganar sace Safiyyerh kwatsam zance ya fita a shafin daddyn "wanda shi kansa bai san yaya aka yi ba, wayarsa kullum na hannunsa balle ya ce wani ya ɗauka ya yi posting cikin yaran, ya tabbatar kuma ba hacking wayar aka yi ba, aka fara kiran wayarsa domin tabbatar" da gaskiyar al'amarin ya rasa ya ya zai yi kawai ya ɗauki wayar ya kashe. ***Mutallab na zaune yana sauraren Goje Safiyyerh ta fito ta saka hijabi har ƙasa bai kalle ta sai haɗe fuska da ya yi ta ce """Abokina Goje barka ya jiki naga an yi maka treatment, ku siyo ka yayyenki na dinga yi muku tunda dai" "dabar ya zama dole na iya ai"" murmushi ya yi" """Na ɗauka lissafin kuɗi kawai kike ai? Ashe likita ce""" "Ta yi murmushi ta ce ""Ina yini?"" Ta faɗa tana kallon Moh ya yi kicin-kicin da fuska bai amsa ba." """Wallahi kyau kake mini idan kana haɗa fuskar nan, na ji ina son ka kuma zan iya aurenka wallahi"" ya" juya ya kalleta da sauri ta kashe masa idanu ɗaya ta ce """What if I tell you, I love you?"" Ta sake cewa" """Idan fa ka amince zan so ka har numfashina na ƙarshe a duniya, kawai dai kar ka wulaƙanta ni""" """Ke bar nan""" "Ya furta a kausashe kamar ya ce ya shiga uku ""Na san saboda na ce maka ina da aure ne, wasa nake yi" "don kar ku yi mini wani abun ne na faɗa fa, trust me i love you kuma na ji zan iya aurenka a yadda kake, zan baka farinciki walwala da jin daɗi ka amince mini ka ji dear"" Moh ya dinga kallon ta wani irin kallo wanda bai ma san yana yi ba,sai dai ba'a tantance kallon na mene yanayin fuskarsa bai bada damar hakan ba, kaifin idanunsa ya saka Safiyyerh ƙasa da nata idanun, duk da shaye-shayen da ya ke yi da ɗaukar wuƙa matsayin abokiyar rayuwa da tarin raunukan da suke fuskar bai hana wani irin tsoro da shakkarsa ta gitta a zuciyar Safiyyerh Abdu Marafa ba, wani kwarjinin take hango wa na musamman a fuskar Mutallab Tahhb haibarsa da kwarjininsa mai ban tsoro ga namiji balle ɗiya mace sai yanzu take ji ta yi tsaurin idanu wajan tunkarar shi da wannan maganar mai kama da tatsuniya a gare shi, gare shi kallon kin raina mini wayo ya kewa Safiyyerh da tunanin ko ta samu matsala da nata tunanin tunanin ne? Idan ba matsala ta samu na gushewar tunani ba abu mamaki ne gare shi da jin furucinta ya yunƙura zai" tashi ta riga shi miƙewa kanta a ƙasa hawaye na zuba a idanunta. """Don darajar da Allah Ya yiwa Manzon Sallallahu alaihi Wasallama ka saurare ni, ba zan taɓa juya maka" "baya ko da nasani b a kasancewa ta da kai, kai musulmi ne nima musulma ce babu haramci idan mace ta ƙaunaci namijin daya kwanta a ƙasan zuciyarta, a kullum na ganka sai na ji zuciyata na kiran Safiyyerh wannan shine ƙaddararki zaɓin da kike jira irin namijin da kike fata, idan zuciyata ta kusanci zuciyarka sai na ji tawa zuciyar ta sake buɗewa da tarin tausayinka, kullum mutuwa nake da farfaɗuwa da soyayyarka ta yan kwanakin nan data rutsa da zuciyar Safiyyerh Abdu Marafa, kullum mutuwa nake da son ka, wallahi...,"" kasa cigaba ta yi saboda kukan daya ƙwace mata da gaske, da ace ita ƴar wasan kwaikwayo ce irin fina finai da ake haskawa sai ta ce a yanzu acting take, duk abin da take faɗa she doesn't mean it, iya laɓɓanta ne kawai ta yi hakanne saboda ta yi kutse cikin rayuwarsa ta san waye shi me ya sa ya zama" "abin da ya zama, tana son jin labarai mai kama da hikaya ko almara ko na soyayya." """Will you love me?"" Ta ce tana marairace masa fuska tare da ɗan turo masa jajayen cute lips ɗinta, ya bi" lips ɗin da kallo ta haɗe hannaye waje guda ta langwaɓar da kai """Please, Safiyyerh loves you a nan a cikin nan ɗina""" Ta nuna masa saitin ƙirjinta wajan zuciya da yatsarta manuniyya sai ƙifta idanu take. Har lokacin bai ce mata komai ba kamar yadda ta lura yawan magana ba ɗabi'arsa bane yana wanzuwa da shiru da tunanin ya fi masa. A duk maganarta ɗaya ƙare haɗe fuska yake yi ya zaro sigari ya kunna ya saka a baki da ƙarfi ya zuƙi hayaƙin yana jin saukar hayaƙin ƙasan ƙirjinsa ya hura kumatu ya matsa dab ya fesa mata a fuska ya yi gaba abin shi yana taku ɗaiɗai irin he don't care. Safiyyerh ta bisa da idanu ta yi shiru ta ji ta damu sosai a ranta tana Astagafirulla data tuna da gaske ita matar aure ce matar Aliyu Abdu Marafa ce ita halaliyyarsa ta jingina da jikin bango tana lumshe idanunta. "Moh bai ƙara dawowa cikin gidan ba, har dare ya nutsa bama shi ɗaya ba kusan dukkan su basa nan ta" "dinga sallah tana addu'a har girki ta yi musu ta ajjiye amma ya yi sanyi. Tana haka ta ji an buɗe gidan da sauri an shigo ta buɗe ƙofa ba tsoro ta fito Mangal sai nishi yake yana kallon ta, da gudu Goje shima ya shigo yana shigowa kuma ya rufe ƙofar ya zube a ƙasa ta kalle su cikin sigar damuwa ta ce ""Ka rufe ƙofar" "shi kuma fa?""" """Bai shigo ba?"" Ta jinjina masa kai ya miƙe tsaye ya ce ""Jagwal kenan, ai kuwa bama tare""" """Innalillahi kamarya like how bakwa tare?""" """Ke bafa wani abu saɓe kawai ki je ki yi kasa ko"". ""A'a don Allah ka je ka nemo shi ka ji ɗan'uwanka ne fa" "idan wani abu ya same shi ai ba za ka ji daɗi ba, shi ma ba zai bari komai ya same ku ba"" ya yi murmushi ta lura yana da fara'a ba kamar sauran ba ""Ubangiji nada kyakkyawan tanadi a rayuwar Mai dawa, ba" "yanzu zai mutu ba kin ji ko?""" """Na kawo muku abinci?""" """Dar daidai kenan kin taimaki ƴan hanjina jagwalo shi nan a ɓatar da shi a rufawa ciki asiri"" abincin ta" "ɗakko ta kawo musu duk yadda taso su wanke hannu ƙi sukai Kodayake haka ogan nasu shima yake. Har bacci ya ɗauke ta bata saka shi a idanunta ba. Sai da asuba ta fito dafa ruwan wanka kamar jiya haka ta ganshi ya yi shiru yana kallon sama, tunanin maganganun da Abbasa ta yi masa yake da abin da Ali wali" ya dinga nanata masa akan Safiyyerh. """Bai kamata gwarzona ya wanzu yana tunanin da zai iya illata masa rayuwarsa da zuciyarsa ba, haba" "mafaraucina"" ya juya ya kalle ta, ta kashe masa idanu ta ce ""Yes, ba farautar dabbobi kawai ka iya ba ka yi dacen farautar zuciyar ƴar Professor Abdu Marafa"" kamar a buge yake haka ta lura da shi musamman yanayin zaman da ya yi, sai a lokacin ta lura da yankan dake damtsen hannunsa ta ƙarasa ta duƙa ta ce ""Subuhanallahi faɗa ka je ka yi haba mai sunan manya, Muhammad Mutallab fa masu sunanku salihan" "banyi ne""" "Ya duƙar da kan shi ƙasa ta je ta ɗakko kayan da Goje ya kawo ta zauna dab da shi, ta kamo hannun nasa" "sarai ya jita amma bai kula ta ba, tunani ne ya addaba masa. Ya shiga hura masa iskar bakinsa ganin" yankan na kumfa data saka magani ta gama yi masa treatment ta kalle shi taga ya rufe idanu miƙewa ta yi zata fita kamar daga sama ta ji ya ce """Cikakken sunanki""" """Safiyyerh Abdu Marafa""" """Cikakke"" ya sake maimaitawa ""Haka sunan yake fa Jarumi""" """Shi Abdu?""" """E, sunan daddy kenan Abdu"" ya buɗe jajayen idanunsa ya watsa mata su ta yi saurin yin ƙasa da nata" "idanun ta fidda ran zai yi magana har zata juya ya ce ""Ƙarya, idan na tuna miki na kwaɗa miki mari ko?"". ""Allah ni dai haka na sani babana ne fa""" """Uhmm"" ganin kamar da magana a bakinsa kuma a buge yake ta matsa ta zauna ta ce ""Jarumi, do you" "want to say something? Say it. Ka ce wani abu Jarumi""" """Faɗi mana Jarumi""" """Tiger"" ya ce a hankali ta ce ""Me ka ce? Ban ji ba""" """Ammm, hmm kika ce ba ki da aure?"" Ta ce ""E, bani da shi like a told you"" ya buɗe ido ya zura mata" "idanu yana ta kallon ta da ƙyar ya iya cewa ""za ki so ni?""" """Zan aure ka na rayu da kai idan ka faɗa mini labarinka waye kai?"" Ya sake yi mata shiru ""Ina ji""" """Zana ba ki labarina idan za ki aure ni""" """Ni Safiyyerh na yi maka wannan alƙawarin zan rayu da kai a duk yadda rayuwa ta yi da kai Jarumi"" ya" "miƙa mata tafin hannunsa a hankali kamar mai jin tsoro ta kalli hannun cike da rashin fahimta, jiran ba'asi take shi kuma ya yi shiru sun ɗauki minti biyar da wasu daƙiƙo a hankali ya sake furta ""Promise"" ta dinga kallon hannun kafin ta yi Astagafirulla da tunanin Ubangiji ya yafe mata saboda igiyar auren wani ce a kanta ta ɗora ɗan ƙaramin hannunta cikin nasa, tana sawa ya damƙe kamar abin da yake jira kenan ya yi shiru ya lumshe idanunsa muryarta na rawa ta ce ""I Promise you Jarumi"" yana riƙe da hannun bai cika ba bai kuma yi magana ba can ya sake ta, ta fara masa magana sai dai ko tari bai kuma yi ba" tunaninta bacci yake yi ta dinga kallon shi tana son hango kyau ko ko muninsa. A daren ranar su Goje basa nan sai shi ɗaya yana busa hayaƙi a sama yake jinsa sosai ya ji an buɗe ƙofa "an shigo, maza ne har su huɗu sun rufe fuskokinsu ya damƙi wuƙarsa kafin ya miƙe ɗaya ya cafki wajan yankan da Safiyyerh ta gyara masa ya janyo hadda naman wajan suka fara kokawa yana buga su da ƙasa, cikin sauri Safiyyerh dake bacci ta farka zata fito daga cikin ɗakin ya yi baya da ƙarfi ya tura ta ciki ya rufe ƙofar ta taga ta leƙo tana kiran shi, taga ya ɗaga wuƙa ya sokawa ɗaya a gefen wuya ya ƙara soka masa a ciki ya watsar da shi can gefe yana kakari, Safiyyerh ta zaro idanu tana rufe baki saboda ihu za ta yi ganin yadda aka yi kisan kai akan idanunta, bata san mene ya faru ba taga ɗaya ya zaro sirinjin allura ya zirarawa Moh a damtsen shi, ya sake zaro wani ya yi masa da azama Moh ya ɗaga wuƙar hannunsa ya sari wanda ya yi masa hakan ya goce ganin sun yi masa allurar suka ja wanda yake kwance kamar gawa" "suka bar gidan, a hankali ya yi baya ya zube saman kujera jini na ɗiga jikinsa" "Ilahirin jikin Safiyyerh rawa yake cikinta ya ƙulle ta shiga uku, kisan kai aka yi akan idanunta haka dabar" "take dama? Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un. Moh kuma minti goma ya yi yawa ya ji zufa na yanko masa jikinsa ya yi sanyi wani irin baƙon al'amarin ya fara ziyartar gangar jikinsa yana sauka a mararsa, abin da bai taɓa tunani ba idanunsa ya shige ciki ya ɗauki ƙwaya ya zura a ƙasan harshen shi da tunanin zai daina ji, amma ina kan shi ya hau ciwo ya miƙe da ƙyar ya nufi ɗaki jin tsigar jikinsa na miƙewa da zubewa sanyi na ratsa shi komai na jikinsa ya bubbuɗe al'amarin buƙatuwar wani abu. Ya kwanta ya yi shiru can ya mirgina ya yi rufda ciki ya lumshe idanunsa ya jiƙe shimfiɗar lokacin ɗaya da zufa da jinin da yake zufa a jikinsa, ya rasa ciwon ciki yake ko mara ko zazzaɓi? Jijiyoyin kan shi sun miƙe raɗau lallai ya ji akwai abin da yake buƙata ya dinga juyi ya shanye sigari kwali wajan biyu amma ba abin da ya sauya ba zai ce" tsautsayi ne ya kai shi ɗakin Safiyyerh ba saboda kawai tsintar kan shi ya yi a ciki. Safiyyerh na bacci ta ji hucin numfashin mutum a fuskarta ta buɗe idanu da sauri ihu za ta yi ganin "fuskarsa kamar zai haɗe da tata ta yunƙura zata tashi ya saka hannu ya mayar da ita kwancan ""Dan Allah" "karka mini komai ka yi haƙuri ba zan sake kula ka ba, innalillahi na shiga uku daddy ka yi na tuba don" "Allah"" bai kulata ba yana daga durƙushen da yake dab da ita ya miƙa hannu ya kashe wutar ɗakin gabaɗaya." LAST FREE PAGES Waye Mutallab? Waye Scorpion? Wace Safiyyerh? Waye Daddy? Mene FS WORLD INVESTMENT COMPANY? Labarin Mutallab da tarihinsa ya fi wannan da muke ciki yanzu ai za ku zo jin wannan soyayyar ta ƙuruciya ba? Mene yake saka a fara daba da shaye-shaye? Wanne ganganci iyaye suke yi akan yara? Mece siyasa da cikakken tarihin dimokuraɗiyya? Za ku su sanin ya ake mulki a ƙasar nan? Har ku yi supporting yaran ku? Soyayya na saka shaye-shaye ne ko daba? Me ya sa Mata har uku suka mutu ta sadanadin MOH me ya sa ya kashe matarsa SAFIYYERH? YAUSHE SAFIYYERH TA HAIFI YARO? maza hanzarta yin payment chat with me on WhatsApp 08164069385 BRIGHT PENS... 2ND BATCH "[10/1, 9:36 PM] Nanameera: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 1 Nimcyluv Bright pens. second batch *Marubuciyar. ❤🔥* *Mijin malama* *Munafukin miji* *Moon* *Idan ba ke* ..... E.t.c and now *MUTALLAB* "* for some reasons. Akwai copywrite kar a haɗa mini ducoment, banda YouTube a bar mini kayana" haƙƙina ne* "Jami'an tsaro ne ta ko'ina cikin kayan kaki ma bambanta, duk da cewa yammacin ranar lahadi ne a watan" Fabrairu bai hana ta gane fuskarsa ba. Cikin tashin hankali jikinta na rawa da kyarma ta nufe shi tare da "ƙoƙarin cakomo wuyan babbar rigarsa tana furta cewa ""Shi ne, wallahi shi ne, daman na ce zan gano shi""" a gigice mutumin dake ƙoƙarin shiga motarsa da aka buɗe masa ya yi baya yana mai ƙarewa matar kallo sosai sai dai ya kasa gano ko wace ita? Daga ina me kuma take buƙata. """Wace ita?"" Ya furta yana tambayar zuciyarsa tare da kallon gefe. ""Wallahi shi ne, mugu azzalumi sai ka" "yi kuka, ka wulaƙanta "" Jin furucinta ya saka ƴan'jarida dawowa kan ta, suka fara tambayar ""Kin san" "shine? Mene haɗinki da shi?"" Kafin ta yi magana wani ya ce ""Arrest her, ku kamata""" "A hankali ya jingina da jikin motar can ya numfasa yana kallon yaronsa ya ce ""Wace ce? Na santa ne? To" "me ya sa take abu kamar ta sanni?""" """Sir da gaske ta sanka bana jin ko mutuwa ta yi ta dawo zata manta fuskarka, kuma zamanta a raye yana" "nufin abubuwan da yawa dole a yi wa tufkar hanci, kar a bari ƴan'jarida su samu ganawa da ita, even your securites, wannan matsalar kai da kai ce kuma zata shafi kimarka"" cike da mamaki ya yi ta kallon yaron nasa na tsayin sacanni da ƙyar ya cije leɓe ya ce ""To ina na santa? Me ya sa zata zama" "damuwata?""" """Sir ita ce wacce ka saka aka kawo maka ita, wacce ka yi wa fyaɗe a lokacin ,""" """Ya isa!"" Ya ce yana jin jiri na neman ɗauke shi, ya dubi tarin jama'ar da suke wajan can ya yi murmushi" "yana ɗauke fuska sai kuma ya ƙurawa yaron idanu ya juya ya kalli matar ya gyatsine fuska ya ce ""kuma ta" "kasance a raye ya haka? To a yi hanzarin toshe wannan ɓarnar ya zama kamar ba a yi ba""" """Amma me ya kamata a yi mata?""" """A yi mata allurar hauka, wacce ake yi duk shekara da wata wata kana a kaita gidan yari, life in prison har" "ta mutu. Bayan haukan zata mance komai, su ƴanƴan talakawa wama ya damu da su mutu ko su yi rai bata da wani mai tsaya mata kai mutuwa ma za ta yi"" yana faɗin hakan ya shige mota. Tana takure a jikin ƙofar ɗakin da aka ajjiyeta idanunta ƙur a kan photonsa zuciyarta sai zafi take mata wani abu ya tsaya mata. Da sauri ta juya jin an buɗe ƙofa wani mutum ne sanye da farar riga ya rufe fuskarsa hannunsa riƙe da ƙaton sirinji iya ruwan allurar da ya yi ja abin tsoro ne, ta fara ja da baya amma a haka ya fincikota tare da yin cilli da ita,ta faɗi saman carpet bai tsaya jiran komai ba ya caka mata allurar a ƙashin" bayanta wajan spinal cord ihu ta fara da birgima idanunta ya shiga ƙaƙƙafewa jikinta na sandarewa ta dinga buga kanta da jikin bango tana buge-buge a hankali jini ya fara fitowa ta cikin hanci da bakinta tabbacin allurar ta amshe ta za kuma ta yi aikin da ake buƙata a jiki da ƙwaƙwalwarta. ****** Cikin sauri suke tafiya a wani ɗan dogon lungu mai duhun gaske tsarin wajan gabaɗaya a ƙuntacce yake kamar zunubin gidan yari. Magana suke ƙasa-ƙasa ɗaya daga cikin su kuma yana duba agogon dake hannunsa tare da duba cikar lokacin fuskarsa a haɗe take sosai. Sai da suka kawo ƙarshen ginin suka tsaya ya ɗaga kai a hankali ya dubi saman da kansa ke taɓowa ya ɗan rusuna sai kuma ya dubi jami'in "tsaron dake wajan ya yi masa nuni daya buɗe ƙofar. ""Yes sir!""" Bayan ya sara ya ƙame ya buɗe ƙaton kwaɗon yana toshe hanci saboda wari da zarnin wajan. SP Gali ya kalli team ɗin nasa cikin bada umarni ya ce """Ku jira nan, idan akwai damuwa zan muku alama na san dai he can't do anything, ba zai iya komai ba""" "gabaɗaya suka jinjina masa kai tare da zagaye ƙofar fuskar kowannen su manne da baƙin gilas. A hankali Sp Gali ya tura ƙofar ya shiga yana durƙosawa saboda rashin girman wajan. Tunda kafin su ƙarasu wajan ya san da zuwan nasu har aka buɗe ƙofar tare da shigowa, yana durƙushe inda yake ya kifa kansa a ƙasa hannunsa dunƙule ya damƙe abu wanda tun kafin a kawo shi gidan abu yake a hannunsa, yin duniya yaƙi" buɗe abun balle a san menene shi. """Hey you!"" Sp Gali ya ce yana saka ƙafa tare da buge ƙafarsa ganin yaƙi motsawa, tamkar gunki haka yaƙi" "motsi ya kuma ƙi ɗago kansa Sp Gali ya shiga kallon wajan ya rasa wanne irin hali ne da wannan yaron mai baƙar zuciya da taurin kai ya sauke numfashi cikin kwantar da murya ya ce ""Ni idan na ce maka ina da tausayi na yi maka ƙarya, amma ka saka zuciyata karaya kana bawa kanka wahala kana bawa jami'anmu wahala. Me zai hana ka sauƙaƙa mana wahalar nan ka faɗa mana gaskiyar abin da ya faru a wannan rana kuma a wannan daren? Me ya sa ka aika abin da ka aikata? Ka kashe matarka, ka kashe ta har lahira kuma kaƙi magana shekara uku kenan kana wajanmu ka rainawa hukuma hankali da kotu, kai baka da zuciya ne dame kake taƙama saboda kana da tsari a jikinka ƙarfe ba zai ratsa naman jikinka ba, muna da kalolin azaba nau'i-nau'i amma gaskiya muke buƙata, ka amsa cewa ka kashe matarka a zaman" "kotu na yau shikenan sai a yanke maka hukunci daidai da zaluncin da ka aikata""" "Har Sp Gali ya kammala maganarsa bai motsa ba, babu alamun zai ɗago kai balle ya tanka. Sp ya miƙa" hannu zuwa hannun mutumin dake dunƙule da abu zai amsa a firgice ya ɗago kansa yana buɗe dara- daran idanuwansa akan Sp Gali sai da zuciyarsa Sp ta motsa saboda wani mugun jaa da idanunsa ya yi. Fuska ɗaure ya yi wa Sp kallon warning har lokacin bai yi magana ba dukkan naman jikinsa rawa yake kamar zai kaiwa Sp damƙa fuskarsa baibaye da gashi kansa ma cunkus yake ba'a gane kamanninsa sosai saboda cikar gashi. "Sp ya duba lokaci sai kuma ya shafa kai ya ce ""SCORPIO"" nan ma ya sake ɗago kai da sauri ya zubawa Sp" "idanu ""Idan ka bari na gano cewa kai ne Scorpio """ "Ya cije baki yana miƙewa tsaye ya furta ""Zan addabi rayuwarka, gwara ka zauna a iya wanda ya kashe" "matarsa da dai ka kasance kai ne Scorpio. Mene asalin sunan naka?"" Ya tambaya yana juyawa kamar zai fita saukar gurnanin da ya ji ya saka ya yi saurin juyawa idanunsa ya sauka wanda ake zargi da kashe matar tasa yaga ya dafe kai da hannu bibbiyu yana jujjuyawa ya dinga haɗa kansa da bango cikin sauri Sp" Gali ya ce """Team"" a guje suka shigo hakan ya saka ɗan ƙaramin ɗakin cika fuskar Sp ba wasa ya ce ""Ku danne shi a" "karɓo abin hannunsa dole mu san mene babu mamaki zamu samu hujja a ciki"" yana cewa haka ya fita yana amsa kira. Ganin sunyo kansa ya yunƙura gabaɗaya ya fisu faɗin ƙirji da damtse amma suka rufar masa sanin cewa sarkin yawa ya fi sarkin ƙarfi ya saka shi damƙe hannunsa da kyau yana ɓoye abun da suka karɓa, kokawa suke da shi ya dinga haɗa su da bango ya kama hannun ɗayan ya karya bisa dole suka fice a wahale. Sp ya saka wasu manyan mutane fito da shi suka ɗaure shi da ankwa tare da sarƙa" tun daga ƙafa har zuwa kansa. A harabar Criminal Investigation department CID aka tsaya dashi domin tafiya zuwa kuto a rana ta "ƙarshe wanda ke nuna ko a sake shi, ko a kashe shi ko kuma ya tafi gidan ɗan'kande. Team guda ne masu matuƙar basira da ƙwarewa akan aikinsu team ɗin ya haɗa da wanda yake ɓangaren Legal section, Anti- human trafficking, Medical Staff, Legal services, NDLEA, FID Federal investigation department. Gabaɗaya idanunsu yana kansa kowanne yana karantar yanayinsa amma shi ko a jikinsa banda faratansa na hannu dana ƙafa da aka ciccire wajan gana masa azaba babu wani rauni a tattare da shi sai matsanancin baƙi da ya yi ya zama kamar mahaukaci saboda shekarun daya ɗauka a kulle daga kuto zuwa state cid zuwa Fid amma har tsayin shekarun bai buɗe baki ya yi magana da kowa ba, babu kuma wanda ya damu daya tsaya masa. Suna ta surutai ƙasa-ƙasa duk yana jinsu har sanda wani yake cewa ""Babu hanyar da za a" "tilasta shi ya yi magana ne? Muna buƙatar muryarsa""" "Sp Gali ya ce ""Ina zargin wani abu game da matarsa daya kashe""" """Wanne abu? A binciken da mukai a wajan iyayen yarinyar tun farko ita ta nuna tana son shi, shi da ita" "class mate ne kuma age mate, tun suna shekaru 15 a secondary school suke soyayya. Me ya sa ya zaɓi ya kashe ta? Sun ɗauki shekaru tare bai taɓa yunƙurin rabata da duniya ba sai ranar da aka ɗaura musu" "aure? This is complicated"" C.i.d Research ya jinjina kai ya ce" """Duk binciken da aka yi shine a ruwa, gwajin hannu, yatsun hannu da sahun tafin ƙafa da CCTV camera" "na kan titin unguwar da aka kai amaryar tasa duk bincika shine""" Shiru sukai suna tunanin gabaɗaya kansu ya ɗauki zafi. Yana da can inda yake ya ja idanunsa ya lumshe yana fesar da iska daga cikin hancin wacce hucinta ya sauka har saman fuskarsa “BESTIE” haka ya ji saukar muryarta a kunnensa kamar yanzu ne suke tare da ita. Ya sake lumshe idanunsa yana jin saukar dariyarta sosai ya tuna lokacin yana zaune shi kaɗai a cikin class ranar aka dawo hutun makaranta shi kaɗai ne zaune ciki yana sanye da farar riga sai wando blue black ya ɗora ƙafarsa ɗaya saman benci tare da yin baya. "A hankali ta shigo cikin class ɗin hannunta riƙe da lunchbox da textbook sai school bag data goya, hijab" ɗinta daidai da ƙirjinta ita ce ta fara shigowa da mamaki take kallonsa zuciyarta na bugawa ta je ga zauna "inda yake ta zuba masa idanu sai kuma ta ce ""Ka yi holiday assignment?""" "Ya buɗe manyan idanunsa bai ce komai ba ta sake ƙasa da murya ta ce ""Na san bama ka yi ba ka daina" "haɗe mini fuska, ka naso a yi ta faɗa da kai da teachers"" nan ma bai kula ta ba a hankali taci sautin da cikinsa yake yi sai ta jawo lunchbox ɗinta ta buɗe tare da tura masa gabansa ta ce ""Your breakfast, ka ci kafin a shigo na san baka karya ba"" sai a lokacin ya buɗe idanu ya juya gabaɗaya yana kallonta sosai ta yi" ƙasa da murya kamar zai yi faɗa sai kuma a hankali ya ce """Kuma ga mayunwaci ko?"" Ta yi murmushi ta ce ""Da ƙyar na jure ban biyoka gida ba, na yi kewar ka" "sosai bestie"" ya yi mata shiru sai kuma ya haɗe fuska sosai yana janyo abincin yaga dankali ne aka soya" da ƙwai ya yi ɗan tsaki ya ajjiye spoon ɗin ya damƙa ya kai bakinsa ta yi saurin kama hannunsa ta ce """Kai baka iya komai bane? Sai a yi maka dariya cin abinci da hannu"" ya ware idanu sai kuma ya murtuke" "fuska ya ture hannunta a hankali duk da muryarsa a kumbure take ya ce ""Ki daina kusanta kan ki dani, ni fa ba ɗan iska bane""" """Laaa Allah Ya baka haƙuri kai duk abin soyayya baka iya ba"" a taƙaice ya ce ""Ke kika santa"" ta ja baya" "tana ɗaga hannu ta ce ""Lalala to shikenan ni dai ƙaddararka ce, na faɗa a gida a yi mini aure, ka san me" "na ce?"" Ya girgiza mata kai kawai yana sake damƙo dankalin yana dannawa cikin bakinsa saboda yunwa" ko gani baya yi sosai ta buɗe gorar ruwa ta miƙa masa a hankali ta ce """Na ce su yi mini aure wallahi bana son karatun nan, na ji aure nake so kuma na faɗa musu kai nake so," "amma wai ban isa ba karatu ya zama dole kuma shekaruna sun yi kaɗan amma ai ma girma shekararmu 15 years fa, ko kai baka isa aure bane?"" Ya yi mata shiru sai ta fashe da kuka sosai ta ce ""I love you so much Bestie, don Allah ka aure ni zan zauna dakai a duk yadda kake ka taimakawa rayuwata"" ya zame hannunsa tas ta miƙa masa tissue ya goge ya ja baya yana lumshe idanunsa har yanzu students basu fara" "shigowa ba, ta ɗan yi gaba kamar za ta shige masa ya cikin tsawa ya ce ""Zan kwaɗe ki kuwa""" """But what if i told you i love bestie? You mean the world to me, wallahi aure nake so ba karatu ba"" ta" faɗa tana shassheƙar kuka sai a lokacin ya kalleta fuska babu walwala ya dubi yadda take kukan sosai ya ce """Ke, babanki ne ya mutu? Ko uwarki ce?"" Ta girgiza masa kai ya sake haɗe fuska yana rarraba idanu a" "cikin ajin kamar mai neman wani abu can ya ce ""To kece za ki mutu kenan?"" Ta girgiza kai sai kuma ta ce ""A'a""" """Kukan fa?""" """Na soyayyarka ne bestie taɓa ƙirjina ka ji wallahi ni ce ƙaddararka ba zaka gane hakan a yanzu ba, da ina" da ikon cire abin da nake ji a ƙirjina da na yi hakan ina jin dama na mutu na huta kuma idan ban aure ka "ba zuciyata zata iya bugawa""" """To gwara ta buga na huta da na ci, shekaruna 15 za ki lalata ni da batun aure, ke tashi ki ware daga nan" "ɗauki kwananki kar ki ƙara kawo mini abinci"" ta miƙe jiki a sanyaye zata bar wajan ya nuna mata" "lunchbox ɗin daya cinye komai ""Ko daɗi bai yi ba abincin""" "Sai a lokacin ta kyalkyale da dariya kamar ba ita ta yi kukan ba, dimples ɗinta na lomawa ta ajjiye masa" "500 ta yi waje tana cewa ""You're my darling jarumina, i love you Mai dawa da jeji"" ta faɗa tana sake yin dariya tare da yin waje......." Ya yi saurin dafe kansa jikinsa na rawa yana jin dariyar nata na yi masa amasa kuwwa a kunne kamar "yanzu ne take yi jikinsa ya ɗauki rawa sosai daidai lokacin aka tura shi cikin motar shiga babu biya, aka nufi kuto. Tun kafin a shigar da shi suka ci karo da wani saƙo daya basu mamaki ainun suka tsaya suna kallon juna sosai cike da tsoro da shakku musamman Sp Gali ya juya ya kalli wanda ake zargin a karo na" farko yaga ya yi wani irin murmushin kefen baki wanda ya bada sauti kamat na tsaki yana murza kai gefe. "Cikin sauri Sp Gali ya ce ""Amma wane ya yi hakan? Bayan ba a gama bincike an tabbatar da hakan ba," "mene matsayin ran yarinyar daya kashe ina matsayin iyayenta"" ""Sp Ghali ka yi abin da aka ce, kuto ta" "wanke shi daga zargin da ake yi masa ku sake shi ya tafi gida baku da ikon riƙe shi""" "Sp Gali ya girgiza kai cike da damuwa ya ce ""Sir kana nufin bashi ya kashe ta ba"" cikin tsawa ya ce ""Ko" "shine ya zaka yi? Ka yi abin da ya dace a matsayinka na jami'i Sp Ghali karka matsa"" jiki a matuƙar sanyaye Sp Ghali ya kunce shi tas ya ce ""Congratulations. Ka sani shari'a saɓanin hankali ce"" shi dai bai ce komai ba ya ciri biron gaban rigar Sp Gali ya fara yi masa rubutu a tafin hannunsa dam zuciyar Sp ta buga ganin ya rubuta kalmar SCORPIO kafin ya yi magana tuni ya juya ya fara tafiya cikin sauri duk da" rashin kuzarin da yake dashi yana jin inda iskar ƴanci ke ratsa jikinsa yana shaƙa tare da kaiwa hunhunsa. Kano/Birget Dambe suke yi a tsakiyar tsakar gidan mata wajan uku ne kowacce da ɗaurin ƙirji ga tukunyar abincin dake saman murhu. Banda sautin hayaniyarsu babu abin da ake ji hatta Malam dake waje da Almajirai yana jin yadda suke aibata juna da zagin juna hakan ya saka ya miƙe riƙe da bulala yana ajjiye allon hannunsu da yake rubutu ya yi cikin gidan. """Ke har kin isa ki ce za ki hana Mufeederh abinci a gidan nan? Wace ke?"" Cikin ɗagawa Inna Binta ta ce" """Ni Binta matar malam ki faɗa mini nawa Mufee ta bayar aka haɗa wajan yin abincin nan? Ke uban yaran nan bai bada kuɗin abinci ba, ba zai yiwuwa yara su haɗa kuɗi kuɗi a siyo dusar awara a yi dambun nan ki ce wai na zubawa Mufee ba ƴar banzar yarinyar da bata da kunya, kina kallo sauran ƴan'uwanta suka fita nemo kuɗi ita ta yi kwanciyarta tunda ƴar mai ce ai yanzu sai ta ci hantar ubanta Malam gashi can" "yana zaman banza ba fuss""" "Mama dake ƙoƙarin ganin ta wafcin dambun a kwano ta ce ""Daɗin abin dai ba yaranki kawai suka haɗa" "kuɗin ba, hadda Saudat ko Zaituna?""" """A'a ba ruwan Zaituna tun jiya nake ganin hazo-hazo a idanuna cikina banda salati ba abin da yake," "Saudat da ciwon ciki ta kwana Olser ta buge ta saboda yunwa ki yi ta kan ki kawai wannan rayuwa Allah dai ya fisshe mu, amma yunwa za ta yi ajalin rabin jama'a a wannan zamanin"" Mama Zaituna ta faɗa tana turo kwanan Saudat da nufin a zuba mata ta ɗan tsakura a ciki ta yafa a nata cikin. Inna Binta ta shammafe ce ta yi sama da tukunyar kasancewar ta sharifiya ta ce ""Wallahi sai Mufee ta ci abincin nan"" Mama Zaituna ta ce ""To Allah Ya isa daman kun saba cin kayan Allah Ya isa in sha Allah sai ta yi aman" "shi"" Inna Binta ta ji an cauɗa mata bulala a ɗuwawu ta yi saurin dire tukunyar ta ce" """Kan uba wanne mai tsautsayin ne haka?...,"" shiru ta yi ganin Malam ya ce ""Kina sake magana ina ƙara" "cauɗa muku shasha kawai mara kan gado""" "Ya juya wajansu ya ce ""Mayu marasa godiyar Ubangiji kawai akan abinci duk maƙota da unguwa sai" "anjiku"" Inna Binta ta ce ""Yaushe rabon da muga sisi taka banda masifar tsiya kana bamu za mu yi haka ne?"" Kan ta ya yi da bulala ta yi saurin waftar dambun a hannu ta yi ɗaki tana ""Ohho dai na ɗiba na mai" "da mugun miyau""" Haushin karnuka suka ji wanda rabon da su ji shekaru uku kenan gabaɗaya suka juya wani ihu Mama Zaituna ta yi tare da fatali da dambun da ake ta yin masifa akan shi har zaninta na kuncewa zuwa ƙasa ta yi saurin juyawa zata ɗakko ta zame da ɓawan albasa ta faɗi dif a ƙasa Kasancewar ƙatuwa ce sosai ta fasa ƙara da jan ɗuwawu ta shige ɗakinta hankali tashe. Shi kansa Malam sai da zuciyarsa ta motsa saboda tsoro ya dinga kallon karnukan da idanu yadda suke ɗaga jela tare da zaro harshe waje jibga- jibga dasu sai zagaye wanda ya shigo suke yi. Da ƙyar Malam ya ja numfashi ya ce """Muɗallabi Ɗanmalam nake gani haka? Ya suka sake ka basu kashe ka ba, ni na ɗauka ma tuni ka mutu" "wallahi, ikon Allah"" sosai kansa ke masa ciwo kamar zai rabe ga wani ciwo da jikinsa yake yana jin fatarsa" "na rawa, ya yi baƙi sosai amma manyan idanunsa na nan kayan jikinsa duk a yage ya zubawa Malam" idanu. """Kai Muɗallabi ba da kai nake magana ba? Yanzu da suka sake ka me suke nufi ka kashe ƴar mutane a" "banza kenan? Ba zan goyi bayan gaskiya ba dole na je wajan jami'an tsaron yanzu na bi ba'asi""" Cikin sauri Ammo ta fito daga ɗakinta jin sunan wanda aka kira zuciyarta har rawa take tana fitowa suka haɗa idanu dashi ya kafe jikin bango a hankali yaran gidan suka fara fitowa ya dinga bin guntattakin "yaran da kallo wasu duk bai san su ba. Ya nufi Ammo ta yi saurin ɗaga masa hannu ta ce. ""Ina jin tsoron" "kiran ka a matsayin ɗana na ji na yi dana sanin haihuwarka wallahi""" Ya buɗe manyan idanunsa sai kawai ya ja ya lumshe yana ƙara yunƙurin zuwa wajanta kenan ya ji ihu a waje kafin ya motsa Goje ya shigo da sauri yana cewa """Mai dawa ƴan unguwa ne ɗauke da makamai wai za su ɗauki fansar. "" Da sauri MOH ya ɗagawa Goje" "hannu baya son ma a kira sunanta a kusa da shi zuciyarsa buɗewa take sosai. Goje ya sake cewa ""Ba ƴan" "unguwa kaɗai ba har da gajoji da cinnakun layi"" kafin Goje ya ƙarasa sun ji ana cewa" """Ba iya Mai dawa ba har Malam da babarsa yau sai sun mutu da duka mutanen gidan sai mun ɗauki" "fansar yarinyar daka kashe tunda jami'ai sun sake shi a banza"" Mutallab ya kalli karnukansa ya musu inkiya Tiger ne ya fara zuwa ƙofar ɗakin Ammo ya tsaya Rainbow ya je ƙofar gidan ya tsaya, Spider kuma ya tsaya yana kewaye Malam. Goje ya ce ""Kai ƙarfe baya cinka tsine baya ratsa jikinka su Malam sune matsalar"" bai magana ba kai tsaye ya nufi waje gaban Ammo ya faɗi ganin ba makami a hannun Mutallab. Inna Binta ta fito tana zunduma ihu tana jama'a su kawo musu ɗauki tana leƙa ƴar ƙaramar katangar gidan ganin tarin matasan da suke waje ɗauke da makamai ya saka Inna Binta kurma ihu tana faɗin ""Ya gafilan zanbi waya kashifal gammi "" Bata gama ba aka raɗa mata gora aka ta faɗo ɗaga" saman katangar ta baje wanwar a ƙasa Mufee ta fasa ihu tana yin wajan Inna Binta ganin haka sauran mutanen gidan suka shige ɗaki banda Ammo da Malam. Moh na fita suka yi masa ƙawanya kasancewar akwai shafi a hannunsa duk wanda ya daka sai ya baje a "wajan, suna da yawa sosai cike da rashin sanin cewa tsarin jikinsa ya karye ya shiga tsakiyar su ɗaya ya ɗauki dutse ya buga masa aka nan take ya fashe, wani ya ɗaga wuƙa ya soka masa a ciki nan take wuƙar ta shige Goje ya zaro idanu ganin sun yi nasara ya saka suka zagaye Moh suna kai masa sarawa, baya faɗa da makami bai san kuma ya ake yi ba, kafin wani lokaci sun kai shi kasa ko'ina na jikinsa jini ke fitarwa daidai lokacin tawagar mafarauta suka ƙarasu wajan tare da zugar karnuka faɗan ya koma tsakanin ƴan unguwa da mafarauta cikin mawuyacin hali Moh ya ja jikinsa a hankali jin wani yana waya da ƴan'sanda ji ya yi dama layya zana na wajansa a yanzu haka? Ya dinga tafiya yana jan jiki har ya bar unguwar ya shiga cikin wani waje mai kama da gonaki kuma jeji-jeji. Tana zaune cikin bukkar hannunta" riƙe da ƙwaryar nono ta ji an faɗo cikin bukkar a gigice ta miƙe tsaye... "*To ga dai shi nan ban san ya zaku amshe shi ba, amma tabbas zai zama daidai da ra'ayinku musamman" iyayenmu mata da maza da suke wasa akan yaransu. MUTALLAB zai zo da sabon salo in sha Allah za a yi kuka sosai kuma za a yi dariya fatana kar ku yi mini zagin da kukai a MIJIN MALAMA ku amshi labarin da hannu bibbiyu ku tayani isar da saƙon zuwa ga manya ta hanyar yin sharing saboda Allah* 08164069385 WhatsApp only "[10/2, 8:40 PM] Nanameera: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 2 Nimcyluv Bright pens. Second batch * Warning... For criminal issues* "Cikin bukkar ya faɗa jikinsa jina-jina da jini sara ta ko'ina da ƙyar yake iya fidda numfashi, ya zube a" "gabanta idanuwansa a lumshe har yanzu yana jiyu sautin ihu da kukanta, ya kasa ceton ta, ta sake mutuwa, yaushe zata ci-gaba da rayuwa tana sake macewa akan idanuwansa? Ya cije jajayen laɓɓansa wanda jini ya ɓata sam bai damu da yadda yake shanye jinin yana koma masa ciki ba, a matuƙar fisge ya yi maganar mai sautin gurnani ya ce ""Na amince, da gaske na amince Abbasa, zan zama mata maza, ki mayar dani jinsin mace ina tunanin zama macen ya yi daidai da tafiyar ƙaddarata! Zan zama mata maza," "bana iya kwanaki ba, bana iya wa'adin sa'a ba, ba kuma iya na tafiyar sakwanni ba, ba kuma iya na" "gilmawar kwanaki ko shuɗewar watanni da nisan shekaru ba, a'a Abbasa, a'a Abbasa ina son zama mata" "maza ne na daidai da tafiyar agogo da adadin shekarun da zan yi a duniya""" "Yadda furucin ke fitar da kan su, da yadda yake magana idanuwansa na fiddowa waje duka jikinsa rawa" "yake da ɓari yana wani irin tsuma bakinsa har wani hayaƙi yake yi jijiyoyin kansa tamkar zasu ratsa fata bakwai su keto, ganin halin daya shiga ya saka Abbasa cewa. ""Iya zubin tunanin naka kenan? Iya jarumtar kenan? Mayar da suffarka zuwa abi mafi nakasu a rayuwarka? Ka zama mace shin ko ka mace" "da. """ """Abbasa!""" "Ya kira sunanta a karo na farko a tsawa ce, domin baya son tuna abinda take ƙoƙarin cewa ""Shikenan" "shikenan, zaka zama jinsi biyu, mai halitti biyu"" ya girgiza mata kai yana jin amo da sautin muryarta cikin wutar da suka babbaka ta ciki ""Kawai ki nakasta ni"" ""Tabbas zaka nakasa, zaka zama kamar jaririn da aka haifa yau, zaka zama riƙaƙƙe zaka gagara, ubanka zai alfaharin haihuwarka duk da tsinuwarsa na tattare da kai, zaka sake yi rashi, rashi irin wanda baka taɓa yin irinsa ba, zaka samu dukkan wata shahara da" "ɗaukaka da kake buƙata, amma zaka dauwama a matsayin mata maza""" Ihu ya fasa yana ƙoƙarin miƙewa tsaye da ya yunƙura gefen cikinsa yake sake buɗewa saboda shafcecen "saran da aka yi masa, jikinsa bashi da wani gurbin da babu sara.Abbasa ta miƙe ta ɗakko wani farin abu a hannunta tana zuwa kan shi ta danne shi da duka ƙarfin daya zo mata, ta ɗauki garin abun ta fara shaƙa masa a hanci yana shaƙa da ƙyar da sauri ya damƙi hannunta ya kifa fuskarsa da hancinsa gabaɗaya," "yana ihu da gurnani jikinsa na rawa ya fara sambatu, Abbasa ta ce ""A me ka zo waje na?""" """Taya"" ya bata amsa a raunace idanunsa na lumshewa. ""Wasu sun biyo ka ne?"" Ya girgiza kai can ya ce" """Cinnaku, Cinnaku na fi ƙarfin su"" ya dinga juyya kansa can ya ce ""Akwai Kimini a tattare dani, ya faɗawa ƙashi wani abu, sun nemi asawa da Tsohuwa. !"" Ya kasa cewa komai idanuwansa har yanzu na hango" yadda gangar jikinta take ci a wuta. "Ita dai Abbasa ta kasa cewa komai ta zuba masa idanu, ta dinga kallon yadda jikinsa je rawa a hankali" "kuma ya fara saki idanunsa ƙur a saman bukkar cikin fitar hayyaci da yanayi irin na maye yake sambatu tare da kiran sunayen da ita kanta mata sani ba. A hankali ta ce ""Mutallab"" bai amsa ba sai zuciyarsa kawai dake rawa ta hango hakan ne a yanayin yadda ƙirjinsa ke ɗagawa. Ganin ya zama kamar matacce" "tsoro ya kama Abbasa ta tuna ashe bai taɓa shaƙar abin da ta bashi ba a yanzu, maganin ƙarfe dana tauri" kawai yake sha gashi kuma zaman da ya yi na shekara uku a hannun jami'an tsaro ya sa tsarin ya karye. Ƙwarya ta ɗakko ta jiƙon wani magani tare da ruwa mai zafi ta fara danna goge masa jinin jikinsa sai a "lokacin ta lura da gabaɗaya farcen yatsun ƙafafuwansa dana hannu babu ga jikinsa duk alamar an jona masa shokin akan tilasta masa amsa laifin da babu wanda yake da masaniyar komai akai, sun yi masa haka ne da nufin ya amsa laifin kashe matarsa da ya yi. Ta sauke numfashi tare da kallon bakinsa a" hankali ta kara kunnenta a tausashe yake cewa. """Ina son ta, ina son ta zuciyata zata fito ita ce wajan ta uku me ya sa.... Ina jinta a ƙasan zuciyata"" Tunda" "suke bai taɓa yi mata zance ɗiya mace ba, haka bai taɓa magana mai tsayin da ya yi a yanzu ba, duk abin da ya saka Mutallab magantuwa ba ƙaramin abu bane ba. Miƙewa ta yi ganin kamar ya samu yin bacci ta fita waje zuciyarta cike da saƙe-saƙe." Unguwar ta yi shiru saboda zuwan ƴan'sanda wanda da ƙyar suka raba tsakanin mafarauta da jama'ar da "suka zo ɗaukar fansan wacce aka kashe zai ya zama kamar an saka kafiyo ne kasancewar babu wanda bai san labarin kisan rashin mutuncin da aka yi wa yarinyar ba. Tiger, spider, rainbow sune suke ta kai kawo a ƙofar gidan Malam saboda basu tsaro kamar yadda Moh ya saba musu ya raine su tamkar mutane hatta mara gaskiya suna ganewa. Da sauri suke tafiya hankali tashe gabaɗaya basa cikin nutsuwa ɗaya" "sai ɗaga hannu sama take ba'a jin maganarta sai sautin murya. ""Ki yi haƙuri""" Sa'adah ta ce tana shafa hannunta a ƙirji alamar ban haƙuri da yaran kuramen da zata gane ta girgiza kai "tare da sunkuyawa tana buga ƙasa ta ɗaga yatsa sama alamar rantsuwa. ""Allah Ya kyauta, da kin bari mun ƙarasa gani ai ya kori ji Bafullatana"" daidai nan suka ƙarasu ƙofar gidan ba kowa a rumfar Almajiran sai allonansu da rubar tadawa da ƴan rubobi na bara. Tiger ya ƙare musu kallo yana shinshina su sai" kuma ya ja da baya yana ɗaga ƙafa ya basu hanya suka shige cikin gidan. Da Inna Binta dake yashe a ƙasa suka fara cin karo jini na zuba a gefen goshinta ɗan tofinta a bankaɗe "Allah Ya sa ba yara a wajan cikin hanzari Sa'adah ta nufeta tana girgizata ta juya ta yi wa Bafullatana alama data bata ruwa bata fahimci komai sai kawai ta kinkimo ruwa bokici guda ta kwarawa Inna Binta ajjiyar zuwa ta sauke a firgice ta miƙe zaune tana furta ""Dambun Mufee, a kawo ɗauki jama'a dambun Mufee ƴan ta'adda za su kashe ni"" ta ƙanƙame hannunta jikinta ya jiƙe jagab amma har yanzu dambun na hannunta ta miƙe ganin Sa'adah da Bafullatana sai kuma ta ja tsaki ""Irin bala'i wallahi Ammo ta haifawa unguwar Birget masifa ɗai-ɗai da ɗai-ɗai zai dinga kashe mu yana zuƙe jininmu ku duba wannan" "yarinyar ma ya kashe ta kari na uku""" Idanun Sa'adah ya cika da hawaye amma ta ɗauke kai ba tare data tanka Inna Binta ba. Inna Binta ta "watsawa Bafullatana harara wacce ke ta ihu tana taɓo Sa'adah ta ja tsaki ""Kurman banza da wofi gayya masifar, daga haihuwar kurma sai ta ɗan jagaliya"" tana kaiwa nan ta shige daƙinta ta samu Mufee tana bacci ta yi maza ta tashe ta, tura mata ɗan guntun dambun ta yi a baki bayan ta cinye ta ce ""to sha ruwa kiji abin da kika samu sai kuma gobe, ki yi addu'a ki goge Allah ki gode Muhammadur Rasulullah. Banda ina buɗe ido a gidan nan kema mutuwa za ki yi saboda yunwa kamar taki ƴar'uwar"" sai kuma saka dariya" "sosai ""Inna mene?""" """Tukunyar dambu ta kife dan ubanki da tuni ba ki lasa ba kema"" Mufee dai ta buɗe manyan idanunta irin" na Mutallab tana kallon Inna Binta. "Ammo ta dinga bin Sa'adah da idanu ganin yadda take kuka kamar ranta zai fita, Bafullatana kuma ta" "haɗe rai sai girgiza kai take ""Ammo don Allah ina Mutallab yake? Da gaske ya dawo an sake shi? Sun wanke shi daga zargin da ake masa, yana ina?"" Ammo ta ɗauke idanunta zuwa can gefe tana kallon wani waje daban a ɗakin nata can ta ce ""Ki daina kira mini sunansa sallamamman yaron nan a kunnena" "Sa'adah, ki yi hankali watarana zai iya kashe ki""" """Ba zai taɓa kashe ni ba, duk lalacewar shi jinina ne ɗan'uwana ne a wannan halin da yake ciki na ɗauka" "za ki yi murna Ammo? Za ki ja yaronki jikinki ki nuna masa kulawa gudun kar ya sake lalacewa, kar ki ce za ki yi abin da kikai a baya duk lalacewar Mutallab kece wacce kika haife shi, tun yana ƙaramin kin san zuciyarsa yadda yake da zafin nama taurin kai. Kin san yadda yake da ƙulafucin uwa kodayaushe yana manne dake, me ya sa za ki yi haka?"" Miƙewa Ammo ta yi ta nunawa Sa'adah hanya ta ce ""Tashi ki tafi gidan mijinki, banga dalilin zuwanku ba ni bani da wani ɗa Mutallab kuma na sani kuskurena ya saka na haifeshi. Wallahi kika sake yi mini maganar tsinannen yaron nan sai na daina amsa gaisuwar ki har abada"" tana kaiwa nan ta fice ta bar musu ɗakin, fuuu Bafullatana ta fice daga ɗakin zuciyarta na yi mata zafi Sa'adah ta yi shiru ita dai tana mugun son ƙannin nata ai da ba haka yake ba, ya kamata su amshi" hakan matsayin ƙaddara! Washegari Malam na zaune a rumfa yana sauraren karatun wani sabon almajirin shi. Ɗanyaro ne zauna "gefe kusa da Malam yana lissafa sabbin kuɗin hannunsa ƴan dubu-dubu sai sheƙi yake ya duba yaga dubu biyar cif ya mayar aljihu ya zaro baƙar leda mai cike da gurasa da nama ya ya fara ci yana ajjiye lemo fanta a gefe. Ajjiye bulalar Malam ya yi ya ce ""Ɗanyaro ina ka samu kuɗi da nama haka?""" """Bani aka yi Malam"" kafin Malam ya sake magana Ɗanyaro ya miƙawa Malam baƙar leda guda mai" "ɗauke da gurasa a ciki da nama ya haɗa masa da dubu biyu ya ce ""A yiwa su Mufee girki Malam""" "Jiki na rawa ya amsa yana buɗe bakinsa ""Da kyau yaron arziƙi, ina ka samu kuɗi fal haka sana'ar me ka" "fara?"" Ɗanyaro ya girgiza kai kawai can kuma ya kalli Malam ya ce ""Bana yin sana'a, kyauta ake bani kullum, bani kaɗai ba har Muhajeed da Iro"" Malam ya yi sak tunani fal ransa ya sake kallon Ɗanyaro shekarunsa goma rak a duniya a hankali ya miƙe ya yi cikin gida." **** A kusan tare manyan motoci biyun suka tunkaro babban gate ɗin ganin ya rigata kai hancin motarsa ya "saka ta rage ta fiya, hannunta ɗaya a saman sitiyarin motar ɗayan kuma ta ɗan riƙe fuskarta a hankali ta lumshe idanunta gajiya ce a jikinta sosai da ƙyar take buɗe tuƙa motar don dai bata san wahalar driver ne." """Fiyya"" Ya kira sunanta a hankali cikin muryarsa mai cike da nutsuwa ta buɗe idanunta da sukai mata" "nauyi ta kalli wayarta ta manta video call suke yi ma suna haɗa idanu da shi ta ɗauke kan ta gefe tana ya motsa fuska ""Fiyya na miki wani laifi ne? Kin sauya""" """I am sorry ina driving we'll make a call later"" ya zuba mata idanu cike da so da ƙauna yana jin ina ma a" "janyo ranar aurensu da Fiyya a ce gobe ne? Ya sauke numfashi zuciyarsa na buɗe a hankali ya ce “I adore you Fiyya"" ta buɗe idanu ta kalli cikin idanunsa sai kuma ta murguɗa masa baki ya buɗe idanu sosai sai" "ya girgiza kai yana dariya ya matso da fuskarsa dab da camerar ""Na ji kamar ina shaƙar numfashinki """ "Ya yi shiru jin ana knocking ƙofar motar da take ciki, itama ta juya ganin wanda yake tsaye ya saka ta ɗan" "yi murmushi baya ganinta saboda duhun gilas ɗin motar amma murmushi mai kyau ne a fuskarsa. Ta cikin wayar ya ce ""Waye?"" Tana ɗaukar jakarta a taƙaice ta ce ""Yaya Junaid ne""" """Ok"" ya yi sai kuma ya ce ""Fiyya"" ta ɗago idanunta da sukai laushi ta kalle shi dasu can ƙasan maƙoshi ya" "ce “I love you Fiyya"" da sauri ta kashe call ɗin tana haɗe fuska ta ɗauki wayar ta fita daga motar." """Yaya J"" yana murmushi ya ce ""Manager"" ta ɗan yi murmushi kawai ya amshi jakar hannunta ""Me kika" "zo da shi""" """Ba kyau bincike J"" ya jinjina kai suka nufi shiga gate J ya kalli driver ya ce ""Ka shigo mata da motar, she" "left the key inside the car"" Fiyya ta marairai ce fuska tana mannewa jikin J ta ce ""Yaya J na gaji sosai""" """Sannu Manager, ko goyaki zan yi?"" Ta buɗe idanu sannu yake ta yi mata har suka shiga babban parlon" "gidan ƴan samari wajan biyar a zaune a parlon duk dawowar su daga aiki kenan. Wajan tare suka dinga cewa ""Sannu Manager"" ta shige tsakiyar su tana kwanciya a cinyar Marafa ta ce ""Thank you brothers, ku yi mini tausa akwai labari""" """Gulma dai ba labari ba, daka dawowa ko wanka ba ki yi ba kin zaunawa mutane a jiki ƙazamar banza""" "Shiru ta yi masa don basu fiye shiri ba sosai ta juya idanunta rufe, tana jin yadda Marafa ke ta danna mata farar ƙafarta. Yaya J kallonta kawai yake with different thinking running on his mind. Gabaɗaya suka juya jin tafiya cikin sauri ana sakkowa daga saman bene shiru duk sukai suna binsa da idanu domin basu san ya dawo gidan ba, hannunsa ɗaya zube cikin aljihu farar riga ce a jikinsa ta kakin sojoji a gaban" rigar wajan gefe an rubuta A.A MARAFA. """Kee!"" Ya faɗa a tsawace da sauri Fiyya ta buɗe idanunta lokaci ɗaya kanta ta sara sosai tsawar ta ratsa" "kanta, ta miƙe zaune fuskarsa babu walwala kamar yadda itama ta yi kicin kicin da rai ""Tashi a nan, stupid kawai"" ta miƙe tsaye tana murguɗa baki ko inda yake bata kalla ba ta nufi saman bene kai tsaye daƙinta ta nufa idanunta cike da bacci ta faɗa saman gado cikin ƙaramin lokaci bacci ya ɗauke ta. Firgigit ta farka jin sautin labaran ɗ da ake faɗa a gidan rediyo wacce take cikin ɗakin nata, ta miƙe tsaye ta ɗauki rediyon ta ƙanƙame a jikinta tare da lumshe idanunta wasu hawaye masu zafi suna shiga bin idanunta. Ta cikin idanunta take hango fuskarsa a lokacin da rigima ta haɗa su da ita sai take ganin" kamar yanzu ne komai yake faruwa. Students ne an cika sosai saboda class partyn da ake yi na kammala exam maza da mata babu teacher ko ɗaya tunda ta shigo hall ɗin makarantar tasu take duban inda zata ganshi. Cikin sa'a ta ganshi yana zaune saman window sanye da gajeren wando fari tas sai armless ɗin riga wacce duk aka yanke hannunta gashin kansa rabi a aske ya zubawa wani tafkeken gidan masu kuɗi idanu ta waje baya ko ƙiftawa kamar an ce ya juya ya ganta tsaye ta zuba masa idanu yaja tsaki kafin ta yi magana an shigo an "ce ""Mutallab, principal yana nemanka an kai ƙarar ka wai kana son Fiyya""" "Ya ware idanu abin da bai taɓa zuwa tunaninsa ba kenan sai kuma ya cije baki ""Shi principal ɗin ubana" "ne Malam Abdullahi kenan?"" Ya juya ya kalleta sosai ya ce ""Sai godiya, ni? Kuma ke hauka kenan""" """Kai ne mahaukaci"" furucin ya fita daga bakin Fiyya ""Kuma na yi maka nisa, kasan yadda nake da masoya" "a makarantar nan amma ni ubana ba soyayya ya kawo ni ba, karatu zan yi ina da buri mai faɗi da zan" "cimma"" Ya miƙe tsaye yana kallonta daga sama har ƙasa a ransa yana ƙissima abu ""Shi uban naki can ta" "matse masa, karatun banza kawai ka zama mai iko shine""" """Ba dai ubana sai dai "" Ya buɗe idanu sai kuma ya fasa abin da ya yi niyya ganin hawaye a idanunta" abin da bai taɓa gani ba. Da sauri ta fice daga hall ɗin ta zaga baya ta durƙushe a wajan tana fashewa da "wani irin kuka kamar zata haɗiye zuciya ""Daddy na shiga uku ina son Mutallab""" "Ƙanƙame redion ta yi tana sake fashewa da kuka jikinta har jijiiga yake ta ce ""Na shiga uku Daddy, ba zan" iya ba I can't do it ina son shi. "Kamar daga sama haka ya faɗo cikin gidan, jikinsa duk liƙe da bandeji jini na ɗiga kaɗan-kaɗan kwana" "biyu yana jinyar raunin bai san waye ya yi masa ɗinki ba. Idanunsa jajur har lokacin saboda bai gama dawowa daidai ba sai muzurai yake yi ya ja ya tsaya yana kallon murhun da aka sauke abinci akai ya juya ya kalli ɗanwaken dawar da Inna Binta ta yi ta shiga daƙi ɗakko magi ta barbaɗa ko arziƙin yaji bai samu ba, yaja kwanon da hurɗu-hurɗu yake tura ɗanwaken kafin wani lokaci ya kammala cinyewa tas ya zube a wajan ya kwanta ya rufe idanu, wata nutsuwa yake jin daya kwanta a tsakar gidan mahaifin nasa. Ya yi kamar bacci yake yana jin Inna Binta ta lailayo ashar ta ƙunduma ta ce ""Wanne ɗan abu takazar ne ya cinye mini abinci Mufee wanne mayunwacin ne mara godiyar Ubangiji"" tsit ta yi ganin Moh kwance hannunsa duk manja taja baki ta tsuke ta ɗauke kwanan tana suɗewa a zuciyarta tana jan Allah Ya isa. Har ya shiga ɗakin Ammo ta bankaɗa labule ta ce ""Wallahi abincin da ɗan ta'addar ɗanki ya cinye mini Allah Ya isa, kawai kin haifa mana jaraba ko ɗanɗana ɗanwaken ban yi bafa ya cinye"" ta dinga zagin Ammo ta uwa ta uba ta shige ɗaki tana sake suɗe kwanon da ƙyar ta samu rancen ɗari biyu ta yi cefane" da ledoji ta dafa. Tana shiga ɗaki ba jimawa ta ji an bankaɗo labule sai ta zuciyarta ta buga ganin shi tsaye hannunsa riƙe "da gora ya suke askara a gefen ƙugunsa ga gori a hannunsa, ya juya ya kalli Mufee da hannu ya yi mata alama data fita cikin sauri ta fice tana fita muryarsa a daƙushe kamar dole ya ce ""Tiger spider a yi mata aiki"" manyan karnukan suka faɗa cikin ɗakin Inna Binta ta fara ihu tana maƙale jikin sif ""Nafsi nafsi jama'a na shiga uku ya Allahu Ya Rahmanu, don Allah ka yi haƙuri Muɗallabi zan bawa Ammo haƙuri ka rufa mini asiri kar Mufee ta zama marainiyya"" Haushi kawai karnukan suke Tiger na kai mata cafka Inna" "Binta ta fashe da kuka fitsari na bin ƙafarta ta ce ""Hal'àtaka hadisul gashiya ni Binta na shiga uku""" "Moh ya ce ""Sai godiya"" gabaɗaya karnukan suka tsaya cak Inna Binta na haki ta jiƙe gabaɗaya da fitsari" "har lokacin tana maƙale jikin sif kamar ba zai magana ba ya ce ""Bani ƙudin nan"" jiki na rawa ta miƙa masa ɗari biyar ɗin hannunta ya amshe ya yi waje ta sake sif ɗin ta fashe da kuka tana faɗin ""Tsinannen yaro manta ganin yaron dake son uwarsa kamar mutuwa ba irin shi"" Moh na fita ya leƙa ɗakin Ammo ta ɗaga kai tana ganinsa ta ɗauke fuska ya yi ta kallonta ya jima tsage kafin ya sauke labulan ya juya. Yana fita wani babur na tsayawa a gabansa aka cillo masa takarda da gudu aka ja babur ɗin tare da barin" wajan. Ya ɗauki takardar ya buɗe rubutu ne bai fi layi biyu ba a hankali ya fara karantawa. _Mai dawa baka gajiya? Sau dubu zaka kula mace sau dubu zamu kashe ta. Karo na uku kenan ga misali akan matarka nan_ da jan biro akai rubutun ya juya da sauri amma tuni babur ɗin ya ɓace ɓat waye wannan? Su duka shi ne silar mutuwar su kenan? Waya ya amsa hannun wani Almajiri ya kira wata "number ana ɗaga aka ce ""Sai godiya"" Ya numfasha" """Duk inda ƴan daba suke ka haɗa mini su"" ta cikin wayar aka ce ""Mene haɗinka da daba ko dai ka fara" "shaye-shaye a state cid ɗin?"" Moh ya cije baki ya ce ""Zan fitini mutane, na ji daɗin zama can""" """To me za su yi maka?"" Wannan yaran da suka sare ni iyayensu za su ɗauki sabbin ciki yau, ƴan cikin gari" "ne a yi mini kan me uwa jawabi"" yana faɗin hakan ya kashe kiran ya goge number tas ya lumshe idanunsa ya buɗe sai kuma ya cije leɓe zuciyarsa zafi take sosai ji yake dama ya yi kuka, amma ba a haife shi don ya zubar da hawaye ba ya ɗaga idanu sama ya ce ""Da gaske ni na kashe ta amma ba zaku taɓa sani ba"" daidai lokacin mafarauta suka kawo kai suna busa ƙaho da buga gangaga suka zagaye Moh ana ""Sai Mai dawa ina uban wasu ga namu wuya a ina wuya a daji, kai ne mai Tiger kai ne mai gadon tawada"" Jikinsa ya hau ɓari da karkarwa tsumin shi ya motsa idanunsa na ƙaƙƙafewa ya yi kururuwa tare da ɗaga gora sama ya ja ya ƙame sai jikinsa dake rawa ya fara ""La'ilahaillahu, sai ni ɗan babana Malam Abdullahi ɗan malam ɗan gatan Ammo ƙanin Sa'adah ƙanin Bafullatana waye ce bani ba Muɗallabi sarki Mai dawa da jeji"" gabaɗaya suka zagaye shi suna sake zuga shi daidai lokacin kuma suka ganta kamar" daga sama..... *In sha Allah za ku ji abin da baku taɓa ji ba * 08164069385 WhatsApp only "[10/4, 9:17 PM] Nanameera: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 3 Nimcyluv Bright pens. Second batch "Da sauri ya nufe ta kamar zai kai mata cafka, ta yi saurin ja baya idanunta cikin nasa. Yana tangaɗi ya ja" "ya tsaya a gabanta tare da ƙura mata idanunsa da suke lumshewa, har yanzu jikinsa ɓari yake domin" basu daina buga ganga da ƙahon da suke busawa ba kamar masu yin gangi. "Hannunsa ya ɗaga musu cikin sauri suka daina abin da suke, cikin izza da gadara ya basu umarnin tafiya" "har lokacin idanunsa yana kanta ganin yadda take kallon shi kamar ya ta saba ganin halittarsa. ""Ban yi zaton a haka zan ganka ba, autan Ammo me ya sa?"" Ya ɗauke kansa yana haɗe fuska sosai ba wargi banda cewa ita ce ba zai taɓa tsayawa ba. Cikin raunin murya kamar za ta yi kuka ta ce ""Me za ka yi da wuƙa haka?"" Ya buɗe ido sosai sai bai magana ba, a hankali ma ya bi gefen ta zai huce ta yi saurin riƙe masa hannunsa tana faɗin ""Ni ɗin ma? Yau za a ji kan mu da kai, kar ka faɗa mini sauyin da ka yi ya" "zagayo har kai na?""" "Ya ɗago kai ya kalle ta ya kalli hannun data riƙe shi da shi, hannunta fari tas saɓanin nasa da yake mai" "kauri kuma baƙi irin na majiya ƙarfin nan wanda suke tashe akan shekarunsu. ""Don Allah ka tsaya mu yi magana, ni ko gidan ba zan shiga ba wajanka na zo"" ya cije bakinsa ya mai da kai gefe cikin muryar mai kauri ya ce ""Kin ci darajar Ɗan Amina, mene sakin?"" Ta girgiza kai kawai tana duban gefe dakalin dake wajan ta gani ta je ta zauna akai, ta yi masa alama ya zauna amma ko motsi bai yi ba, ta san cewa yana jinta amma hankalinsa na kan hanya sai waige-waige ""Mutallab ka kalle ni bafa wani zai kawo maka farmaki ba"" ta nisa idanunta cike da ƙwalla ta ce ""Don Allah kai ne ka kashe ta? Ba zargin ka nake ba Autan Ammo ni me iya rufa maka asiri ce idan ya zama kana da laifi ka faɗa mini gaskiya na maka" "alƙawarin ko Ammo ba zan faɗawa ba, ka kashe matarka ko ba kai bane?""" "Ya juya da wani irin sauri yana kallon fuskarta da take kallon shi cike da damuwa, idanunsa ya yi jajur" "naman jikinsa na motsawa ya kasa furta komai. Miƙewa Anty Hameeda ta yi tana girgiza kai kuka na cin ƙarfinta ""Ko minti ashirin ba mu yi da kai maka matarka ba, sai labarin mutuwar ta muka ji da kisan wulaƙancin da aka yi mata. Mutallab kai ne fa muka gani tsaye akan gawarta, kai ne fa riƙe da wuƙar da aka kashe ta da ita jikinka duk jinin matarka innalillahi wa'inna ilaihirraji'un na kasa yadda ka kashe ta, daman soyayyar da ka nuna mata na iya fatar baki ne?"" Wani irin ihu Anty Hameeda ta yi tana kaiwa jikin bango ganin ya ɗaga hannunsa ya yo kanta sai kuma ya tsaya cak, a hankali da baya da baya ya dinga ja yana ƙare mata kallo sai kuma ya taune bakinsa idanunsa kamar zasu zazzago don girma kallo ɗaya idan ya yi dasu sai an razana da ƙyar ya iya ware laɓɓansa biyu da sukai masa nauyi sosai ƙasan" zuciyarsa na ta fasa banda cewa Anty Hameeda ce tabbas da sai ya karya ta gida huɗu. """Ni na kashe ta, ta cancanci haka ne"" ya juya da sauri Tiger da spider da rainbow suka bi bayansa kamar" "zai tashi sama haka ya sha kwana. Zubewa Anty Hameeda ta yi a wajan tana rushewa da kukan baƙin ciki, su waye suke da saka hannu wajan lalacewar Mutallab? Ba komai ta sani ba ita ba ma'abociyar zaman garin bace ita da mijinta ta dinga kuka da ƙyar ta rarrashi kan ta, ta miƙe tsaye kamar zata shiga gidan nasu sai kuma ta fasa tana ƙoƙarin barin wajan ta ji Malam ya ce ""Hameedatu me kike anan ina mijin da yaran naki?"" Kanta a ƙasa ta ce ""Suna gida, ina yini Malam?"" Ya jujjuya yana kallon hannunta ganin babu komai ya ce ""Ba za ki shiga bane?"" Ta girgiza masa ""Zan juya wajan Mutallab na zo"" ya jinjina kai domin" ba wannan ne a gabansa ba. """Ba wata mutalla da zan iya samu a wajanki na siyo wainar rogo?"" Ta buɗe jakarta ta zaro kuɗi tana" "irgawa ya yi maza ya fisge ya ce ""Mene na lissafi? Maza jeki wajan yaranki kuma na ja kunnenki babu ke babu yaron nan idan ba su kike watarana ya ja miki masifar da za ki ƙare rayuwarki a gidan ɗan kande ba"" bata ce komai ba sai data juya zata tafi ta ce ""Duk lalacewar Mutallab kai ne ka haife shi, jininka na wanzuwa a nasa"" tana kaiwa nan ta yi gaba abinta saboda ɓacin rai da damuwa ko gabanta bata gani" sosai. Moh na kwance a saman wani dutse idanunsa a rufe tun bayan barin shi wajan Anty Hameeda ya zo "wajan ya kwanta, zuciyarsa a cunkushe take babu gurbin samun sauƙi a cikinta duk yadda ya ke son tuna waye shi me ya sa ya zama haka sai ƙwaƙwalwarsa ta yi hooking, ya ɗauki zafi sosai ta yi ta processing ya ji Ammo ɗinsa kawai yake son kasancewa da ita yanzu. Ya motsa kaɗan zazzaɓi ne sosai a jikinsa saboda saran da aka yi masa bai gama warkewa ba, baya kuma shan magani wacce zata iya kula da shi baya jin zai iya zuwa wajanta. Ya ƙanƙame jikinsa sosai abubuwa da yawa baya son tunawa sai ya cimma muradin zuciyarsa sai ya ɗauki fansa na abin da aka aika, sai ya bayyana abubuwa da dama tunda har suka bari ya shiga cikin gidan yari ya kuma yi shekaru uku a Cid ya rayuwa cikin masu aikata manyan laifuka. A sama" ya ji an kira sunansa """Mai dawa, sarki mai jeji"" bai buɗe idanunsa ba, bai kuma ɗauki murya ba haka baya buƙatar sanin waye" "don hakan babu abin da zai ƙare shi da shi. Ya nemi waje ya zauna yana furta ""Ka saɓe Mai dawa ka basar, fansa kake buƙata ba raunin zuciya ba, ka ajjiye tunanin baya ka fuskanci burinka ka zama abin da kake muradi kafin aga bayanka"" har lokacin bai buɗe idanu ba, ko inuwarsa bata motsa ba. Mangal ya ɗaga kai yana busawa samaniya hayaƙin sigari ""Idan kana son yin bacci cikin nutsuwa ka manta komai ya kamata ka sha wannan"" ya zaro abu a aljihu yana kalle-kalle sai a lokacin Mai dawa ya buɗe rinannun idanunsa ya juya ya kalli mai maganar irin kallon waye kai? Mangal ya ce ""Ka dake musulmi akul" "musulmu, zuwa na yi na taimaka maka""" """Riƙe wannan tiramol ce, ko doki ya sha sai ya gane barno gabas take kana afawa za ka ji zam-zam komai" "ya zama labari"" Mai dawa zubawa ƙwayar idanu shi bai taɓa shan ta ba, bai taɓa shaye-shaye ba ya juya ya kalli Mangal ""Da gaske zan yi bacci?"" ""Darr ne ai aikin wannan kamar yankan wuƙa ne, mai ƙirin ce da ƙyar aka bani ita ina karɓa na doƙu nan"" jikin Mai dawa na rawa ya amshi ƙwayar guda ɗaya ya cilla cikin bakinsa, yana runtse idanu ya yi shiru. Mangal ya zubawa Moh idanu a ransa yana jin wani daɗi da kuma farinciki bai taɓa yin aikin da za a bashi kuɗi masu yawan da aka ce ba irin na yau, gashi ya yi nasara Moh ya sha ƙwayar. Jikin Moh ya ɗauki rawar zafin zazzaɓi duk da irin dariyar da yake da ita, gashi duk inda ya motsa ciwon shi jini yake babu wani wanda zai iya duba lamarinsa sannu a hankali ya fara dafe kan shi da wani irin gurnani yaga sama na jujjuya masa ya ɗaga hannu da niyyar ya tare sama ya faɗo daga saman dutsen sai saka hannu yake yana tare sama a hankali kuma jikinsa ya fara saki yana jin wani shuu a tsakiyar kansa yana game jikinsa gabaɗaya zuciyarsa da tunaninsa suka dinga kissima masa kawai ya" kashe kansa ko ya cinnawa gidansu huta gabaɗaya kowa ya mutu har shi. Ganin laɓɓansa na motsawa alamar yana magana ba'a ji sosai ya saka Mangal matsawa tare da kafa "kunnensa a bakin Mai dawa cikin mawuyacin hali yake furta ""Safiyyerh... Safiyyerh...Safiyyerh"" Mangal ya maimaita sunan a fili “Safiyya?” wace haka? Ko ita ce wacce ta mutun wacce aka kashe? Ya miƙe" tsaye ya ɗauki wayarsa wata number daya haddace ya saka ya kira ana ɗagawa Mangal ya ce """Sakin nan ya kammalu, yanzu zan zo a taya na amshi fararen"" shiru ya yi yana sauraren mai maganar" "kafin ya ce ""Jira jira jira nifa cikin uwata aka haifan ba ɗan zina ba, na maka al'ƙawarin dole zan bawa Mai dawa ƙwayar kuma da sannu zai zama namu. Sai dai na ji yana kiran sunan wata ɗawa wai Safinu ko Safiya?"" Ya ƙara yin shiru ya numfasa ya kalli Moh dake kwance a wajan ya ce ""A'a Oga ni bana sabga da masu ɗan kwalin nan. Da ƙirin ka oga kanka baya kullewa a fice kake sai na doƙu yanzu"" Kashe wayar" Mangal ya yi kuma ya goge kiran cikin sauri kuma ya bar wajan. "Baya tantance halin da yake ciki, sai dai yanayin na yi masa daɗi sosai shi ba'a sama ba shi ba'a ƙasa yana" fatan ya dauwama har ƙarshen rayuwarsa. Duk da a cikin giyar maye yake bai hana shi gano fararen "kyawawan idanunta masu matuƙar ɗaukan hankali ba, a lokacin da take masa wannan duban ji yake" kamar ba zai taɓa aikata abu makamancin haka ba amma ƙuruciya da wawta ya saka komai ya wakana a lokacin da duk su biyun basu ankara ba. Gani ranar yake kamar yanzu a cikin idanunsa ya juya da ƙyar yana buɗe idanu zuwa gefe guda sai fara hango kansu su biyun a shekarun da suka huce suna tsaye tana jifansa da wani irin kallo. "Suna tsaye za su shiga practical a lokacin, ya jingina da jikin bango ƙafarsa ɗaya a jikin bangon ɗaya a" "ƙasa ya harɗe hannayensa duka biyun a ƙirji students ɗin yake kallo yana mamakin abin da ya saka ƴan mata ke burge wasu mazan, as a man kuma good man kawai ka nemi kuɗi ka yi arziƙi ka shahara a duniya shi ya fi, ka zama mai iƙo da faɗa a ji, ka zama wanda zai iya samun abincin da zai ci da safe kuma ya ci da rana ya ci kuma da dare ya bawa ƴan'uwasa da duk mai jin yunwa ya zamana kuma ka kasance mutumin da ake shakka duniya ta san da zamansa bawai kana namiji ka ƙare a wajan wata yarinya ba." Yana cikin wannan tunanin ya ji an ja mugun tsaki ya buɗe idanu ya ganta sosai ya buɗe idanunsa da suke a rufe kodayaushe cike da gashin idanu masu tsayi. """Kai ai babu macen da zata soka a school ɗin nan, sai dai kaga ana soyayya"" bai taɓa tsayawa ya tanka ta" "ba sai lokacin har zai mata shiru sai ya ce ""Ok"" ta haɗe fuska ""Saboda macen abinci ce ko iskar shaƙa daya zama dole Mutallab ya amfana dasu?"" Ta yi masa sheƙeƙe tana nuna masa ɗaliban makarantar da kana ganinsu zaka san iyayensu nada arziƙi sosai kowanne a students ƙuruciya da tashen balaga na ɗawainiyya da su. Ta ce ""Mata ai sune jin daɗin maza, kai fa mace ko kiss bata taɓa yi maka ba a school ɗin nan"" Mutallab ya yi ta kallonta daga sama har ƙasa ""Matar Moh zata zama mai irin halin MOH"" har ya juya sai yaga bata ci bulus ba ya tako har inda take ya zuba idanunsa cikin nata kamar yadda take kallon tsakiyar nasa idanun yana sake matso da fuskarta ""About the kiss, ƙilan Moh ya ji ƙan ki ya yi miki" "don naga shi kike buƙata""" Tsoro ya kamata amma ta dake ta fara ja baya ya yi saurin saka ƙata ya falleta kamar zata kita ya saka "hannu ya cafko gaban wandon uniform ɗinta ya dawo da ita dab dashi yana sauke mata numfashi a hankali kuma ya ɗora fuskarsa. ""Mai dawa"" kiran da aka yi masa ya saka bidiyon abin da ya faru a baya" "saurin gogewa a idanunsa har lokacin idanunsa na kafe waje guda sosai yake son sake tuna abin da ya faru a lokacin ya gagara. Goje ya ce ""Nan ka auno kenan, na samo sha ɗayan gayen nan. Ya naga kamar a buge kake?"" Goje ya faɗa yana tattaɓa jikin Moh ya ji zafi sosai idanunsa kuma ya kaɗa ya yi ja ya san babu abin da zai fahimta koda ya yi masa bayani ""Mene haɗin mafarauci da shaye-shaye?"" Shi dai ya yi shiru kawai zumbur kuma ya miƙe tsaye kamar wanda ya tuna wani abu ya juya idanu wuƙar da ya gani a jikin Goge ya fusga duk yadda Goje ya yi da shi amma ya kasa amsar wuƙar cikin sauri kuma ya mara" masa domin ganin me zai aikata? Tafiya suka dinga yi har suka kawo titi ya tsayar da mai napep ya faɗa shima Goje ya faɗa ciki. Shi kansa "bai san ina za a kaisa ba. Tafiya suka sosai har suka ƙarasu daidai wajan wani ƙaton kamfani wanda kaf Kano babu wanda bai san zaman wannan kamfanin ba. Iya haɗuwa ya haɗu ginin kamfanin ma abin sha'awa ne ga masu tsaro ta ko'ina. Ya tsayar da mai napep ɗin ya sauka ""Kuɗi na?"" Ya buɗe ido sai ya" "share ""Malam haƙƙina na daƙƙoka daka waje mai nisa ina da wajan zuwa"" Goje ya ce ""An cinye""" """Kut, ni da haƙƙina daman tunda na daƙƙo ku na ji kuna warin wiwi na san cewa ɓarayi ne ku, cikakken" "ɗan zamani ne nima ku bani kuɗina yanzu ku na daki kuɗin"" Goje ya ce ""dan babarka zo ka daka idan ka haifu"" mai napep ɗin ya share shi, ganin Mai dawa ya yi shiru yana kallo kamfanin ya nufi inda yake ya damƙi wuyansa ya ce ""Kai ka tsare ni ai ,"" kafin ya ƙarasa maganar Mai dawa ya damƙi hannunsa ya" "matse ya bada sauti ƙass har lokacin ya kafe kamfanin da idanu. Mai napep ɗin na ihu yana neman ɗauki Goje ya zaro wuƙa yana bubbuɗe jajayen idanu hakan ya saka ba wanda ya zo wajan kowa saurin barin hanyar yake gudun kar tsautsayi ya faɗa masa. Mai dawa ya saki karyayyen hannun mai napep ɗin ya ƙara damƙar ɗayan zuciyarsa na tafasa har yanzu ba komai yake ganewa ba, ya sake karya hannun" daman ba tare daya sake shi ba ya ce """Goje""" """Mai dawa sarki mai jeji, sai godiya""" """Kamfanin meye wannan? Na waye kuma?"" Goje ya kalli tafkeken kamfanin da manyan motoci ke ya" "shiga da fita kafin ya ce ""Sai godiya, ciki ne a kan sabgar nan bani da ilimi akan wannan massarafar""" Mai dawa ya saki mai napep ɗin da ya karya masa duka hannunsa biyu yana ja da baya a hankali ya ce """Ina son shi, ina son ya zama mallakina"" cikin sauri Goje ya ce ""Me kake so?""" """Kamfanin""" "Tana zaune akan kujerar dake haɗɗan office ɗin, cikin nutsuwa dake danna system ɗin gabanta files da" yawa cike saman table ɗin hankalinta na kan aiki sosai kana kallon fuskarta zaka san serious ce ita akan aikinta bata da wasa ko kaɗan. Brown suit ce a jikinta mai riga da wando ta yi rolling kanta da mayafi zagayayyiyar fuskar ta fito sosai ta saka wani shade a idanunta baƙi. Wayarta ta fara ƙara alamar kiran ta "san tunda ya fara ba zai daina ba, cikin nutsuwa ta murja kujerar ta yi ba, suu kuma ta kujerar zuwa inda wayar take ta ɗaga kiran tana sawa a hands free" """My manager"" ta ɗan buɗe idanu ta cikin glasses ɗin ta yi shiru tana ta danna system a hankali ya ce" """Maamah"" ya kira ta kamar yadda suka ce mata ta sake yin shiru domin bama ta jinsa sosai ""Fiyya ina miki magana?""" """Yaya J yaushe zaka fara ɗaukan aikinka very serious, ina kan aiki fa"" ya yi murmushi mai kyau tana jin" "sautin shi a kunnenta ""Sanda kika so na zama Mamaa""" """Uhm kiran fa?""" """Kin ci abinci, nina manta Captain ya saka na kira na tambaye ki"" cak Fiyya ta tsaya da abin da take ko dai" "bata ji daidai ba ""what?"" Ya ce ""Kin ji ai"" a taƙaice ta ce ""Na ci"" ya ce ""Good, ƙarfe nawa za ki tashi?""" """Ina da meeting Yaya J ka biyo ka ɗauke ni i can't drive cikina ciwo"" cikin sauri ya ce ""Subuhanallahi! Bari" "na zo na duba ki ko kawai mu tafi gida"" kashe wayar ta yi domin ba wani ciwon ciki da take so take ta saka kanta busy sosai ko zata manta da wasu abubuwan. Knocking aka fara tana ji ta yi shiru can ta ce ""In"" ya buɗe ya shigo idanunsa ya sauka a jikin sunanta dake manne a table ɗin “SAFIYYERH A. MARAFA”" "ya ɗauke idanunsa yana rusunawa ya ce ""Good day Maa""" "Da hannu ta yi masa nuni ya zauna bayan ya zauna, still idanunta akan system tana danna keyboard ta" "miƙo masa file ya ɗauka ya ce ""Wannan fa?"" A nutse ta ce ""I have to ask, daga ina file ɗin nan? Wanne kaya aka fitar aka samu ruɓanyar kuɗi kashi wajan goma cikin awa guda Accounter?"" Ya ɗan shafa kai ya" "ce ""Maa ni ma haka na gani, kawai aka ce na kawo ki saka hannu""" """To ba zan ba"" ta ce a taƙaice. ""Maa ya zama dole fa""" A hankali ta ɗago idanunta sai kuma ta cire glasses ɗin idanunta manyan fararen idanunta tas a kan shi "ya yi saurin ɗauke nasa idanun saboda kwarjin da ta yi masa ""Ni ce Manager, ka faɗawa duk wanda ya" "turo ka cewa ba zan ba, ina buƙatar explanation me aka siyar a kamfanina nan har aka samu shigowar" "kuɗi kimanin 5.1B cikin awa guda, ba details na abin da aka siya sai file na zuwan kuɗin kuma yanzu ana buƙatar fitar dasu daka account ɗin kamfani? This is complicated"" zai yi magana cikin tsawa ta ce ""Out of my office accouter"" cikin saurin ya miƙe tsaye yana ficewa daga officer ɗin. Numfashi Fiyya ta sauke ta rufe idanunta da sauri kuma ta buɗe jin an shigo ba tare data bada umarnin a shigo mata officer ba." Cikin sauri ta miƙe tsaye tana ɗan ja baya ta shiga ƙare masa kallo daga sama har ƙasa ta yi mamaki to babu security a ƙofar office ɗin nata ne? Da ƙyar ta ja numfashi tana saukewa ta ce. """Who are you? Waye kai." For more information 08164069385 "WhatsApp only.[10/6, 9:07 AM] Nanameera: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 4 Nimcyluv *Bright pens. Second batch* Ƙarewa office ɗin kallo ya yi yana buɗe idanunsa akan Fiyya wacce ta ɗan ja da baya tana ɗauke kanta "gefe. ""Ya Allah i really missed her, Safiyya A. Marafa"" ya furta yana kallon makaken photon Fiyya dake cikin office ɗin kafin ya ƙarasa ciki murya a hankali ya ce" """Wa kike tunanin zai zo banda mijinki Fiyya? You're enjoying teasing me"" sai a lokacin ta sauke ajjiyar" "zuciya a ɓoye tare da ɗan yin murmushi mai kyau wanda ya saka shi lumshe idanunsa ya buɗe ""Like this. I missed you completely Fiyya ba shiri na dawo gida fa""" """Ina yini ya hanya?"" Ashraf na kallon files ɗin gabanta ya ce ""Allahamdulilah. Ya naki aikin Manager?"" Ta" "ce ""Lafiya, me ka zo yi a kamfanin ko kana da business damu ne?""" """Eh, babban business ma"" tana kallon system ba yabo babu fallasa ta ce ""Ohh"" kallon ta ya dinga yi" "yadda take operating system ɗin cike da nutsuwa fuskarta a kame ba wargi hakan bai hana kyan fuskarta bayyana ba ya ja numfashi ya sauke yana jin wani abu sosai na fuskarsa a kan Fiyya ya kalli agogon hannunsa ya ce ""Ko gida ban je ba, ina son na samu nutsuwa da kallon fuskarki dear"" kamar baza ta ce komai ba sai kuma ta ce ""Ok"" mamakin halinta na ko ina kula yana damunsa cikin damuwa yana sassauta" "murya ya ce ""Fiyya"" ta ɗago ta kalle shi sai kuma ta zame idanunta." """Na kasa fahimtar me kike nufi dani Fiyya anya kina so na kamar yadda nima nake son ki? I told you na" "dawo saboda ke amma ki ce mini wani ok? To hell with the ok ɗin na tsani irin wannan ɗabi'un naki, da na yi miki uzurin rashin sabo ne amma for good 5years muna abu ɗaya dake? Idan customers ne kya musu fara'a ki yi welcoming nasu, amma ni da zan zama mijinki kwana kwana nan kike ma haka, ko wanne gardi ya zo office naki kin zama wata kamar jerry abar kallon kowa"" ya girgiza kai cikin damuwa" da ƙunci yana zare gilas ɗin idanunsa tare da buga table ɗin gabanta ya ce """A cikin abu biyu dole ne a yi guda""" Kallon Ashraf kawai take ta tabbatar yana da anger issues tama rasa me za ta ce masa don takaici ya zo "har office ɗin ta kuma yana yi mata hayaniya, yana ƙoƙarin tara mata jama'a. Ko motsi ba ta yi ba, tana" "juya kujerar da take kai a hankali idanunta zube a kansa. ""Ina ji Ashraf"" bata taɓa kiran sunansa ba sai" yau hakan ya saka ya kalleta da sauri ransa ya ƙara ɓaci. """Aure ko aiki, ya zama dole ki zaɓi guda ɗaya a ciki""" """Ok"" ta sake cewa tana miƙewa tsaye tare da ɗaukar jakarta da wayarta da makullin mota ta zaga a" hankali zata shige shi ya yi saurin saka hannu ya riƙo nata hannun cikin sauri ta kalle shi tare da jefa masa wata iriyar harara sakinta ya yi ya matsa dab da ita yana sauke mata hucin numfashin ɓacin ransa dake fitowa tun daga ƙasan zuciyarsa. """Ki bani amsar abin da na buƙata kafin ki fita, aikin ki ko aure""" Ta taune leɓenta tana ware masa manyan idanunta sai kuma ta kalli wayarta tare da buɗewa ta shiga "wajan photos pictures ɗinsa ta nemo wanda ya yi kyau sosai ya saka ƙananun kaya lokacin bashi da lafiya ta je duba shi ya fito harabar gidan tana murmushi ta ce ""My patient, bari na ɗauki photo as evidence karka mutu bani photon nunawa yarana masoyin da ya tafi ya bar Fiyya"" a lokacin juyawa ya yi ya kalleta daga kwancan da yake ya wurga mata harara sai kuma ya miƙe tsaye yana nufar inda take ta yi saurin yin" baya tana masa wani irin murmushi ya tsaya yana kallon ta sai kuma ya ce """To make you clear, ba ki da wasu yara sai na Ashraf, ba ki da wani miji sai Ashraf ba wanda za ki yi wa" "takaba sai Ashraf. Ashraf na Fiyya ne Fiyya kuma ta Ashraf ce in sha Allah"" murmushi kawai ta yi bata" ce komai ba ta ɗauke shi photon yana langwaɓe kai gefe. Fiyya ta shafa screen ɗin wayarta tana kallon photon kamar yanzu ta ɗauka cikin muryar mara hayaniya "idan tasu ta ce ""Ya ce wai na zaɓa aiki ko shi, kar ya buƙaci jin amsar daga bakin Fiyya"" fisge wayar ya yi ""Dole ki bani amsa yanzu ba sai anjima ba"" ta gyara tsaiwa tana fuskantar shi da kyau a hankali ta matsa dab da shi ta ce ""Allah Ya baka wacce ta fi Fiyya"" Ashraf ya yi sak can ya ce ""Me kike nufi?""" """Ina nufin na haƙura da auren, na zaɓi aikin"" tana kaiwa nan ta fisge wayarta cikin sauri ta yi waje ya bita" "da kallo zuciyarsa na ta fasa. Tana fita ta kalli security ta ce ""Idan ya fito a rufe mini office"" waje ta yi ko Elevator bata tsaya shiga ba ta sakko ta bene dake a wajan 5 floor office ɗin nata yake. Sai gaisheta ake yi amma ba wanda ta saurara idanunta har dishi-dishi yake saboda ɓacin rai." Misalin 1:43 dare ya nutsa ana samawa zuciya nutsuwa ya yinda kowa yake bacci a lokacin ne safiyarsa "ta waye. Ya tsaya a ƙofar gidan yana kallon gate sosai ya jima a wajan kafin ya juya ya kalli Goge da Darma cikin hanzari Goje ya shiga buga gate ɗin gidan kamar zai cire shi, sun jima kafin daga bakin ƙofar suji an ce ""Waye?"" ""Buɗe"" Goje ya ce yana zare wuƙa tare da matsawa jikin ƙofar mai gadin a ruɗe yake" "sosai ya ce ""Kamarya na buɗe a wannan zamanin da muke cikin insecurity na sani ma ko ƴan fashi ne?""" """Sune"" Darma ya ce yana yin muzurai shi kaɗai ne a cikin su yake a buge shi Moh abin da Mangal ya" "bashi har yanzu bai gama sakin shi ba, shi ya sa ba komai yake ganewa ba. ""Wallahi ba zan buɗe ba, babu mamaki kun ji Alhaji Wada ya dawo gari shine za ku yi masa fashi""" """Ko ka buɗe gidan nan na rantse da Ɗan Amina na shigo sai na yi maka ɓalli-ɓalli"" ai kowa mai gadin ya" "ce ""Ka yi mini ɗari-ɗari ma amma babu abin da zai saka na buɗe daman ƙasa babu lafiya ga yaron can daya dawo abin tsoro ana ta surutu a unguwa ya kashe matarsa kuma ya shigo cikin al'umma zai lalata jama'a..."" Kafin ya ƙarasa faɗa Moh ya saka ƙafa ya daki ƙaramar ƙofar nan take ta ɓalle ya faɗa cikin gidan, da sauri mai gadi ya ja baya ba wani sanin Moh ya yi ba kawai zancen ya dawo kunnensa da labarin kisan daya game ko'ina a shekaru uku da suka shige. Goje ya daƙo mai gadin ya falle shi ya faɗi" """Kai har ana cewa ka buɗe ƙofa kana ƙi?""" """Goje""" """Sai godiya"" Moh ya numfasa yana durƙosawa daidai fuskar mai gadin ""Me ya ce a yi masa?"" ""Sai godiya" "ɗari-ɗari ya ce yana buƙatar tsini"" ihu mai gadin ya saka ya ce ""Wallahi tallahi ƙarya nake""" """Zaɓi ɗaya"" cewar Moh yana fito da askira ya ajjiye gefe ya sake fito da wata wuƙar ya ajjiye ya jima a" "duƙe kamar mai tunani sai ya ce ""Ko ɓalli-ɓalli ko ƴan uku ko na jaki""" """Ɓalli-ɓalli"" mai gadin ya ce da sauri ya ɗauka wani abun za a ɓalle da idanu ya kalli Goje da Darma suka" "riƙe mai gadin tare da juya shi yana ihu da komai Moh ya ɗauki ankarar ya dinga tsaga masa a baya jini na fitowa shi kansa zuciyarsa ce kawai ke ingiza shi ya yi hakan kuma daidai gani yake yanzu daidai yake da tsarar kowanne mutum haka ƙwaƙwalwarsa ke karantar da zuciyarsa. Tun mai gadin na kuka har ya yi laƙwas sai nishi yake fitarwa, suka yar da shi a wajan cike da tafiyar taƙama yana taku ɗaiɗai jikinsa na buɗewa cikakken namiji a tsaye matashi dake kan lokacinsa. Cikin sa'a ya samu ƙofar shiga babban parlon gidan a buɗe ya kutsa kai yana kallon tangamemen parlon ya dinga kallon komai, iya haɗuwa ya haɗu sai ƙarar a.c ya lumshe idanunsa ya buɗe ya jima kafin ya ƙara shiga cikin ɗaya parlon su Goje na" biye dashi. Alhaji Wada na zaune shi da iyalansa basu da jima da sauka daga ƙasar ba. Yana saman kujera matarsa "na gefe sai yaransa guda biyu mace da namiji kayan ciye-ciye fal a gabansu bama su damu da cin abincin ba sai ice-cream dake hannunsu suna sha. Da sauri Alhaji Wada ya miƙe tsaye yana kallon matasan da suka shigo ya juya ya kalli matarsa da yaran ya ce ""Su waye ku? Me kuka zo yi mini a gidana a irin" "wannan lokacin?""" Moh bai ce komai ya zaga ya zauna saman kujera ya jingina ya ɗora ƙafarsa a saman table ɗin yana kallon abincin Goje da Darma na tsaye sai muzurai suke yi cikin sauri Alhaji Wada ya ɗauki wayarsa zai "kira ƴan'sanda ""Ba wani abu da zai bani tsoro, yadda aka fara dakai dole a ƙare da kai Alhaji Wada""" """Waye kai? Me aka fara dani"" fuskar Moh a rufe ya saka hannu ya zame abin da ya rufe fuskar da shi" """Idan maye ya ci ya manta ai uwa ba zata manta ba, idan kare na yawo zabo na yawo za a haɗe ya ranar""" "ƙirjin Alhaji Wada ya buga ya yi baya da sauri ya ce ""Kai ne? Me na yi maka""" """Ba labari na zo baka ba, ba fansa na zo ɗauka ba na zo ka ganni kasan ina raye ina numfashi ka san cewa" "na cika ɗan babata Ammo Mai dawa nake sarki mai jeji, na gode Ɗan Amina da ka zama kai ne silar da ya saka na gano wasu abubuwan"" Alhaji Wada jikinsa rawa kawai yake ya ce ""Don Allah kar ka yi mini komai kar ka taɓa yarana basu san abin da ya faru ba"" ""Idan zan yi mana jira, idan na yi sai ta ɓaci. Ina je store ɗin gidan nan?"" Da hannu Alhaji Wada ya nuna masa hanya ita kam matar ta kasa motsi saboda tashin hankali bata taɓa ganin fuska mai ban tsoro irin wannan ba, yaran sai takurewa waje guda suke yi ko haɗa idanu da Moh basa son yi"" ganin har lokacin Moh bai tashi ba ya saka Alhaji Wada cewa ""kar ka ce zaka mini komai"" shi dai Moh kallon Alhaji Wada kawai yake zuciyarsa na tuna masa irin zaluncin da ya yi masa da hannu ya nuna masa yaran cikin kakkausar murya ya ce ""Ko dan waɗan nan, ba zan so su zama abin da na zama ba"" ya juya ya kalli Goje ya yi masa fito da inkiya suka nufi store ɗin kayan abinci kamar hauka haka suka dinga fito da buhun shinkafa katon na taliya da maroni su magi da galan na mai suka" jide waje guda. "Yana bada faɗi ya miƙe tsaye ya nuna kayan abincin ""Ka raba a masallaci ka haɗawa mutane da haushin" "kare guda goma-goma, ka kai har gidanmu"" Ya juya zai fita sai ya tsaya ya saka hannu a aljihu ya zaro kunama ƙatuwa baƙa ƙirin da ita ta ɗaga ƙari sama ya damƙi hannun Alhaji Wada ba tare da yaran sun gani ba, ya cilla kunamar ciki ya damƙe hannun. Azaɓa ta saka Alhaji Wada zubar da hawaye zufa na yanko masa sosai da sosai a hankali cikin ƙasa da murya ya ce ""Ka kira cinnaku ƴan'sanda kenan ka faɗa musu an yi maka fashi, idan sun tambayi waye karka yadda ka ce Mai dawa, ka ce SCORPIO"" yana kaiwa" "nan ya kashe kunamar ya soke jikin bango da sauri ya fice kamar walƙiya, su Goje suka mara masa baya." "Fiyya na durƙushe a gabansa kanta a ƙasa ji take dama tana da ƙarfin yin kuka a yanzu, ta kasa fahimtar" sai yaushe ne komai zai daidaita ya tafi daidai? Tana haɗiye abubuwa da dama ba tare da kowa ya sani ba bata bari a san rauninta amma yau ita aka saka gaba akan abin da sam bai kai ya kawo ba? Ita zaiwa haka?. """Safiyyerh A. Marafa""" Ya kira sunanta a karo na uku sai a lokacin ta ɗago kai ta kalli Daddy dake zaune saman kujera hannunsa riƙe da carɓi fuska ba wasa ya lura sai ya dage sosai akan Safiyyerh. """Ya kuka yi da Ashraf me neman auren ki?"" A hankali ta ce ""Ba komai Daddy""" """Ba komai Daddy, na gaji da jin wannan daga bakin ki Safiyyerh ke kina nuna mini ke mai wayo ce kuma" "kin girma kin isa ki yi handling dukkan wasu matsalolinki ko? Ke jaruma mai experience akan aikinta Managern FS WORLD INVESTMENT COMPANY? na yarda kina da wayo tunda na kasa sanin damuwarki tsayin shekaru na yarda kina da experience hakan ya sa cikin ƙaramin lokaci kika zama Manager but amma.."" ya yi shiru yana kallon ta sai kuma ya ce" """Safiyyerh kina buƙatar aure shine cika da ƙimar kowacce mace, me kike buƙata a rayuwa da ba a yi miki" "ba, wanne gata ban yi miki ba da kika ce kin fasa auren Ashraf?""" """Daddy ya ce na zaɓi aiki ko aure""" """Sai kika zaɓi me?""" """Aiki"" Daddy ya dinga kallon ƴar tasa shi ya rasa gane wani mataki zai ɗauka a kanta." """Ba za ki yi auren ba kenan, baƙin cikin jikoki kike mimi Maama? Sai na faɗi na mutu za ki yi auren me ya" "sa kika kasance stubborn ne, ko don kinga ina biye miki?"" Fashewa ta yi da kuka sosai ita kanta bata san" "kukan ya ƙwace ba, kalmar mutuwar da Daddy ya faɗa ya firgitar da ita sosai idan Daddy ya mutu ta shiga uku." """Daddy gasu Yaya J, su Marafa, su Captain Daddy me ya sa sai ni za a yi aure ne? Ni ce ƙarama fa nawa" nake gabaɗaya ko aure za ka mini ka ƙara mini lokaci Ashraf zafin zuciya ne dashi baya fahimta ta a "kodayaushe""" """Maama kuma taurin kai, ji da kai while zafin zuciya, Safiyyerh dole za ki yi aure"" runtse idanunta sosai" kenan duk abin da take ya tashi a banza? Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un me ya sa Ashraf zai yi mata haka me ya sa zai haɗata da mahaifinta? Ta kasa cigaba da kukan abu ya tsaya mata a wuya sosai. Har Daddy ya je bakin ƙofar shiga sashinsa ya tsaya ba tare daya juya ba ya ce """Cikin satin nan zan ɗaura miki aure da Ashraf in sha Allah""" "Dum! Haka ta ji zuciyarta ta buga da ƙarfi har tsakiyar kanta kuma ta ji hakan, ta runtse idanunta sosai" "take ƙoƙarin jan numfashi ta kasa ta yi saurin riƙe wuyanta da take jin kamar an soka mata abu a ciki saboda zafin da yake. Cikin sauri J ya ƙarasu parlon daman ya shigo da nufin yiwa Daddy sai da safe ya nufeta yana riƙo hannunta ya ce ""Manager lafiya? Mene?"" Kafin ta bashi amsa Marafa shima ya shigo ya nufe ta, haka Dr Hash gabaɗaya suka zagaye ta suna tambayarta lafiya kasancewar suna mugun son ƙanwar tasu kamar rai. Hannun J ta riƙe gam tana nishi hawaye na zubu mata sosai ta kasa magana hakan ya saka Dr Hash miƙewa ya ɗakko ruwa mai sanyi ya yiwa J alamar ya ɗago ta, a hankali ya dinga" bata ruwan tana sha ya zame rubar ruwan. """Junaid kwantar da ita saman kujera ko ka kai ta ɗaki""" """Bari ta ƙara jin dama dama a dai ƙaro gudun acn ta fi shaƙar iska da kyau"" cikin sauri Marafa ya nufi" wajan ƙaro a.c a hankali suka ji an ce """Kar ka ƙaro"" ya juya ya kalli Captain dake zaune kan kujera abin shi yana dannawa, yana zaune Daddy" "ya kira Fiyya duk maganganun da sukai yana zaune har halin data shiga. ""Captain daman kana ciki kana kallo Maama ba lafiya?""" """Ni na ɗora mata?""" """Amma baka ce mata sannu ba, she's our little sis our favourite"" kallon da Captain ya yi wa Marafa ya" "saka dole ya yi shiru dukkan su ba wanda ya iya cewa Captain komai domin sun san hali basa shiri da Fiyya bai shiga sabgarta ba, duk abin da ya shafe ta babu ruwansa da shi. Ko magana bai fiya yi ba ana" ganinsa kowa ke nutsuwa domin shine babba a cikin su Fiyya kuma Auta. Fiyya ta yi lamo jikin J tana sauke numfashi Dr Hash na riƙe da hannunta jin jikinta ya fara ɗaukan zafi sosai. Da ƙyar ta lallaɓa J na riƙe da ita suka haura sama duka sauran mazan suka bi bayansu banda Captain da yake harkar gabansa. Wajejen 2:30 Daddy ya sauke numfashi yana kallon yadda take sauke numfashi a hankali ko a baccin "bata da walwala ya juya ya kalli Captain dake tsaye hannunsa zube cikin aljihu ""Aliyu me na ragi Maama da shi a duniya dana kasa fahimtar meke damunta? Ita ɗaya ce mace ƴata laifi ne don na so ta yi aure?""" Captain dai ya yi shiru idanunsa a saman fuskar Fiyya Daddy ya miƙa hannu ya taɓa goshinta ya ji har "lokacin da zafi daman ya fi ƙarfin awa guda zaune a wajan, yana cikin Captain ya buɗe ƙofa ya shigo da" "tunanin babu kowa cikin ganin Daddy ya saka dole ya tsaya. ""Maama ki yi mini alfama ki yi auren nan, shi" "ne abin da za ki yi ki faranta rai na"" ya gyara mata hannunta daya lanƙwashe kana ya miƙe tsaye zai fita" """Aliyu mu je""" """After you daddy""" Daddy ya jinjina kai ya fita yana janyo ƙofar. A hankali Captain ya nemi waje ya zauna a gefen gadon ya "zuba mata idanu sosai, a nutse a kamo hannunta ya riƙe cikin nasa jin jikinta zafi sosai ya saka ya saki hannun ya ɗakko towel da ruwa ya dinga goga mata a goshi har lokacin yana riƙe da hannunta har sai da zafin ya ragu, bai tashi ba yana zaune aka fara kiran sallar farko cikin sauri saki hannunta ya miƙe tsaye yana haɗe fuska J ne ya shigo a hankali ya bi Captain da idanu har ya fice daga cikin bedroom ɗin na" Fiyya. ***** Cikin gidan ya faɗo babu ko sallama Inna Binta na zaune har za ta yi magana ganinsa tsaye ya saka ta yi shiru da bakinta. Yau ranta fari tas an yi musu rabon abinci Malam ya basu ya ɓoye sauran. Ɗakin Ammo ya nufa yana ɗaga labulan ɗakin ya ganta zaune tana ɗaura kuɓewa tun kan ya shigo jikinta ya bata yana hanya saboda gabanta daya tsananta faɗuwa. "Ya shiga ɗakin ya zauna ita dai bata kalle shi ba, sai kallon ta ya ke yi can ƙasa da murya kamar ba shi ba" "ya ce ""Ina yini Ammo?""" "Miƙewa ta yi maimakon ta amsa masa, ya cije bakinsa yana rufe idanu kwanon abinci ya jenyo ya buɗe" yaga taliya ce jallof ta ji albasa nan da nan yawunsa ya tsinke ya tuna rabon shi da abinci har ya manta. """Alhaji Wada ya bawa Malam, idan da zuciya ai ba za ka ci abincin daya bamu ba"" cak ya tsaya yana" "kallon abincin kamar zai tashi sai kuma ya nutsa hannunsa ciki ya ɗebo lauma zai kai bakinsa cikin sauri aka ce ""Allah Ya isa ban baka ba ida ka ci abincin nan"" Malam ya kalli Ammo ya ce" """Bana ce kar ki yarda ya shigo gidan nan ba? Wato har abinci kika bashi ko?"" Ta girgiza kai ta ce ""Ɗauka" "ya yi""" Jiki a sanyaye Moh ya miƙe ya fice daga cikin ɗakin yana saka ƙafa ya banko ƙofar da ƙarfin gaske yana "zuwa daidai inda Inna Binta ke gyara shinkafa ya saka ƙafa ya yi fatali da farantin shinkafar ta tarwatse ya yi waje kamar zai tashi sama. Ta dafe ƙirji tana rafka salati ""Ƴar gwamnati ce fa Allah ya isa wallahi""." "Goje ya dubu Mangal ya ce ""Me ka bashi wai? Yake wannan sambatu da mimmiƙar haka?""" """Sha fara kaga aljan ce, ita za ta yi aiki a jikinsa, daga sama aka bani ita"" Goje ya juya ya kalli Mai dawa" "ya sauke numfashi cikin damuwa ya ce ""Dole sai ka koya masa shan waɗannan abubuwan ne?""" """A'a ina zaune ya zo mini kamar an koro shi yana huci ya ce na bashi irin abin da na bashi kwanaki" "saboda damuwar zuciyarsa ta kau ya manta da komai ni kuma na bashi sha fara kaga aljan""" """To gashi nan yana ganin aljanin ai"" da ƙyar ya samu ya yi bacci a wajan. Bayan ya farka Mangal ya bashi" "abinci ya girgiza kai ""Mai dawa idan kuɗi kake so ina da hanyar da zan yi maka ka dinga samun kuɗi sosai cikin sauƙi har ma ka taimaki wasu"" tunda ya farka sai lokacin ya ɗaga kai ya kalli Mangal alamar ina ne? ""Bangar siyasa kasan yanzu muna gab da fara shiga sabgogin siyasa uban gidana cikakken ɗan siyasa ne," "shima yana da uban gida kuɗi zaka samu sosai a sabgar nan ina faɗa maka""" """Kai ni"" kawai ya iya cewa yana miƙewa tsaye." Suna zaune a wani haɗaɗɗan parlo inda suke karɓe wa su yi meeting na sirri. Gabaɗaya suka kalli MUTALLAB TAHHB SCORPIO ɗaya daga cikin su ne ya ce. """Mene sunanka""" """Mai dawa""" """Kai mafarauci ne?"" Ba tare daya kalli mutumin ba ya ce ""Darr"" babban mutumin ya jinjina kai sosai ya" "zaro wani photo a aljihu ya ce ""Kafin mu yi maka bayanin su waye mu, me muke buƙata da kai, fara ganin wannan ka saka dai a ranka mu ƴan siyasa ne""" "Shi dai Mai dawa bai ce komai ba, aka ajjiye masa photon a gabansa ""Ɗauki ka buɗe ka gani mana""" "Wani daga cikin mutanen ya ce ""Manager ce a FS WORLD INVESTMENT COMPANY aiki za ka yi mana a" "kanta kafin mu faɗa maka aikin mene ka fara ɗaukan photon kaga wacece"" a sanyaye ya ɗauki photon kafin ya kai idanunsa kai...." 08164069385 For more information WhatsApp only "[10/8, 7:59 AM] null: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 5 """Safiyyerh Abdu Marafa Manager ce a Kamfanin FS WORLD INVESTMENT COMPANY kuma ƴa a wajan" "tsohon leccara, muna buƙatar ka yi mana kidnaping ɗin ta"" Moh Kallo ɗaya ya yi wa photon da suka bashi ya ɗauke kai" """Ka santa?"" Shi dai bai ce komai ba." "Eng Ali wali ya dinga kallon Moh yana tunanin abubuwa da yawa a ransa kafin ya ce ""baka gama ganin" "photon bane, ko da yake yana da kyau da ƙare mata kallo maybe ka zama silar mutuwar ta ko ka kashe" "ta da hannunka, ka ya zama dole ka gane kamamminta""" "Goje ne ya ɗago kai da sauri yana kallon Eng Ali wali kafin ""Sai da kai mai gida wannan aikin ai ko ni zan" "iya yin shi ba sai Mai dawa ba, ka huta ka sarara mai gida""" Eng Ali wali ya yi murmushi yana jingina da kujera ya ɗauki ƙafarsa ya ɗora akan ɗaya ya kalli Mai dawa "wanda ko motsi bai yi ba sai jujjuya photon da aka bashi yake. ""Ko Mangal ba zai iya aikin nan ba da ya fika wayo a sabgar balle kai da na sani yanzu, shi wannan Mai dawan idanunsa na kalla na san zuciyarsa za ta iya aikata komai""" "Ya yi shiru sai kuma ya ce ""Ni ɗan siyasa ne babu mamaki ka taɓa ganin poster na ko bana, shekaruna" "takwas ina riƙe muƙamin Ɗan majalisa na tarayya a jam'iyyar da nake ta kara, bani da ra'ayin haƙura da kujerata kamar yadda ake yi mini kirarin idan na yi na gama na karya kujerar. Siyasa jinina ce Mai dawa, bana jin akwai wani dalili da zai zo ya saka na haƙura da kujerar na amma wannan karon na yi karo da muruci wanda yake shirin yi mini wahalar dafawa ko ta halin yaya ne dole na sake hawa kujerar nan a karo na huɗu. Hon Maɗatai yana tare da manya wanda suka san kan siyasa ciki da bai dole mu fito da salo na musamman wanda zai kai su ƙasa. Hon Maɗatai shine ɗan takarar jam'iyyar hamayya kuma yana da ƙarfi har yanzu ba'a san mene rauni ko aibun shi ba amma akwai jita-jitar data zo kunne na domin" "tabbatar da gaskiyar al'amari ya saka na kawowa cikin jama'ata""" Sai a lokacin Mai dawa ya ɗago kansa ya ɗan kalli Eng Ali wali kamar ba zai ce komai ba sai ya cije baki yana karkatar da kai gefe ya haɗa hannayensa biyu suka bada sauti mai ƙara cikin wata murya ta izza ya ce """Mene haɗin ta da maganar yawar ku?""" "Eng Ali wali ya ce ""Wa kake magana""" """Ita ɗawar mai ɗan kwalin?""" "Cikin rashin fahimta Eng Ali wali ya ce ""Meye ɗawa da ɗan kwali kuma?"" Mangal ya yi murmushi yana" """Ka fice Mai gida, ɗawa da mai ɗan kwali mace kenan ake kwafa maka zancen"" Ya ce ""Yaran naku sai ku""" Miƙewa Mai dawa ya yi tsaye yana ɗora ƙafarsa a saman farar kujerar dake parlon kallonsa kawai Eng Ali "wali ya yi bai ce komai ba. Sai wani ya ce ""Mai dawa farar kujera ce fa?"" ""Ko takaddar jikinka zan ɗora ƙafa akai"" wanda ya yi maganar ya yi saurin kallon farar shaddar dake jikinsa fara tas da ita sai ya ja bakinsa ya yi shiru. Moh ya kalli gefe yana furzar da iska daga bakinsa ya ce" """Me ya sa ka neman, bayan kana da gajojinka?""" """Saboda kai ne baƙuwar fuska a cikin wannan sabgar tamu, ba wanda zai gano cewa a tsagina kake za ka" "yi aiki mai kyau hankalina ya kwanta da kai Mutallab"" wani irin kallo Mutallab ya jefa masa idanunsa sun sauya kala ya yi murmushi ya ce" """Oh Mai dawa da jeji, ya batun yarinyar ka santa ne ko ka taɓa ganin fuskarta?""" """Na santa ko ban santa ba ina jin bashi kake buƙata ba. Yaushe kake so a kawo maka ita?"" Girgiza kai Eng" "Ali wali ya yi ya ɗauki ruwa ya kurɓa ya ajjiye kana ya miƙe tsaye yana zagaye parlon hannunsa a baya ""Ka jira umarni na, kawai ka zama cikin shiri a koyaushe zaka iya jin kira. Akwai gidan dana samu a bayan gari zan baka makullin ko ka ɗakko ta can zaka ajjiyeta kai ne zaka dinga kula da ita har yanzu lokacin da muka shirya abin da mukai niya, a cikin gidan akwai kayan aiki irin naku wanda za su sama muku" "nutsuwa""" "Goje ya jinjina kai cike da jin daɗi kafin ya ce ""Mai gida za a siya mana mota mai iska kamar yadda muke" "ƴaƴan iska?""" """Za a yi muku komai, ku riƙe amana. Sai dai kawai sharaɗi ko da wasa kar ku nuna kun sanni idan ina" "buƙatar ganin ku a wannan gidan zamu dinga haɗuwa, ku buɗewa kowa idanu kar ku ji tsoro da shakkar komai ni zan tsaya muku har zuwa ci zaɓe"" Moh ya ce ""Bayan cin zaɓan fa?""" """Kamarya?""" "Ya buɗe manyan idanunsa sosai a kan Eng Ali wali a karo na farko ya ƙare masa kallo ""Mene farashin" "aikina?"" ""Nawa kake so?"" Ya yi shiru yana tunani can ya ce ""Zan sanar""" "Eng Ali wali ya ɗakko ƙatuwar bana da fastoci ya bawa Goje da yawa ya ce ""Kuje ku fara da aikin liƙawa" "wannan a unguwanni da saƙo da lungu ya zamana babu wanda ake ganin sai Eng Ali wali, bayan wannan akwai wani dattijo da yake zuwa gidan rediyo yana yi sojan baka kuma duk ni yake kushewa yana son jiƙa mini aiki a tabbatar an saka shi yin shiru da baki da kowacce hanya"" kuɗi ya ciro daga cikin Aljihu ya miƙawa Goje ya ce ""Aje a yi caji a huta"" har Moh zai juya sai kuma ya tsaya ya cake waje guda kamar" "saƙago ya ce ""Me ya sa kuke son a kamata?""" """Aiki ne kawai naka wani abu ba sai ka sani ba, mune shuwagabanni ku dai a baku kuɗi da kayan" "sararawa shine"" kai tsaye Moh ya ce ""To nemi wani"" Eng Ali wali ya ce ""Me ya sa? Bayan kai ka cancanta?""" """Ba zan ba""" """Shikenan na gane, Safiyya Abdu Marafa na faɗa maka ƴa ce wajan tsohon leccara, yana kawo mini" "barazana a sabgar siyasa tare da nuna rashin cancanta a fili. Matasa na jin maganarsa abin da ya zaɓa kuma da shi suke yin aiki a yau ɗin da muke ciki matasa sune siyasa ina so a sa shi yin mubaya'a dole. Kasan da yawan lokaci Malamai suna kawo mana cikas"" Mai dawa ya jinjina kansa alamar ya ji sai dai bai" "yi magana ba a hankali ya duƙa yana buɗe hannu ya ce ""Sai godiya""" """Sai godiya"" Mangal da Goje suka faɗa suna zagaye shi. Cikin sauri kuma ya fice daga cikin parlon suna" mara mishi baya. "Eng Ali wali ya dubi wanda ke zaune sai kuma ya yi dariya sosai ya ce ""Amfanin su kenan fa babu wani" "aiki da ɗan daba zai iya yi maka banda bangar siyasa kashe kashe da sare-sare mu kuma sai mu jefe su da abin da sukewa""" Fiyya na tsaye gaban madubu tana gyara rolling mayafin kanta yau ma suit ce a jikinta ta mata riga da "wando blue black ta amshe ta sosai ta kalli kanta a madubin she missed the old Safiyyerh komai nata sabo take jin shi, ta ji kamar ta rasa wani abu mai amfani a tattare da ita amma mene? Shi ne abin da sam ta gaza fahimta ko a cikin bacci. Ta sauke numfashi tare da ɗaukan wayarta da jakarta tana ƙoƙarin buɗe ƙofa ta fita Ummi na shigowa cikin ɗakin Fiyya ta yi baya tana bata hanya kafin ta ce ""Good morning Ummi"" daga sama har ƙasa Ummi ta kalle ta sai kuma ta je can bakin gado ta zauna tana sake" "kallon Fiyya ""Ina za ki?"" ""Ummi Company""" """Junaid told me ba ki da lafiya, na yi bacci da wuri"" a hankali ta ce ""Lafiya lou nake Ummi ga alama kin" "gani zani aiki""" """Fiyya bana son irin wannan shigar taki, kuma ki haƙura da aikin nan yau za a kawo kayan auren ki"" da" "sauri ta ce ""Aure kuma Ummi? Ba sai nan da watanni ba?""" """To Daddynku ya ce cikin satin nan""" """Shikenan zan je aiki""" """A'a ki haƙura yau"" marairai ce fuska ta yi sosai kamar za ta yi kuka ta ce ""Ummi akwai buƙatar na je, ina" "da meeting da ma'aikata ba zan jima ba"" Ummi bata san damuwar Fiyya dole a hankali ta ce ""Allah Ya tsare ki dinga kula ke dai macace ba namiji ba, kina lura da abubuwa da kike yi"" Fiyya ta yi dariya tana yin waje ta ce ""Kuma ki saka tsoron Allah a ran ki Fiyya ban da wulaƙanta jama'a, al'umma ta Annabi ce""" "Ummi ta girgiza kai kawai ta ce ""Wato kin haddace kenan""" """Dole na Ummi""" "Cak ta tsaya tana riƙe kan ta Ummi ta ce ""Subuhanallahi Fiyya kina lafiya? Ba za ki haƙura da zuwa aikin" "nan ba?"" Ta ɗan ya tsuna fuska da nuna alamar ba komai ta ce ""Kawai na ji kaina kamar an saka mini shocking"" gaban Ummi ya faɗi sosai sai bata nuna ba ta kama hannun Fiyya suka sakko ƙasa." "Dr Hash ne ya fito shima sanye da farar riga ta likitoci Fiyya na kallonta ta ce ""Likita bokan ture, kuma" "fiɗe ku ɗinke""" """Kamar wasu mahauta"" ta yi murmushinta mai kyau tana lumshe idanu ""Barka da safiya Dr"" ya yi mata" "murmushi ""The whole Manager in the world"" Ta buɗe ido shima ya buɗe kafin su ce komai J ya fito shima yana cewa ""In the world mana, wannan kamfanin nan ku ina ne basu da reshe ni dai watarana zan zauna ki bani labarin kamfanin sosai na ji ai na yin wanda yake da shi"" ""Kai Yaya J nima ban san ko na" "waye"" ya buɗe ido ya ce ""Ban gane ba?""" """Da gaske nake Yaya ban san asalin me shi ba, kawai dai na san ni Manager ce""" """Ji nake Ashraf's father is the owner of the company""" "Ta tura baki gama tana harar shi ""Kuma ka sani kake tambayata"" ya ɗaga mata gira ya ce ""Zan zo ki nema" "mini alfarma wajan surukin naki nima ya bani ko messenger ne"" bata kula shi ba. Ɗago kai ta yi suka" "haɗa idanu da shi yana zaune ya watsa mata harara yana ɗauke kan shi gefe ""Aliyu ba yau zaka tafi bane"" ya yi shiru a hankali kuma ba tare daya ɗago kai ba ya ce ""A'a""" """Ok na ɗauka yau ne, ni wallahi duk firgitar dani kake mutum ba walwala kamar a filin yaƙi nan fa gida ne," "amma kodayaushe kamar an yi maka dariya ko yaya ne ka dinga murmushi""" """Ban iya ba Ummi""" """Murmushin ne baka iya ba Aliyu? Ka gwada zaka iya"" ya miƙe tsaye yana yin waje ""Ban san yadda zan" "ba"" ""Ina kwana Captain?"" Fiyya ta faɗa tana haɗe fuska ko inda take bai kalla ba ya yi waje abin shi. Shi dai J murmushi kawai yake yi halin Captain na bashi malam sosai suka jera shi da Fiyya suka fita. Mota ta shiga yana ɗaga mata hannu shima ya shiga tasa motar kowa ya kama hanyar wajan aikin shi. Fiyya na driving a nutse ta hangi wata mota na bin duk inda ta yi sai ta taɓe fuska ko a jikinta a fili ta ce ""Ɗan" "wahala ko waye""" "Daddy dake zaune bayan shigowar Ummi cikin parlon sama ya kalleta ya ce ""Me kike cewa Ummi?"" Ta" "damuwa ta ce ""Kwana biyu ba a amshi maganin Fiyya ba, kuma kamar ciwon zai tashi"" ya ajjiye littafin hannunsu yana saka glasses ya ce ""Wani abin ya faru?"" Ta numfasa yana faɗin ""Irin abin da ya faru kwana ki tana jin kamar ana mata shocking a kanta, ni wallahi bana son ma ta dawo daidai bana fatan ubangiji ya ƙara gwada mini tashin hankali dana gani shekarun baya"" Daddy ya jinjina kai ""Nima addu'ar da nake a raina shi ya sa ma na matsu kawai a yi ai maganar auren nan, wallahi bana son Maama ta" "dawo old Safiyyerh""" """In sha Allah hakan ba zai kasance ba""" Meeting hall ɗin ya yi shiru sai muryarta dake tashi cikin faɗa tana ɗan buɗe hannayenta tare da yin "baya ta ce ""Wanne irin rainin wayo da hankali ne, file ɗin dana ajjiye shi a office ɗina ina jiran a kawo mini proof hujjar abin da aka fitar aka samu shigowar kuɗi zuwa asusun kamfani kamar yadda Accounter ya faɗa mini shine za a ce wai na yi signature a file aljana ce ni da zan taso da gida na zo kamfani na saka hannu, idan zan saka me ya sa ban yi ba tun da file ɗin ya zo table ɗina?"" Ta miƙe tsaye tana kallon su gabaɗaya duka maza ne ita kaɗai ce mace ta koma ta zauna tana juyi a kan kujerar ""I need to find out the truth, meke faruwa a wannan kanfanin. Md da kai da secretary za ku kai ni na duba ko'ina a wannan kamfanin yau ɗin nan, kai kuma Director ka kawo mini record ɗin komai daga watan daya shige zuwa yau ɗin nan, ina buƙatar statement yanzu a office nawa"" ta sauke numfashi fuska a haɗe sosai ""An" "gama"" secretary ne ya kalleta kamar a tsora ce yake ya ce ""Manager akwai baƙi da suke jiran ki""" File ta ɗauka ta miƙe tare da ficewa daga cikin meeting hall ɗin. Bata nufi office ɗin ta ba inda suke "ganawa da baƙi ta nufa ta tura office ɗin a hankali a hankali ta yi sallama ta shiga. Manyan mutane ta gani su biyu zaune a kan kujera kana ganin su ba sai an yi magana ba ta zauna kan kujera mai cin mutum biyu a ladabce ta ce ""Ina kwanan ku? Welcome to FS WORLD INVESTMENT COMPANY i am Safiyya A. Marafa how can i help you?"" Wani rushehen mutum ne daya Hakim ce a kan kujera ya dinga kallon ta kamar zai haɗiye ta idanunta dai na kan system tana ta dannawa da aikin tura saƙo can ta ɗago kai suka" "haɗa idanu ta sake kame fuska ta ce ""How can I you? Ta ya ya zan iya taimaka muku""" """Ba ki gane ni ba""" "Sarai ta gane ko waye ta ce ""Yau na taɓa ganinka""" """To ma sha Allah. Sunana Hon Maɗatai zan saka hannun jari ne a cikin wannan Company""" """Ok, me kake buƙata?""" "Ya gyara zama sosai ya ce ""Za a dinga bani shinkafa, suger, wake a kan farashin yadda Company yake" "siyarwa ni kuma zan ɗora kaso 50 domin cin riba amma daga lokacin Company ba zai sake siyarwa da kowa kaya ba sai ni"" Fiyya ta dinga kallon shi sosai a ranta tana mamakin son zuciyar wasu ya suke so talakawa su yi da ran su ne? Burin shuwagabanni talaka ya faɗi ya mutu saboda yunwa? Ta yi jim sai" kuma ta ce """Da wata ce matsayin Manager ba Safiyya A. Marafa ba do wataƙila ka samu wannan damar a yanzu ina" "maka murna da cewar we're not interesting anymore, da wannan zai fi kyau ka buɗe naka masana'antar ka nemi matasa marasa aikin yi wanda suke lalacewa ka basu abin yi"" ya dinga kallon ta can ya ce ""Kin" "san waye ni? Ƴan'mata ki bi a hankali fa""" """Ai ba a yi wa Fiyya maimaici Hon Maɗatai ba zamu baka hannun jari ba You can leave"" ya miƙe tsaye" "yana jin ba'a taɓa yi masa wulaƙancin da yarinyar ta yi masa ba ""Safiyyerh ko? Ki bi a hankali haɗuwar farko ce wannan, zan tafi amma zan dawo""" Ficewa ya yi rai ɓace zuciyarsa na zafi. Fiyya ta ɗauki kayanta ta nufi office. A hankali take bin bayan Md "da Secretary ɓangaren kayan abinci aka kaita kana da mai daga can baya wajan shara inda ake ajjiye bukar kamfanin ta dinga jiyo wari da sauri ta nufi wajan Md ya ce ""Manager sharar kamfani ce nan"" bata kula shi ta nufi wajan sharar tana rufe hanci da f facemask kamar an ce ta juya idanunta ya sauka akan" yatsun hannu guda huɗu da suke a leda ƙuda na bin su. Tunda ya nufu layin su tiger na biye masa baya hannunsa riƙe da gora yara suke watsewa sai waje ake "bashi hatta almajirin Malam sai da wasu suka bar wajan banda Ɗanyaro dake zaune yana danna sabuwar wayar daya siya sosai Malam yake ji da shi yanzu lokaci zuwa lokaci yake yi malam alheri na kuɗi ga nama da yake kawo masa, sai dai cikin dare Ɗanyaro zai lallaɓa ya gudu ba zai dawo ba sai safiya. Moh na ƙoƙarin shiga gidan Malam ya tare ƙofar ya ce ""Na haifi yaro sunan shi Muɗallabi amma yanzu bani da wannan yaron na bar wa ƴan iska shi da ƴaƴan banza tunda ya zama shaiɗani ba zaka ja mini masifar da zan mutu a gidan ɗan kande ba"" Moh zuciyarsa ta fara tafasa har wani hayaƙi ke fita ta cikin bakinsa ya dinga kallon asawan nasa ya kasa cewa komai ya leƙa surar gidan ko zai ga Ammo amma sai Inna Binta" "dake suɗe tukunya tana faɗin ""Matsalata ɗaya a duniyar nan abinci idan na ci na ƙoshi Mufee ta ci ni fa" "ko a jikina"" Juyawa Moh ya yi kamar zai yafi sai kuma ya nufi saman katanga ya kama ya dire ta cikin" "gidan Inna Binta ta zabura tana faɗin ""ƙulna naru ƙulni bar dan wasalamun Allah Ibrahim, auzubillahi"" jikinta sai rawa yake masifar tsoron Mai dawa take kamar ran ta sauran jama'ar gidan duk suka shige ɗaki banda Mufee da ta yi tsaye tana kallon shi sosai idanunsu yake iri shi bai san wace ita a gidan ba, bai" damu daya sani ba yara ne kamar yaƙi wasu iyayensu basa cikin gidan. Labulan ɗakin Ammo ya ɗaga ya ganta zaune tana ninke kaya ya fi minti goma tsaye kamar zai juya sai "kuma ya shiga cikin ɗakin idanunsa akan kwanon abinci sosai yake jin yunwa idanunsa na rufewa ya miƙa hannu zai ɗauki abincin Malam ya ce ""Kana ci zan maka Allah Ya isa ka tashi ka bar mini gida tsinannen yaro"" da sauri Ammo ta kalli Malam sai kuma ta ɗauke kai." Jikin Moh ya fara rawa jijiyoyin kansa na mimmiƙewa jin uban daya kawo shi duniya na yi masa Allah Ya "isa ya yi ƙasa da kansa idanunsa kamar za su fito waje ya ji babu abin da yake buƙata sai ƙwayar da Mangal ya bashi ya sha, ita kawai zata sauke masa abin da yake ji ya manta da komai, yaushe ne zai zama daidai kamar kowanne mai rai an ci zalin shi an lalata masa rayuwa. Ya miƙe da sauri yana banko" "ƙofar ya yi waje ""Sallamammen yaro Allah dai ya rabani da ƙaddara na huta""" "Kai tsaye Moh dabarsu ya nufa yana zuwa suka mimmiƙe Darma na faɗin ""sai godiya Mai dawa sarki mai" "jeji, wani ya ce ba kai ba yanzu mu fito mu yi farfesun hanjinsa""" Yanayin fuskar Mai dawa a bar tsoro ce ya takure waje guda yana jin kamar zuciyata zata fito waje don "baƙin ciki. ""A sama yake ku bashi sha fara kaga aljan"" cewar Darma Mangal ya girgiza kai ya ce ""Ba za ta" "yi masa ba, kawai a yi masa allurar fenta""" """A'a ta yi masa girma yaushe ya faɗo sabgar kar ka luda masa ya yi mana na jakuna yanzu"" zaro sirinjin" "ya yi Moh ya ƙurawa siririn idanu ganin yadda Mangal ke zuƙo ruwan ciki ya fara girgiza kai da ƙyar ya ce ""Kar ka yi mini Ka bar ni da tunanin bana son mantawa"" kokawa suka fara yi da shi ya ɗauki Darma ya buga da ƙasa Mangal ya faki idanunsa ya caka masa allurar a gadon baya. Jinjiga ya fara sosai cikin ƙaramin lokaci ya yi shiru yana jin shi kamar a samaniya yana yawo yanayin ya yi masa daɗi sosai ya ji zuciyarsa wasai a wannan yanayin bacci ya ɗauke shi. Can cikin dare ya farka kam shi ya yi masa nauyi har yanzu bai dawo daidai ba, babu komai a cikinsa ya miƙe tsaye yana layi kamar zai faɗi Mangal ya ce" """Mai dawa""" "Ya yi masa shiru yana ɗaukar wuƙa ya soke ya ɗauki fitila ya riƙe ""Dare ya yi ba, kana fita waɗancan" "ɗankokin za su iya kama ka gashi babu da goge a hannu ka zauna, kasan kuma ƴan cikin gari sun shigo sun samu labarin mun yage musu poster bama wannan ba ɗazo an ga gawar wani to ana tunanin mu ne kuma yaron ɗan cikin garin ne fansa suka zo ɗauka,na bibiyi abun shi yaron ƙwacan abar magana ya yi" jama'a kuma sun fara ɗaukan doka a hannunsu suka rufe yaron da duka har ya mutu. Su Cokali kuma ba "za su haƙura ba kar muna zaune su ci mu da yaƙi""" """Sai godiya""" "Ya furta da ƙyar daga nan sake yin shiru yana shirin barin wajan kamar zai kifa ""Ina zaka ne? Ka dawo ka" "kwanta""" """Kai fa ba Malam zan haɗaka da Rainbow""" """Shikenan ina zaka yanzu"" ya cije leɓe zuciyarsa na ayyana masa abin da zai yi shi ne daidai allurar sai" "gaibu take faɗa masa a hankali ya ce ""Zan kashe Malam ya baza lahira""" For more information 08164069385 WhatsApp only "[10/9, 5:16 PM] Nanameera: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 6 *Bright pens... 2nd batch* * for the adults and criminal side please just take it as a lessons* "Goje daya farka daga bacci ya yi saurin miƙewa yana furta ""Malam ɗin zaka kashe mahaifin naka?"" Ya yi" "shiru bai yi magana ba, yana sake riƙe wuƙar a hannunsa da kyau duk jikinsa rawa yake, ga wani irin ciwo da kansa yake yi masa sosai, idan ya tuna abubuwan da aka aikata masa sai ya ji zuciyarsa ta bushe ta kuma ƙeƙashewa. Ya saka ƙafa ya banga je Mangal dake tsaye zai shige Goje ya yi saurin shan gabansa yana ɗaure fuska sosai ya ce ""Saboda kana jin kanka a sama ta bakwai kake jin komai za ka iya yi? Me ya sa ba zaka yarda sarki sammai ke yin komai ba, mu fa ba haihuwar ta zubar bane ko yaya ne mun san abin da ya dace kashe mahaifinka ba shi ne mafita ba Mai dawa"" ya ɗaga jajayen idanunsa kamar zai ci babu yadda ƙwaƙwalwarsa take faɗa masa ba daidai haka komai na duniyar yake yi masa babu daɗi" maƙoshinsa na yi masa zafi da raɗaɗi wani abu ya tsaya masa da ƙyar ya iya buɗe bakinsa ya ce """Ya zan yi?""" "Kai tsaye Goje ya ce ""haƙuri, ka bi komai a sannu mai dawa ita gaggawa aikin ƴan annaru ce. Kashe" "Malam a yanzu ba zai rage maka kashi goma a cikin ɗari na damuwar da kake ciki ba, iya wuya iyaye ne su""" """Ba iyaye na bane, ka bari ko ɓalli-ɓalli na yi masa"" ganin da gaske shirin tafiya ya ke yi ya ce ""Idan kaga" "ka bar wajan nan sai dai ni za ka fara kashewa"" Ya ƙuri da idanu yana kallon Goje har wani hayaƙi ke fita ta cikin bakinsa ya wani cije gefen baki yana karkatar da kai gefe. Kamar wasa Goje ya ga Moh ya nufe shi da wuƙar shima yaƙi matsawa yana ganin kamar wasa ne yana ƙoƙarin kawai Goje sara su kaga mutane kamar daga sama sun zagaye su. Moh yaƙi motsawa sai Goje da ya yi baya ya cake yana zazzaro idanu tare da ɗaga gora sama. A kallon farko Mai dawa ya gane cinnaku ne ƴan'sanda sai ya ɗauke kai" shi Goje bai faɗa da labarin ba saboda shigar fararen kaya suka yi. """Eng Ali wali ya aiko mu wajan ku kawo muku kaya"" sai a lokacin Mangal ya ƙarasu yana tale ƙafa ya ce" """Kaya sun sauka da zafin su kenan yallaɓai, amma eh kun razana mu shigowa ba notice sai mu ɗauka dire aka yi mana"" ɗan'sandan ya yi murmushi kawai ya ce ""Kuna da kamar Ali wali za ku ji tsoro? Kune matasan da yake ji daku a yanzu musamman wannan da naga ko kallo bamu ishe shi ba"" Goje ya juya ya kalli Mai dawa da yake kallon wani sashi daban alamar baya ma jin me suke cewa ""Mai dawa sarki me" "jeji wajanka aka aiko mu domin aikin bana yara bane""" """Faɗi""" Moh ya ce yana bada faɗi ba tare daya kalli da ɗan'sandan ba. Abu ya fito da shi a jaka ya miƙawa "Mangal ya amsa ya ce ""Ka a dana kada a je a yi ta sha ana ɓarna, Eng Ali wali ya ce akwai fita ta musamman kuma ƙauyen da za shi basu da kirki dole tafiyar sai daku a ranar zaku cake ku bawa samaniya yazo ta yi hadari"" Mangal ya buɗa ya ce ""Dar hakan ya yi mana, sai Eng Ali wali ko ana su ko ba'a su ya zama dole don uwatar"" Police ɗin ya juya kan Mai dawa a hankali cikin magana mai muƙamin" ya ce """Ka taɓa jin mai suna Scorpio?""" """Wa?"" Goje ya ce da sauri yana kallon Mai dawa da sai a lokacin ya juyo ya kalli Jafar shima Jafar ya kalle" shi da kyau ya ce """Akwai matsala ne babba, Scorpio yana yi wa Eng Ali wali barazana, yana da babbar hujjar da zai iya" "kawo masa matsala a mulkinsa kuma babu shakka ko waye Scorpio akwai alamar ya shirya fito na fito da Eng Ali wali, to muna jami'ai ba zamu bari ba tunda a jikin shugabannin da ƴan dabarun mu muke samun namu rabon. Ali wali yana buƙatar ka taya shi gano waye wannan Scorpio da sunan shi kawai ake ji ba" "kamanni""" """Kamarya kenan?""" Mai dawa ya tambaya a taƙaice yana jin ƙirjinsa na buɗewa saƙo ya fara isa kenan a fili kuma ya sha kunu "sosai. Jafar ya dafa kafaɗar Mai dawa ya ce ""Kamar kai yanzu kowa ya san sunanka Mutallab inkiya Mai dawa saɓanin shi da sunan Scorpio kawai muka sani, babu wanda Eng Ali wali ya yarda da shi sai jami'an Dss ka baza jama'arka su tayaka binciko asalin waye Scorpio akwai kyauta mai yawa idan hakan ya" "tabbata, kuma ya ce ka faɗi kome kake so zai baka""" "Wani irin kallo Moh ya dinga yi wa Jafar na kan kaga biri, biri ya ganka kifi na ganinka mai jar koma sai" "kuma ya ɗaga kai sama yana kallo sama cikin kumburarriyar murya ya ce ""Bayan Dss da shi uban gidan naku waye ka ji yana neman SCORPIO?"" Jafar ya ce ""Me ya sa kake tambaya?""" """To kuje ku yi aikin da kan ku"" ya faɗa yana juyawa cikin sauri Jafar ya riƙo shi ya ce ""ka dinga" "sassautawa zuciyarka da fushi. Bayan Dss akwai jami'ai mafi hatsari da suke neman shi idanu rufe FID Federal investigation department, basu da imani wannan mutanen jami'ai ne da ba zaka taɓa tunanin ta" "ina zasu cimmaka ba, suna iya zuwa a suffar mahaukata ma ko mai neman taimako, su kakkarya mutum" "ko su kashe shi ko haukata shi ba wani abu bane a wajan su""" """Suka kasa kama Scorpio?"" Jafar ya watsa hannu ya ce ""Sannu sannu da zarar sun gane kamanmin su," "babu mamaki su ɓullo ta wata hanyar kafin hakan ta fara ka ruga su kai hari,mun gama magana da kai" "Mai jeji"" ya yi shiru bai ƙara cewa komai ba ""Ka yi shiru?""" """Ka bada sha ɗayanka, zamu jauwalo ka idan akwai sagi"" cewar Goje Jafar ya girgiza kai ""Ka bar shi ya yi" "magana"" Moh ya sake kame fuska babu wasa kuma yaƙi cewa komai sai ma fito daya fara yi yana kallon bindigar dake hannun ɗaya ɗan'sandan. Bisa dole suka juya suka tafi ba tare daya tanka su ba,daman Goje ya san ba maganar zai yi ba. Goje ya juya ya kalli Mangal da yake zuƙar wiwi a hankali ya ce ""Ka" "raina musu hankali waye Mai dawa waye Scorpio""" """Ni ne, MUTALLAB TAHHB SCORPIO""" Mai dawa ya ce yana zare idanu waje manya gwanin tsoro da razani har sai da Goje ya ja da baya don bai taɓa ganin halittar idanu kamar ta Moh ba ƙwayar ta juye kamar bata mutane ba kuma sai ƙara ware manyan idanun yake yi. """Akwai matsala Moh idan suka gano cewa kai ne Scorpio, za su yi maka illa gwara ka ɓace kawai daga" "yankin kafin komai ya sarara"" ""Gawata za su iya gani su haƙura da nema na"" Ya furzar da iska daga cikin" bakinsa kansa ya yi masa nauyi """Goje an yi sake tunda aka bari na je state cid,ba san komai ba amma a fitar dani. Zan iya haƙura da" "komai banda abin da yake damuna a zuciya ni da kai na zan bayyana cewa nine Mutallab Tahhb Scorpio da zarar na cika muradina na abin da na yi niyya""" """Mai dawa""" """Sai godiya""" """Ina tunanin ka haƙura ka bar wa Allah komai duk zamu baza mu je gare shi ya yi mana eh hisabi"" Moh" "ya taune harshe yana kaɗa leɓe tare da saka harshe ya kashe wuƙar dake hannunsa ""Zafin nake ji a" "zuciyata zan yi ɓarna, zan sha jini""" """Kamar wani maye? Shi Ali wali ɗin me ka yi masa ne?""" "Mai dawa ya ja idanunsa ya lumshe ko yaya idan ya yi shiru sautin kuka biyu yaje ji a kunnen shi, tare da" "jiyo ƙarar wutar dake cinye jikin nata hakan ya saka baya iya runtsawa idan ba wani abu ya afa ba haukwata shi ake son yi. ""Na yarda da kai Goje, ka ci amanata askira zan saka maka a maƙoshi"" ""Ni ɗan halak ne. Yanzu ya batun Manager ɗin? Ka santa ne na ji baka bashi amsa ba"" jin ya yi shiru ya saka shi" cewa """Ko dai ka san Managern kamfanin?""" """Karka ka daman""" ***** Fiyya na zaune a saman gadonta tunda ta dawo take kwace tunani ne fal a cikin zuriyarta ga wani irin "tsoro da bata taɓa jin shi ba, a karo na farko ta ji tana son sanin komai da komai na Kamfanin FS WORLD INVESTMENT COMPANY, da duk mutanen da suka saka hannun jari a ciki data rufe idanunta yatsun hannun take ganin da aka yanka aka zuba cikin leda sosai taga rubutu jikin ledar amma ta manta bata duba ba. Ta juya a hankali tana kallon wayarta kamar mai tunanin wani abu kuma sai ta ɗauki wayar tana dannawa numbersa ta kira aka danna line busy. Har zata ajjiye wayar sai ta ji an kira ta zubawa" sunan idanun kafin ta ce. """Ashraf...""" Kiran ta ɗaga ta kara a kunne ta yi shiru ta cikin wayar ya sauke numfashi da ƙyar muryarsa a hankali. """Na ji tsoro Fiyya"" ta ɗan tura bakinta gaba kamar yana kallonta muryarta mai daɗi ta ce ""He said he was" "scared"" ya ƙara fidda numfashi kamar tana gabansa ""Maama kina wahalar dani da kika zaɓi aikin nan na kusa mutuwa, na ji ba zan iya barin ki ba kuma ke ce dai wacce nake so Fiyyar nan tawa""" """Ba na ce ka daina ce mini Maama, why not Fiyya kawai?"" Kamar mai raɗa a hankali Ashraf ya ce ""I am" "sorry bestie me""" Dum! Haka ta ji kan ta ya yi masifar sarawa da sauri ta dafe kan nata tana jin kamar wani abu na janta a "gigice cikin faɗa ta ce ""Karka sake kira na da wannan sunan"" ta cikin wayar ya ce ""Ba zan sake ba amma lafiya kike? Yanzu kike mini magana cikin soyayya Fiyya me ya sa sometimes kike abu kamar bake ba?" "Are You okay?""" """Kai na ke ciwo""" Tana cewa haka ta kashe kiran ta cillar da wayar nata zuwa gefe guda. Da sauri ta miƙe babu ko hula a "kan gashinta yana tashi sama tana dafe da kanta bata ganin ko gabanta duhu ne a cikin idanunta haka ta dinga sauka akan matattakalar benen. Karo ta yi da mutum cikin sauri ta kama hannunsa tana ɗorawa a kanta ""Yaya J kai na zai cire wani abu nake ji, ciwo yake mini kamar ana jana"" gabaɗaya ta rikice ta" ƙanƙame shi har zufa ke tsattsafo mata. Kama hannunta ya yi ya jata saman kujera taƙi sakin shi ya zauna a hankali tare da zaunar da ita ta yi saurin ɗora kanta a cinyarsa ya riƙe mata kan yana murza goshinta nata very careful kar ta ji zafi. Sun jima kana ta shiga sauke ajjiyar zuciya numfashinta na sauka ya ɗan leƙa fuskantarta yaga bacci take ya saka hannu ya juyo da fuskarsa yana zuba mata idanu ya riƙe hannunta har lokacin bai ce komai ba. """Aliyu""" "Da sauri ya saki hannun nata yana zame ta ya miƙe tsaye Ummi ta kalli Fiyya ta kalle shi ta ce ""Ita kuma" "lafiya take bacci a nan? Yaushe ta shigo gidan ai lokacin tashi bai ba?"" Captain dai ya yi shiru ta juya ta kalle shi sosai ta ce" """Lafiya take?""" """Ban sani ba""" """To ya naga kana haɗe rai duka zaka kawo mini me kai komai naka babu walwala Aliyu ka dubi girman" "Allah ka dinga murmushi shifa yin murmushi sunna ne ta ma'aiki"" ya shafa kan shi yana zuba hannu a aljihu cikin gaskiyarsa ya ce ""Ban iya ba wallahi Ummi ki koyan""" """Shi murmushin? Allah ya rufa asiri to wannan matarka ta shiga uku"" yana dai tsaye bai ce komai ba." """Maama?""" """Ummi""" """Maama ta shi yammaci za ki yi ƙunci ko ciwon kai idan kikai bacci"" ta buɗe fararen idanunta suka haɗa" idanu ta sha kunu sosai tana tura baki ya zabga mata uwar harara ta yi baya zata koma baccin. """Kee"" ya kira sunanta ta buɗe idanu ""Tashi kafin na yi balle da wannan silar ƙafafuwan"" miƙewa tsaye ta" yi ta murguɗa masa baki bata ce komai ba shi kuma ya yi kamar zai juya ya damƙo hannunta ta ƙwalla ihu daidai nan Daddy ya shigo parlon cikin sauri ya sake ta. """Da kyau Soja gwara ka nuna ƙarfinka akan ɗiyata, yanzu zaka tattara ka koma inda ka fito""" Captain ya juya ya bar parlon gabaɗaya yarinyar haushi take bashi har zuciyarsa. Daddy ya kalli Fiyya ya "ce ""Maama, yaushe za ki girma ina ganin wawtar wanda ya ɗauki muƙa min Manager ya ba ki wallahi""" """Daddy kune kuke raina ni wallahi, na girma am matured enough"" ya girgiza kai kawai kasancewar t.v. na" "kunne aka fara karato taƙaitattun labarai. Sunan Scorpio aka fara ambata matsayin wanda jami'an tsaro na hukumar FID Federal investigation department suke nema idanu rufe. Dake t.v a hankali ta juya ta kalli mai karanto labaran matashin ɗan jarida dake aiki a gidan t.v na VOA juyawa ta yi ta ce ""Daddy ɗan" "bani aron wayarka""" """Ki yi me da ita?""" """Wayata zan kira, ina son fita ne wajan Kinal"" ya miƙa mata wayar ta ɗan jim tana ɗaga hannunta tare da" "copy na wasu numbersa sai kuma ta miƙa masa bayan ta yi deleting tana murmushi ""La la la na tuna inda" "na sata""" "Ya kalli t.v ya kalleta ya kuma kalli wayarsa, ya dai amsa a ransa yana mai jin tsoro da mamakin kaifin" "tunanin Maama. Ummi kuma ta ce ""Ayi ta neman mutum kamar kiyashi shi kuma ya rasa sunan da zai" "sawa kan shi sai kunama?"" Daddy bai yi magana ba Ummi da abin ke ta cinta ta kalli Fiyya dake shirin" "haurawa sama ta ce ""Maama ta shi me ya yi ne?""" """Ummi ina zan sani, idan kika ɗauke yadda ake juya biyar ta zama goma ba abin da Fiyya ta sani"" tana" "cewa haka ta haura cikin sauri tana nanata numbersa dake kanta cikin sauri ta yi wanka ta shirya cikin abaya ta yi rolling tare da fesa turare sauri-sauri take a haka ta sakko hannunta riƙe da waya ko jaka bata ɗauka ba. Daddy ya dube ta ya kalli lokaci ""Wai zuwa wajan Kinal baya tashi sai yamma? Ita Kinal ɗin nan" "ta dinga zuwa mana zai fi""" """Daddy ba jimawa zan yi ba, na jima ban je ba mun gaisa ba""" """Maama bani da nutsuwa haka kawai idan kika fita gari ya hargitse bani number Kinal ɗin nan na kira ta""" "kafin ta yi magana J ya yi saurin ƙwace wayar Fiyya ya ce ""Bari na kira maka ita Daddy"" babu sunan Kinal a jerin wanda ta yi waya dasu yau cikin sauri ta amsa ta ce ""Number Kinal a kashe yaje fa J wai ni yarinya ce na san yadda zan kare kai na no body can come and hit me"" Ta kalli Daddy da Ummi ta juya ta kalli J" "ta ce ""To tsoran na mene ni Safiyya A Marafa?""" """Allah Ya tsare Maama jeki"" amsawa ta yi da amin ta raɗawa J kunne ""J akwai gulma yau bari na je na" "dawo"" tana fita harabar gidan mota ta shiga ta yi mata key cikin nutsuwa dake driving har ta fita ganin ta" hau kan titi ta dubi bayan motarta ta cikin gilas wata ajjiyar ta sauke mau nauyi ta rufe idanunta ta buɗe sai kuma ta ɗauke hanyar ta nufi wani titin daban a zuciyarta addu'a take yi sosai. ***** Eng Ali wali na zaune a parlo cikin wani gidansa da yake ganawa da ƴan siyasa masu mara masa baya a "kujerar shi. Ya dubi CSP chief Superintendent of Police ya ce ""Ina son ku ɗauke idanunku akan yarana, ko me kuke buƙata zan baku idan ɓarna sukai zan ji da komai"" Csp ya ce ""Hon yaushe za mu cigaba da zuba idanu ƴan dabarka suna yin yadda su kaga dama a garin nan musamman a unguwar Birget gashi lamarin na shirin haddasa faɗa tsakanin ƴan cikin gari da su ƴan Birget, mu jami'ai ne mun san gaskiya muke take" "ta""" """Ku cigaba da takewar su wannan yaran suna da wa'adi dana samu na ci zaɓe ko inuwata babu mai gani" "a cikin su. Don haka ku rufe idanunku a toshe kunnuwa, zuwa gaba har matsayi zan saka a ƙara maka mu yi ƴan dabaru"" CSP ya jinjina kai Eng Ali wali ya ɗakko kuɗi mai yawa ya miƙa masa yana cewa ""Idan kun" kama masu dilar ƙwayoyi da kayan maye na san ana miƙa su hannun NDLEA ko? Ka tabbatar ƙwayoyin "na zuwa wajan Jafar shi kuma zai bawa yarana, kar ka sake sunana ya fito daman ai ƴaƴan asara ne ko an" "kama su ba za su taɓa furta ni suke yi wa aiki ba, lastly magana akan Scorpio ɗin nan yana neman bani ciwon kai bana son ya zama damuwata, idan F.i.d suka riga ku kama shi akwai matsala""" """Karka damu hon mun zuba yaran mu ta ko'ina""" "Eng Ali wali ya ce ""Lallai Scorpio ya zo hannu kafin zaɓe""" Cikin sauri Fiyya ta fito daga cikin motarta tana shiga cikin wajan data zo a reception ta tsaya na wasu "mintina tana zaune ta fito tana murmushi ta ce ""Ikon Allah kamar tare kuke?"" Fiyya ta buɗe idanunta sosai ta ce" """Wa?""" """Captain yayanki""" "Gabanta ya faɗi ta kasa cewa komai Kinal ta zauna ta ce ""Wallahi zuwan shi biyu fa, nima dai na yi" mamaki amma ya ce aiki yake dubawa shi ne ya leƙo mu gaisa har ma na tambaye shi ke sai bai bani "amsa. Amarya ya kike ya sabgogi""" """Good. Yanzu lokacin ku ne Kinal siyasa ta matso ana ta fama da habaice-habaice""" """Kamarya habaici?""" "Fiyya ta cire gilas ɗin idanunta ta ce ""babu abin da mawaƙa suka iya sai habaici wallahi ku zagi wanda" "kuke so kuma ku yabi wanda ku kaga dama"" Kinal ta yi murmushi ta ce ""A'a ni ba ruwana idan an kira ni" "dai waƙa ina yi amma ai ni ta soyayya nake yi tunda a nan na fi kauri, ina nan ina shirya miki ke da" "Ashraf"" Fiyya ta sauke numfashi ta ce" """Ina cikin matsala Kinal ban so faɗawa kowa ba wallahi""" """Subuhanallahi matsala wacce kuma? A kamfanin ko gida ko wani wajan?""" """Kema kin san a gida ba wanda zai mini komai sai mai baƙin halin nan, tunda ya dawo ya uzzura mini ko" "parlo bana fitowa mutum sai baƙar zuciya ɗan wahala kawai aikin kawai"" Kinal dai ta zuba mata idanu kafin ta ce ""Mene damuwar?""" """Kwana biyu da suka shige ana bibiyata kullum idan na fita, harta nan wajan da na zo sai da aka biyo ni," "ni ba damuwata kai na ina tsoron su Daddy su sani kin san abu idan ya same ni tashin hankali suke shiga. Kinal ban san su waye ba me kuma suke buƙata saboda bani da issues akan kowa wallahi na ji kawai ina son sanin wanda ke following nawa duk inda na je gwara mu yi fito na fito da shi, da na ce ko na yi hayar ƴan daba nima suna take mini baya?"" Kinal ta buɗe idanunta sosai ta ce ""Daman na fara zargin kina da taɓin hankali Fiyya, ke yanzu ina kika san inda ƴan daba suke bare ki je? Bakya tsoro ko shakka ai matsalarki police ne wannan ina ganin a gayawa Captain kawai"" tsaki Fiyya ta yi tana miƙewa tsaye ""gwara duk abin da zai same ni ya zaman da dai na faɗawa Captain ni ina da abin yi"" ""Ƴan daban za ki yi" "haya yanzu kenan?""" """E"" sai kuma ta koma ta zauna cikin nutsuwa ta kalli Kinal ta ce ""Akwai abubuwan da bana ganewa" "kwana biyu kamfaninmu ina son na yi bincike duk abin da na samu ba daidai ba wallahi sai na kaiwa hukuma Kinal yatsun hannun mutum na gani a cikin kamfanin fa?"" Kinal ta zare idanu waje ta ce ""A'a ki fara samun mai kamfanin ku yi magana dashi tunda ke ce Manager"" ""Sai yanzu na fara tunani, i wonder aka bani Manager a kamfanina bayan akwai maza da yawa sosai da na yi tunanin ko experience ɗina ne" "yanzu kawai na ji ina zargi""" """Zargin me?""" "Ta ɗaga kafaɗa ta ce ""I don't know, na fara bincike dole zan gano gaskiya"" Kinal ta ce ""To ki bi a hankali" "Please Fiyya we care about you ni ma zani anniversary na makarantarmu FGC dana shigo Kamfanin gobe," "har waƙa na yi mana yanzu haka wani Eng Ali wali na yi wa waƙar da aka saka ni"" shiru Fiyya ta yi tana" "nanata sunan FGC a ranta ""Na ji kamar na san makarantar nan fa""" """Ke da ba ita kika yi ba ina za ki sami, ni a can na yi secondary school kinga""" """Haka ne bari na je""" """To ki kula Please kar ki saka kan ki cikin matsala don Allah Fiyya"" murmushi kawai Fiyya ta yi tana ficewa" daga cikin studio ɗin. ***** Kamar an cillo shi haka yaga Mai dawa ya faɗo masa cikin office ɗin nasa da yake tare da manyan "mutane sosai tun kafin ya yi magana ya ce ""Kowa zai iya tafiya"" duk suka fice ya ɗaga kai ya kalli Mai dawa ya ce" """Ka daina zuwa ina nake ni zan dinga neman ka""" """Ka yi ƙarya""" """Ni nake maka ƙarya Mai dawa?"" Ya wani haɗe fuska tamau fuskarsa ɗauke da sabon yankan da aka yi" "masa jiya har yanzu ba'a gyara ba. ""Kai ai ba Malam Abdullahi bane da ba zan ce kana ƙarya ba""" "Eng Ali wali ya jinjina kai ya ce ""Me ya kawo ka yanzu? Har cikin office nawa""" """Ka saka ni aiki har biyu, da kamo maka ɗawar can da nemo Scorpio"" ya shagiɗar da baki gefe ya yi fito" "wanda ya cika office ɗin sosai ""Na je gidan asawanta jiya""" """Kana nufin gidan Abdu Marafa?"" Ali wali ya ce yana miƙewa tsaye cike da tsoro Mai dawa ya ɗaga ƙafa" "ya ɗora a saman table ɗin gaban Ali wali ""sharaɗin kawo maka ita barewar shi ne mallaka mini kamfanin FS WORLD INVESTMENT COMPANY, aikin Scorpio kuma ka saka cinnakunka cire hannu daga sabgar ka bar mini ni zan nemo maka shi, bana haɗa aiki da wasu""" "Ali wali ya ce ""Mene haɗina da kamfanin nan? Karka saka ni rigimar da tafi ƙarfina da ka san ma'anar" "abin da FS WORLD INVESTMENT COMPANY yake nufi ba zaka haɗa kan da shi ba, wannan Kamfanin ciwon idanu ne"" Mai dawa ya ce ""Ni Mutallab Tahhb ɗan babana Abdullahi da inkiya Mai dawa bana harin abu na haƙura, wannan kamfanin shi ne burina"" Ali wali ya goge zufa ya ce ""baka san kamfanin ba shi ya sa a ba ki yake maka wahalar faɗa ni Ali wali sabgar siyasa na sani na saka gaba, ka bar ni a haka" "ba zaka saka ni a masifa ba""" """Waye mai kamfanin?""" """Sannin hakan daidai yake da tunuwar asirin manyan mutane da dama, ka bar komai yadda ka sani""" "jinjina kai Mai dawa ya yi ya ce ""Zan maka jahilanci ne, ka riƙe amana ka bi sharuɗan da na ce zan maka komai ni ɗan daba ne kai mai neman iko da muƙa mi ni na sare na kashe mu bauta maka shi ne. Batun kamfanin zan yi bincike da kai na, kar ka zama butu don wallahi sai na yi maka daƙiƙanci""" """In sha Allah, daga nan har bayan zan yi maka komai""" """Dar zan doƙa yanzu sai godiya""" "Yana fita Eng Ali wali ya ɗauki waya ya kira Csp ya ce ""Waye Mutallab yaron da ya fito daga wajan state" "cid kwanan nan bayan ya yi shekaru uku a wajan su"" ta cikin wayar Csp ya ce ""Sunan shi dai Mutallab ya kashe matarsa aka aka kama shi, daga baya kotu ta sake shi a zama na ƙarshe ba wanda ya san dalili"" Ali wali ya kashe wayar yana sauke numfashi a fili ya ce ""waye MUTALLAB?""" For more information 08164069385 "WhatsApp only.[10/11, 9:21 PM] Nanameera: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 7 *Bright pens... 2nd batch * The door is open... Ga masu buƙatar ayi musu tallah. Na hango wasu ƙwailaye a conversation group da Mikiya writers Maman Sayed ta ce a faɗa muku akwai maganin gargajiya cikin sati guda komai zai kankama haɗaɗɗan maganin da Fiyyar Ashraf ke amfani da su ta ce a baku numberta ba... 08063114606 "Washegari da safe Fiyya na ƙoƙarin buɗe ƙofa ta fito da nufin zuwa office ya rigata buɗe ƙofar, kallo ɗaya" "ta yi masa ta ɗauke kan ta zuwa gefe a hankali kuma can ta ce ""Ina kwana?"" bai amsa ba sai cewa da ya yi ""You told Abba za ki wajan wata, amma kin yi ƙarya ina kika je?"" Manyan idanunta ta ɗago ta kalle shi ta ce ""Ƙarya kuma?"" Ya rufe ƙofar ya tsaya ""Idan kina yi mini kamar ba ki gane ba, kwaɗa miki mari zan yi maybe it will help you to understand it very well"" ita mamakin shi take yi ""Ni fa Manager ce business zai iya fitar dani ko'ina"" ya buɗe mata manyan idanunsa sosai sai kuma ya ce ""ina kika je"" ta tura baki gaba sosai ta yi gefensa za ta shige ya saka hannu ya fisgota kafin ta yi motsi ya ɗago fuskarta ya wanka mata mari ƙwayar idanunsa tamkar zata fito waje yana ihu a saman kan ta ya ce ""Idan na sake maimaita miki" "tambayar sai na tabbatar yatsun hannuna sun kwanta fuskarki""" """Sai dai ka kashe ni"" ta yi maganar ko gezau gefen fuskarta ya yi jajur dakakkiyar zuciyarta kuma ya saka" "ta nuna ko a jikin ta, ƙasan zuciyarta kuma wani zafi da raɗaɗi take ji ""ni kike cewa na kashe ki?"" Hannu ta saka zata ƙwace nata hannu idanunta cikin nasa ba tsoro ta ce ""Me kake so na yi maka? Ka shigo kana tambayata abin da ban sani ba, ka saka hannu ka mari fuskar da kullum nake shafa mata mayuka masu tsada, ni ka mara ban maka komai ba, tunda ka tsane ni ka kashe ni kawai"" da ƙyar ta iya ƙare maganar saboda muryarta dake rawa Captain ya saka hannu ya sake ɗauke fuskar Fiyya da mari yana huci ya ƙara ɗaga hannu zai mare ta cikin sauri ya tsayar da hannun nasa ganin hancinta na fitar da jini sosai kuma" yaƙi tsayawa. "Ta yi masa ƙuri da idanunta da ruwa ya kwanta a ciki, jinin kuma bai fasa zuba ba daidai nan aka buɗe" ƙofar tare da shigowa ciki da sauri Fiyya ta nufi wajan Daddy ta riƙe shi tana fashewa da kukan dake cin "ran ta jikinta har wani irin rawa yake yi da ɓari jinin dake fita a hancinta kuma ya shiga ɓata masa farar rigar jikinsa. Daddy ya juya ya kalli Captain daya haɗe fuskarsa ""Aliyu me ka yi mata?""" """Ni kuma?"" Ya tambayi daddy irin bai ma san me ya faru ba ""To ita da waye haka ji bi yadda take kuka" "hancinta na jini kuma kai na gani a ɗakin, dole kasan mene ya faru"" cikin damuwa daddy ya yi maganar wacce sai da ta bayyana saman fuskarsa ya ɗago Fiyya yana duban ta sosai ya ƙara kallon Captain" """Maama wannan jinin fa? Daman kina yin haɓo ne wani abun Aliyu ya yi miki?"" Ita dai Fiyya taƙi cewa" "komai sai shassheƙar kuka take yi numfashinta na yin sama, Daddy duk ya rikice baya wasa da al'amarin daya shafi Maama ko kaɗan a ƙasan zuciyarsa yake jin soyayyarta ya kuma tabbatar ita ce rauninsa Fiyya kawai za a taɓa a iya nakasta rayuwarsa. ""Ya isa daina kukan haka nan, Allah Ya nuna mini sati mai kamawa ki tafi gidan mijinki ni ma zan fi samun nutsuwa da hakan zan fi samu nutsuwa idan kikai auren" "nan Safiyyerh""" """I love you daddy"" Fiyya ta ce a hankali tana rungume daddy ya shafa kan ta cike da soyayya ""daddy love" "Safiyyerh"" tuni Captain ya fice daga cikin parlon. Anty Turai da zuwan ta gidan kenan ta ce ""Ikon Allah. Yaya kai ne kake ɗaurewar yarinyar nan gindi wallahi ka lalata da soyayya take yin abin data ga dama, ko" "Aliyu baka tambaya abin da ta yi masa ba ta wannan figaggiyar yarinyar kake""" """Fita daga ɗakin nan Turai"" rai ɓace Anty Turai ta fice tana zabgawa Fiyya harara ranta duk a ɓace." "Daddy ya kalli Fiyya sosai kamar zai yi magana sai kuma ya ce ""jeki wanke fuskarki I'll drop you""" """Daddy daman i missed your drive wallahi"" murmushi ya yi mata a duk santa zai kalli Fiyya sai gabansa" "ya faɗi ya juya a hankali ya dubi picture ɗinta dake gaban madubi sanye da kayan graduation ta yi wani kyakkyawan murmushi ta rungume hannunta tana kallon gefe guda. Ya ƙarasa ya ɗauki photon ya shafa a hankali ""Maama na ni kamar na yi ba daidai ba, bani da wani zaɓi ne i am sorry Safiyyerh Abdu Marafa"" ya lumshe idanu ya buɗe a kan photon ""kina tunanin kin yi girman da za ki iya kula da kan ki, ki" "kuma yankewa kan ki hukunci? Maama ba kin san komai ba a rayuwa you're nothing but a stubborn girl""" Ya ajjiya photon ya ɗauki wayarta babu wani password a kai dudduba abu ya fara a nutse yana yi yana "kallon ƙofar banɗaki can ya sauke ajjiyar zuciya ya ajjiyar wayar daidai nan ta fito. Ya yi waje yana ""Ki" "same ni a ƙasa""" "Suna tafe a hanya daddy na driving a nutse ta ce ""Daddy"" bai kalleta ba yana dai sauraren ta domin" "program ɗin da ake yi da Eng Ali wali a redio shi ne ya ɗauke masa hankali. ""Zan raka Kinal FGC""" "Wani burki ya ja a kusan tsakiyar titin Fiyya ta dafe kai tana ""Subuhanallahi""" """Mene haɗin ki da FGC Maama?""" """Daddy Kinal zan raka suna yin taro na makarantar zan bita idan na tashi aiki"" zufa har fitowa daddy take" "a saman goshi sunan FGC ba ƙaramin gigita masa lissafi ya yi ba. ""ba za ki ba"" shagwaɓe fuska ta yi ""don Allah daddy wallahi na ji ina son zuwa""" """Wallahi mistakenly kika je shegiyar makarantar nan sai ranki ya ɓaci kuma sai kin daina fita hatta aikin" sai kin ajjiye. Wallahi Safiyyerh Abdu Marafa idan kika je za ki san waye Abdu sai na zane miki jiki da "carbi ko bulala"" ta yi ƙasa da kanta zuciyarta duk babu daɗi idanunta na cika da hawaye tun tana ƙarama take yin biyaya a komai akan abin da ya yi crossing da buƙatar daddy." "Hannunta riƙe da jakarta ɗaya hannun wayarta data kara a kunne suna magana da Kinal, duguwa ce" "hakan yasa bata fiya saka takalmi mai tsayi ba suit ce jikinta as always fara tas mai riga da wando ta yi rolling da black ɗin mayafi idanunta sanye cikin wani shade glasses mai kyau a hankali take tafiya tana ɗan jinjinawa mutanen kamfanin kai with so much respect tana da girmama mutane kawai rainin hankali ne bata ɗauka ""Kinal ki je kawai idan na koma gida za mu yi magana, daddy ya hana"" yadda ta yi furucin" ya bayyana ainihin abin da take jin a zuciyarta. """To shikenan nima na zo studio ne zan yi waƙa idan na koma gida zan shirya za mu yi video call na nuna" "miki cikin FGC ɗin"" Fiyya ta ɗan taɓe baki daidai lokacin da take isa bakin ƙofar office nata security ya" "matsa ta buɗe ta shiga ta buɗe idanu ganin Ashraf zaune a office ɗin ""Kinal mu yi magana anjima"" ta cire" wayar tana kallon Ashraf daya miƙe tsaye yana mata murmushi """Kuma da permission ɗin wa ka shigo?""" """Wake neman permission idan ana batun ganin mata, na zo ganin matata ne"" ta ajjiye jakar hannunta" "tana zama saman duguwar kujera ""Sannu mai mata"" ya miƙe ya dawo kan kujerar yana leƙa fuskarta" """Miji ɗaya gare ki a duniya kuma nine"" cikin wasa ta ce ""Ai kowa ba zan aure ka don ka ji""" """Funny Fiyya"" a yanayinta na rashin damuwa da soyayyar ta ce ""How are you?"" Yana kallonta yana ji" "wani abu sosai game da ita ""Fiyya na yi kuskure wallahi bana sanin ina shige limit ɗina sai na yi wani abu. Ni na san ba wani sona kike ba amma idan kika yi haƙuri watarana za ki ji son nan ko yaya ne kullum kina ƙara nesanta kan ki dani yayinta zuciyata ke ƙara kusanto kanta gare ki. Komai da lokacin shi idan mukai aure muka rayuwa inuwa guda I'll definitely be honest to you, ina jin kishin ki a ƙirjina ne a nan nake ji" "kina mini motsi Fiyya"" ya nuna ƙirjinsa saitin zuciyarsa sai ya ɗan juya gwanin tausayi" """Amma bakya so na""" """Who told you that?""" "Ashraf ya buɗe idanunsa ""When are you gonna tell me you love me?"" Tana kallon shi tana murmushi ita" "tana son shi sosai kawai bata san ya zata nuna bane sometimes rigimarsa ke sawa ta bijire itama ta miƙe tsaye tana danna kiran number messenger bayan ya ɗaga ta ce ""Call Md for me, ka kira mini Md da Secretary hadda accouter"" ta ajjiye ta ce ta haɗa shayi a cup guda biyu ta saka cokali tana miƙawa Ashraf" "ɗaya idanunta cikin nasa ta ce ""San da aka kai ni gidanka matsayin mata"" ya lumshe idanu ya buɗe" """I'll wait as far as you're with me. Abin da kawai nake buƙata shine ki so ni. Ki so ni ko da kaɗan cikin" "yadda nake sonki ne""" ***** Anty Hameeda na sunkuye a madaidaicin parlon gidanta tana duba jarkokin lemon ginger ɗin da take "siyarwa ta ji hucin mutum da sauri ta miƙe sai kuma ta yi baya a razane ganinsa tsaye a gabanta yana waige-waige kamar wanda aka biyo ga wani irin yanka a ƙarƙashin wuyansa da alama yanzu akai masa jini ja zuba, ya yi zuru-zuru sai huci yake yi naman jikinsa musamman na ƙirjinsa na motsawa ""Ɗan autan Ammo wannan hucin fa kamar an biyoka wani abun ka yi? Wane ya yanke ka haka me ka yi masa?"" Bai kula ta ba ya juya ta bi bayan shi kitchen taga ya nufa ba jimawa ya fito da kwanon abinci daidai nan" wata mata ta fito tana ganin Mai dawa ta yi saurin sakin butar hannunta ta ce """Wannan tantirin ƙanin naki uban ne ya zo yi mana a gida? Yaushe ma aka sake shi innalillahi wa'inna" ilaihirraji'un mugun ji da mugun gani Ubangiji ya kare Allah wadaran ƴan daba ya tsine musu albarka ya "saka su fita a cikin ajalin su"" matar ta faɗa hawaye ya cika idanun Anty Hameeda ta ce ""Baba ina laifin ki" "ce Allah ya shirya ɗa fa na kowa ne bawa kuma sai me shi, ciki ne mai haife-haife baka san me Ubangiji" "ya ɓoye ba suma fa ƙaddara ce ba wanda ya zaɓi yadda rayuwarsa zata kasance""" """Ai duk wani ɗan daba ƙarshe wulaƙantacciyar mutuwa ce ko idan sun sha ta faɗa musu babu daɗi su" "kashe kan su, ko kuma su haukace garin shaye-shaye ko garin faɗan daban su a kashe su. Allah wadai"" Moh dai bai yi magana ba abinci kawai yake ci hannunsa ko wankewa bai ba duk jini Anty Hameeda ta shige ɗaki bayan ta share hawayen idanunta lemo ta ɗakko masa da ruwa ta ajjiye tana kallon yadda kusan rabin fuskarsa ya yi tabo da yanka yaro ba ya kalle shi ihu zai yi ba annuri a fuskar nan. Duk yawan abincin ya cinye ta sha ruwa ya shanye lemon tas ""Na Ammo yanzu kana jin abin da ka zaɓawa rayuwarka shine daidai ka ji tausayin mu don girman Allah. Wallahi daka kasance cikin wannan rayuwar gwara ka dinga aikata abubuwan da kake a baya, jibi yadda ka yi muni ka zama ƙazami sai warin dauɗa kake yi. Na je gida sun ce sun fi sati uku ko gilmawar ka basa gani wai malam aure zai ƙara kuma da ƙyar idan ba Ammo zai saka ba, na rasa wake bashi kuɗi ya fi son ya yi ta auri saki ana haifa masa yara yana" "kasa kulawa da tarbiyyar su""" Tamkar bada shi take ba haka ya yi ko gezau can ya miƙe tsaye ta ciro kuɗi dubu ɗaya ta bashi ya kalle ta ya kalli kuɗin idanun nasa a rine kamar gauta yaƙi amsar kuɗi ganin inda ya nufa hannunsa riƙe da wuƙa ya saka Anty Hameeda ihu ta ce """Me za ka yi ka rufa mini asiri kar ka kashe mini aure na shiga uku"" ko kallon ta bai yi ba, ya ɗaga labulan" "ɗakin Baba tana sujjada ya same ta. Tsartuwa ya yi ya fito da kunama ya cilla mata a cikin hijabi kafin ta ankare ta ɗago jin abu na bin bayanta kamar kunamar tsafi ta shige mata riga ya zaro askira ya daidaici ɗuwawunta ya lafta mana wani uban yanka, baba ta saki ihu tana ta shiga uku ya yi saurin fita askirar na" zubar da jini da. Yana fita su spider suka rufa masa baya. A cikin wani kango ya kwanta ya yi shiru cikinsa zafi saboda faɗan da sukai da ƴan cikin gari akan fita wajan kamfel da sukai kilashin. Ya rufe idanu zuciyarsa na buɗewa wani irin ɗaci yake ji a cikin maƙoshinsa wani a ya tokare masa kamar yanzu komai ke faruwa haka yaga magic ɗin idanunsa ke hasko masa bidiyon komai ta ciki inda take tsaye. Yana zaune a gida a lokacin yana jin yadda karatun Almajirai ya cika masa kunne ya yi kicin-kicin da fuska. "Ammo ta kalle shi ta ce ""Yau kuma waya taɓa jarumin Ammo?"" Ya yi mata shiru don bai fiya cewa komai ba idan ran shi ya ɓaci kafin ta sake magana wani yaro ya yi sallama ya ce ""Wai bestie ya zo in ji bestie""" """Waye bestie? Injiwa jeka tambayo""" "Mutallab a lokacin bai motsa ba ya hakimce kamar sarki kansa a ƙasa yaron ya dawo ya ce ""Wai in ji" "Safiyyerh matar Mutallab bestie""" "Baki buɗe Ammo ke kallon Mutallab ta ce ""Na Ammo yaushe ka yi aure bani da labari yau naga abin da" "ya fi ƙarfina, yara ƙananu daku wacece Safiyya"" ya miƙe tsaye daga shi sai gajeren wando ta wata riga ƙarama ""ban san ta ba""" """Ikon Allah""" Fita ya yi yana shan kunu ganinta tsaye suna haɗa idanu ta yi ƙasa da kan ta. Ya dinga kallon ta yana jiran "ya ji mene ""meye ne?"" Ya tambaya." "Hawaye ya gani a idanunta fal ""Ni a gidanku zan kwana"" tar ya gama buɗe shanyayyun idanunsa a kanta" """wanne gidan?"" Ta nuna masa gidan ""sai ki ce ke wa?"" Tana masa shagwaɓa wacce daman ya san hali" """Matar Mutallab, baka zo makaranta ba yau ba kyau fashi"" da wani irin ƙarfi ya ce ""Safiyyerh!"" Gani an yi" kanta. *** “Safiyyerh” ya ƙwalla kiran sunanta yana zabura kamar yanzu ne abin ke faruwa jikinsa duk rawa "yake ganinsa shi kaɗai a kangon ya saka ya kifa kansa zuciyarsa na wani irin tsalle tana huci jijiyin kansa sun fito sun yi kwance saman kan shi. Ƙwayar Rohypnol ya ɓalle ya haɗiye har huɗu ya yi shiru jikinsa ya yi weak yana ganin kangon na jujjuya masa lokacin gudu yadda idanunsa suka gane masa cikin jini kwance saman gado ya sake faɗo masa, ya dinga jujjuya kansa ƙwaƙwalwarsa ta tsaya cak kamar wacce ta yi hooking da sauri ya zaro takardar daga cikin aljihu tsoron ƙara kalla yake ya yi saurin damƙe ta cikin hannunsa sai kuma Ammo ta faɗo masa a rai bai damu da jinin dake fita a wuyansa ba ya yi kwance a" ƙasa shi kaɗai kamar maraya. "Yammaci liƙis yana zaune gaban ta, ya kalleta a karo na farko ya ce ""Me ya sa kika buƙaci na ce ina son" "company?"" Abbasa ta ajjiye abin hannunta ta kalli cikin bukkar ta ce ""Sanda ka faɗa mini waye Mutallab," ka bani labarinka zan faɗa maka hujjata tare da dalilin cewa ka cewa Ali wali kana son kamfanin FS "WORLD INVESTMENT COMPANY""" """Bakya tsoro na kashe ki?"" Ta dube shi ta saka hannu tana goge masa wajan ciwon ""ba zaka iya kashe ni" "ba babu abin da zaka iya yi wa Abbasa. Ya batun zama mata mazan? Mene dalilin daya saka kake so ka zama?""" """Bana son haɗa danganta da kowacce kurciyya, ba idan aka yi baru aure kenan ana wani abu ba, to bana" "so ba wacce za ta yi sha'awar zama dani mata uku kenan babu su saboda ni ki mayar dani mata mazan""" """baka watarana zaka iya buƙatar lafiya ko kasancewa da mace""" """Sai godiya kafin lokacin na cika muradaina na baza ƙiyama ki mayar dani"" ta dinga kallon shi ta ce ""Ka" "tabbata ka yi tunani""" """Ki aikata kawai""" """An gama, riƙe wannan"" abu ta bashi ya amsa ya sha ba jimawa bacci ya ɗauke shi. Bai san lokacin daya" shafe ba sai farkawa ya yi ya gan shi an wanke masa ciwon an saka audiga ya yi shiru yana jin he just missed something very important. Message ɗin Eng Ali wali ya gani kan yana son ganinsa da gaggawa ya tura masa address ɗin wajan. Mai "dawa na tsaye yana kallon Eng Ali wali da ya yi badda kama ya zame facemask ɗin fuskarsa yana kallon Mai dawa ya ce ""Mai dawa"" bai magana ba sai fito yake yi." """Abdu Marafa ya shiga gidan rediyo yau da safe ya sake jaddada ra'ayinsa akan ƙin takara ta yana kuma" "janyo hankalin matasa da su farka a daina amfani da su, domin yanzu matasa sunw siyasar wannan mazanin. Gwara youth su haɗa ƙungiya suna fitar da wanda suke ganin ya cancanta ya zana shugaba ba irina ni Eng Ali wali ba. Mutallab a fara shirin ɗakko yarinyar nan yadda zamu saka harshen Abdu Marafa" "ya yi laushi dole zai kawo kasa ya yi mubaya'a a gare ni Eng Ali wali"" Mutallab dai ya yi shiru abin shi." """Mutallab ina magana ka yi shiru?""" """Yau kake so a kawo ta ko gobe? Kai yanzu tukun mene ra'ayin naka akan matasa?""" """Bangane ba""" """Ka gane mana, ka zama ɗan halak cikin gyatuma idan ka ƙi cika mini alƙawari bayan cin zaɓe zan maka" jahilci. Jinin malam Abdullahi ke guna a jikina idan na so dole na janyo maka farinjini amma na daina wannan sabgar yanzu. Na rantse da ɗan Amina ka yi mini ba daidai ba za kaga ba daidai ba ɗan malam "nake ka daina ganina haka"" Ali wali yace" """Ai kai ƙanina ne, amma waye kai? Zan so jin tarihinka ka faɗa mini waye kai Mutallab?"" Nan da nan" "Mutallab ya sake haɗe fuska tamau ya yi shiru. ""Shikenan zan maka komai ka tabbatar ka sato mini" "yarinyar nan babu lokaci ban san me Hon Maɗatai yake shiryawar ba amma shirun da ya yi yana nufin komai. Sai batun nemo Scorpion""" """Zan tafi zan aiko Mangal anjima"" yana faɗin hakan ya fice kamar walƙiya." "Kwana biyu da faruwar abin da Captain ya yi bata ta ɗauke walwala daga gidan kodayaushe tana sama," "tun lokacin bata sake jin motsin shi ba. Abubuwa da yawa ke damunta yadda ciwon kai ke damunta tana jin kamar ana jona mata wani abu, bata iya bacci. Ga matsalar kamfani da kullum manyan kuɗaɗe ke shigowa cikin asoson kamfanin an rasa daga ina? Ta yi duk binciken daya kamata ta kasa gano bakin zare masu gadi sun tabbatar mata da cikin dare manyan motoci na zarya a kamfanin hakan ya saka ta ɗauki niyyar dole yau zata saci hanya ko wajan ƙarfe ɗaya na dare ta fita tana jin hakƙin kula da kamfanin yana kanta ne. Ta ƙara adding number cikin jerin numbersa ɗin abubuwan da take buƙatar sanin abu kai ma'ana hadda hujjar daddy na hanata yin wasu abubuwan. Miƙewa ta yi tare da yin wanka ta tare da alwala ta gabatar da sallar issha ta yi addu'a sosai da azkar wanda ke sanya mata nutsuwa tare da kusantata ga Ubangiji. Fiyya ta dinga kallon kanta cikin madubi sometimes tana jin kamar ba ita ba, she" missed the old Safiyyerh. Buɗe ƙofar akai tare da shigowa """Zaman ɗaki manager ta fara kenan?"" Murmushi kawai ta yi tana juyawa ta saka hijabi" """Yaya J, how are you?"" Ya yi murmushi" """Nothing without manager, ki fito daddy na kira an kawo invitation card"" ta haɗe fuska ya yi baya yana" "ɗaga hannu ya ce ""cut me out Fiyya da kan shi ya saka akai yi komai"" ""wai dole sai an yi mini aure ko me daddy ke tsoro?""" "Shiru J ya yi sukai waje ta samu Dr Hash zaune ta ce ""Dr good day, ina gefen kan mutum na ciwo yana" "ganin reflection na wasu abubuwa what was the problem?""" Dr Hash ya ɗago kai haka J da kuma Marafa Ummi ma kallo Safiyyerh take daddy na zaune yana ji bai "ɗago ba. Ta buɗe musu manyan idanunta Dr Hash ya ce ""Me kike gani?"" Kawai ta haɗe fuska ta ce ""babu"" wajan daddy ta ƙarasa ta durƙusa har ƙasa ta kashe shi ya miƙo mata waya Ummi ta ce ""Ki zaɓi furnitures ɗin da kike so"" ta yi sak tana kallon su dai daddy ya Aman wayar ya ce ""Babu buƙata, zuciyata ta kasa nutsuwa zan yi requesting da an ɗaura auren kawai Ashraf ya bar ƙasar dake"" da sauri ta kalli daddy ""Daddy aikina fa?"" ""Za ki bar aikin"" ta girgiza kai ta ce ""ba zan maka musu ba daddy kai mahaifina ne ina yin biyayya a komai, amma don girman Allah ka bar ni daddy akwai binciken da nake yi a kamfani da zarar na kammala zan je duk ƙasar da kake so idan ma ƙare rayuwata ne a can zan yi"" daddy bai kulata ba ya miƙe ya bar wajan J yana jin babu daɗi Ummi ma ta yi shiru babu yadda za ta yi da daddy idan abu akan Maama ne sai dai a kalle shi ta jawo Fiyya jikinta ta dinga bata haƙuri tana kwantar mata da hankali, Fiyya ta rungume Ummi tana kuka. Kamar kullum J Kalla ne yake sanar da an samu gawar wani babban mutum mai suna Alhaji Haladu da aka shiga aka kashe har gidan shi ana kuma zargin Scorpion ne saboda shaidar daya bari na sunan Scorpion a jikin bango. Ta dinga kallon screen ɗin t.v sai" "kuma ta miƙe ""kin ci abinci?"" Ta girgiza kai ""na ƙoshi an yi mini formatted folder a wayata Yaya J""" """Formatted kuma ko dai kin shiga wani wajan ne"" ta ɗaga masa kafaɗa ranta duk a ɓaci. Kwanciya ta yi" sukai waya da Ashraf yana ta mata maganganun masu daɗi har ta yi bacci. "**** Idanunta ya kalla muryarsa a hankali ya ce ""There's something about you that make me feel like" "you actually use magic about me, many things I do because you, many things I don't even know or remembered when I started doing them. The love I have for you is so real baby. Yet, ban san me ya sa zuciyata take yawan bijiromin da kokwanton yiwuwar samunki a rayuwata ba. I love you Safiyyerh""" “I love you Safiyyerh” A gigice ta farka daga baccin tana ihu da ƙanƙame pillow jikinta na rawa sosai da ɓari da sauri Daddy ya "buɗe ƙofa ya shigo haka Ummi da Yaya J wajan karfe biyu na dare ""Fiyya mene? Maama mene?"" Ta" sakko daga kan gadon a gigice ta nufi wajan daddy bakinta na rawa ta kama hannun daddy ta ce """Mutallab daddy, Mutallab who is Mutallab?""" For more information akan littafin MUTALLAB. Via 08164069385 WhatsApp only Na'ima Sulaiman Sarauta Assalama alaikum Hajiya muna da ingantaccen maganin gyaran nono wadda ya amsa sunansa magani Maganinmu ingantaccen maganine da yake tada jijiyon nonon da suka saki y'ar uwa breast dinki ko yakai silifas saboda kwanciya kikai amfani dashi in sha Allah zakiga amfaninshi acikin 1week maganinmu powder ne yana ciko da breast y gyarasu bashi da illa ajikin mutum munyi amfani da saiwoyi da magunguna gargajiya domin gyaran breast 08063114606 ina garin kano karki sanya y'ar uwa nono yana karawa mace martaba a gurin mai gida maganinmu kowa zai iya sha wadda zatai yaye ko gyara budurwa duk zasu iya sha breast dinki ya ciko yayi bull -bull "[10/13, 10:53 PM] Nanameera: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 8 *Bright pens... 2nd batch* """Daddy na ji kamar gangar jikina ta wanzu da wannan mai sunan, na ji ƙirjina ya mini nauyi numfashina" "ya taɓa gauraya da nashi daddy ina jina kamar bani ba, daddy who is Safiyyerh? Daddy tell me something about me, don Allah wallahi zuciyata bugawa take i missed something very important..." "Daddy!""" "Ganin duk sun yi mata shiru ya saka ta girgiza daddy da hannunta biyu ""waye Mutallab daddy?"" Duk" "suka sake yi mata shiru kamar basu fahimci me take nufi ba Dr Hash da bai jima da shigowa gidan ba saboda aikin kwana ya yi a asibiti ya nufi inda Fiyya take tsaye yana leƙa fuskarta ya ce ""Mutallab kuma?"" Ta kasa magana sai bin su take da idanu daddy ya yi namijin ƙoƙarin wajan kama kafaɗun Fiyya ya ce ""Maama waye haka? Kinga irin abin da nake faɗa miki akan muhimmanci da ƙarfin addu'a kina sake da" "gaske kina wasa da azkar""" "Sakin daddy ta yi ta nufi wajan Ummi ta ce ""daddy na san ke za ki faɗa mini"" nan ma Ummi ta kama" "hannun Fiyya ta ce ""Mamaa ban san me kike nufi kowa kike magana akai ba, kamar mai iskokai ki farka kina surutai mene haka kike safiyyerh?"" Da sauri ta saki Ummi ta nufi wajan Yaya J ganin ta nufu shi ya yi saurin juyawa ya fita da sauri yana dafe kan shi. Fiyya ta sake juyawa wajan daddy jikinta duka rawa yake da ɓari kamar mazari ta kama hannun daddy ta ɗora a saitin ƙirjinta idanunta na cika da hawaye bakinta" na rawa da ƙyar ta ce """Ni ban buƙaci sanin wani abu bayan hakan ba, ban ce dole na san wani abu ba ka yi mini alfarma ka" "faɗa mini waye shi waye Mutallab? Daddy please...!""" Kasa magana ta yi jin an tsira mata sirijin allura ta runtse idanunta ta saki daddy ta juya a hankali ta kalli "Dr Hash ta sake nutsa ganinta cikin idanunsa ta kalli allurar hannunsa sai kuma ta yi murmushi ta sake juyawa ta kalli photon daddy dake gefen gadonta ""why? Me ya sa ake mini allura daddy i love you"" sai kuma ta lumshe idanunta jikinta ya saki ta ji kanta ya mata nauyi tunaninta na ruɓanya gudun zuciyarta na ƙaruwa, kamar wacce ake yi wa updating haka take jin ƙwaƙwalwarta ganinta zata faɗi ya saka daddy ya riƙota ya jima bai ji tausayin abu ko wata halitta a duniya irin Fiyyarsa ya dinga kallon fuskarsa cike da so da ƙauna a hankali ya kwantar da ita saman gado ya ɗora kan ta a saman cinyarsa ya dubi Dr Hash ya" ce """Hashim ya zan yi da Fiyya ta fahimta me zan yi Hashim, Awais ya ya zan yi da Maama?"" Ya faɗa yana" kallon Marafa duk suka kasa magana Ummi idanunta ya yi jajur baccin da basu koma ba kenan sukai spending sauran lokacin wajan Fiyya sai addu'a yake yi mata. Dab da asuba ya miƙe ya fice daman shi ya yi saura ya kulle ƙofar. Duk da nauyin da kanta ke mata bai hana ta motsa ba saboda kiran sallah wanda hakan alama ce ta "cewa kai musulmi ne da zarar lokacin asuba ya yi dukkan wani rai a duniya daya kasance musulmi sai ya motsa, bakinta ɗauke da addu'a ta ce" ” لاَ ْ ُ هلل لاِ ي أْ َ انا َ ْ ُ َ ا أَ اَ َ ا إول َ ه "لاَ ُ رو""" "muryarta da ƙyar take fita a hankali ta ji an ɗan matsa hannunta, ta motsa yatsun hannun ta ji shi sarƙe" "dana wani ta rufe ido ta san cewa Yaya J ""ni ka cika mini hannu""" Ya buɗe ido ganin yadda ta murguɗa masa baki bai motsa ba a hankali ya zare yatsun shi ganin tana ƙoƙarin juyo da fuska zuwa ina yake ya miƙa hannu da sauri ya kashe hasken ɗaki the same time ya miƙe ya fice yana rufe ƙofa ta bi door way ɗin da kallo. **** Ammo na zaune a cikin ɗaki kamar yadda ta saba kodayaushe Malam ya ɗaga labule yana daga tsaye ya "kalli Ammo ya ce ""Ba dai tunanin wancan gantalallan kike ba? Kamar wacce aka ce na mutu kike takama ki yi ni ɗaki kwana ɗaki, to idan ma shine ki sawa zuciyarki ruwan sanyi da salama ki sallama shi, yanzu ke ba kifi samun nutsuwa ba da bakya ganin gilmawarsa yana saka miki faɗuwar gaba"" ita dai bata tanka shi" ba ta cigaba da aikin da take yi. Ya sake duban ta da kyau yana furta """Aure zan ƙara na hango wata ƴar duma-dumar bazawara fara tas sakin wawa ku yanke shawara a cikin" "ku wa zan saka"" a sanyaye ta ce ""Allah ya sanya alheri, duk wacce ka saka babu komai ko ni ɗin ce""" Malam ya juya zai fita Anty Hameeda ta shigo idanunta zuru-zuru alamar ta yi kuka gaban malam ya faɗi "ya ce ""mene kuma Hameeda?""" """Malam wajanka na zo da Ammo don Allah ku saurare ni"" ya yi jim sai kuma ya yi ɗakin Ammo ta bi" "bayansa gaishe su ta yi kafin cikin sanyin murya ta ce ""Ammo ke uwa ce kin ɗauki cikin Mutallab watanni wajan 11 ɗaya yake zaune kafin ki haishe shi, kin ji zafi da raɗaɗin naƙida wajan haihuwarsa, kin shayar da shi kin goya shi a bayanki, kin bashi abinci, kin ƙaunaci Mutallab sai dai ƙaunar da yake miki kamar har ta ninka wacce kike masa, idan bashi da lafiya baya yadda kowa ya taɓa shi sai ke ban san yaushe ne ko yaya ne ya zama haka ba, labarin da nake da shi akan Mutallab ba cikakke bane, zamana a Lagos ya saka ban san wasu abubuwan ba, kin ƙi faɗa mini yadda ya zama haka kin hana a faɗa mini, shin bakya jin rauni irin na uwa? Ƙauna irin ta uwa da ɗanta, duka bakya jin hakan kike barranta kan ki da autanki Ammo, hannunka baya taɓa ruɓewa ka yanke ka yar kar ki manta kalmar da ake cewa idan ka ƙi naka duniya ta so shi, idan ka so naka duniya ta ƙi shi, Ammo ga duniya da bakin jama'a na rige-rige kai" "Mutallab kabari idan kyautata zaton watarana za a kashe shi ko ya je inda ba zai taɓa fitowa ba..,""" """Allahamdulilah da zai mutum ai da ya sawwaƙa mini da ƴan'sanda Mutallab masifa ya zame mini ni na" "gode Allah da bana ganinsa cikin idanuna"" kallo malam kawai Anty Hameeda ke yi da ƙyar tana haɗiye abu mai ɗaci a maƙoshi ta ce" """Dukkan iyaye suna saka hannu cikin abin da ya fi gaban sanin mutane.Kowannen su yana ba da kaɗan" "daga jikinsa. Ta haka, abin da ya yi girma a cikin uwa ya zama mutum. Saboda haka, ba abin mamaki ba" "ne, sa’adda da aka haifi jariri, mutane sukan ce _mu’ujizar haihuwa_ , haƙiƙa, haihuwar yara ita ce" "hakƙin iyaye na farko. Da farko, jarirai suna dogara ƙwarai ga iyayensu, amma sa’adda da suke girma," suna buƙatar fiye da a mai da hankali ga abincinsu kawai. Suna bukatar taimako domin su yi girma a "tunaninsu, a motsin rai, a ɗabi’a, da kuma a ruhaniya." "Domin su yi girma da kyau, yara musamman suna bukatar iyayensu su yi ƙaunarsu. Ko da yake yana da" "muhimmanci a furta kalami na ƙauna, ya kamata ayyuka su tokara hakan. Haƙiƙa, yara suna bukatar misali mai kyau daga iyayensu. Suna bukatar ja-gora a ɗabi’a, mizanai da za su bi a rayuwa. Kuma suna bukatar wannan tun suna ƙanƙanana zuwa gaba. Abubuwa masu ɓata rai suna iya faruwa kuma suna" "faruwa sa’adda da ba a taimaki yara ba har sai da ya makara"" kukan da take dannewa ya ci ƙarfinta" """Ammo idan Malam bai fuskanta ba ki daure ki gane don girman Allah, shi kaɗai autanki ɗanki tilo ɗaya" "namiji da Allah Ya ba ki idan babu ranku shi ne zamu kira da sunan uba, zai mana walicci a ko'ina bai kyautu don ƙaddarar Ubangiji ta kitta a rayuwarsa ku ce za ku juya masa baya ko wofitar da rayuwarsa har haka ba, akwai hakƙin iyaye akan yara haka akwai hakƙin yara akan iyaye shin kina buƙatar Ubangiji ya tuhume ki da hakƙin Mutallab? Allah da kan shi cikin hadisi mai girma ya ce; ƴaƴanku amana ce kuma kiwo ne a gare ku, lallai za mu tambaye ku wannan amanar da kiwon idan an ce ki faɗi inda yake a yanzu ba za ki faɗa ba wannan abun da kuke kun bashi dama da lasisin ƙara lalacewa ne idan yaro ya ɗaƙko" "hanyar kangara jawo shi aje jiki a nuna masa ƙauna da soyayya""" "Miƙewa ta yi tsaye tana share idanunta ""ya zo mini jikinsa duk sara kamar korarre mara iyaye a duniyar" "nan har na yi na gama magana bai tanka wani kuskuren iyaye ke haddasa shi""" Tana kaiwa nan ta fice abin ta inda ta shige Inna Binta da Mama Zaituna na kokawa akan wani ƙanzon "tuwon da aka baza ya bushe sai ya yi gwanin sha'awa tana ɓantara da kaiwa baki ta ce ""eh, kya yi kya gama wannan ƙanzon sai na bawa Mufee ke ni fa akan abinci ba wani kirki gare ni ba, ba zan zauna yunwa ta yi ajalina a gidan nan ba, tunda mai gidan zuciyarsa a mace take bai san fus na hakƙin iyali ba sai auri saki da tare yara kamar ƴaƴan ɓeraye kowanne kana kallonsa yunwa zata fara maka sallama a jikinsa haba me ake da hali na..."" Da sauri ta yi shiru ganin malam tsaye ta yi mamaki da bai tanka mata" ba ya shige. Safiyyerh ta sakko daga saman bene tana yi tana duba wayarta ganin saƙon da Ashraf ya tura mata cewa ya ɗan yi tafiya ba ta yi reply ba ta riƙe wayar. Yaya J ta gani zaune ta juya masa manyan idanunta da suka sake fitowa farare tas ta ce """Office ɗin kenan?""" """Ina ni ina zuwa office banga yadda little sis ta farka daddy's favourite"" ta girgiza kai tana ɗan murmushi" "iya leɓe ta ce ""Yaya J kenan, good morning""" """Kin tashi lafiya sai ina?""" """Office, ina da meeting kuma Yaya J ka yi mini addu'a Please da wannan kyakkyawan harshen naka, zan" "baka labari mai daɗi"" ya ware hannunsa ya ce" """To ina jira ko na kai ki office ɗin?"" Ta girgiza kai ta juya tana nufar sashin daddy dake ƙasa. Fiyya tuni ta" "manta abin da ya faru ta manta wani Mutallab fresh take jin kan ta, tana ƴar waƙarta ta turanci tama" manta ta shigo parlon daddy dake zaune ya zuba mata idanu ta yi saurin rufe ba ki ta ce """Ka yi haƙuri daddy i enjoying when i sing a song, don Allah ka yafe wa Maama""" """Sai an yi magana idan kin yi laifi kina buɗe manyan idanunki kinawa jama'a turancin yaran zamani ke ba" "kowa naki da yake bature""" """To babana babban laccara ne wanda ake alfahari da shi dukkan matasa ke son shi saboda ƙoƙari da" "iyawar shi"" Fiyya ta ce tana zaman ƙasan ƙafafun daddy ""Tiger"" sak ta yi jin sunan da ya kira ta da shi," lallai an taɓa donganta ta sa wannan sunan na Tiger ta share kana ta gai da daddy. Ya amsa cikin kulawa duk motsin da take akan idanunsa Fiyya na da mugun wayo dana da wani "experience da Qualities bata yin abun da za a iya following footsteps ɗin ta, she is a clever girl faɗanta har tsoro yake bashi ga taurin kai da miskilanci har addu'a yake Allah ya sassauta mata sai gashi Ubangiji" ya gyara komai a lokacin da bai zato ba. Ya ɗauke kai yana kallon wani gefen """Aliyu yaushe ka dawo?"" Idanunsa a kan waya yana dannawa, wandon uniform na sojoji ne jikinsa sai" fara t.shirt tas wacce ta kama damtsen hannunsa ya saka p.cap ta sojoji fuskarsa kamar ya ce ya shiga uku can ya ce """Da daddare""" """Dare da yaushe? Aliyu kai kana son shigowar dare kamar mara gaskiya?"" Captain ya ɗan kalli daddy ya" "ce ""Tun 12""" """Kuma baka shigo ba me ya sa?""" """Kawai daddy"" ficewa ya yi yana cilla wayar a aljihu yana jin Fiyya na gaishe shi ko inda take bai kalla ba." """daddy ni ba zan iya ɗaukan wannan halin ba wallahi bai ishe ni kallo ba zan daina ko gaishe shi ina dalili, Safiyyerh Abdu Marafa na da class babu mai ɗaga mini shoulder, duk wannan abun da ya yi aure a waje ne yake soja"" Ranta duk a ɓace ta miƙe tana cewa daddy ta tafi ya ce ""Allah Ya tsare Manager ya shirya safiyyerh Abdu Marafa"". Kasancewar sauri take yi ta saka ta yi driving kamar zata tashi saman bata wasa idan tana kan titi, tana isa ta buɗe office ta shiga fahimtar da sabuwar envelope a table ɗin ya saka ta sa hannu ta ɗauka tare da buɗewa taƙaitaccen rubutu ne mai ɗauke da jan biro wanda ke nuna rayuwarta" na cikin matsala. A hankali ta fara duba consent ɗin da takardar ke ɗauke da shi tana ajjiye waya. "“Jarumtarki bai kai ki tsaya bincike akan FS WORLD INVESTMENT COMPANY ba, kina iya ɗaukan rubutun" matsayin wasa amma gargaɗi ne da jan kunne ga yara masu rawar kai irin ki. Ki tsaya da binciken da kike you're nothing but a manager” Ta dinga juya takardar a hannu tana jin confidence nata na ƙara hakan kamar wata dama ce aka haska "mata na nuna cewa lallai akwai ƙullalliyya a wannan kamfanin, kuma ta shirya buɗe faifai ko da za su yi zubaibai ƙwarya ne, ko da gaskiyar da take ƙoƙarin bayyanawa zai yi silar barin ta numfashinta daga ƙirjinta. Ta yi Addison na cikin abubuwan da take ƙarawa a binciken za ta yi komai ko hakan na nufin fito na fito da surukinta ne. Zama ta yi ta fara duba files na sabbin kayan da aka kawo can ta saka aka kira" mata accouter bayan ya shigo ba tare data kalle shi ba ta ce """Accouter kana buƙatar wani abu ne?""" """Allah Ya taimaki manager kamarya fa?"" Still bata kalle shi ba ta yi baya tana duba maganar da aka turo" "mata yanzu a waya ta ce ""kawai kuɗi idan kana so na buƙatun rayuwa""" """Ina jiran lokacin albashi ya yi ai nasan za a sallame mu da wuri"" ta ɗago idanunta masu sanyi ta zuba a" "kan shi sai ta cillo masa ƙaramin file ta ce ""na saka hannu ka yi signature as a accouter ka cire 1m a" "asusun kamfani na baka"" da mamaki ya ce" """Ni kika bawa kuɗin?""" """E, ko baka so?""" """To na ga ban yi wani aikin da na cancanci 1m ba kin sa na fara jin tsoro ba zan iya cin abin da ba haƙƙina" "ba"" ta ɗan yi murmushi ta janyo files ɗin ta yaga ta ce ""meye cikakken sunanka ma?"" Rainin hankalin" "Manager mamaki yake bashi sai kawai ya ce Wazeer"" da hannu ta ce ya je yana fita ta saka aka kira mata MD abin da ta yi wa Accouter shi ta yi wa Md cikin sauri ya ce" """Yanzu kika ɗakko hanya manager da za ki haƙa ramin da za ki iya binne kan ki ciki ai duk sai na raina" "wayonki wallahi da ajin nan naki ko mene a ƙasa ba ruwanki mind your own business rayuwar nan kana kallon wasu abubuwan kake yi kamar baka sani ba, to a haka cibiya ta rai ne mu kuma yanzu hankalin jama'a da yawa na kan siyasa, matasa na neman hanyar karatu, wasu na can suna bautawa ƴan siyasa, wasu sojan baka wasu rayuwar social media wasu bangar siyasa wasu kasuwanci. Safiyyerh da yawa ana yin abin da ya samu ne ko yazo hannu ba wanda kake ganin cancnatar shi ba, ba a duba capacity na abu ko a siyasa kana ji kana ganin wanda ya dace amma kake rufe idanu ka ɗauki baragurbi saboda yana watsa maka hatsi mu ɗin kamar ka ji suka ɗauke mu, think big Fiyya ke macace babu mai ce miki don me," "akwai kuɗin da shi kan shi Alhaji Baihaƙi bai sani""" """Kana son siyasa""" "Md ya yi murmushi ya ce ""Safiyyerh siyasa yanzu ai kusan a jinin kowanne matashi take, kinga muna da" "jam'iyyu uku ɗaya ce mai ƙarfi saboda ita ke riƙe da muƙami ma'ana ƙasar a nan Hon Maɗatai yake neman takarar kujera, sai jam'iyyar su Eng Ali wali sai last jam'iyya wacce mutumin cikin ta ya fi kowanne" "nagarta kuɗi masu dame shi ba, da ƙyar aka taushi zuciyarsa yake muƙamin kusan matashi ne matasa na" son shi amma kasancewar yana cikin jam'iyya ƙarama kusan sabuwa ya sa ba a yin maganar shi ma kuma "da ba musulmi bane"" Safiyyerh ta jinjina masa kai ta ce ""Ka bawa accouter ya yi signature a baka 2m, enjoy yourself MD, but sunan wanda kake bani bayani yanzu?""" "Ya washe bakinsa ba ƙaramin jin daɗi ya yi ba ya ce ""Abraham Denial David, shine ɗan takarar""" """Yana da hannun jari a nan ne?""" """A'a, i don't think zai saka hannun jari a nan gaskiya"" a hankali ta ce ""Me ya sa?""" """Kar ki zurfafa a bar maganar, za mu yi aiki tare"" sallamar shi ta yi tana jin zata yi amfani da Md da" accouter Md zai taimaka wajan sanyawa ta san sirrin kamfanin cikin sauƙi accouter zai taimaka wajan bayyana komai. A gefe guda tana jin kamar ta shiga batun siyasar Abraham ɗin kawai ta ji ya yi mata she just want to help him. **** "Su da kan su sun kwana biyu basu saka shi a idanunsu ba, ba kuma su samu labarin inda yake ba sai" "yanzu da suka ganshi kamar walƙiya kwance a ƙasa idanunsa buɗe yana kallon sama Darma ya ce ""Sai godiya wanda ya ce zai bi sawunka ya wahala, ɗan malam yaƙi halin malam dafinka ƙarinka masifa ne" "idan ka taɓa mutum da shi""" """Darma""" """Ka dake Mai dawa ka jima ka yi lastin irin na dabino, wa kake so a taka a kashe ko a yi masa fiɗa"" Darma" ya ce yana buɗe hannu sama tare da karkatar da baki hannunsa riƙe da ledar pure water ya nannaɗe a "hannu yana kaiwa baki tare da zuƙa. Mutallab ya sake buɗe idanu a sama ya kasa cewa komai tunaninsa ya tafi wani wajan. Goje ya ce ""Sai godiya matsalar goge ce ko wato ka kayan lantarki""" """Zaman gidan yari ba daɗi,amma na ji daɗi""" """Ka ce ka tuna na jakuna nan cinnaku tsakaninmu da su sai ƙarfe ba ma'ana ka tuna na jakin da suka" "haɗa maka kenan""" """Ina jin zafi a ƙirjina farcuna na da suka cire mini sun ƙi fitowa, zan ɗauki fansa Goje""" Kafin su yi magana an yi sallama an ƙarasu cikin sauri Mutallab ya rufe idanunsa jin muryar zabuwa. Goje "ya dinga kallon wacce take tsaye ""Bayin Allah sallama nake muku fa"" Mangal ne ya kalleta sosai ya ce ""Yi batu"" ta ɗan rausayar da kai gefe ta ce ""Amma dai ku musulmai ne amsa sallama wajibi ce""" """To alaiki, mene sagin aiki kike so a yi miki?""" "Kinal ta fito da littafi da biro ta ce ""Sunana Kinal ni mawaƙiya ce, har zan shige na hango ku na ji ina son" tambayarku na ji ina son na yi waƙa akan ku kasan mu da mu da marubuta kusan aikin mu ɗaya muna da "son bin ƙwaƙƙwafi"" Goje ya ce ""To ina ruwan mu? Fece kafin na yi miki lahani""" """Ku ba ƴan shaye-shaye bane? To akan shaye-shayen zan muku tambaya ina yin waƙar zan kawo muku" "ku ji, idan kun yi shaye-shayen me kuke ji mene dalilin daya saka kuka fara shaye-shaye kuma kuke harkar daba""" "Moh na jin su ya juya musu baya zaka ɗauka bacci yake, ransa duk a ɓace saboda jin muryar mace da ya" ji ya san daya juyo zai iya kashe ta tsaf don bashi da wani business da mata. Darma ya ce """Yanzu yadda muke ji za mu faɗa miki kenan?"" Kinal ta yi saurin cewa ""E, wallahi na iya waƙa ina da" "murya sosai babu mamaki idan na yi waƙar na saka a YouTube ta je viral na saka a tiktok ta yi trending"" Darma ya ce ""To ni dai tun daga sanda a gida na yi...,""Da sauri Goje ya tsayar da shi yana cewa ""Kai amma ɗan tsinanniya ne kai, ba haka ake bayani ba""" "Miƙewa ya yi ya ce ""bari na faɗa miki"" wuƙa ya zaro a ƙugunsa Kinal ta zare idanu tana yin baya cikin" "sauri Mangal ya tare bayan jikinta na rawa ta fasa ihu jin yadda Goje ya yanke ta da wuƙa a fuska,ya" danna mata ledan wiwin a baki ta fara zare ido tana ihu. Sai a lokacin Moh ya juyo yana kallon yarinyar ya cije bakinsa tare da juyawa exactly irin ihun da Safiyya ta yi lokacin zata mutu. """Gani ya kore ji, idan kin rero waƙar muna dakon ki a nan sata ƴar munafuka""" "Darma ya dinga tuntsira dariya sosai yana riƙe ciki ""Amma Goje baka da imani kamar fa fitsari ta yi a" "wando gaskiyar kurciyar nan akwai jan ido ga bayani nan kin gani ganin idanunki ai"" ya juya ya kalli Moh ya leƙa ga wata cukurkuɗaɗdiyya takarda yake karantawa shi ba wani karatu ya yi ba ""Wai wannan takardar mece kamar ta asiri kodayaushe tana wajanka, kamar numfashin shaƙa ka faɗa mana ta mece""" cikin sauri ya ɓoye yana damƙe ta a hannu Goje ya ce """Nima sai fakon farar nake na mata karatun makarantar allo, na rasa wacce tsiyar ce a ciki""" """Goje""" """Sai godiya""" """Zan saka maka tsini idan ka taɓa takardar nan ko na saka su tiger cinye ka ɗanye, wallahi zan iya kashe" "ka akan takardar nan""" "Kafin su yi magana an zo da babur an cillo wata takarda da sauri mai babur ɗin ya juya, Mangal ya miƙe" "tsaye ya ɗakko ya buɗe cikin sauri ya kalli Mai dawa dai kuma ya miƙa masa amsa ya yi ya duba, photo" "na gudu biyu ne ɗaya zanen fuskar wata kamar dai mahaukaciya sai kuma photo jira-jirai, photo me mai magana ga wanda yake da cikakken lissafi a gefe an rubuta FS WORLD INVESTMENT COMPANY." **** "Kwana biyu Safiyyerh ta yi busy duk wani family sun zo saboda gobe ne ake ɗaura auren, kamar auren" munafurci ba wata gayya ko shagali ɗaurin aure ne kawai ana yi kuma Ashraf zai ɗauki matarsa su tafi. A daren ranar Safiyyerh ta riga data gama accepting auren Ashraf ta yarda bata da wani miji sai shi zata sawa zuciyarta yadda zata zauna da shi tunda tana son shi ko ba can ba. Waya suka yi da Ashraf ya dinga "tsokanarta ""Har na hango idanun Maama a ɗakin miji, mijin na kuma Ashraf ta yi nasarar samun" "kyakkyawan saurayi"" ta murguɗa masa baki ta ce ""Zan fasa"" ya yi saurin cewa ""Idan ki kaga ba ki auri" "Ashraf to mutuwa na yi ko ke kika mutu, da gaske Fiyya ina son ki Allah shine shaida duk da ina dalilin auren ki ko saka ni akai na yi hakan amma na yi you're my life partner har janna in sha Allah""" """Kamarya? Mene dalilin auren?""" """Ke ba ki da wani favourite words ne sai kamarya, zan faɗa miki komai a daren ranar da kika zama" "halaliyyar Ashraf zan faɗa miki, zan sauƙaƙa miki binciken da kike akan Company"" a ruɗe ta ce ""Ta ya ya kasan ina bincike akan Company""" """Safiyyerh kenan, that's is the difference between man and woman, ina da baƙi sai goben idan na zo" "ganin matata a wannan lokacin dole na rungume ki halal runguma zan miki Safiyyerh"" hankalinta duk a tashe waye Ashraf ne me ya sa daddy ya amince da auren shi? Ta kasa magana har ya kashe kiran sai ya ƙara kiranta video call ƙura mata idanu ya yi taga yana shiri cikin sauri ta ce ""Kuma sai ina?"" ""Inda kika" "aike ni"" ta buɗe idanu" """Kamarya?""" """I miss you Fiyya shine abin da na manta na ce miki, a nan nake jin motsin ki"" ya nuna mata saitin ƙirjinsa," "daga nan ya kashe wayar. Daga ƙarshe ta yi zamanta cikin bedroom Awais har bedroom ya shigo ya dinga mata shira ""Yaya Aiwas ka ɗan yanke mini farce"" ""to ban taɓa ganin amarya irin ba tunda nake a duniya"" ya jawo ƙafar ya fara yanke mata farce ta rufe idanu." "Washegari da sassafe Fiyya na bacci daddy da kan shi ya tashe ta, ta farka da ƙyar saboda kan ta dake" "ciwo mamaki ta yi ganin kusan family a ɗakin ya kalleta ya ce ""Kin dai yi sallah ko?"" Ta ɗaga masa kai ""Daddy lafiya?"" Ya yi shiru ya ce ""Junaid je ku fara yin gaba, Captain an kira shi yanzu daga can headquarter, Ummi ɗakko mini hijabin Maama"" Hijab ya karɓa ya saka mata ya riƙe hannunta Anty Turai ta yi gaba tana zabgawa Fiyya harara har harabar gidan suka je, abin mamaki gidan shiru ta rasa meke faruwa a motar daddy suka shiga yana baya riƙe da ita Awais na jan motar da Ummi. Motar Fiyya kuma da ita Captain ya yi using wajan fita saboda shi bai Fiyya ɗaukan tashi ba. Fiyya ta yi shiru kan ta a ƙasa,har suka ƙarasu cikin babban gidan mai tarin jama'a daidai lokacin aka fito da shi daddy na riƙe da" "hannunta ya ce ""Mamana je ki masa addu'a""" """Addu'a? Daddy waye?"" Ta furta muryarta na rawa ta juya ta kalli makarar da aka ajjiye gabanta ɗauke" "da gawa, ya sake riƙe hannunta da kyau ya jata zuwa gaban makarar ya duƙa tare da yin namijin ƙoƙarin buɗewa. Fiyya numfashinta ta ji ya ɗauke lokacin da idanunta ya yi arba da gawar Ashraf dake kwance cikin makara, jira ya fara ɗaukar gangar jikinta da gaske Ashraf ne kwance ba yau aka ce za a ɗaura musu aure ba shine zai mutu anya gawar Ashraf ce numfashinta ya tsaya cak tana daga tsayen suka ji ta yi" "wani irin ajjiyar zuciya tare da yin baya cikin sauri a tare daddy da J suka tare ta, ta ƙarasa suma a jikinsu." Bayan sallatar gawar Ashraf da binne shi duk ana zaune ana addu'a daddy ya ce yana neman alfarma "don Allah suka ce tame ""Kar a tambayan hujja ko dalili a yanzu ina son a ɗaura auren Safiyyerh da Aliyu""." "*฀for now na san a ranku za ku yi ta wasu wasu, wasu ma su ce ba su gane inda labarin ya nufa ba ku" "dai nutsu tafiyar kura ce mai tsarƙaƙƙiyya har nishaɗi kuke bani idan ana comment tafiyar da hasashe ku lissafi ba zai taɓa kawowa tunanin mutum ba, kar ku ji kun karaya domin na san dole a gaba zaku buƙaci" "labarin, har yanzu shimfiɗa muke yi iya shafi 8 mukai*" Littafin MUTALLAB na kuɗi ne kuma za a ke yin posting kullum. An fara biya yau domin shiga paid group na MUTALLAB. MUTALLAB. "Book 1, 2 &3" 500 Naira 0116886423 Union Bank Na'ima Sulaiman S. A tura shaidar biya ta nan 08164069385 ku yi ku biya a sati uku mu kammala ฀ Domin gyaran nono ❤🔥🔥💃 Assalama alaikum Hajiya muna da ingantaccen maganin gyaran nono wadda ya amsa sunansa magani Maganinmu ingantaccen maganine da yake tada jijiyon nonon da suka saki y'ar uwa breast dinki ko yakai silifas saboda kwanciya kikai amfani dashi in sha Allah zakiga amfaninshi acikin 1week maganinmu powder ne yana ciko da breast y gyarasu bashi da illa ajikin mutum munyi amfani da saiwoyi da magunguna gargajiya domin gyaran breast 08063114606 ina garin kano karki sanya y'ar uwa nono yana karawa mace martaba a gurin mai gida maganinmu kowa zai iya sha wadda zatai yaye ko gyara budurwa duk zasu iya sha breast dinki ya ciko yayi bull -bull "[10/15, 2:30 PM] Nanameera: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 9 *Bright pens..2nd batch* """Bani da wani zaɓi sai na hakan, haɗa auren Aliyu da Safiyyerh kar ku tambayan dalili kar a tambayan" "cikin Safiyyerh da Aliyu waye ba ƙwayar halittata bace ta yi sanadin zuwan shi duniya, hankalina zai fi kwanciya kafin Ashraf ya kwana cikin kabari ya zamana Safiyyerh nada igiyar aure a kan ta"" ajjiyar zuciya Sharfaɗi ya yi idanunsa a kan Prof Abdu Marafa ya ce ""Me kake jin tsoro da kake so dole ka aurar da ita, Allah Ya gani amintar mu ya saka muka yanke hukuncin haɗa yaran nan aure saboda ƙarfafa zumunci, to kana taka Ubangijin talikai na tashi nasa kuma shine gaskiya, Ashraf ya rasu baya duniya ina tunanin ka bar yarinyar nan ta samu nutsuwa ta duba wanda take so yake son ta sai a yi mata aure, kar a ƙuntata" "rayuwar yarinya""" """Sharfaɗi ba zaka fahimta ba, ka yi mini wannan alfarma ka wakilci Aliyu ni zan wakilci Safiyyerh ga" "jama'a su shaida Please sai a haɗa a yi addu'a har ta Ashraf"" J zufa har yanko masa take yi na tsananin mamaki mene haɗin Captain da Safiyyerh da za a yi musu aure? Baya son zuciyarsa ta gasgata abin da yake jin tsoro ko wassafo shi cikin kan shi, Safiyyerh fa and Aliyu? Ya Allah! Shi dai Awais kan shi a ƙasa" Dr Hash daman baya wajan yana can duba Fiyya tunda ta faɗi wajan ya yi shiru can daddy ya ce """Kawai alfarma nake nema zan ji daɗin hakan idan ka yi mini""" """To shikenan, waye maɗaurin auren?""" "Daddy ya nuna wani abokinsa, Sharfaɗi ya ciro kuɗi mai yawa a cikin aljihu ya dire ya ce ""Ni Sharfaɗi ina" "nemawa ɗana Aliyu Abdu Marafa auren Safiyyerh Abdu Marafa a wajan waliyi na wannan yarinya"" daddy ya saka hannu ya ɗauki kuɗin ya ce ""Ni Abdu Marafa uba a wajan Safiyyerh Abdu Marafa na bawa Aliyu Abdu Marafa auren yarinyar wajena Allah Ya sanya musu albarka"" addu'a aka yi nan take kuma aka" ɗaura auren a gaban shaidu ma ɗaurin ya ce """Aure ya ɗauro a kan sadakin da Sharfaɗi ya bawa dubu ɗari biyu, Allah Ya sanya albarka tsakanin Aliyu" "da Safiyyerh ya kuma kaɗe fitinar da kan iya wanzuwa a tsakaninsu"" duk aka amsa da amin. Daddy ya" "lumshe idanunsa yana sauke ɓoyayyiyar ajiyar zuciya nutsuwar ta saukar masa, bashi da sauran fargaba a yanzu Safiyyerh ta zama matar wani." "Kasancewar rasuwar ɗan babban mutum ce kamar Sharfaɗi ya saka manyan mutane zuwa gaisuwa, ƴan" "kasuwa da ƴan siyasa da wanda dai suke jin kansu wasu ne a garin. Kallo kallo aka shiga yi tsakanin Hon Maɗatai da Eng Ali wali dukkan su cikin shiga ta alfarma, ga mutane da take musu baya kowanne da tarin ƴan jagaliya da ƴan daba gudun kota kwana. Hon Maɗatai ya yi murmushi yana miƙawa Ali wali" hannu ya ce """Kwana da yawa Ali wali?"" Ali wali ya ɗauke hannu sai kuma ya juya ya ce" """Ba yanzu ba ka jira na wani lokaci komai zai haska, za a yi tsawa walƙiya ta bayyana munafukan da suke" "ɓoye cikin duhun ciyayi"" murmushi Hon Maɗatai ya yi kawai yana furta ""Allah Ya nuna mana"" gaisuwa duk sukai sai dai daddy tsakaninsu kawai addu'a ya miƙewa daga wajan. Bayan yin ta'aziyya Hon Maɗatai ya ce ""Allah Ya yi wa Ashraf Rahama, ya taƙaita iya kan shi"" Sharfaɗi ya juya ya kalli Hon Maɗatai kana ya kalli Eng Ali wali sai kuma ya ce ""Amin, yanzu ba gashi ba gwanin sha'awa a dinga siyasa bada gaba ba sai an fi samun nutsuwar zuciya data ƙwaƙwalwa duk wanda zai samu wannan kujerar Ubangiji ya gama rubutawa kawai dai lalube ake yi cikin duhu ku haɗa kai da hannu kowa ya yi kamfel nasa babban jin" "daɗin ba jam'iyyarku ɗaya ba""" Cikin jinjina kai Hon Maɗatai ya yi murmushi daman shi bashi da wata matsala da Eng Ali wali shi yake "haukan shi hankalinsa na kan wanda ya yi shiru, shirun nasa kuma yana nufin babbar barazana a gare shi ""Siyasa ai ba zata haɗa musulmi irina faɗa da wani ba, munga jiya mun ga yau muna da tabbacin za muga gobe mai kyau, ni fatana na samu gurbin saka hannun jari a kamfaninka idan aka bani dama an yi" "mini komai Sharfaɗi"" daddy na jin su can aka kira shi waya da sauri ya miƙe tsaye yana neman uzurin" tafiya Eng Ali wali ya bisa da idanu. "Cikin dare Fiyya ta farka da wani irin ciwon kai na ɓari guda, ta kasa buɗe idanunta a hankali ta saka" "hannu ta dafe kan ta duk da halin cewa bai hanata yin addu'a ya yi tashi a baccin ba domin tabbatarwa da kanta ba a cikin kabari ta farka ba. ""Sannu Maama"" shine abin da Ummi ta iya cewa tana hamdala a ranta domin shirun ya yi yawa ta damƙe hannunta sosai" """Ummi kai na ciwo, ciwo nake ji a gefen kaina"" jikinta har rawa yake na tsananin ciwo Ummi ta ce" """Maama zai daina in sha Allah, bari a kira likita""" """Ummi daddy fa?""" """Yanzu ya fita, ki yi ta addu'a komai ya yi farko yana da ƙarshe, wannan ciwon kan zai daina miki" "watarana buɗe idon ki kalle ni"" a hankali ta buɗe idanun ganin yadda idanun ya yi jajir ya saka Ummi cewa ""Subuhanallahi wannan jan kuma na magani da mene?""" """Ummi jimawar da ta yi a kwance da ciwon kan shine ya saka idanun ja yanzu daddy zai shigo Fiyya zata" "ji sauƙi ki kwantar da hankali"" daidai nan daddy ya buɗe ƙofa ya shigo J na bin shi a baya da Dr Hash, ganinsu kuma ya saka komai ya dawo tunanin Fiyya ta runtse idanunta tana jin fargaba na saukar mata. ""Da gaske Ashraf ya mutu daddy? Da gaske an binne Ashraf babu Ashraf ya mutu yanzu haka yana kwance cikin kabari mijin da zan aura ranar ɗaurin aurena ya mutu daddy na shiga uku"" daddy ya kama" hannun Fiyya cikin nutsuwa ya ce """Laa, sam ba ki shiga uku ba tana iya yiyuwa ya shige iyakar shi ne, kuma mutuwa a hannun Ubangiji" "take idan lokacin ya yi kota wacce siga ce dole wannan rai ya koma wajan wanda ya samar dashi, Maama da gaske mijin da za ki aura mutu ki sawa ranki haƙuri ki yi masa addu'a ki saka salama ki ɗauka bashi ne zaɓinki ko alheri gare ki ba, Ubangiji na yin komai a lokacin ya yi niyya babu mai tuhumarsa hujjar hakan domin shi ishasshe ne ki yi addu'a Safiyyerh Ashraf is no longer alive pray for him"" juyawa Fiyya ta yi ta zubawa daddy manyan idanunta wanda yake cike da hawaye da ƙyar ta ce ""Ashraf ya mutu ya bar ni cikin zullumi daddy, inama tuntuni aka ɗaura mini aure da shi, innalillahi wa'inna ilaihirraji'un wayyo ni" "Safiyyerh""" """Zullumi na me kuma Safiyyerh kin ga abubuwa da yawa a rayuwa sai mutuwar Ashraf zai tsaya miki? Ba" "za ki yi addu'a ki sawa zuciyarki sallama, kuma wani hanin ga Allah baiwa ne kamar yadda aka sanar yau ɗaurin auren ki da Ashraf Allah bai yi ba, haka kuma alƙawarin Allah gaskiya ne igiyar auren wani ta hau kan ki Maama"" ta yi shiru don ta tabbatar daddy ba zai fahimce ta ba, ba zai gane me take nufi ba, ta yi missed Ashraf tun ba'a je ko'ina ba ta ji inama ita Ubangiji ya ɗauki rayuwarta ya bar Ashraf ko da bai aure ta ba, babu mamaki ta dalilinsa wani ya san abin da yake ɓoye gashi ta mutu ya barta da wani irin" damuwa ba tare daya bar mata ƙofa ko ɗaya da zata gane ba komai ba. """Daddy me ya sa ka haɗa aure na da Ashraf tun fari?"" Daddy ya kalli Fiyya cikin kwantar da hankali" """Saboda ya cancanta kuma ya dace Maama ki yi shiru da wannan maganganun duk zafin ciwo ne yake sawa kike furta su kamar saukar ruwan sama ki yi addu'a"" ta jinjina masa kai a hankali ta zare hannunta daga cikin nasa idanunta rufe sai sauke numfashi take yi ba tare da ta ce komai ba ta juya ta kwanta maganganun Ashraf na dawo ba, a ranta ta dinga masa addu'a ita bata taɓa sanin bashi da lafiya ba, he" never told her he was sick innalillahi. Dr ne ya shigo zai yi magana daddy ya yi saurin girgiza masa kai alamar kada ya ce wani abu serious Dr "ɗin ya zubawa Safiyyerh idanu ya ce ""za'a sallame ta yau kamar yadda ka buƙaci baka son kwana zan" "mata allura amma before""" """Thank you Dr""" "Dr Hash ya miƙe ya ce ""daddy zan je asibiti ina da aikin dare Awais zai yi dropping nawa bana jin daɗi""" "Ummi ta ce ""Kuma baka jin daɗin zaka tafi kamar dole ka yi kwanan tsaye ba'a ɗaukan uzuri ne"" ya ɗan yi murmushi kawai ya ce ""Ummi ai ba zai yiwu na amshi kuɗi na ƙi aiki ba, sai Ubangiji ya kama ni da" "wannan hakƙin ki yi addu'a zan iya"" ta ce ""To Allah ya sauwaƙe ya bada sa'a ya kuma kare""" """Amin Ummi""" "Dr ɗin ya yi wa Fiyya allura ta samu bacci mai nauyi, Ummi dai kallon daddy take jin ya kira Aliyu ya zo ya" "ɗauki Fiyya nan da 20 minutes shi zai tafi tare da Ummi har lokacin Aliyu bai san da batun auren ba kamar yadda Fiyya bata ɗauki maganar daddy serious ba. Ya gyara mata kwanciya ya miƙe Ummi ta miƙe tana shafa kan Safiyyerh a haka suka fita. Har wajan ƙarfe 1:30 Fiyya na kwance tana bacci lokaci zuwa lokaci wata nurse ke shigowa duba ta. Yana tsaye hannunsa biyu zube cikin aljihu ba zai ce ga abin da yake tunani ba, amma fuskarta kawai yake kallo ganin yadda a bacci ma take ɓata rai ta sauke ajjiyar" "zuciya, ƙofa aka buɗe ya yi saurin yin baya yana kame fuska sosai." "Dr ya kalli Captain ya ce ""Sai yanzu na ɗauka ma ko a nan zata kwana"" Aliyu dai ya yi shiru ya zaro waya" "ya fara dannawa ""ga maganganun nata wannan za a yi amfani da shi lokacin...,"" ""Ka kira su, sai ka musu bayani"" shi daya tsaya tunanin yadda zai tashe ta yake ga daddy sai kiran shi yake banda haka da ba zai zo bama, ya saka ƙafa ya fara zungurun gadon dr ya ce ""Allurar da aka yi mata nada ƙarfi sai dai ka ɗauke ta"" siririn tsaki ya yi ""to ɗauke ta kai"" ganin fuskar Aliyu cikin serious ya sa dr ya nufi Fiyya zai ɗauke ta zuwa waje kafin ya ƙarasa kawai yaga Captain ya saka hannu da drip ɗin da mayafin nata ya ɗaga sama ta zabura ta yi saurin riƙe shi Idan ba kuskuren ji ya yi ba ya ji kamar ta ce ""TAHHB"" ya sata gaban mota" ya kwantar da kujera kamar wanda ake bi haka yake jan motar. **** Yana durƙushe ya tsattsare mutumin da jajayen idanunsa wanda suka shige ciki alamar a buge hannunsa riƙe da askira gefe kuma jibgegen karan shi Tiger ne da duk a cikin karnukan ya fi son shi. Ya saka askira ɗin a cinyar mutumin ya nutsa jini ya fara fita sosai yana ihu da kururuwa cikin tsakiyar daren ga duhu ko'ina ya ce """Wai me ya sa baka da imani ne, zaka raba mini cinya biyu""" "Duk da cewa a buge yake amma tar ya buɗe idanunsa, cikin muryarsa da kana ji ka san shi ba ma'abocin" magana bane da wani kalar sautin mai kama da gurnanin zaki ya ce """Ka gane ni yanzu?"" Ya jinjina kai yana wani irin nishi da kakari kamar na mutuwa ya ce ""Na gane na" "gane, wallahi na gane ka""" """Good"" ya sake nutsa askirar ya yi feshi kunama ta faɗo ta shige cikin wandon birnin ya ce ""Sanda aka yi" "mini baru ma'ana aure, da nazo kai na ganin bakin ƙofar gidana, haka ne?"" Ya sake faɗa yana ƙara cilla masa wata kunamar baƙa ƙirin ta sake shigewa cikin wandon mutumin, Darma da Goje sun tale shi" kowanne ya take hannu ɗaya mutumin ya yi shiru hakan kuma ya sake fusata Moh ainun """Idan aka bani ciwon kai hauka nake yi ba zaka ka ji daɗi ba, a yunwa ce nake, yi batu"" kamar zai mutu" "cikin kakarin mutuwa ya ce ""Zan yi, zan yi magana"" suka sake shi suna kallon shi." """Mutane kala biyu ne suka shigo a wannan daren da aka kawo ta, na farko sun bani kuɗi fuskar su a rufe" "take na biyun ma sun sake bani kuɗi suma fuskar su a rufe take amma sun bani saƙo na baka tun a wannan lokacin, bayan an kama ka na rasa wa zan bawa na dinga bulayi kawai na haƙura, daga baya kuma aka zo aka sake cewa na bada wannan saƙon na ce a'a sai sukai mini tagoma shi da kuɗi har miliyan ɗaya kawai na basu ai kan ƙasar nan yadda muke fama da babu da yunwa ga iyalai ina dasu" "kawai na amsa na bashi""" "Darma ya ce ""ka ji kimini ƴan yankin nan ba za ku gama da duniya lafiya ba, da ƙyar kusha ruwan" "alkausara"" Moh ya zubawa mutumin jajayen idanunsa sai kuma ya miƙe tsaye magana yake son yi amma ta maƙale a harshen shi da ƙyar ya ce ""Ku yi masa ɓalli-ɓalli"" yana cewa haka ya juya." """Baka ji ba, ai na haddace abin da aka rubuta harafi uku ne a jiki. A.M.A, sai wani suna nada ban kamar" "sunan asibiti kamar sunan unguwa idan na tuna zan zo na faɗa maka amma don Allah kar ku yi mini komai a tausaya mini sabuwar amarya ce dani""" """Ni tawa matar ko kwana ban yi ɗakinta ba, duk irin gwagwarmayar dana sha, uhmmm"" ya yi shiru a" lokacin sautin muryarta yake ji na kakarin mutuwa a kunnensa can ya miƙe kawai ya yi gaba. Goje ya ce """Zan dinga zuwa lokaci lokaci domin kana cikin taskar Moh""" "Da sauri suka bi bayansa ganin har ya yi nisa sosai ""Mai dawa daman ka iya yaran nasara na ji ka ce" "Good""" """Na yi kala da wanda iya turanci ko mota ko amfani da waya ne?"" Kallon tsaf sukai masa Darma ya ce" """Ciki ne kai yasin sai fama kake da kan ka ba wannan maganar a basar kawai ya maganar ɗawan nan?""" "Kamar zai yi shiru sai ya ce ""Bana son sabga da mace zan iya kashe ta kamar yadda itama ɗayar na kashe ta""" "Darma ya fashe da dariya sosai yana kaɗa kan shi ya ce ""ba wannan ba wallahi wata figigiya da ita, suma" "dai basu da man kai wai ita ce manja"" Goje ya ce ""matsalar kai daƙiƙi ne ajawo sam ciki ne kai, manager ake cewa dake mayen garau garau ne kai wai manja ai uwar manja gaja kawai"" Darma dai bai kuma Goje ba ya ce ""Maganar gaskiya wannan za a iya karya mata ƙugu a wajan ɗakko ta ma sille kenan, Mai dawa ko kai baka ganta bane"" Ya yi musu shiru yana jinsu dai ""Sai godiya, ina magana baka ganta ba wata ƴar" "shila da ita?""" """Ita wa?""" """Manja ɗin""" """Idan ka ƙara ce mana manja a wajan nan za kaga manja ganin idanunka, ɗan wahalar yaro kawai""" "Mutallab dai idanunsa a lumshe tunanin da yake yi daban, kalmomin da mutumin ya faɗa masa nata yawo a cikin kan shi. A.M.A Ya kasa fahimtar kowanne harafi me yake nufi sai kawai ya taune bakinsa ƙirjinsa na buɗewa duk jikinsa tsami yake masa ya buɗe idanunsa ya kalli sama yana ganin yadda" gajimare ke gudu yana haɗewa tare da warewa muryarsa bata wani fito sosai can ƙasa ya furta kalmar. """her eyes look alike, tiger""." Washegari misalin 12 na rana Safiyyerh na saman bene cikin ɗakinta ta dinga kallon Kinal bata da "nutsuwa sosai da babu abin da zai hanata yin dariya. Kinal ta share hawayenta tana ɓata fuska cikin sanyin murya ta ce ""Kalli yadda sukai mini da fuska daga tambaya na ɗauka za su faɗa mini ashe ƴan" "wahala, ni bada wata munufar na je wajan su ba wallahi kawai su bani amsa na ƙara gaba""" """To ga amsar nan ai""" """Maama fuska ita ce kyan mace fa, yanzu idan tawa ta lalace waye zai aure ni haka? Sun kusa tsaga mini" "baki gashi yanzu ina da aiki a ƙasa sosai har Hon Maɗatai zan yi wa waƙa"" Safiyyerh ta yi shiru tana tunani so take ta fice daga cikin gidan secretly amma no way ""wai ina magana kina ji ba zan shariyar nan naki damuna yake, na zo ɗebe miki damuwa da kewa na rashin Ashraf kamar yadda Ummi ta buƙata duk" "da ciwon da bakina yake mini ina da zuba ke kina ignoring nawa for God sake""" """Idan ba ƙi auro ba sai ki auri ɗan daban kawai"" Kinal ta yi tsaki ta ce ""Kuma zan iya, mene a ciki""" """Shi auren ɗan daban?"" Fiyya ta buƙaci amsa tana kallon Kinal. Kinal ta ce ""Deal, nama yi miki alƙawarin" "in dai ina da numfashi wallahi wallahi sai na auri ɗaya daga cikin ƴan daban nan, kamar ni mawaƙiya za" "su yi wa haka? Uhm"" Fiyya ta lumshe idanu ta buɗe deep down ƙirjinta na bugawa sai ta ce" """You most like them ma, ƴan daban ai sun iya soyayya""" """Ke ta ya kika san sun iya?"" Shoulders kawai Fiyya ta ɗaga ba tare da ta ce komai can ta sauke numfashi" tana kallon Kinal ta ce """Kinal Ashraf ya rasu, mijin da zan aura ya bar ni Kinal ina cikin damuwa ina jin da old Safiyyerh ce ba zan" "ce ina cikin damuwa ba, gwara ta kashe ni haka nake ji"" Kinal ta jinjina kai ""Fiyya something is over doesn't mean your life is over, ki yi haƙuri mu ɗauki ƙaddara ki yi wa Ashraf addu'a Please kar ki saka damuwa wani abun ya zo yana damun ki daman ke idan kika birki ce kamar mai ƴar mero a ka, ƙaddararmu zata zama mai kyau muna tare da addu'ar iyaye ai"" sun jima tare da Kinal har yamma kana" ta tafi gida tana jin dole ta sake komawa wajan ƴan kodin ɗin nan. "Da ƙyar da daddare Fiyya ta sakko ƙasa bayan tayi sallar issha tana sanye da hijabi har ƙasa, fuskarsa" looking ok ba yabo ba fallasa sai dai ta faɗa idanunta ya fito akwai damuwa a tattare da ita. Inda ta yangi "su J ta nufa ta shiga tsakiyar ƴan mazan ta zauna a nutse ta ce ""Sannun ku"" Awais ya ɗago ya kalleta ya" "ce ""Yawwa Manager ya ƙarin haƙuri?"" Idanunta ya juya ta cije baki ta ce" """Allahamdulilah,thank you"" daddy dake kallon ta cike da tausayi ya ce ""tashi a nan wajan Safiyyerh""" """Daddy me ya sa?""" """Ki dai tashi na ce ko?""" "A sanyaye ta miƙe sai kawai ta yi sama ya bita da idanu a hankali ta ce ""Sai yaushe zaka faɗa mata batun" "auren?"" Daddy ya ce ""Da sai an kammala Visa ɗin ta, na san wacce take da ita a baya ta yi expired, to Safiyyerh stubborn girl ce da na yi maganar visa zata kalli cikin idanuna ta fara mini turanci wayonta tsoro yake bani, kuma yanzu i feel very comfortable da Aliyu matsayin mijinta duk da basa shiri amma ba" "zai ɗaga mata ƙafa bana son dai ta yi rayuwa a wajan shi kamar Prisoner, za ta yi shakkar yi masa abu""" """Kana ganin zata amince da auren?"" Ya miƙe tsaye yana haurawa sama ya ce ""In sha Allah"" daman daga" sallah ya dawo shine ya zauna. J dai baya uhm baya uhm'uhm abubuwa da yawa ke yawo a ƙasa wanda baya rasa nasaba da tunanin wace Safiyyerh waye Aliyu? "Ummi ta kalli yadda ya shigo ba wanda ya kula kamar bai ga kowa ba ta ce ""Aliyu tun safe ina ka je ne?""" "Ya buɗe ido ya yi shiru ta ce ""Kuma ka ci abinci ne? Kodayake ba'a tambayar soja ko ya ci abu da za'a buɗe cikin ka duk ganye ne"" kallon Ummi kawai yake kuma ya yi shiru" """Yaushe zaka tafi goben?""" """A'a, night Ummi"" ya ce yana shigewa cikin ɗakin shi dake part ɗin mazan." Fiyya ta ci kuka a ɗaki kamar rai da sauri ta buɗe system ɗinta taga saƙo a e-mail nata tun sanda sukai last called da Ashraf bayan hakan ta minti ashirin da wajan biyar. Maganar daya tura mata ya saka ta buɗe idanu sosai. "_Safiyyerh daddy ya zo ya fita yanzu, ko ma dai menene ki tabbatar ba ki bawa wani damar mallakar FS" "WORLD INVESTMENT COMPANY ba Fiyya mutane biyar sune mamallakan wannan kamfanin mutane masu haɗari ko ni ban san su ba, da ina da yadda zan yi a yanzu zan faɗa miki komai domin sauƙaƙa miki," "ki fara nemo ma'anar FS shine key ɗin binciken, don't cry when you miss me i love you""_" "Safiyyerh was shocked, thinking me ya saka Ashraf ya yi mentioned sunan daddy a lokacin, meke shirin" "faruwa ne gabaɗaya kan ta ya ɗauki zafi da gaske ta yi rashin Ashraf sai yanzu ne take jin gudun zuciyarta na ruɓanya aikinta a kan Ashraf ɗin. Ta kwanta tana rufe idanunta ƙarar notification na wayarta ta saka ta buɗe idanu tana janyo wayar a hankali, rubutu a taƙaice mai ɗauke da azanci da ɓoye manufar abin" da ake so a bayyana. _“laifi akan laifi again? Kodayake shi laifi tudu ne Safiyyerh ke inuwar wani ce ki yi ƙoƙari kar a saka ki shiga wuta”_ "A gigice ta ce ""Na shiga uku ni Safiyyerh""" **** Cikin dare ne wajan biyu da arba'in motarsa na gefen titi cikin duhun daren ya saka facemask ya rufe "fuskarsa tsoro da fargaba ya gaba gitta masa zuciya a hankali ya zuge glasses ɗin motar babu mai cewa shine a ciki, yana buɗewa ya faɗo cikin motar ya ce ""Kira cikin dare? Ban fiya son ina tsaka da wani aikin" "kuma ana kira na wani ba, ya akai?""" Photo ya fito masa da shi na wani kyakkyawan yaro fari tas da shi idanunsa buɗe ya shagwaɓe fuska tare "da miƙa hannu alamar a bashi wani abu, yana sanye cikin wasu ƙananun kaya baƙaƙe. ""Na gani photon" "waye? Wannan yaron fa?""" """Ɗan gidan Safiyyerh ne"" ya furta yana lumshe idanu tare da yin baya ya jingina da kujerar zuciyarsa na" "buɗewa sosai tsoro da fargaba na cika shi ""What! Safiyyerh yaronta kuma?""" """E, idan kaga Safiyyerh ka gan shi kamar an yi kaki ban san ko ta san da yaron ba a tabbatar an gano mini" "inda sa Safiyyerh take""" "Kwanakin wajan biyar da rasuwar Ashraf daddy bai faɗawa Fiyya batun auren ba, haka ma Aliyu Fiyya" "kullum sai ta fita wajan aiki ba kuma ta dawowa da wuri. Yamma wajan magariba take driving a gajiye take sosai fahimtar ana bin bayanta ya saka ta ƙarawa motar giyar da sauri ta ɗakko waya number J ta fara kira amma bai ɗauka ba, ta shiga kiran ta daddy amma a kashe duk wanda take tunanin kiran" "number shi a gidan ta kira bata samu ba," "ta kalli madubin taga har yanzu motar na biye da ita, tare da wasu babura biyu bata iya hango fuskar" "mutanen amma kallo guda ta yi musu ta san ƴan daba ne, ko dai masu satar mota ne ko satar waya ta shiga uku. Baburan guda biyu suka cimma ta ɗaya ya saka hannu ya daki glasses motar nata, ta yi gefe tare da ƙarawa motar gudu suma suka take mata baya a lokacin tsoron da ya yi mata yawa ya saka ta fara gani dishi dishi kan motar na neman kwace mata, cikin sauri tana ƙanƙame steering ta shiga lalubar numbersa bata da tabbacin ko tana da ita cikin sa'a ta gani ta danna kiran sai da ta yi kiran biyar bai" "ɗauka ba, gashi hanya babu mutane a kira na shida ya ɗaga cikin ɗaga murya da fitar hayyaci ta ce" """Yaya na shiga uku Captain wasu ne""" "Ya yi mata shiru can ya ce ""Who are you?""" """Yaya Safiyyerh ce wasu ƴan daba suka biyo ni gashi titi babu kowa, Captain suna da yawa wasu a babur" wasu a mota na kira number kowa a gida basu ɗauka ba gashi ciwon kaina kamar zai tashi bana ganin "hanya sosai kan motar ƙwace mini yake"" ta cikin wayar Captain ya yin siririn tsaki can ya ce" """Ina ruwana?""" """Captain kashe ni fa za su yi innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!""" """Allah Ya ji ƙan ki""" littafin MUTALLAB Na kuɗi ne we're still on free pages. Ka biya a yi adding naka a paid book before mu yi cutting free pages ɗin. MUTALLAB. "Book 1, 2 &3" 500 Naira "0116886423 Union Bank Na'ima Sulaiman S. A tura shaidar biya ta nan 08164069385[10/17, 8:12 PM]" Nanameera: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥* Page 10 *Bright pens..2nd batch* """Kamarya Allah Ya ji ƙai na, Captain ina faɗa maka biyo ni ake yi za'a kashe ni, kana cewa Allah Ya ji ƙai" "na, i called you saboda na rasa wanda zan kira Please help me"" ta cikin wayar Captain ya yi tsaki ya ce" """Kee, ina ruwana idan sun kashe ki who cares about your life, zan kira daddy a ɗauki gawarki ok"" kashe" wayar ya yi. Safiyyerh wani irin zafi ta ji a zuciyarta da raɗaɗi bata san ma wanne gurbi zata saka Aliyu ciki ba idanunta ya kawo hawaye baƙin cikin kiran da ta yi masa tana zargin kanta da laifinta ne. Ta cikin madubin motar take sake kallon motar dake bib bayanta da kuma sauran baburan ta runtse idanunta a "fili ta ce ""Ya Allahu Ya Rahmanu ka dubi Safiyyerh ka kawo mata ɗauki..Daddy!""" Ta kira sunan daddy a gigice tana sakin steering motar bata sake sanin abin da ya faru bayan nan ba. Yana tsaye fitowar shi daga motar kenan ya dubi yadda ta yi flat kwance a ƙasa gefen kanta da jini ya "kalli sauran jami'an tsaron da suke wajan ""Is she ok? Tana numfashi?""" """She is, buguwa ne kuma Allah Ya rufa asiri motar ta tsaya da kanta, ba'a yi nasarar kama ko mutum" "ɗaya ba, yarinyar ce dai bamu san wace ita ba za mu duba id card nata sai a kira iyayenta a shaida musu ko asibiti ne a tafi da ita"" ya yi maganar cikin girmama kan shi a ƙasa, wanda ke tambayar ko Fiyya na raye ya yi baya rungume da hannunsa can ya duba a gogo sai bai ce komai ba ""Sir meeting ɗin naka? Ina tunanin ka je kawai za mu kula da komai tunda shugaban jam'iyya da secretary na jam'iyya na jiran zuwan naka"" kafin ya yi magana cikin sauri wata mota ta ƙarasu wajan kamar zata tashi sama ko gama daidaita tsaiwar motar bai yi ba ya fito idanunsa a kan Safiyyerh, mutumin ya dubi fuskarta shima a" hankali kuma ya ce. """Easy Captain, ka kira ni sanda muke kan titin da take ta kuɓuta Allahamdulilah"" jinjina kai Aliyu ya yi" "cikin girmamawa ya ce ""thank you""" """Anything for you Aliyu, amma ku kula tana da harshe zuciyar nan tata irin take ce, Allah Ya bata lafiya""" "Aliyu dai na tsaye idanunsa akan fuskarta ya kasa magana har mutumin ya shiga motarsa driver ya ja, jami'an tsaron suma suka shiga motar suka marasa masa baya cikin tafiyar sirri. Ya jima yana kallon ta hannunsa riƙe da wayarsa tunanin yadda zai yi da ita, ƴar mitsitsiyar yarinya ta fito da shi, banda darajar daddy da babu abin da ya yi masa zafi sanin cewa idan Fiyya ta mutu hakan na nufin tsayawar numfashi daddy ya saka ya lallashi zuciyarsa. Cak ya ɗauke ta ya saka ta a gaban mota yana yin baya da kujerar a" "ransa ya ji ba zai zama drivernta ba, ya ɗauki wayarta ya rufe motar yana shiga ya tare da zama ya sake" juyawa ya kalle ta da kyau sosai jinin ke fita a goshin nata ya taɓe bakinsa kawai a hankali kuma yana ɗora mata tissue ya furta “Fitinanniyya... Safiii” "Farar safiya ce gari ya yi shiru amma shi idanunsa biyu, yadda ya ga dare haka ya ga rana idanunsa tarwai" "a sararin subuhana yana kallon sama da abubuwan da Ubangiji ya wanzar a cikinta, a hankali ya juya ya kalli Darma da Goje sai kuma Mangal dake can gefe guda ya sha ta gaya masa babu daɗi sai lilo yake da ƙafarsa a sama. Mangal ne ya buɗe idanunsa da sauri ya miƙe zaune yana murza idanunsa alamar bai" gama wastsakewa ba. """Jeji naka dawa taka ka huta mai dawa, ba dai gaba da gaba ko ta baya ƙaryar mutum dan uwatar ya aka" "yi ba ka yi kasa bane ka raya daren da gadin mu?"" Moh ya yi shiru ƙirjinsa sai ɗagawa yake. ""Ina tsoron shirun nan naka don ba zai haifar da ɗa mai ido ba, ka tara dafi a cikinka jira kake ka samu inda zaka sauke ƙarin dake damun jikinka ka sarara a kaiwa mai duka lillahi kukan kawai"" sai a lokacin ya juyo da gajiyayyun idanunsa da suka shige ciki duk girman da suke da shi, sun yi wani bala'in ja ya zubawa" Mangal ido """Talk da turanci kenan da hausa na goga maka yi magana sarkin jeji""" """Mangal""" """Yes inji masu jajayen kunnuwa bi ma'ana na'am"" muryar Moh bata fita sosai a lokacin duk wanda ya" "nutsu zai hango wani irin sanyin murya da yake da shi da sauti maraya hayaniya. ""Wacce cuta aka taɓa yi maka a rayuwa wacce ba zaka iya yafewa ba?""" """Kan uban nan, ni ai ka sani a kusurwa kaina ya kulle wanda sukai mini kuma tuni sun girbe abin da suka" "shuka bana yafiya bana cuta bana bari a cutan"" cije baki kawai Moh ya yi yana lumshe idanunsa da sauri ya buɗe su tar saboda yadda yake jin kakari da numfashin fitar ranta yana yi masa amo a kunne, ya mirgina kaɗan ya ɗauki ƙafarsa ɗaya ya ɗora akan ɗaya yana girgiza wa ya zubawa zara-zaran yatsun" ƙafarsa idanu tare da rungume hannayensa a ƙirji. """Wai what happened Mai dawa?""" """Ka dai na yi mini turanci don uwarka""" """Ɗan tsinanniya ba, ba uban da ya iya kuma ya san ai duk bama ji shima a Legas ya koya"" cewar Goje" "yana farkawa tare da zama dukkan su babu wanda yake da niyyar miƙewa domin yin sallah. Goje ya kalli Mutallab ya ce ""Yaushe za a kwalo berewar nan ne? Ka yi shiru karfa ka jiƙa masa aiki""" Da sauri Mutallab ya kalli Goje jin sunan daya kira na barewa ya lumshe idanu ya buɗe zuciyarsa na "bugawa sosai sai bai ce komai ba can dai ya miƙe zaune a hankali kuma ya tashi tsaye ya zaga bayan katanga ya daɗe kafin ya dawo wajan Darma ya kalli hannun Mai dawa ya buɗe idanu ya ce ""Bura... Wannan ƙwayar ka shanye to kwarankwasa ka shirya zama mahaukaci, ƙwayar doki ce fa? Wai kashe kanka za ka yi akan wasu ƴanƴan jakuna ka fito musu gaba da gaba mana, a yi komai duk abin da zai faru" "ya jima bai faru ba, ƙarshe dai gidan ɗan kande ne kuma mu ba wai baƙin ta bane""" Mutallab ya tsaya cak a tsakiyar wajan naman jikinsa na motsawa musamman kakkauran ƙirjinsa mai "faɗi sai kawai ya shagiɗe bakinsa gefe kamar zai yi murmushi da sauri ya tsuke fuska zuciyarsa na tuna masa shekarun da suka shige a fusge ya furta ""Sai godiya"" gabaɗaya suka miƙe tsaye suna maimaita" """Sai godiya""" Basu fargaba sai ganin tarin wasu ƴan daba suka gani suna fitowa daga wasu lunguna a ƙalla sun fi su "ashirin ɗauke da gorori wasu wuƙaƙe. ""Dara ta ci gida lallai an raina mu, mu wasu daƙiƙai zasu kawowa" "farmaki har lukanmu?"" Cewar Darma Mangal ya kalle su ya ce ""Kuma suwaye ku yara?""" "Wani daga cikin su ya fito ya tsaya a gaba ya ce ""Sanin sunana ko waye ni bashi da wata fa'ida a gare ka," "da zaka tambayi wanne kalar kisa zan maka zai fi maka, amma saboda gudun tilawa ko tafiya ƙiyama da tunanin wanda ya kashe ka lallai zan goga maka sunan nawa"". Ya zaro wuƙa daga cikin ƙugunsa idanunsa akan Moh da bai ma kalle su ba sama kawai yake kallo yana jin yanayin na yi masa daɗi ya ɗora da ""Uban ƴan daba nake maganin ƙananun yara masu ɓoyewa a saƙo, to cut you short sunana Lauje, ban duƙo dan na saka muku makami ba, na zo na tafi da uban gidan naku salin alin akasin hakan wajan bijire mini zai" "saka an samu kwacewar lissafi dar kenan"" wanda ke kusa da Lauje mai suna Modara ya ce" """Ka saɓo shi a wuya mana sai ka tsaya ɓata yawun da Ubangiji ya halitta a bakinka Oga?""" """Ban zo don rigima ba, bisa umarnin Hon na zo wannan shine""" "Darma ya matsa gefe yana nuna musu Mai dawa Moh kenan ya ce ""Bisimillah gashi nan kuje da shi kuna" "da hannu na san"" Moh ya sake juya musu baya maganganunsu da gaske ciwon kai da zafin zuciya suke" ƙara masa hannunsa kawai yake dunƙulewa yana hura iska sama ko yaushe ya zama sa'annin yara irin su Lauje? """Ji mana""" "Mutallab ya juyo yana gyara tsaiwa idanunsa a birkice Lauje ya dinga kallon Mai dawa, shi bai ya yi" tunanin haka yake ba yaji ana Mai dawa da Mutallab sai ya ji sunan Mutallab kamar na ƙananun yaran "ganin Mutallab cikakken namiji a tsaye mai kakkauran hannu da buɗaɗɗan ƙirji gabaɗaya jikinsa a murɗe yake musamman damtsen hannun ya basar ya ce ""Shige muje""" "Da hannu Mutallab ya yi masa alama da ya zo ya tafi dashi, Lauje ya nufi wajan Mutallab ba tare da sanin" "cewa akwai shafin hannu a jikinsa ba ganin ba wani makamani hannunsa ya saka ya nufe shi. Yana miƙa hannu da sunan kama shi Mutallab ya yi masa wani naushi a gefen ƙirji, nan take Lauje ya fara fari da idanu ƙashin gefen ƙirjinsa ya yi ƙara ya sulale a wajan ba numfashi. Ganin hakan ya saka su Modara ja" baya a tsora ce ya ce """Kut ya bazar dashi ba, wannan mahaukaci ne""" """Bai mutu ba tafiyar zango ƙalilan ya yi kawai ya samu karaya a ƙirji, kar dai ku manta da Mai dawa kuke" "magana masu jeji da namomin jejin da kansu matsalar gajanci kenan kun tari mutumin dake da shafi a hannunsa duka ɗaya ka sume gwara ya saka maka kaifi daya saka hannu, ya zame muku hadda. Yi batu" "waye ya aiko ku?""" """Hon Maɗatai""" """Wani abu ne haka? Me za a yi masa?""" "Modara ya ce ""Bamu sani ba, ya ce yana buƙatar ganinsa shi kaɗai kuma a sirrince""" """To ba zan zo ba""" "Cewar Moh yana cije bakinsa hannunsa har yanzu rawa yake baya son yin kisa, idan ya riƙe wuƙa bai san" "me zai iya yi ba kuma sam. Da mamaki Modara ya ce ""Kasan waye hon Maɗatai kowa? Wallahi taimako" "zai baka shine kawai yake jin tausayin ƴan daba irin mu""" """Ɗan daba irin ka dai, shi Malam Abdullahi ne balle ya yi mini baki, ko Malam Abdullahi can ta matse" "masa"" Modara ya buɗe baki da nufin sake magana ""Kana kira mini sunansa sai na yi maka sabuwar kaciya"" ba shiri ya tsuke bakinsa suka ja Lauje tare da barin wajan cike da takaici." "Safiyyerh na kwance tana bacci tun bayan sallar asuba da ta yi, Dr Hash ya sake ɗaura mata ruwa a" "hankali kuma ya ji tana surutai ƙasa-ƙasa ya kasa kunne da kyau ko zai ji mene take cewa ""Ashraf ka taimaka ka dawo ka faɗa mini ma'anar FS, ka faɗa mini suwaye mutane biyar ɗin da kake magana akai, Ashraf the company is belong to your father,ko a mafarki ne ka faɗa mini ko a fatalwa ne ka zo mini bazan ji tsoro ba, Ashraf i really really need your help, don ka dawo"" Dr Hash ya juya ya kalli daddy da ya" yi ƙasa da kan shi """Daddy akwai damuwa fa, meke faruwa da Fiyya ne? Me take buƙata wajan matacce ne Ashraf zai fito" "daga kabarinsa kuma ya yi mata, daddy Ashraf ya rasu fa ranar da za a ɗaura musu aure da Fiyya me ya sa ba za ta yi tawakakkali ba, me ya sa wai?""" """She loves him so much, tana son Ashraf ne shi ne dalili"" cewar daddy yana sake matsawa tare da zama" "a bakin gadon ya kama hannun Fiyya ya riƙe cikin nasa da kyau ""wannan zafin hannun fa? Her temperature is too high, bana son zazzaɓi a jikin Maama ka yi wani abu Dr Hashim"" Dr Hash ya ce ""Ciwon kanta da bugawar ne ya saka mata zazzaɓi, na yi mata allura zuwa anjima zai sauka ai""" "Maimakon Fiyya ta yi shiru sai ta cigaba da surutan sosai tana furta ""Ni ba Tiger ba ce Tahhb, why are" "you decided to call me Tiger?"" Kamar a gaske kamar kuma yanzu ne ta ji saukar muryarsa a tsakiyar kanta, sautin ya sauka a ƙirjinta ""Saboda ke matar Moh ce Tiger, zama matar Moh is not easy we most fight together halinki irin na tiger ne, matar Moh"" tar da buɗe idanunta a gigice a kuma sauti na ruɗani" "ta ce ""Motar Moh""" Daddy da Dr Hash suka kalli juna jin abin da ta furta kafin su yi magana Safiyyerh ta juyo ta kalli daddy sai "ta yi murmushi mai kyau wanda suka jima basu gani a saman fuskarta ba, ainahin murmushi da kyawun Safiyyerh daya shuɗe ya dawo fil ta riƙe hannun daddy a nutse ta ce ""His voice daddy, muryarsa ce""" """Shi wa?""" """Tahhb"" daddy ya yi murmushi yana shafa sumar kanta ya ce ""ai kuwa na ji nima, ki yi bacci Maama za ki" "samu sauƙi in sha Allah"" ta jinjina masa kai tana riƙe da hannunsa har lokacin ta ce ""In sha Allah daddy," "in sha Allah daddy"" jikinta ya saki ta koma bacci daddy ya sauke numfashi ko samun sukunin karyawa bai yi ba, ya dubi Dr Hash ya sake duban Fiyya ya ce ""Ka yi mata allura kafin ta farka""" """Daddy ka duba Maama tana cikin damuwa ba, baka jin allurar zai saka ta dawo da ɗabi'unta na baya" "daddy yin allurar ba mafita ba musamman ga lafiyarta, tsayin shekaru na daddy har yaushe ne ka duba Safiyyerh don Allah"" miƙewa tsaye daddy ya yi ya ce ""Ka yi hakan Dr Hashim Abdu Marafa, completely tsayin rayuwa haka nake son ganin Safiyyerh"" jinjina kai Dr Hash ya yi sai ya haɗa allurar har guda biyu ya juya bayanta ya caka mata cikin sauri ta ƙanƙame jikinta wani irin azaba da raɗaɗi take ji a duk sanda aka yi mata allurar. Yana yi mata ya fice ba tare daya sake kallon daddy ba. Ya zubawa photonta idanu" yana juya mata baya a hankali ya ce """Ki yafe mini Safiyyerh ki fahimce ni ki fahimci mahaifinki, i am sorry Safiyyerh"" fita ya yi ya rufo ƙofar ya" nufi parlonsa a zaune ya tarar da Ummi tana kallon shi ta ce """Ya jikin nata? Ta farka ne?"" Ya zauna yana numfasawa ""Ta sake yin bacci, ina Aliyu?"" ""Kasan sai ya yi" "niyya yake shigowa"" daddy ya ɗauki wayarsa ya kira number Aliyu yana ɗagawa ya ce Aliyu zo mana ya ajjiye ya kalli Ummi cikin kulawa ya ce" """Ina jin kamar haɗa auren Aliyu da Safiyyerh na yi kuskure ina jin kuma hakan shine mafita, ina jin tsoron" "tambayar da dukkan su za su yi mini wacce bani da amsar su, da gaske bani da wannan amsar tasu Ummi," ba komai Safiyyerh take ganewa tana jin ta isa ta yankewa kanta hukunci ita ba kowa face yarinya mai "wayon gaske da tunani Safiyyerh bata san komai ba ita kawai yarinya ce""" """Ka san dole zaka jira amsar wannan tambayar da kake tsoro, amma sanar dasu auren shine zai fi maka a" "raina ina jin Maama ba zata yi maka gardama ba"" kafin ya ce wani abu Aliyu ya buɗe ƙofar ya shigo da izinin daddy kamar kodayaushe wandon sojoji ne a jijinsa da farar riga tas ya ɗora hula p.cap a kan shi ya zauna kansa a ƙasa yana furta ""barkan ku da safiya""" """Aliyu ya aiki, baka san Maama ba lafiya bane naga baka shigo ba?""" """Na sani"" ya ce kawai a taƙaice yana danna wayarsa ""Ka sani kuma? Shine ba ka yi mata sannu ba me ya" "sa kake haka ne Gadanga, me ya sa kai zuciyarka bata motsawa sai akan Maama meke damun tunaninka baka ɗaukan responsibility ɗinka as a brother""" """Idan bai ɗauki responsibility nasa matsayin yaya ba, yanzu zan ɗauki responsibility Safiyyerh a matsayin" "mijinta"" da wani irin yanayi Aliyu ya juya ya kalli daddy yana son sake tabbatar da abin da ya faɗa masa a" "zuciyarsa wani irin fargaba ne ya wanzu ciki a fili kuma ko gezau ya dai zubawa daddy idanu can ya ce ""kamarya?""" """Da kai da Safiyyerh baku da wata kalma da za ku replying mutum ko responding maganarsa sai kamarya?" "To kamarya dai yadda ka ji ai aikin da ka yi na soja bai saka ka daina jin Hausa ba, har gwara Safiyyerh" "ma"" daddy ya gyara zama Aliyu dai kallon mahaifin nasa kawai yake da wani irin yanayi mai ɗauke da zallar mamaki." """Aliyu ni ban isa na saka dole ba, ban kuma isa na tilasta rayuwarka yin abin da ka yi niyya ko baka so ba," "Aliyu ni dai mahaifinka ne ka saka hakan a zuciyarka. Bani da wanda zai mini wannan rufin asirin kaf family, ka manta da batun Junaid da Awais da kuma Dr, kar ka tambayi mai ya saka na zaɓe ka na ji a raina zaka kula da Safiyyerh ko bayan bana numfashi ko bayan ƙasa ta rufe mini idanu na zaɓi aura maka ita saboda dalili mai ƙarfi, na yarda da ingancinka"" Ya yi shiru Ummi kuma Aliyun take kallo shi kuma yana kallon daddy da duk nutsuwarsa. ""Ranar da Ashraf ya rasu a ranar aka ɗaura maka aure da Safiyyerh, don Allah don girman Allah karka tambayan tsakaninka da Safiyyerh waye ba jinina ba, wannan tambayar shine abu mafi girman laifi a gare ni, ka taimaka ka yi mini alfarma ka riƙe Maama ka" "amshe ta matsayin matarka""" "Captain ya kasa motsi balle magana bai ma san mene zai ce ba. Daddy ya matsa hannunsa ""Don Allah" "Aliyu""" """Ita ta sani?""" """A'a, kai na fara sanarwa Safiyyerh bata da wata matsala ga umarni na"" Aliyu ya sake yin shiru idanunsa" "a ƙasa har ya juya baya ya sake juyawa ya kalli daddy a hankali ya ce ""tell her first, ko bana son ta zan yi ƙoƙarin ganin na fara son Safii in sha Allah""" """Ba zan tambaye ka ni ne ba ɗanka ba ko ita, zan bar tambayar a raina har sanda ka shirya faɗa mana" "gaskiya ni da ita, zan rayuwa da fargabar sanin amsa, da gaske daddy zan so Safii iya tsayin numfashi tunda kai ka zaɓa mini ita""" Daga Ummi har daddy kallon Aliyu suke musamman daddy bai yi tunanin jin wannan amsar ba ya dinga "kallon Aliyu ba ko ƙiftawa ""da gaske zaka so Safiyyerh? Ka san Safiyyan da nake nufi Aliyu?"" Aliyu ya" buɗe idanunsa wanda hula ta ɗan rufe masa su """Safiyyerh Abdu Marafa ko ba ita ba?""" """Ita, zaka so ta ka ce?"" Daddy ya sake faɗa da mamaki" """Bata da Qualities ɗin da za a sota ne?""" """Haka ne tana da shi, na shirya tafiyar ku za ku bar ƙasar nan nan da kwana biyu bana buƙatar ku" "gabaɗaya a yanzu domin nutsuwar zuciya"" Aliyu ya sake duban daddy ya ce" """Kuma? Ka bar tafiyar nan daddy"" sai kuma ya juya gabaɗaya ya kalli Ummi da daddy" """Aliyu soja ne, so i will be with her always""" Yana cewa haka ya fita da ƙyar ya yi jarumtar kai kansa ɗaki ya cire p.cap ɗin kansa ya shiru ba auran ke "damun shi ba, tunani ya fara wa daddy ya haifa tsakanin shi da Safii?" Da yamma Safiyyerh ta ɗakko ƙasa bayan tafiyar Kinal daga ita sai duguwar rigar bacci kanta ba hula "sosai ƙuruciyar nan tata ya bayyana, ta zauna saman kujera ta lumshe idanunta ta zama wata ira tun bayan tashin ta daga bacci jikinta ba ƙwari. I dake kallonta ya ce ""Sannu Manager, ya jikin yanzu?""" """Bayana ke mini ciwo Yaya J, ina jin Dr Hash ya mini allura, bana son allurar nan Yaya J bana jin daɗin ta" "watarana zata kashe ni don Allah ka cewa daddy ya daina sawa Dr ya yi mini"" idanunta ya shiga kawo" "ruwa ta yi lamo da kanta saman hannun kujera. Daman yana bakin ƙofa jin abin da take cewa sai kawai ya juya shi kuma Yaya J ya ce ""Ki yi haƙuri Maama za a daina miki in sha Allah"" ta yi shiru kawai." Dr Hash na zaune a lambun gidan yana waya kasancewar baya da wani aiki a asibiti hutawa yake kashe "wayar ya yi ganin Captain tsaye a kan shi. ""Babban yaya barka da fitowa"" kamar ba zai zauna ba sai kuma" "ya nemi waje ya zauna fuskarsa kamar kodayaushe babu walwala ya jima a haka kana ya ɗaga kai ya kalli Dr Hash ""Akwai wani abu da kake son faɗa ne Captain?""" """Ka daina yi mata allurar da kake mata""" """Me ya sa?""" """Haka dai na ce, idan kuma ka yi zaka sha mamaki"" Dr Hash ya ce ""Wannan kam ai daddy zaka faɗawa" "shine ke bada umarni""" """Wa kake da suna, ka da ka sake ka kuma yi mata idan ba haka ba kuma wallahi zaka kwana ɗakin duhu""" yana cewa haka ya miƙe tare da barin wajan. ***** Hon Maɗatai na zaune gabansa zube da fastocinsa yana magana da wani yaronsa wajan keɓantacce ne kamar lambu haka yake bai san da zuwan mutum ba sai huci da ya ji ta bayansa ya juya da sauri sau kuma ya buɗe idanu waje kafin ya ce """Ya zaka faɗo mini kamar ɓarawo?""" """Da ɗan siyasa da ɓarawo uwa ɗaya ta haife su, waye kai?""" """Baka san waye ni ba a garin kake nufi?""" """Ba'a haife ni da na sanka ba, ka aika akawo ni ina fatan saƙona ya iske ka?""" "Hon Maɗatai ya kalli mutumin gabansa da wani ya ce ""Waƙa ta yi, da ita za'a fara fita yawon kamfel a" "biya a dinga sawa a gidajen rediyo"" ya ciro kuɗi miliyan biyu ya bawa mawaƙin ya ce ""Ga sadakin ka, ina fatan waƙar gaba tafi wannan akwai wata zabiya wai ita Kinal A Awaya"" cikin jin daɗi mawaƙin ya amshi kuɗin ya ce ""Na san Kinal ai ta iya waƙa, ba dai ta shahara sosai bane""" """To sai mu saka ta shahara na ji ta yi Ali wali waƙa, ta yi sosai ta zuba kalamai na fikira harshen nata" "akwai zaƙi dani kuma kawai ya dace a nemo mini ita"" ""zan kawo ta in sha Allah hon, ka yi ka gama ka karya kujerar dambu mai hawa uku Allah Ya kare ka ɗan Majilisa kai ne da nasara Hon"" ""zaka iya tafiya sai na jika""" """Akwai taliya da atamfa da su Omo suger, a tabbata duk local government ɗin da aka je kamfel an basu," "a kuma ɗauki photo da bidiyo za a bawa ƴan social media su baza shi ko'ina. Sai sauran magana na siyan ƙuri'u za ku yi da p.a you can leave Musbah"" Musbah ya miƙe tsaye ya fice sai a lokacin ya juya ya kalli" Moh dake tsaye fuskarsa duk rauni """Nan ai ba jeji bane, ni kuma ba naman jeji bane ba have a seat""" """Bana zama""" """Saboda me?""" """Tsaro, yi magana""" """Shi wanda kakewa aikin baya kula da lafiyarka ne dubi fuskarka Mutallab""" """Ka kira ni da Moh ko Mai dawa sai mu yi magana"" Hon Maɗatai ya jinjina kai ya ce ""Ina son sanar maka" "na haɗa hannu da Dr Abraham, ta yiyuwa ya janye muƙamin da yake nema ƙarƙashin jam'iyyarsa idan haka ta gaske zamu kai Ali wali ƙasa ne, ka haɗa hannu dani lallai za ka ji daɗi""" """Me ka shirya yi wa matasa idan kaci zaɓen?"" Hon Maɗatai ya ɗaga kai ya kalli Moh sai kuma ya yi" murmushi ya ce """Inganta ilimin su, rage musu kuɗin makaranta samar musu da ayyukan yi cusa musu ra'ayin noma da" "muhimmanci yinta""" """Su kuma ƴan daba fa? Wanda kuke anfani da su wajan cimma burikan ku, bayan yaran ku na keɓe kuna" "tattalin tarbiyar su ba ruwansu da sabgar siyasa sai mu ƴaƴan talakawa ƴan wahala kuma ƴan daba mashaya mune ƴan bangar siyasar ku a yau, a gobe a manta damu jibi kuma a neme mu shine ko?"" Hon Maɗatai ya yi murmushi ya ce ""Mutallab kenan, duk wata nasara da muka samu ai daku zamu rabata ni mulki da siyasa tamkar don su ne aka haifan, ina da kyakkyawan tanadi akan ku ba za a bar rayuwarku" "haka ba""" """Me kake buƙata""" """An saka ka kamo Manager ta kamfanin FS WORLD INVESTMENT COMPANY ko?""" """Wanne kiminin ya faɗa maka?"" Hon Maɗatai ya miƙe tsaye yana zagayawa ya ɗauki fasta ɗinsa ya dinga" "kallon kansa ta ciki can ya ce ""kai yin aikin ne a gabanka, mu ƴan siyasa da idanu ɗaya muke bacci mun" "raba kunnuwanmu ko'ina, ka dai sani a siyasa babu masoyi na dindin haka ma maƙiyi, iya ruwa je fidda kai kowa ya iya allonsa ya ce wanke kuma ni da Ali wali ai sahun qiwa ne ya take na raƙumi kowa da abin" "da yake buƙata, idan ka yi kidnaping yarinyar ka tilasata maka ta saka mini hannu domin na saka hannun" "jari a wannan kamfanin shine abin da nake buƙata"" Jin Mutallab ya yi shiru ya saka ya ce ""Ko baka ji ba?""" """Na ji""" """Mene alaƙar ka da makarantar FGC?""" """Ban sani ba, maganar kuɗin aikinka sai na yi aikin zai sanar. Sai godiya"" yana cewa haka ya bar wajan." Kasancewar Monday ce Safiyyerh ta shirya da wuri zuwa office har yanzu jikinta bai warware ba dole "amma ya zama sai taje. Ba jimawa Md ya shigo bayan sun gaisa fuskarta dai a kame ya shafa kai ya ce ""Manager gari ya ci wuta fa"" idanunta akan wani ducoment tana juya kujera a hankali kamar ba za ta yi magana ba sai kuma ta ce ""Nawa kake buƙata Md?""" """Ko dubu ɗari biyar ne zan yi maleji""" """Zan saka accouter ya baka miliyan ɗaya"" ya dinga mata godiya sosai ta yi murmushi kawai ta ce ""Mene" "ma'anar FS ni kam Md?"" Tsam ya yi da ransa sai kuma ya ce ""Ba zan iya ba ki wannan amsar ba Safiyyerh, zan dai faɗa miki abin da ba ki sani ba"" ta sake juya kujerar hannunta a haɓarta tana murmushi mai kyau" """Ina ji Md""" """Yatsun da kika gani kwanaki gaskiya ne, ana siyar da ƙodar mutane a wannan kanfanin tare da jarirai," "ana kuma dillacin ƙwayoyi, sauran abun ki yi bincike da kan ki za ki iya dacewa"" yana cewa haka ya fita. Kasa motsi Safiyyerh ta yi numfashinta ya tsaya cak da ƙyar ta miƙe ta ɗauki ruwa ta sha ta dawo saman duguwar kujera ta zauna zufa ta dinga yanko mata a hankali ta ware rolling na kanta ta rufe idanu tana" "kiran sunan Allah. Knocking aka yi da ƙyar ta ce ""In""" "Ta buɗe idanu da mamakin ganin wanda ya shigo, ya ƙarasu cikin office ɗin ""Ba dole ki buɗe idanu ba" "Safiyyerh, idanunki kenan?"" Ta yi murmushi tana gyara zamanta" """I. Qasim kai ne""" """Ni ne Safiyyerh""" "Ya nemi waje ya gaisa ta ce ""Yaushe gari kuma?"" Ya yi murmushi ya ce ""Zama likita a garin nan is not" "easy Fiyya, ya batun ciwon kan ki kowa?"" Ta ce" """Yana nan""" """Ayya sorry, akwai maganganu da zan ba ki in sha Allah da allura, gudun kar ki dinga sha ba daidai ba zan" "dinga zuwa dasu kina sha a gabana na yi miki allurar, za ki samu sauƙi in sha Allah""" """Thank you I. Qasim na gode sosai"" wayarsa aka kira ya kalleta sai kuma ya miƙe tsaye tare da yi mata" alama da yana zuwa. Ta bishi da idanu har ya fita. ***** "Safiyyerh ta dinga kallon daddy kamar mahaukaciya saboda rashin fahimta ta ce ""Daddy, aure da Yaya" "Aliyu ka ce dani kuma Safiyyerh, mu duka ƴaƴanka ne fa"" hawaye ya fara suntiri a saman fuskarta ta saka hannunta ta toshe kunnuwata tana girgiza kanta gabaɗaya ta jiƙa hijabin da ta yi sallah da shi da hawaye ""ruɗanin da kake sani a kullum yana shirin haukatar dani daddy, ba auren ne ban yi na'am da shi ba na" "kasa fahimta ne dani da Captain waye wanda ka haifa waye ba ɗanka ba""" """Ku duka yarana ne Maama, idan har kin yarda ni uba ne a gare ki kuma kina so na da ƙaunar farincikina" "ki amince da auren Maama, ba zan taɓa cutar dake ba ni ubana ne, uban ƙwarai kuma yana zaɓawa yaransa abun ƙwarai ne ki yi mini biyayya Safiyyerh, kin ji ko?""" """Na amince daddy zan amince da abin da ya fi wannan ma, Allah Ya sa shine mafi alheri a gare ni"" ta faɗa" "tana rushewa da kuka da sauri kuma ta yi waje ta nufi ɗakinta ta faɗa saman gado ta dinga wani irin kunjin kukan kamar ranta zai fita wai wanne irin abu ne haka? Ta shiga uku meke faruwa aure fa, auren ma da Captain innalillahi wa'inna ilaihirraji'un addu'a take Allah ya yafe mata komai ta fahimta da ƙyar" bacci ya ɗauke ta ko abinci bata ci ba. Cikin dare ta farka ganinta ta yi rufe da bargo ta yi saurin buɗe ido don bata san kwanciya a duhu gashi an kashe mata hasken ɗakin babu mamaki Yaya J ne. Gani ta yi "wajan ɗaya da rabi ta miƙe ta ɗauki ɗan makullin mota da wayarta ta saka hijabi har ƙasa, ƙofa ta buɗe ta sauka downstairs ba kowa ta buɗe ƙofa ta fita mota ta shiga mai gadi ya buɗe mata cikin sauri ta nufi kamfani gari shiru sai hasken fitilo na titi ta dinga duban hanya ba wanda ke biye da ita a haka ta isa kamfanin ta ajjiye motar a waje, ciki ta shiga wajan mai gadi sun jima suna magana ya ce ""Ana shigo da mata cikin dare ana kuma fita da su, na yi bincike abin da ya saka ke iya ɓangaren abinci kika sani to" "akwai asibiti a cikin wannan kamfanin"" ta ce ""Ka ɗauki number motar ko haddacewa?""" """A'a ranki ya daɗe""" """To shikenan na gode Baba, ga wannan"" ta ɗauki kuɗi ta bashi a cikin aljihun rigarta. Tana ƙoƙarin buɗe" "gate ɗin kamfanin ta fita kawai ta ji ƙarar dingowar mutane, ta juya da sauri suka haɗa idanu da Darma" da kuma Goje da Mangal wani irin mummunan faduwar gaba ne ya sameta lokacin da idanunta ya shige cikin nasa shi bai kai ga dingowar ba yana zaune saman katangar shima ɗin ita yake kallo babu ƙiftawa... MUTALLAB PAID BOOK ne a jerin littafan bright pens. We're still on free pages kar ki bari a yi bake. MUTALLAB. "Book 1, 2 &3" 500 Naira 0116886423 Union Bank Na'ima Sulaiman S a tura shaidar biya ta nan 08164069385 via WhatsApp only. DOMIN INGANTA NONO Assalama alaikum Hajiya muna da ingantaccen maganin gyaran nono wadda ya amsa sunansa magani Maganinmu ingantaccen maganine da yake tada jijiyon nonon da suka saki y'ar uwa breast dinki ko yakai silifas saboda kwanciya kikai amfani dashi in sha Allah zakiga amfaninshi acikin 1week maganinmu powder ne yana ciko da breast y gyarasu bashi da illa ajikin mutum munyi amfani da saiwoyi da magunguna gargajiya domin gyaran breast 08063114606 ina garin kano karki sanya y'ar uwa nono yana karawa mace martaba a gurin mai gida maganinmu kowa zai iya sha wadda zatai yaye ko gyara budurwa duk zasu iya sha breast dinki ya ciko yayi bull -bull "[10/18, 9:23 PM] Nanameera: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 11 *Bright pens.. 2nd batch* "Ya ƙura mata idanu yana daga zaune saman katangar a hankali yake girgiza ƙafarsa, fuskarsa rufe da" "baƙin ƙyalle a lokacin duniyar ya ji tana masa daɗi yana jinsa kamar a cikin jirgi ana juyawa dashi, shi ya sa yaƙi sakkowa ƙasa daga katangar, shi kansa bai san wacce irin ƙwaya Mangal ya kawo masa ba. Fiyya ma shi take kallo ganin shi kaɗai ne ya rufe fuskarsa Goje da Darma da Mangal suka zagaye ta, ta juya ta" kalli securityn da yake on duty ranar ta nuna masa Goje """Su kuma waɗannan fa security?"" Kai tsaye ya bata amsa da ""Ban san su ba, amma Hajiya akwai hatsari" "bamu san me suka zo nema ba"" Goje ya matsa kusa da ita yana kallon ta" """Mai dawa wannan ce ƙuruciyar? A hotun kamar bata kai haka girma ba, ƴar firit da ita kamar benu, nan" "kuma an ci kuɗin jama'a an sha madara da milo an yi ɓulɓul"" sai ƙarewa Fiyya kallo yake ita kuma ta yi tsaye tana jin yadda warin wiwi ke dukan hancinta kamar za ta yi amai amma taƙi matasa saboda taurin kai irin na Safiyyerh Abdu Marafa da rashin tsoro. Tsaki ta yi kawai ƙasan zuciyarta kuma tsoro ne fal ga" ƙirjinta dake bugawa kamar zai fito waje sai buɗe manyan idanu waje take yi. """And what is my business with you? Me kuke nema a wannan kamfanin kun zo sai warin ganye kuke" "mini"" Mutallab ya sake buɗe manyan idanunsa jin sautin muryarta zaƙwai a cikin kansa ya kalli bakinta dake motsawa cike da masifa duhun dare ne amma kamfanin haske tar tar ko'ina. Mangal ya lailayo ashar ya dannawa Safiyyerh ""ke dan ƙaniyarki mune muke warin ganyen, su waye sila idan baku ba, ƴar" "wahalar yarinya idan ban bawa tiger namanki ɗanye ya cinye ba""" "Safiyyerh ta juya ta kalli tiger daya hauro ya zauna kusa da Moh, yana zaro harshe waje ta nuna karan da" "hannu ta ce ""abin da ya fi namana ɗanye, banda rainin hankali jikin nawa zaka ɗauka ka bawa shegen karan naku, idan kuɗi kuke buƙata na baku don nasa na yin caji kuke nema, stupid"" Goje ya juya ya kalli" "Mai dawa ya ce ""ba zamu rage wa yarinyar nan tsayin harshe ba kuwa? Kauɗinta ya yi over, ka je ka" "zauna matsalar idan ka sha wannan ƙwayar baka gane komai yanzu babu mamaki jinka kake a saudia""" Moh ya lumshe idanunsa ya sake buɗe su a kan Fiyya duk motsin da take yi a kan idanunsa sai dai ba "wani fahimta yake ba muryarsa a cunkushe mai ban tsoro ya shafa kan tiger ya ce ""shiit""" Tiger ya diro shima ya diro ya tsaya a kan ƙafafuwansa hannunsa ɗaya yana murza gashin kansa wanda ya zama wani iri ba kyan gani na shegun shahararrun ƴan daba ɗin nan. """Mai jeji ƙirit ka ankare ba lokaci ka ɗaƙkota a kafaɗa mu fece kafin kwalawa su kawo kai dan akwai" "kimini a nan wancan mai fararen kayan"" ya nuna securityn wajan wanda shi kaɗai ne kawai ya rage. Safiyyerh ta ja baya tana juya idanunta ta ce ""ban gane ya saɓo ni kafaɗa ba kamar wata ƴar iska ko mara gata, kai naga alamar kai ne shugabansu ko? To wallahi ba wuƙa ba ko bindiga ce bana tsoro kana taɓa ni sai na raba ai an ce ba wani ƙwari ne daku ba"" ta ƙare maganar tana kallon cikin idanun Mutallab" wanda tun ɗazo shi take kallo shi kuma yaƙi furta komai. """Ki iya harshenki ƴar kanzagi ko na fitar miki da jini yanzu na shata miki bille a wannan fuskar kamar" "gwada"" juyawa ta yi ta ce ""Baba wai where are the securities? Where are the rest ka kira su yanzu"" kafin" "baban ya motsa Mangal ya saka ƙafa ya kwarfe shi zuwa ƙasa, ya sake saka ƙafa ya danne masa baki. Darma ya zaro wuƙa ya ce ""Ke fitsararriya ce ko? Ba wata uwar muke nema ba ke muka zo ɗauka, don ke muka cikin wannan kamfanin ke za mu yi kidnaping yanzu kin fahimta kin gane ko, ki shige salin alin ko" "na ɗauke ki yanzu na haura dake wallahi""" Fiyya ta buɗe idanu tana kallon wuƙar dashi kansa Darma ɗin ta yi murmushi zuciyarta kuma bugawa "tsoro ya shige ta, ƙoƙarin danna recoding take a wayarta hannunta ya shiga rawa ta dake a ƙasan zuciyarta tana kiran sunan Allah da ƙyar ta furta ""kidnaping kuma ni, ni Safiyyerh Abdu Marafa za ku sace," "ni Safiyyerh matar soja guda kuna hauka ne ko kuna tunanin mijina zai bari hakan ta kasance?""" "Jin furucin Safiyyerh ya saka Moh sake kallonta da sauri yana hana zuciyarsa abin da yake ji, haka kawai" "ya dinga jin tafasar zuciya ya nufi wajan Safiyyerh jikinsa na rawa idanunsa suka fito waje kamar zasu faɗo da muryar mai ban tsoro mafi muni ba muryar ba ita kanta fuskarsa abar tsoro ce tsaf mutum zai dinga mafarkin ta. Hannunsa riƙe da wuƙa yana kallon cikin idanunta da kyau dab da ita ya ce ""Ba mijinki ba ko ubanki Abdu Marafa aka bani umarnin daƙƙowa ko kashewa sai na yi balle ke"" ya cije bakinsa ya feshi ya cilla mata ƙatuwar baƙar kunama ta shige ƙirjinta kai tsaye, zufa ta dinga yanko mata saboda" "tsananin azaba ta kasa ihu ko kuka ga warin da yake yi yana neman kashe ta, idanunta ya juye ya yi ja ta" "zuba masa idanu tana kallon fuskarsa data yaye,ta miƙa hannu da nufin shafo fuskarsa ta ji ya caka mata" "wuƙar a gefen cikinta ta yi wata ƙara tana buɗe idanu duk yadda jikinta ke rawa ga jini na zuba mai hanata sake kai hannunta ta shafo fuskarsa ba, daidai nan ya yunƙura zai saɓata a kafaɗa suka ji shigowar motoci na jami'an tsaro, bai niyyar barinta ba yadda Goje ke jan shi da ƙarfi ya saka kawai ya" sake ta a wajan yana furta “Mutallab” Ɗaya bayan ɗaya suka kama katangar suka haure daman kuma kaf kamfanin ita ce ƙaramar katanga wacce babu kwalabe jikinta. Securities kala biyu ne dana fararen kaya da masu uniform sai shi da yake sanye da wando three qauter "da farin takalmi da riga baƙa ko p.cap ɗin kansa babu, ya nufe ta sauran suka nufi wajan baba suka fara ɗaukan statement ""Baba kwantar da hankalinka babu abin da zai sameka in sha Allah, bayan waɗannan ƴan daban da suka zo, an bamu tabbacin a daidai yanzu Scorpion ma yana wajan nan ko kuma ya zo"" a hankali Aliyu ya juya ya kalli baban jin tambayar da ake masa, sai kuma ya ɗauke kai ya saka hannu ya ɗauki Fiyya zuwa cikin mota bayan ya kwantar da ita ya tsaya yana kallon wanda ke ɗaya motar a tsaye" "da yake ce masa ""Ya akai kuka barta ta fito cikin dare haka? Macace ita fa""" """Sir ƙuruciya, thanks for the call""" """Anything for you Captain Aliyu"" suka shiga mota duk suka bar wajan ya rage sai jami'an F.i.d kawai da" suke tambayar baba. "Su Goje cikin kwalabati suka shige suka ɓoye suna zare idanu da muzurai a hankali ya ce ""Akwai matsala" "jami'an tsaro ne fal yasin, baka dai bar sheda ba kuma me ya saka ka caka mata wuƙa idan ta mutu fa?""" Moh ya yi shiru can ya ce """Ba zata mutu ba""" """A ciki ka soka mata wuƙar fa? Baka kalli yadda jini ke zuba bane da zaka ce wai ba zata mutu ba?"" Kai" "tsaye Moh ya ce ""ba zata mutu ba""" """A buge kake shi ya sa, askira ka caka mata fa na ɗauka tsoratar da ita kawai za ta yi""" "A firgice ya kalli Goje idanunsa kamar za su faɗo ""Goje, idan ka sake maimaita mini cewa na saka mata" "wuƙa zan maka jahilci yanzu wallahi zan iya kashe ka""" """Kashe ni mana daman ai daba babu wata amana a ciki dole na faɗa, ɗaƙkota aka ce kawai ka yi ba kashe" "ta ba"" Mutallab ya wani juya cikin zafin nama ya damƙo wuyan Goje cikin sauri Darma ya shiga tsakiya ya ce ""Sai godiya kar a yi haka akwai amana, kai Goje ka iya bakinka idan ba farkawa kake so ka yi ka ganka a ƙiyama ba"" Moh ya cije bakinsa kansa na wani irin sara masa yana girgiza kansa ya kalli sama ""duk sanda na sake ganinta sai na kashe ta don uwarka"" duk sukai masa shiru sun daɗe a wajan kafin jami'an tsaron su bar wajan suka fito tare da barin wajan suma kallo ɗaya za ka yi wa Moh ka ɗauke kai saboda" yadda yake huci ya fiddo da ƙarin jikinsa neman inda zai sauke kawai yake. The following days. "I. Qasim ya ce ""Tunda ta bar I.c.u ai Allahamdulilah, she will soon recovering""" """Dr Qasim ba dai abin ku kuke mana na likitoci ba, ya jikin Maama don Allah ita ce kawai last hope ɗina""" "Dr Qasim ya yi murmushi ya ce ""Safiyyerh zata ji sauƙi in sha Allah, ba'a caka mata wuƙar inda za ta yi" "mata illa ba ta zubar da jini sosai ne sai kuma zuriyarta data ninka gudun da take yi, ka yi mata addu'a""" """Shikenan Allah Ya bawa Maama lafiya,zan iya shiga ai kwana biyu ba'a barin mu shiga sai na ji kamar" "har yanzu bata dawo hayyacinta ba"" I. Qasim ya girgiza kai ya ce ""Daddy kana son Safiyyerh da yawa, shiga ka ganta"" har bakin room ɗin da take ciki ya shiga ya shiga sanye da kayan daya dace a shiga aga mara lafiya. I. Qasim ya juya ya fita daddy ya zubawa Safiyyerh idanu tana ƙwace ta sake yin fari a barka da farar mace ta ɗan faɗa an ja mata rigar marasa lafiya zuwa saman ƙirjinta duk da baya kaya a jikin sai iya rigar an buɗe wajan ciwon da akai mata aiki a wajan ya zuba mata idanu ya matsa a hankali yana kama hannunta addu'a ya shiga yi mata sosai ta samu sauƙi zuciyarsa duk babu daɗi idan ya rasa Maama" bai san yaya zai yi ba kuma. """Allah Ya baki lafiya Maama, don Allah ki rage wa kan ki fitina da zaƙewa cikin wasu al'amuran kalli" "yadda za ki saka rayuwarki ta lalace, Safiyyerh ban shirya ba ban shirya ba Safiyyerh"" ya damƙe hannunta" yaga bakinta na motsawa amma sam baya jin me take cewa. Ta shi ya yi ya fita yana sake yi mata addu'a a ransa na samun sauƙi da rangwame. "Bayan ya fito waya ya saka ya kira Aliyu yana ɗagawa ya ce ""Aliyu kana ina ne, an fito ita daga i.c.u amma" "babu kai a wajan bana son haka fa, da baya da yanzu ba ɗaya bane matsayin Safiyyerh ya jima da sauyawa""" """Allah Ya sauwaƙe""" Kawai Aliyu ya furta ta cikin wayar daga nan ya yi shiru ran daddy ya sake ɓaci yana jin kamar ya yi "kuskure na aurawa Aliyu Safiyyerh na damƙa masa dukkan ragamar rayuwarta da tunanin zai kula da lamarin Safiyyerh amma ba lallai hakan ta kasance ba, sosai abubuwa da yawa ke damun zuciyarsa yana hana shi sukuni tare da rashin isasshen bacci, idan Safiyyerh ta tare a gidan mijinta dole ne ya amshi" responsibility da Ubangiji ya ɗora masa na mijinta. "Ummi na kallon daddy da jajayen idanunta ta ce ""Ina ta zuba idanu rayuwar yarinyarta na neman" "lalacewa, ka yi abubuwa da yawa Professor na ja baki na yi shiru da tunanin duk abin da ka yi daidai ne, zuciyata ba zata ɗauka ba Safiyyerh gabaɗaya nawa take ni kawai ta haƙura da aikin wannan Companyn da bana gane masa ai shekarunta bai kai ya kawo ba, ban shirya rasata ba"" daddy ya yi shiru yana kallon" yadda Ummi ke kuka. """Ki tashi muje dare na yi"" da sauri ta kalle shi tana share hawaye ta ce" """Kuma ban gane muje ba zuwa ina?""" """Ai kin san majinyata basa kwana a wannan hospital ɗin, patient ne kawai yake da alhakin kwana"" tun" "kafin ya kammala magana take girgiza masa kai ""i don't think zan iya barin wannan asibitin da Safiyyerh ita kaɗai, ni bana ma ganewa irin haka ka yi musu magana ko a nan zan iya kwana I'll manage"" Daddy ya" "yi gaba yana furta ""Kar na sake maimaita miki"" dole ta miƙe bayan ta sake leƙa Fiyya ta yi waje." "Kafin a rufe shigowar masu ziyara Yaya J ya daɗe zaune gaban Fiyya yana kallon fuskarta, da kwanakin" "baya ne zai riƙe hannunta cikin nasa yana ta mata sannu da addu'a yanzu kallon ta kawai ya kasa koda yin addu'ar ma, can ya miƙe ya fice haka Awais da Dr Hash duk suka shigo basu da tabbacin bacci take ko farkowa ne ba ta yi ba. Wajajen 2 na dare ya buɗe ƙofar ya shigo bayan I. Qasim ya bashi damar hakan daman aikin kwana zai yi idanunsa a kanta har ya shigo ya rufe ƙofar a hankali ya tsaya gabanta" hannunsa biyun zube cikin aljihu ya ɗauki minti a ƙalla ashirin kafin ya ƙarasa ya zauna bakin gadon har yanzu bacci take ya dubi hannun da ruwa yake shiga ya dubi ɗaya hannun da jini ke shiga a hankali ya kama hannun drip ɗin da yake ɗan mitsi-mitsi ya riƙe cikin nasa a hankali yake murza yatsunta can ya ji ta riƙe hannunsa ya ɗaga kai yaga tana jujjuya kanta sai a lokacin ya lura da sauyin ƙarar da na'urar ke yi. Safiyyerh tana buɗe idanu ta rufe saboda wani fau ɗin haske daya shige mata ciki sai kuma hawaye ya "fara bin idanunta ya ɗan sunkuya yana kallon fuskarta. Ta sake buɗe ido ta kalle shi ta dudduba taga ba kowa ta rufe idon still ta buɗe har lokacin jujjuya kanta take yi ""Yaya"" ya yi mata shiru ya sake cewa" """Me na yi musu?"" Still shiru ya yi mata ta buɗe idanu ta kalle sai ta fashe da kuka sosai ƙirjinta na" ɗagawa ya damƙe hannunta """Yaya""" """Safii..."" Ya kira sunanta a hankali ta ce ""Kai na zai cire ƙirjina ciwo cikina ciwo yaya mutuwa zan yi""" """Allah Ya yi miki Rahma"" sai kuma ya matsa dab da kan nata ta saka hannu ta riƙe nashi ta yi shiru a" "hankali ta sake cewa ""Captain""" """Manager""" """Na ce musu mijina soja ne, wai ko sojan zasu kashe balle ni"" ta yi shiru ta sake cewa ""Ka riƙe mini kai na" "ciwo yake mini sosai na shiga uku daddy wayyo"" maimakon ya riƙe kan nata sai ya ɗora goshinsa saman" "nata, ta buɗe idanu ta kalli fuskar Captain kamar zau haɗe da data a nutse ya ce ""sun kashe kin?"" Ta girgiza kai" """Me ya sa?""" """Ban sani ba"" ya ɗan murza mata goshinsa yana kallon cikin idanunta ya ce" """Saboda ke matar soja ce"" ta yi shiru kawai tana kallon shi can ya matsa yana sauka ya zauna saman" kujera. "Washegari da sassafe ƴan sanda suka shigo room ɗin lokacin tana zaune ta ɗan jingina da jikin gado," statement na abin da ya faru suke tambaya. Sp Ghali ya kalli Safiyyerh data sunkuyar da kanta ƙasa ya ce """Da suka zo sun faɗa miki abin da suke buƙata?"" Ta girgiza musu kai." """Za ki iya gane wani daga cikin su? Suna ko kammani?"" Ta ɗago ta kalli Sp Ghali dake tsaye ta ce ""Idan na" "gane kamannin sai me za'a yi to?"" ""Zamu kira a zana mana fuskar wanda kika gane ne""" """To ban gane ba""" "Duk suka tsora mata idanu musamman daddy ta buɗe idanunta itama ta ce ""Kamarya? To na gane ne?""" "Daddy ya ce ""Maama wa kija ji ya ce wani abu?""" Sp Ghali ya dinga kallon Safiyyerh yana jin wani irin abu a ransa na motsa masa sai ya yi murmushi ya ce """dear kin ce basu nemi komai ba, ba wanda kika gane ba suna amma haka kawai sai su caka miki wuƙa" "think Safiyyerh"" sarai Safiyyerh ta tuna sunan da ta ji ya ambata na Mutallab sai ta yi shiru a hankali kuma ta ce" """Sp kasan matsalar da ƙasar nan take ciki musamman Jiharmu akan ƙwacan waya, wayata zasu ƙwace ni" "kuma na hana saboda ina da abubuwa a ciki shine sukai mini haka"" ya jinjina kai ya ce ""Haka ne dear za mu yi bincike zan gano kowaye za mu hukunta shi ƙarƙashin hukuma bisa kundin da aka wanzar, get well soon dear"" ya sake faɗa yana murmushi kan ta dai a ƙasa yake. Sallama sukai dasu daddy suka tafi." Captain na zaune ko tari bai yi ba wayarsa kawai yake dannawa can ya miƙe ya fita daddy ya bisa da kallo haka Yaya J ganin ko sannu bai yi Fiyya ba daman bai jima da zuwa ba. Eng Ali wali ya dinga kaiwa yana kawowa ransa duka a ɓace ya kalli Mai dawa ya ce """Yanzu daka kashe ta fa? Wai me kake nufi da wannan abin da ka yi ne Mutallab?""" """Ka dai na yi mini ihu kamar Malam Abdullahi"" Ali wali ya jinjina kai kawai ya ce ""Kasan ka raina ya ɓaci" "kake cewa haka? Ya zan aike ka ka yi sato yarinya kuma ka caka mata wuƙa salon ka ɓata mini aiki da sanyin safe ake kama fara ba mai dawa""" """To na fasa""" "Ali wali ya buɗe idanu ya ce ""Meka fasa ɗin? Ba dai ɗakko yarinyar ba kake nufi?"" A taƙaice ya ce ""Shi""" """Haba uban mafarauta, kai baka san wasa ba kai kamar ɗa kake a wajena fa"" sai a lokacin Moh ya buɗe" "idanu ya kalli Ali wali yanzu dai normal yake ba'a buge ba ""baka haifan ba, san da aka haifan baka da labari"" ya yi fito yana miƙar da ƙafa ya ce ""To ka kira ɗan naka ya yi maka aikin, mu fa kuke sawa a wahala har a yi zaɓe aci a cinye ka hau kujerar ba lallai yaranka suna ƙasar ba, ba'a rainawa Moh hankali" "ka bar mu matsayin ƴan daban kawai"" Ali wali ya ce" """Ya batun yarinyar?""" """Na ji"" ya ce yana miƙewa tsaye har zai shige ya dawo ya ɗauki bandir ɗin kuɗi ƴan dubu-dubu ya watsa" "cikin aljihu. Sautin daya ji kamar gurnani kamar kuka kuma ya sa ya nufi ƙofar da yaje jin hakan ya murɗa handle zai buɗe cikin sauri Eng Ali wali ya riga shi ya ce ""Haba Mutallab idan iyalina ne a ciki fa?"" Moh ya zubawa Ali wali ido ya kalli ƙofar sai kawai ya fice yabar wajan. ""Ɗan wahalar yaro ɗan jaraba Allah Ya" "nufa na lashe kujerar ganina sai ya yi maka wahala""" "Hon Maɗatai yana zaune ya kalli Sp Ghali ya ce ""Ka lemo record ɗin nasa?""" """Na samu Hon amma cin dai amana ne irin namu na jami'an tsaro amma fidda record ɗin wani criminal" "ya saɓawa kudin tsarin ƙasa"" Hon Maɗatai ya ce ""Waye Mutallab?"" Sp Ghali ya ce ""Nothing serious about him hon, shekaru uku da suka shige an kama shi da laifin kashe matarsa ranar da aka kai masa ita matsayin amarya, kafin nan yana da record na zama gidan yari na watanni sai kuma taɓa guduwa Legas," "a baya kuma kafin hakan shi mafarauci ne ma'abocin shiga jeji ya yi farauta""" """Hon akwai matsala ne? Na ga ka yi shiru?""" """Batun Scorpion ba, case ɗin yarinyar nan Manager a ranar ance shima Scorpion ya je wajan"" Sp Ghali ya" "ce ""Hon Scorpion da ƴan siyasa irin ku yake da matsala fa, ko mutumin daya kashe last yana da za hujjar kisan mune dai bamu sani ba, waye Scorpion ba wanda ya sani jami'an mu na neman shi haka F.i.d Federal investigation department wallahi suna kama shi wannan kisa ne nan take ko su yi masa allurar hauka"" ""Al'amarin Scorpion ya yi kama da ɗaukan fansa fa, za mu zuba ido ya kashe mu ne? Ku hanzarta" "nemo ko waye Sp Ghali""" """In sha Allah Hon""" "Aliyu na zaune saman kujera daddy ya ce ""Kaji ai ko?"" Ya jinjina kai kawai ""Zuwa dare sai ka ɗauke ta ku" "tafi can part ɗin dake gidan daman tuni an zuba komai empty dai yake to ɗazo an kaiwa Safiyyerh kayanta, Aliyu Safiyyerh amana ce idan ka ci amana ba zan yafe maka ba, na yi haƙuri na rabu da kai amma na so kun bar ƙasar gabaɗaya"" addu'a daddy ya yi musu sosai duk da Fiyya bata wajan. Aliyu ya tashi ya fita. A daren ranar ƴan jarida suka shigo saboda hirar da za su da daddy. Sosai aka yi hirar inda yake cewa. ""har kullum ni Professor Abdu Marafa bana goyan mutumin da bashi da wata nagarta wanda baya duba rayuwar yaranmu matsa wanda kuma zuwa gaba sune zasu gaje mu, duk wanda ya buƙaci ku zaɓe shi ku fara duba nagartar shi waye shi, bane background na rayuwarsa waye shi tun farko? kar a yi amfani da talauci da rashin iliminku a saka ku yi zaɓan tumun dare a wannan lokacin matasa yana da kyau ku yi gangami ku magana da murya ku saka iyaye na gida ƙanne da yan'uwa su zaɓi cancanta, wannan masu gamu taliya gishiri ko masu siyan ƙuri'ar mu basu ne wanda suka dace ba, ƙuri'armu ita ce ƴa'cinmu kana siyarwa baka da damar yin zaɓe ku kalli yadda ake mayar da ƙananan yaran ƴan daba masu bangar siyasa ana basu ƙwaya suna aikata zunubi suna kai kansu inda za'a kashe su, ku faɗa mini ko sau kun taɓa ganin ɗan wani daga cikin ƴan takarkarun nan? no! Sai yaran talakawa wanda basu da ilimi ko basu da sana'a sai a yi amfani da wannan damar a janyo su a kurɓata musu rayuwa a ƙarshe kuma ko gidan yari yaro ya tafi wallahi sai dai iyayensa su yi fafutuka duk da cewa har da laifin wasu iyayen a lalacewar yaran, matasa ku haɗa ƙungiya da za ku dinga taimakon juna kar ku yadda da mulkin" "kama karya kuna kallon shekaru huɗu da suka shige yadda zaɓe ya kasance""" """Professor Abdu Marafa kenan a yayin da yake bawa matasa shawara akan su miƙe tsaye domin" "ƙwatuwa jiha ƴan'cinta. Professor mai ya sa duk maganar da zaka yi akan matasa ne? Da batun shaye- shaye ko daba?"" Daddy ya rantse idanunsa yana jin zuciyarsa na yi masa zafi can ya ce" """Ɗan jarida kenan baki abin magana, saboda matasa sune yau, sune gobe haka jibi matasa sune cigaban" "ƙasan idan har aka tsaya musu aka fitar da iri mai kyau, shaye-shaye kuma. ,"" sai kawai ya yi shiru." "Yakasai ya ce ""Gabaɗaya abin da zamu iya naɗa kenan a wannan satin, zamu cigaba da bibiyar professor" Abdu Marafa domin ganin haƙar tasa zata cimma ruwa ko yaya ne? Ni Khalid A Yakasai nake cewa a huta "lafiya""" **** Numfashi Mutallab ke fitarwa a hankali jikinsa duk yanka saboda faɗan da suka yi da ƴan cikin gari bai "san adadin mutanen daya sara ya fitarwa da jini ba, bashi da tabbacin ko bai yi kisa bama rabin fuskarsa duk yanka ne wani wajan har ya zame masa tabo. Goje shima cikinsa rauni ne da ƙyar yake fidda numfashi a hankali ya ce ""Sun kashe Darma fa, ni ban ɗauka haka zuwa kamfel ɗin yake ba, wallahi sun" "kashe Darma na yi ƙoƙarin kai masa ɗauki amma ta kai nake""" """Goje""" """Na'am, Sarki""" """Nemi maɓoya"" ya ce ""Idan na ɓoye kai fa? Naga ba zaka iya tashi ba gwara ni ma kai ma da tuni sun kai" "ka kushewa, gashi wannan ɗan jakar Mangal ban san inda yake ba, balle a jira Ali wali a faɗa masa koda taimakon da zai mana""" """Wai baka jina idan ba ƙiyama kake shirin zuwa ba ka tashi ka face Goje"" da sauri Goje ya miƙe ya yi" "kwana saboda ƙarar motar kwalawa da ya ji, Moh ya saka hannunsa a aljihu ya danna laya tuni ya ɓace a wajan." Abbasa ta dinga kallon Mutallab kamar baya numfashi ta girgiza kawai ta kalli mai yi masa treatment ɗin "bayan ya gama ya miƙe ta ce ""Sannu da ƙoƙari"" ya jinjina mata kai ya fice kawai. Ta yi shiru tana sake kallon Ɗan'malam." "Kamar yadda daddy ya buƙata Safiyyerh ta tare cikin part guda da yake gidan daga can baya, ita dai da to" "kawai take binsa sai kuma idanu ta yarda ba zai zaɓa mata abin da bai dace da rayuwarta ba, ta amince zata zauna da Captain Aliyu zata koyi son shi. Cikin sauri yake gudanar da komai kamar mai tsoran wani abu. A harabar gidan Aliyu na tsaye yana kallon Awais da yake cewa ""Yaya ban gane tambayar da kake" "mini ba""" """Ya sunanka ma?""" "Da mamaki Awais ya ce ""Ikon Allah Yaya ni fa ƙaninka ne tsayin shekaru baka san sunana ba?"" Aliyu ya" "haɗe fuska ba wasa ya ce ""Kuma dole akai na haddace, seriously bana iya tunawa""" """To kai ne Baba captain Aliyu sai Junaid sai Dr Hash sai ni Awais sai Maama"" ""Ok, shi likitan wanne allura" "ya ke yi mata ban damu na san ba a baya yanzu ina so""" """Wai Dr Hash da ya kewa Fiyya? Ban sani ba gaskiya Yaya why not ka tambaye shi?"" Wata tsawa ya" "dakawa Awais yana cewa ""Get lost mumu"" fita ya yi daga cikin gidan gabaɗaya." Har ɗaya saura Safiyyerh na kwance a bedroom ta yi shiru tana jin ciwon na yi mata zafi ta yi kuka sosai "na rashin sanin dalili har bacci ya ɗauke ta. Cikin bacci ta ji an buɗe ƙofar an shigo ta yi saurin rufe idanu yana sanye da kayan bacci farare ya ƙarasu ya duba magungunan yaga ko ɗaya bata sha ba, ya ƙarasa bakin gadon ya zauna shi gabadaya ya manta cikakken sunanta na gaskiya rashin sanin ne zai ce kawai ya saka hannu ya janyo ƙafafuwanta zuwa ƙasa ta matso dab da shi da sauri ta buɗe idanu, suna haɗa idanu" ta tura baki tana juya fuska """Zan saka bindiga na harbe ki a iska kina juyawa"" ta kalle shi ta ce ""To yaya ciwona ka fama mini"" kallon" "da yake mata ya saka ta miƙe zaune ""kin accepting auren?"" Ta jinjina kai ta ce ""Na yi kamar yadda ka yi na san daddy yana da nasa dalilin damuwata ɗaya na rashin sanin gaskiyar ni ce ƴar daddy ko kai, amma aure tun kafin na zo duniya Allah Ya rubuta wanda zai zamo miji gare ni ina da sani daidai gwargwado" "zan zauna ƙarƙashinka duk da baka so na, ko kana so na?"" Ya girgiza mata kai alamar" """A'a""" """Ni ma,sai mu koyi son juna"" ya kalleta kawai sai ya ce ""Muga ciwon"" ""Yaya a wajan ƙirjina ciwon yake" "fa"" da rashin fahimta ya kalli ƙirjin ya kalleta kuma ya nisa ya ce ""Kuma mene a ƙirjin?"" Ya faɗa yana yaye rigar." WE'LL SOON END OF THE FREE PAGES. Ku hanzarta biyan 500 domin karanta Mutallab posting za mu "babu ɓata lokacin ba lallai ku fahimta a yanzu wanda suka shiga paid group sune da batu ko rabin book 1 babu shiga ba. Tsakiyar labarin akwai muke, mene ya faru a farko me zai faru tsakiya ba zaku taɓa sani" ba ko a sashe. MUTALLAB. "Book 1, 2 &3" 500 Naira 0116886423 Union Bank Na'ima Sulaiman S a tura shaidar biya ta nan 08164069385 "[10/21, 2:10 PM] Nanameera: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 12 *Bright pens..2nd batch* "Hannunsa ta cire da sauri ta ce ""ciwon fa a wajan ƙirjin yake yaya"" da mamaki Captain ya kalleta ya kalli" "ƙirjin, da gaske bai san mene matsalarta da hakan ba. Ya ɗauki lokaci kafin ya ce ""kuma mene special a" "ƙirjin?""" """Baka sani ba?"" Fiyya ta buƙaci jin amsa ganin har lokacin kallon ta yake da alama processing" "ƙwaƙwalwarsa take yi shi dai ya san wajan da aka caka mata wuƙar kawai zai gani. Bai sake cewa komai ya miƙe tsaye ya nufi fita, Fiyya ta bisa da idanu tana jinjina rainin wayon Captain yana abu kamar baya fahimta. Ta yi shiru bayan fitar tasa, ta ɗan jingina da jikin gadon thinking me ya sa abubuwa suke juyawa tare da faruwa ne? Ba wani tsanar Captain ne a zuciyarta sosai ba, kawai yadda yake abubuwansa ke ƙular da ita amma kaf yayyanta tana matuƙar so da ƙaunar su. Damuwar bai shige dalilin" "daddy na aura mata Captain ba, bayan shi blood brother ɗinta ne. Yanzu ita ce ba jinin daddy ba ko Aliyu?" Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un! "Da sauri ta riƙe ƙirjinta jin zuciyarta na harbawa, duk yadda take ƙoƙarin ko a cikin bacci ta sake ganin" "gilmar reflection ɗin shi ta gagara, ko sautin muryar tasa ma ta mata sai kuma tunanin mahaukacin daya" caka mata wuƙa ya faɗo cikin ranta wai shi Mutallab? Who is he? """Who is he?""" "Muryarta ta sauka a tsakar kanta tana nanata mata tambayar da zuciyarta ta yi mata a fili. ""To ya ɗauke" "ni ya yi mini me? Safiyyerh Abdu Marafa ai ba sa'ar yara bace, bata zama teddy ba, the whole manager anya ya san me yake ce mini? Ba sai ya sake ganin ko inuwar fiyya ba balle ya aiwatar da abin da ya yi niyya a kaina, aikin banza aikin wofi don ma dai ban san ya zaro wuƙar bane zuwa gaba Captain zan" "lallaɓa ya ara mini bindigarsa problem solved""" Ita kaɗai take ta yin mita ta zubawa madubi idanu bayan ta miƙe tsaye. Wanka ta yi tare da alwala bayan "ta idar da sallah ta ɗauki skin products mai kyau dake sa fatarta laushi ta yi ta ƙyalli, tana son amfani da kayan Aisha s bayero skin care nd herbal medice, ta ɗauki riga mara nauyi saboda ciwon jikin nata. Kasa bacci ta yi ta ɗauki system ɗinta ta fara dannawa hannunta riƙe da ruwan zafi ta jima suna tattaunawa da Md da Secretary ta email kafin ta rufe system ta yi addu'ar bacci ta kwanta sai dai ciwon ya dameta" da zafi har zazzaɓi ya saka ta. "Washegari da ƙyar ta yi sallar asuba don bata yarda ta shige ta, ta rufe jikinta da duvet ta girgiza kai da" "ƙyar baccin ya sake ɗauke ta. Har 12 bata fito ba, sanin abin da ya faru da ita ya saka ba'a nemi ba'asin rashin zuwan nata kamfani ba." "Wajejen ƙarfe biyu ta buɗe idanunta dalilin ƙamshin da ta ji da kuma goshinta da ake murzawa a hankali," ta juya ta kalle shi taga waya ya ke yi muryarsa ƙasa tana jin yadda yake magana one by one jin ana "kallon shi cikin sauri ya ce ""i will call you later""" "Ya juya suka haɗa ido a hankali ta ce ""Ina yini?"" Ya yi mata shiru yana kallon kanta da sauri itama ta kalla" "sai yanzu ta lura kan nata yana cinyarsa ne shi kuma hannunsa na gefen fuskarta ""ɗaga ni""" """Yaya bani lafiya fa"" ya harareta kawai ya yi shiru shima ya ji zazzaɓin ta juya masa baya tana sauke" kanta idanunta rufe zafin zazzaɓin na ƙaruwa ji tayi ya ɗago ta zaune kamar wacce zai zaunar a cinyarsa "ya faki idanunta ya damƙe gefen cikinta ta yi ƙara tana riƙe shi ""Ki dai na yi mini sauti haka, za ki je" "zaman barrack lazy"" ta haɗe fuska tana ji yana taɓa cikinta yaga wajan ciwon na jini ya saka hannu ya" shafi ciwon ya taɓo jinin da hannu can ya miƙe yana juyawa. """Captain jini wajan yake yi ka fama mini na shiga uku"" idan ba kuskuren ji ta yi ba, muryarsa ta ji ya furta" """Allah Ya ƙara""" Cikin dare ne yana tsaye ya fito daga cikin motarsa sanye da manyan kaya na alfarma da fuskarsa rufe da "facemask ya dubi yaran da suke gabansa ya ce ""Ina buƙatar aiki cikin gaggawa bana son wani mistake" "idan aka samu akasi ina cikin taraddi, kuna kallo abu ya taho lokacin na neman cimmana"" Ya buɗe idanu yana sake dudduba inda yake tsaye gani yake kamar ana ganinsa za kuma a iya gane wanene shi." """Mai gida wanne kalar aiki ne ya fito da kai cikin duhuwar nan, faɗa taka cikawa tamu sai da kai iya wuya" "ba wani shege a baya wallahi"" ya ɗan yi murmushin jin daɗi yana kallon mai maganar da kana ganin shi zaka san a buge yake cikin maye kamar kullum" """Idanun mutane nake so, maza uku mata uku"" ya ce yana kallon wanda yake faɗawa maganar ganin" "yadda ya yi shiru kamar dai ban fahimta ba. ""Aiki ja idanun bama na mutum ɗaya ba? Akwai kuskure fa""" """Yanzu akwai wani aiki da zan iya sakawa ka yi mini da zai fi ƙarfinka? Kai ɗin amintacce nane na kuma" "yarda da ƙwarewarka ina jin daɗin business da kai wallahi"" ya zaro kuɗi masu yawan gaske ya miƙa masa, ya sake zaro wata ƙwaya kala daban-daban masu kyan gaske da tsada kana gani kasan manya ne ke shan irin ta. ""Ka fara riƙe wannan kuɗin nasan kana buƙatar caji a kanka kafi yin aiki yadda ya kamata, idan ka kammala ka sanar mini zan faɗa maka inda zaka ajjiye ko?"". ""Ka yi ƙarko irin na dabino sai da kai wallahi yau zam dani, ko kan mutum ka ce na kawo maka a yadda ƙwayar nan ke buɗe mini tunani kawowa zan, ba ƙaramin ilimi ne dani ba da tuni fa ni zan yi ministan kuɗi nace na fasa, kaf ƙasar waye bai sanni ba don uwar mutum"" sambatu kawai yake na maye ya bugu ƙarshen buguwa, shi mutumin dariya kawai yake basa hakan kuma na yi masa daɗi ainun. Mota ya shiga ya bar wajan shi kuma ya gangara ya shiga lungun titin da suke. Tunda ya tafi ya zauna cikin yan'uwansa mashaya yake tunanin ta ina zai fara? Ina zai samu mutane har ya ƙwaƙwule idanunsu hankali kwance? Ya yi shiru yana kallon sama yana ta furzar" da iska mai ɗauke da warin sholi dana bakin gabaɗaya. ***** Mutallab ya tanƙwashe ƙafafuwansa kamar wani sarki ya kuma ɗora hannunsa saman cinyarsa cikin "kowacce ƙafa, kallon Abbasa yake tun ɗazo take magana yaƙi cewa komai ko tari kuma bai yi ba, raunukan jikinsa ya kame sai saura, ido biyu za ka yi da shi ba zaka ƙara marmarin kallon nasa ba, babu rahama a fuskarsa nan zaka ɗauka tunda Ammo ta kawo shi duniya bai taɓa yin murmushi ba, ko haɗa" hanya da inda fara'a take. """Kalli nan""" "Ya dubi abin da take nuna masa, zanen kamfanin ne da photon jariran sai kuma kalmar A.M.A ""Da fari" "mu fara gano ma'anar kalmar A.M.A, photon jariran kuma mai sauƙi ne ana nuna maka har jarirai da aka haifa yau ana siyar da shi a kamfanin FS WORLD INVESTMENT COMPANY, abu biyu ne wanda dole za ka yi ko kusan ukun, da fari sato ita wannan yarinyar ta yiwu a samu wani haske tattare da ita, na biyu kasan yadda duk ka yi ka mallake wannan kamfanin cikin sauƙi, na uku. ,"" sai kuma ta yi shiru ta dinga" kallon Moh ciki da bai """Waye Mutallab, waye kai, dole ka faɗa mini asalin waye kai kana ji na?""" """To na haƙura""" "Ya miƙe tsaye a hankali a lokacin ras yake sai abubuwan da sukai masa tsaye a zuciya da maƙoshi ""Dole" "na san waye kai, ko ka faɗa mini ko ba ka faɗa ba, abu na uku sai ranar da asalin naka ya zo kunnuwana zan furta maka shi"" bai dai yi magana ba, hannunsa zube cikin alijun kayan da Abbasa ta basa ya sauya da ƙyar yafi ƙarfin minti ashirin a tsayen yana harhaɗa kalmomin abin da zai ce mata ransa duk a jagole." """Lalacewar Moh bai kai ya sato yarinya ba""" """Kuma dole a yi hakan fa""" "Ya yi waje abinsa yana yana ƙoƙarin ficewa daga cikin bukkar ta ce ""Baka da lokaci fa Mutallab, kuma" "baka da ikon taɓa ta a waje idan ba kana shirin komawa gidan yari bane, kasan yadda za ka yi dai wish you all the Mutallab""" "Bai ƙara bi ta kanta ba, ya dinga ɗora ƙafafuwansa a ƙasa kamar mai tsoron taka ƙasa sai haɗe fuska yake" "yana kwaɓewa duniyar ya ji ta yi maza zafi ta ko'ina, ya rasa ina zai je me kuma zai yi sai ɗaga yatsun ƙafarsa yake wanda suke zara-zara matar nan Abbasa ta fara takura masa ko waye ya ce ta yi masa gyaran farce? Yama a ka yi ta samu mai yin aski ya wani kwashe masa suma? Bakin bishiya ya samu ya zauna ya sunkuyar da kansa ƙasa, zufa ta shiga tsattsafo masa ta tsakiyar goshi ya sa yatsa ɗaya yana gogewa ya shafa jikinsa ba kayan garawa ko ɗaya yana buƙatar fita daga yanayin da yake ciki, baya son" tunawa ko da wasa. "_“One day i will leave you, duk son nan da nake maka”_" "Ya ji saukar muryarta a kansa ta sauka har ƙasan zuciyarsa a ɗan lumshe idanunsa da ya yi, ya juya zuwa" "gefe sai yake ganin bidiyon abin da ya faru bayan kammala assembly, at that time yana can baya zaune ya yi shiru yana kallon students bai san da zuwanta ba sai ganinta ya yi ta baya kamar zata shige jikinsa ya fiddo manyan idanunsa waje yana miƙewa tsaye hannunsa ɗaya zube a aljihu ya dinga kallon ta da" "ƙyar ya furta ""And what is this Safiyyerh?""" """Bestie shi ake cewa love mana"" ta langwaɓar da kai gefe yana sake kallon yaluwar fuskarta kamar" "zabiya. ""To iskanci za ki mini?""" """Iskanci kuma bestie? Me ya sa kake haka ne, son ka kawai nake yi fa why are you doing this to me? Kai" "ba'a gane maka sam? Ko murmushin masoya ne ka dinga yi mini mana, bafa ni na ɗorawa kai na son ka ba"" idanunta ya cika da waye tana jin zuciyarta na yi mata zafi bata ganin komai a idanunta sai fuskar Mutallab." """A love? Shine za a yi wa mutum fyaɗe a soyayyar??"" Ta buɗe idanu tana rufe baki jikinta har rawa yake" "tana jin kamar ta idda abin da zuriyarta ke umartar ta ""To ka yi haƙuri idan dai na mutu ka huta, kuma idan baka zo gidanmu yau ba Allah a wajan Ammo zan kwana"" fuskar nan a ɗaure ya ja sirirn tsaki ya shige cikin class kafin ya ƙarasa ya ƙara jiyo ta a bayansa tana sake yunƙurin riƙe shi da sauri ta juya sai" kuma ta ɗauki school bag ɗinta ta fice daga makarantar tana kuka. "*** ""i missed the hug"" ya furta ƙasan zuciyarsa lokacin da bidiyon abin ya ɗauke daga kusa da shi, ya yi" shiru yana tunani har yamma ta yi lis bashi da niyyar tashi daga wajan baya son shiga cikin jama'a yana jin nan ɗin shine daidai da ina ya kamata ya ɓoyewa kwalawa. He feels uncomfortable a cikin jama'a haka nan. Safiyyerh na zaune bayan ta dawo daga kamfani ko ɗaki bata shiga ba idan ta tuna yadda Hon Maɗatai "ya sake matsa mata akan hannun jarin da yake son sawa a FS WORLD INVESTMENT COMPANY sai ranta ya sake ɓaci, duk dukiyar da Ubangiji Ya bashi bai gode Allah ba, mutane nawa ne a wannan duniyar da basa ci, idan anci na safe ana fargabar na rana, idan na rana ya samu dare kuma sai dai a yi salatin Annabi a sha ruwa a kwanta, masifar rayuwa ta yi wa talaka dirar mikiya, yunwa na neman illata su ga lalura ga rashin aikin yi? Amma hon Maɗatai shi dukiya yake nema idanu rufe ƴan siyasa da yawa kansu kawai suka sani suke ginawa, mene amfanin talaka ya je ya yi zaɓen? Gabaɗaya sabgogin dimokuraɗiyya ya lalace son zuciya kowa yake bi. Ta yi tsaki tana jin ko zata rasa kujerar Manager ɗin ba zata taɓa bari" Hon Maɗatai ya saka hannu a kamfanin ba. "Miƙewa ta yi ta nufi bedroom bata ɗauki wani lokaci ba ta fito sanye da wando da riga,wandon iya cinya" "kanta ko ɗan kwali babu da mamaki take kallon Captain ganin ya ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya yana danna mata system ga wayarta a hannunsa kafin ta ƙarasu ya kashe system ɗin ya ajjiye har wayar. ""Yaya me kake nema a system ɗita kuma?"" Ya yi mata shiru ta zauna kawai tana buɗewa bata sake kallon shi ba, ta shiga duba dukkan ayyukan da aka fitar yau da sauri ta kira accouter da number da take amfani da shi na" kamfanin tana girgiza ƙafa a hankali cikin faɗa ta ce """Accouter me nake gani a haka? Kuɗi fa kimanin miliyan 500m yanzu sun shigo account na kamfani dana" "gani a bayanai, bayan tafiyata me aka fitar ne shinkafa ko me?"" Faɗa take sosai domin ta iya faɗa ajin" ƙarshe ce a fannin. """Manager nifa kina tunawa accouter ne kawai, bani ke da alhakin saka hannu a fitar kaya ko shigowar su" "ba, kawai ni ke saka hannu a duk wani kuɗi da zai shigo ya fita, i am nothing but a Accounter""" "Miƙewa tsaye ta yi tana riƙe ƙugu ta ce ""Rubbish; ka tura mini ducoment na PDF via email na abin da aka" "siya har miliyan 500m yanzu yanzu accouter""" """Ki yi magana da Md ni kawai kuɗin naga shigowar su babu wani file daya zo officer nawa, trust me" "manager ba zan ɓoye miki, na san dai bayan tafiyarki Professor Abdu Marafa ya shigo kamfanin"" ""daddy!""" "Ta furta da ƙarfi ""E, mahaifinki shi""" """Kamarya to?""" """Shine ban sani ba"" sai kawai ta kashe wayar ta ajjiye waje guda, ta sauke numfashi da ƙyar ta shiga uku" "meke shirin faruwa ya ake ƙoƙarin amfani da ita ba tare data sani ba?""" """Yaya"" bai amsa ba idanunsa a ƙafarta ta ce ""Yaya bacci nake ji"" ""to ina ruwana""" Sai kawai yaga ta ɗora kanta a cinyarsa maimakon ta juya masa baya sai ta juyo wajan cikinsa ta yi shiru "tana kallon ƙirjinsa dake buɗe. Ta yi shiru tana sauke numfashi shi dai bai yi magana ba, bai ɗauka haka take da masifa ba yana jin ƙirjinta na ɗagawa a hankali kuma bacci ya ɗauke ta. Cikin baccin ta ji hucin numfashi ta buɗe idanu kallonsa ta dinga yi yadda ya kifa fuskarsa a tata hannunsa ɗaya tamƙe cikin nata ""Captain"" da sauri ya buɗe idanun ya ƙurawa cikin idanunta ido sai kuma ya ɗauke fuska yana haɗe rai. Fiyya bata ce komai ba ta miƙe zaune shi kuma ya shige cikin part ɗinsa yana taku da sauri sai shafa" kai yake yi. Notification ta gani kamar wancan lokacin saƙo ne ta dm nata. Ta buɗe ba wani magana mai tsayi bane sai dai maganar dab take da rusa tunaninta ta bi saƙon da kallo inda ake cewa. "_“bai ci a ce kin yi mantuwa mai nisan haka ba, ki tuna akwai hakƙin wani kan ki Allah Yana kallon ki" TIGER“_ ta dafe kan ta to hakƙin waye a kanta waye mai wannan saƙon kuma? Tsaki ta yi ta miƙe ta bar parlon. Bata sake ganin Captain ba har dare ta yi kwanciyarta. **** Cikin sauri take tafiya tana yi tana juyawa sauri take ta isa chemist amsar maganin ga dare ya raba mijin "nata ya fita. Kamar daga sama taga mutane sun tsaya gabanta fuska rufe ""Su waye ku? Don Allah ku rufa mini asiri magani zan siyo"" muryarta na rawa ta yi maganar. Haɗa idanu sukai sai suka ɗaga ta sama tare da danna ta cikin napep ɗin basu tsaya ko'ina ba sai wani kango a nan taga wasu mutanen kwance kamar basu da rai, kuka take tana duk addu'ar data zo bakinta ""Don Allah kar ku cutar dani don Allah ku" "rufa mini asiri da yarana da rayuwarsu""" Tana ji tana gani suka danneta tun tana ihu har ta kasa jini kamar an yanka rago babu imani suka cire ƙwayar idanunta duk biyun tare da watsa su cikin aliju da gudu suka fice daga kangon. "Bayan ta dawo daga wajan aiki ta shige gidan Anty Turai saboda kiran da ta yi mata, a parlo ta samu Anty" "Turai da yaranta da kuma wasu ƴan mata zaune. ""Ina yini Anty?""" """Sannu matar Captain Aliyu Marafa?"" Cewar Anty Turai ita dai Safiyyerh idanunta akan waya bata ce" "komai ba Waheeda ta ce ""Mama wai shi Uncle captain ɗin son ta yake yi ne? Ni banga abin so a jikin wannan zabiyar ba sam sam wallahi"" Zahiderh ta yi saurin cewa ""Ina fa? Captain ne zai ce yana son Fiyya" "never wallahi, kawai dai auren dole aka yi masa, wannan fari ko na lalura""" "Safiyyerh dai jinsu take Anty Turai ta ce ""Sannu Safiyyerh, ya kamfanin yanzu ai Aliyun ya bar nan wajan" "Zahiderh ya zo ki dinga haƙuri da shi ya jaddada mini baya buƙatar ki cikin rayuwarsa bai san me zai yi da zabiya ba"" miƙewa Safiyyerh ta yi ta ce ""To Anty a ɗaura masa aure da Zahiderh ni bani da wata matsala, zabiya kuma ina jira ku halitto irin kalar idan da sauƙi, so kuma ba abin da ya yi mini zafi da shi zan zauna da mijina haka tunda zaɓin daddy ne, wallahi babu wanda ya kai level ɗin ɗagawa Fiyya hankali"" Anty Turai ta miƙe tana nuna Fiyya idanunta ya rufe sam bata kula da shigowar shi ba, balle ankarar da ita da" su Waheeda suke ta ɗaga hannu zata mari Fiyya dake tsaye tana juya idanunta ta ji an riƙe hannun. "Tun zuwan shi ta ji ƙamshin turaren nasa, ya tsaya a bayanta Anty Turai ta kalli Aliyu ta kasa cewa komai" "ya saki hannunta yana matsawa bayan Fiyya ya zagaye hannunsa a ƙugunta ya jata jikinsa daga baya yana sake kallon Anty Turai ""Shekararki nawa Anty yaushe na zo gidan naki kuma? And who told you bana son ta?"" Duk a dagule yake maganar yana sake haɗe Fiyya da ƙirjinsa kasancewarta duguwa sosai" "so ma sha Allah. ""Aliyu ni zaka shigo gida ka faɗawa haka?""" Bai kalleta ba sai Fiyya daya kalla wacce take shirin juyawa idanunta cike da hawaye ya yi saurin riƙo "hannunta yana ""Wait"" sai kawai ta kifa kanta a ƙirjinsa tana shassheƙar kukan da bata shirya saboda" "ganin idanunsa ""Anty karki sake mini haka""" """Idan na sake me za ka yi Aliyu na ce me za ka yi?"" Ya girgiza kai ya rungume Fiyya tsam a jikinsa ya ce" """Ban san me zan iya yi ba, kawai dai na faɗa miki, kuma i love my wife"" Fiyya ta yi saurin ɗago kai ta kalle shi ya ɗage mata gira ""Yes, I Iove You Safii"" yana cewa haka ya kama hannunta suka fice." *** Suna zaune a dabarsu ya yi sauri ya miƙe tsaye Goje ya ce """Sai godiya, ina aka nufa don shirwa kake baka jewar banza, ɓauna mai tafiyar ɗaukan rai jeji naka" "dabbobi naka, a lafiya mai dawa"" jikinsa ya ji ya fara kakkarwa tsohon tsuminsa na neman tashi ya yi ƙasa da kansa yana ƙoƙarin hana kansa yin kirari da amsar saƙon Goje, ya bar wannan layin tuni. Da ƙyar yana girgiza kai ya ce" """Goje""" """Sai godiya, wuya a ina wuya a daji kai ne mai dawa da jeji na Malam Abdu shalelen Ammo, ƙanin" "Sa'adah da Bafullatana a lafiya aminin Hamida, ɓauna taka mesa taka ba wani bayanka jan biro maganin daƙiƙin yaro Allah Ya ja da ran mai dawa"" gabaɗaya jikin Mai dawa ɓari yake yana damƙe hannunsa wajan ganin mai ɗaga su sama ba har can cikin kansa yake jin kirarin. Kawai ya juya ya bar wajan ""Wai" "ina zaka ne kasan yanayin da ake ciki fa akwai cinnaku""" """Baka haifan ba balle ka tambayan karka biyo ni"" yana cewa haka ya bar wajan ya jima yana tafiya kafin" ya ƙarasu gidan sai ya saka maƙulli ya buɗe ya shiga. A ɓangaren su Safiyyerh tunda suka bar gidan Anty Turai suka shiga mota basu ce komai ba ya kuma "haɗe fuska itama bata ce komai ba, daidai wani gida a bakin titi taga ya tsaya ya kalle ta ""Kar ki fito jira ni nan"" ta jinjina masa kai. Fita ya yi ta jingina tana ɗaukan waya, abin da ta fara cin karo da shi a X picture ɗin wani kyakkyawan yaro yana murmushi ya rufe idanunsa saboda hasken da ya yi masa yawa kamar ka" "taɓa shi jini ya fito, ta dinga kallon picture ɗin sai kawai ta yi skipping zuwa next tweet." "A hankali ya buɗe ƙofar ya shiga idanunsa zube a saman tafkeken screen ɗin computer dake jikin bango," "gabaɗaya wajan nau'in kayan computer ne kala-kala. Ya ɗan dafa kafaɗar wanda yake zaune akan kujera yana juyawa a hankali, kallo ɗaya zaka yi masa kasan mayen computer ne masanin hakin da duk wani surƙulle. Captain ya ce ""Where are you hiding?"" Ya ɗaga idanunsa a hankali ya kalli Captain bai ce komai ba kuma ya cigaba da danna wayar, Captain ya saka hannu ya dungure masa kai ya nemi waje ya zauna yana taɓa computer shima. Da sauri ya miƙe kuma jin sautin muryarta da yadda take ƙoƙarin buɗe ƙofar ya yi saurin miƙewa ya nufi ƙofar daidai nan Fiyya ta shigo ""Yaya gaskiya yunwa nake ji akwai hadari" "sosai a gari ina tsoron ruwa""" """Muje""" Ya yi saurin faɗa yana kama hannunta tare da rufe ta da jikinsa leƙawa take son yi ya saka hannu ya juyar "da fuskarta ya jata waje, shima ɗin dake zaune ya juyo a nutse ganin sun fita ya saka ya cigaba da abin da yake yi." "Cikin dare Fiyya na bacci ta ji ana buga ƙofar parlon kamar za a cire ta, ta miƙe da sauri riga da wando ne" "jikinta na bacci wandon iya cinya ta saka slipper ta fito, tana mamakin mai ya sa Captain ya kai dare har haka? Ta buɗe ƙofar ""Yaya ka tashe ni daga musulmin bacci da nake..."" Shiru ta yi tana yin baya ganin shi tsaye a bakin ƙofa su Goje da Mangal a bayansa ""Kai ne me ka zo yi mini har gidan mijina, matar aure ce" "ni fa"" banko ƙofar Moh ya yi ya shiga yana ƙarewa parlon kallo" """Mai dawa ɗauke ta mu shige kar a yi ta kwanaki"" ta gudu Fiyya ta juya zuwa part ɗin Captain tana kirin" "sunansa a tsora ce kafin ta ƙarasa Moh ya saka ƙafa ya falleta ta faɗi ƙasan tayal idanunsa ya yi jajur domin ba haka ya zo da su ba, jin ana shirin buɗe ƙofar ɗakin Captain Moh ya kalli Goje da sauri Goje ya laɓe a baya kafin Captain ya fito, cikin sauri ya rufe fuskarsa da ƙyalle." """Safii are you ok? Peanut ihun nan fa wife?"" Yana fitowa Goje ya saka gora ya maka masa a ka" kasancewar Captain bai shirya ba ya faɗi a wajan da sauri kuma Moh ya ce Goje ya ɗauki Fiyya ko me ya tuna sai ya saka hannu ɗaya ya sunkuceta a kafaɗa yana ɗaga wuƙa sama suka fice daga gidan... MUTALLAB. "Book 1, 2 &3" 500 Naira 0116886423 Union Bank Na'ima Sulaiman S a tura shaidar biya ta nan 08164069385 Zan yi cutting free a shafi na 15 in sha Allah. Wannan shafin ku hanzarta yin payment "kafin wannan lokacin yanzu kuma na labarin a rufe yake zuwa gaba za ku ce kun shiga uku ashe haka abin yake ina ƙara tuna muku ba fa farkon labarin muke a tsakiya muke waya san mene ya faru a farkon? Me kuma zai faru a gaba? Just pay 500 naira only.[10/23, 5:43 PM] Nanameera: *❤🔥" MUTALLAB ❤🔥* Page 13 *Bright pens..2nd batch* "Safiyyerh na durƙushe a ɗan ƙaramin ɗakin da suka ajjiye ta ciki, warin sigari ya cika ɗakin sai yunƙurin" "amai take yi ta kasa, ta shiga tashin hankali da tunanin suwaye waɗannan da suka je har gidan mijinta suka dake shi tare da yin kidnapped ɗinta? Me suke buƙata a wajanta waya saka su yin hakan? Da alama ba kuɗi suke nema ba wani muradi ne a ran su da suke son cikawa manufar da bata san ta mece ce ba. Ta ɗago kanta da ƙyar tana buɗe kumburarrun idanunta saboda kukan da ta yi da hanzari ta fara buga" ƙofar da hannunta tana girgizawa tare da faɗin. """Wai baku da imani ne me na yi muku idan kuɗi kuke buƙata ku bani waya na kira daddyna zai biya duk" "abin da kuka buƙata na fansa ta, macace ni fa a gidan mijina kuka je har gabansa kuka sato ni, don Allah ku buɗe mini wallahi wari zai kashe ni babu iska a ɗakin ku tausaya mini"" abin da take faɗa tana dukan ƙofar da hannu, amma ko tari ba ta ji sun yi ba, kuma tana da tabbacin suna jinta ta sake ɗaga murya ta" ce """For the sake of Allah, da girman iyayenku ku mayar dani gida gaban iyayena me na yi da za a yi garkuwa" "dani,ku barni da raina kar ku kashe ni zan muku kwatancen gidanmu ku je wajan daddyna a baku dukkan kuɗin da kuke buƙata, idan ba ku yarda ba ku a cikin kuɗina zan baku wallahi mahaifina ya ji abin da ya same ni mutuwa zai yi, innalillahi wa'inna ilaihirraji'un me na yi muku ne kukai garkuwa dani na shiga uku ni Safiyyerh Allah ka kawo mini ɗauki"" ta sake durƙushewa a bakin ƙofar ta tura kanta cikin cinyoyinta saboda warin sholi daya gama hautsina mata ciki kamar kayan cikinta zai fito haka Safiyyerh ke ji, duk girman idanunta sai da ya yi mitsi-mitsi abin ka da zabiya da ƙyar take buɗe idanun nan, ba sunan wanda bata kira ba hadda Anty Turai akan su kawo mata ɗauki Yaya J ya sha kira. Ta sauke ajjiyar zuciya tana karanta addu'ar neman tsari da kuɓuta daga magauta ta yi zumbur ta miƙe saboda fitsarin" dake mintsinin mararta. "A can wajan ɗakin a cikin gidan da su Goje basu san da shi ba, duk suna zaune suna busa kayan shaye-" "shayensu hayaƙi ya cika wajan, wani na shan sigari wani na shan sholi wani wiwi sun hautsina sai surutai suke yi. Moh na gefe ɗaya ƙwance ƙafarsa ya ɗora akan ɗaya idan yana acting ka ɗauka jinin sarauta ne ko wanda yake da aljanu sarakai a kansa, duk ihun da Fiyya take yi da surutai yana jinta. Goje ya kalle shi" "ya ce ""Wannan yarinyar tafa dame mu wallahi, ka kira ka faɗa masa tunjiya mun ɗakko ta ya san abin yi""" Shiru ya yi yana sake kaɗa ƙafarsa a hankali har lokacin idanunsa a rufe yake. Goje ya kalli ƙofar ɗakin da "Fiyya ke ciki ya sake kallon Moh kafin ya miƙe tsaye ya ce ""Ina da matsala da jin kuka gaskiya, ko dai a" "rufe mata bakin ko a ɓara bakin biyu yanzu da askira""" """Mangal""" "Da sauri Mangal ya kalli Moh jin ya kira shi domin tunjiya da suka ɗakko Fiyya ko tari bai sake yi ba, bai" "runtsa ba har gari ya hawaye ba wanda kuma ya kula a cikin su. ""Ankar sarki, faɗa taka cikawa tamu" "akwai wani sagi a ƙasa ne?""" """Bana son hayaƙin nan"" lokaci guda suka kalle shi a take suka cillar da sigarin tare da saka ƙafa suka" "murje ""Angama sai mene na gaba?"" Bai magana ba ya juya musu baya a hankali ya buɗe idanunsa ya zaro takardar da yake faman ajjiya kamar rai, kusan kullum yana karantawa sama da sau wajan biyar a rana abu ɗaya ne amma sai ya ji baya fahimta,baya kuma ganewa, ya zubawa rubutun idanu Goje shima ya leƙo kai yana kallo ganin ya ninke ya ɓoye ya saka ya yi siririn tsaki ""Na ji takaicin rashin makarantar" "da ban, shi ilimi ko yaya yana da rana""" """Ina zargin wannan takardar bata tsafi bace, kamar ita ce ransa ko iskar dake shaƙa ya manta da komai" "amma banda ita, watarana sai na sace ta yasin"" dariya Goje kawai ya yi ya san Mangal faɗa kawai yake yi. ""Mai dawa kasan a yankinmu an sace mutane har biyu, yau da sakaliya anga gawar ɗaya ba idanu"" ya juyo a hankali ya zubawa Goje idanu kamar mai tunani sai kawai ya miƙe yana taku ɗaiɗai ya fice daga" "cikin gidan, suka bisa da idanu ganin yau ya zama wani so silence kamar ba Moh ba." "Safiyyerh ta ji an turo ƙofar da sauri ta miƙe tsaye tare da ja baya, mutum biyu take gani Goje da Mangal" "shi kuwa tunda ya cillar da ita a ɗakin bata ƙara ganin shi ba. Abincin hannunsa ya cilla mata da ledar ruwa pure water ta kalli takeaway ɗin da ruwan, ta ɗauke kai a hankali tana sake ja baya ""Saura ki ƙi ci kamar na ɗazo, idan kuma kika sake yi mana amai a nan sai kin lashe abin ki tas"" ta ƙurawa wajan ido ta ce ""Ba zan iya cin abinci a nan ba, ni bana shan ruwan leda abincin ma ba irin wannan nake so ba, ko" "nama babu akai""" """Kuma a ina kike tunanin ganin nama? Don ma kin samu an kawo miki dar yarinya saboda kina Manager" "kun saba cin mai kyau a sha mai kyau, a saka suttura a shiga mota a kwana cikin a.c ga naru a gida 24/7, a ci shinkafa basmati da ruwan gora dole ki ce haka, ɗiyar ƙaruna""" "Girgiza masa kai ta yi muryarta na rawa ta ce ""Da gaske nake maka, ni kawai a bani ruwan jakar da lemo" "ko snacks"" Goje ya dinga kallon ta ganin she is serious juyawa ya yi zai bar wajan ta yi saurin cewa ""Don" Allah ku bani waya na kira daddy na maka alƙawarin yanzu za a kawo kuɗin da kuke buƙata wajan nan "akwai sauro headache da fever zai kamani"" ta langwaɓar da kai gefe alamar neman alfama." """Ki jira Mai dawa ya zo, sai ki tambaya bani da ikon haka. Da kike maganar kuɗi kin ji mun ce muna" "buƙata ne? Ba kidnapped ɗin ki mukai domin a bamu kuɗin fansa ba, mun sato ki saboda a koyawa asawa hankali a rage masa tsayin harshensa da yake da kauɗi kin gane? Daga yanzu ki cire rai da samun" "ƴanci""" """Daddy?""" "Safiyyerh ta faɗa a gigice tana dafe kan ta idanunta ya cika da hawaye, tausayin kanta dana daddy ya" "cika mata zuciya babu wani wanda take so a duniya sama da daddy da Ummi me za su yi masa rayuwarta suke son kassarawa tabbas idan suka taɓa kimar mahaifinta. ""Me daddy ya yi muki, mene alaƙae sato ni da kukai da mahaifina me kuke nema a wajansa na roƙe ka da girman Allah kar ku cutar da mahaifinsa kar ku illata rayuwarsa, shi ne jin daɗi da farincikin zuciyata, ku duka kuna da iyaye na tabbata ba za ku" "so rasa su a rayuwarku ba ka ji tausayina Please brother""" """Ni ba brother naki bane ni ɗan daba ne sunana Goje kin gane, idan kina buƙatar wani abu kina iya" "bubbuga ƙofar"" kafin Safiyyerh ta yi magana ya yi sauri rufo ƙofar ya fita. Ya je ya samu Moh a wajen gidan zaune ya sake tanƙwashe ƙafafuwansa ya kalle shi sosai kana ya ce" """Scorpion""" """Kana son faɗar sunan, zan manna maka hauka Goje zan ja maka ruwa"". ""Me ya sa baka son na dinga" "faɗa ne? Ai dafinka ma ya fi na kunama ni ina son sunan"" Moh ya yi shiru yana sake harɗe hannayensa duka biyun ya zubawa samaniyya idanu. ""Idan zan nuna maka asalin kalata a Scorpion ba zaka ɗauka ba," "za ka daina haɗa idanuwa dani sauƙin sunan na wajan faɗa ne, ka kalle ni a Moh ko Mai dawa ok""" """Yadda ka ce haka za a yi, ya zamu yi da yarinyar nan yanzu? Kwananta ɗaya da wuni fa, kuma bata cin" "abinci""" Cikin rashin fahimta Moh ke kallon Goje su yake ya tambaye shi wacce yarinyar bakinsa kuma ya yi masa "nauyi ya dinga juya idanunsa akan fuskar Goje, fahimtar hakan ya saka shima Goje cewa" """Manager wacce Ali wali ya saka mu ɗakko yarinyar da muka je gidansu jiya"" haɗe fuska sosai Mai dawa" ya yi idanunsa ya shige ciki haka kawai ɓacin ransa ya sake ninkuwa ya yi shiru ya datse laɓɓansa kamar "zai raba su gida biyu ya yunƙura zai tashi Goje ya ce ""Wannan sauyin na yanzu na mene? Na fara jin daɗi" "a raina kwana biyu baka sha ƙwaya ba, lafiya dai?""" """Mutallab"" still ya yi shiru Goje ya sake kiran sunansa yana leƙa fuskarsa ganin babu alamar zai kula shi" kawai ya miƙe ya fice ya bar wajan. "***Gabaɗaya suna zaune a cikin parlon banda shi dake tsaye, zuwan nasan ake jira amma tunda ya shigo" "bai kalli kowa ba balle ya yi magana, fuskar nan a murtuke kamar kodayaushe. Yaya J, Awais Dr Hash, Anty Turai Waheeda sai Ummi dake zan gefe bata cewa komai sai goge hawayen da yaƙi tsaya mata take yi. Daddy baya uhm baya uhm'uhm kansa a ƙasa zuciyarsa ta bugawa da ƙarfi yama kasa yarda da abin da ake faɗa har lokacin gani yake wasa ake yi masa da hankali da kuma wahalar da zuciyarsa da ake" saboda anga yana ƙaunar Safiyyerh ƙauna mai tarin yawa an fahimci ita ce rauninsa. """Captain Aliyu Abdu Marafa shiru ba naka bane, ba muzo nan da a shiru ba a matsalar kidnapping ba a yi" "mana wasa"" cewar Sp Ghali daya ƙara amsar case ɗin Safiyyerh a karo na biyu ya ɗaga kai ya kalli masu gadin asalin gidan da kuma na part ɗin su Captain sai kuma ya ce ""Heyy you man, mene sunanka da aikin" "da kake yi?"" Cikin rawar murya ya ce ""Sunana Isma'il ni mai gadi ne Yallaɓai""" """Isma'il sanda abin ya faru ƙarfe nawa ne? A daidai lokacin kana ina kuma?"" ""Ban san ƙarfe nawa bane a" "lokacin don ban duba a gogo ba, sanda abin ya faru kuma ina bakin gate ne amma kafin nan na miƙe na" "shiga banɗaki kama ruwa wallahi gaskiya nake faɗa maka Yallaɓai""" """To na ƙaryata ka ne? Kenan Isma'il bashi da sani akan waɗanda suka shigo gidan ko? Da ɗauke" "Safiyyerh?"". ""Duk abin da na ce maka na yi ƙarya abu ɗaya na sani fitowar su ɗauke da ita, hannunsu riƙe" "da makamai ɗaya ya ce na buɗe ko ya ɓola mini ciki na ji tsoro haƙiƙa sai na buɗe ashe sun yi parking mota wata ɓaka mai kyau daga can gefe""" "Murmushi kawai Sp Ghali ya yi yana duban ɗaya ma'aikacin ya ce ""Kai kuma fa? Mene information?"" Shi" "wannan jikinsa har ɓari yake don tsoro ya ce ""Yadda na gansu Allah Ya sa naga Annabin Rahama, misalin biyu da arba'in ne ina zaune na ji ana dirowa ta katanga kafin na yi magana ɗaya ya make ni yana nuna yatsarsa a baki alamun na yi shiru, ni kuwa na yi shirun don wallahi a lokacin na ɗauka mai gida shi sojan kenan daman shi ke kai wa dare a waje saboda yanayin aikin nasa, suka ɗaure ni ina hango sanda suka nufi part ɗin tunda can babu masu gadi daga nan ban san mene ya faru ciki ba sai gani mukai sun fito da" "ita a kafaɗa kamar ma a sume take yadda ta langwaɓar da kai""" "Daddy da Captain suka runtse idanunsu lokaci ɗaya, kowanne tunanin da yake daban a ransa, is he a" "loser? Captain ke tambayar kansa or he is falled as a husband maybe da yana kwana ɗaki ɗaya da Safii da hakan bai faru ba, idanunsa ya ƙara sauya kala. Daddy ma nasa tunanin dabanne, ko dai ya yi gaggawa ne ba yanzu ya dace ba? Ko mistake ya yi daya aurawa Aliyu Safiyyernsa ne? Is he a loser? Daya" kasa tsare rayuwar yarinyarsa mace ɗaya tilo a duniya ko dai da gaske he is falled as a father? "Kafin kowa ya yi magana ta shigo cikin gidan a gigice duk da nutsuwar da take da ita, da sauri kuma" Daddy ya miƙe tsaye cike da tsoro da mamaki hatta Captain sai da ya ji wani abu mai kama da faɗuwar "gaba, who told her? Tun kafin ta yi magana daddy ya yi saurin matsawa kusa da ita ganin yadda take ta zare idanu fararen idanunta fuskar nan nata ya ɗakko rana kamar ta yage don fari ""Zahiyerh""" "Girgizawa daddy kai ta yi a daburce ta ce ""Ina Maama?"" Ya yi shiru yana ƙoƙarin riƙe hannunta ta ƙwace" ta yi baya da ƙarfi kuma ta ce """Ina Maama? Ka bani ita na tafi da ita where is Safiyyerh""" """Safiyyerh has been kidnapped""" """Kidnapped?"" Ta maimaita tana juyawa ta kalli Sp Ghali anya ya san wacece ita da yake furta mata" "maganar anyi garkuwa da Safiyyerh kai tsaye bai tauna harshe ko ya lissafa maganar ba, Safiyyerh fa? Sp Ghali zai yi magana daddy ya girgiza masa kai yana sake kallon Zahiyerh wacce zuciyarsa ke buɗewa a duk sanda ya kalle ta. ""Ummimi please ki kwantar da hankali ki samu nutsuwa tafiyar nesa kikai jirgi kika" "hau""" """To na ji, ka faɗa mini meke faruwa da Safiyyerh?"" Daddy ya sauke numfashi a hankali kuma ya nuna Sp" "Ghali ya ce ""As he said, he told you already Safiyyerh has been kidnapped""" """Uhm""" """Komai zai daidaita Ummimi"" ita dai bata sake magana ba can ta ɗaga kai ta kalli Aliyu da sauri ya zame" "idanunsa ƙasa ta harɗe hannayenta a ƙirji ta tsaya jikin hawa steps ɗin bene. ""Afuwa Sp muje ko?""" """Next question ɗin mu akan Captain ne""" """Ok ka yi mana"" in ji Anty Turai." """Aliyu kafa yi haƙuri kalar aikin ku na sojoji daban, namu daban kowa da nasa iyawa da ƙwarewar a nasa" "ɓangaren ok. Aliyu kai ne zaka faɗa mana abin da ya faru a cikin gidan su waye suka sace maka mata har cikin gidanka a matsayinka na soja wanda kodayaushe zaka iya samun ƙarin matsayi na aiki, ya akai haka ta faru? Su waye?""" """Ban sani ba""" "Kai tsaye Captain ya bada amsa ""Baka sani ba? Har kuma suka ji maka ciwo kada ka saka na fara zarginka" "na yi tunanin sace Safiyyerh set up ne kuma ne ka yi plans ɗin hakan, ka sace matarka?""" "Aliyu ya dinga kallon Sp Ghali a hankali kuma ya ce ""E"". ""kana nufin ka sace matarka Safiyyerh?""" """E"" ya sake cewa" """Aliyu!!"" Daddy ya kira Aliyu da ƙarfi ya miƙe ya ce ""Da gaske ka sace Safiyyerh?"" Kamar idanun Captain" "za su faɗo ƙasa saboda yadda suka fito waje sai kawai ya lumshe ido ya buɗe ya ce ""E, na sace ta daddy""" "yana cewa ya fita daga parlon yana banko ƙofar da ƙarfi kamar ya cire ta. ""Innalillahi wa'inna" "ilaihirraji'un!"" Muryar Ummi ta karaɗe parlon ƴan mazan dai sukai shiru." """Karya yake yi"" Ummimi ta ce har yanzu taƙi zama lokaci zuwa lokaci kuma tana duba wayarta kawai sai" tabi bayan Aliyu. Daddy har jiri yake gani baya so a fitar da maganar ya fiso a yi komai secretly har Safiyyerh ta dawo gare su amma sai yaushe ne?. Only God knows. ****Ammo na zaune ta yi shiru a ɗakinta kamar kodayaushe ta yi nisa a tunaninta bata ma san Malam "ya shigo ba sai muryar Inna Binta da ta ji a sama wajan ƙofar ɗakin tana faɗin ""Yanzu don Allah Ammo da rana ma ba za ki daina kwantar miji kina satar kwana ba, wacce irin jaraba da masifa ce haka ni Bintalo jaraba kala-kala Malam ɗin duk da basir ya cinye shi da rana ma ba za a bar mana miji mu dinga ganinsa duk da ba wata tsiyar yake yi mana ba"" Ammo ta cira kai ta kalli Inna Binta ta juya ta kalli gefe har yanzu" ba taga Malam ba cikin rashin fahimta ta ce """Kamarya?""" """Ohho shafa ki ji mace an girma amma sai shegen munafurci da kissa wato kafin ki gama sallama ɗan" naki wa duniya kafin ya gama zama ɗan ta'adda ya miki aikin mallake malam ko? Shi ya sa kaf gidan nan "kin fi kowa yawan yara"" Ammo ta kasa cewa komai da ƙyar ta buɗe baki ta ce" """To ina Malam ɗin yake yaushe ya shigo mini?"" Ta banka mata harara ta nuna mata malam dake zaune" "ya yi shiru a hankali ta furta ""Ikon Allah ki yi haƙuri ban san ya shigo ba"" Malam ya yi gyaran murya ko" "kallon Inna Binta bai yi ba cikin damuwa ya ce ""Ammo ki nutsu ki ji me zan ce miki babu tabbacin abin" "dai har yanzu, ki yi haƙuri idan har hakan ya kasance gaskiya""" Jin haka ya saka Inna Binta neman waje ta zauna a bakin dakalin ɗakin Ammo ita dai wacce ake maganar "domin ta shiru ta yi tana bin Malam da kallo gabanta na faɗuwa ba wai yanzu ta saba da faɗuwar gaba ba, ta ji wannan ta musamman ce. ""Gawa aka tsinta. ,"" ""Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un! Na Ammo?""" "Malam ya ƙura mata idanu bai taɓa zaton tunanin wancan gantalallan yaron mara amfani a duniya zai zo ranta bq, ya girgiza kai kana ya yi shiru caraf Inna Binta ta ce ""Idan shine ai gwara ka faɗa ko kuwa? Kai aka cire masa ko wuƙa ce harsashi ne ko rayata ko babbake shi aka yi kasan haka ake yi wa ƴan daba, wallahi wani da aka rutsa shi ƴan unguwar jahilin duka sukai masa, ashe shima dai irin tsinannen yaron naka ne wuƙa bata huda shi, suka dinga rutsa masa dutse aka ina sai da kan ya ya yi dugu-dugu a nan cikin gari akai abin, da iyayen nasa suka je wajan ƴan sanda cewa sukai su yi haƙuri gawar ba zata ɗakko ba ta yi muni yaron nan dai da yake bashi da rabon rahama ko sallah ba a yi masa ba, yana can za a yi" "gwaje-gwaje da gawar ƴan makaranta daman ƙarshen duk wani ɗan daba kenan""" "Malam ya yi shiru bai yi zaton haka Inna Binta take ba, Ammo rasa kalmar da za ta yi amfani da ita ta yi" "wajan yi wa Inna Binta, ta yi shiru tana sunkuyar da kai." """Malam ka faɗa mata kawai sai ta ɗauki don gana""" """Wallahi tallahi ko""" Mama ta yi caraf ta faɗa ashe itama tana laɓe a jikin taga daga waje. Ya girgiza kai kawai cike da takaici "kana ya ce ""Gawa aka tsinta ta mace an cire mata idanu biyu kuma an cillar da ita bakin hanya, aka kira" "ana tunanin kamar gawar"" haka kawai ya ji yana jin tsoron kalmar da abin da zai biyo baya Ammo ta ƙura" "masa idanu a sanyaye ta ce ""Sa'adah ce ko Bafullatana ko Hameeda?""" """Hameeda""" """Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un! Astagafirulla Allah mun tuba jama'a an cire idanun Hameeda gatan na" "ammo ta shige jama'ar gida Hameeda ta mutu a kawo mana ɗauki"" a gigice Inna Binta ta zari mayafi tana ficewa zuwa maƙota. Mama kuma ta yi shiru idan haka ne ba ƙaramin gigita mutuwar Hameeda ya saka ta ba. Ammo bata ce komai ba a ranta tana nanata kalmar Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un! Ita kawai ta yi mata saura a cikin baki ""Ba a tabbatar bata, saboda haka ki taso muje a gani ƙila ki fini ganewa sosai"" kafin Ammo ta yi magana Baba uwar mijin Anty Hameeda ta shigo tare da mijin idanunta ya yi ja" cikin sauri Mama ta ce """Yaya lafiya dai Baba?""" """Ina lafiya, Hameeda ce daga fita siyo magani da daddare mun neme ta mun rasa kwana biyu kenan" "wallahi"". ""Shikenan ta tabbata an kashe Hameeda"" kafin ka ce me cikin gidan ya cika Inna Binta sai rusa ihu take yi tana sun shiga uku an kashe musu yarinya. Koda aka kawo gawar Hameeda ba kowa ya iya gani ba kamar dodo har ta fara wari an cire kyakkyawan idanun nan nata. Ammo ta dinga tuna nasihar Hameeda ta ƙarshe da ta yi musu,daga nan bata sake dawowa gidan ba wani abu ya tokare wuyan" Ammo ta kasa magana balle kuka sai kallon gawar take cike da sarewa. ****Kamar kullum yau na Goje ya buɗe ƙofar tana durƙushe duk ta fita daga cikin hayyacinta idanunta ya faɗa ba zaka taɓa cewa Safiyyerh bace. Ya dire mata abincin yau dai pure water ɗin hadda sanyin shi """Kar ki sake buga mana ƙofa domin ba wanda zai buɗe miki""" """Ka ɗauke bana ci""" """Dar kin yi kyan kai ƴar kurciya"" ya juya baya ta faki idanunsa ta zare ƙaramar wayar data gani a jikin" aljihunsa ta yi saurin ɓoyewa. Goje kuma ya dawo cikin harabar gidan Moh ya gani zaune yana sake karanta takardar sai ya yi murmushi yana dafa kafaɗar Moh ya ce """Ni dai na fara gajiya da siyo abinci gaskiya"" banza Moh ya yi yana ninke takardar tun daren da aka kawo" "Safiyyerh bai sake ganin kamarta ba sai sautin kukanta da yake ji kullum yanzu ma kukan take tana buga musu ƙofa da ƙarfi a fusace ya miƙe tsaye ya nufi ƙofar ɗakin Goje ya bisa da kallo can ya miƙe ya bi bayansa. Da ƙafa ya daki ƙofar ta buɗe da sauri Safiyyerh ta miƙe cak kukan nata ya tsaya a maƙoshi ta tattare ta haɗiye ta mayar zuwa cikinta, fitsarin dake mintsinin mararta ya saki kansa ya fara zuba a gefen ƙafarta, dukkan wata gaɓa ta jikinta ɓari take yi. Ashe da bata san waye ba, bata san waye ya yi kidnapping nata ba sai yanzu cikakkiyar siffarsa ta bayyana zubi da tsarin da halittar da Ubangiji ya yi masa mai firgitarwa bata san waye mafi muni a cikin ƴan daba amma ta san wannan tantirin ne ko daga tsaiwar da ya yi, cikakken namiji a tsaye majiyin ƙarfi matashi kuma mai jini a jika da cikakkiyar lafiya shine matsayin ɗan daba tsaye a gabanta gefen fuskarsa wani zabcecen yanka wanda akai masa ɗinki har ya zama tabo. Salati take ƙoƙarin yi ta kasa ta gama jiƙa wajan da fitsari ƙiris ne babu numfashinta ya" yi ƙaura daga ƙirjinta ta yi saurin ƙasa da idanunta. """Ka yi haƙuri kar ka mini komai, don Allah ko nan waje ne ku bar ni na fito kalli skin ɗina zai lalace akwai" "ants a nan waje"" ta tattare hannun rigarta tana nuna masa farar fatarta da ta yi wani irin tabo ritsi-ritsi kamar kwanciyar ji fuskarsa ta kumbura ta yi jaa sai susa take yi saboda ƙaiƙayi. Ta langwaɓar da kai ta ce ""Ka gani ko na sake nuna maka har bayana"" ta juya bayan tana ƙoƙarin ɗaga rigar ta ji ya daki ƙofar da" mahaukacin ƙarfi kafin ta juyo ya bar wajan. Ta sauke ajjiyar zuciya feeling reliver ganin ƙofar a buɗe. "Tana fitowa suka haɗa idanu da shi da sauri ta juya kanta na bugewa da jikin bango, anya tana da hankali" da lissafi kuwa? Fitsari fa a wando sai ya tsuke fuska. Suna zaune Mangal ya shigo yana hakki da sauri Goje ya zare wuƙa sama tiger ya yi zumbur ya miƙe tsaye yana gurnani Moh kuma kallon Mangal yake yana jiran ya ji suwaye suka biyo shi don yana da yaƙinin ba wanda ya san gidan da suke. """Kai ɗan wahala mene su waye suka biyo ka?""" """Daga layin su Mai jeji naje an yi rasuwa kuma a gidansu Moh aka anyata lahira wallahi"" duk suka juya" suka kalli Moh shima ɗin kallon nasu yake fuskarsa ba wani sauyi kawai ƙarashen maganar yake jiran ji. """Sai aka ce waye ya baza? Iyayen Moh dai akwai sauran rai wannan dar in sha Allah""" """Wai ko Hamida ko Hamda, idanu aka ƙwaƙule mata ashe tana cikin mutanen da aka sace ta"" Moh" "tunani yake yi ina ma ya san mai sunan Hameeda tasa Hameedan ba zata taɓa mutuwa a irin wannan halin ba, sam ba zata mutu ba duk da yanzu ba ruwansa da ita. Bayan wasu shuɗewar daƙiƙo zumbur ya" "miƙe tsaye kansa na sarawa a dagule ya furta ""Amini?""" Da sauri kuma ya yi wani ɗaki suna shiga suka same shi yana cakawa kasan wata sabuwar allura da Ali "wali ya basu da maye, bayan ya zuƙe ruwan a jikinsa ya ƙara ɗakko wata ya sake cakawa kansa sirinjin ana ukun Goje ya yi saurin matsawa ya ce ""Easy Mutallab,zaka haukata kanka a banza kasan wacce irin" "allura ce ko dan baka jin turanci muma bama ji, haukatar da mutane take yi fa?""" "Sakar masa allurar ya yi ya sake ɗakko wata Goje ya sake riƙe wa ya ce ""Wallahi in dai ina nan ba zaka" "sake yi ba"" ya ƙara sakar masa ya ɗakko fenta zai yi Goje ya ƙara riƙe, Moh ya shammaci Goje ya ɗauke shi ya damfara shi da ƙasa ya saka ƙafa ya take hannunsa hannun ya yi ƙara, ganin yana shirin kashe shi ya sa Mangal ya ɗakko abu ya makawa Moh aka, ya ɗauke ƙafarsa ya juya yana kallon Mangal da sauri" Mangal ya zare Goje ya fito da shi daga ɗakin da gudu suka fice daga cikin gidan. **The following days. Buɗe ƙofa Captain ya yi ya shiga ɗakin a hankali wanda ya yi wa Aliyu mugun sani shi zai lura da ramewar da ya yi. Idanunsa akan Ummimi dake zaune gefen gado hannunta tsakanin cinyoyinta ta sunkuyar da kanta ƙasa ya ƙarasa ya duƙa gabanta ya ɗora hannunsa a cinyarta a hankali kuma ya leƙa kansa ta ƙasa ya kalli fuskarta suka haɗa idanu ta zabga masa harara lallausan murmushi ya yi mata a hankali ya ce """Love""" """Aliyu fita""" "Ya girgiza mata kai ya yi shiru sai lokacin ta yi shiru tana ƙare masa kallo ""Ciwo ka yi ne Gadanga?""" """A'a love""" """Kuma yaushe ka damu da Maama har haka ka dame?""" """Love, Safii is my wife"" ta wani buɗe idanunta na rashin fahimta ""Waye Safii?""" """Safiyyerh, your Maama"" da sauri ta miƙe tsaye tana girgiza kai ""Yaushe aka yi haka? Tunanin waye" "hakan decision ɗin waye wannan professor ko?"" Gani take sauri take yi amma sai ta cire ƙafa ɗaya take mayar da ɗaya ta fice daga ɗakin a parlo taga duka mutanen gidan hadda police da team na musamman da suka fara bincike akan sace Safiyyerh Abdu Marafa. ""Ashe daman baka yarda ba professor za ka iya mini haka? Bana baƙin ciki da auren da ka yi musu amma ina da hakƙi na sanin ka haɗa Safiyyerh da Aliyu aure, Professor burinka ya cika ƙudirinka ya tabbata ka aurawa Safiyyerh Aliyu"" masifa Zahiyerh take yi tai Hausa tai turanci ta koma larabci ba wanda ya tanka ta, kan Abba a ƙasa. Da ƙyar Aliyu ya janye ta a ransa ya gode Allah da bata ce a raba auren ba tsaf zata iya. Ta nemi kujira ta zauna sai nishi" take yi na rashin lafiya. """Zo Aliyu"" ya ƙarasa wajanta ta nuna masa kusa da ita ya zauna, sai kawai ta rufe idanu ta kwanta ta yi" shiru a hankali ya fara danna mata kanta Dr Hash shima ya ɗauki ƙafarta data kumbura ya fara danna mata sai a lokacin Daddy ya buɗe idanu ya kalleta ya girgiza kai fatansa kafin ta farka Safiyyerh ta dawo gida. """Sp har yanzu ba wani kira da muka samu akan batun sace Safiyyerh, ina zargin anya issues na" "kidnapping ne?"". ""Za su kira ai sun sauya salo ina mai tabbatar maka cewa za a kira Safiyyerh zata dawo gida"" daddy ya jinjina kai ya yi shiru." Wayar Aliyu ce ta fara ƙara yana dubawa yaga kamar private number har sai share sai ya yi tunanin ko masu sace Safiyyerh ne? Da sauri ya amsa kiran was the first abin da ya ji daya nemi buɗe masa zuciya "sautin kukan Safiyyerh ƙasa ƙasa ya runtse idanu can ya ji ya ce ""Yaya Please help ants za su cinye mini" "fata Yaya za su kashe ni""" """Safiyyerh listen""" "Karo na farko daya kira sunanta ""Take a heart peanut, ke matar soja zama jaruma"". ""Yaya am scared" "wuƙaƙe"" ya buɗe idanu ya ga duk kallonsa suke yi hadda daddy Sp Ghali ya yi masa alama ya saka speaker. ""Kina ji na?"" Kamar tana gabansa ta ɗaga kai ""Be strong Maama, daddy is here for you, Ummi kowa ma hadda ni am here for you ƴan mata, hadda Ummimi"" da wani irin sauri ta ce ""Ummimi?" "Ummimita Yaya?""" """Sure, ki nutsu wanne waje suka kai ki, za ki iya tuna suna ko wanne abu da zai bamu haske?""" """Yaya sun rufe mini idanu ban san komai ba, don Allah ka taimaka mini daddy help me please"" idanun" daddy ya yi jajur already anyi connecting na wayar an fara bincke da ƙoƙarin tracking daga ina wayar ke zuwa. Shima kuma daga can haɗaɗɗan ɗakinsa da suke zube da kayan na'ura kamar hauka ya saka abu a kunne ya ɗora ƙafa yana girgiza kai a hankali yana jin conversation ɗin Safiyyerh da Aliyu yana yi yana duba time da cije leɓe. Abin da Aliyu bai taɓa yi ba kenan ƙoƙarin jan Safiyyerh da hira da ya ji Ummimi zata motsa zai yi saurin "girgiza ƙafarsa ""In sha Allah i will save you Safii, ki yi ƙoƙarin gane wani abu ki yi addu'a"" tana ƙoƙarin sake magana suka ji ihunta da ƙarar buga wayar da ƙasa ""Safiyyerh kina nan kina kan kayi baby?"" Aliyu ya jere tambayar. Kafin sun an kare daddy ya sulale a wajan babu numfashi." "****Tunda su Goje suka fita yake abu ɗaya kamar wanda za'a zarewa rai, sai buge buge yake yana fasa" "komai na gidan kumfa na fita a bakinsa ihun da ya yi da gurnani shi ya saka Safiyyerh sakin ihu tana yin cilli da wayar a gigice ta miƙe har lokacin kayan bacci ne a jikinta, tana fita ta ganshi a tsakar gidan ya yi tumu-tumu wani irin mahaukacin tausayinsa ya ratsa zuciyarta ta duba babu kowa a gidan sai ta yi tunanin wannan opportunity ne da zata bar gidan hankali kwance, bata damu da kayan jikinta ba sai kawai ta nufi ƙofa da gudu tana ƙoƙarin fita ta ji muryarsa cikin mawuyacin hali kamar ana fisgar ransa abin da ta ji ya saka ta tsaya ta yi jim itama kanta na sarawa tana gani bibbiyu ta sake yunƙurin buɗe ƙofar ta ji ya ce ""Safiyyerh. !"" Ya faɗa da ƙarfi a gigice ta juya taga ita yake kallo yana ƙoƙarin tashi ya" kasa yana miƙo mata hannu... *MUTALLAB IS NOT FREE* We'll soon end the free pages. ka yi payment a yi naka a paid group. MUTALLAB. "Book 1, 2 &3" 500 Naira 0116886423 Union Bank Na'ima Sulaiman S a tura shaidar biya ta nan 08164069385 Ƴan Niger kuma ya gadda tsarin yake. 'Yan Nijar ku turo carte airtel ta 300fcfa saman wannan layin 84506476 "[10/25, 11:14 AM] Nanameera: *This is not a love story,but a love that builds a story, and a love that" destroys the story.* *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥* Page 14 *Bright pens...2nd batch* *Author's books* Munafukin miji Moon Mijin malama Tsintacciya Idan ba ke Sirrinmu E.t.c Follow on Arewabooks Follow on telegram Remain 1 free page Jikinta rawa yake ganin ya kafe ta da idanunsa har lokacin kuma kakkarwa nasa jikin yake yana fesar da numfashi. Ina ya san sunanta? Take tambayar kanta. A hankali Moh ya lumshe idanunsa bayan ya janye su daga gare ta yana ɗan ciccije bakinsa. "Safiyyerh ta kasa fita, idan ta bar shi ya mutu alhalin zata iya taimaka masa Ubangiji zai kamata da laifin" "rashin tausayi da imani, ta salwantar da rai ta hanyar ganganci da son zuciyarta." """Safiyyerh taki rayuwar fa? Kashe ki za su suma fa, ya kamata ki bar wajan nan tunda kin samu dama, shi" "kinga kamar mahaukaci ne maybe"" zuciyarta ta bata shawara cike da gamsuwa ta jinjina kai tare da kama handle ɗin zata fice." Haɗa idanu suka sake sanda ta juyo ya dinga kallon ta rinannun idanunsa sai ta saki hannun ƙofar tana ɗaga ƙafa zata nufe shi. """Run Safiyyerh, run away run Safiyyerh""" Ta sautin muryar zuciyarta a cikin kunnenta ta sauka har tsakiyar kanta ƙirjinta ya dinga ɗagawa tana son tafiya bata kuma san meke janta zuwa gare shi ba. Ta girgiza kai """Save him frist"" ta furta a iya harshenta. Yana ganin ta nufo inda yake ya rufe idanu kafin ta ƙaraso ya" juya baya yadda ba zata ga fuskarsa ba. Jikinta a sanyaye ta durƙusa cike da tsoro ta kasa magana can ta yi ƙarfin halin furta """Ina ke maka ciwo?""" "Ya mata shiru ba bacci yake ba, domin tana hango yadda ƙirjinsa ke ɗagawa sosai yana ƙoƙarin ganin ya" "hana kansa yin abin da ƙwaƙwalwarsa ke umarta shi. ""To faɗa mini inda maganin yake na ɗakko maka""" Jin shirun ya yi yawa ta matsa tana leƙa fuskarsa suka haɗa ido ya zaro mata manyan jajeyen ƙwayar "idanun ta yi saurin ɗauke nata idon ""Tab kalli idanunka fa, ko asibiti zaka je?"" Ta yi maganar tana ƙoƙarin kai hannu zata taɓa shi ya mirgina gefe yana haɗe fuska kamar ya ce ya shiga uku, da zata gane to tabbas ita ɗin ce baya son gani ko jin muryarta ta kura masa hakan" yake yi sosai ya tsuke fuska yana rufe idanu Safiyyerh ta miƙe gabaɗaya hopefully ya buɗe ido ko ya bata "amsa ba sarewa ta sake miƙa hannu dukan da ta ji ya kaiwa jikin bango ne ya saka ta yi baya tana zaman ƴan bori,shima ya tashi zaune yana zazzaro idanu daidai lokacin su Goje suka shigo ya kalli Safiyyerh da" take yarfe hannu saboda bugewar da ta yi ya dubi Moh daya miƙe tsaye yana tangaɗi ya shige ɗaki yana "rufo kansa a ciki. ""Ke me kikai masa?""" """Ƙato da shi me zan masa?""" """Abu a duhu na san matan yanzu ba kunya ce da su ba, idanu rufe suke afkawa maza"" da mamaki" "Safiyyerh take kallon Goje zuciyarta babu daɗi ga takaicin rashin guduwa gana wancan da ko inda take bai kalla ba duk maganar da ta yi masa, ta matsa tana takure jikinta waje guda sai yanzu ma take jin kunyar shigar jikinta sosai, ita Safiyyerh yau ita ce take rayuwa a wajan ƴan daba mashaya kuma ƴan ta'adda hawaye ya cika idanunta sosai mutanen da sam basu suwaye su ba, basu san kansu ba basu da" wani amfani a wajan al'umma. """Ke kina ji ko?""" """Safiyyerh sunana""" """Mene ya daman kuma warning zan miki kar ki kuskure ki sake zuwa wajan shi idan kina son tsira da" "ranki ba, ba kema ko Abdu Marafa bane a nan wallahi zai iya ganin bayansa, ki yi abin da ya shafe ki kawai ki tsaya iya matsayin ki na wacce akai garkuwa da ita kuma ɓarayin gwamnati"". ""Shi wa?""" "Ya nuna mata ƙofa ""kin gane ai""" """A'a"" wuƙa ya zaro yana gwalo idanu waje ya ce ""Idan na cire miki yatsa ɗaya za ki gane ai""" """Ni mu yi magana ta fahimta daku, me kuke buƙata zan baku koma mene amma ku rabu dani don Allah" "ina kyakkyawan fata da muradan da nake son cimma a rayuwa naga ku babu inda kuka saka gaba rayukan ku ma sam baku damu dasu, wallahi ina buƙatar rayuwa mai tsayi da zan bar baya mai kyau ba zaku ɓata mini rayuwata ba, kuma warin sigarin nan juya mini kai yake da ƙyar nake shaƙar numfashi, ni macace mai hankali da ilimi wacce iyayena suka bawa tarbiyya daidai gwargwado in da ilimin addini" "saɓanin ku da ba lallai ko ummul kitahhb kun iya ba, ƴan daba ne ko masu laifi rayuwarku a gurɓace take" "ba a yi muku tarbiyya ba"" hatta Moh dake cikin ɗaki idanunsa a sama yana kallon rufin kwano sai da ya" "waro ido yana sauraren maganganun da take cewa, Mangal ya yi mata ƙuri da nasa idanun haka Goje" """Wuyanki ya isa yanka ba laifinki bane za mu yi maganinki""" """To me na ce na ba daidai ba, don Allah ku ba ƴan daba bane ƴan ta'adda kuma ga tantirin can shine" "shugaban naku da alama asalin daƙiƙi ne ajin ƙarshe sai wari dauɗa dana rana ga na shaye-shaye wallahi...,"" saurin haɗiye maganar ta yi ganin shi tsaye a kanta yana huci ta miƙe tsaye hannu ya ɗaga kamar zai kwaɗa mata mari ta kurma ihu tana ƙanƙame jikinta ""Don Allah ka yi haƙuri ƙarya nake yi wayyo daddy wayyo captain"" sai idanunsa suka sake jirkicewa ta buɗe idanu taga ya zuba mata nasa idanun fuskarsa dab da nata sai juya ƙwayar idonsa yake a saman fuskarta kamar mai son tantancewa" wani abu. "Ta tura baki cike da tsiwa ta ce ""Kana kwaɗa mini mari zan rama tunaninka rabuwa zan yi dakai ka ci" "bulus? Bayan an ce duk wani ɗan shaye-shaye bashi da wani ƙarfi hayaƙi ya cinye shi"" Goje ya ce" """Wannan yarinyar ƴar wasa ce bayan kuɗi data iya sarrafawa har rashin kunya ta iya Allah kar ka rabu da" "ita"" Shi dai Moh na tsaye yana kallon ta ita kuma ta kasa jure ganin ƙwayar idanunsa ta yi ƙasa da kanta tana murguɗa masa baki, bata ankara ba ta ji ya cilla mata baƙar kunawa cikin riga ta zumduma ihu a gigice ta yi kansa zata riƙe shi ya yi saurin baya yana ficewa daga gidan Goje yana ta dariya da buga ƙafa" """Kinga aikin Mai jeji gana Scorpion nan""" ****Eng Ali wali yana zaune a gidan wutawarsa yana zantawa da wasu manyan mutane masu taimaka "masa a harkar kamfel ya dubi P.a ya ce ""P.A ina tunanin iya abin da ake buƙata kenan kuma na bada, ka" "sani ba kuɗi yanzu a ƙasa kamfen ya cinye komai, you can manage ko?""" """Ba damuwa amma muna da raguwar list na local government wajan biyar da bamu je ba yanzu haka, ga" "ƴan media sun matsa kasan mutane babu amana gwara a fara watsa musu hatsi tun yanzu fa a yi maganin yunwar data addaba musu"" Ali wali ya yi murmushi yana juya kai kafin ya ce ""Ku je za mu yi" "magana zuwa dare ina da hira da ƴan zuwa dare we'll talk"" P.A ya kalli mutanen ya ce" """Don't make any mistakes idan kun shiga gidan rediyon ku tabbatar kun yi abin da ya dace, kar kuma ku" "nuna wata alaƙa tsakaninmu da ku yadda na faɗa muku haka zaku faɗa"" ""In sha Allah, ai harma da abin" "da baku buƙata ba mu indai za a biya mu ai buƙatar maje hajji sallah zamu farfaɗi ayyukan bogi da ya yi kuma ya yi mana""" """Nice to hear this, you can leave ku je""" Tafiya suka yi suna murnar ƴar dubu biyar biyar ɗin da za a basu akan faɗar abin da ba haka bane. Ali "wali na shirin miƙewa ya ji numfashi a bayansa ya juya da sauri, tsaye ya ga Moh fuskarsa rufe sai ƙwayar" "idanunsa da take a fili ya cake yana muzurai. ""ka bani tsoro amma""" """Mara gaskiya ko a ruwa zufa yake""" """Me na yi na rashin gaskiya?"" Ya yi masa shiru yana wani irin fito ya ɗauki ƙafarsa ɗaya ya ɗora saman" "kujera yana zaro kunama ya ajjiye saman kujerar wajan ta fara yawo tana ɗaga ƙari sama ta kumbura sosai. ""Yaushe ka shigo? Na ce ni zan dinga nemanka bawai ka dinga biyo ni duk inda nake ba, bana so a san ina mu'amala da kai""" """Saboda annoba ne ni? Tunda ka jawo ni haka zaka shanye duk abin da na dama, na kwalo yarinyar" "mene next?"" Murmushi Ali wali ya yi ya ce ""Ai na san kun ɗakko ta, tunda CSP ya yi mini magana akan case ɗin kidnaping sannu namijin duniya""" """Zan kawo ta nan""" """Ina? A'a ka bar ta nan wajanku zan baka key ɗin wani gida sai ku tafi can kwafi sararawa ni bani da" "gaske koda zaka dinga huta gajiyarka a wajanta kana rage zafi"" Moh ya ɗaga kai ya kalli Ali wali da kyau." """Wacce gajiyar, sanyi ne a jikinta?""" """Kana abu kamar ba wayayye ba, mu bar maganar ka yi mini aiki na farko and i appreciate it. Sai batun" "Scorpion"" daidai nan kunamar dake yawo a wajan ta shige hannun Moh ya matse ta ya yar waje guda Ali wali ya cigaba da cewa ""Scorpion ba zai bar mu ba, Hon Maɗatai yake hari a yanzu nasan kuma bayan nan ni ne a list, yana neman zame mana masifa yana kawo mana barazana a akan siyasarmu gwara Hon Maɗatai ya samu dukkan abin da yake nema a mulki ya samu nasa rabon ni yaushe na fara? I will never" "let that happen ba zan bari ya yi galaba akai na ba""" """Me za ka yi?""" """Zan tabbatar an nemo shi an ɓatar da shi, don ba haka kawai yake yin abin da yake ba akwai abin da ya" "taka yake taƙama da gadara dashi, ka yi ƙoƙarin nemo mini shi kafin hukumar FID su kama shi zan" "ruɓanya maka abin da duk na yi niyya""" """To kuna da case da shi?"" Ali wali yace ""Pardon? Kamarya kenan""" """Basar""" "Key ɗin gidan ya basa, hadda na mota Moh yaƙi amsa wai he don't know how to drive ya basa kuɗin" abincin Fiyya mai kyau da duk abin da take so. """Kaƙi faɗa mini waye kai dai ban san komai dangane da kai ba Moh, sunanka kawai na sani Mutallab" "without surname and middle name, whatever shikenan dai"" Moh ya ƙara ɗaga ƙafa zai fita Eng Ali wali" yace """One more think Mutallab""" """Ali wali ka kira ni da ɗan daba ko ɗan ta'adda sai mu yi magana"" Ali wali ya yi murmushi ya ce ""Sai" "godiya"" ya tsuke fuska Moh." """Professor Abdu Marafa ya mini mummunan tabo a zuciyar matasan jihar nan,ya ɓata mini suna na ji ina" "son ɗanɗana masa kwatankwacin abin da ya yi mini ta hanyar ramuwar gayya wacce ake cewa tafi ta gayya daɗi, kamar yadda ya ɓata ni shima haka nake so a ɓata tarihin tarbiyyar gidansa da sunan da yake taƙama da shi, a dinga masa kallo a matsayin wanda ya gaza"" Ya yi shiru yana sauke numfashi yana duba" wayarsa ganin shugaban jam'iyya na kiran shi ya miƙe tsaye. """Bayan sato budurwar ƴarsa da kuka yi har gida, ina son ka yi Safiyyerh Abdu Marafa fyaɗe, ina son ka yi" "wa Safiyyerh Abdu Marafa ciki kaga tana da auren wani, wani kuma daban ya yi mata ciki wanin ma ɗan daba, ɗan daban da basu san waye shi ba, kaga Safiyyerh zata haifi ɗan zina ko""" """Ɗan zina?""" "Moh ya maimaita a fili Ali wali ya ce ""To ɗan mene? Yayinda da wani wanda ba mijin yarinyar ba ya keɓe" "da yarinya har ta samu ciki wannan cikin ya sunan shi? Cikin shege ba haka lissafin yake, idan na ce wani" "zan bawa wani aikin lissafin Eng Ali wali bai gama cika ɗari over ɗari ba, dole kai zaka aikata haka Mutallab dole kai zaka yi wa Safiyyerh ciki domin dauɗar gora ciki kan shata""" """Wanne zunubi ita yarinyar ta aikata, gyatuminta ne kamar batun nan ba zan ba, shi kuma daman cikin" "yinsa ake yi? Ba kawai girma yake ba?"" ""Au baka san yin ciki ake ba? Shekarar nawa?""" """Koma mene ba za a yi ba"" Ali wali ya yi murmushi ya ce ""Dole zaka yi, ka rubuta kuma ka ajjiye sanda za" "ka yi baka sani ba jeka"" bai wani ɗauki maganar Eng Ali wali da muhimmanci ba ya fice daga gidan." "***Safiyyerh ta rufo ƙofar bayan ta gama dubawa ta kalli Goje ta ce ""Kawai ku siyo mini kayan abincin na" "dinga dafawa sai ina san muku?""" """Kin iya wato ne?""" """Mene wato?"" Ya ce ""Shi girkin nake batu"" ta jinjina masa kai ya miƙe tsaye ya ce ""Da kin yi dabara" daman ba ki da wani amfani. Ita mamaki ta yi ganin kitchen hadda tukunya plates da spoons ga risho da sauran tarkace. Babu jimawa Goje ya dawo hannunsa riƙe da Indomie guda biyar da ƙwai guda goma hadda kayan miya da magi ya bata ya ce """Ta yi musulmin daɗi kin ji Manager""" Ta samu kanta da yin murmushi a ranta kuwa dabara take yi ta samu hanyar guduwa. Suna tsaye ya faɗo "cikin gidan sai ya yi turus yana kallon Goje yaƙi yadda ya kalle ta, ta ƙasan idanu ita kuma take binsa da" "idanu mamakin yadda jikinsa yake a murɗe take har ƙasan zuciyarta ta ji tana shakkarsa. ""Barka da antayowa mai jeji ya ƙarin haƙuri"" banza ya yi masa ya shige ciki Safiyyerh ta ce" """Au rashi ma aka yi masa?""" """Yayarsa aka sace sai jiya aka kanta an ƙwaƙwale mata idanu"" Safiyyerh ta zare idanu tana dafe ƙirji sai" "tausayinsa ya kamata a raunace ta ce ""Kuma bai je gida ba? Anya yana son yayar tasa kuma kun tabbatar wannan ba mahaukaci bane?"" Shi dai tuni Goje ya bar wajan. Ta gama dafa Indomie wacce ta ji azabar Attahiru rabon da ta shiga kitchen a rayuwa ta manta fuskarta ta yi jajir da wani irin roɗi-roɗi idanun" sukai micin-micin ta dinga mata ƙaiƙayi fuskar saboda zafin wuta ta nemi kaɗan ta juye musu a faranti. Moh yana kallon yadda ruga lauma kamar mayunwata sai jan yaji suke yi ya kalli Indomien ya kalle su "can ya miƙe ta ce ""Kai baza ka ci ba? Ni ina son yin sallah fa"" duk suka share ta, suna gama ci suka fice tare da rufo ƙofar ya rage sai ita kaɗai ta haɗe kai da qwwia ta dinga kuka kamar ranta zai fita har bacci ya ɗauke ta a wajan." Cikin bacci ta ji an cillo mata abu ta miƙe da buɗe idanu tsaye ta ganshi ya juya baya leda ce ya cillo ta buɗe taga duguwar riga guda biyu da hijabi da takalmi ta yi ta mamakin yadda ya san size ɗinta ta miƙe tsaye yana jin zata zo wajansa ya nufi hanyar fita ta sha gabansa ya yi turus ta dinga kallonsa shima yana kallonta """Wai kai baka yin magana ne, ko ƴar dariya babu kafin na tafi mu ƙulla mu zama abokai"" ta miƙo masa" "hannu ya kalli hannunta mai ɗauke da siririn zobe sai yatsunta zara zara da su ""Am Safiyyerh Abdu Marafa You?"" Ya sake yin shiru ta langwaɓar da kanta gefe guda ta ce ""Ina son zama ƙawarka fa, zan maka labarin daddyna da yadda yake so na, da labarin kamfanin da nake aiki hadda labarin Ashraf wanda zan aura ya mutu aka aura mini captain labarin Ummimi da Kinal ƙawata i will tell you everything," "abota Frist?"" Ta sake miƙa masa hannun a karo na uku. Gefenta ya bi ya shige yana rufe ƙofar gidan ya" bar ta tsaye da hannu a ƙaƙe takaici ya ishe ta shi wannan yana ɗan ta'adda yana jin kansa kamar ɗan gidan ƙaruna saboda faɗin rai ga miskilancin masifa the manager ita Safiyyerh take magana ake sharewa bai san cewa akan dole take yin maganar ba? Ta lumshe idanunta hawaye na cika cikinsu da ƙyar ta yi alwala ta fara jero salloli. Goje ne ya shigo da sauri ya ce """Ke kina ina fito maza taso"" ta miƙe za ta yi masa gaddama kawar Moh ya shigo ya damƙi hannunta ta" kalli baƙin hannunsa da ɗan mitsitsin nata farin hannun ya jata sukai waje mota ta gani bai tsaya jiran komai ba ya dannata a gaba Goje ya shiga baya Mangal dake tsaye ya ce """Waye zai ja motar yanzu? Ni ban iya ba kuma haka?""" Moh dake shirin shiga mazaunin driver ko me ya tuna ya kalli Safiyyerh a karo na farko ta ji muryarsa a "sake ya ce ""Dawo nan"" tsoran shi take ji ta fito ta koma wajan driver ya dawo ita ta tashi, ya cilla mata" "key ɗin motar ""Muje"" bisimillah ta yi ta fara driving ta juya ta kalle shi ta ce ""Ina?"" Ya bata wayar hannunsa wacce yanzu ya shigo da ita ta duba location da ya fara driving cikin sauri har suka bar wajan." Mintuna kaɗan da barin su motoci suka tsaya a ƙofar gidan Captain ya fito jikinsa danye da uniform na "sojoji da suka amshe shi sosai ga ƙatuwar bindiga sauran yaransa suka fito a hankali ya dinga bin wajan da kallo har ya shiga cikin gidan abin da ya fara cin karo da shi ya sanya zuciyarsa bugawa ganin rigar baccin Fiyya yashe a ƙasa ya ɗuka ya ɗauki rigar idanunsa ya sauka akan wani busasshen jini ya dinga kallon gidan a nan ya kalli ƙwayoyi kala-kala da wuƙaƙe da gorori ya lumshe idanunsa ""Where are you" "Wife? Ina suka kai mini mata?""" """Captain kuma ka tabbatar tracking ɗin nan ya nuna?"" Ya jinjina kai don baya jin zai iya magana. ""Sun" "gudu, amma ya akai sukai san an yi tracking location nasu har suka gudu da wuri haka?""" "Captain ya girgiza kai irin bai sani ba ""Ka kwantar da hankalinka matarka zata kuɓuta ko kana tunanin" "sun yi mata wani abu ne?"" Captain ya nuna masa rigar baccin Safiyyerh da jinin dake wajan mutumin ya dafe kai ya ce" """Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, in sha Allah ba abin da muke zato bane muje"" fita sukai Captain ya ji a" ransa ba zai bar abin haka nan ba. Mutallab wani gida ya kai su madaidaici mai kyau da tsari da yake can bayan gari duk suna zaune "Safiyyerh kanta na ƙasa tana mamakin yawan shiriun bawan Allan nan, idan ya yi shiru shi kaɗai sai ya" saki ajjiyar zuciya ko ya ƙurawa waje guda ido. ***Wajan sati guda babu labari akan batun sace Safiyyerh ba kiran waya babu komai Daddy ya hana a faɗi maganar ko a social media ko a gidan rediyo ya ce a bar ta tsakaninsu. Yana ƙwace hannunsa maƙale "da ruwa muryarsa a hankali ya ce ""Aliyu waye ya saka?""" """She is my wife daddy""" """And? Ɗan sanda ne kai ko soja?""" """Zan iya amfani da uniform ɗina ko babu haka ai she is my responsibilities yanzu na kula da haƙƙina zan" "ji na zama lusari idan ban nemo Safii ba, kar ka dakatar dani daddy police su yi nasu aikin ni na yi nawa""" """Ka cire hannunka a ciki Aliyu""" """Ok zan jire akan wanne dalili?""" """Aliyu yanzu baka tunanin dalilin hakan su yi mata wani abu ne? Baka san su waye mutanen nan ba, duk" "abin da zaka ji a bayan nawa dana Zahiyerh yake kar ka yi kuskuren da za su salwantar da rayuwar Maama na roƙe ka, mutanen ba mutunci ne da su ba kamar komai hannun Sp Ghali"" Aliyu ya miƙe ya nufi ƙofa ""I am sorry daddy idan kaga na tsaya to na mutu ne, idan da numfashi a ƙirjina ba zan gusa ba" "sai na dawo da Safiyyerh cikin rayuwata i am sorry"" yana cewa haka ya bar ɗakin." "Daddy ya rufe idanunsa daya cika da ƙwalla ya wani irin ramewa ko abinci baya ci Ummi ta ce ""Ka san" "halin Aliyu da baka fito masa ta haka ba, gwara ka saka Ummimi yi masa magana"" daddy yaƙi cewa komai. Wayarsa ta fara ƙara number ya gani sai ya yi sauri ya ɗaga yana kaiwa kunne aka ce." """Barka, ina magana da Professor Abdu Marafa na sani ko baka amsa, zan fara da yi maka ya jiki don ina" "da yaƙinin kana nan zuciyarka na ciwo bari na ɗora maka da wata maganar ban sani ba ko zaka iya jure jin abin da zan faɗa. Yarinyar da kake ji da ita ni na saka a sato mini ita Safiyyerh kenan ina son ka lashe aman da ka yi da kanka. Professor ni ɗan siyasa ne lissafin ɗan siyasa daban yake dana Malami, bana barin kota kwana daman mun saba saka jama'a a uku, wallahi ka shiga komata yanzu nine da wasan ka" "fara lissafa ranakun mutuwar yarinyarka daga yanzu"" da sauri Daddy ya ce" """Waye kai?""" """Sarai ka ɗauki ne muryarta professor, kana magana da Eng Ali wali mai neman takarar ɗan majalisa, ka" "hanani bacci yanzu lokaci ne da zaka ji abin da nake ji"". ""Ali wali me kake buƙata me Safiyyerh ta yi maka" "karka cutar mini da yarinyar don girman Allah kar ka taɓa ta""" """E, ba zan taɓa ta ba muddin ka yi abin da nake so""" """Me kake so?""" """Ka dawo jam'iyyata kuma tsagina ka lashe aman da ka yi ka kuma gyara ɓarnar da ka mini na rusa mini" "dukkan shirina, yadda ka ɓata sunana a wajan matasa da al'umma a gidan rediyo da kai da ɗan jaridar da" "yake mara maka baya ku sake sabon lale wajan wanke ni inma kana buƙatar kuɗi zan bayar hakan ba laifi bane ba""" """Uhm Ali wali kenan tun yanzu har ya yi sauri haka? Ni kake cewa idan ina buƙatar kuɗi kaga na yi maka" "kala da mabuƙaci? Kamar dai ka manta waye Professor kana buƙatar tuni na, laaa la la dama sauran lokaci ai. And da kake batun Safiyyerh tunaninka ita ce raunina ko?"" Daddy ya tsige ruwan hannunsa da ake ƙara masa ya sakko daga saman gadonsa daman tuni ya nunawa Ummi ƙofar fita tun kafin ma ya" ɗaga kiran. """Ka yi kuskure sosai, Safiyyerh is nothing to me kuma she never be my headache idan ka so ka saka wuƙa" "ka yankata a yanzu is doesn't matter for me, idan akan Safiyyerh ka kira ka mini warning ka makara Ali wali tunda Safiyyerh ta bar gidan nan ko da dai da rana ban taɓa tunaninta ba siyasa ce kai kuma yaro ne" "mu zuba mu gani""" "A ɓangaren Ali wali dariya shima ya yi ya ce ""Lallai prof ka cika ɗan siyasa, to wallahi ka shirya ganin" "gawar Safiyyerh a wannan daren ku tara ƴan jana'izarta"". ""Idan ka haifo kuma kai cikakken ɗan iska ne idan har ba zina akai ka haifeka ba na roƙeƙa Ali wali don Allah ka kashe Safiyyerh nima fa wani aikin ka rage mini..,"" ƙit Ali wali ya kashe wayar daddy ya saki dariya yana wani irin murmushi wata number ya kira ana ɗagawa ya shige toilet yana saka key, ya jima ciki kafin ya fito ya zauna saman gado Dr Hash ya shigo da Yaya J ganin daddy zaune ya saka dr cewa ""Daddy ya jikin naka?"" Hawaye ya cika idanun daddy ya ce ""ba abin da zai tafi daidai babu Safiyyerh zuciyata zafi take my innocent Fiyya, Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un ina tsoran halin da Ummimi zata shiga"" ganin hawaye a idon mahaifin nasu ya saka Junaid" ficewa dr ya zauna ya dinga lallaɓa daddy da bashi bakin za a ga Safiyyerh in sha Allah. Aliyu yana zaune a ɗakinsa aka buɗe ƙofa tare da shigowa ya ɗaga kai ya kalleta ya miƙe da sauri duk da "babu fara'a a fuskarsa amma sai da ya saki ajjiyar zuciya. Ta juya idanunta ""Nan ka ɓoye?"" Ya girgiza mata kai" """Ka cigaba da binciken inda Safiyyerh take Aliyu kar ka saurari mahaifinka ka ji ko?"" ""in sha Allah" "Ummimi"" ta zuba masa ido sai ta juya ya ce ""Tafiya za ki yi?""" """Me zan maka?""" """Love, ganin ki nake son yi"" ta haɗe rai tana cewa ""To ɗakko zani na goyaka"" ya buɗe idanunsa ya yi" "wajanta yana rungume ta ya saki ajjiyar zuciya ""I love you Ummimi, and I love Safii too""" "Kan shi ta shafa ta ce ""Kawai ka zaɓa ni ko ita"" ya lumshe idanunsa ya yi mata shiru, rungume shi ta yi a" "jikinta ta yi shiru tunani daban daban a ranta sai kuma ta sake shi ta ce ""Fito waje"" saƙo Aliyu ya samu cikin gaggawa sunansa ya fito a jerin sojojin da za a yi posting nasu wajan aiki ya dinga kallon saƙon yaushe ma ya dawo da za a sake tura shi wani wajan bayan babu shi a sojojin da aka yi list? Sai kawai ya fita da nufin zuwa kiran da ya samu domin bata uzurin yana da wani muhimmin aiki akan nasa iyalin ya" manta da batun a tsarin aikin sojoji babu sauyi idan har a zaɓe ka. ****Mafarki ta yi mai ban tsoro ta farka a gigice tana kiran sunan TAHHB sai haki take yi fitila taga an "kunna an hasko ta ya zuba mata idanu a ransa yana ƙara mamakin wannan hasken nata gefensa zabtareriyar addace saboda tsaro ya miƙe a hankali ya kunna hasken parlon sai a lokacin Fiyya ta lura da Goje dake cikin kwance cikin jini haka Mangal ga wuƙaƙe a gefen su sai numfarfashi suke yi. Ya taka ya je gabanta ya tsaya can ya duƙa dab da ita baki ta buɗe za ta yi ihu ya saka yatsarsa a bakinsa ""Shhhh"" ta yi" tsit ya cake addar """Mene?""" """Ban kira ka ba wallahi"" ya zuba mata idanunsa masu kaifi ta janye nata ""sunan wa kika kira to?""" """Tahhb""" """Sunanki ne? Ko na Abdu Marafa?"" Ta girgiza kai ""Mafarki na yi a mafarkin na ji sunan, amma ban sani" "ba ni na manta komai na mafarkin ma kai na ciwo yake i have a headache""" "Ya ɗaga addar ya cake ta tsakanin ƙafafuwanta sai sheƙi take yi ya ce ""Ko dai ki faɗa mini waye Tahhb ɗin" "da kika dame ni da kiran sunansa yanzu ki na ɓula miki cinya""" """Don Allah ka yi haƙuri wallahi ban san shi ba""" """Ke wace?"" Moh ya tambaya ""Safiyyerh sunana"" ya cije bakinsa sosai ya ce ""Matar soja ko?"" Ta jinjina" masa kai """To ni waye? Kuma ya nake a wajanki?""" """Wallahi ban san ka ba, kai ba kuwa bane a wajane"" idanunsa har ruwa yake ya daka mata tsawa a gigice" "ya ce ""Waye ni? Waye ni waye tell me...." "❤🔥🔥💃1 page remain ba zan taɓa buɗe komai ba shafi 15 is nothing nothing ku biya you'll never regret sai mun yi nutsu za ku fahimci labarin MUTALLAB bai haɗa hanya da kowanne kalar labari ba, idan za ka yi kuka ka fara tun yanzu ba kuma zan taɓa sauya labarina a yadda nake ba, you better shut" up... MUTALLAB. "Book 1, 2 &3" 500 Naira 0116886423 Union Bank Na'ima Sulaiman S a tura shaidar biya ta nan 08164069385 'Yan Nijar ku turo carte airtel ta 300fcfa saman wannan layin 84506476 "[10/27, 4:07 PM] Nanameera: *The story of a thug husband MUTALLAB, as a good parents za ku bada" "auren yarinyarki ga ɗan daba ɗan ta'adda? Ban ce ku fara kuka tun yanzu ba,ban ce ku ji soyayyar ciki" kamar a ƙirjinku ake wanzar da ita ba.* *The story of TIGER and MOH The destiny of CAPTAIN and FIYYA. Finally the eternal love* *between..The love that separate them and back them together❤🔥😭* *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥* Page 15 last free episode *Bright pens.. 2nd batch* For more updates follow Mutallab on Arewabooks in sha Allah ❤🔥 "Page 15 shine last free pages na labarin, kar ka yi tunanin ganin wani page ɗin a waje ka yi payment a yi" "naka into paid group akan 500 kacal, love ɗin da kuke showing yanzu ne zai yi aiki฀MUTALLAB." "Book 1, 2 &3" 500 Naira 0116886423 Union Bank Na'ima Sulaiman S a tura shaidar biya ta nan 08164069385 'Yan Nijar tsarin biyan zai kasance ta *Stock na airtel*. Ku yi wa wannan layin 84506476 magana sai ta ba ku lambar da za ku turo mata stock ɗin. Kafin ɗorawa da inda muka tsaya zamu ɗauki hutun zango na sati ɗaya tal maybe har a yi albashi ko masu mining ta fashe musu. Godiya ga Hajja Aisha Abubakar Khadhfsum data biyawa mutane 8 ga masu business zaku iya badawa a tallata muku idan kun ɗauki nauyin page in sha Allah. Ba zan manta da BESTIE ba I so much love her wish you all the best Aunty Nazeefah Sabo Nashe ta ce HADARIN GABAS yana hanya. Ina son ta sosai Gaisuwa ga haƙarƙarina uwar gidan Viper tunda mun amince Nabila ce amarya Ayushercool masoyiya. My beb Zee kumurya sai tallafe ƙirji muke muna sata a addu'a gashi zata fara yi mana ZAYTOON a watan Nuwamba i love them sosai "Conversation bana ce kuci kanku ba, saboda ina ƙaunarku Sarautar's library Mutallab fans, Nimcy paid" group my ArewaBooks people. Mikiya writers Association Mikiya fans AUTAR MANYA❤🔥 Ubangiji Ya bar ƙauna. Page 15 Last free pages "*What if I tell you, I love you?*" """kar ki ce ba ki sanni ba, kar ki ce haka dole ma tarihin rayuwarki ba zai taɓa cika ba sai da sunana, dole a" "same ni a cikin rayuwarki sai dai idan za ki cire wani sashi na cikin tarihin"" ya furta yana huci da gwame numfashi Safiyyerh was shocked and speechless at the same time ta kasa kallon shi wani irin tsoro shi" take ji mai girma ya ratsa zuciyarta. A hankali ta ɗago kanta zuwa gare shi hawaye na taruwa cikinsu yana sauka akan fuskarta "Ta ƙura masa ido da sauri kuma ta girgiza kai ta ce ""Wallahi da gaske ban san ka ba, ban taɓa ganin ka ba" "sai kwanakin nan, i don't even know your name balle kai,me ya sa zan sanka to?"" za ta sakar masa kuka ya ɗora yatsarsa a baki ya ce" """Shhhh"" ba shiri ta yi shiru tana sauke ajjiyar zuciya shi dai har lokacin fuskarta yake kallo yana murza" "tsinin wuƙar a ƙasa. ""To kai ka sanni ne? Ni ka cire mini wuƙar nan ka ji ɗan baƙi"" ta furta tana juya idanu" ta langwaɓar da kanta gefe guda. """Ki daina kiran sunana daga yau""" """Sai na dinga ce maka me to? Ka faɗa mini ban ma san sunan ba ai"" ƙoƙarin biye mata yake wajan ganin" ya samu abin da yake buƙata amma a duk kalma ɗaya daya furta ko kafin ya furta sai ya fama hautsina kan shi kafin ya san me zai furta mata. Wuƙar ya ɗauke ya cilar gefe guda ya juya ya kalli Goje jira ya ke yi safiya ta yi ya fara tunanin yadda zai samu likita ya ji ta ce """Kai ne ka yanke su ko? Ba kyau wallahi ka mutu a haka wuta zaka tafi babu fashi kana kallo za mu shige" "aljanna muna jiyo ihunka a cikin lazza ko saƙara tunda baka da wani aiki a rayuwarka sai daba da bushe- bushe cikinka ba komai sai ƙwaya da hayaƙi, gabaɗaya gudanawa kake daka zaɓi wannan rayuwar ne ɗan baƙi? Bayan rayuwa akwai mutuwa fa karka bari ka mutu cikin wannan halin ba zaka ji da kyau" "wajan Mala'iku ba""" """Kina da ɗan'uwa mala'ika ne?""" """Subuhanallahi, kai ko wa'azin baka so kamar jinin fir'auna ni tausayinka kawai nake ji tunda baka gani" "shikenan"" ta haɗe fuska irin ta ji haushin nan har ƙasan zuciyarta ita ƙyamar shi take yi rayuwarsa a gurɓace take babu wani abu na birgewa ko ban sha'awa a ciki deep down kuma tausayin rayuwar tasu take ji tana jin da tana da iko tabbas ba zata taɓa gazawa ba wajan ganin ta taimaka musu. Ya rufe idanunsa yana daga zaunen saman kujera ya ɗauki ƙafa ɗaya ya ɗora akan ɗaya ya fara yin fito wanda ya" cika ɗakin a hankali kuma ya zaro sigari zai kunna ta yi saurin cewa. """Matsalar daƙiƙi kenan a rayuwa, shi da kansa bature ya ce tana lalata lafiya dake babu arabi ba boko" "ba'a gane komai ai shikenan, goodness Safiyyerh what exactly wrong with you, that's not your business"" ta faɗa lokaci guda kuma tana miƙewa tsaye sai dai bata kai ga zuwa inda ta yi niyya ba ta gan shi tsaye a gabanta hannunsa riƙe da sigarin yana zuƙa da fesarwa, ta saka zata rufe hancinta ya sa hannu ya tukare jikin bango ya sata a tsakiya sigarin a bakinsa yana binta da jajayen idanu bakinta na rawa ta girgiza kai" "ta ce ""Mene haka wai?"" Ya yi shiru yana duƙawa fuskarsa dab da nata har lokacin ita ɗin da yake kallo" """Iskanci ne wannan matar aure ce ni fa, saboda ƙwaƙwalwarka bata faɗa maka daidai ko? Idan ka sato ni" "a gidan mijina shine yake nufin me? Zan barka ka yi yadda ka so ko ƙazamin jikinka ya taɓa fatar Safiyyerh ba zan taɓa yafewa kai na ba, da babbar murya ina faɗa maka ni Safiyyerh matar aure ce ka ji ko? Kana jin Hausa ai?""" "Ya zare sigari hayaƙin daya zuƙa ta cikin bakinsa ya dinga fesa mata a fuska ta fara tari tana ɗauke kai, ya" "ƙara zuƙar sigarin a baki ya matsa dab da fuskar tata ya sake fesa mata lokacin ta buɗe baki za ta yi magana gabaɗaya ta haɗiye hayaƙin, a gigice ta fara tari tare da kakarin amai ganin da gaske aman za ta yi,ya matsa a wajan tare da shigewa wani ɗakin. Safiyyerh ta durƙusa tana riƙe ciki saboda wani irin ciwo da yake yi mata ga amai dake ƙara hautsina mata kayan ciki ta rasa yadda za ta yi ta kwanta tana riƙe cikin da dinga rusa kuka. Duk abin da ya fara Goje na jinsu kawai yana cikin wani hali ne tsautsayi ya saka su fita a daren sukai karo da ƴan daban cikin gari sun shigo ɗaukar fansar wani faɗa da aka yi can kwanaki shine suka rufar musu, a cikin ƴan daban cikin garin wanda yake jagorantar su me suna Bakin wuta shine ya sare su shi kuma Moh sai da ya sari wajan mutum goma a yaran Bakin wuta wanda kuma shine faɗan su na farko a rayuwa ba wanda ya san wani, a cikin yaran ba sai da aka buɗewa wani ciki" kuma duka aikin Moh ne yana da tabbacin kuma Bakin wuta ba zai bari haka nan a ci bulus akan shi ba. Goje ya juya kaɗan ya kalli Safiyyerh dake kuka sosai kamar ranta zai fita itama yarinyar naci gare ta ga "bakin tsiwa da Moh na taɓa mace da tuni Safiyyerh bata duniya ya san ba zai iya kashe ta ba amma zuwa gaba zata gane bata da wayo idan ta cigaba da kai shi bango. Tana kukan a haka bacci ya ɗauke ta bata ji kiran sallah ba amma tunda ta motsa bakinta ɗauke da addu'a ta san asuba ta yi ta miƙe da ƙyar ta nufi banɗaki ta yi alwala ta jima tana azkar kafin ta yi raka'atul fijr kana ta yi sallar asuba. A hankali ta dinga leƙa shi abin da ya bata mamaki bai shige ganinsa durƙushe a kan qwiwinsa ba yana kallon gabas ba kuma sallah ya yi ba, kan shi a ƙasa ya yi shiru kamar zata shiga sai kuma ta fasa ta tsaya cak ta samu" kanta da yi masa addu'a samun sauƙi da mafita a rayuwarsa da shiriya idan yana da rabo. """Allah Ya shiryarka idan kana da rabo""" "Ya ɗago kan shi ya juya kaɗan suka haɗa ido, ba ƙaramin gigita ta yi da ganin idanunsa a haka ba, ya ƙura" "mata ido a ransa girman nacinta yake ƙara jinjinawa duk da bai yi mamaki bai kuma zama sabon abu ba," "bai fiya son takura ba wani lokacin. Safiyyerh ta harɗe hannayenta a ƙirji ta ce ""Ko yunwa kake ji na daba" "maka abinci? Ko shayi?""" """To na zo na yi maka shira? Ko waƙa?""" """Get out...""" "Ya ce a hankali muryarsa ƙasa ta buɗe ido jin ya yi turanci ta ce ""Wow ashe a ɗan san wani abu, nifa ba" "zan fita ba bakina ciwo yake na rashin magana gaskiya"" kafin ya yi magana ta shiga cikin ɗakin ya yi saurin tashi da ƙyar ya nufi kujera ya kwanta ƙafarsa ɗaya a armchair ɗaya a can saman kujera hannayensa ya harɗe a ƙirji idanunsa rufe. Safiyyerh ta zauna a ƙasa ita kanta bata san me ya sa take son yin magana da shi ba, ta ji kuma tana barin wajansu zata haɗa Kinal da shi ita take son auren ɗan daba a hankali muryarta a nutse ta ce ""Sunana Safiyyerh Abdu Marafa, ni ce auta a gidanmu..."" Ta ɗan yi shiru bata ga alamar yana ma jinta ba kamar bacci yake yi haka yanayinsa ya nuna bata karaya ba ta sake" matsawa ta ɗora da faɗin. """Mahaifina professor ne ya koyar a jami'o'i da yawa a wannan ƙasar cikakken lakcara ne matasa na son" "shi sosai saboda yana taimaka musu da shawarwari. Ina da yayyi huɗu babban yayenmu sunansa Aliyu muna ce masa Captain shi soja ne, bashi da kirki gabaɗaya baya dariya kamar kai ɗin nan amma shi ba baƙi bane fari tas, yana da ilimi he is educated, sai mai bi masa Dr Hash likita shi a ɓangaren kwakwalwa Neurologist, shi rayuwarsa ba sawa ba hanawa sai my favourite Yaya J sunansa Junaid shi aiki biyu yake yi aikin banki da business, ina son shi sosai kamar yadda yake so na, rayuwarsa abar sha'awa ce wallahi. The last one Awais Shi kuma ɓangaren siyasa yake so amma daddy baya so yanzu dai ya ce yana son zama shahararren ɗan kasuwa ne, sai kuma ni Safiyyerh nima na yi karatu ina aiki yanzu matsayin Manager a FS WORLD INVESTMENT COMPANY, ina da saurayina da nake so kuma yake so na Ashraf sunansa ɗan mai kamfanin da nake aiki ne, akwai wasu abubuwa da bana ganewa a kamfanin..."" Shiru ta" yi da sauri kuma ta kalle shi taga har yanzu idanunsa rufe yake bai motsa ba """Kodayake shikenan, saura kwana ɗaya auren mu da Ashraf ya rasu, Ashraf died ya mutu ya bar ni cikin" "tsoro da fargaba, a ranar daya rasu a ranar ne aka aura mini yayana Aliyu, da dai bana jituwa da shi sam" "amma ƙaddara ta haɗa kuma Ubangiji kaɗai ya san dalilin hakan, wannan shine labarin Safiyyerh Abdu" "Marafa""" "Ta leƙa fuskarsa taga idonsa still a rufe ta tura bakinta gaba ""Nima sai ka bani labarinka ai muna zaune" "waje guda bai kamata bamu san juna ba"" miƙewa taga ya yi ya nufi ƙofa kafin ta bi bayansa har ya fice" daga cikin gidan. "****Eng Ali wali ya dinga kallon Moh da yake tsaye kafin ya ce ""Ina wayar daka amsa wajena? Mene" "amfaninta ina kira baka ɗauka wai?""" """Ba gani gabanka ba?"" Moh ya ce yana kame fuskarsa kamar kodayaushe." """Yarinyar nan tana wajanka ko Mutallab?"" Moh ya yi tsaki a fili da ƙarfi kuma ya ce ""Ni a tarihina sau" "ɗaya ake faɗa mini magana na haddace ka yi batu kawai"" ya ƙarasa maganar yana jawo flask ɗin shayi ya tsiyayi ruwan zafi ya saka madara da su milo ya nemi waje ya zauna ya janyo biredi da plate ɗin ƙwai ya" fara ci duk zafinsa da taurin kan shi a nutse yake cin abinci sai dai baya laumar wasa """Daman kai aka kawowa abincin karin Mutallab? Ai shikenan magana nake so mu yi very important akan" "yarinyar nan daka ɗakko"" ya yi shiru can ya ce ""magana nake maka fa ka yi shiru""" """Kunne ke ji""" """Professor ya raina mini hankali wai ko kashe yarinyar nan zan yi ko a jikinsa yana nufin bai damu da ita" "bane ko mene? To wallahi ni Ali wali zan bashi mamaki, yarinyar nan kafin ya ganta sai ikon Allah don haka ka yi yadda na ce a kanta, ka yi mata fyaɗe ka yi yadda ka so da ita har ta samu ciki yadda zamu watsa labaran yarinyar professor Abdu Marafa ta yi cikin shege ya kore ta daga gida ni kuma na ɗauke ta na kula da ita har zuwa haihuwa,kaga daga nan hankalin jama'a zai yi kan Professor Abdu a bar batuna ni kuma na yi amfani da wannan opportunity wajan cin nasara a zaɓen da yake gabatuwa, don this time ba zan taɓa barin Hon Maɗatai ya yi nasara a zaɓe ba zan yi duk abin da zai tabbatar dani ne na ci zaɓe ko a can hukumar zaɓan inec na shirya tsaf ba gudu ba jada baya siyasa sai ɗan siyasa, harkar siyasa da zama wani a harkar ƙasar nan sai ka nuna ba wani shege ka cire tausayi da imani, ba ri ka ji Mutallab duk wani" "ɗan siyasa kan shi kawai ya sani"" ya numfasa yana ɗaukar ruwa ya sha." "Moh dai har lokacin shayin yake sha hankali kwance abin shi. Ali wali ya duƙa ya ce ""Dole ka yi wa" "Safiyyerh fyaɗe dole ne ka yi wa yarinyar nan ciki, samun cikinta shine plan ɗina na farko da zai kai ni matakin hawa kujerar ɗan majalisa""" """To ya ake cikin?""" """Baka san yadda ake yin ciki ba, ciki na haihu fa?""" """E, ban sani ba""" """Mutallab, da ake cewa ka yi aure a ranar an kashe maka matarka da me za ka yi da auren da ka yi""" """Bayan a yi wa mutum girki ya ci ya yi bacci akwai wani abu ne? To ni ban iya yin ciki ba, sara da soka" "kawai na sani a rayuwa da shiga jeji, ka bar batun hakan bani ba ko waye ba za a yi mata wani abu ba""" """Moh""" """Ali wali"" Mutallab ya ce yana yin kyatsa yana miƙewa tsaye kuma. ""Mutallab yadda aka fara aikin nan" "da kai, to da kai za a ɗora kuma a ƙarashe dole zaka yi wa Safiyyerh fyaɗe i am telling you this, za ka ce na faɗa maka""" """To ka fara bani matarka na yi mata ai kana da ita, sai kace Professor ɗinne ya yi mata"" Ali wali ya dinga" "kallon Moh ganin how serious he is da maganar kuma da gaske yake. ""Ni zan shige zan na ji kira idan ka" "shirya bani matar taka tunda yarinyarka Noor bata ƙasar""" """Ina kasan ina da yarinyar Noor?""" """Ali wali kenan""" Hanyar fita ya yi kamar wancan karan ya ƙara jin sauti mai kama da ihu ya dinga kallon ƙofar kafin Ali wali ya ƙarasu har Moh ya buɗe ƙofar ya shiga cak ya tsaya ganin wata mahaukaciya zaune sai ihu take "ita kaɗai gashinta ya rufe mata fuska ya juya ya kalli Ali wali ya ƙara kallon matar bai yi magana ba ya saki ƙofar zai fita Ali wali ya ce ""Ka manta kaga wannan, sirrina ne""" Ko magana Mutallab bai yi ba ya kwashi kuɗi ya yi waje abinsa yana rufe fuskarsa. Bayan ya fita Ali wali "ya ɗauki waya ya yi kira ana ɗauka ya ce ""an samu matsala P.A yau wani yaga ajjiyata, fitar maganar nan daidai yake da zuwana gidan yari"" ta cikin wayar P.A ya ce" """Kafin ka je gidan yarin ka fara tura wanda yaga ajjiyar taka can""" """Mutallab ne""" """Tab, matsala kenan ina ruwan ciwon idanu wannan yana matsala kuna samun akasi za kaga ba daidai" "ba"" Ali wali ya yi murmushi ya ce ""Ina da tsari P.A idan na tabbatar na ci wannan kujerar zan yi tuggun da za a yi wa Mai dawa ɗaurin rai da rai a gidan yari, ka zo mu yi magana wai kasan har batun ƴa ta Noor ya" "sani, uhm sai ka zo dai""" Yana gama wayar ya duba interview ɗin da za a yi da dukkan wani ɗan takarar ɗan majalisa daka mabanbanta jam'iyyu wanda BBC ke shiryawa hakan yana nufin za su haɗu waje guda da Hon Maɗatai da Dr Abraham Denial David yana da buƙatar ya zauna ya rubuta dukkan abin da zai faɗa a wajan. ***Yana zaune ya zubawa yaron idanu gabaɗaya ba zai shige shekaru biyu da watanni ba a duniya ya yi "wayo gwanin sha'awa duk wanda yaga yaron sai ya burge shi akwai shiga rai da ƙyar yake buɗe idanu saboda farin da yake da shi ya sauke ajjiyar zuciya yaushe zai rabu da damuwar ran shi sai yaushe zai ga Safiyyerh ya nuna mata abin da Ubangiji ya bata, daga samun cikin har haihuwar ba wanda ta sani. A fili ya ce ""Come back please Safiyyerh, where are you ina kika shiga haka me ya sa hakan? Jininki fa" "Safiyyerh haba my innocent Mahmah""" """Ka dinga yin addu'a komai zai daidaita ya zama tarihi Ubangiji yana gani kuma yana kallo ba zai bar" "addu'ar ta tashi a banza ba, zata dawo ta damu ɗan ta, zata dawo a faɗa mata gaskiya, mu ma muna da namu laifin""" """I missed Safiyyerh dear, ki bar ni na koka"" ya ƙarasa ya ɗauki babyn ya rungume a jikinsa hatta farinsa" "irin na uwarsa ne sak yaushe zai ga Safiyyerh ne? Wayarsa ya ɗauka ya yi kira ana ɗauka ya ce ""Har yanzu ba wani information akai ko?"" Ya yi shiru can ya ƙara cewa ""Ka san komai ba, ka san yadda na samu na tsira da raina bana sha'awar komawa kuma ni da aikin lauya har abada, komai namu a can muka baro bani da picture ɗin Safiyyerh ko guda wallahi zan yi ƙoƙarin neman ƙwararren mai zane na" "gani ko za a dace thank you""" "Kashe kiran ya yi ya ajjiye wayar yana sake rungume yaron da ko ɗomin jikin uwa bai sani ba, balle ya sha" nono kamar yadda kowacce uwa ke shayar da nata ɗan. "***Safiyyerh na zaune bayan ta gama musu girki Goje yana ci da sauri yana ƙona harshe ta ce ""Kaci a" "hankali mana akwai zafi"" ya yi murmushi ya ce ""Allah dai ya ba ki kada Manager""" """Amin""" "Suka yi shiru can ta ce ""Wai ba ka ce yayar wannan babban naku ce ta mutu ba? Me ya sa yake zaune a" "nan wai, ina yayenku suke"" Goje ya ce ""Babata ta mutu ni haka baba, shi kuma iyayensa suna nan cikin" "Birget Scorpion ai baya son zuwa gida ko unguwarsu baya son zuwa, tun bayan daya dawo daga gidan yari wajan state cid""" """Kai me ya yi haka to? Kwanansa nawa a wajansu""" """Shekara uku""" "Safiyyerh ta jinjina kai har ranta ta ji tana son cin labarinsa waye shi a hankali ta ce ""Ai daman naga baya" "ji shikenan da wuƙa a hannu ya sari wani wacce kalar rayuwa ce haka?""" "Goje ya ce ""Manager kenan, ai yanayi ne ke sanyawa a zama haka babu wanda ke son zama mutumin" "banza fa, ki gane hakan"". ""Son zuciya dai, Ubangiji daya halicci bayinsa an ce baya ɗora musu abin da ba za su iya ba, a tsaftace halicci kowa tun daga cikin uwa mahaifiya, a nan son zuciya ne da rashin" "wadataccen imani a zuciya da kuma yana da ilimi ai ba zai yi hakan ba"" Goje ya ce" """Ko? Kin san shi ne kin san waye shi? To ki maye masa gurbin abin da ya rasa sai kiga ya dawo daidai idan" "an yi sa'a""" """Me ya rasa shi ɗin?""" """Soyayya, ta uwa, ta mahaifi, ta mata""" """Ok nan wai a haka yana da mata?""" """Ta rasu"" Goje ya ce a taƙaice ta yi shiru ""Ki gwada cewa kina son kiga ki ce za ki aure shi"" da sauri" "Safiyyerh ta kalli Goje ta ce ""Kasan me kake cewa ne? Ina da aure fa ai zunubi ne haka""" """Zance kenan, ba ki da wani aure yarinya haka kalar masu auren take kenan?"" Safiyyerh ta yi shiru ita dai" "ko bata aure shi ba kawai za ta yi using opportunityn ɗin nan ya bata labarinsa, ko a lissafin ƙaddarorinta babu batun zama da ɗan daba balle soyayya har ace aure amma idan har zai bata labarinsa lallai za ta yi wani abu. Ta yi murmushi ta ce" """Kana da gaskiya ka gano ni, ai kaf ƙawayena ni ce bani da aure to bana son gori shine fa nake cewa ina" "da aure shi Captain ɗin ai yayana ne don ka ji, amma kana ganin zai so ni? He is such a arrogant, boring person yana da matsala""" """Ki gwada mana""" """Zan ƙoƙarta, ya sunan shi ok ka ce Scorpion ko?""" """Mutallab sunan shi, mantawa na yi""" """Wow a nice name, sunan shi ya fi shi kyau shine kuje ce masa mai jeji? Kai ya sunanka?"" Ya yi mata" shiru kawai sai ta miƙe ta shige ɗaki. "***A karo na biyu Aliyu ya kalli Commander ya ce ""Sir ka yi replacing nawa da wani mana""" """Aliyu me ya sa kake yin haka, na lura kamar aikin soja ya fara fita daga ranka ko? Ka je ka yi tunanin tun" "farko wahalar daka sha kafin zama abin da ka zama, ƙiriƙiri an ƙara maka muƙami amma ka nuna baka son ana kiranka da sunan muƙamin sai Captain? Why?""" """Sir to a ɗan bani sati guda ok?""" """Ba zai yiwu ba, ka je ka fara shiri cikin daren nan da kwana biyu za a poster ku"" rai ɓace Aliyu ya miƙe" "ya fita bai taɓa Jin takaici da kuma dana sanin zama soja ba a rayuwarsa sai wannan lokacin, shekarunsa nawa a duniya sai yaushe zai cigaba da jurewa yaushe zai ta yin haƙuri baya son shiga cikin ko barrack ne balle a nisanta shi da garin, ya samu sauƙi daga matsalar mata ga kuma wannan matsalar he need his" "wife, seriously he need his Safii yana buƙatar Safiyyerh a gefensa." "Daddy ya dinga kallon Aliyu kafin ya ce ""Aliyu mene plan ɗinka akan case ɗin nan wai? Sp Ghali yana" "neman information ka ja baki ka yi shiru na ce ka cire hannunka a wannan matsalar ko, ka san me hakan yake nufi?""" """Daddy Safiyyerh fa matata ce hakƙin kare ta yana wajena so allow me to do daddy ka rabu dani""" """Allow me to do daddy"" daddy ya maimaita ya juya ya kalli Ummimi dake zaune tana kallon Aliyu ya ce" """Kin gani ko Zahiyerh idan Aliyu ya saka na rasa Maama zai yi mamakina"" murmushi kawai ta yi ta ce ""Matarsa ce fa, ta ya ya zai yi wasa da ranta bayan yana buƙatar ta cikin tasa rayuwar, bana son wani magana mai tsayi da bayane babu mai yi wa Safiyyerh kutse a rayuwarta ka sani, su yi nasu binciken" "shima ya yi""" """Aliyu bar wajan nan""" "Fita ya yi rama rasa wanne kalar tunani zai yi, daddy ya lumshe idanunsa a fili ake ganin bugawar" "zuciyarsa bai shirya ba sam, baya jin kuma akwai abin da zai iya kawo masa cikas bai yi maganinsa ba." Daddy ya gargaɗi kowa akan kar a fitar da maganar sace Safiyyerh kwatsam zance ya fita a shafin daddyn "wanda shi kansa bai san yaya aka yi ba, wayarsa kullum na hannunsa balle ya ce wani ya ɗauka ya yi posting cikin yaran, ya tabbatar kuma ba hacking wayar aka yi ba, aka fara kiran wayarsa domin tabbatar" da gaskiyar al'amarin ya rasa ya ya zai yi kawai ya ɗauki wayar ya kashe. ***Mutallab na zaune yana sauraren Goje Safiyyerh ta fito ta saka hijabi har ƙasa bai kalle ta sai haɗe fuska da ya yi ta ce """Abokina Goje barka ya jiki naga an yi maka treatment, ku siyo ka yayyenki na dinga yi muku tunda dai" "dabar ya zama dole na iya ai"" murmushi ya yi" """Na ɗauka lissafin kuɗi kawai kike ai? Ashe likita ce""" "Ta yi murmushi ta ce ""Ina yini?"" Ta faɗa tana kallon Moh ya yi kicin-kicin da fuska bai amsa ba." """Wallahi kyau kake mini idan kana haɗa fuskar nan, na ji ina son ka kuma zan iya aurenka wallahi"" ya" juya ya kalleta da sauri ta kashe masa idanu ɗaya ta ce """What if I tell you, I love you?"" Ta sake cewa" """Idan fa ka amince zan so ka har numfashina na ƙarshe a duniya, kawai dai kar ka wulaƙanta ni""" """Ke bar nan""" "Ya furta a kausashe kamar ya ce ya shiga uku ""Na san saboda na ce maka ina da aure ne, wasa nake yi" "don kar ku yi mini wani abun ne na faɗa fa, trust me i love you kuma na ji zan iya aurenka a yadda kake, zan baka farinciki walwala da jin daɗi ka amince mini ka ji dear"" Moh ya dinga kallon ta wani irin kallo wanda bai ma san yana yi ba,sai dai ba'a tantance kallon na mene yanayin fuskarsa bai bada damar hakan ba, kaifin idanunsa ya saka Safiyyerh ƙasa da nata idanun, duk da shaye-shayen da ya ke yi da ɗaukar wuƙa matsayin abokiyar rayuwa da tarin raunukan da suke fuskar bai hana wani irin tsoro da shakkarsa ta gitta a zuciyar Safiyyerh Abdu Marafa ba, wani kwarjinin take hango wa na musamman a fuskar Mutallab Tahhb haibarsa da kwarjininsa mai ban tsoro ga namiji balle ɗiya mace sai yanzu take ji ta yi tsaurin idanu wajan tunkarar shi da wannan maganar mai kama da tatsuniya a gare shi, gare shi kallon kin raina mini wayo ya kewa Safiyyerh da tunanin ko ta samu matsala da nata tunanin tunanin ne? Idan ba matsala ta samu na gushewar tunani ba abu mamaki ne gare shi da jin furucinta ya yunƙura zai" tashi ta riga shi miƙewa kanta a ƙasa hawaye na zuba a idanunta. """Don darajar da Allah Ya yiwa Manzon Sallallahu alaihi Wasallama ka saurare ni, ba zan taɓa juya maka" "baya ko da nasani b a kasancewa ta da kai, kai musulmi ne nima musulma ce babu haramci idan mace ta ƙaunaci namijin daya kwanta a ƙasan zuciyarta, a kullum na ganka sai na ji zuciyata na kiran Safiyyerh wannan shine ƙaddararki zaɓin da kike jira irin namijin da kike fata, idan zuciyata ta kusanci zuciyarka sai na ji tawa zuciyar ta sake buɗewa da tarin tausayinka, kullum mutuwa nake da farfaɗuwa da soyayyarka ta yan kwanakin nan data rutsa da zuciyar Safiyyerh Abdu Marafa, kullum mutuwa nake da son ka, wallahi...,"" kasa cigaba ta yi saboda kukan daya ƙwace mata da gaske, da ace ita ƴar wasan kwaikwayo ce irin fina finai da ake haskawa sai ta ce a yanzu acting take, duk abin da take faɗa she doesn't mean it, iya laɓɓanta ne kawai ta yi hakanne saboda ta yi kutse cikin rayuwarsa ta san waye shi me ya sa ya zama" "abin da ya zama, tana son jin labarai mai kama da hikaya ko almara ko na soyayya." """Will you love me?"" Ta ce tana marairace masa fuska tare da ɗan turo masa jajayen cute lips ɗinta, ya bi" lips ɗin da kallo ta haɗe hannaye waje guda ta langwaɓar da kai """Please, Safiyyerh loves you a nan a cikin nan ɗina""" Ta nuna masa saitin ƙirjinta wajan zuciya da yatsarta manuniyya sai ƙifta idanu take. Har lokacin bai ce mata komai ba kamar yadda ta lura yawan magana ba ɗabi'arsa bane yana wanzuwa da shiru da tunanin ya fi masa. A duk maganarta ɗaya ƙare haɗe fuska yake yi ya zaro sigari ya kunna ya saka a baki da ƙarfi ya zuƙi hayaƙin yana jin saukar hayaƙin ƙasan ƙirjinsa ya hura kumatu ya matsa dab ya fesa mata a fuska ya yi gaba abin shi yana taku ɗaiɗai irin he don't care. Safiyyerh ta bisa da idanu ta yi shiru ta ji ta damu sosai a ranta tana Astagafirulla data tuna da gaske ita matar aure ce matar Aliyu Abdu Marafa ce ita halaliyyarsa ta jingina da jikin bango tana lumshe idanunta. "Moh bai ƙara dawowa cikin gidan ba, har dare ya nutsa bama shi ɗaya ba kusan dukkan su basa nan ta" "dinga sallah tana addu'a har girki ta yi musu ta ajjiye amma ya yi sanyi. Tana haka ta ji an buɗe gidan da sauri an shigo ta buɗe ƙofa ba tsoro ta fito Mangal sai nishi yake yana kallon ta, da gudu Goje shima ya shigo yana shigowa kuma ya rufe ƙofar ya zube a ƙasa ta kalle su cikin sigar damuwa ta ce ""Ka rufe ƙofar" "shi kuma fa?""" """Bai shigo ba?"" Ta jinjina masa kai ya miƙe tsaye ya ce ""Jagwal kenan, ai kuwa bama tare""" """Innalillahi kamarya like how bakwa tare?""" """Ke bafa wani abu saɓe kawai ki je ki yi kasa ko"". ""A'a don Allah ka je ka nemo shi ka ji ɗan'uwanka ne fa" "idan wani abu ya same shi ai ba za ka ji daɗi ba, shi ma ba zai bari komai ya same ku ba"" ya yi murmushi ta lura yana da fara'a ba kamar sauran ba ""Ubangiji nada kyakkyawan tanadi a rayuwar Mai dawa, ba" "yanzu zai mutu ba kin ji ko?""" """Na kawo muku abinci?""" """Dar daidai kenan kin taimaki ƴan hanjina jagwalo shi nan a ɓatar da shi a rufawa ciki asiri"" abincin ta" "ɗakko ta kawo musu duk yadda taso su wanke hannu ƙi sukai Kodayake haka ogan nasu shima yake. Har bacci ya ɗauke ta bata saka shi a idanunta ba. Sai da asuba ta fito dafa ruwan wanka kamar jiya haka ta ganshi ya yi shiru yana kallon sama, tunanin maganganun da Abbasa ta yi masa yake da abin da Ali wali" ya dinga nanata masa akan Safiyyerh. """Bai kamata gwarzona ya wanzu yana tunanin da zai iya illata masa rayuwarsa da zuciyarsa ba, haba" "mafaraucina"" ya juya ya kalle ta, ta kashe masa idanu ta ce ""Yes, ba farautar dabbobi kawai ka iya ba ka yi dacen farautar zuciyar ƴar Professor Abdu Marafa"" kamar a buge yake haka ta lura da shi musamman yanayin zaman da ya yi, sai a lokacin ta lura da yankan dake damtsen hannunsa ta ƙarasa ta duƙa ta ce ""Subuhanallahi faɗa ka je ka yi haba mai sunan manya, Muhammad Mutallab fa masu sunanku salihan" "banyi ne""" "Ya duƙar da kan shi ƙasa ta je ta ɗakko kayan da Goje ya kawo ta zauna dab da shi, ta kamo hannun nasa" "sarai ya jita amma bai kula ta ba, tunani ne ya addaba masa. Ya shiga hura masa iskar bakinsa ganin" yankan na kumfa data saka magani ta gama yi masa treatment ta kalle shi taga ya rufe idanu miƙewa ta yi zata fita kamar daga sama ta ji ya ce """Cikakken sunanki""" """Safiyyerh Abdu Marafa""" """Cikakke"" ya sake maimaitawa ""Haka sunan yake fa Jarumi""" """Shi Abdu?""" """E, sunan daddy kenan Abdu"" ya buɗe jajayen idanunsa ya watsa mata su ta yi saurin yin ƙasa da nata" "idanun ta fidda ran zai yi magana har zata juya ya ce ""Ƙarya, idan na tuna miki na kwaɗa miki mari ko?"". ""Allah ni dai haka na sani babana ne fa""" """Uhmm"" ganin kamar da magana a bakinsa kuma a buge yake ta matsa ta zauna ta ce ""Jarumi, do you" "want to say something? Say it. Ka ce wani abu Jarumi""" """Faɗi mana Jarumi""" """Tiger"" ya ce a hankali ta ce ""Me ka ce? Ban ji ba""" """Ammm, hmm kika ce ba ki da aure?"" Ta ce ""E, bani da shi like a told you"" ya buɗe ido ya zura mata" "idanu yana ta kallon ta da ƙyar ya iya cewa ""za ki so ni?""" """Zan aure ka na rayu da kai idan ka faɗa mini labarinka waye kai?"" Ya sake yi mata shiru ""Ina ji""" """Zana ba ki labarina idan za ki aure ni""" """Ni Safiyyerh na yi maka wannan alƙawarin zan rayu da kai a duk yadda rayuwa ta yi da kai Jarumi"" ya" "miƙa mata tafin hannunsa a hankali kamar mai jin tsoro ta kalli hannun cike da rashin fahimta, jiran ba'asi take shi kuma ya yi shiru sun ɗauki minti biyar da wasu daƙiƙo a hankali ya sake furta ""Promise"" ta dinga kallon hannun kafin ta yi Astagafirulla da tunanin Ubangiji ya yafe mata saboda igiyar auren wani ce a kanta ta ɗora ɗan ƙaramin hannunta cikin nasa, tana sawa ya damƙe kamar abin da yake jira kenan ya yi shiru ya lumshe idanunsa muryarta na rawa ta ce ""I Promise you Jarumi"" yana riƙe da hannun bai cika ba bai kuma yi magana ba can ya sake ta, ta fara masa magana sai dai ko tari bai kuma yi ba" tunaninta bacci yake yi ta dinga kallon shi tana son hango kyau ko ko muninsa. A daren ranar su Goje basa nan sai shi ɗaya yana busa hayaƙi a sama yake jinsa sosai ya ji an buɗe ƙofa "an shigo, maza ne har su huɗu sun rufe fuskokinsu ya damƙi wuƙarsa kafin ya miƙe ɗaya ya cafki wajan yankan da Safiyyerh ta gyara masa ya janyo hadda naman wajan suka fara kokawa yana buga su da ƙasa, cikin sauri Safiyyerh dake bacci ta farka zata fito daga cikin ɗakin ya yi baya da ƙarfi ya tura ta ciki ya rufe ƙofar ta taga ta leƙo tana kiran shi, taga ya ɗaga wuƙa ya sokawa ɗaya a gefen wuya ya ƙara soka masa a ciki ya watsar da shi can gefe yana kakari, Safiyyerh ta zaro idanu tana rufe baki saboda ihu za ta yi ganin yadda aka yi kisan kai akan idanunta, bata san mene ya faru ba taga ɗaya ya zaro sirinjin allura ya zirarawa Moh a damtsen shi, ya sake zaro wani ya yi masa da azama Moh ya ɗaga wuƙar hannunsa ya sari wanda ya yi masa hakan ya goce ganin sun yi masa allurar suka ja wanda yake kwance kamar gawa" "suka bar gidan, a hankali ya yi baya ya zube saman kujera jini na ɗiga jikinsa" "Ilahirin jikin Safiyyerh rawa yake cikinta ya ƙulle ta shiga uku, kisan kai aka yi akan idanunta haka dabar" "take dama? Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un. Moh kuma minti goma ya yi yawa ya ji zufa na yanko masa jikinsa ya yi sanyi wani irin baƙon al'amarin ya fara ziyartar gangar jikinsa yana sauka a mararsa, abin da bai taɓa tunani ba idanunsa ya shige ciki ya ɗauki ƙwaya ya zura a ƙasan harshen shi da tunanin zai daina ji, amma ina kan shi ya hau ciwo ya miƙe da ƙyar ya nufi ɗaki jin tsigar jikinsa na miƙewa da zubewa sanyi na ratsa shi komai na jikinsa ya bubbuɗe al'amarin buƙatuwar wani abu. Ya kwanta ya yi shiru can ya mirgina ya yi rufda ciki ya lumshe idanunsa ya jiƙe shimfiɗar lokacin ɗaya da zufa da jinin da yake zufa a jikinsa, ya rasa ciwon ciki yake ko mara ko zazzaɓi? Jijiyoyin kan shi sun miƙe raɗau lallai ya ji akwai abin da yake buƙata ya dinga juyi ya shanye sigari kwali wajan biyu amma ba abin da ya sauya ba zai ce" tsautsayi ne ya kai shi ɗakin Safiyyerh ba saboda kawai tsintar kan shi ya yi a ciki. Safiyyerh na bacci ta ji hucin numfashin mutum a fuskarta ta buɗe idanu da sauri ihu za ta yi ganin "fuskarsa kamar zai haɗe da tata ta yunƙura zata tashi ya saka hannu ya mayar da ita kwancan ""Dan Allah" "karka mini komai ka yi haƙuri ba zan sake kula ka ba, innalillahi na shiga uku daddy ka yi na tuba don" "Allah"" bai kulata ba yana daga durƙushen da yake dab da ita ya miƙa hannu ya kashe wutar ɗakin gabaɗaya." LAST FREE PAGES Waye Mutallab? Waye Scorpion? Wace Safiyyerh? Waye Daddy? Mene FS WORLD INVESTMENT COMPANY? Labarin Mutallab da tarihinsa ya fi wannan da muke ciki yanzu ai za ku zo jin wannan soyayyar ta ƙuruciya ba? Mene yake saka a fara daba da shaye-shaye? Wanne ganganci iyaye suke yi akan yara? Mece siyasa da cikakken tarihin dimokuraɗiyya? Za ku su sanin ya ake mulki a ƙasar nan? Har ku yi supporting yaran ku? Soyayya na saka shaye-shaye ne ko daba? Me ya sa Mata har uku suka mutu ta sadanadin MOH me ya sa ya kashe matarsa SAFIYYERH? YAUSHE SAFIYYERH TA HAIFI YARO? maza hanzarta yin payment chat with me on WhatsApp 08164069385 BRIGHT PENS... 2ND BATCH 💥MUƊALLAB 💥 B2: chapter 1: fire and ice Dig Johar bai bawa Aafiyyah damar juyawa zuwa ga Moh dake ɗaure cikin sarƙar da jami'an tsaron da suke team ɗin Aafiyyah suka saka mishi ba, ya yi saurin jan hannunta zuwa waje duk da ƙoƙarin turjewa da take yi kanta na matsanancin sarawa. Suna fita waje sauran team ɗin suka sarawa Dig Johar daya fito hannunsa riƙe dana Aafiyyah yana murmushi saboda yau ya cika wani burinsa na tsayin shekaru. Ɗaya daga cikin team ɗin ya kalli Aafiyyah da idanunta ke lumshewa a hankali ya sara mata alamar salute cikin turanci ya ce. "I congratulate you Maah" Calmly ta ce "Thank you" Ta faɗa tana shiga bayan motar da Paaahh ya buɗe mata, shima ɗin shiga ya yi bayan motar bayan ya gama magana da IP Inspector of police under FCID ranks. Ajjiyar zuciya Paaah ya sauke lokacin da driver ya yi reverse na motar tare da juyawa da ita zuwa saman titi idanunsa lumshe wani irin daɗi yake ji a cikin zuciyarsa burinsa na kama Scorpion ya cika ta dalilin ƴar daya haifa ashe sanya Aafiyyah matsayin staff ɗinsu ba ƙaramin taimako ya yi wa team nasa ba, hakan ya ƙarfafa masa qwwia ne wajan ganin how smart she is da kuma son sanya Aafiyyah cikin busy gudun kar ta samu isasshen lokacin yin tunanin abin da zai iya recovering tunaninta. Ya juya ya kalli Aafiyyah a sanda suke tafiya saman kwalta cikin nutsuwa ya kamo hannunta duk da kanta a sunkuye yake ya ce "You made it Maamah, daddy yana farinciki da nasarar daya samu ta dalilinki" "Abin da keke so shi nake so, nasararka tawa ce Dig Abdul-Johar Marafa, the latest father in the whole duniya, the special professor Abdu Marafa" Aafiyyah ta ce a hankali tana murmushi idanunta na sake lumshe tunaninta ya ɗan fara daidai kawai tana ƙoƙarin danne ciwon kan da take ji ne wanda yake ƙoƙarin ɗauke duk wani pleasure da take ciki a yanzu ɗin na dalilin kama Scorpion kamar yadda suke tunani. Paaah ya jinjina kai yana sake riƙe hannunta tare da dubanta a tsanake ya ce. "Wanne Professor?" "Professor dai wannan tsohon laccarar da muka sani" ta ce silently. Ya jinjina kai ya ce "Haka ne. Fuskar dana so nunawa jama'a dai, i love my job ina son yin nasara ko ta halin yaya ne Safiyyerh. Kin san har zuwa jami'a da na yi koyarwa duk set up ne, na yi shekaru ina zuwa a ƙoƙarin gano wani tsohon mai laifi, na rayu cikin ɗaliban jami'ar ba tare da sun cewa ni jam'i bane, kafin na gama aikina sai na ji ina sha'awar koyarwa domin tana ɓatar da asalin aikina kuma ba kowa muka yarda yasan suwaye mu ba, sai kawai na cigaba da zama ina koyarwa as volunteer" ya ce yana murmushi ita ɗin ma murmushi take yi ta ce "Oh Ya rabbi! Wayon Dig Johar staff and manager Aafiyyah ta ɗakko kenan" Ya ce "Sure, wannan shine jinin" "Paaahh cigaba da bani labarin" A hankali ya ce "Dole na ai, you make me happy Safiyyerh Abdul-Johar M" Ya ɗaga kai yaga sun ƙarasu babban gate ɗin gidan nasa, cikin sauri mai gadi ya buɗe tangamemen gate ɗin driver ya zura hancin motar ciki, jikin Aafiyyah na rawa ta fara ƙoƙarin buɗe mota a lokacin hankalinta yana ga Maj Aliyu domin har yanzu tana iya jiyo damuwa da ɓacin rai a muryarsa sanda ta kira shi yake maganar babu inda zata tunawa inda kidnappers ɗin suka kai ta? Kafin ta fita Paaah ya fito ya zago ya buɗe mata ta fito. Daidai nan Dr Hash ya fito daga cikin gidan kamar mai jiran zuwan nasu, a lokacin ma J ya fito shi da Awais sai Ummi. Daman suna tare da Paaah ɗin suka ga ya miƙe zumbur hankali tashe ya yi waje sai suka razana tare da tunanin ko wani abu ya samu Aafiyyah? Shine duk suke tsaye har kawo yanzu da suka jiyo shigowar mota. Murmushi sosai a fuskar Aafiyyah ta kalli J ta ce "Muhammad Junaid MJ I made it, na cika aikina" ta ce tana fari da idanunta duk da cewa ta rame kuma idanun nata ya yi laushi sosai. "You made what?" Awais said yana kallon Aafiyyah ya kasa shanye mamakinsa da gaza haƙurin bayani tare da jiran ji daga bakin Paaahh ya ce "Daddy ina aka gano Maamah?" "Zan yi muku bayani. Dr Hash" Ya kira Dr Hash yana masa kallo sai kuma ya kama Aafiyyah ya juyo da ita gabansa suna kallon juna ya ce "Ki yi wanka ki sallah ki ci abinci ki kwanta ki wuta sosai" baki ta buɗe za ta yi magana ta ji saukar sirinji a ƙasan wuyanta, ta riƙe hannun Paaah da ƙarfi wani irin zafi da azaba take ji a duk sanda za'ayi mata allurar musamman da ake yi mata unexpected. Ta yi ƙasa da kanta idanunta na sauya alamar bacci na shirin ɗaukar ta a wajan dalilin allurar kuma. Ɗago kai ta yi sai kuma ta yi murmushin nan nata ta ce. "Ba zan tambayi dalili ba Paaahh kamar kullum kana da naka dalilin wanda ya danne na Maamah" Ta saki hannunsa idanunta ya sauka akan Ummimi dake mata murmushi ta kuma tsare ta da idanu, a fili suka ji sauke ajjiyar zuciyar da Aafiyyah ta yi sai ta ji zafin allurar ya kau a sanda ta yi tozali da Ummimi. Cikin sauri ta saki hannun Paaah tana zuwa wajan Ummimi ta faɗa jikinta tana ƙanƙameta ta kasa yin kuka domin ta san tabbas an raunata zuciyar Ummimi ɗin a zahirance. "Autata always be mine" cewar Ummimi tana rungume Aafiyyah duk da nauyin idanun Ummi dana Paaah da ta ji amma ta gaza jure ganin Aafiyyah a gabanta ba tare da ta ji ɗuminta a jikinta ba, itama ɗin mantawa ta yi da idanun mutanen wajan ya riƙe Ummimi tana bubbuga ƙafarta tare da nuna mata taɓararta a fili wajan faɗin "Uhm'uhm na yi kewarki love, kika barni" "Dake mu ba mutane bane ko?" Cewar Dig Johar ya faɗa yana cillawa Aafiyyah harar wasa Ummi ta ce "Tayani gani dai, wai namiji da suna hajara kinibibin Maamah" "Kai Ummi" Aafiyyah ta ce "Kya ji da shi, barka da dawowa daga wajan Kidnappers" Murmushi kawai ta yi tana jan hannun Ummimi zuwa cikin gidan, shi dai J kallon Aafiyyah kawai yake gabaɗaya bashi da kuzari ko confidence ɗin kallonta tun ranar da batun aurenta da AA MARAFA ya sauka a kunnensa ya ji bawai kawai favourite ɗinsa bace akwai wani abu nada ban da bai sani ba, mikin zuciyarsa ƙara yawa yake ya ji ya tsani duk wani kusancin su da AA hasalima zafin AA nake yake ji a cikin tsokar dake rayuwa kullum a ƙirjinsa tana numfashi tare da tunatar da shi Aafiyyah lil sis ɗinsu ce madadin ya amshi wannan tunanin sai tunaninsa ya kurɓata na son sake kusanta zuciyarsa a dole zuwa ga Maamah ɗin. Rinannun idanunsa ya cire daga bayanta ya juya kawai tare da barin gidan gabaɗaya yana ji a waje zai samu nutsuwar da cikin gidan ya kasa samar masa a kullum. Awais, Dr Hashim cikin gidan suka nufa lokacin da suka marawa mahaifin nasu baya Dig AM. "Wash i feel helpless" "Malama jeki wanka ki zo ki bamu labari kin ji ko?" Ta ɗan harari Awais tare da share shi a hankali ta miƙe tsaye tare da ajjiye vail ɗin kan nata, sai lokacin ta lura da ƴar ƙaramar na'urar dake jikinta mai ɗaukan sauti murya da vedio da kuma wata ta daban mai nuna location ko da za'ayi tracking location na mutum wanda kuma ta nan ta kwashi duka bayanan da MM BLACKMAN yake bata. Yalwatacciyar sumar kanta mai zubin jaa ta sauka har bayanta a hankali take tafiya shap ɗin bayanta na juyawa gwanin sha'awa duk da bata da jiki kuma cikinta a shafe yake amma dukkan wata ƙibarta ta tattare waje guda tare da zama a hips ɗinta da kuma ƙirjinta shi ya sa take yawan saka abaya ko kaya ovar size gudun bayyanar dirin nata a fili steps ɗin benen take takawa har zuwa bedroom ɗinta. Zubawa kanta idanu ta yi ta cikin madubin dake ɗakin nata, sai ta ji wani abu mai kama da rauni ya mamaye zuciyarta ta ji kamar bata kyauta ba, ta ji kamar kama Scorpion shine abu mafi muni da girman laifin data aikatawa rayuwarta, ta ƙara jin kamar kanta da kanta ta cuta tare da zalunta ɗin, ta dinga tuna labaran daya bata idan ta haɗa daga farko zuwa ƙarshe sai ta ji akwai wani abu da ta yi missing a cikin labarin, mene shi?. "What is this? What did i missed?" Ta furta a fili lokacin da take zama a gefen gadon nata, ta yi shiru sai ta ji bata da kuzarin yin wankan ta kwanta a hankali tare da janyo teddynta ta rungume a ƙirjinta tare da lumshe idanunta ciwon kan nata na sauka a hankali. Sexcy eyes ɗinsa with his red lips sune suka fara mata gizau cikin idanunta, da sauri ta buɗe idanunta ta cewa "Oh! No please" Madadin ta daina ganin ƙwayar idanunsa a lokacin da yake kallonta cikin maye da gushewar hankali yake tambayarta ina ɗansa sai hakan ya faskara idanunta ya dinga hango masa faffaɗan ƙirjinsa dake cike da zanen Scorpion, da cukurkuɗaɗɗan gashin kansa har yankan gefen fuskarsa, juyawa ta yi tana murmushi can ta yi tsaki ta ce "You never be my headache Scorpion" tattara shi ta yi ta kwanta ko a cikin baccinta mafarkinsa ta dinga yi, idan ya kalle ta a mamakance cikin sexcy looking ɗin nan sai ya girgiza kai ko ya suɗe lips ɗinsa, ta fara tuna sanda ya ƙanƙameta a lokacin da take kuka daya shaƙeta kamar zai kashe ta. "Maamah" Paaah ya kira sunanta ganin ta ƙanƙame teddyn jikinta kamar zata tsaga ƙirjinta tare da mayar da teddyn ciki. Ya duba agogo ta shafe wajan awa huɗu da fara bacci ashe ko wanka ba ta yi ba, ya duba sai kawai ya girgiza kai ya fice yana janyo mata ƙofar bedroom ɗin nata. Sanda ya sakko main parlor suka haɗa idanu da Ummimi da sauri ya ɗauke nasa idanun, ba komai ke bashi tsoro ba amma yana tsananin tsoron shirun Ummimi da kame fuskarta, ɗakin baƙi ya nufa kamar yadda Awais ya sanar dashi yana da baƙi, yana ƙoƙarin fita Ummi ta ce "Batun Aliyu ka yi shiru baka ce komai ba, kuma kasan muna cikin tsoro da jimamin rashin jin nasa ko?" Ya ɗan tsaya sai ya juyo ya kalli Ummi ya jinjina kai ya ce "Aliyu yana hanya yanzu haka, ni nasa a rufe mini shi" ya ce yana duba agogon hannunsa. "Rufewa kuma?" Ya sake cewa "Haka ma ce" A hankali Ummimi ta ɗago kai ta kalli Paaah sai bata ce komai ba. Ummi ta ce "A bisa wanne dalilin?" "I will explain, ki mini uzurin shigowar shi gida ok?" "Allah Ya nuna mana" cewar Ummi furucin nata ya sake nuna rashin jin daɗin abin da Paaah ɗin ya aikata. Gently ya buɗe ƙofar part ɗin da yake amsar baƙin nasa, cikin sauri wanda yake tsaye ya kasa zama ya miƙe tsaye tare da nufar Paaah ya ce "Ka yi mini uziri na rashin haƙurin jiran kiran naka, wallahi Allah Ya sani i can't wait any longer, ina tsananin buƙatar ganinka Dig Abdul-Johar" shima Paaah jinjina kai ya yi bayan sun yi musabaha ya nuna masa kujera ya ce "Please have a seat Prof Abdulwahab" wanda aka kira da Prof Abdulwahab ɗin kasa zama ya yi, idanunsa ya yi zuru-zuru Paaahh ya ce "Don Allah zauna" sai kawai ya fashe da kuka sosai kamar jira yake yi, Paaahh ya yi shiru sai ya juya ya kalli sauran baƙin cikin kuka ya ce "Ya kashe mini gudaliyata, ya rabani da gudaliya he killed my daughter" "Subuhanallahi!" "Na yi kuskure a rayuwata babban kuskure, na ɗauka komai ya shige a sanda na dawo Naija a kuma sanda na ruski takwarar ƴar wajanka Safiyyerh tana cikin farinciki, na ɗauka da gaske yana son ta ashe yaudarar kai na nake, ya kashe mini gudaliyata ya rabani da Safiyyerh" magana yake yana kuka cikin tashin hankali idanunsa ya yi jajur bai gusa ba wajan furta "Na rasa kyakkyawar yarinyata, a lokacin da shekarun farinciki da jin daɗinta ya gama bayyana ina jin cewa i failed as a father, ni na jawa Safiyyerh dukkan abin da ya faru da ita, ni na lalata tarbiyarta wacce ta yi sanadin haɗuwarta da mutumin daya rabata da duniya ya yi mata kisan wulaƙanci an ganawa Safiyyerh azaba wajan rabata da ranta, ko zan rasa komai nawa wallahi sai an amsar mata haƙƙinta" ya ce yana sakin wani kukan har yanzu mikin abun sabunta kansa yake a cikin zuciyar Prof. Dig Johar ya ce "May her soul rest in peace in jannatul-firdausi" A hankali budurwar yarinyar ta ce "Amin" Dig Johar ya kalleta ya ce "Sunanki fa? Tare kuke?" "E. Sunana Waheebah ana ce mini Wahee ai tare muka yi makarantar Fgc da Aafiyyah" Paaahh ya ɗan kame fuska ya juya sai kuma ya tuna Aafiyyah bacci take yi. "Allah sarki" Prof ya ce "Ƴar ƙanwata ce Waheebah ƴar wajan Musbah, wannan kuma sunansa Aliyu ƙanina ne ciki ɗaya muke dashi duk abin da ya faruwa da gudaliya bashi da lafiya bai fiya zama ba sai lokaci zuwa lokaci, ko yazo kan je wajan Hajiyata ne kawai, shi costom ne muna kiransa da Haydar" Wanda yake zaune cikin nutsuwa ya juya ya kalli Dig Johar ya ce "Ina yini?" paaahh ya ce "Good day Aliyu Haydar" "Thank you " Paaahh ya ce "Ikon Allah. Prof Abdulwahab kamar mun haɗa zuri'a ɗaya? Ina da yarinya Safiyyerh kai ma kana da ita, nima ƴar kwanta Turai sunanta Wahee amma asalin sunan Waheeda ne kai kuma Waheebah, ina kuma da yaro mai suna Aliyu shi kuma soja ne. Anyway yanzu ya ake ciki? Ba shi yaron an kama shi bane? Ko har yanzu shari'a kuke yi dashi?" Prof Abdulwahab ya ce "An kama shi shekaru uku yana wajan jami'ai a ranar ƙarshe na zaman kuto aka samu sanarwar wai a sake shi, da alama manya ne suka shiga maganar yanzu haka sun jima da sakinsa yana yawo tare da ta'addanci ya zama cikakken ɗandaba na nemi hujjar sakinsa amma ance umarni ne daga can sama sunƙi faɗa mana sunan wanda ya saka a sake shi. Yanzu na saka a kama uban nasa domin ko komai nawa zai ƙare wallahi sai an ɗauki fansar ran gudaliya in sha Allah" ya faɗa yana jinjina kansa cike da damuwa. Miƙewa tsaye Dig Johar ya yi a hankali yana takawa sai kuma ya tsaya ya ce "Lallai duk wanda ya saka aka saki wannan yaron ba ƙaramin babban mutum bane a jihar nan ko ƙasar nan" Paaahh ya kalli Prof ya ce "Safiyyerh ƴa ce a wajena ko dan amincin dake tsakaninta da Maamah zan tsaya mata in sha Allah wajan ganin an hukunta shi ya biya bashin abin da ya yi in sha Allah. Zan iya ganin yaron?" "I have his photo on my phone" Waheebah ta ce tana duba wayarta sai ga picture ɗin MUTALLAB ya bayyana ta miƙawa masa with respect ya amsa, wani shock Paaahh ya ke kallon photon Mutallab kafin ya ce "This is complicated" "Mene ya faru?" Haydar asked. "Wannan yaron yau ɗin nan na kama shi fa? Yana hannun FCID yanzu haka ai komai yazo da sauƙi in sha Allah" Paaahh ya faɗa yana sake kallon photon Mutallab ɗin dake sanye da sport wear sai ya ce "Amma mene haɗinsa da Fgc?" Waheebah ta ce "A can ya yi karatu ai, class mate ɗin su Aafiyyah ne, a nan ma Safiyyerh ta ganshi har ta fara son shi har dai aka yi auren kamar alamara" "Na fahimta" ya ce a sanyaye. Sallama suka yi da zasu tafi Waheebah ta ce "Sir ko zan iya gaisawa da Aafiyyah Please?" Ya girgiza kai can ya nisa ya ce "ta ɗan fita ai sai kun sake zuwa in sha Allah" gabaɗaya suka fita waje a harabar gidan Waheebah ta samu Nahyan yana zaman jiran nasu hannunsu riƙe da wata kyakkyawar yarinya wacce suka haifa shi da Waheebah. Mota suka shiga gabaɗaya daidai lokacin Aafiyyah ta fito tana amsa waya saboda wayar sirri take yi da Accounter da sauri ta juya jin an ce "Nahyan kazo mu tafi" ƙoƙarin juyawa ta yi sai taga mota tana yin waje zasu fita daga cikin gidan, da sauri ta ce "Mahadi tsayar da motar nan yanzu" Paaahh dake tsaye ya ce "Ki yi musu me?" Ta ce "Na ji kamar na taɓa jin suna Nahyan, kuma na ji kamar na taɓa jin muryar mai maganar" Ya ce "Baƙina ne ko kina ai" Girgiza kai ta yi sai kuma ta ce "Ina zuwa Paaahh i knw them" Kafin ya yi magana ta yi saurin sauka daga steps ɗin tana kiran maigadi kafin ta ƙarasa wata mota ƙirar Range Rover Vogue black colour ta shigo cikin gidan da sauri, sai kuma wasu manyan motoci na sojoji da suka marawa motar farko baya cikin sauri suka fara diddrirowa kafin wani seconds sun zagaye gidan Dig Johar da bindigo a hannunsu fuska babu walwala. Wani magidancin saurayi ne mai ƙirar ƙarfi Captain Rafiq ya ƙarasu wajan motar cikin sauri ya buɗe murfin baya ya ce "welcome back Sir" ya ce yana sarawa tare da ƙamewa waje guda. Ƙafarsa mai sanye cikin Nike Killshort shoe, ita ce ta fara fitowa daga cikin motar a hankali ya ƙarasa fito da gangar jikinsa duk da cewar ya rame, amma ramar ya ɓoye saboda uniform ɗin jikinsa mai ɗauke da tambarin tsuntsu ya rufe ramar ga p.cap ɗin kansa da glasses ɗin daya rufe idanunsa dasu. Welcome sojojin suke ta yi masa bai kalli ko guda ba sai Rolex Submariner dake maƙale a hannunsa daya shiga dubawa. Cikin sauri kuma dib-dib yake taka ƙafafuwanta tun a shigowar tasu idanunsa ya sauka akan Maamah amma daya zo dab da ita sai ya yi banza da ita idanunsa akan Paaahh daya ja ya tsaya a gabanta. "Welcome Maj Aliyu Abdul-Johar Marafa" cewar Dig Johar. "Thanks sir" Itama Maamah banza ta yi wa Maj hankalinta na kan gate sai ta juya ta shige cikin gidan Maj ya taka zuwa ciki shima idanunsa zube a ƙugun Aafiyyah ransa na ɗan bacci ganin wandon jeans dake jikinta. Cikin sauri Ummimi ta miƙe tsaye shima ɗin da nasa saurin saboda kasa jurewa da ya yi ya nufi wajan Ummimi yana zuwa ya durƙusa gaban Ummimi akan ƙafafuwansa baya ta yi ta zauna akan kujera sai ya ɗora hannunta a saman kansa da suma ta ɗan taro ta shafa kan nasa ya sauke ajjiyar zuciya a hankali Ummimi ta ce "Simba". "Love" ya furta can ƙasan zuciyarsa yadda ita kaɗai zata ji. Sai ya ɗago idanunsa ya zubawa Ummimi ido. "Ban san me ya sa Aliyu yake zama yaro a gaban Zahiyerh ba" Anty Turai ta ce tana shigowa tare da Waheeda da kuma ƴar ƙanin mijinta Zahiderh. Bai bari wani ya sake magana ba ya yi saurin miƙewa ya nufi part ɗinsa, suka zuba masa ido musamman Ummi ita kuma Ummimi murmushi ta yi tana harɗe ƙafarta tare da ƙara jin ƙwarin jikinta ganin Maamah da Gadanga a gabanta a kuma kusa da ita. Anty Turai ta zauna ta ce "Ina yini Yaya? Hajiya Muwaddat ina yini" Paaahh ya jinjina kai kawai Ummi ta amsa ta "Alhamd ya kwanan su Waheeda?" Anty Turai ta ce "Lafiya" Sai ta juya kan Ummimi ta ce "Sannu Zahiyerh ina yini ya ƙarfin jiki?" "Sannu Turai" Ummimi ta ce tana miƙewa su Waheeda suka gaida mutanen wajan. Ita dai Zahiderh hankalinta yana kan Maj Aliyu tana jin kamar ta yi tsuntsunwa tare da aron fiffike ta je wajansa ko zuciyarta zata samu nutsuwa tana azabtuwa da so da begensa a cikin zuciyarta yana wahalar da ita tabbas kuma zuciyarta ta yi wa alƙawarin dole ta aure shi. "Maamah je kiwa Glory magana ya shiryawa Aliyu abinci ko?" Cikin sauri Waheeda ta ce "Ummi bari na yi masa sai Zahiderh ta taya ni?" Aafiyyah dai na jinsu domin ba wanda ta kalla hatta Anty Turai. Ummi ta ce "kayya, Aliyu ba abincin kowa yake ci ba wannan ma ni na yi wa babansu sai kuma gashi ya dawo, sai dai idan kai masa za ki yi part nasa" miƙewa Waheeda ta yi ta ce "Bari na kai masa, Zahiderh zo ki taya ni Please" miƙewa ta yi. Cikin suka nufa. "Wahee...!" Aka kira sunan Waheeda ta juya ƙirjinta na bugawa, Allah Ya ɗora mata tsoron Ummimi. Ta juya ta ce "Na'am Ummimi" "Gadanga ai yana da iyalin da zasu iya yi masa ɗawainiyya kar a wahalar dake kin ji? Je ki huta" "Ummimi zan iya" "Wahee go and seat" ta ce babu walwala a maganar. Sai kuma ta kalli Aafiyyah ta ce "da kike tsaye kamar sanda what are you waiting for?" Sai Aafiyyah ta fara rarraba idanu can ta ce "Kamarya?" "Bana son shirme, je ki kai wa mijinki abinci ko? Ko kuma ki fara zuwa ki tambaye shi me yake so abincin ya yi sanyi ko an yi warming nasa he won't eat gaskiya" Aafiyyah dai na tsaye ganin Ummimi na shirin miƙewa ta yi saurin shigewa cikin kitchen ɗin. Takaici ya cika zuciyar Anty Turai har ta kasa jurewa ta ce "Zahiderh me kike nufi ne? Me ya sa kike ƙoƙarin raba Aliyu da Waheeda ne? Me ya sa kuke son ƙulla zuƙatan da suka kasance fire and ice waje guda? Babu shiri da jituwa tsakanin Aliyu da ƴar gwal ɗin taki ki bar Aliyu ya auri Zahiderh domin ita yake so" Ummi dai murmushi take yi Ummimi ta ce "Turai" ta kira sunan a kausashe kafin ta ce "Ki aura mishi Zahiderh mana ai ban hana ba, bani na haɗa auren Aliyu da Aafiyyah ba, je ki tambayi yayan naki Dig Abdul-Johar sai kuma ki tambayi Aliyu yana son Maamah ko baya so? Sai kuma ki faɗa masa kin haɗa aurensa dana ƴar ƙanin mijinki" ta faɗa tana miƙewa. "Idan ma gatse kike za ki gani" Ummimi ta juyo ta ce "Ki daina ƙoƙarin cewa zan gani Turai, kin san waye mijina? Ki duba Aliyu Maj ne ki duba Maamah kiga matsayinta, ki tsaya iya limit naki ok?" "Zahiyerh idan naƙi fa?" "Turai!" Paaahh ya kira sunanta da ƙarfi yana nuna ta da yatsa ya ce "mutuniyar banza mutuniyar wofi ashe ba ki da lissafi? Kin san dawa kike magana ne Turai?" Ta yi masa banza ta san tana saki magana zata iya jin saukar mari ko ya ce a rufe masa ita don haka ta ja bakinta ta yi shiru tana girgiza ƙafa fuska ba walwala. Waheeda ta ji ta tuzarta da abin da akaiwa mahaifiyarta shi Paaahh baya tuna cewa Turai ƙanwarsa ciki ɗaya sai ta ji ta sake ninka tsanar da ta yi wa Aafiyyah a ranta tunanin zuciyar Zahiderh ya bambanta dana Waheeda ita ji take ko za ta yi yawo tsirara sai ta auri Maj Aliyu. * A hankali Aafiyyah ta tura ƙofar ɗakin ganin ba'a bata izinin shiga ba, komai na ɗakin a tsaftace yake gwanin sha'awa da birgewa, duk da baya nan amma sai baza ƙamshi yake ba kowa cikin bedroom ɗin sai ta yi tunanin ko yana cikin bathroom wanka? Ta ɗaga shoulders alamar rashin damuwa ta nufi gaban madubi, tarin turarruka a wajan jere da mayuka. Wani man cire gashi ta gani ta ɗauka tana dubawa sai ta yi murmushi kawai can ta ce "su Maj an girma har wani cire gashi ake yi?" Sai ta yi saurin saka hannunta ta rufe bakinta ta ce "Oh my mouth" ta ce tana lumshe idanunta, ƙoƙarin nemo waje take a zuriyarta inda zata saka Aliyu tare da bashi gurbin miji da kuma matsayi na musamman, sai a yanzu take jin tsananin kewar Alhassan Ashraf a zuciyarta, sai yanzu ta ji cewa tana son Ashraf da gaske ya jure abubuwa da yawa wanda take yi masa tsayin shekaru ya mutu ya bar ta a lokacin da take tsananin buƙatar taimakonsa sai ta fara tunanin ya aka yi Scorpion ya san batun binciken da take yi akan FS word? Tabbas tana buƙatar shiga office gobe. "Allah Ya ji ƙan ka Ashraf my love" Ta ce tana juya tare da sake duba mayukan Maj. Lokaci ɗaya hannunsu ya sauka akan body oil ɗin, nata ne a ƙasa sai hannunsa a sama saboda ta riga shi sauke nata hannun, ya zubawa mitsitsin hannun nata ido, ƙoƙarin cirewa take sai ya haɗa da man da hannun nata ya damƙe, rawa zuciyarta ta fara da kyau saboda wani irin abu da ta ji a jikinta, adadin yadda hannunta ke rawa haka zuciyarta take tana numfashinsa a wuyanta tare da saukar ruwan kansa a wuyan nata still sakin man ta yi da nufin juyawa sai kanta ya daki ƙirjinsa ta buɗe ido, ganinta ya sauka a gashin ƙirjin nasa da suke kwance suna zubar da ruwa ta runtse idanun nata bata san mene ya sa ba, a duk sanda za ta yi wani kusanci da namiji sai ta ji kanta yana sara mata tare da ƙoƙarin tuna makamancin hakan daya faru da ita, shi ya sa ko a baya bata son kusancinta da Ashraf sam. Ta dage tana cewa "Yaya". Ya dinga kallon fuskarta yana son ganin inda kidnappers ɗin sukai mata illa amma babu sai wuyanta da yake zane da shatin yatsun hannu. "Ina yayan yake?" Ya ce yana duƙawa gaba ya rufe ta da ƙirjinsa gabaɗaya a ƙoƙarin ɗaukan wani body spray da yake yi, ƙamshin shower gel ya shiga hancin Aafiyyah ta kasa jurewa saboda hucin zuriyarta da take ji a maƙoshi ta yi saurin riƙe shi tana "zaka yar dani" Abin da zai ɗauka ya ɗakko, ya ɗan matsa zata fita ta ji ya ce "Da kin tsaya kinga na isa cire gashi ko a'a?" Ta zazzare ido ashe ya ji bai kula ta ba, ya fara shiryawa ta ce "Me za'a dafa maka in ji Love" "Waye Love" Maj asked without looking at her yana fesa body spray. "Ummimi" Sai ya ɗago gabaɗaya a lokacin na farko taga ya ɗan saki fuskarsa can ya tsuke fuska ya ce "Tea" Fita ta yi da sauri, babu jimawa ta dawo lokaci yana palronsa sanye da baƙin wando ya saka riga mai buɗewa waya ce a kunnensa gabaɗaya ya tattara nutsuwarsa ga wayar da yake yi, system ɗin gabansa ma Vc yake cikin nutsuwa yana nuna Aafiyyah kusa da shi sai ta yi tsaye, baya son magana mai tsayi sai ya ja hannun ta zuwa armchair ya jinjina kai ya ce "In sha Allah, abar meeting ɗin zuwa 12 na dare ko?" Ya sake yin shiru sai ya juya ya kalli Aafiyyah da take danna wayarta ya ce "Tana lafiya, kamar ba su yi mata komai ba zan bincika" ya ce yana ajjiye wayar sai ya kalli cikin screen ɗin system ɗin tasa, fuskarsa na ɗan faɗaɗa calmly ya ce "how are you Muhammad?" Jin sunan Muhammad ya saka kan Aafiyyah sarawa ya runtse idanunta tana maimaita “Muhammad” a zuciyarta ƙirjinta na bugawa da ƙarfi. Muhammad dage zauna saman kujera mai juyawa hannunsa riƙe da cork kamat kodayaushe armless mai tsadar gaske a jikinsa ya ɗan yi unzipping rigar zuwa ƙasa, dark skin ɗin nan sai ɗaukan idanu take asalin American man har shinny yake yi sai jajayen laɓɓansa. Ya lumshe idanunsa ya buɗe yana kai cork ɗin bakinsa idanunsa akan yatsun macen daya gani a gefen Maj ya cikin Vcall ɗin, ya jinjina kai bai ce komai ba. Maj ya ce "Muhammad ina magana" "Oh! ka ce me?" "Ya kake?" Ya cije lips yana taɓa bandanar dake kansa wacce ya tukare gashinsa da ita sai ya ce "Waye right hand naka?" Maj ya san Muhammad ciki da bai ƙin amsa shi da ya yi alama ce dake nuna yana fushi don haka ya ce "Are you angry with me?" Ya ɗan tsare Maj da manyan idanunsa sai ya ɗaga kafaɗa yana girgiza kai ya ce. "Why should i?" Sai Maj ya jinjina kai, ya dubi Muhammad dake juyi akan kujerar da yake kai can Muhammad ya ce "Is she okay?" Sai Maj ya ce "Who?" "Sophie" "Oh, she is. Ban san plan nasu ba ita da Dig Johar kamar staff ɗinsu ce" "I knw, na je inda suke via the location da na yi tracking" Da sauri Maj ya buɗe idanunsa a tsorace ya ce "Kana nufin ka fita waje? Kana nufin fita ka yi?" Muhammad ya miƙe tsaye tare da laptop ɗin hannunsa zuwa ɗakin computer ya ce "Me kana tsoro? Fita dai na fita Allahu ya tsare gaba, na gaji da zaman nan you lefted ba tare da wani bayani ba, ni kam na gaji" "Muhammad!" Maj ya kira sunansa cikin tsawa, sai yaga idanun Muhammad na yin jaa yana ɗan dafe kansa ya sani sarai Muhammad baya son tsawa ko da wasa balle faɗa, sai ya yi shiru yana ƙarewa Maj Aliyu kallo idanunsa jajur jijiyoyin kansa na harbawa kamar ya fasa laptop ɗin haka Maj Aliyu yake hango abin a cikin idanun Muhammad. Sai Muhammad ya cije lips kawai yana taɓa zanen tattoo ɗin dage gefen wuyansa. "Muhammad say sorry" "Why? Laifin me na yi?" Da ƙarfi Maj Aliyu ya ce "say sorry ina saka maka bindiga aka tunda baka jin magana kasan hatsarin fita daga cikin gidan nan yake? Kasan hatsarin dake tattare da fitarka waje cikin mutane yake? Muhammad are you mad? Are you crazy wallahi billahi sai na cillaka cikin gadirom a rufe mini kai sai sanda na yi niyya" Glasses ɗin hannunsa da yake tsiyaya win a ciki ya damƙe sai har daya fasa hannunsa na ɗigar da jini zuciyar sojoji ta motsa shima Muhammad zuciyar tasa a kusa take yama mance da batun waye Maj Aliyu, Aafiyyah dai na jin su ita kanta bata fahimta muryar Muhammad ke mata amsa kuwwa cikin kunne tana hargitsa mata tunaninta zuriyarta na bugawa ƙafafuwanta na yin tabbas ta san muryar haka take ji nan da nan kanta ya fara ciwo ɗakin na juya mata. Muhammad dake cikin system ya ce "Good, tashin hankalin nake so na ji reason na ɓoye ni da ka yi, I'm tired" Ya ce yana nufar waje cikin sauri Maj ya ce "Bad boy" Sai Muhammad ya yi shiru yana sauke ajjiyar zuciya kafin ya ce "Ok, i am sorry..... I am sorry Yaya" "Shikenan" "But you lefted me why?" Cewar Muhammad ɗin yana sake ɗaukan wata win idanunsa jajur. "Zan maka bayani, na faɗa maka an yi kidnapped matata i will come" Sai yaga Muhammad ya yi murmushi ya ce "Liar..... Ta kai kanta ko akai kidnapped nata? Me ya sa take yi kamar tafi kowa iya wayo ne? Har fa cewa ta yi wai bata da aure" "Wa?" Maj ya tambaya da mamaki, Aafiyyah bata nutsuwarta amma hakan bai hana fahimta da ta yi cewa Maj na mutuwar ƙaunar wannan Muhammad ɗin ba, sai kuma ta fara jin tsoro domin banda ita da Scorpion ɗin ai babu wanda ya san cewa ta faɗawa Mutallab bata da aure ba, ba wanda ya san wannan maganar Who's Muhammad? Shima Muhammad ɗaga kafaɗa ya yi ya ce "Matarka, a san cewa zaka gano inda take shine aka rufe ka a can Kaduna ne or Abuja?" "Ina ka san duka wannan?" Muhammad ya ce "Yaya, don't ask" "Ok" sai Maj ya juya ya kamo hannun Aafiyyah kai tsaye ya yi mata masauki a cinyarsa, sai tsigar jikinta ya mimmiƙe yana zubewa wani abu mai kama da feelings na sauka a jikinta a kuma masarrafar dake sadar da wanzuwar faruwar wani abu a jikin mutum, ƙoƙarin tashi take sai ta ji Maj Aliyu ya zaga hannunsa ta cikinta kansa a kafaɗar ta muryarsa a hankali daidai kunnenta ya ce "Safii my wife, ƴar leƙen asiri" Kasa magana ta yi jin Maj na magana a tausashe can ya ce "cikin nan kamar ya taɓa ajjiye baby ko?" Da sauri ta juya ta kalli Maj cikin rashin fahimta ya ɗage mata girarsa ya ce "akwai motherhood a tattare dake Mahmah" can ya ce "Muhammad wannan ce wacce kake faɗa ka gani?" Ya faɗa yana saka hannunsa a fuskar Aafiyyah tare da juya duka fuskar tata a screen system nasa wani irin bugawa ƙirin Aafiyyah ya yi shima ɗin Muhammad tsaye ya miƙe lokacin da sexcy eyes ɗinsa ya shiga cikin lulu eyes ɗin Aafiyyah a tare kuma suka nuna juna ta cikin Vcall ɗin. Idan an yi comments a conversation group maybe na fanshe muku na jibi na yi posting gobe 💥MUTALLAB B2: chapter 2: Who am i seeing Kallon juna suka yi na wani lokaci, Muhammad cikin idanunta ya dinga kallo kamar kallo na tuhuma ko zargi, sai ta ji kaifin idanunsa na tsinkar mata da zuciya, haka kawai take jin akwai wanda ya taɓa yi mata irin wannan kallon, duk ƙoƙarinta na son tunawa ta kasa, zuciyarta na sake ƙarfafarta wajan kallon sake ci-gaba da kallonsa wanda take jin wani abu mai kama da nutsuwa na sauka a ƙirjinta yana ratsa zuciyarta. Shi ɗin ma ita yake kallo musamman cikinta kafin ya ɗan sake buɗe idanunsa tar saman fuskarta yana cije lips ɗinsa. "Muhammad" Maj ya kira sunan muryarsa a buɗe kuma a kausashe yana mai ɗan buɗe idanunsa akan screen ɗin system ɗin. Muhammad ya yi shiru, sai idanunsa daya janye cikin nutsuwa yana yin baya tare da daidaita zamansa a kan kujerar daya nema ya zauna, ya ɗan kwanta kaɗan jin ɗakin na juya masa ƙirjinsa na buɗewa zuciyar dake ƙirjin na tsukewa tana ƙuntata bugun da ƙirjisa ke masa sai ya lumshe idanunsa tare da yin shiru bayan ɗan kallon daya jefawa AA MAJ ɗin. "Ka san ta? Ita ce wacce kake magana akan ta ko? Kana da tabbacin hakan?" Maj ya tambaya yana kallon tea ɗin dage gefe wanda ya ɗan fara yin daidai da shan shi. Madadin Muhammad ya bada amsa, sai ya ɗaga kafaɗa kawai yana danna wayar hannunsa ba tare da ya ce komai ba, dukda cewa akwai tarin kalamai cikin bakinsa sai dai baya jin za su yi aiki a yanzu bashi da tabbaci da ƙwarin zuciyar sanin hakan. "are you deaf?" Maj ya sake magana. Silently Muhammad ya ce "Ask your wife idan ta san Muhammad, tambaya matarka mana idan ta sanni" cewarsa yana sake cilla idanunsa akan Aafiyyah itama ɗin haryanzu shi take kallo musamman zanen tattoo ɗin dage wuyansa. "Kin san shi?" Juya idanunta Maamah ta yi, tana ɗaga kafaɗa itama kamar ba za ta yi magana ba sai ta ce "Gashi ina ganinsa yanzu?" Maj ya ce "Kafin yanzu ɗin" ta sake ɗaga shoulders ta ce "A'a, his voice seems familiar to me" ta ce tana sake yin shiru. Muhammad ya yi murmushin da bai taɓa yi ba, yana ci-gaba da speeding cork ɗinsa daya sake tsiyayawa cikin glasses cup ɗin ya ce "Uhm" Maj ya ce "amma ka ce ka taɓa ganinta da ci....," cikin sauri Muhammad ya buɗe idanunsa sai ya girgiza kai kawai yana ɗaga hannunsa ɗaya ya zura cikin sumar kansa ya ce "No no no please" yana faɗin hakan ya kashe Vcall ɗin. Maj ɗin ma shiru ya yi yana zubawa system ɗin idanu, a iya saninsa bai taɓa ganin murmushin Muhammad har haka ba, ko faɗa yake masa sai dai ya kafe shi da idanu har ya yi ya gama ko tari ba zai yi ba, da yawan lokaci idan ya ce "Muhammad magana nake fa?" Sai yaga Muhammad ɗin ya cije lips ya ce "kace me?" "Faɗa nake maka" a wannan lokacin Muhammad ya kan ɗaga kafaɗarsa ya ce "Bafa komai ke damun Muhammad ba". A hankali Maj ya jingina bayansa da jikin kujerar yana miƙar da ƙafafuwansa saman table ɗin gabansa, a hankali ya ɗauki tea ɗin ya fara speeding nasa a nutse a kuma kame, bawai alamun haihuwa ya gani a tattare da cikin Aafiyyah ba, ya faɗi hakanne saboda yaga reaction nata da yadda za ta yi acting idan ta ji furucin haihuwar, babu alamun haihuwa tattare da Maamah a duk sanda yake tunani ko yake rufe idanunsa murmushin Amsh ke cikin idanunsa tare da hasken farar fatar jikinsa irin hasken nan na Maamah na zabiya hattta idanunsu ɗaya ne da yatsun hannun da kuma yanayin sumar kan. Har ya kwashe kwanaki cikin gadirom na sojoji tunanin Aafiyyah ne a zuciyarsa su waye suka ɗauke ta amma ya san tabbas M. General zai dage wajan bincika masa abin da yake faruwa da kuma inda Aafiyyah take, tsoro da mamaki ne kuma ya cika shi ganin an rufe shi ba tare da wani dalili ba wannan cin mutumcin har rauni ya yi masa a zuciya. A ɓoye kuma Major General ya kira can hedkwata ta Abuja aka haɗa shi da Major Maj wata Maj Aliyu ya shaida masa cewa tabbas an yi kidnapped Aafiyyah amma binciken sirri da suka gudanar a ɓoye ya nuna ɗauke Aafiyyah set up ne na hukumar FCID kuma staff ɗinsu ce kuma tana bincike akan Scorpion ne. Jin sunan Scorpion ya saka AA MAJ yin murmushi kawai tare da kashe wayar. A hankali ya juyo ya kalli Aafiyyah har ya yi shiru zai miƙe sai kuma ya ja numfashi ya ce "Wa kikai arrested?" "Scorpion" ta bashi amsa. "Kin tabbata shine?" "Why are you question me?" Ya miƙe tsaye hannunsa riƙe da cup ɗin tea ɗin, ita ɗin ma miƙewa ta yi tana ƙoƙarin juyawa ta ji ya ce "Ki yi a hankali dai Safii" "Me ya sa? Ni fa jami'a ce ta Fid ina da bindiga tattare dani me zan ji tsoro? Babu abin da zai firgita Safiyyerh Dig Abdul-Johar Marafa" Ya jinjina kai kawai yana miƙa mata raguwar tea ɗin hannunsa tare da ɗauke idanunsa zuwa ga agogon hannunsa yana duba lokaci cikin kamewa ya ce "ke nan za ki iya arresting mijinki?" Ta juya idanunta tare da yin farfari da idanunta sai ya dubi idanun da bakin nata ya ɗan ja idanunsa ya lumshe lokacin daya kalli mitsitsin bakin nata wani abu ya gitta a zuciyarsa alamun buƙatarsa zuwa ga matarsa, idan ba mancewa ya yi ba ya jima da bawa 30yrs baya he need his wife by his side. Ta ce "sai dai idan Maj bai shiga komar Fid ba, aikin mu ba sani ba sabo hatta shi Dig Abdul-Johar ɗin da kansa Safiyyerh can arrest him" Ta ce tana ficewa daga cikin ɗakin a nutse ta je bakin ƙofar ta juyo suka haɗa ido kafin kuma ta ɗauke idanunta ta ji an buɗe ƙofar, idanunta ya sauka akan Waheeda dake tsaye bakin ƙofar sai kuma Zahiderh dake taunar cimgam. "Bamu waje malama" cewar Waheeda har tana ƙoƙarin bangaje Aafiyyah ta shige, ita Aafiyyah dariya ma Waheeda take mata har yanzu ta lura bata gama sanin halinta ba, sai ta matsa ta bata waje har ta yi ƙoƙarin tsayawa sai kuma ta fita ganin bata da wani issues da abinda ya kawo su nan ɗin musamman Zahiderh. Bayan ta fita Maj ya kalle su sau ɗaya sai kuma ya yi poiting Waheeda ya ce "Out... Out of my room" "Uncle A gaishe....." "Dalla can fitar mini a ɗaki" "Uncle A please ka bani dama ka ji me zan ce maka akan Zahiderh" bata san ya ƙarasu wajanta ba sai da ta ji saukar wasu jerarrun maruka a fuskarta ya yi mata ɓarin mahaukaciya, nan take bakinta ya fashe ya fara jini, cikin sauri Zahiderh ta juya a gigice wani fitsari na neman ƙwace mata a wando a gigice itama Waheeda ta yi waje tana fasa kuka tare da rufe hancinta suna fita ya rufe ƙofarsa ya shige cikin bedroom a gurguje ya shirya cikin uniform ɗinsa ya fito a cikkaken soja M MAJ ALIYU MARAFA. Bindigo wajan uku ne a ƙugunsa cikin sauri ta a fito yana jin Anty Turai na kiransa a kiɗime tare da riƙe Waheeda amma ya share ta, ta saki Waheeda ta biyo bayansa yana fita compound ita kuma tana entrance "Aliyu ni nake magana kake iska dani? Ta faɗa tana nufarsa a haukace a zuriyarta tana tsinewa Aafiyyah. "Ka ɗaukar mini cikin Waheeda ne balle kuma ka tayani naƙudarta da zaka saka hannu ka yi mata wannan marin? Wallahi i can't take it" Tafi ya yi yana poiting Anty Turai tare da yin wani yare na sojoji, wasu manyan sojoji ne riƙe da bindiga sukai kan Anty Turai suna bubbuɗe mata manyan idanunsu wani murɗawa cikinta ya yi ganin tana yin wani motsi za su iya harbinta. Sai kawai ta yi ƙwafa ta juya tana kiran sunan Zahiyerh wato Ummimi. AA MAJ da sauri ya nufi ɓakar motar dake kunne tana jiransa, cikin sauri Lance Corporal Leo da kuma Sergeant Arma Sergeant Timo suka sarawa Maj tare da buɗe masa murfin ƙofa ya shiga, wasu motocin suka shiga daban suka marawa motar Maj baya sauran sojojin suka tsattsaya bakin gate da cikin gidan suna zagayewa.. * Yana durƙushe baya iya ko motsi saboda tsananin ɗaurin da aka yi masa, daga shi sai gajeren wando jikinsa duka shatin duka farcensa na zubar da jini saboda cire masa su da aka yi, kamar wancan karon tunda aka kawo shi ko tari bai yi ba, balle ya basu haɗin kai wajan sake tabbatar musu da cewa shine Scorpion ɗin da suke nema. Baya bawa zuciyarsa damar tunani shi dai ya san ko zai dauwama a nan dole na cika wasiyyar Zinariyarsa tabbas, ya kuma rasa sai yaushe ne abubuwa zasu zama daidai a rayuwarsa? Ya rasa Muneeberh, ya rasa Diyna da Jaaanah, ya sake rasa uncle Ade ya sake rasa Anty Hameeda. Shin annobar daga wajansa ne ko yaya? Duk sanda aka samu mutuwar wani shine yake zama suspect wajan mutane da jami'ai, a rikice yake shine Scorpion bashi da wani shaidar kare kansa, zanen ƙirjinsa ma kaɗai ya wanzar da amsar da suke buƙata for a year. A sanda ya ɗakko Goje suka hau napep zuwa FS WORLD ya ganta, ya kalle ta a lokacin da take ɗaukar photonsa, a lokacin shocked ɗin ganin nata ya saka bai ɗauki ɗaukan da ta yi masa serious abu ba, rashin tabbacin ganinta a Nigeria gabaɗaya bama Kano ba ya saka ya yi shiru a lokacin, duk da maganar da Goje ke yi masa, bai ɗauka zai yi saurin ganinta bayan fitowarsa ba. She changed, ta sauya completely kamar yadda rayuwarta ya sauya, a lokacin kuma sai ya ji ɗaukan da ta yi masa yana da alaƙa da soyayyar da take masa kamar yadda ya samu labari kuma ya fahimta ɗin, ya ɗauka zata yi masa magana a lokacin sai yaga akasin hakan bayan ta ɗauke shi photon ta juya cikin companyn tana waya tare da ɗagawa security hannu. A sanda Eng Ali wali ya kira shi akan batun sace Aafiyyah bai yi niyya ba, sai kuma ya ji tsoron su bawa wani aiki a yi mata wani abu, wannan dalilin ya saka ya amsa amma har lokacin mamakin rayuwa da sauyin da Aafiyyah ta samu yake yi, mene ya faruwa bayan ya barta cikin ɗaki a can Lagos? A sanda ya sake nutsa idanuna cikin nata sanda ya je Companyn a zaune da yake saman katanga ji ya yi zuciyarsa ta sake tsinkewa, bai san yaushe ya caka mata wuƙa ba ya rasa tunaninsa a lokacin da ya ji furucin tana da aure har take iƙirarin soja ne mijinta, babban abin da ya sake hauhawar zafin zuciyarsa yadda ta nuna bata san wata halitta wai shi MUTALLAB ba, balle ta yi masa uzuri, irin uzurin da soyayya ke samarwa, ya caka mata wuƙa a inda ya caka mata a Lagos, yana da tabbacin kuma ba zata mutu ba, a tiger most be a tiger always Damisa bata zuwa ƙasa kamar yadda dafin kunama kan iya razana tunani da gigita nutsuwarsa nan take. Buɗe ƙofar ake ƙoƙarin yi yayi saurin dunƙule takaddar hannunsa tare da cilla wani abu a ƙasan harshensa, ya san dole za su iya amsar takaddar sai ya nannaɗe ta tas ya cusa cikin boxer ɗinsa daya kama ƙugunsa sosai. CI Chief Inspector of police tare da ASP Assistant Superintendent of police under FCID ranks na matakin Junior ranks ne suka shigo sai kuma Deputy Director Civil a Civilian ranks, a yadda suka barshi a haka suka same shi a hankali suka dinga kallonsa sai CI ya ce "Na jima banga tantirin yaro irin wannan ba, wallahi da muke neman Scorpion ido rufe ban ɗauka zan ga wannan matsayin Scorpion ba sam" sai ASP ya ce "Shima ɗin abin tsoro ne, ka duba ƙirar da Ubangiji ya yi masa, idanunsa abin tsoro haka jikinsa ka sake kallon zanen ƙirjinsa na bani da shakku akan cewa bamu ɗana tarkwanmu akan daidai ba, he is the one shine dai Scorpion" CI ya jinjina kai ya ce "Sure, bai kamata mu ja lokaci ba domin cikin abu biyu za'ayi ɗaya kamar yadda Dig Abdul-Johar ya sanar damu, ko dai mu kashe shi ko kuma a yi masa allurar hauka ya zama bashi da amfani". Director ya ce "I agree with you guys, ku duba mini takaddar wajansa muna buƙatar ganin abin da yake rufe mana" kafin su ƙarasa wajansa MOH ya yi namijin ƙoƙarin miƙewa tsaye akan ƙafafuwansa da basa iya ɗaukan gangar jikinsa sai su kaga kaf ya kare su a tsayi da girma da faɗi a hankali kuma ya dinga binsu da kallo. "Where is the paper?" Ya yi shiru. "Ku bincike shi" Jikinsa suka fara dubawa babu komai cikin sauri CI ya kama wandon Moh yana zamewa ƙasa ya ji saukar fitsari a fuskarsa, hakan ya saka da sauri ya yi baya tare kakarin aman saboda saukar fitsarin cikin bakinsa, da sauri Moh ya ja wandon sama ganin ya yi nasarar rufe takardar hakan ya saka rukunin suka kira masu bada huro suka junawa Moh shocking nan da nan suka gigita shi, suka ƙarasa cire masa farcen hannunsa zafi da raɗaɗi da azabar da yake ciki ya saka ya fara fasa kansa da dukkan ƙarfinsa, motsin rashin lafiyar ƙwaƙwalwarsa ya tashi a lokacin a cikin idanunsa Deer kawai yake iya hango, da murmushinta da take yi sometimes idan ranta ya ɓaci, sai ya ji wannan haƙurin nata ba zai tafi a banza ba, ya daddage ya kurma ihun daya saka jami'an suka bar ɗakin tare da barinsa yashe jini yana zuba, ya dinga huci kansa na zubar da jini. Sunansa ya ji ana kira, ya kasa buɗe idanu amma a muryar ya san cewa Abbasa ce yana mamakin ya aka yi ta shigo har nan? "Za su iya kashe ka idar baka bar nan ba, kana da dama da ikon fita ga layarka nan" Ya buɗe idanunsa jajur yana gani dishi dishi Abbasa ta ce "Ba lokaci, na zo na faɗa maka ma'anar A.M.A ne amma sai sanda ka bar wajan nan" "I can't...," ya furta silently kuma a wahale. Ta ce "Za ka iya fa, domin Ubangiji bai halicci ruhinka domin su ba, domin su kashe ka ba, mutuwarka ba'a hannunsu take ba kar ka basu damar haka" Ya buɗe rinannun idanunsa yana jin ƙirjinsa na masa nauyi burinsa a yi masa allura ko kuma a bashi ƙwaya ya sha ko zai daina jin zafin da yake ji a zuciyarsa, ji yake kamar ya kashe kansa ya bi matarsa lahira su yi rayuwar su a can. "Ki bani abin da kike bani" ta girgiza kai ta ce. "Za su tuhumeka ina ka samu abin maye ka danna layar nan ka bar cikin gurin nan". Ya yi shiru kawai yana rufe idanunsa wata gigitacciyar tsawa Abbasa ta yi wa Moh wajan ya amsa sautin muryarta, da sauri kuma ta buga sandan hannunta ta rufe su cikin yana ita da Moh yadda babu wanda zai iya shigowa cikin ɗakin, hayaƙi ne ya fara fita daga cikin bakinta da idanunta, harshenta kamar ya faɗo sama ta ce "Ka san adadin yadda suka cutar da rayuwarka tun kafin kazo duniya? Ba iya ita kaɗai take buƙatarka ba, mutane da yawa suna buƙatar kasancewarka a duniya, daga cikin har mahafinka Moddibo, an fi cutar da rayuwarsa fiye da kai" "Moddibo?" Moh speak very loudly. "Ina nufin Abdullahi" Ya girgiza kai ya ce "Ba ki da gaskiya Abbasa, da gaske ba ki gaskiya" A ransa ya ji ba mistake ta yi ba wajan ambaton Aby da Moddibo. Ta ce "Tashi, ba zaka cimma komai ba kana nan wajan ba zaka cimma komai ba, akwai wata rayuwar albarkatacciya wacce ke jiranka ba'a nan ba, wacce kake hauka dominta ba zaka same ta a nan ba" A hankali ya miƙe zaune da ƙyar ya zubawa Abbasa idanu da gaske bata da gaskiya anya ita ɗin mutum ce? Tabbas kuma da Aljanna ce ita kallo ɗaya zai yi mata ya gane hakan. A hankali ta sauke ajjiyar zuciya tare da juya sandan hannunta sai gashi ya zama kujera ta zauna ta hakimce ta ce "Mutuwar Diyna da Jaaanah abin da ka shuka ne ka girbe tabbas kai ne ka kashe su, zafin zuciya ya saka ka faɗawa Hameeda cewa Safiyyerh ta cancanci mutuwa, saboda ba zaka iya zama ka yi mata bayani ba. Ka kashe Diyna da Jaaanah da hannunka tabbas ba tare daka sani ba kuma dole hakan zai faru domin mutuwarsa tana rataye da ƙaddararka ne. Amma mutuwar Safiyyerh manufa ce, auren Aafiyyah shine zai buɗe babin komai da kawo ƙarshen komai, domin aurenta lashakka sai ka fita daga cikin gidan nan MUTALLAB. Kai inuwar da mutane da dama suke jiran shan iska daga cikinta ne, abin da zan furta maka kafin kashe Zinariya sai da aka yi mata fyaɗe idan na ce ta mutu da cikin tagwaye a cikinta kar ka ji mamaki, ban kuma faɗa maka tabbacin cikin ba. Safiyyerh ƙaddararka ce Safiyyerh kuskure wani da zunubin wani ne" ta jinjina kai ta ce "Kafin samun FS WORLD da Aafiyyah dole acikin mutane huɗu wani zai mutu, ko a rasa ita kanta Aafiyyah, ko a rasa mahaifiyarka Ammo ko dai a rasa Aliyu mijin Aafiyyah ko a rasa.....," ta yi shiru. "Wa?" Ya tambaya. "Lokaci zai bayyana na ƙarshen" "Bata da aure, liar....," "Injiwa waye? Tana da aure mijinta ne kuma sojan da take magana akai, shima ƙaddararsa na jingine data Aafiyyah ne. Ka tashi mu tafi" Wani irin soya da raɗaɗi yake ji, numfashinsa ya tsaya cak wani irin tashin hankali da bai taɓa shiga cikinsa ba ya ruski Moh ya ji duniya na neman yi masa atishawar tsaki, fyaɗen da Abbasa ta faɗa ya saka ya daddage ya kurma ihu iya ƙarfinsa bai san tafiyar Abbasa ba sai ganinsu ya yi a kansa. Dig Johar ya kalli Moh kana ya juya ya fita waje da sauri ya ce "We can't kill him, sai mun fara gwada ƙwaƙwalwarsa idan mun tabbatar yana da taɓin hankali kamar yadda shekarun baya aka shaida mini ba zamu iya kashe shi ba, saboda doka bata aiki akan mahaukaci maybe mu sake yi masa allurar da zata ƙarasa haukata shi gabaɗaya yadda ba zai iya aikata komai ba" wani ya ce "Sir. Duk kisan da yake yi yana sane fa, kamar ɗaukan fansa ne yake yi mu fara bincikar dalilin kisan ina tunanin shine muka fi buƙata kawai" "Good Idea". Bayan fitar su ya zaro takaddar a lokacin da babu adadi da yake ganin kamar rubutun yanzu yake karanta shi, duk ta yage ya zubawa rubutun ido ya fara karantawa kamar haka; "Ban san yaushe ne wannan saƙon zai ruski ga ruhin Safiyyerh ba, mijin Safiyyerh. Ina son shaida maka a lokacin da nake rubutun nan babu zafi ko haushinka a zuciyar matarka bestie, ina maka rubutun nan ne a lokacin da nake jin ƙarar bugun ƙofar gidan daka tanatar mini domin bani farinciki mara iyaka, ban san suwaye ba na san dai ba mutanen arziƙi bane. Ina son ka yafe mini akan hakƙin zuciyarki dana ɗauka da kai da Aafiyyah na zaɓi daidai wannan lokacinne wajan faɗa maka gaskiya domin bani da tabbacin zaka so ka ruski ruhi a jikina ba iya gangar jikina ba. Ubangiji yana da ikonsa akan kowanne bawa kullum ina addu'ar Allah Ya zaɓa mini abin da yafi zama alheri a gare ni da rayuwata. Bestie ka yi mini afuwa ka roƙa mini yafiyar Aafiyyah a yadda Aafiyyah ke so na da ƙaunata bai kamata na rama sakayyar nan ta wannan hanyar ba. Wannan wasiƙun dana maka bani ce mamallakiyasu ba, Aafiyyah used my handwritten ta iya rubutuna tun ba yanzu ba, she is smart a kodayaushe. Wasiƙun soyayyar nan da kake karantawa kake jin daɗinsu Aafiyyah ce ta rubuta su, ba iya a takadda ta rubuta ba hakan a rubuce yake a cikin zuciyar dake rayuwa a ƙirjinta. Aafiyyah loves you so much, duk ciwon da take yi saboda kai ne, ta ɓoye maka saboda alƙawarin da ta yi wa mahafinta na cewa sai ta kammala karatu zai aura maka ita, ƴaƴanta J ya san komai. Wallahi wallahi ni da kaina na san na raunata zuciyar Aafiyyah raunin da har abada ba zai goge ba ko warkewa amma kana iya zama maganinsa, Aafiyyah ta zo gidanmu ranar da zata bar ƙasar nan bata da lafiya ta buƙaci na rakata wajanka na ce ban san gidanku ba, bani da numberka, ina hango tashin hankali da sarewa a cikin idanunta kuma tunda ta karya wannan alƙawarin na Paaahhh tazo ta gaya maka na san cewa ya gama fidda rai da rayuwa, ta amince mu yi rayuwar aure tare ka aure mu amma tsananin son zuciya da kishi irin nawa na ce ban amince ba, na amshi wasiƙun da niyyar zan baka nace injita na ji ba zan iya ba ban sani ba ko kasan Aafiyyah na mutuwa kullum tana farfaɗuwa da soyayyarka, na ji tabbas zaka iya neman Aafiyyah na duba wahalar dana sha hakan ya saka na ce maka nina rubuta wannan dalilin ka yi accepted soyayyar da nake maka. Idan Ubangiji ya bani ikon ci-gaba da rayuwa zan tayaka neman Aafiyyah a duk duniyar da take idan har tana raye, idan wannan shine rubutuna na ƙarshe da ranata ta ƙarshe ka ɗauki maganata matsayin WASIYYA. Na yafe maka komai a rayuwa amma ba zan taɓa yafe maka ba idan Aafiyyah ta yi rayuwa da wani ba kai mijina MUTALLAB ba, Aafiyyah tana yi maka soyayyar da bana yi maka ita. Allah bestie ba zan yafe maka ba, Allah ba zan yafe maka Allah ba zan yafe maka, zan ta gigitaka da fatalwata har san ka cika mini WASIYYATA. Duk abin da same ni a wannan daren kar ka yafe kamar yadda ba zan yafe ba, kar ka sare kar gwarzo ne a koyaushe ka iya yinka wajan ganin ka ɗaukar mini fansar abinda ya saman, ka iya yinka wajan ganin ka cika mini WASIYYATA ka san wasiyya ga mamaci rashin cikata azaba ne ga ruhinsa. Oh see har na ji gabanka ya faɗi ni bance zan mutu ba, amma ina jin ƙamshin furanni ina jin kamar ina da gidan da yafi duniyar nan daɗi yana can yana jirana, idan na rigaka zuwa wannan gidan zan kasance cikin kewar ɗan baƙin mijina. KA AURI AAFIYYAH KA AURI AAFIYYAH KA AURI AAFIYYAH idan ka cutar da ita ko ka bari aka cuceta Allah bestie kamar ganin ina maka kawaici this time ba zan yafe ba. I want to see goodbye maybe forever and ever sai a mafarki kuma. I love you so much karka manta ni don Allah kar ka manta Barewata ina son dai ka kula da wannan Damisar. And bestie ka san me? Ina da albashir da zan maka amma tukwaicina duk sanda ka haɗu da Aafiyyah ka ɗauke ta ka goyata ka bata kulawar dana rasa, ban ce na raina wacce ka ban ba, ina son ko a mafarki ka bani labarin yadda ka cirewa Aafiyyah lizards a wannan ranar zan tafi da kwaɗayin jin labarin nan. Albishir ɗin shine Ummeyh ta yi mini gwaji...... Subuhanallahi bestie sun ɓalle ƙofar sun shigo bye Safiyyerh love you!" Iya ƙarshen rubutun wasiƙar kenan, Moh ko a mafarki bai taɓa tunanin Aafiyyah na son shi ba, ganin babu jituwa a tattare dasu bata ma da kunya bayan hakan kimiyya ke son ta. Shiru ya yi idanunsa na kallon sama yana jin duniyar na fita daga ransa gabaɗaya. * Bacci Aafiyyah take yi amma muryar Muhammad na yi mata amsa kuwwa a cikin kunnenta a gigice ta farka tana addu'a ta buɗe idanunsa cikin makami ta ce "Kimiyya's voice" "And who's Kimiyya?" Ta sake tambaya sai kawai ta juya ta cigaba da baccin gajiya tana mannewa a jikin Ummimi lokacin wajan ƙarfe 2 da wani abu na dare. Sai biyu AA MAJ na buɗe ƙofar ɗakin Ummimi yana shiga sai ya yi tsaye yana kallon fuskar Maamah data Ummimi nutsuwa na ƙara saukar masa, wannan karan ma tsaye ya yi daman bai wani jima da shigowa gidan ba bacci yake ji haka kawai kuma yanzu daya samu nutsuwa bashi da damuwar komai sai ta son jin kai wacece matarsa da Dr Hash yake bashi raddi a kansa? Rashin damuwar ya saka dukkan wasu tsofaffin feelings suke farfaɗuwa tare da yara kansu a ƙirjin AA MAJ yana jin wani irin tsananin buƙatar Maamah a gefensa yana sun jin wannan kusancin da suka rasa a baya shi da ita yana buƙatarsa a yanzu, yana jin buƙatar miji zuwa ga matarsa yana son ya ji ya zama cikakken namiji mai shirin tara zuri'a da Maamah ya ji duniyar ma'auratan da ko a mafarki bai taɓa hango kansa ciki ba. Yana son dasawa Maamah so da ƙaunarsa da sabo da shi a zuciyarta amma tayaya? Ya san cewa aurensu babu haramci tunda dai Paaahh ya san me yake yi wa, ya kuma yi alƙawarin ba zai taɓa tambayar Paaahh waye ba jininsa ba tsakanin shi da Aafiyyah. Idan AA MAJ ya ce baya jin motsin Maamah a zuciyarsa ya yi ƙarya, wannan motsin da shi zai koma ga mahaliccinsa, motsin ya fara tun ranar da idanunsa ya sauka akan Aafiyyah tana zanin haihuwa matsayin ƙanwarsa, akwai wani abu mai kama da ƙauna dake wanzuwa a jikin AA MAJ ƙaunar Aafiyyah, zafi da raɗaɗin da yake ji da ƙaunarta ya saka yake nisanta kanshi da ita, ya saka yake mata mugunta da nuna mata tsana wai duk a dalilin abin da yake ji a zuciyarsa game da ita ko zai ji sauƙi. A duk sanda Aafiyyah bata da lafiya a zuciyarsa yake jin hakan, ko a faɗa masa ko ba'a faɗa masa ba, ko kuka take sai ya ji a jikinsa yana dawowa gida ne kuma saboda ita, ita kawai bai san meke damunsa ba amma ya ji zan iya kashe kowa domin ta, wanda ya yi yunƙurin aurenta tun bai san cewa aure ya halatta akansu ba, gwara ta dauwama babu aure. Wani abu mai kama da zalunci da tauye rayuwar Maamah wannan dalilin ya saka ya sauka ana saura kwana ɗaya aurenta da Ashraf. Ya durƙusa daidai kanta ya dubi yadda ta marairace fuska, duk da zabiya ce ita amma kyan da Ubangiji ya yi wa Safiyyerh Dig Abdul-Johar Marafa daban ne Ubangiji ya yi ikonsa na tsarin halitta a fuskarta. "Aliyu's wife" Ya ce a ƙasan zuciyarsa yana kama hannunta dana Ummimi ya riƙe cikin nasa, ya dinga bin lips ɗinta da kallo da suke pech gwanin sha'awa a hankali ya sumbaci goshinta bai san ta yadda zai fara shirin rayuwar aure da ita ba kawai dai yana buƙatar matarsa. "Aliyu's dream wife" ya ce yana sake yi wa French kisses sanyin laɓɓansa ya saka ya tura bakinta tana sauke ajjiyar zuciya. Hannunsa ya saka ya tura ta cikin gadon ta zama tana tsakiya Ummimi na gefe, sai ya kwanta a gefe ya ja musu duvet su duka ukan cikin bacci Aafiyyah ta shige cikin jikin AA MAJ ta ɗora kanta a ƙirjinsa ya saka hannunsa ɗaya ya rungometa ya zubawa fuskarsa ido da kyau sai ya sake shigar da ita jikinsa da kyau yana yi mata halak hug. Ummimi ta farka daga bacci mamakin ganin Gadanga ya cikata, idanunta ya cika da hawaye ta ɗora hannunta a saman na AA MAJ da Maamah ta dinga yi musu addu'a daga ƙarshe ta ja musu bargo ta rungume su duka. Kafin su farka daga bacci tuni ya sulale ya bar bedroom ɗin ya nufi haɗaɗɗan part ɗinsa a lokacin ya gama yin magana da masu gyara masa gidansa. Cikin sauri Aafiyyah ta gama shirinta na zuwa aiki brown colour ɗin Abaya ce a jikinta wacce ta gama gajiya da haɗuwa, hannunta riƙe da L G handbag ta manna shade glasses ɗinta ƙafarta cikin flat shoe mai kyau baƙi, rolling ta yi sai baza ƙamshi take yi she looks so beautiful and classy ganin Aafiyyah dole ya girgiza zuriyar mutane ga tarin kwarjini. A hankali take sakkowa hannunta riƙe da bag ɗinta tare da key ɗin motarta, lokacin suka Marafa's family na zaune saman dining area domin yin breakfast,ita ce kawai da Maj babu a wajan kamar kuma haɗin baki tana sakkowa yana fitowa shima jikinsa sanye da uniform wannan karan ba p.cap saman kan shi, J da Dr Hashim da Awais da Waheeda data kwana a gidan suka miƙe da sauri tare da haɗa baki wajan faɗin "Good morning Maj" Waheeda kuma ta ce Uncle. Bai kalli kowa ba sai kujera daya nema ya zauna wacce ke kusa da Ummimi, itama ɗin Aafiyyah kujerar kusa da Maj Aliyu ta nema ta zauna saboda ita ta yi saura. Aliyu ya gaida Ummi da Paaahhh tuni don haka ya ja ya tsaya sai kuma ya ja tea ɗin da Ummimi ke sha ya ɗauka ya kai nasa bakin. "Yaa J Dr Hash namu na gargajiya Yaa Awais good morning" "Morning Manager, ya kike?" Cewar Dr Hash yana zuba mata ido. "How are favourite?" J ya furta "Kai kace Manager kai ka ce Favourite ni me zance ƴar leƙen asiri?" Cewar Awais. Aafiyyah dai bata sake cewa komai ba sai wayarta da take danna, a hankali kuma ta ce "Morning Maj" Bai kulata ba tea ɗin kawai yake sha, sai ya juya kamar zai tashi daidai kunnen Ummimi ya ce "Barka da safiya Love" kai kawai ta girgiza masa. Paaahh ya ce "Maamah karyawa za ki yi ko waya za ki danna?" Sai ta buɗe ido ta ce "No zan ƙarya a Company" ta miƙe kafin ta fita tuni AA MAJ ya ragata fita ta ce "Bye Ummi, Paaahh, brothers" Ummimi ta sumbata a kumatu ta ce "Bye love i miss you" ta fita J ya bita da idanu shima ɗin ta shi ya yi ya bar wajan, Paaahh da Dr Hash suka kalli juna. Aafiyyah na fita daidai corridor ta ji an ɗora mata bindiga aka, sai ta yi tsaye can kuma ta ƙame tare da sarawa irin salute ɗin nan. Ta juya ta kalli AA MAJ shima kallon nata ya yi yana zame bindigar tare da mayarwa cikin ƙugunsa. "Zani aiki" ta ce a hankali Ya rufe ido ya buɗe yana sake ganin lips ɗin nata, kamar ana jansa ya sake kusanta kansa gare ta, a hankali ya rige kafaɗunta masauki ya yi mata da jikinsa ya ɗan rungumeta sai ta lumshe idanunta, shima ɗin rufe idanun ya yi jin Aafiyyah yau a jikin nasa musamman da ta saka hannu ta dafe bayansa, igiyar rigarta ya ƙarasa ɗaure mata wacce ita ce dalilin fitowar tasa, a hankali ya ɗan zame yana kame kansa a ƙoƙarinta na cewa thank you sai ta kasa breakfast ɗin da bata samu damar yi ba sai ta samu kyakkyawar sumbata daga wajan Gadanga na Ummimi, ta samu karyawa ta musamman daga wajan soja, kissing ɗinta yake slowly ya ɗan matse ta a ƙirjinsa rufe idanu ta yi, jin kamar zuriyarta na rinjayarta wajan mayar masa da martani saboda Aafiyyah a waye take she know what she is doing, ta san komai. Bayan ya bata special breakfast ya manna mata forehead kiss sai ya ja baya yana juyawa tare da danna wayarsa gently. Maamah ta sauke numfashi ta juya tana buɗe motarta tare da shiga zamunin driver saƙo biyu ne ya shigo ɗaya na Paaahhh ɗaya ba suna bata ma da number ɗin. Ta buɗe saƙon Paaahh "Ki same ni a office za mu office ɗin Eng Ali wali na fitar dashi daga kokwanto dana saka shi na cewa ban damu da rayuwark" Replied ta yi masa da "Yes sir" Sai ta buɗe ɗaya saƙon magana ce a gajerce mai muna kulawa da gargaɗi "Ki kula da cikin ki, You are now a house wife" aka ce kawai. A fili ta ce "Idan naƙi fa Maj Aliyu Abdu Marafa?" Ta faɗa tana ajjiye wayar. Driving take a hankali cikin mutuwa har ta ƙarasa companyn aka dinga murna da dawowarta sanda Accounter da ya ji labarin dawowar Madam Aafiyyah jikinsa har rawa yake yi, bata bi ta kansu ba kai tsaye office ɗin CEO kuma MD ta nufa wato office ɗin mahaifin Ashraf ma'ana wajan Sharfaɗi. Ya yi murna da dawowarta kana ta nufi office aiki ta dinga yi kuɗin data ganin duk ƙwarewarta a lissafi kasa lissafawa ta yi, ta dinga duba tarin files wayarta ta ɗauka da niyyar kiran Accounter ta ji ana knocking an daɗe kafin ta ce "In". Shigowa ya yi yana kallon office ɗin itama ƙure shi da kallo ta yi tana jin kamar ta taɓa rayuwa da shi kafin yanzu uwa ta san shi, jin muryarsa ya saka ta fara tunanin muryar Muhammad sak iri guda ce. "Wannan kallon fa Aaffi....," sai ya yi saurin yin shiru. "What?" Ya ɗaga kafaɗa ya ce "Nop, mistake ne Safiyyerh zan ce" waje ya nema ya zauna ya ce "How are you? Congratulations kin kuɓuta" shiru ta yi tana kallonsa tare da juyawa a saman kujerar ya ce "Wannan kallon bashi ko tara ko kin sanni ne?" Harara ta watsa masa ta miƙewa tsaye ta nufi wajan haɗa tea, shayi ta haɗa mai zafi ta dawo saman 3seater tana harɗe ƙafafuwanta a nutse bayan ta kurɓi shayin gently ta ce "I.Qasim how are you?" "As you can see, good" "Kamarya?" Ya ce "Couldn't be better, and you?" "I'm chill" Ya ce "Good. Ya ciwon kan naki na zo da maganin da allura?" "Lau, kawai ina yawan ganin mutanen da nake jin kamar na san so idan zan tuna sai a yi mini allura shikenan na manta fa" ya yi ta kallonta sai ya bata magani ta amsa ta sha ya miƙe ya ce "bari na ɗakko allurar cikin mota, na yi miki in sha Allah komai zai dawo nrml Fiyya" Ta haɗe fuska jin ya ce allura I.Qasim ya ce "Allah sai na yi miki" sosai muryarsa iri ɗaya data Muhammad na system ɗin, who's he?" I.Qasim na fita ya ci karo da Sp Ghali yana zuwa ya buɗe baki da ido ya ce "Goodness wa nake gani kamar Sp Ghali the great class captain?" Sp Ghali na murmushi ya miƙawa I.Qasim hannu ya ce "Nima wa nake gani kamar I.Qasim kimiyya?.... Waye wannan kamar Qasim Abraham Kimiyya? A fafata a comment section domin samun update na gaba. 💥B2: chapter: 3: I Screwed up Dariya suka yi lokaci guda suna haɗa hannu tare da tafawa cikin farinciki Sp Ghali ya ce "I. Qasim.... I. Qasim duniya" ya ce yana jijiiga hannun I.Qasim tare da dukan kafaɗarsa. Shima ɗin dariya ya yi yana juyawa zuwa ƙofar office ɗin Aafiyyah ya ce "Class captain namu, ya bayan rabuwa?" Cewar I. Qasim yana murmushi mai cike da jin daɗi. "Kimiyya ɗan iskan kaya" Cikin sauri Kimiyya ɗin ya saka hannu a saman bakinsa ya ce "Shittt, akwai matsala muje daga wajan motata sai mu yi magana ko?" Sp Ghali ya ce "As your wish Dr" A tare suka nufi harabar companyn suna magana cikin jin daɗi, bayan sun jingina da jikin motar kimiyya data kasance fara tas sabuwa sai ɗaukan idanu take yi ya juya ya kalli Sp Ghali ya ce "Wai ya aka yi aka haihu a ragaya ne? Na ganka da uniform?" Kimiyya ya tambaya yana mamakin ganin rayuwar dayan ƴan Fgc ta sauya sai wanda ba za'a rasa ba. Sp Ghali ya ce "To ya za'ayi da hukuncin Ubangiji? Ban taɓa tunanin zan yi aikin ƴan'sanda ba sai yanzu, kasan na rigaku yin graduate, duk da cewa kai ba'a makarantar ƙarasa ba, Abba ne ya sauya mini ra'ayi bisa wani dalilinsa sai karatuna a jami'a ya sauya zuwa fannin police kuma ba'a Nigeria na yi University ba, kasan kuma yanayin ƙasar nan idan babanka wani ne aiki ba zai wahala ba, duk wata ɓaraka za'a ɓoye ta wajan ganin irinmu mun samu shiga, ko matakin Sp ɗin ai shige da fice ne kawai irin na manya shine" ya ce yana murmushi yana jin kansa wani na musamman ga mutane na musamman irin shi. Kimiyya ya ce "abu ne mai kyau ai, na ji mamaki saboda na san ba shine mafarkinka ba, zama jami'i" "To ya za'ayi , my father's wish is my command, I have no choice" "To Allah Ya taimaka ya sa ka tsaida gaskiyar da ka yi rantsuwa a kanta" kimiyya ya ce yana buɗe gaban motarsa ya ɗauki wata mini box. Sai Sp Ghali ya ce "Amma ya aka yi ka fara kirana da Sp without knowing na zama police? Ya ka zama Doctor ina barrister ɗin? Mene ya kawo ka wannan kamfanin?" Kimiyya ya buɗe ido ya ce "What a questions! Son na zama Barrister ra'ayin Jeddah ne ai, Mimina kuma bata son barrister wai dole dr zan yi na zama kamar Papi, to ya zan yi kasan uwa uwa ce duk yadda nake ƙaunar Jeddah dole na haƙura na bi ra'ayin Malama" sai kuma ya yi shiru yana ɗaga kansa sama ya ce "Sanda aka yi hutu a Fgc wajan Mimi na koma da nufin yin hutu kasan Jeddah ce a nan, Mimina da Papi suna Germany, ina zuwa tace idan har ita ta haife ni ba zan dawo Nigeria ba, tana kwace mini sim kamar wani yaro, to ya zan yi ina son Mimi sosai, ina kewar mutane da yawa kodayaushe hankalina yana Nigeria wallahi musamman Fgc da Jeddah. A haka na daddage na yi karatun da take so kasan karatun ƙasar waje ba kamar na nan ba, bayan na kammala Papi ya ce wa'adin zamanmu a Germany ya ƙare dole na yi wa Nigeria aiki kamar yadda yayi shima, ni dai nafi kowa farinciki fa, a ranar da muka dawo na je Fgc sai dai i feels bad na ji dama ban dawo ba saboda abubuwan dana tarar na yi kukan zuci na yi na fili i don't know ma ko zuciyata bai samu matsala ba, ina doubt ma" Sai ya yi shiru yana ɗan sauke numfashi yana yin na sake ruskar zuciyarsa a yanzu, wani kimi ne mai tsananin rauni a cikin zuciyarsa da baya jin zai warke sai ya yi murmushi yana kallon Sp Ghali ya ce "Look at yourself captain, or Sp Ghali" Sp Ghali ya kalli kansa da kyau sai yaga bai ga abin da Kimiyya ke son nuna masa ba. Ya ce "Ban fahimta ba, me kake son nunawa?" "Ka ce ina na san ka zama police da matsayin Sp ɗin dana ambata ko?" I. Qasim kimiyya ya ce, yana nuna uniform jikin Sp Ghali da kuma ina aka rubuta matsayin Sp ɗin wajan kafaɗarsa ya ce "Gashi nan ai" "Oh na manta da uniform a jikina. Kimiyya na tambayeka kana da labarin mutuwar Safiyyerh ko na ce kisan da aka yi mata?" Kimiyya ya girgiza kai ya ce "Safiyyerh ta rasu na sani, Aafiyyah ta yi lossing memory domin sanda na dawo ƙasar nan mahaifin Aafiyyah da kansa ya kira ni ya ce kar na kuskure na ambaci suna kimiyya ko na yi mata maganar data shafi Fgc, wannan dalilin ya saka data ganni take tambayar ni kuma waye sai aka ce mata sunana I. Qasim kuma dr ne ni da wannan muka saba muka zama kamar abokai, haka Paaah ya sake jawa Kinal kunne. Ban san wani accident aka samu mai muni daya saka har ayi ta manta rayuwarta ta bawa, still Safiyyerh died" ya faɗa cikin rashin jin daɗi da walwala damuwarsa na sauka a fuskarsa tare da sake fasalta yanayin da zuciyarsa ke ciki koyaushe yana tuna Safiyyerh a ransa da yadda take yawan kuka akan MOH ya san dai duk irin kukan da zata yi a bayan na Aafiyyah kawai yake, duk wanda zai bada labarin how much Aafiyyah loves Mutallab a bayansa yake. Sp Ghali ya katse tunanin I. Qasim kimiyya wajan furta "Uhm ya kashe Safiyyerh, yana yi kamar bai san ni na amshi case ɗin ba ya yi kyau" Kimiyya refused to answer, sai ya share maganar wajan cewa "Zaka shiga wajan Aafiyyah ɗin ne?" Shima Sp Ghali ganin kimiyya baya son maganar Moh, kuma kamar bai fahimci me yake faruwa ba sai ya ce "E, na zo ganinta akan amsar statement ɗin kidnapped ɗinta da aka yi but he survived Alhamd. Kai me ya kawo ka? Ko kana da hannun jari ne?" Sai kimiyya ya yi murmushi yana ɗaga kafaɗa ya ce. "Kamar ka manta Aafiyyah is my crush? Yanzu kuma abokai" "Ah, lallai nima dana tabbatar na rasa Safiyyerh sai na ji ina ƙaunar Aafiyyah sai gashi kuma ta zama matar Maj Aliyu. Yanzu ina tunanin zan koma kawai sai na sake shigowa ka gaishe ta Please?" Sp Ghali ya ce sanda suke sake gaisawa da Kimiyya sai ya buɗe mota ya shiga tare da tayar da ita ya bar cikin companyn a guje I. Qasim ya bi bayan motar da kallo yana murmushi a hankali ya fara takawa tare da komawa cikin office ɗin Aafiyyah. Tana zaune inda ya bar ta a lokacin hannunta riƙe da waya tana dannawa gefenta kuma plate ɗin chips ne tana ci a hankali ta harɗe ƙafarta ɗaya saman ɗaya, ta ji motsi amma bata ɗago ba sai a hankali can ƙasa ta ce. "Can you help me with water pls?" "Ok Maamah" cewar Kimiyya. Wajan deep freezer ɗin dake cikin office ɗin nata ya je ya buɗe ya ɗakko ruwa mara sanyi shi kuma ya ɗakko juice a ciki. Ya dawo ya zauna yana miƙa mata amsa ta yi ta buɗe ta sha kaɗan sai ta ajjiye shiru ba wanda ya yi magana sai shi ne ya ce. "Ance na gaida ke" Juyuwa ta yi ta ɗan kalle shi for a second kafin ya ɗauke ta ce "na ji a bakin ƙofa ance kimiyya, i think na san kimiyya ɗin nan haka nake ji" Sai ya kalle ta ya ce "Haba? A ina kika san shi waye shi? Mene alaƙarki da shi ma tukunna?" Ya yi tambayoyin zuciyarsa cike da zullimi tare da fatan ta gano ko yaya ne cewa I. Qasim ɗin da yake gabanta shine Kimiyya ɗin da take magana akai, abubuwa da yawa sun yiwa zuciyarsa ƙawanya tare da cunkushe ta burinsa a yanzu abu biyu ne, yaga Aafiyyah ta dawo cikin tunaninta tun kafin komai ya zurfafa kar ta dauwama cikin halin da take domin akwai cutarwa yana ganin kuma hakƙin hakan akan shi ne, idan ya kasance aboki na ƙwarai kuma masoyi na gaskiya dole ne ya jajirce wajan ganin Aafiyyah ta dawo asalin Safiyyerh ɗinta kuma cikakkiyar Aafiyyah. Madadin jin abin da yake son jin domin zuciyarsa har zillo take yi sai ya ji ta ce "ban shi ba, amma kamar na san sunan haka zuciya da ƙwaƙwalwata suke faɗa mini, musamman idan na yi bacci ina jin sunan raɗau, ba iya kimiyya ba hadda mai suna MUTALLAB. Kafin na fahimci komai nake farkawa daga bacci a tsorace kuma ina farkawa na tambayi waye Mutallab ana nuna mini babu wanda ya san shi sai kuma Dr Hash ya yi mini allura shikenan, abubuwan nan suna damuna a zuciya ina kasa bacci wajan ganin na zurfafa tunanina akan tilastawa kaina sanin mene haɗina da Mutallab da kuma kimiyya ɗin, na fara gazawa, na fara gazawa na gaji matuƙar gajiya I.QASIM" Sai ya yi mata shiru yana kallon ta cike da tausayawa, zuciyarsa na girgiza tare da rawa a ƙirjinsa wani irin tsofaffin feelings na motsa masa, idan ya ce baya son Aafiyyah ya yi ƙarya amma buƙatarta ita ce gaba da son da yake mata sai ya kasa huɓɓasa zuciyarsa wajan yin magana da idanu yake bin ta ganin ta lumshe idanun nata tana sauke numfashi a hankali tare kuma da dafe kanta. "Za ka taimaka mini ko?" Ta ce a raunace tana ɗan kwanciya ka ɗan. Sai ya ji jinin jikinsa ya tsinke daga daskarewar da ya yi. "Help me please Qasim Ibrahim, do me a favour" "I will crush...," ya ce a nutse. Sai ya miƙe tsaye yana ɗakko maganin ya miƙa mata tare da ruwa ta ɗan marairace fuska sai ya jinjina mata kai ya ce "Wannan shine taimakon Safiyyerh, the only thing i can do....!" amsa ta yi. Sai kuma ta ce "Kamarya?" "Kamar yadda kika ji. Zan taimaka miki da dukkan iyawata, da dukkan zuciyata, da dukkan abin da nake ji game dake zan taimaka miki gwargwadon abin da Ubangiji ya bani ikon taimaka miki da shi, zan taimaka, taimakon da zai nuna adadin soyayyar nan da nake miki" Sai ta ce "Soyayya?" Ya ɗan jinjina kai yana ware hannunsa ya ce "Shine kika zaɓi Ashraf kika bar ni, dalilin barina ƙasar kenan sai yanzu na dawo kuma na dawo a gaɓar da kika zama matar AA MAJ. kinga mafarkina ya mutu soyayyar ce ke raya kanta a zuciyar Qasim Ibrahim. Let's bygones be bygones yanzu abokai ne mu" Bata kalle shi ba, sai kwanciya da ta yi saman 3seater ɗin saboda maganin ya fara sata bacci, irin baccin dake samar da cikakkiyar nutsuwa a ƙwaƙwalwa da zai bawa ƙwaƙwalwa damar yin tunanin abubuwa masu kyau ɗin. "Oh! ka san wani Muhammad please?" Sai ya ce "Muhammad?" He repeated the same loudly da mamaki tare da shi. Ta jinjina kai tare da faɗin "E. Akwai wani friend ɗin Yaa Aliyu sunansa Muhammad muryarsa da na ji a system suna Vcall sai na ji tamkar muryar I. Qasim muryar Muhammad irin taka ce sosai Qasim" "Ikon Allah. Kin san Ubangiji kan iya halittar bayinsa a gari daban-daban sai kuma a samu kamanni ko wani abu dake tattare dana wani ki gansa ana wani. Hakan kuma ya samu asali ne dalilin kasancewar mu jinin Annabi Adam Alaihissalam. Idan kika ɗauke haka ko family bani da wani ɗan'uwa mai suna haka. Babban Yayanmu Khalil sunansa mai irin sunan Papi muna ce masa Yaa K sai Mami ta haifi tagwaye Alhassan da Al Hussaini. Alhassan bai bar komai wajan ɗauke halin Papi ba, bayansu kuma Mami ta sake Haihuwar tagwaye mata Soha da Noha sai kuma ni last born kasancewar Jeddah bata taɓa haihuwa ba ya saka na ke zama wajanta amma bada son ran Mimi ba kisan mata akwai kishi sosai" surutu take ta yi mata ba tare daya lura ta yi bacci ba, sai daya ɗago idanu yaga numfashinta na sauka slowly a ƙirjinta ya zuba mata idanu, sai kuma ya ɗauki allurar ya yi mata a hannunta duk da bacci take sai data buɗe ido ta kalle shi irin Why?. Cikin sauri ya shiga wayarta tare connecting ya tura mata pictures na calture day, amma babu Mutallab ciki ita da Kimiyya ne sai Safiyyerh dake gefe tana murmushin nan dimples nata ya loma cikin bakinta ta rungume Aafiyyah, ita kuma Aafiyyah ya riƙe hannun Safiyyerh tana yin wani irin killer smile. Bayan wannan picture ɗin sai ya sake tura mata pictures ɗinsu suna team work da su Kinal sai kuma filin ball jikinta sanye da sportswear ta ɗan cilla ball ɗin aka ɗauki picture gefe an rubuta Fgc yana gama turawa ya ajjiye mata wayar ya fara ƙoƙarin kiran Papi. * Eng Ali wali na zaune cikin office ɗinsa da yake amsa baƙi na musamman idanunsa akan P.a ɗinsa ya ce "Ina ta kiran wannan Ɗan'daban yaron bana samu kuma hakan yana nufin akwai babbar matsala, ina son ya kawo mini yarinyar waje zan saka wani daban ya aiwatar da abin da nake nufi. Dr Abraham Denial David da Hon Maɗatai suna son kawo mini matsala dole na dawo da Professor Abdu cikin tafiyata" ya yi furucin yana mai sake danna wayarsa wacce ba ko yaushe yake amfani da ita ba, tashin hankali ƙarara ya gama bayyana a saman fuskarsa tsoron rasa Aafiyyah wajan yin amfani da ita shine yake tarwatsa zuciyarsa da nutsuwarsa. "Distinguish. Ina ganin muje da kanmu mana mu same shi? Ba suna gidan daka bashi ba ko?" Eng Ali ya kalli P.a kafin ya ce "Na tura Ja'afar yanzu lemme give him a call?" Sai ya kasa kiran ma gabaɗaya ya cillawa P.a wayar ya ce "Call him" Wayar P.a ya ɗauka ya ce shine Jafar ko? Cike da masifa Eng Ali wali ya ce "Wai meke damunka ne P.a ya ina abi cikin gaggawa kana mini tambayar daka riga ka san amsarta tuntuni eh?" Haƙuri P.a ya bawa Ali wali kana ya kira Jafar magana sukai a takaice sai ya kashe kiran ya ce "Yana hanyar dawowa sun je gidan wai babu komai a ciki" Ali wali ya yi baya yana dafe kai sai kuma ya ce "Akwai matsala idan yarinyar nan ta suɓuce mini ina ji a jikina Mai dawa ba zai ci amanata ba, P.a ka yi maza ka nemi Jafar duk inda Mai dawa ya kai yarinyar nan a nemo tun kafin kuzo nan a nemi mai yi mata fyaɗe kungane? A tilasta mata cewa Professor Abdu Marafa shine yayi mata fyaɗen tunda ya nuna mini ita ba jininsa bace kaga dalilin hakan dole ya yi baƙin jini a idanun jama'a, a je a nemo mini Safiyyerh right now ok?" Daga baƙin ƙofar office suka ji an turo ƙofar tare faɗin "Safiyyerh A Marafa is finally here" Daga P.a har Eng Ali wali miƙewa sukai tsaye, bakin P.a hangame yake bin fuskar Aafiyyah da kallo, sai kuma wanda yake tare da ita. Ali wali wani yawo ya ji ya tsaya masa a saman harshensa ya dinga ƙoƙarin haɗiyewa zuwa cikin maƙoshinsa daya bushe nan take saboda gigita haɗi ta kiɗima, ƙafafuwansa suka dinga rawa kamar yadda zuciyarsa ke rawa, idanunsa zube a fuskar Professor Abdu Marafa yana masa wani irin kallo mai kama da ya haka?zufa ta dinga yanko masa amma ya dake tare da shanye mamakinsa cikin ransa yana sassauta yanayin kiɗimar. Paaahh ya kalli Aafiyyah sai ya kama hannunta suka ƙarasa shiga cikin office ɗin, tare da neman wajan zama ya zauna itama Aafiyyah ta zauna sai Paaahh ya kalli Eng Ali wali yana murmushi haryanzu kafin ya ce "Eng Ali wali mai neman kujerar ɗan majalissar tarayya a karo na babu adadi". Sai ya yi shiru yana nuna kujerar da Ali wali ya tashi akai ya ɗora da "zauna kan kujerarka kar razani ya sake raunata gajeren tunaninka Distinguish" "Me ya kawo ka wajena? Ya aka yi ka kuɓutar da yarinyar da bata zama damuwarka ba, ko da zan yayyanka naman jikinta kamar yadda ka ce?" "Shi ya sa na ce maka ka zauna, kuma yau na sake tabbatarwa Hon Maɗatai da ilimi yake amfani wajan kai ka ƙasa basa ƙwaƙwalwa kuma da ka kamar kai yadda kake yi ba. Zauna na feɗe maka biri har wutsiyarsa na buɗe ka daga cikin ƙullin kokwanton dana cilla zuciyarka, babu mamaki maganata ya sake fama jinyar zuciyarka da ƙara haukatar da kai" Paaahh ya yi magana yana ƙara nunawa Eng Ali wali kujera. Kujerar ya ja ya zauna yana kallon Aafiyyah wacce ta harɗe ƙafafuwanta tana danna waya ba tare data sake magana ko kallon Eng Ali wali ba. Paaahh ya ce "A zahiri Professor aka sanni dani, mai bawa matasa shawara akan inganta rayuwarsu da abin da ya dace dasu musamman sanin ciwon kansu da gudun tarzoma da kama karya irin na ƴan siyasa tare da gargaɗi akan bangar siyasa hani ga shaye-shaye" murmushi Paaahh ya yi yana girgiza ƙafa ya ce "Sunana Dig Abdul-Johar Marafa jami'i a hukumar jami'an tsaro ta FCID mai matsayin Dig. Shekarun baya da suka shige ina ɗaya daga cikin jama'am SSS wanda kuma a hankali aka ware mutane na musamman daga SSS aka samu FCID jami'ai na musamman, mun jima muna neman Scorpion idanu rufe sai gashi mun samu damar kama Scorpion ta dalilin naka zaluncin da son zuciya da ƙoƙarin ganin dole sai ka ja ƙafafuwana zuwa gare ka wajan tarwatsa rayuwar yarinyata. Aafiyyah bawai iya Manager bace staff ɗin Fcid ce, tun kafin ka saka a yi kidnapped nata ta san cewa ana bibiyarta kuma ta ɗauki photon yaron ta tura mini a nan na sake yarda cewa kai zero ne kuma minus zero war wuƙar da suka caka mata a Company na sani, kuma nina hana ta faɗi ko waye. Wanda muke nema sai gashi ya shigo komar mu cikin ruwan sanyi, tun daga ranar yarinyarta ke shirin kota kwana saboda mun bata huro na musamman, a sanda nake faɗa maka cewa ta je inda ya tace ne ai satar amsa na baka madadin ka yi tunani sai ka sake zama zero. Na faɗa maka Safiyyerh ba zata taɓa zama ciwon kai na ba saboda ɓatar da tunaninka na san idan na nuna rashin ko inkula ka sace tan zaka jinkirta ƙudirinka har zuwa sanda zata gama aikinta. Safiyyerh rayuwar Abdul-Johar ce jinin jikinsa da ace bani da wani plan wallahi ka yi kaɗan na rabu da kai" Miƙewa tsaye ya yi yana sake murmushi ya ce "Ban taɓa cewa kar a zaɓeka ba, hanya kawai nake buɗewa matasa daga kai har Hon Maɗatai da ruwan kallo da gajiya tsakanina daku ni ba ɗan siyasa bane, wakilin matasa ne ka ɗauke idanunka daga kan ƴata Safiyyerh. Daga ƙarshe ina mai yi maka albashirin mun kama Scorpion yaron daka saka ya sace Safiyyerh shine Scorpion ɗin na barka lafiya Eng Ali wali" miƙewa tsaye Aafiyyah ta yi tana bin bayan mahaifinta zuwa waje, mota ya shiga ita ke driving shi kuma yana gefe ta lumshe idanunta tana jin sauƙin ciwon kan. "Daddy...!" "Maamah" "Ka san nasha wahala a wajan ƴan'daban nan musamman Scorpion baya magana sam kullum zuciyarsa a ƙuntace take mashayi ne sosai ya dinga hauka da kururuwa so bad" Paaahh ya jinjina kai ya ce "Uhm" Tana kallon titi daidai sanda zata shiga estate nasu ta ce "Ya sani ciwon baki, idan na yi masa magana mai tsayi duk don ya saki jiki dani amma baya magana, har ƙasa bakina nake saboda yawan magana kasan ban saba ba, gashi wari suke yi basa wanka at all. Har labarin su J na bashi amma bai tanka ni ba ka san sai da na ce masa ina son shi ya fara sakewa? I told him, i love him and i want to marry him" Da sauri Paaahh ya juya ya kalli Aafiyyah da tsananin mamaki kafin ya ce "You love him? Auren dake rataye a wuyanki ba? Auren Aliyun fa?" Sai ta zubawa titi idanu ta yi shiru kawai gabanta na faɗuwa tare da samun fargaba a zuriyarta musamman idan ta hango tsakiyar cikin idanun Mai dawa kamar yadda su Goje ke ce masa, sai ta dinga jin kamar bata kyauta masa ba ta yarda a dalilin SO ya bata labarinsa dalilin SO ya sake amincewa da ita dalilin alfamar SO ya faɗa mata komai dake cikin littafin rayuwarsa saboda jin furucin zata aure shi, bai san cewa a iya harshen Aafiyyah kawai so ɗin ya tsaya ba, babu shi ba a zuriyarta domin Ubangiji dake samar da SO bai riga ya haliccin Mai dawa a zuciyar dake rayuwar a ƙirjinta ba. Wasu raunatattun abubuwa take ji suna famo kansu da taso mata da shuɗaɗɗan miki a cikin ƙirjinta, sai ta ji kamar ana raya wani abu mai kama da SO ɗin ya mace a ƙirjinta abubuwan da suka jima da tarwatsewa suna tattaro kawunansu ta waje guda tare da matsewa a ƙirjinta suka dokawa da ƙarfin gaske a kalbim dake ƙirjin da ƙoƙarin tunasar da zuciya da gangar jikinta cewa akwai halittar dake jirin wannan matattun feelings ɗin. "Ya Rabbi!" Ta ɗan matse kan motar a zuciya ta ce "I screwed up* Ta ce a zuciya tana ɗan sauke glasses ɗin motar tare da ƙaro gudun acn cikin motar ko zata samu damar shaƙar iska da kyau. "Mene hakan?" She asked herself. Paaahh dake kula da yanayinta daya jirkice nan take ya ce "Kika cewa Ɗan'daban kina son shi? Kuma za ki aure shi? Ɗan'daba?" Ya yi furucin a gaggauce saboda zullumi. Aafiyyah ta juya ta kalli mahaifin nata da idanunta dake mata wani yaji-yaji sai ta girgiza kai kawai ta ce. "Ni jami'a ce Daddy, kowanne jima'i yana da nasa salon aikin. Na yi masa karyar ina son she sai da ya aminta da wannan son da nake masa ya yarda ya bani labarin komai, a kuma iya kwanakin da na yi wajansu sanda suka sace ni na tabbatar daya kamo da son ƴar gidan Dig Abdul-Johar Marafa na hango soyayyata a idanunsa. Na ce ina son shi ne kawai a harshena ba'a zuci ba, i don't meant it kawai pretend ne kalar nawa passion ɗin kenan" sai Daddy ya ji nutsuwa na saukar masa a ƙirjinsa ƙofofin gashin dake saman fatarsa suka fara rufewa tare da kwanciya daga mimmiƙewar tashin hankalin da sukai ya ɗan yi shiru for a seconds kana ya sake duban yarinyar tasa "Ya matsayin aurenki? Kin yi furucin so akan wani bayan kina da aure?" "I told him bani da aure gaskiya and he believed. Yanzu komai ya ƙare na yi survived shi yana wajan jami'an FCID shikenan. Akwai ƙaryar da kan iya zama halattacciya domin kare kai wannan ba laifi bane a wani ɓangaren just trust me Daddy" Ta sake cewa "baka yarda dani ba?" "I do" Daddy ya ce a sanyaye. Wani soja ne ya buɗe musu gate ɗin Aafiyyah ta danna hancin motar cikin harabar gidan, Paaahh ya fara fitowa sai Aafiyyah daidai lokacin shima AA MAJ ya fito daga cikin motarsa wacce Sergeant Timo ya buɗe masa murfin motar, da sauri Lance Corporal Leo da Sergeant Arma suka sarawa Maj Aliyu Abdul-Johar bai kula su ba, ya fara takawa saman ƙafafuwansa kallo ɗaya ya yi wa Aafiyyah ya ɗauke kai ita ɗin ko kallon shi ba ta yi ba, ta nufi cikin gidan tana waya da Kinal, lokaci ɗaya suka kai hannunsu ga handle ɗin ƙofar, wannan karan ba ita ta fara ɗora hannunta shi kuma nasa ya sauka akan nata, ta haɗiye ajjiyar zuciyar data taho mata tana daidai kanta fuskarta a ɗan kame, hannunta ya damƙe cikin nasa ya ɗan matsa kaɗan wanda ya tilasta mata ɗaga gajiyayyun idanunta zuwa ga fuskarsa, ƙoƙarin daidaita idanunsa yake cikin nata tare son hango matsayinsa a cikin idanunta sai da haryanzu ba'a iya hango komai cikin idanun Aafiyyah. "Ku bani hanya ni kam" cewar Paaahh yana yin kamar bai gansu ba duk da cewa daman kusancin nasu yake so yake buƙata. Gently Maj ya janye hannunsa ita kuma ta yi saurin buɗe ƙofar ta shiga. Mutanen da suke zaune a main parlor suka juyo ta gaida Ummi da Ummimi sai ta nufi wajan kujerar data hango yayyinta akai, ta cillawa Awais jakarta tana ɗora kanta a kafaɗar Dr Hash ta ce "Wash, I'm starving" ture kanta ya yi ya ce "Ba dole ki ji yunwa ba, ke kenan aiki kamar robot. Tashi ki shiga kitchen" "Uhm'uhm ni uhm" ta ce Ya sake tura kanta ya ce "ɗaga mini jiki kar ki kassarawa matata ni" jikin J ta koma da bai sake kallon ta ba, tun kallon farko ta ce "Ummi plz yunwa zata kassara mini hanji ko bonvita ne a bani na sha" Yadda J bai kalle ta ba, haka bai motsa ba yana jin tana yi masa allan dungure a jiki sai ta yi saurin juyawa ta ɗora hannunta a ƙirjin J ta ce "Subuhanallahi! J zuciyata haka take gudu da masifar ƙarfi are you ok? Ya yi mata shiru hannunta ta kai zata juyo fuskarsa ta ji saukar wata razananniyar tsawa a saman kanta ta yi saurin rufe idanu ta riga ta san ko waye. "What stupidly? Mahaukatan ina ne zaku dinga bari tana zama cikinku? Dalla malamai get out of here" Maj ya faɗa cikin hargagi da wata muguwar tsawa ya kuma kalli Aafiyyah ya ce. "Dilla tashi a nan kafin na watsa miki yatsu a fuska nonsense" Kin tashi ta yi, ya yunƙura kanta tare da fisgota tsaye ta ɗaga idanu ta kalle shi yadda yake huci haka take huci jikinta duk rawa yake haka shima ɗin. Hannunsa ya ɗaga zai mare ta ya ji Ummimi ta ce "No please" sai ya dunƙule hannun yana fesar da huci. "Maamah mene hakan?" Aafiyyah ta juya ta kalli Ummi irin kallon “kamarya?” sai taƙi magana "Gadanga karka karya mini kafaɗun yarinya ka ji ko? Allah ka saka ta yi kuka sai ranka ya ɓaci" cewar Ummimi. Sai Ummi ta ce "Kike tunanin za ta yi kuka? Da dai kukan banza ne banda wannan" "For real?" Ummimi said. Tana miƙewa tsaye ta ce "To su ci kansu tunda baƙar zuciya gare su" Maj ya matse kafaɗun Aafiyyah sai kawai ya figi hannunta zuwa upstarts har bedroom ɗinta ya tura ƙofar da ƙarfi kana ya saka key wani irin kallo yake jefe mata kafin ya ce "Are you ok?" Ta yi masa shiru tare da bawa iska ajjiyar shi. Wata tsawar ya sakar mata wacce ta saka kanta sarawa ƙafafuwanta na rawa ta nemi durƙushewa a wajan a gigice kafin ta kai ƙasa ta jita a cikin jikin AA MAJ ya riƙeta tare da rungumo ta zuwa jikin nasa dake sanye da farar t.shirt sai amy colour ɗin p.cap dake saman kansa, ta yi ƙoƙarin haɗiye kukan sai kuma ta saki wani irin maraitaccen kukan sangarta tana diddire ƙafafuwanta a ƙasa tare yarfe hannunta, hakan ya saka Maj sake ƙarfin rungumar da ya yi mata a cikin jikinsa a kunnenta ya ce "ke da waye?" Ya ce, his voice barely above a whisper. She looked up at him, tears streaming down her face ta ce "Maj ne" "Mijinki dai" he replied. Ta ɗauke kan ta daga ƙirjinsa tana marairace fuska ta ce "Mijina ba zai mini tsawa ba, mijina ba zai ce zai mare ni ba, wannan ba mijin Safiyyerh bane" idanunta rau- rau He pulled her close, placing her head back on his chest, ya fiddo idanunsa ya ce "What do you think?" "You hated me....." She started to say, but he cut her off "Ya isa, ya isa, ya isa" ya ce yana sakinta tare da juyawa a hankali ya bar bedroom ɗin fuska ɗaure. Aafiyyah ta bi bayansa da kallo sai kawai ta ɗaga kafaɗa ta nufi bathroom domin yin wanka bayan ta fito ta shirya cikin kaya masu ɗan sulɓi pech ɗin jallabiya ta mata mai kyau da ratsin white ta saka sallah ta yi bayan ta kammala ta shafa oil ɗin S Bayero da aka yi mata recommended kuma ya amshe ta sosai ta fesa humra duk ta S Bayero laptop ta janyo ta fara duba abubuwa masu muhimmanci, ta mail ta turawa su Accounter da sectary da Md cewa tana da meeting nasu. Sai a lokacin ta ci karo da wani saƙo a mail ɗin batu ne akan Hon Maɗatai dole yana buƙatar sanya hannun jarin sai kawai ta yi tsaki ta ɗauki number Md kira ɗaya ya ɗauka kafin ma ya gaishe ta, ta katse shi da faɗin "10:30 za mu gidan maɗatai" "Ok Mahh" ta kashe kiran. Gajeren message ɗin Maj ne ya shigo wayarta ta ɗan duba taga abin da ya ce. "Meet me at my room, with food" Ta lumshe idanunta, bawai damuwa ne ba ta yi akan son sanin tsakanin ita da Maj waye ba jinin Paaahh ba? Tsoron jin amsar ya saka bata tsawaita tunaninta balle har ta yi yunƙurin tambaya, dole ta yi ƙoƙarin samawa Aliyu waje a zuciyarta ta bashi gurbi miji na son iya mu'amala da shi akan dole domin sauke haƙƙinta matsayin mata. Glory ta kira ta sanar mata ta ɗan sama mata abu mara nauyi mai ɗan ruwa-ruwa. Sai ta kunna data maganar Kinal ta gani da I.Qasim ba wanda ta kula ta kashe datar gabaɗaya. * Kuka take sosai duk da ta yi kyau da ƙiba alamar hutawa amma babu kwanciyar hankali a tattare da ita, gashin kanta a birkice tana kukan tana ƙafe shi da idanunta alamar tuhuma da zarfin. Ya nufe ta zai riƙe ta, ta yi saurin ja-da-baya. "Allah ba ruwana da kai" ta ce tana shassheƙar kuka wajan da take inuwa ce shimfiɗe ga wasu tarin furanni sai ruwan ƙorama na gudana tsuntsaye sun baibayeta suna ɗan tashi kaɗan-kaɗan. Ya zuba ƙasan ƙafafuwansa ya ce "Kina azabtar dani Zinariya ni ne bestie, Bestien beastie fa?" "You're no longer my bestie" Ya yi saurin cewa "Don Allah ki sassauta mini, ki bar ni na shigo cikin inuwarki ko zan samu saƙin ciwon da zuciyata ke ciki haba gudaliyar Prof" Sai ta kalle shi ta ce "Kana son shigowa cikin wannan inuwar?" Ya yi saurin ɗaga mata kai ta ce "Kalli nan" Ya yi saurin juyawa, kyakkyawar budurwa ya gani farinta na shigar masa idanu, jikinta ɗaure da sarƙoƙi ta ƙanƙame wani yaro a ƙirjinta tana kuka yaron na kuka, sai ƙoƙarin ƙwace yaron wasu gardawa suke ta hana jikinta jina-jina da jini. Ya juya ya kalli Bestie ya ce "Deer na gani, wacece ita? Waye ɗan, su waye za su ɗauke yaron?" "Aafiyyah ce da yaron ta. Bestie waɗancan jininka ne alhalinka ne ka je ka ceci matarka da yaron ta, maza jeka gaggauta tafiya Allah idan baka ɗauke Aafiyyah zuwa gare ka ba, babu ruwana da kai babu ruwana" Sai ya miƙa mata hannu ya ce "But i want you, ni wajanki nake so Barewata please ina son jinki a jikina" ya ce a raunace. "Allah Ya shirya ka. Jikin Aafiyyah ya fi nawa ƙamshi. Mutallab! Ba zan taɓa yafe maka ba ba zan taɓa yafe maka kana wofintar da wasiyyata kana hanani bacci cikin sukuni a cikin kyakkyawan gidana, kukan Aafiyyah nake ji zan maka Allah....," *A gigice Moh ya farka daga baccin da yake wanda tsabar wahala ya saka shi ba tare daya sani ba. Mafarkin Deer ya gigita shi ya sake fahimtar a yanzu ba wai fansar ranta take buƙata ba, kasancewarsa da Aafiyyah take so, su waye waɗannan? Waye wannan yaron? Ya ƙanƙame takadda a ƙirjinsa yana jin rauni na son bayyana a fuskarsa, idan har abin da yake so gaskiya ne wallahi mutuwa yake buƙata, Safiyyerh yake so kusa da shi not Aafiyyah, ɗomin jikin barewa yake buƙata. ya runtse idanunsa ƙoƙarin kokawa yake amma idanunsa ya bushe zafi da raɗaɗi zuciyarsa ke masa yana jin wani yaji-yaji a maƙoshinsa gargasar jikinsa na buɗewa sanyi na ratsa jikinsa, duk rauni ne a jikinsa sun sagar masa da gaɓɓai ya gama yarda shi maraya ne bashi da kowa a duniya bashi da gata babu mai zuwa gare shi babu mai jin tausayinsa shi sam bai san me ya yi iyayensa da mutanen duniya ba, wani irin kewa da maraicin Barewarsa yake ji yana huda ƙirjinsa tare ratsa ƙofofin zuciyarsa, ko zaiwa deer faɗa ya ji dama tana kusa da shi kewar Anty Hameeda ta mamaye gangar jikinsa tare da jikkata ƙwaƙwalwarsa ya rufe idanunsa da tunanin zai sake ganin deer ta gitta a cikinsu. Ya kasa koda ihu ne ya dinga buga kansa da wajan da yake kwance fuskarsa caɓa-caɓa da jini jin za'a shigo ya yi saurin hura iska ya muzar hannunsa a wajan ya damƙo ƙasa ya murza tare da takaddar hannunsa cikin ƙaramin lokaci takaddar ta zama ɗan ƙaramin dutse. Magana suka fara yi masa amma ya yi shiru wani ya ce. "Ko ƙara saka masa lantarki" Tsananin azaba ya saka Moh ɗago idanunsa a hankali ya ce "Zan yi, ku kira mini ita" "Ita wa" Ya yi shiru. Sai wani ya ce "Ƴar Dig Johar yake nufi. Safiyyerh" A take suka kira ta, har kira uku ana haɗun ta ɗauka "Mahh, Scorpion zai yi magana amma ya ce sai ki nan" ta cikin wayar ta ce "And?" "Please, you need to come" Yana ƙoƙarin magana ya ji ta kashe kiran gabaɗaya ya zubawa wayar ido. * Haɗaɗɗan parlour ne daya gama gajiya da ƙawatuwa iya kujerun kaɗai abin kallo ne ga wani ƙamshi da yake tashi yana sauka a zuciyar mutum tare da bawa zuciya nutsuwa. Tana hakimce tare da danna laptop ɗin gabanta jikinta sanye cikin wani golden ɗin lace siriryar sarƙar gold ce a wuyanta can ta ɗago kai ta ce. "Me kake cewa ne?" Sai ya ɗan shafa kansa ya ce "Yana da kyau kiwa Papi magana akan takarar nan wai ya ce ya haɗa hannu da Hon Maɗatai" sai ta ɗago idanunta sosai tana nazartar Khalil ta ce "Idan kana da wata magana bayan wannan yi" Ya girgiza kai, sai ta ce "Good" I. Qasim dake zaune yana ji ya ce "Yaa K ya jikin naka? Da jikin baby?" "Allahamdulillah" Khalil ya ce yana miƙewa tsaye tare da fita waje. A hankali ta sauke ajjiyar zuciya, Malama Majeederh ta bi ɗan nata da kallo sai kuma ta haɗe fuska ta ce. "Kimiyya baka ji" "Kai Mami me na yi? Ga marasa ji can Soha sai dai kullum ta ce tazo gida kwana saboda shima mijin nata bai san me yake yi ba" Mami ta ce "Yayarka ce, kar na kuma ji" "An gama Mami. Jeddah na gaishe ki" Ta yi masa shiru. Ƙamshin turaren shi na musamman shi ya fara sanarwar Majeederh Abraham is here, ta ɗago kai ta kalle shi sai ya watsa mata harara ya nemi waje kusa da ita ya zauna. Kimiyya ya ce "Papi barka da wannan lokaci" "Qasim, ku yi magana da Ceo ka fara zuwa Company ok?" Qasim ya ce "In sha Allah" Sai ya yi shiru can ya ce "Na sake zana wani company da za'a fara gininsa a Lagos a think lokacin dawowar yayanka daga Germany ya kusa na gaji haka nan" sai gaban Kimiyya ya faɗi ya ce "Zai dawo ya addabi kowa da masifa da mitar tsiya, kuma baka masa faɗa Allah Papi kafi son shi ai" Abraham ya ce "Kuma Mimi na tafi son ku ai, kai da kake da Iyaye biyu?" Ya juya ga Majeederh ya ce "I am right jee?" Ya ce yana leƙa laptop ɗin gabanta da take duba kayan da Aaliyyah ta turo mata. Kimiyya ya miƙe ya bar wajan, yana fita Abraham ya ƙwace laptop Majeederh za ta yi magana ya ce "Takarar na nan, Abraham bai yadda da faɗuwa ba, Abraham Denial David zai yi nasara just pray for me jee" * 10:30 ta yi wa Aafiyyah da Md a parlourn amsar baƙi na gidan Hon Maɗatai. Ya yi murmushi ya ce "Na san dole za ki kawo kan ki ai, dole za ki amince da buƙatata na sanya hannun jari a FS WORLD" Ta ɗan kalle shi ta ce "Haba?" "Haka nake ji a raina" Sai ta harɗe ƙafafuwanta sosai ta cire glasses ɗin idanunta tana yi masa wani irin kallo, shima idanun nata yake kallo kafin ta ce "You got it wrong. Hon Maɗatai; gargaɗi mai kama da jan kunne nazo yi maka, stay away from my company ka ɗauke idanunta daga kai na, wallahi ko zaka mutu ka dawo baka isa ka samu abin da kake so ba, bama buƙata we're not interested, kuma wallahi sai na saka hannu ka faɗi zaɓe" da sauri Md ya kalli Aafiyyah ya buɗe zai yi magana ta yi saurin saka yatsa a bakinta ta ce. "Quiet..... Md" Ta miƙe tana kallon Hon Maɗatai daya miƙe tsaye ta ce "Kai da a tunaninka zan zo wannan kangon gidan naka just to say i agree? Kawai don na ce na amince or poor Hon Maɗatai baka san wace a gabanka. Idan kuɗi kake buƙata ka faɗa na ranta maka daga cikin arziƙin da Ubangiji ya yi mini na baka da kuɗina, ni ba mai arziƙi bane amma I'm born to be riche, kuma thank God i richer than you" "Shut up" "If not? Idan naƙi fa?" Aafiyyah ta ce. Sai ya ɗaga hannu zai mare ta cikin sauri Md ya shiga tsakiya ya ce "Don Allah ka yi haƙuri zan yi magana da Ceo, zan wa Sharfaɗi magana kar ka ce zaka ɗauki mataki akan Madam, ita macace kasan halin mata" Takaici ya ishi Aafiyyah ta ɗaga hannu ta zabgawa Md mari ta ce "Useless, ka barshi ya mare ni ya gani da yaga abin da ya turewa buzu naɗi" tana cewa haka ta fice daman a sabuwar motar da Paaahh ya bata gift ɗinta ta zo she left Md ta yi tafiyarta. Md na fitowa motar Eng Ali wali na shigowa cikin gidan don haka sun samu saɓani da Aafiyyah. Eng Ali wali ya shiga parlour yaushe rabonsa da gidan Hon Maɗatai? Suka kalli juna shi da Hon Maɗatai kallon kar ta san kar. A hankali Hon Maɗatai ya ce "Yes, follow her" yana cewa haka ya kashe wayar gabaɗaya. Sake kallon juna suka yi kafin Hon Maɗatai ta ce "Eng Ali wali" shima Eng Ali wali ya kalli Hon Maɗatai kafin ya ce "Hon Boɗejo Maɗatai..... MUTALLAB BOOK NE PAY BEFORE YOU READ DOMIN SAMUN UPDATE AKAN KARI KA BIYA KA SHIGA GROUP NAMU. 08164069685 💥MUTALLAB Chapter 4: Behind the secret Ya yi murmushi ya ce "Zauna mana Eng Ali wali?" Hon Boɗejo Maɗatai ya faɗa yana nuna wa Ali wali kyakkyawar kujerar dake bayansa kafin a hankali shima ya yi baya tare da komawa ya zauna yana haɗe ƙafarsa hannayensa cikin na juna ya riƙe. Da wani irin kallo Ali wali ke bin madaidacin parlourn wanda ya gama haɗuwa aka narka uwar dukiya a cikinsa. Duk da cewa Ali wali ya riƙe muƙamin kujerar ɗan majalissar tarayya har sau babu adadi, a karon baya ne kuma aminin nasa ya yi masa tawaye ba tare da saninsa ba, ya fito takara har ya samu nasara wannan abu ya sake jijjiga zuciyar Ali wali har ya kasa ɓoye mamakinsa na nasarar da Hon Maɗatai ya samu. A wannan karon ma ya sake neman tsayawa gashi ya samu nasarar tsallakawa zaɓen cikin gidan duk wasu manyan ƴan siyasa suna tsagin Hon Maɗatai. Ali wali ya jinjina kai ya ce "Da zama nazo yi dana sanar maka da zuwana tun kafin ka gani yanzu a gabanka Hon Boɗejo Maɗatai. Haryanzu mamaki kake bani na kasa farkawa daga baccin daya ɗauke ni wanda nake jin kamar mafarki nake yi" ya yi furucin cikin zafin zuciya wani irin tsanar Boɗejo yake ji a ƙasan zuciyarsa musamman yadda ya mamaye komai nasa yake ƙoƙarin kai shi ƙasa bisa dole tare da watsa masa tulin ƙasa a cikin idanu. Hon Boɗejo ya yi murmushi kafin ya miƙe tsaye yana takawa sannu a hankali cikin izza, taƙama da jinkima da arziƙin da yake da shi wanda ya samu ta gurɓatacciyar hanya. Ya jinjina kai lokacin da yake ɗaukan gorar ruwa mai sanyi ya tsiyaya a cup ya dawo kusa da Ali wali ya ce. "Abokina Ali wali, sha ruwa" "Da kai da duk wani abu dake cikin gidanka bai ishe ni kallo ba, bana buƙata nazo jin dalilin da adole kake son ganin sai na durƙusa a kan ƙafafuwana, kake so fito dani rana" Ali wali ya yi raddin maganar cikin ƙonar rai, ji yake kamar ya ɗauki ƙarfe ya caka a ƙahon zuciyar Boɗejo ɗin saboda zallar tsanar da take gudana a jikinsa. Sai ya cije kawai. Hon Boɗejo ya ce "Kana jin kamar ka kashe ni ko Ali wali?" Ya tambaya yana sake kurɓar ruwan. Kafin ya ce "Sai dai ko inuwata ta yi maka nisa balle gangar jikina, ina da taurin kai Ali wali ina da kyakkyawar fuskar nunawa jama'a bayan wannan fuskar da kake gani a gabanka. Ali wali babba ne kai da ƙwaƙwalwar yara, siyasa ƴar zamba ce yaƙi ne inma ka yi nasara inma na yi, wannan kuma takobin nasarar a hannuna take a yanzu, idan naso zan iya cire kan ka, ko kuma na yanke ƙafafuwansa na kwantar da kai kamar yadda ka salwantar da ƙafafuwan Bebeji akan muƙamin Chief whip" Da sauri Ali wali ya ce "Ina ka san wannan maganar? Waya faɗa maka?" Sai Boɗejo ya ɗaga kafaɗa ya ce "Like this...... Kamar dai haka zaka dinga kwafsawa madadin ka zama 9 ko 10 sai ka sake komawa sifili. Da bakinka ka faɗa mini cewa ka yi wa Bebeji asiri a lokacin kuma ka fara faɗa mini irin daɗin da ake ji a siyasa. Tun daga wannan lokacin ka fara kwaɗaita mini son siyasa, a wannan daren ban bar gidanka ba sai da burin zama ɗan majalissar tarayya ko ta halin yaya. Domin cimma nasara a rayuwa dole a kaucewa hanya a kuma toshe kunne hanyoyin da bani samun kujerar nan kunnenka ba zai iya ɗauka ba...," "Good! Da kyau" cewar Ali wali. Kana ya ɗago kai ya kalli Boɗejo ya ce "Ni da kai abokai ne, aminan juna tun muna ƙanana shine ka zaɓi ka ci amanata? Ka nemi abin da nake nema ko? Kai ba ɗan halak bane Boɗejo yadda ka raunata ni sai na tabbatar ka shiga uku, wallahi sai na ɓata sunan daka ɓoye a bayansa kake yin abin da kaga dama" "Ali wali kenan. Ban ce bani da imani ba, ina kyautatawa zuciyata zato akan kai ba tsara na bane, ni da kai na ina jin tsoron kai na. Akan wannan har kimar matata na taɓa balle wani aboki. So do what ever you want to do i can't care. Ba dan kuɗi na shiga siyasa ba ɗaukaka da shahara nake buƙata ok?" Cikin zafin kai shima Ali wali ya ce "Ka dinga yi kana tuna baya, na san komai nake hatta gidanka da abin da yake faruwa game da waɗannan ƴan'matan sauti ɗaya a gidan rediyo zai juya rayuwar zuwa atishawar tsaki, duk abin da kake ɓoyewa zai fito a fili jama'a su san da shi kaga daga lokacin kai ne ka dawo zero?" Jikin Ali wali har rawa yake yi sosai abu goma da ashirin ne ke neman zautar da tunaninsa a halin yanzu, tsoron ƙara rasa damar hawa kujerar ita tafi gigita shi gefe guda ga Scorpion da aka kama,idan kuma Scorpion ya buɗe bakinsa ya yi magana hakan ya nufi zasu fito tsirara akan idanun juma'a duk da har yanzu basu san me sukai masa ba, akan wacce hujja yake neman raba su da rayuwa da kuma jin daɗin duniyar da yanzu suka cilla cokalin cinta, babban tashin hankalinsa jin cewa wai Mai dawa shine Scorpion ɗin? Wannan shine makashinka na gindinka daman da ruwan ciki ake jan na rijiya, ba'a raina allura domin ita ce ƙarfen da kan iya gurguntar da ƙafafuwan mutum. Hon Boɗejo ya katse tunanin Ali wali da faɗin "Waya ɗaya ta isa ta saka a yanka wuyan yarinyarka Sabrina da zarar ka yi yunƙurin yin magana akan wannan ƴan'matan, to ko ban kashe Sabrina Noor ba zata iya shiga jadawalin ƴan'matan wannan shiri nane" a wannan karan Boɗejo idanunsa ne suka firfito waje domin ya lura Ali wali bai san wuta ba sai ya taka gwara na a nuna masa gurbin idano, ba idon bane. Furucin Hon Boɗejo ya jikkita tunanin Ali wali sai ya sassauta fushin da yanayin ya ce "Noor zaka aikatawa haka? Ita ɗin zaka yi wa fyaɗe eh? Ko saboda baka san ciwon ƴa ba tunda baka taɓa haihuwa ba?" "Akasin hakan, don Allah get out of my house fita a gidana Ali wali" "Boɗejo ni kake cewa na fita daga cikin gidanka? Ka iya bakinka baka san ta ina zan raunataka ba, idan siyasa ce kuma dani da kai shege ka fasa yanzu muka fara Allah Ya kaimu zaɓe zaka gani?. Na san abubuwan da baka sani ba akan ka" Sai Boɗejo ya yi murmushi kawai yana danna wayarsa can ya ce "Shi Jaa'afar ɗin ya faɗa maka wani abin don gane dani ne?" Cikin rashin fahimta shima Ali wali ya ce "Ban fahimci me kake nufi ba, wane Ja'aafar kake nufi kenan?" "Ali wali kenan. Kana tunanin ban san cewa yarona Jaa'afar na tare da kai ba, domin ya dinga maka wasu ayyukan fa ka janye shi tare da tura shi ƙasar waje ƙaro ilimi yana dawowa ka saka aka bashi matsayi a cikin ƴan'sanda. Boɗejo ba mahaukaci bane wannan Bafullatanin da kake gani a gabanka ba irin fulanin da wasu suke ɗauka bane ka fahimta?" Ya ƙarasa maganar yana kara waya a kunnensa sai ya yi murmushi ya ce "Alhaji Wada shigo mana, kai nake jira daman ai" abin da ya ce kenan ya sake danna waya alamar kira bayan an ɗauka ya ce "ku daina bibiyar yarinyar nan, akwai plan B dana tsara ku dawo kawai". Ya ajjiye wayar a gefensa. Sai Eng Ali wali ya yi ƙwafa ya juya tare da barin cikin gidan gabaɗaya. Tunani Boɗejo ya fara sai ya ji hankalinsa bai nutsu ba, yana buƙatar ɗinke wata ɓaraka don haka sanda Alhaji Wada ya shigo suka gaisa sai ya kalle shi ya ce "Alhaji Wada a sauyawa yaran nan gida, cikin dare a fitar dasu ok?" Alhaji Wada ta ce "Yadda ka ce haka za'ayi Distinguish. Na je zan inda ka name na samu wata sabuwar mai aiki wacce za ta yi mana komai cikin gaggawa matsayi ce ita" Murmushi ya mamaye fuskar Boɗejo ya ce "Nice, very nice. Wacece ita? Yaushe zaka je?" Alhaji Wada ya ce. "Sunanta Abbasa ita kaɗai ce za ta iya yi mana abinda muke buƙata zan je duk yadda mukai da ita zan kira ka?" "Ok. Cewar Boɗejo. * Tsaye suke a harabar wajan wanda da ƙyar aka basu damar zuwa a wannan karon domin ganin Malam dake tsare a dalilin rashin bayyana musu Mutallab da bai yi ba, basu san cewa ko shi bai san inda Mutallab yake ba wanda da ace ya sani daya jima da basu amsar tambayar da suke masa wanda suke gana masa azaba. Mama Zaituna ce ta kalli Sa'adah dake kuka sosai wanda a wannan karon matsanancin tausayin Sa'adah ɗin ya saukar mata a zuciya cikin damuwa da yanayi na rarrashi ta ce "Sa'adatu don Allah ki tsahirtawa ranki da wannan kukan haka nan, duk abin da ya samu shamuwa ai watan bakwai ya ja mata ko?" Sa'adah ta share majina idanunta jajur ta ce "Mama Zaituna wacce irin ƙaddara ce mai tsananin nauyi da nuni haka? Wacce irin ƙaddara ce wacce lokacin ya kasa kawo ƙarshen ta? Wacce irin rayuwa Malam ya gina mu akan ta haka? Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un! Wallahi ji nake dama ni ba ƴar ma.....," cikin sauri Mama Zaituna ta rufe bakin Sa'adah wajan girgiza kai tare da faɗin "Kul, a hir ɗinki Sa'adatu. Iyaye duk inda suke sunansu iyaye ba'a taɓa sauyawa tuwo suna ki ɗauki hakan matsayin jarrabawa kin ji?" "Har yaushe hakan zai dinga faruwa? Yaushe Malam zai san cewa abin da yake baya haifar da ɗa mai idanu? Ko sai duk mun lalace mun bi duniya zai gane kuskuren nan? Zuciyata zafi take yi mini Mama Zaituna, raɗaɗi nake ji a cikin ƙirjina, ciwo zuciyata take mini na kasa jurewa zaman aure na neman gagarata saboda gorin da ake mini a kan gidanmu. Allah kai ne Allah kai ne gatanmu Ubangiji ka shirya mana mahaifinmu" wani irin raunataccen kuka ta saki, numfashinta na tsayawa a ƙirji idanunta na yi nata raɗaɗin saboda rashin baccin da take samu ji take dama ita ta mutu ba Anty Hameeda ba, abubuwan sunwa zuciyarta yawa. Bafullatana ta cika fum sai muzurai take yi tama ƙi kallon Sa'adah domin dole Sa'adah ta yi mata wajan zuwa belin Malam ɗin. Suna nan tsaye wani officer ya fito bayan Malam Abdullahi ne tafe duk ya gigice saboda wahalar da yake ciki. Ajjiyar zuciya Sa'adah ta sauke lokacin data saka idanunta cikin na Malam ɗin, Bafullatana kuma baya ta yi tare da barin wajan ita kanta Mama Zaituna ɗauke ganinta ta yi daga kan Malam ɗin. Officer ɗin ya kalle su kafin ya kalli Sa'adah ya ce "Daga yau sai ki tsahirta da yi mana sintiri gashi nan anfito dashi za ku iya tafiya mun samu abin da muke buƙata kin ji?" Sai Sa'adah ta ji jikinta ya yi sanyi ta idanunta da suka jeme ta ce "Officer me kuka samu? Ko kun samu Mutallab ɗin ne? Wallahi wallahi Mutallab ba zai taɓa kashe Safiyyerh ba, ni kaɗai na san irin son da yake mata duk da ba'a sanin abin da yake zuciyarsa amma na fahimci rauninsa a fili akan Safiyyerh. Don Allah don Allah ku tausaya mishi ku sake bincike kar ku raunata shi akan abin da bashi da laifi" Officer ɗin kallon Sa'adah kawai yake irin ba za ki gane ba. Can ta ce "Yana wajanku?" "Wa?" Sp Ghali ya tambayi Sa'adah yana tsare ta da idanu, yana ƙoƙarin hango kama ko yanayi na jini tsakaninta da Mutallab ɗin. Ta bashi amsa da "Mutallab" "Ok, baya wajan mu" zata sake magana Sp Ghali ya yi saurin nuna musu hanya ya ce "Leave please. Matsiyata irin ku har abada rayuwa ba za'a ta taɓa yi muku daidai ba,duk inda talaka yake sai ya nuna shi jahili ne na bugawa a jarida babu komai cikin kawunanku sai miyar kuka. Banda hauka har ni ne za ki tambaya cewa bai yi komai ba, bai kashe Safiyyerh ba? Are you stupid? Wallahi yau ko ba shi bane babu yadda kuka iya a banza za'a kashe shi, kuma an kashe banza yaron da bashi da wani gata sai na allo da tawada" kalaman Sp Ghali suka soki zuciyar Sa'adah ta ƙura Sp Ghali idanu a wannan lokacin ma hawayen tsaya mata ya yi ta dinga haɗiyar zuciya ta ce "Ubangiji daya halicce mu ya yi sanadin zuwanmu duniya bai manta damu ba, a wajansa da kai da mu da Mutallab duk ɗaya muke kuma jinin Annabi Adam Alaihissalam da Hawwa. Arziƙi nufin Allah yau gare ka gobe ga waninka daɗin abin bada shi kazo duniya ba, bana jin kuma idan ka mutu za'a haɗaka sa arziƙin a cikin kabari ɗaya. Kamar yadda Ubangiji ya samar da bambancin dake tsakanin fir'auna da Annabi Musa, haka watarana za kaga bambancin dake tsakaninka da Mutallab kuma zaka san cewa allo da tawada ba abin wulaƙanta wa bane wallahi...," Bata ƙarasa maganar ba Sa'adah ta ji Sp Ghali ya sauke mata tagwayen maruka a fuska ta yi saurin dafe fuska idanunta cike da ƙwalla. Kafin kuma ya sauke hannunsa daga fuskar Sa'adah, Bafullatana ta sharara masa mari har uku a gigice Sp ya ɗago kansa hannu ya ɗaga zai mari Bafullatana sai yaga jikinta na jijjiga idanunta na firfitowa waje, mutanenta da suka jima basu motsa ba sune suke shirin tashi. "Ni kika mara? Waye ubanki a garin nan?" "Ka yi haƙuri kurma ce" Sp ya kalli Malam da ya yi maganar ya ce "Daga kurma sai ɗan'daba cikinka ya iya haihuwa? Tunda kurma ce ita mari na rama a kan ka" Sp ya ɗaga hannu ya shararawa Malam Abdullahi mari wani kukan kura Bafullatana ta yi tare da damƙar wuyan Sp idanunta rufe tana wani ihu jikinta na girgiza a haukace take kai masa duka cikin ƙarfi irin na aljanu ta keta rigar Sp gida biyu ta cafki matar kumatunsa ta kantsara masa cizo ya saki ƙara yana ture ta amma kamar dutse taƙi motsawa da ƙyar aka janye ta, bakinta ya ɗayo fatar wajan jini na zuba. Sp ya dinga faɗin mayya ce shegiya sai na yi maganinki dangin matsiyata. Sa'adah durƙushewa ta yi a wajan kanta na juyawa ta kasa motsawa banda sunan Allah babu abin da take kira a zuciyarta. Da ƙyar suka tura Bafullatana cikin napep suka nufi. Sanda suka isa gida Ammo na ɗaki tana ji taƙi fitowa, har suka shigo aka kwantar da Bafullatana Sa'adah ta nemi waje ta zauna kanta a ƙasa ita kanta Ammo ɗin bata ɗago kanta ba, ta yi saurin ɓoye photon dake hannunta. A sanyaye Sa'adah ta ce "Ammo wanne laifi muka yi wa Ubangiji ne?" Cikin sauri Ammo ta ɗago kanta sai a lokacin Sa'adah ta lura da idanun Ammo daya kumbura suntum ya yi ja kamar gaushin wuta sai taga kamar ba Ammo ɗin ba, ita kanta Ammo ɗin kallon Sa'adah take ya ji me ta ce tabbas ta dai kasa fahimta ne kamar wacce kanta ya samu matsala haka take kallon Sa'adah cikin sauri kuma ta miƙe tsaye tare da ɗaukan hijabi ta saka bama ta lura da babu takalmi a ƙafarta ba, balle ta ji kiran da Sa'adah da Mama Zaituna suke mata ba, ta saka ƙafarta ta nufi waje idanunta rufe take tafiya har zuwa gidan da Anty Hameeda ta yi aure tana shiga ta samu uwar mijin Hameeda. Baba ta ajjiye tsintsiyar hannunta ta miƙe da ƙyar haryanzu abin da Mutallab ya yi mata bai warke ba "Lafiya dai Ammo daga ina haka?" "Hamida nazo gani, tana nan ko?" Sai Baba ta yi sak ta dinga kallon Ammo cikin yanayi na tausayawa ta kasa cewa komai ba. Ganin ta yi shiru ya saka Ammo cewa "Kira mini ita, ina buƙatar ta sake tuna mini wasu abubuwan, kira mini Hamida" Baba ta ce "Ikon Allah! Wacce Hadima ko dai jikokinki kika zo gani?" Sai ta girgiza kai alamar “A'a” "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un! Hamidar yaushe? Ko kin manta Allah Ya amshi abar shi? Hamida ta rasu" cewar Baba tana goge hawayen idanunta. Sai Ammo ta ce "Hadimar ce ta rasu kenan ko?" Ta bata amsa da "E. Ta rasu" Ammo ta yi jim sai kuma ta ce "Allah Ya ji ƙan ta" tana cewa haka ta fita daga gidan. Wani waje ta samu ta zaune sai ta rushe da kuka da iyakar ƙarfinta "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!" Shi kawai take faɗa a gigice sai ta koma kiran sunan Allah mutane na shigewa suna kallon ta. * Aafiyyah sanda ta fito daga cikin gidan Hon Boɗejo Maɗatai idanunta rufe ta shiga cikin mota tana jin wani irin zafi da raɗaɗi a zuciyarta kanta na mugun sara mata bata taɓa jin cewa Md macace shi ba sai yau, bata ɗauka lusarin shi ya yi girman hakan ba, ta yi takaicin zuwa da shi dama kimiyya ta saka ya raku ta zaifi taimaka mata. Wannan dalilin ya saka ta shiga mota tare da yi mata key ta jata da mugun gudu idanunta rufe zuriyarta har wani hayaƙi take yi mata, wata irin dauwamammiyar tsanar Hon Boɗejo Maɗatai ta samu gurbin zama a zuciyar Safiyyerh Abdul-Johar Marafa, ta ji ta yi masa tsana mafi munin tsana zai wahala ta ji ƙiyayyar abu balle na mutum amma a karo na farko ta ji idan akwai wanda taƙi jin gani bai huce Boɗejo ba. Motoci kawai take gani saman shimfiɗaɗɗen titin ba tare da sanin a gabanta suke ba ko bayanta ta san dai tabbas tana cikin tsakiyar motocin ne maimakon ta sassauta gudun motarta sai ta ƙara giyar motar hannunta ɗaya na rawa idanunta ya wani irin ƙanƙancewa saboda zafin da suke mata abarka da zabiya, ga wani irin zafi zafi da fatarta take yi, gabaɗaya ma bata san ina zata ba, sannu a hankali tunanin Ashraf ke dawo mata cikin kanta raɗau kamar yanzu. "Fiyya you're my wife ba ki da wani miji a duniya wanda ya shige Ashraf Baihaƙi Sharfaɗi, i love you Safiyyerh" Cije lips ɗinta kawai ta yi tana ci gaba da gudun motar tana ganin yadda mutane ke ɗago mata hannu alamar ta tsaya da gudun ko ta rage. Hawayen daya cika idanunta ya saka ta fara gani dishi-dishi. Sai ta sake jin muryar Ashraf cikin kunnenta "When are you gonna tell me, you love me?" "Ok.. I will wait. As far as you're with me Ashraf's love you" "Funny Fiyya....," Haka maganganun Ashraf suke dawo mata ɗaya bayan ɗaya sai ta sake jin muryarsa na cewa "Ah lallai yarinya kin girma wuyanƙi ya isa yanka, ni kike harara ko Fiyya? Zan kama ki ne. I love you Safiyyerh!" Hawayen da suka cika mata idanu sune suka sakko saman idanunta fuskarta ta yi jajur musamman karan hancinta, ta sake gudun motar kamar hakan yana sassauta zuciyarta "Fiyya Daddy ya zo yanzu ya tafi, ki tabbatar ba ki bawa wani damar mallakar FS WORLD ba" Horn ake danna mata amma sam bata fahimta ita bata san ma ma'anar horn ba, yanayin driving nata zai tabbatar maka da cewa she is good don har Dr Hash da J tafi su iya driving da nutsuwa akan titi. Kasancewar glasses ɗin motar tata a sauke yake sai ta ɗan kalli madubin motar a lokacin ta ankare da wata ɓakar mota da take biye da ita, cikin sauri ta sha corner sai taga baƙar motar ma ta shawo corner a hankali ta ce "Poor Boɗejo" tana cikin driving kuma ta hango motar sojoji har biyu sai kuma taga baƙar motar ta yi saurin yin wani lungu. Muryar wani ta ji yana cewa "Madam Please stop the car, tayar motarki na hayaƙi" Muryar Sergeant Timo ce. "Madam Please, akwai problem you have to stop the car ok?" Sai ma ta ƙara gudun motar lokacin da take fashewa da wani irin gigitaccen kuka, tana zame rolling kanta ji take duniyar ta yi mata zafi haka kawai. Paaah is here, Ummi, Ummimi her brothers amma zuriyarta tana faɗa mata she missed the part of the, ta yi rashin wani abu ta kasa fahimtar mene ya ɗauka Ashraf ne amma tunanin Ashraf baya hanata jin wannan kewar, wannan kuskuren, wannan muradin, wannan shauƙin, wannan soyayyar. Kuka take sosai kamar an yi mata mutuwa fuskarta ta rine sosai. A hankali ta ji saukar muryarsa a tausashe ya ce. "Are you mad?" Ta ɗan juyo ta kalle shi kaɗan, cikin idanunta kawai ya kalla ya ji zuciyarsa ta buɗe tare da bugawa. "Maamah stop the car" "I want to die, leave me....," she said "Ok, you can die idan kina so firstly stop the car, ki bani wasiyya" Sai ta juyo ta sake kallon shi, kallon juna suka yi sai ta marairace masa fuska ba tare data lura motar Sergeant Timo ya shiga gaban motarta hakan ya tilastawa motarta tsayawa, sai kawai ta kifa kanta ta cigaba da kuka gently ya fito daga bayan motar ba tare daya jira Sergeant Arma ya buɗe masa ba, hannunsa zube cikin aljihu fuskarsa babu ɗigon rahama saboda gashin Aafiyyah ɗin da yake a bayyane yana zuwa ya saka hannunsa ya ja motar yaji a rufe, sai ya tsaya can kuma ya zura hannunsa ta cikin motar ya buɗe ƙofar ya zuba mata idanu yana ɗan kame fuska, bai kula ta ba kawai ya damƙi hannunta zuwa motar da yake ciki, driver ɗin ya kalla yana motsa yatsunnsa guda biyu cikin sauri Sergeant Arma ya nufi motar Aafiyyah tare da kwaso komai nata ya zuba a bayan kotar AA MAJ kana ya shiga gaban motar ya jata da gudu, shima Sergeant Timo ɗin motar da yake ciki ya ja tare da marawa S.Arma baya domin sautin yatsun AA MAJ da ya yi yana nufin su yi nasu waje. AA MAJ ya buɗewa Aafiyyah gaban mota ya zaunar da ita shima ya koma ya zauna, a hankali ya fara driving madadin ya nufi gida sai ya nufi gidansa daya ajjiye Muhammad ciki lokacin daya isa Muhammad na zaune a gaban ƙatuwar computer dake jikin bango ya zubawa screen ɗin computer idanu hannunsa riƙe da handle yana buga game jikinsa sanye da wata red ɗin riga data kama damtsen hannunsa tare da wani 3gauter ya saka bandana a gaban kamaa laɓɓansa jajir sai fararen idanunsa tas. "Close the door" ya ce silently. Domin motsin da ya ji ya san cewa Aliyu ne ba kowa ba, banda shi babu mai zuwa cikin gidan. AA MAJ da yake tsaye bayan Muhammad yana ɗaukan cup gefen Muhammad ɗin ya shanshan a hankali. "Huh, cork ne" "I see" cewar AA MAJ. Muhammad ya cigaba da buga game ɗinsa ba tare daya juyo ba. Aafiyyah ta zuba masa idanu gabanta na faɗuwa sosai zuriyarta na rawa wani irin yanayi take ji na saukar mata a gaɓɓanta kanta na sarawa sai ta ji jinin jikinta na tsinkewa tare da gudana a jikinta cikin sauri. "Why are you here?" "Are questioning me Muhammad?" AA MAJ ya tambaya yana durƙosawa tare da fara duba wata computer ya zubawa titin idanu. Shi kuma Muhammad sai ya saki handle ɗin lokacin daya kammala game ɗin ya ɗaga shoulders ɗinsa tare da miƙewa tsaye hannunsa ɗaya cikin aljihu ɗaya kuma cikin sumar gashinsa ya ce "A titin ka same ta ko? Where she is?" Ya ce a hankali. Juyuwa ya yi gabaɗaya lokacin daya gama tsiyaya cork ɗin glasses ɗin ɗin hannunsa, ba ki ya buɗe da niyyar yin magana yana ɗan marairace fuska sai ya yi saurin yin shiru yana tattare fuska tare tsuke ta waje guda ya kame fuska sosai lokacin da idanunsa ya shiga cikin na Aafiyyah ɗin, kallon ta yake from head to toe itama ɗin kallon shi take yi ba tare da ƙiftawa ba. A hankali ya janye idanunsa ya nufar kujera ya zauna hannunsa riƙe da remote ya fara danne danne shi kansa bai san me yake dannawa ba, domin yana jin idanun Aafiyyah na yawo a jikinsa da kyau. Itama ɗin waje ta nema ta zauna kanta a ƙasa tana mayar da numfashi a hankali idanunta rufe saboda ciwon da kanta yake mata. AA MAJ ya juyo ya kalle su sai ya nemi waje ya zauna yana ɗaukan laptop tare da dudduba a hankali ya ce "Muhammad me kake yi haka?" Ganin yana ta danna remote da sauri Muhammad dai bai juyo ba, Aliyu na ƙaunar Muhammad yana jin kamar shi ya haife shi yana kula da dukkan lamuransa sosai ƙwarai. Sai ya ce "Ka gane number motar?" Nan ma Muhammad ya yi shiru kawai domin bai san me zai ce ba, bashi da niyyar magana sam. Cikin tsawa AA MAJ ya ce "Muhammad are you ok?" Nan ma Muhammad ya yi Aliyu na ƙoƙarin magana yaga Muhammad ya yi masa sharing number motar ta cikin laptop ɗin hannunsa sai kawai Maj ya miƙe tsaye yabar wajan ya nufi wani ɗakin nada ban domin samun nutsuwar yin abin da yake buƙata ɗin. Aafiyyah ta ɗan miƙe ta kwanta tana danna wayarta, shima ɗin Muhammad sabgar gabansa kawai yake yi. Almost 30 minutes ya ji shiru sai ya juyo a hankali idanunsa ya sake sauka akan Aafiyyah ashe bacci ta yi, ya gyara zamansa tare da zuba mata idanu kamar ya cinye ta a tausashe ya ce "Sophie!" * A hankali Saudat ƴar wajan Mama Zaituna take bin bango saboda yunwar data ci galaba a cikinta jiri na ɗaukan ta, ta gama yawan babu abinda ta samu yanayin idanunta ya nuna kukan da ta yi, tana dab da gida ta nemi waje ta zauna tana cigaba da kuka da riƙe cikinta dake murɗa mata. "Saudat..." Ta ji an kira sunanta ta ɗago kai da sauri Ɗan'yaro ta gani tsaye gabanta sai ta kasa magana ya ce "Me kike a nan wajan ke ɗaya? Kukan me kike?" "Don Allah ka bani kuɗi na siyi ko awara ce mutuwa zan yi yunwa nake ji, wayyo Allah na wayyo cikina" Ta sake rushewa da wani irin kuka, shi kam har ya gaji da mata kuɗi sai ya nemi waje ya zauna ya ce "Idan na ba ki kuɗin ke me za ki bani Saudat? Kullum a gida ke bakya cin abinci ne?" Ta yi saurin ɗaga masa kai idanunta cike da hawaye, ya dubi kyawun fuskarta sai ya girgiza kai ya ce "Ni kam gaskiya na gaji" "Don Allah, tun jiya banci komai ba" Ya ƙanƙantar da idanunsa cike da iskanci ya yi mitsi-mitsi da su akan Saudat musamman saman matasan ƙirjinta da suka ɗan fara tasawa ya ce "sai dai a yi ban gishiri na baka manda, na baki kuɗin siyan awara ki bani wannan matasan ƙirjin naki Saudat idan kikai hakan za ki samu kullum daga gare ni" ta yi shiru na rashin fahimta can ta ce "Idan zaka bani kuɗin shikenan ko na koma gida ba zan samu abinci ba, Malam baya bamu abinci kullum" Ɗan'yaro ya jinjina kai ya fiddo dubu ɗaya ya miƙa mata ya ce "Ki siya kin ji?" Hannunta na rawa ta amshi kuɗin tana miƙewa tsaye, jiri ya saka ta yi baya zata faɗi ya yi saurin tare ta yana shafo mazaunenta ya ce "kula" "Na gode Yaya" Juyawa ta yi da sauri da zumuɗin za ta ji awara ta ƙoshi yau sai ya yi saurin cewa "Jira Saudah" ta tsaya tana kallonsa ya ce "Kar ki faɗa a gida ni na ba ki, ko an tambaya ki yi shiru ko kuma ki nemi wani waje ki cinye awarar kullum kizo na ba ki kuɗi kin ki Saudena?" Ta washe fararen haƙoranta ta ce "To yaya" Sai ya ɗan shafa kansa ya ce "Yawwa Saudah. Kin san a waje akwai banɗakinmu na alamjirai ko?" Ta ɗaya kai sai ya ce "Yawwa. To a cikin banɗakin namu akwai ƙofa ta ciki, kuma idan an buɗe ƙofar kai tsaye mutum zai shigo banɗakin cikin gidan malam, banɗakinku ko?" Nan ma ta sake jinjina masa kai sai ya suɗe laɓɓansa ya ce "Yawwa Sadaula, ƙarfe goma daidai kar ki yi bacci zan zo miki da abu mai daɗin gaske, ki shigo banɗakin naku kamar za ki yi fitsari haka sai na buɗe ƙofar na shigo na ba ki abin daɗin" Saudat ta ɗan yi sak ta ce "Yaya abin daɗi da gaske? Ba zan ji yunwa ba ko? Yunwa na azbatar da cikina yaya" "Ke da jin yunwa har abada Saudah. Ƙarfe goma daidai ki cire komai na jikinki sai ki sako hijabi kamar zafi ya dame ki za ki watsa ruwa, wallahi abin daɗi zan ba ki Saudah kar ki faɗawa Malam kin ji? Daman kwana biyu ban zauna a makarantar allo ba" ta yi murmushi ta ce "Shikenan Yaya na gode sosai Allah Ya amfana" "Kar ki manta banda saka kaya hijabi kawai kin ji ƙarfe goma na dare" Tayi gaba tana cewa "Ban mantawa" * Da sauri yake takawa cikin emergency ɗin hankali tashe, ko uniform na likitoci bai saka ba, idanunsa akan wani Dr ya ce "Dr Hamza what is going on ka kira ni a gigice? Ina kan hanya zani airport ɗakko yayana" cewar I. QASIM Dr Hamza ya ce "Dr Qasim jikin patient naka ya motsa, ina daga nan na jiyo sautin na'urar dake ɗakin" Cikin wani irin firgice Qasim ya ce "What? Subuhanallahi. Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un innalillahi " ya faɗa yana yin gaba a hanya ya amshi green riga ya saka da hula da takalmi da safar hannu yana gama shiryawa ya nufi ɗakin zuciyarsa cike da tsoro da fargaba Allah Ya sa ba mutuwa ta yi ba, shikam idan ta mutu ya shiga uku ya lalace bai san da wanne baki zai yi bayani ba, kullum cikin burin sanar da ranar farkawarta yake da ranar da zai sadata da wanda ya dace tsoron sanin abin da yake faruwa cikin room ɗin da abin da kan iya samunta ya saka kimiyya tsayawa a ƙofar idanunsa cike da hawaye a hankali kuma ya buɗe ƙofar ya shiga yana shiga idanunsa ya sauka akan kyakkyawar farar ƙafarta. Muryarsa na rawa da ƙyar ya ce "S....S Wace a wajan Kimiyya? Waye Muhammad? Moh zai iya auren Aafiyyah? AA MAJ zai iya sakin Maamah? Manage.... Ban yini a gida ba 5k words ne. 💥Chapter 5: She got a pregnant. Gani ya yi ɗan cikinta na juyawa da ƙarfi ta cikin cikin, ya yinda na'urorin dake maƙale a jikinta suna bada sautin ƙara alamar majinyaciyar tana cikin critical condition ya sanya I. Qasim yin shiru a lokacin daya buɗe baki da niyar faɗin “Subuhanallahi” a kiɗime kuma ya nufe ta ya fara duba abin da ya yi sanadiyar tashin ciwon nata cikin ƙaramin lokaci. Numfashinta ne gabaɗaya ya tsaya a gigice ya sake fita ba tare da ya yi magana ba, ya nufi ɗakin tiyata yana yi wa su Dr Hamza alama da hannunsa, shiryawa suka yi cikin sauri cikin green uniform. Dr Hamza ne ya kalli Kimiyya kafin ya ce "Dr Qasim what is happening?" "Emergency operation" Qasim ya bawa Dr Hamza amsa a lokacin da yake tura wani bed zuwa ɗaya room ɗin da mara lafiyar ke ciki. Da taimakon Dr Hamza ya samu ya yi exchange nata zuwa bed da zai kaita operation room ɗin, har yanzu kuma da taimakon na'urar shaƙar iska numfashinta ke tsaye cak a ƙirjinta, kawo lokacin kuma abin dake rayuwa a cikin nata ya fara haƙurtawa kansa da yin motsi kaɗan kaɗan mararta ke harbawa abin dake alamtawa Qasim cewa the baby is still alive, he can save the baby. Tura ta ya da sauri zuwa ɗakin tiyatar, yana zuwa aka sake sauya mata gado shi kuma ya fita da sauri saboda wani irin rauni daya mamaye masa zuciya, wani wanda ya jima bai motsa zuciyarsa ba, raunin dake ƙoƙarin sashi zubar da hawaye daga cikin idanunsa. Ya ɗan jingina da cikin bangon dake corridor ɗin daya tsaya kansa a ƙasa, thinking what if ta mutu wajan aikin? What if yaran cikinta ya mutu? What if aka rasa duka biyun? Da wanne baki zai yi bayani bayan ya jima yana jiran ranar da zata fahimci waye a kanta dawa kuma take tare, ranar daya jima yaga ya haɗata da wanda ya dace, ranar da zata goge dukkan wani tunani da shakku a cikin zuƙatan wasu, ranar da dukkan wani hijabin mugun abu da aka rufe shi da shi zai yaye, ranar da mutane da yawa zasu shiga inuwa wasu su fito rana, ranar da gaskiya ce kawai za ta yi aikinta, ranar da baƙin cikin wasu zai fara, ranar da gaskiya zata kore ƙarya. "Dr Qasim mu je mana" Ya ɗago jajeyen idanunsa masu nauyi ya kalli Dr Hamza dasu kafin ya girgiza kai ya ce "Ku yi komai Dr Hamza i will wait here, zan yi addu'a" Sai Dr Hamza ya dafa kafaɗar Qasim cikin kulawa da tausasawa ya ce "Qasim Ibrahim David. You're a doctor, a good doctor da muke da shi a cikin kanon nan da wannan asibitin, babu kalar ƙalubalen da baka gani ba, babu kalar ciwon da baka gani ba, bana jin idan baka ƙarfafa mana qwwia ba ya zamana mune masu ƙarfafa maka, at least you have to be with her side, sai mu yi aikin ba, ka yi keeping nata company?" Qasim ya yi shiru. "Please kimiyya" Sai kimiyya ya girgiza kai ya ce "Dr Hamza duk juriyar likita da nuna rashin tausayinsa mukan samu kan mu cikin rauni da sarewar tsammani idan aikinmu ya biyo ta kan jininmu ko wani namu, bana jin zan iya jure ganinta cikin wannan halin, idanuna, idanun Qasim Ibrahim kimiyya ba za su jure ganinta ba, tsoran faruwar wani abin nake...," cikin sauri Dr Hamza ya katse Qasim da faɗin. "In sha Allah lafiya lou zamu gama, nothing will happen, nothing" "I hope so, i pray for it" cewar Qasim. Dr Hamza ya dubi yadda ogan nasu duk ya gigice daga kiran waya ɗaya, tunda ya kawo marar lafiyar hankalinsu yaƙi ɗaya bashi da nutsuwa baya bari kowa ya je wajanta har wasu securities ya saka na musamman suna kula da sashin da take, ko wacece wannan tabbas akwai wani dalili daya saka I. Qasim lura da al'amuranta da gaske. Sai Dr Hamza ya samu kansa da tambayar "Who is she to you Dr?" Qasim couldn't speak ya nufi room ɗin bakinsa ɗauke da addu'a, sanda ya shiga an gama shiryata har an yi mata allura idanunta da ya yi nauyi take buɗe su da ƙyar tare da sake lumshe su, idanun sun yi ƙanana tare da kumbura, ɗan motsin hannun likitocin dake sauka cikin kunnenta sai take jin kamar hayaniyar mugawayen mutanen, kamar kuma yaushe komai ke faruwa. Hawaye ne masu zafi suka fara bin gefen fuskarta tare da gangarawa cikin kunnenta, a hankali kuma dr Hamza ya raba tsakaninta cikinta zuwa ƙirjinta Qasim kuma ya zagaya tare da neman waje ya zauna dab da kanta, bata iya juya kanta domin a tokare wuyanta yake yi. Qasim ya dinga kallon ta, ya kasa aiwatar da komai har sai da Dr Hamza ya zuro hannunsa tare da wara yatsu biyu kana ya ɗan fara magana a tausashe. "Buɗe idanunki, in sha Allah....," sai ya kasa cewa komai ganin jikinta na rawa tana mimmiƙewa hannunta na buɗewa, alamar alkawarin da ta yi wa Ubangiji na warware alamu ne da when all is gone, alamu na this is my time to leave. Hannunsa ya saka ya riƙe nata yana duba kansa tare da duba computer ɗin jikinta. "Dr Hamza.... Dr Hamza" nan ma ɗin shiru ya yi yana sake damƙe hannunta hawayen dake maƙale a idanunsa ya samu damar sakkowa. Shuɗewar mintuna 20 kafin Dr Hamza ya ajjiye babyn hannunsa, cikin sauri wani dr ma ya yanke cibiyar ɗaya babyn yana cewa "Call nurse Zuby for me, yaran sun wahala muna buƙatar a saka su cikin kwalba" ya yi maganar a hankali yadda ba zata ji ba har lokacin da aka gama ɗinke ta. Sai dai cikin rashin sa'a ana gama ɗinkewa jikinta ya hau jijiiga da sauri kimiyya ya miƙe da hannu yake nuna masu komai sai ya ji ta cafki hannunsa ta riƙe gam, ya juyo ya kalleta a lokacin kamar almara itama shi ɗin take kallo, yanayin kallon ya daskarar da jinin jikinsa ya kasa jan numfashi, kallon sani take masa, kallon ka taimaka mini take masa, kallon ka kula da abin da na haifa take masa, kallon neman wani abu a tattare da shi take masa, kamar yadda take ƙoƙarin yin magana haka numfashinta yake ƙoƙarin barin jikinta. Da sauri Dr Hamza ya janye Qasim suna fita Qasim ya shige office ɗinsa ƙafafuwansa na rawa ya zuba akan ƙafafun ba tare da sanin abin ya taɓa zuciyarsa har haka ba sai da ya ji ya fashe da wani irin kuka, kuka yake da dukkan ƙarfinsa domin bashi da tabbacin tana raye. "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un! Allah na tuba, na tuba na tuba kar ka tuhume ne da laifin ɓoye Muhimmin abu ga wani. Astagafirulla!" Ya kifa kansa jikin kujerar dake kusa da shi, sosai zuciyarsa ke masa ciwo har ya cinye awa guda a wajan kafin ya ji an buɗe ƙofa. Dr Hamza ya zauna ya ce "Ban san ya take ba gaskiya, babies ɗin na ɓangaren jaririyar sun sha wahala sosai..," "It's okay. I need privacy" "Shikenan, amma ka kula Please" Dr Hamza ya ce yana buɗe ƙofa tare da ficewa daga cikin office ɗin Qasim. * Adadin awannin data ɗauka tana bacci a saman kujerar adadin awannin daya ɗauka hakimce a saman kujerar ƙafarsa harɗe yana kallon fuskarta, kallon ta yake da kyau baya ko ƙifatawa, baya motsi balle tari wani irin kallo yake mata kamar mai nazarin jikinta ko a tunaninta an sauya tane ko wani abu ya samu jikin nata ne. A hankali yaga ya marairace fuska tana sake mannewa jikin kujerar numfashinta na sauka a hankali kuma bacci take peacefully. Muhammad ya jinjina kansa yana ɗan cije lips kafin slowly ya buɗe bakinsa ya ce. "Ba ki da gaskiya Sophie, Allah ba ki da gaskiya Sophie" "Wanne rashin gaskiya?" Maj ya tambaya yana rufe ƙofar ɗakin daya shiga tun ɗazo tare da neman kujera ya zauna ya ɗan juya kaɗan ya dubi Aafiyyah yaga bacci take yi fuskarta na kallon direction ɗin Muhammad. "Muhammad me ya sa kake bibiyar Maamah all the time ne?" " I don't know" cewar Muhammad yana ɗan tsuke fuska sosai. "Meka sani game da sace ta da aka yi?" Maj ya tambaya. Muhammad ya ɗan dire ƙafarsa ɗaya ƙasa kamar mai tsoron sauke ta saman carpet ɗin kafin ya ce "I told you set up ɗinta ne" shima Maj ya ce "Ta ce kidnapped ne" Da sauri Muhammad ya juya ya kalli Maj Aliyu, domin tunda Maj ɗin ya shigo cikin parlourn bai sake kallon Aafiyyah ba sai ya ɗan bubbuɗe idanu ya ce "For real?" Sai kuma ya fara girgiza kansa gently ya ce. "Liar.... "A liar....." share maganar Maj ya yi ya fara jan Muhammad da magana saboda ɗeɓe masa kewa, jefi jefi Muhammad kan ɗan girgiza kai ya ce "Ohhh" ko ya ce "Yaya kenan" wani sa'in ya ce "halina da ɗabi'una nawa ne, na Muhammad ne kawai, ni kawai" magana Maj ya yi sai ya ji Muhammad ya yi shiru kamar ruwa ya cinye shi, a hankali Maj Aliyu ya ɗago kansa daga kan wayarsa sai ya lura Muhammad lokaci guda yake sauya hali yanzua he looks so dolls and moody ya sunkuyar da kansa ƙasa. Sai ya lura ashe Aafiyyah ya farka daga baccin. Itama Aafiyyah a cikin baccin ta ji kanta da ƙwaƙwalwarta sun yi fresh kamar ana wanke mata dattin kanta, domin tunda I. Qasim kimiyya ya fara yi mata allurar take yawan bacci kuma sai ta daɗe cikin bacci, wani ikon Allah kuma bata fiya tunanin abubuwan da suka shige ba, kawai nutsuwa ƙwaƙwalwar ke samu. A cikin baccin kuma take jin muryar Muhammad a tausashe yana yin magana kamar baya so, baya da hargagi cikin maganarsa sam har ta kasa jurewa ta buɗe lulu eyes ɗinta masu laushi wanda zara-zaran gashin idanun suka kwanta saman fatar wajan, idanunta ya sauka cikin na Muhammad da yake ɗan jingine saman kujerar yanayin yadda ya zauna kamar kwanciya ya yi, hannunsa harɗe a ƙirjinsa yana ɗan girgiza ƙafarsa a hankali, 4eyes suka yi, ya ɗan kalle ta da kyau for a while sao yaga ya ɗan buɗe masa ido. "Ba ki da hankali Sophie" ya ce a zuciyarsa yana janye idanunsa tare da yin shiru, har Maj Aliyu na magana yana jinsa. Itama Aafiyyah ɗin janye nata idanun ta yi, tana sakko da ƙafafunta zuwa ƙasa cikin sauri ta ɗauki mayafinta ta yi rolling ta ɗauki wayar ta. Without looking at her direction ya ce. "So....?" "Gida" ta bawa Maj amsa very shortly. Wayarta ce ta fara ringing ganin sunan I. Qasim ya saka ta ɗan a kasalance ta ce "Qasim lafiya?" Ta cikin wayar muryarsa na fita da ƙyar ya ce "Kina ina Maamah?" "Lafiya?" Ya ce "I want to see you, I want to talk to you please" ta ɗan yi shiru. Muhammad kuma ya miƙe ya nufi bedroom daidai nan kuma ya ji muryar I.Qasim na sauka cikin kunnensa, da ɗan sauri ya tsaya cak yana zubawa ƙasa idanu zuciyarsa na bugawa da ƙarfi a ƙirjinsa. Kansa ya ɗaga ya kalli gefen Aafiyyah sanda kimiyya ke cewa "Idan kin koma gida ki sanar mini, don Allah Fiyya" "I will, zan yi" Muhammad ya juya ya kalli Maj, sosai shima Maj ɗin ya ji muryar kimiyya raɗau a kunnensa sai yaƙi ɗago kai duk da a jikinsa yake jin idanun Muhammad. Sai ya miƙe yana ajjiye abin hannunsa kai tsaye ya nufi ƙofa cikin takunsa na sojoji a ɗan ƙarfafe kafaɗunsa na buɗewa, daman Aafiyyah tuni ta fice tuni hankalinta ya yi gida sai yanzu ta tuna meeting ɗin da za ta yi da ma'aikatan FS WORLD. Maj na ƙoƙarin fita ya ji Muhammad ya ce "Wannan shine dalilin ajjiye ni a nan? Waye ni?" Ya yi maganar a kumbure idanunsa na shigewa ciki sai Maj ya yi masa shiru, cikin sauri da zafin nama Muhammad ya sha gaban Maj ya ce "Waye ni?" Ya ce jikinsa na rawa zafin zuciyarsa ya bayyana a fili alamu dake nuna haƙurinsa da kawaicinsa ya gama ƙarewa, ya dinga kallon Maj kamar yadda Maj ɗin shima ke kallon Muhammad kafin da ƙarfi ya ce "Waye ni?" Maj ya ɗora yatsa a bakinsa ya ce "Quiet... Quiet!" "Why? Why me ya sa?" "Waye kai kake tambaya?" Maj ya ce "Exactly as i said waye ni?" Sai Maj ya ce "I don't know" Muhammad ya jinjina kai yana murmushi idanunsa jajur yana yin baya a hankali ya ce "Ok ok, zan fita waje zan fita duniya duk me zai faru ya faru duk abin da zai faru i don't care" Maj ya kalli Muhammad yana ganin taurin kai ƙarara a fuskar yaron sai ya kasa cewa komai kamar yadda ya kasa tsayar da Muhammad daka ƙoƙarin fita daga cikin gidan. Muhammad na buɗe ƙofa Maj ya ce "Kana fita zan harbeka" sai Muhammad ya yi jim ba tare daya juyo ba ya ce "To bisimillah" Maj ya sakawa Muhammad ƙafa kana ya finciko shi baya ya ɗaga hannunsa ya zabga masa maruka masu sanya mutum gigita da sauri ya fara jansa zuwa ɗaki yana shiga ya cilla Muhammad ciki tare da janyo ƙofar ya sanya mata password. AA MAJ ya sauke numfashi shima nasa idanun a juye kansa na juyawa yana jin kamar lokaci ya yi kamar kuma da saura ɗin cikin sauri ya fita ya samu Aafiyyah zaune cikin motar ta kifa kanta a cinyoyinta bai kula ta ya yi wa motar ke a hankali ya fice daga cikin gidan bakiɗaya, har suka isa ba wanda ya kula ɗan'uwansa duk da kasancewar su miji da mata na sunna. Aafiyyah ta samu Ummi zaune a parlo tana waya, ganin waya take yi sai ta nemi waje ta zauna har ta kammala kafin ta ce "Maamah sai yanzu?" A hankali Aafiyyah ta ce "E. Barka da yamma Ummi" "Yawwa Maamah je ki yi sallah ki ci abinci ina buƙatar ganinki ok?" Ta jinjina wa Ummi kai kana da nufi upstarts. Handbag ɗinta ta ajjiye wajan ajjiye bags ɗinta ya ajjiye takalmin da komai, a gurguje ta yi wanka kana ta ɗaura alwala ta gabatar da sallah sai ta samu kanta da yin addu'a mai tsayi tare da roƙan Allah ya bayyana mata abubuwan da suke ɓoye ya cire daga hijjabin makkuwa da take ciki, ya bata ikon yin abubuwan da suka dace ta ji tana buƙatar yin azumi akan wannan dalilin don haka da ƙudurcin ɗaukan azumi a daren yau ɗin duk da cewa tana yin na Alhamis da Litinin. Kiran Kinal ta gani kamar za tabi bayan kiran sai ta share, haka ta ji zuciya ta janta zuwa ga pictures ɗin wayarta a hankali ta shiga ta fara gani, wasu tana gadon asibiti wasu kuma tana cin abinci wasu jingina da bango wasu tana kwance jikin J. Sai ta dinga tunanin yaushe ne ta yi wannan picture ɗin me kuma ya same ta har haka tana ƙoƙarin shiga picture ɗin da I. Qasim kimiyya ya tura mata na makarantar Fgc sai ta ajjiye wayar ta nufin zata je ta dawo. Miƙewa tsaye ta yi jikinta sanye da silk body short mai ɗan sulɓi sumarta ta sauka a baya kanta ta zubawa idanu ta cikin madubin dake bedroom ɗin nata. Komai da komai nata take kallo daga sumar kanta da take ja zuwa girarta idanunta ya sauka akan siririn hancinta zuwa madaidacin bakinta mai ɗauke da pech ɗin lips idanunta ya sauka saman ƙirjinta ita sai ta dinga ganin kamar ba haka ƙirjin kowa yake ba, musamman nata dake cike sosai a ƙirjinta ita har ɗan damunta suke yi har tunani take ko mene amfanin su? Sai kuma ta yi murmushi idan ta tuna wani abu sosai. Duk dauriyarta a wannan karan tana rasa ƙwarin zuciya dana qwwia idanunta na cika da hawaye amma ta kasa zubar dasu tun ranar data kama Scorpion take jinta da rashin walwala zuriyarta a cunkushe tun kafin hakan ma tunda ta tsinci kanta a Safiyyerh ta yanzu takan rasa meke damunta meke going a zuciyarta, da farin sai ta ji ƙuncin zuciyarta baya rasa nasaba da auren Ashraf idan ta yi auren zuciyarta ke faɗa mata kamar bata kyauta ba, bayan banu Ashraf sai ta ji auren Maj kamar wani babban zunubi da kuskure ne a gare ta, yanzu gabaɗaya ta rasa meke damun zuciyarta ta rasa ƙarfin qwwia. "Safiyyerh who are you? Wace ni?" Ta tambayi kanta a hankali tana rungume ƙirjinta tare da zagaya bedroom ɗin a hankali kuma ta nemi waje bakin gado ta jingina da frame ɗin bed ɗin cikin rashin sani wani baccin ya sake ɗauke ta a nan. A hankali ya turo ƙofar bedroom ɗin nata cikin nutsuwa da niyyar yin magana da ita sai yaga bacci take yi. Ya zuba mata idanu sosai,ya hango ramarta a fili sai ya ji ko ƙawa zuci ne irin na iyaye ke damunta? Paaahh ya dinga kallon ƴar tasa cike da tausayawa kafin a hankali ya gyara mata da kwanciya ya ja mata duvet ya ɗan zauna a gefen gadon yana kama hannunta da yawan lokaci ya kan rasa me Aafiyyah take so? Me kuma take buƙata a rayuwarta wanda ya gaza yi mata shi? Mene damuwar Maamah? Me take so? Ya sauke numfashi a hankali ya ce "I am sorry Safiyyerh i am sorry Maamah will you forgive your father?" Ya jima zaune yana kallon ta kana ya kalli wayarta, wayar ya ɗauka ya fara duba pictures ɗin wata iriyar zabura ya yi lokacin da idanunsa ya sauka akan photon Fgc tsinannen sunan daya tsana a rayuwa fiye da komai, da sauri kuma ya miƙe jikinsa na rawa soaai ganin pictures ɗin Aafiyyah sanye da kayan makarantar Fgc gasu Kinal da kimiyya wajan pictures uku zuwa huɗu innalillahi wa'inna ilaihirraji'un! Paaahh ya dinga maimaitawa a zuciyarsa ina ta samu pictures ɗin nan? Bayan ya toshe dukkan wata hanya da zata saka ta fahimta ta haɗa alaka da Fgc ɗin balle mutanen cikinta? Ba dai Aafiyyah taga wannan pictures ɗin ba? Wata zufa ce ta fara tsasttsafo masa a jiki ta zallar tashin hankali domin a yanzu abin da Dig Abdul-Johar Marafa ke tsoro da gudu shine dawowar Maamah cikin hayyacinta ta koma old Safiyyerh ɗin data nemi kassara zuciyoyinsu a kanta zuciyarsa ta kusan bugawa a kanta ya zubar da hawaye a kanta Ummi ta samu hawan jini akan ta dukkan wata walwala ta Marafa's family ta tsaya cak sun shiga tashin hankalin mafi ƙoluluwa. Cikin sauri Paaahh ya goge pictures ɗin tas ya ajjiye wayar da sauri ya fita yana kiran Dr Hash suka ci karo a main parlor dawowarsa kenan daga asibiti Paaahh ya ce "Meet me at my room" Ya ce yana tafiya da sauri kana ganin yanayinsa a yanzu ya sauka daga asalin jami'i Dig Abdul-Johar ya koma Professor Abdul-Johar. Dr Hash ya marawa Paaahh baya yana shiga ya ce "Gani Daddy" "Hashim!" Paaahh ya kira sunan Dr Hash a ƙagauce hannunta goye a bayansa ganin yanayin na Paaahh ya saka Dr Hash cewa "Ba dai Maamah ba?" "Ita" Paaahh ya furta idanunsa jajur yana haɗiye damuwar a zuciyarsa sai Dr Hash ya ce "Daddy mu yi magana opening ta fahimta mana?" Shi dai Paaahh bai ce komai ba idanunsa zube akan Dr Hash "As long as za'a cigaba da yi wa Maamah wannan allurar za'a iya cigaba da rasa tunaninta gabaɗaya har abada ba zai yi recovering ba, hakan yana nufin zata iya samun matsalar tunani dana ƙwalƙwalwa" murmushin takaici kawai Paaahh ya yi ya ce "Kana son ka ce na bar Maamah ta dawo tunaninta? Kasan me hakan yake nufi? Kasan wanne abu hakan zai janyo Hashim?" Dr Hash couldn't speak kallon mahaifin nasa yake kawai. Paaahh ya jinjina kai ya ce "Wannan fara'ar da nake yi ta dole ce, wannan murmushin da nake yi na dole ne. A cikin ƙirjina nake jin zafi da raɗaɗin halin da Maamah ta shiga da halin da muka shiga, Ubangiji ne kawai ya kawo mana mafita a lokacin da muka rasa mafitar wallahi wallahi zuciyata kullum cikin kuka take idan na tuna wacece Maamah akwai raɗaɗi da zafi a zuciya ka ji cewa kamar ƴar daka haifa da cikinka tafi ƙarfin ka. Ba don bana son Maamah ba, ba don bana ƙaunar ta ba, i will do this saboda ita, i will do this for her love, i will do this just to save her life. Allah idan Maamah ta yi recovering zan iya jin kamar zan sallamata ne, wallahi sai tafi ƙarfinmu sai jikinmu ya faɗa mana. Maamah stubborn ce mai tsananin wayo ko a yanzu akwai abin da yake damunta wanda na rasa mene" "Ask Junaid, zai iya sani" Dr Hash ya ce a sanyaye na jin tausayin mahaifin nasu. A hankali Paaahh ya juya ya kalli frame ɗin huton Aafiyyah ya yi ɗan jim kana ya ce "Har abada uba ba zai taɓa cutar da jininsa ba, ba zai taɓa zaluntar abin da ya fito daga jikinsa ba, ban yi haka don na cuce ki ba Maamah don Allah ki fahimce as your father, mu iyaye ko zamu rasa wani abu mukan rasa ne domin cigaban yaranmu mu dai burinmu yaranmu su yi nasara" "Daddy mene benefit ɗin barin Maamah cikin halin mantau?" Paaahh ya juyo ya kalli Dr Hash idanuna na cika da ƙwalla muryarsa na rawa alamar karaya ya ce "Hashim tambaya kake yi? Ka manta cewa Maamah ciki ta yi? Cikin haihuwa ko ka yi makkuwa ne? Ta ya zan so ta san cewa ta yi ciki? Duk wanda ya san wannan ba zai taɓa auren ɗiyata ba, ba ina nufin cewa zan zalunci wani bane, ka duba girman da ake bani musamman matasa, ka duba yadda nake hani ga shaye-shaye da wanne idanu zan kalli jama'a idan suka ji labarin cewa ƴar cikina ta yi ciki kuma ta yi shaye-shaye? Ba zan iya ba, ba zan iya ba wannan abin ya yi mini nauyi a zuciya da harshe" ya sunkuyar da kansa a hankali ya ciro hanky ya goge hawayen idanunsa. ya jima yana share hawaye kafin ya ɗago kai ya yi murmushi ya ce. "Tell me something Dr Hashim Abdul-Johar Marafa, da gaske na zalunci rayuwar Safiyyerh ne? Na kasa fahimta wallahi" "Daddy don Allah ka daina zubar da hawaye akan Maamah" "Astagafirulla! Ta ya zan zubar da hawaye domin ta bana fatan hakan domin azaba ce a gare ta, mikin dake zuciyata ne ya tashi. Wannan dalilin ya saka na haɗa aurenta da Aliyu, na san zai faruwa Maamah asiri...," Maj Aliyu da Ummimi da suke bakin ƙofa suka kalli juna, idanun AA MAJ kamar ya zazzago ƙasa jiyiyon kansa sai harbawa suke yi jikinta na wani irin rawa ya yi yunƙurin buɗe ƙofar ɗakin Ummimi ta yi saurin riƙe masa hannu tana girgiza masa kai idanunta hawaye ne kawai yake zuba ciwonta na neman tashi "Ni ne ba jinin Daddy ba? Ni ne... Da gaske ni ne?" Ummimi ta kasa magana halin da ta ji cewa wai Maamah ta shiga yafi girgiza zuriyarta fiye da tambayar da Gadanga ke jefa mata. Maj ya yi saurin barin wajan tare da fita daga gidan bakiɗaya. Kuka sosai Ummimi ta yi a bakin ƙofar me ya saka ta bar Maamah hannun Paaahh? Shin ita ɗin wacce irin uwa ce? Me za ta cewa Maamah innalillahi wa'inna ilaihirraji'un! Sai kuma ta miƙe da sauri ta buɗe ƙofar ɗakin a gigice Paaahh da Dr Hash suka kalli juna cikin gigita dr Hash ya yi saurin ɓoyewa a bayan paaahh Baki Paaahh ya buɗe zai yi magana sai Ummimi ta buɗe idanunta ta ce "Kamarya?" "Zahiyerh Please ki saurare ni....," Sai ta katse shi da cewa "Kamarya?" Nan ta fara magana cikin turanci domin idan tana son magana mai tsayi da turanci take yi ko German language idan ta yi ta yi sai ta nuna Dr Hash da jikinsa ke rawa. "Don Allah don Allah don Annabi Zahiyerh ke saurare ni ta ya za ki fahimta baki saurara ba we need to talk please" "Maimaita mini kamarya? Ka cuce ni Abdul-Johar ban san me zan ce maka ba.." ta juya ta Dr Hash ta ce "Kai kuma zan saka a ɗaure mini kai...," kuka ta fashe da shi sosai sai ta fara tari tana riƙe kanta saboda dishi dishi take gani ta cikin idanunta kafin ta yanke jiki ta faɗi a wajan. * Alhaji Wada na zaune gaban tsohuwa Abbasa yana yi mata bayanin abin da yake tafe da shi kafin ya ɗora da "Muna buƙatar wannan kujerar muna tsananin son ta dubban al'umma sun dogara gamu, idan har Eng Ali wali ya ci zaɓe ba ƙaramin tashin hankali za'a shiga ba, muna so duk yadda za'ayi a san cewa Hon Maɗatai shine ya yi galaba, kana a sawa mutane soyayyarsa a zuciya, a kuma rufe idanun mutane daga ganin aibunsa wannan shine burinmu" Abbasa kanta a ƙasa ta jibga wani babban buzu a kanta hannunta riƙe da sanda ɗaya hannun tana jan wani carbi mai dubu zanƙalele taƙi ɗago kan nata. Hayaƙi Alhaji Wada ya gani yana fita ya cikin bakinta tare da mamaye bukkar gabaɗaya kafin ya fara jiyo kukan jarirai na tashi tun yana ji a hankali har ya fara ji da ƙarfi. Ihu ya fasa ganin jariri a hannunsa jikinsa da jini face-face ji ya yi wani irin fitsari na bin wandonsa ya ce "Mene wannan? Don Allah ki cire mini shi ki rabani da shi" Ɓat! Jinjirin ya ɓace dashi da jinin jikinsa gani ya yi tsohuwa Abbasa ya ɗago kanta ai bai san sanda fitsarin ya ƙarasa fitar da kansa daga jikin mararsa ba. Sai ta ƙyaƙyace da dariya kafin wani kuka ya cika bukkar kuka mai kama da kukan neman taimako carbin hannunta ta ajjiye ta ce "Zaɓi ɗaya" Hannunsa na rawa ya ɗauki ɗaya, ya miƙa mata ta amsa ta sake cewa ya ɗauka sai da suka yi sau uku ta yi saurin sakin carbin a gigice kana ta shafa ƙasa da zana a yatsu biyu can ta ce "Ya naga ganshi a gidan shaɗaya bayan Ɗan'adam baya zuwa gidan shaɗaya. Zunubi roma" Shi dai Alhaji Wada ya kasa motsi ta ce "Ubangidan naka yana da wani amini can a baya wanda a yanzu basa tare, wannan aminin ya taɓa tarayyar aure da matarsa Laylerh wannan dalilin ya saka Ali wali yake ƙoƙarin yin galaba akan Madatai domin samun daidaito dole ne Maɗatai ya kwanta da yarinyar ƴar wajan Ali wali mai suna Sabrina Noor" Jikin Alhaji Wada rawa kawai yake yi ya buɗe baki zai yi magana tsohuwa Abbasa ta buga masa tsawa ya ce "Ɗan matsiyaci mai mugun halin masifa saurarawa tsohuwa Abbasa ta gama jawabinta ga hallakakken bawa mai son duniya fiye da lahira lallai sai samu nasara domin samun nasara dole ya kwanta da Noor ƴar Ali wali sauran bayani zan saka fulani ta kawo maka" Alhaji Wada ya ce "A'a don Allah bana buƙatar ganin wata Fulani kiwa Allah ki mini rai kar ki turo mini Alhaja" "Kaga jinin fir'auna da hamana kaga jinin ibni salu baka ji tsoron Allah ba sai na Fulani tashi ka fice ka bawa tsohuwa Abbasa waje" ta bugawa Alhaji Wada tsawa ya fice da rarrafe jikinsa jiƙe da fitsari. * Ƙarfe goma daidai Saudat na cikin banɗakinsu sanye da ƙaton hijabin Mama Zaituna sai murmushi take yi yau ma zata ci abinci kuma harda tsire shi ya sa ma da Mama Zaituna ke yi mata faɗan ta je gidan Hanne ko zata samu ƙanzon awara ta ƙanƙare ta ci sai bata damu ba domin ta san Ɗan'yaro zai bata. Ƙofar banɗakin waje na alamjirai ta ji ana buɗewa tana tsaye har ya buɗe ya shigo, jikinsa sanye da jallabiya hannunsa riƙe da baƙar leda kasancewar banɗakin kuma a bushe yake Saudat ta share tas sai babu wani ƙazanta. "My Saudat na Oyoyo?" Murmushi ta yi ta ce "Kai yaya" Sai ya ɗan ɓata rai ya ce "Bani son yayan nan da gaske Saudat" ya ce yana ɗan kashe mata idanu ta hasken wutar nepa gidan shiru iyaye na can baki sake suna bacci. "To shikenan" Ya ɗan kamo hannunta yana murzawa murmushi ƙasa-ƙasa ya ce "Ya tsiren jiya to Saudalana?" "Daɗi sosai, yau ma da shi ka kawo mini ne?" Ya jinjina mata kai ya ce "E, har da rufaida mai sanyi amma yau tukucina bana iya sumbata bane,kiss ɗin nan zautar dani yake da gaske Saudat ina buƙatar ƙari" Saudat ta ɗan shagwaɓe fuska ta ce "Uhm to mene? Me kake so?" "Ina buƙatar runguma mai sanyi, ina buƙatar matasan ƙirjin nan, ki mini shafa a waje na musamman ni kuma na yi al'ƙawarin zan siya miki rangaɗeɗiyyar atamfa da takalmi" wani irin daɗi Saudat ta ji domin rabon data saka sabon tufafi a rayuwa har ta manta, Malam ba ya yi Mama bata yi musu sai ta ji muryar Ɗan'yaro yana cewa "Samawa kan ki lafiya da hijabin nan Saudat, barni na miki kallon ƙurilla" ya saka hannu ya zare hijabin nata sai ga jikin Saudat ya bayyana tsirara ƙirjin nan daidai ma sha Allah, ta yi saurin dira ƙafa ta ce "Ba kaya jikina fa?" "To nima ai yanzu za mu yi anko ai" bata ankare ba taga ya zare jallabiyar jikinsa, ihu ta kusan yi tana rufe idanunta ganin namiji haihuwar uwarsa ba kaya abinda tunda take a rayuwa bata taɓa gani ba, cikin sauri ya janyota jikinsa yana rufe mata bakinta da hannu daidai lokacin aka ɗauke wuta a hankali ya ce "Ya za ki buɗe mini hijjabin sirri Saudat, idan bakya so shikenan sai na rabu dake kinga ki yi ta zama da yunwa har ya suɗe miki kayan ciki ki mutu tunda iyayenki babu mai baku abinci" cikin sauri ta ce "A'a don Allah ka rufa mini asiri na tuba yunwa tana wahalar dani sosai" "To zo ki ji" Kissing ɗinta ya fara, yana shafa ƙirjinta wani irin abu ya kewa Saudat wanda tunaninta da hankalinta bai kai ga sani ba, amma babu yadda ta iya ganin yana tura abu ta ƙarfin gaske yana danna mata marasa ya saka ta saki kuka ta ce "Wayyo yaya, wayyo gabana baffi zai cire ba zan iya ba wayyo Allah" ta fita hankalinta sosai ya riƙo ta ya ce "Raguwata Saudala ba yi zan ba, titi zan fara sharewa sannu a hankali har motata ta samu nutsa kai cikin lungu ta shimfiɗa titi, kar ki yi kuka idan na yau na yi gobe da jibi gata sai na shiga fada, ina sake gargaɗi da kar ki faɗawa kowa kin ji ko?" Tana shassheƙar kuka ta ɗaga masa kai ya shafa kanta ya ce"Yawwa gonata daina kukan to minti biyu" Shiru ta yi hawaye na bin fuskarta azaba take ji sosai da raɗaɗi har ya gama abin da zai yi ya sake ta. Hijjabin ya saka mata yana shafo ƙirjinta da yanzu kawai ya ƙara tasawa ya ce "Ya kamata a fara sanya kayan marmarina a gidansu gaskiya" ta yi masa shiru ya ɗauki ledar daya kawo mata abu fal ya damƙa mata "Na gode. Allah Ya amfana" ta ce muryarta na rarrabewa kamar za ta yi kuka sai ya ce "Ya naga kina fushi ko na miki dole ne?" Ta girgiza kai ya ce "to yi murmushi agwalumata" Murmushi ta yi masa mai sanyi ya saka jallabiyarsa ya ce "Ki wanwanke ƙafarki da fuska kamar wanka kikai kin ji ko" ta jinjina masa kai ya buɗe ƙofar waje ya fita. Yana fita ya samu malam kishingiɗe yana gyangyaɗi ya ce "Ɗan'yaro daga ina haka?" Ya shafa kai ya ce. "Malam na zaga bayi ne" Malam zai sake magana Ɗan'yaro ya ciro dubu ɗaya ya bashi sai ya fara sakawa Ɗan'yaro albarka. Saudat kuka ta yi sosai a banɗakin kafin ta fita zuwa ɗakin Mama tana tafiya a hankali saboda raɗaɗin da ƙasanta yake mata duk da ba wani abu ya yi mata ba amma ta ji zafi sosai. Tana shiga ta kashe hasken ɗakin ta fara cin abincin ta ci ta ƙoshi ta tashi Zaituna ta bata bayan sun gama ta ɗauki ledar ta yi waje ta yayyafa mata kalanzir kar ma a ji ƙamshin nama jakar rufaida kuma ta tura ƙasan shara ta koma ta kwanta. * Ta cikin idanunta take hango nasa idanun da yake ƙoƙarin faɗa mata wani abu, ƙwayar idanunsa ta yi kama data wanda take mafarkin samu matsayin miji shine kalar test ɗin mutumin da take addu'a akan shi ajjiyar zuciya ta sauke tana zagaye office ɗin nata sai kuma ta tuna password ɗin FS daya faɗa mata, ya akayi ya sani? Labarin daya bata ya fara tunawa idan ta fara farko da ƙarshen sai ta ji labarin bai cika ba, babu tsakiya akwai abin da ya cire alabarin. Mene ya faru sanda ya shiga state cid tsayin shekaru biyu? A ina ya san ma'anar FS? "You missed Safiyyerh!" Da sauri ta ɗauki wayarta da jakarta I. Qasim dake shigowa ya ce "Sai ina?" Key ɗin hannunta ta cilla masa ta ce "Muje Federal investigation department now" ta faɗa tana yin waje bayanta kimiyya ya bi, ya shiga wajan driver itama ta shiga ya jasu suka ɗauki hanya. "I. Qasim kana siyasa ne?" Ya ɗan yi shiru can ya girgiza kai ya ce "A'a. mene?" "Kasan wani me neman takarar kujerar ɗan majalissar tarayya Dr Abraham?" Da sauri ya juya ya kalle ta sai ya tuna ashe shi yana amfani da Qasim Ibrahim ne, babu sunan kaka ma kuma Aafiyyah bata taɓa ganin babansa ba koda a picture ne "Bana jin cewa na san shi, is there any problem?" Ta ce. "Ina son taimakonsa wajan janyo hankalin mutane izuwa kansa ina buƙatar naga ya yi nasara?" Ya sake kallon ta kaɗan da mamaki ya ce "Ke mene tabbacinki a kansa ne? Bafa ki san wanann dr Abraham ɗin ba har kike son taya shi yekowa?" Ta yi murmushi ta ce "Qasim kenan. "Ok. How can i help you?" Ta yi ƙasa da murya ta ce "Join me" "Done" ya ce yana buɗe hannunsa. * AA MAJ na zaune tun bayan faruwar abin da ya ji yake zaune a gidan computer ɗinsa. Abin da ya saita da motar Aafiyyah yaga yana yin wuta ya yi saurin dubawa yaga direction yana nuna hanyar zuwa Federal investigation department ya tuna maganar Muhammad da yake cewa Aafiyyah har cewa ta yi bata da aure har cewa ta yi tana son wanda ta kama ɗin sai ya saurin miƙewa fuskarsa babu alamar annori ya yi waje ya shiga mota kai tsaye shima FCID ɗin ya nufa. AA MAJ na fita Muhammad ya buɗe ƙofa shima ya fito har wata ajjiyar zuciya ya sauke sanda ya shaƙi iskar ƴanci da sauri ya tare mai napep yana nuna masa motar AA MAJ ya ce "Follow the car" Aafiyyah na tare da Kimiyya zuwa FCID kamar yadda Aliyu ke hanyar zuwa yayinda Muhammad ke bin bayansa domin zuwa duk inda Aliyu za shi. Napep ɗin Muhammad ya riga motar Aliyu sauka don haka ya yi saurin bin bayan Aafiyyah da yaga ta fito daga mota, securities basu kula Muhammad ba domin tunaninsu tare suke da Madam a haka Muhammad ya dinga bin bayan Aafiyyah har ta isa ɗakin da MUTALLAB yake ciki, tana shiga shi kuma Muhammad ya zuro kansa cikin ɗakin daidai sanda Mutallab ya ɗago kansa idanunsa ya sauka akan Muhammad da fuskarsa take rufe da facemask a hankali Muhammad ya zame takunkumin suka zubawa juna idanu shi da Mutallab lokaci ɗaya kuma suka sakarwa juna murmushi.... 💥Chapter 6: Promise me, you'll stay with me. Zuciyar Aafiyyah ce ta buga da ƙarfi jinin jikinta ya daskare ta ji gargasar jikinta na mimmiƙewa, wani abu mai kama da shauƙi yana mamaye zuciyarta. Ta jima ba taga murmushi mai kyau a fuskar baƙin mutum kamar yanzu ba, murmushin fuskar Blackman a yanzu shine abu na farko daya sanyaya zuciyarta ba tare data sani ba, he is more handsome idan yana murmushi duk da yankan wuƙar dake fuskarsa da wuya da goshi hakan bai sanya murmushin ya yi muni a fuskarsa ba. Sai ta ji jikinta na yin sanyin kamar ba ita ce ta shigo da ƙwarin zuciyar tunkarar Scorpion domin jin labarin abin da ya cire cikin labarinsa daya bata, a hankali ta ja nata idanun ta lumshe tare da harɗe hannayenta a ƙirji saboda yadda ta ji zuciyarta na rawa sosai, irin rawar data jima ba ta yi ba, sai ta ji kamar irin rawar da zuciyarta ke mata a yanzu, irin yadda take mata ne a cikin bacci a lokacin da zuciyarta ta yi kusanci da Yaa Muhammad ɗinta. Buɗe ido ta yi a hankali ta juya zuwa sashen da Mutallab yake kallo yana sake faɗaɗa murmushin nasa, madadin taga mutum tsaye sai taga babu kowa ƙofa kawai ya kewa murmushin kamar wanda ya samu taɓin hankali, sai ta ji zuciyarta ta raunata ƙwarai. Ganin tana ƙoƙarin bada kanta da gaske ya saka ta kame fuska tare da gyara murya, ta jiran ganin Mutallab ya juyo amma sai taga ya yi ƙasa da kansa kawai yana wasa da yatsun hannunsa, ta dinga kallon shi idan ta ji kamar tana jin tausayinsa sai kuma ta fara tunanin mutane nawa ya kashe? Ba tare da sun yi masa komai ba, saboda wani dalilinsa wanda har yanzu basu san shi ba. A hankali ta ce "Criminal" ta ce tana danna waya. Babu alamar zai ɗago domin kamar yana avoiding ɗinta ne, ganinta, maganarta, da ita ɗi kanta gabaɗaya. "Banzo nan akan cewa kana buƙatar ganina ba, na zo ne domin ka yi mini bayanin abin da na gaza sani da fahimtar hakan". Ta ɗan yi shiru kafin ta ce "labarin daka bani ba cikakke bane, ka cire tsakiya ko ƙarshen dole akwai abin da baka faɗa mini ba. Na farko me ya sa kai da ka sato abinci gidan Alhaji Wada za'a tuhumeka da cewa anga bindiga a wajanka? Na biyu sanda Dig Johar ya keɓe da kai akwai abin da kuka tattaunawa mene shi? Na uku sanda aka kama ka da zargin kashe matarka da kaje state cid tsayin shekaru uku mene ya faru ciki? Ya aka yi kuma ka yi free? The last question da Safiyyerh za ta yi maka shine...," Shiru ta yi, tana sake ƙare masa kallo haka kawai take jin kamar ta taɓa ganin mai irin ƙirarsa kamar ta taɓa yi wa mai irin suffar nan al'ƙawarin wani abu. Mene shi? Moh shima ɗago kai ya yi kamar zai kalle ta, saboda sunan Safiyyerh da ya ji sai kuma ya yi saurin mayar da kansa ƙasa, yana jin idanun Aafiyyah na bin jikinsa kallon shi take yi, irin kallon da take yi masa tun a makarantar Fgc idan ta saka glasses ɗinta, irin wannan kallon shi take masa a yanzu can ya ji ta sauke numfashi da ajjiyar zuciya kafin ta ce "Ta ina ka san FS WORLD? Ya aka yi kasan key ɗin da nake nema? And ya aka yi kasan cewa ina bincike akan Company?" Ta ce tana jingina da jikin kujerar da take kai, tana sake kallon shi, idanunta na lumshewa tana jin wani abu mai kamar da kwarjini na shigar mata cikin idanu da gaske kwarjini Scorpion ɗin yake mata, gashi dai matsayinsa bai kai ya yi mata kwarjinin ba, yadda take jin wani irin sanyi a saman fatar jikinta tsoro yake bata, wani irin abu take ji mai kama da feelings emotions na motsa ta sosai fiye da yadda take tunani. "I am talking to you!" Kamar Moh baya wajan, ko yatsarsa bai motsa ba, bawai jinta ne ba ya yi ba, a'a; fahimta ne kawai ba ya yi, maganarta hautsina masa kai take juya masa ƙwaƙwalwa take yi sosai. "You, stupid!" Ta ce da ƙarfi. Bai amsa ba, kuma bai ɗago ba, Aafiyyah kuma bata lura cewa babu sarƙa a jikinsa da hannunsa ba, bata lura da yadda jikinsa ya fara rawa ba sai ta cigaba da magana "What nonsense! Ina magana kana yin shiru saboda ina bi da kai ta lallami? Zan iya sawa ka yi magana ta dole zan saka a gana maka azaba criminal person kawai" ta ce tana miƙewa tsaye zata kira wani staff ta ji saukar muryarsa a cikin kunnenta, da wani irin sauti mai razanarwa murya kuma a kumbure ta ji furucin ya saukar mata cikin bazata wanda ya sata jin zafi a ƙirji. "Ko Dig Abdul-Johar Marafa ya yi kaɗan wajan sanya Moh magana" "Ubana kake cewa ya yi kaɗan? Kaf cikin jami'ai a wannan team ɗin shine babba yana da ikon kashe ka, babu mai cewa komai kuma a banza" "Yarinya kenan" ya ce a daƙile. "Ban fahimci ma'anar yarinya ba, me kake nufi da yarinya, I'm not a kids" Sai a lokacin ya ɗago kansa, a hankali ya zuba mata birkitattun idanunsa da sukai wani irin juyewa sukai laushi sosai, tare da yin ja a duk sanda zai kalli Aafiyyah da abu biyu zuwa uku yake kallon ta, yana manta kallo i never expected this from you, yana mata kallon where is my child, ina yarona? Abu na ukun har yanzu ya kasa tantance shi a zuciyarsa baya ma son ya takura kansa akan wannan dalilin sam, koma yaya ne ya ji baya da ra'ayin ita kanta Aafiyyah ɗin, bashi da muradin kasancewa da ita, da zinariya za ta yi masa adalci da bata bashi damar yi mata kishiya ba, babu motsin kowa a zuciyarsa sai na bestie, yana jin da zata faranta masa data barshi ya dauwama babu wata ƴa mace a rayuwarsa a har sanda wa'adinsa zai yi, har sanda zai dawo gare ta, ranar da Ubangiji ya ƙaddara mutuwarsa, ko ranar da jami'an FCID suka yanke masa na mutuwa ya je lahira wajan bestie, su yi rayuwarsu a can,idan hakan bai samu ba sai ya dauwama yana amsa sunan mijin matacciyya. A yadda yake ji a zuciyarsa, a yadda zuciya ke ƙissima masa shine ya kashe kansa, idan bai kashe kansa ba ya samu ace ko gangar jikin Safiyyerh ya samu a kusa da ruhinsa hakan ya wadatar da shi. Idan ya buƙaci mutuwa ta ɗauke shi sai ya fara tunanin mene matsayin wasiyyar Safiyyerh a gare shi? Wanda suka kashe masa sunci bulus kenan?. A hankali ya runtse idanunsa yana furzar da iska ta cikin hancinsa da bakinsa. Gaf! Gaf! Haka haƙoransa ke rawa da haɗe juna ta cikin bakinsa kafin ya saka harshensa a tsakiya ya datse. "Ba ki ma da hankali" ya sake cewa silently yana motsa hannunsa alamar zai miƙe tsaye amma yana nawar hakan. "Ka bani amsar tambayoyina" Ya sake ɗagowa ya kalle ta, har abada ita dai baza ta sauya ba. Miƙewa ya yi gabaɗayansa, Aafiyyah a wannan karan ba iya zuciyarta ke jijjiga ba, hadda gangar jikinta domin Mutallab a tsayi ya shige inda take tunani, za su yi tsayi ɗaya da Muhammad, shi Muhammad kuma ya zarta AA MAJ a tsayi da ɗan jiki domin yanayinsa ya bayyana cewa yana motsa jikinsa saboda buɗewar da ƙirjisa ya yi, saɓanin Mutallab da wahala haɗi da dabar da yake yi ce ta saka jikinsa buɗewa ainun. A tsaye yake gabanta daga shi sai wandon da sukar basa, ƙirjisa zanen Scorpion daya zama tattoo ne raɗau ko yaya ya motsa hannunsa sai ta ji ƙashin hannun na ƙara damtsen hannunsa ya rarrabe. Ya ɗora hannunsa a ƙugunsa tare da karkatar da kansa gefe yana cije lips. "Liar...," ya ce calmly. "Scorpion!" Ta kira shi da ƙarfi. Gani ta yi yana yin kanta ta yi saurin dakewa ta ce "akwai bindiga tattare dani, ka matsa ni matar aure ce, ko can baya dana ce ina son ka, ko can baya dana furta zan aure ka, ko can baya da na ce bani da aure....," sai ya yi saurin katse ta, ta hanya ɗalla mata yatsa laɓɓanta kana ya ɗora yatsarsa ɗaya a baki ya ce "Quiet" "Kin ce, but you don't meant it, you listen, you don't judge great" sai ya lumshe idanunsa yana sake watsa su a fuskarta ya ɗauki minti zuwa daƙiƙo kafin yaja numfashi ta ƙirji kamar zai matse ta a bango ya ce "Nasan dole za ki dawo domin buƙatarki, kuma na shirya faɗa miki ba dan saboda ke ba, ra'ayin Moh ne hakan. Ba'a taɓa yin sirri da kurciya, ba'a yadda da benu Moh baya shiga sabgar masu ɗankwali amma ke na faɗa dake saboda dalilina. Tabbas kin yi nasara akai ne nasarar da kika yi kuma dalilin matata ce da ace tana raye kusa dani wallahi da ko inuwarki bata ishi Moh ba. Kin ce kina so na yarda domin ba yau kika fara, kina so na kamar ranki kamar ruwan shanki, kamar iskar shaƙar ki kin rayuwa da soyayya kamar yadda mutuwa ke bibiyar ɗan'adam"A fusace Aafiyyah ta ce. "Da na yi babbar asara na so jahilin mutum kamar ka, da na yi asara na ƙaunaci ɗan'daba like you " "Kin jima da zama asararriya" ya ce a kumbure anger ɗinsa na motsawa. Aafiyyah idanunta kamar za su fito waje ta nuna shi da yatsa ta ce "Da ni na so ka, gwara na yi addu'ar cewa Ubangiji ya ɗauki rayuwata, dana ƙauna ce ka gwara a ce ɓarina aka yi ba haihuwuta ba, you're not my type my test kai ba irin tsarina bane" Da ace yana da ikon sanya kansa dariya tabbas daya murmusa amma tuni wami jin daɗi da farinciki suka yi ƙwaura daga duniyarsa baya buƙatar dariya,baya buƙatar jin daɗi, duk wani abu da zai yi idan har babi bestie to bashi da ma'ana a wajansa ƙaddararsa ce ita, kamar yadda take yawan faɗa masa, gashi yanzu wasu sun datsi ƙaddararsa ba tare da laifin komai ba. Sun raba shi da yarinyar data bashi farincikin da iyayensa suka gaza bashi, he feels heartbroken. Huci ya dinga fesawa Aafiyyah a fuska yana sake matsawa da kai ta ƙarshen hancin ya zuba mata idanunsa da suka gama birkice ya ce "zan tabbatar da kin maimaita abin da kika faɗa, ba ƙiyayyar ba za ki fara nemana ido rufe a lokacin da bakya buƙatar mijin naki. Duk soyayyar da mace zata iya baka kanta a ba ƙaramar soyayya bace kin jima da mutuwa a kaina" Baki ta buɗe za ta yi magana ya yi saurin zare mata manyan idanunsa sai ta ji fitsari na cika mata mara yana ƙoƙarin kwace mata tare da biyo cinyoyinta, dakewa ta yi tare da shanye dukkan wani tsoro. Harara ta watsa masa ta ce "Allah wadaran ka...," kafin ta ƙarasa taga ya yi saurin ɗaga hannunsa sai ɗauke ta da mari sai ta yi ƙwafa tana jinjina kanta ta ce "kana tunanin zaka mare ni na ƙyale ka? Wallahi kwaɗa maka mari zan yi" Hannunsa ya saka ya cafko gaban rigarta ita kuma ta ɗaga hannunta zata damƙo wuyansa sai taga babu riga a jikinsa, zuriyarta na tafarfasa tasa hannu da damƙo wandonsa ya yi saurin kallon ta. "Baka da wannan lasisin har yanzu baka san wacece ni ba ko? Baka da wani muhimmanci a wajena kai da banza duk ɗaya suke wallahi" sai ya sake ta a hankali ya fara yin baya wani irin kallo yake mata kafin da ƙyar ya ce "Muhimmancin nawa ya saka kika bani budurciki ko?" Da rashin fahimta Aafiyyah ta ce "Are you ok? Allah Ya rufa mini asiri mutuncina sai gidan mijina ba dai ɗan iska, ɗan ta'adda, ɗan'daba irinka ba" sai ya ɗaga kafaɗa ya ce. "Shiyasa kike tsoron mijinki ya san ki? Ke kin daman. Zan ba ki amsar abin da kike tambayana, abin da ya faru a shigata state security service ba zai faɗu a nan ba, maganar da muka tattauna da asawanki, ki je ki tambaye shi. Ya akai nasan kina bincike akan kamfanin FS WORLD INVESTMENT wannan baiwar Moh ce. Key ɗin da Ashraf ya saka ki tambaya ai na faɗa miki. F tana nufin friends S kuma dukkan friends ɗin nan yaran da suka haifa sunansu ya fara da S. Misali kamar Eng Ali wali sunan ƴarsa Sabrina ana ce mata Noor sai kuma ke Dig Abdul-Johar ɗin...." A gigice Aafiyyah ta ce. "Bangane Dig Abdul-Johar ba? Me zai kawo Daddy haɗaka da waɗannan mutanen?" Ta ce jikinta na rawa. "Sunanki Safiyyerh Abdul-Johar Marafa, ki je ki yi searching mutane biyar a FS WORLD domin mutane biyar suna masu kamfanin ki cire Sharfaɗi a ciki amfani aka yi dashi, shi kansa bai san masu haƙiƙanin masu kamfanin ba, shi fasinja ne kawai ki nemi wanda ya san komai" Wata iriyar zufa ce ta dinga yankowa a fuskar Aafiyyah hankalinta ya yi mugun tashi ta dinga nanata sunanta Safiyyerh kuma sunan ya fara da S tabbas,sai ta fara tunanin sanda maigadin company ya ce mata daddy yaje yaga motar daddy, haka ma accounter again ta sake tuna maganar Ashraf da yake ce mata "Daddy is here" kenan Paaahh yana cikin mutane biyar ɗin? innalillahi wa'inna ilaihirraji'un! Paaahh? Hannu ta saka ta dafe kanta dake mata ciwo sosai. A hankali ta kalli Moh taga ya juya mata baya sai ta ce "Don Allah idan ka san raguwar mutane da kun ka faɗa mini tunda alamu ya nuna kasan komai" ko tari bai yi ba, balle ya kula ta idanunsa ya yi jajir babu abin da yake buƙata a yanzu irin sha fara kaga aljan ko ƙwayar doki. Ta girgiza kai ta ce "Talk" "Say something" Madadin ya bata amsa sai ta ji da ƙarfi ya ce "Out, out fita a nan" "Babu inda zani" Gadan-gadan ya yi kanta yana zuwa ya saka hannunsa ya damƙi wuyanta ya haɗata da jikin bango, idanunsa jajir jikinsa na rawa da kakkarwa cikin ƙaramin lokaci ya fita hayyacinsa. Aafiyyah ta kasa kwacewa numfashinta ya fara kokawa da ƙarfin gaske ji take kamar zata bar duniya ne saboda azabar da take ji. A hankali nata tunanin ya fara kurɓata sai take hango kanta sanda Mutallab ya shaƙe mata wuya a makarantar Fgc sanda ya yi mata jahilin duka ta cikin idanunta take hango yadda yake taka mata ciki da kuma yadda take hango fuskarsa da sanda take roƙan ya daina dukanta sanda ta durƙusa akan ƙafafuwanta. Wani ihu Aafiyyah ta kurma da ƙarfi jikinta na jijjiga da dukkan ƙarfinta ta ce "Please Please Yaa Muhammad" "Zaka kashe ni Tayo, zaka kashe ni Yaa Muhammad wayyo Daddy" Cak! Moh ya tsaya da sheƙetan jikinsa na rawa ya saka hannunsa ya damƙo ta ya ce "Remember?" Hawaye ya cika idanunta ta ƙanƙame jikinta da ƙarfi ya ce "Kin tuna ni?" Slowly slowly ta buɗe idanunta ta kasa magana jikinta na rawa ya sake yin kanta ya ce "Kin tuna Fgc? Kin tuna ni? Kin tuna Safiyyerh, kimiyya, Nahyan? Kinal? Kin tuna?" Kuka kawai Aafiyyah take yi kamar numfashinsu zai bar ƙirjinta tana binsa da idanu kanta da ɗakin na juya mata da tsananin ƙarfi tana ganninsa bibbiyu. Kamar mai tsoro ko mai shirin taɓa wuta ya saka hannunsa a kafaɗunta ya girgiza da ƙarfi ya jijjigata kafin ya yi magana sauran team ɗin suka shigo a guje da ƙyar suka ƙwace Aafiyyah a hannun Moh da sauri ta fice daga cikin wajan. Moh ya fara buga kansa da jikin bango sai kuma ya durƙushe ƙasan ƙafafuwansa saboda wani irin murɗawa da cikinsa ya yi, ya damƙe kasan mararsa wata azaba yake ji tana ratsa fatarsa tare da sauka a tsokar dake jikinsa tana kaiwa ƙasosuwan wajan farmaki wani irin duhu yake gani ta cikin idanunsa sai ya dinga jin muryar bestie a gefensa. "Mai dawa na, bestie ta mai dawa" Haka ya ji sautin muryarta cikin ƙaramar muryarta mai laushi a hankali. Juyawa ya yi a hankali sai ya hangota can gefensa jikinta sanye da fararen kaya wasu furanni sun lulluɓe ta, ga wasu mutane da fararen kaya sun zagaye ta, murmushin take yi masa tana lumshe idanunta hannunta harɗe riƙe da fararen yara sai jijjiga su take tana nuna masa yaran murmushinta kasa gushewa. Muryarsa na rawa ya ce. "Zinariya, bestie" Harara ta watsa masa ta ce "Allah Ya shiryar ka, Allah Ya shirya ka" "Amin. Me na yi?" Ya furta a sanyaye yana langwaɓar mata da kai gefe idanunsa na sauya sosai ta ce. "Kar ka yi mini kuka, idan ba haka ba zan koma" cikin sauri ya girgiza kai sai ta yi taku ɗaya biyu kana ta ajjiye yaran can gefe cikin nutsuwa take takawa zuwa gare shi, tun kafin ta ƙarasa ya miƙa hannunsa ya cakomo ta zuwa jikinsa sai ya ji tana wani irinn ƙamshi da bai taɓa jin irinsa ba, dariya take yi masa sai ya ɓata rai ya ce "Allah bestie ba ki da gaskiya" "A'a wannan karan dai ina da ita" ta ce tana masa farfari da idanunta kafin ta saka hannunta cikin sumar kansa sai ta shanshana ta ce "Uhmm ƙazami wari kake yi baka wanka?" Ya jinjina mata kai, yana sake shigewa jikinta kamar za'a ƙwace ta, idanunsa na cika da ƙwalla ya ce "Kina raye a duniya kika bar ni?" Ta ce "Ba na ce kar ka zo kabarina kana mini kuka ba, ba zan jure ba? Haba bestie ba kyau zama da ƙazanta , tsafta cikon addini ce a haka zaka ke wajan Maamah?" "Mahmah?" Ya maimaita. "Yes. Aafiyyah is waiting for you, ba za ta ji daɗi ba idan ta ganka cikin mummunan hali, haba nawan" ta ce tana shafo gemunsa da laɓɓansa. Kallon ta kawai yake yi, ta sauya kamar irin matan aljanna ɗin nan jikinta kamar jini ya yi tsartuwa saboda haske da ja a hankali ya ce. "Uhm" "E ɗin, uhm ɗin" Ya sake cewa "Uhm" Ta haɗe hannunsu da kyau waje guda ta ce "Mai hali baya fasawa. Bestie please love Aafiyyah ai kana son ta ma, ka yi ƙoƙarin ganin ka mallake ta" laɓɓansa na rawa sosai kamar zai tsaga su da haƙoransa da suke cikin bakinsa ya ce "Safiyyerh!" Ta kalle shi tana murmushi sosai tare da ɗage masa girarta biyu ta ce "Me?" A hankali taga ya janye ta daga cikin jikinsa ya miƙe tsaye can ya juya hannunsa tare da fusa iska sai taga takobi a hannunsu sai sheƙi take yi ta bubbuɗe idanunta ta ce "Mene haka? Ashe abin da nake gani gaskiya ne? Zan yi tafiyata, zan ɗauke yarana mu tafi mu barka ba ruwanmu da kai" Kai ya dinga girgiza mata sai taga ya zube a kan ƙafafuwansa ya durƙushe a gabanta kamar mai roƙan gafara ya ce "We're forever together Fiyya, you're not going anywhere ki yafe mini na gaza kulawa dake na tattaka kare hakkin wani daya rataya a kai na, na tuba bestie, na tuba, na bi Allah na biki Safiyyerh don Allah ki rayu dani ban ƙare ƙara bari a yi miki komai, look kalli nan Fiyya..," takobin ya riƙe ya nuna mata ya ce "For you, saboda kare ki ba mai sake rabaki da ranki kin ji ko?" Ƙura masa ido ta yi kawai tana kallon shi tana murmushi mai san yi ya ce "Za ki rayu dani?" Sai ta ɗauke kan ta zuwa gefe tana kallon yaran nata ta ce "Lallai zan rayu da kai, rayuwa a inda bamu mai rabani da kai. Zan rayu da kai idan ka dawo gare ni, zan rayu da kai a sanda babu Aafiyyah yanzu ta fini buƙatarka ni kuma na fi jin daɗin zama a inda nake yanzu. Kaga na manta ban faɗa baka ma, Jaaanah na gaisheka sosai da Anty Hameeda da Diyna da favourite ɗinka Muneeberh wajanmu ɗaya muna jin daɗin rayuwa a can, har uncle Ade muna tare bacci muke cikin kwanciyar hankali iska mai daɗi waje mai ni'ima bestie ban taɓa tunanin akwai waje me daɗi ba wajan ya shige nan, na ɗauka zan samu farinciki ne kawai a sanda nake kwance saman ƙirjinka sanda nake jin ɗomin jikinka ashe i was mistaken, Allah don ka ji can ya fi ƙirjinka lusarin mijina daɗi" Muryarsa na rawa sosai ya ce "Lusari?" Ta ce "E. Lusari mana gashi ka tsaya kaƙi ɗaukan mini fansa ka kasa cika mini wasiyyata ka daman da kuka bana iya cikakken bacci a cikin gidana" ya yi shiru kamar bai fahimta ba a hankali ta amshe takobin ta ajjiye ta ce "Ba kyau" Still yaƙi magana ta ce "I love you" "I love you, I love you to Zauja, I love you bestie i love you all the time" Ta kyalkyale da dariya ta ce "Lalala Allah Ya kama mini kai, ashe kana so na?" Ta ce tana damƙe hannunsa. Muryarsa cike da rauni yana sake kallon annurin fuskarsa Safiyyerh ya ce "My love for you will never die Deer. I love you and i want to keep loving you coz da son ki nake samun sukuni a cikin zuciyata. Kece wacce kasancewa dake yake sanya ni farinciki, rashin ki kusa dani ke sani kewar da ke ƙara wanzar da son ki a cikin zuciyata. There's something about the love i have for you that's making me so addicted to you each day that come to pass. Ina sonki so mara adadi! So mara adadi Barewata" Sai idanunta ya cika da hawaye ta ce "Wannan son na sadaukarwa da Aafiyyah har abada ka ji Bestien beastie?" Zai yi magana ta ce "Zo na ɗan sammaka ƙamshin jikina, zo mu yi sallama na ɗan rungome ka" matsawa ya yi jikinta a ƙoƙarin ganin ya shige jikinta wanda yake tsananin kewa a kodayaushe a kullum......, "Kai!" Aka ce masa, ya yi saurin buɗe idanunsa wanda ya haddasa masa farkawa daga duniyar mafarkin Deer. * AA MAJ bayan ya yi parking motarsa a harabar Federal investigation department ɗin yana ƙoƙarin fitowa ya samu kiran gaggawa daga wajan ogansa hakan ya tilasta masa juya kan motar yana mai takaicin kiran a cikin ranshi hakan ya saka yaja motar a guje ya nufi inda ake kiran nashi rai matuƙar ɓace. I.Qasim na cikin motar Aafiyyah yana waya da mahaifinsa Dr Abraham Denial David wanda suke kira da Papi ya hango motar AA MAJ ɗin na fita daga cikin wajan ya yi shiru yana tunanin ko saboda ya biyo Aafiyyah ne? Mene ya kawo mijin Aafiyyah nan ɗin? Ya ja numfashi ya ce "Bana son ka nuna mata ka sanni balle ka nuna ka haife ni, leave the innocent Maamah ta yi aikinta cikin nutsuwa kawai zan yi supporting nata ne kamar yadda na saba don Allah" ta cikin wayar Dr Abraham ya ɗan yi shiru ba tare da ya ce komai ba. "Please Papi" cewar Kimiyya. A hankali ya ji Dr Abraham ya ce "Baka da gaskiya QASIM" "No. Da gaskiyata kawai agree" "Uhm" Qasim ya ce "Haba mana Papi da ALHASSAN ne da tuni ka ce to" Ta cikin wayar ya ɗan yi murmushi ya ce "Kawo abin sadaƙa to" "Ni yanzu bani da kuɗi, zan saka Jeddah ta tura maka to" daga can ɓangaren Dr Abraham dake tsaye hannunsa ɗaya yana ɗan shafa kansa ya ɗan jima bai amsawa Qasim ɗin ma sai can ya ce "Bani son kuɗi, call Mimi ka ce ta buɗe ƙofa kaga a bakin ƙofa" Qasim ya tuntsire da dariya ya ce "Rest in peace kawai Papi tunda Mimi ta rufe maka ƙofa" sai Abraham ya kame fuska yana juya manyan idanunsa, da sauri ya shige corridor ya ce "Qasim inda Alhassan ya fika kenan,kai ba'a sirri da kai, ka kira Jee ka ce ta buɗe ƙofa now!" "Amma deal za mu yi" "Mene Deal ɗin?" Papi asked. "Zan faɗa maka, bari na kira ta" Kafin Qasim ya kashe kiran tuni Papi ya kashe nasa, domin ba'a kashe masa waya a kunne yana ta tsaye zuciya na faɗa masa ya ɓalla ƙofar ko ya haura ta window, amma idan ya tuna da ba yanzu bane sai ya sake tsuke girarsa waje guda. Qasim ya kira Mimi tana ɗagawa ya ce "Uwargida ran gida, uwar gidan Khalil, uwargidan Dr Abraham mata a wajan Ibrahim, kaga gimbiya wajan tsohon sarkinmu Allah Ya ja da ran jee Allah Ya ƙarawa Malama ilimi" "QASIM! Ta kira shi alamar warning. "Mimi gani bakin ƙofa" Malama Majeederh ta yi shiru, ta san cewa idan Alhassan ne zai iya haɗa baki da ubansa ko ya ɗakko sifana ya ƙunce ƙofar ɗakin tas Kimiyya kuma baya hakan sai ta ce Ok kawai tana miƙewa ta nufi ƙofa buɗewa ta yi kafin ta yi magana Abraham ya shige ciki yana watsa mata harara ta ce "Na gode maka Qasim Allah Ya yi maka albarka" dariya ya yi ya kashe wayar. "Amin. Da ni mijin malama dana bada shawarar a kira ki" Mimi ta girgiza kai ta san halin mijinta ne faɗar gaskiya gashi ya kuncewa Qasim zani a kasuwa. Banɗaki ta nufa sai ya yi saurin bin bayanta yana magana ƙasa-ƙasa. * I. Qasim murmushi kawai yake yi yana mai jin daɗin dramar iyayen nasa yana ƙaunarsu sosai fiye da komai ba'a sanin sun yi faɗa sai dai a ji shiryawar su. Daga can nesa ya hango Aafiyyah ta fito a hargitsa cikin sauri ya buɗe ƙofa ya fito kafin ya ƙarasu ta durƙusa ƙasa saman qwiwoyinta kanta ta tura cikin cinyoyinta wani irin raunataccen kuka take yi jikinta na jijjiga kamar mazari ta kasa daina kukan a hankali ya durƙusa gabanta ya kasa magana kukanta yake ji sosai har cikin zuciyarsa nan da nan hankalinsa ya sake tashi fiye da koyaushe. "Maamah" ya kira sunanta a hankali sai ta ɗago abinka da zabiya idanunta ya ƙanƙance da ƙyar take gani a gigice take kallon Qasim kafin ta riƙe hannunsa ta ce "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, innalillahi wa'inna ilaihirraji'un innalillahi wa'inna" Cikin sauri shima ya maimaita "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!" "Qasim na shiga uku, na shiga uku Qasim wayyo Allah" ta sake riƙe shi. "Maganin shiga uku Allah" Ta girgiza kai ta ce "Wallahi na shiga uku wayyo ni Safiyyerh meke damuna ne? Qasim wacece ni?" Ya tausasa muryarsa ya ce "Tashi mu je gida Please" kallon shi ta yi sai kawai ta miƙe tsaye ta nufi mota cikin sauri. Duk abin da ya faru Muhammad yaga komai sai ya zama statue kamar irin kumakan nan ya rasa meke faruwa, tsananin kamanninsa daya gani a fuskar Moh ya saka ya yi masa murmushi ba tare daya shirya ba, kamar an yi photocopy an ajjiye haka kamanninsa suke shi da Moh, hatta baƙin da jikin har tsayi komai banbanci ɗaya ne Moh akwai yanka a fuskarsa sosai shi kuma ba komai a fuskarsa yanzu kuma ya fito da niyyar yadda zai fara tunanin abin goge tabo ko ta halin yaya ne sai gashi ya ci karo da muryar I. Qasim kimiyya wacce ta sake daskarar dashi meke faruwa? Waye shi Muhammad, waye Qasim da muryarsu take iri ɗaya sak? Waye kuma wancan na cikin kurkukun. Something is going wrong. "Maamah kar ki yi driving....," Qasim ya ce sai ya yi saurin yin shiru jin ya yi tuntuɓe da ƙafar wani, kafin ya ɗago kai Muhammadu ya yi saurin juyawa ya sanya facemask ya rufe fuskarsa. "Hyy You" cewar Qasim. Muhammad ya tsaya a hankali kuma ya juyo ya ce "Your computer pen" Qasim ya ce yana miƙawa Muhammad sai ya amsa zai juya Qasim ya sake cewa "No thank you?" Kafaɗa kawai Muhammad ya ɗaga yana ƙurawa kimiyya idanu sai kuma ya yi sauri ya bar wajan. A mota ya samu Aafiyyah sai sauke ajjiyar zuciya take yi a haka ya yi driving nata zuwa gida. Sanda ta shiga babu wanda ta kula ta yi upstarts har aka yi issha'i bata fito ba, ƙofarta a rufe har Paaahh ya zo da kansa amma taƙi buɗewa ta yi shiru zaune akan prayer mat. * Ƙarfe 9:00 Soha da Kimiyya na harabar jirgi suna jiran fitowar mutanen da jirgin ya sauke juyawa ta yi ta ce "Bro" Qasim ya ce "Yaya" "Wallahi na gaji kamar na tafi mun daɗe a nan fa, kuma gabana faɗuwa yake ban san me bawan Allan nan zai ce mini ba" Qasim ya yi murmushi ya ce "Ki shirya gashi nan" Soha ta ce "Don Allah?" "Kalli gabanki yanzu yi zai yi kamar bai ganmu ba" juyawa ta yi ta hango shi tsaye yana duba Cartier Rotonde luxury watches dake maƙale a hannunsa, ƙananun kaya ne a jikinsa da suka kama shi sosai sukai masa kyau ash colour kansa sanye da Flat cap sai fuskarsa daya manna mata sunglasses mai kyau baka ganin komai a fuskarsa sai jajayen laɓɓansa, a hankali ya fara takawa yana cillawa wayarsa aljihu ƙafarsa cikin Rainbow sandals yanayin tafiyarsa da fuskarsa ya gama bayyana cewa shi jinin Dr Abraham Denial David ne, alamu rashin son dawowarsa ƙasar ya gama bayyana tuni. A hankali Qasim ya ce. "Welcome back Alhassan Abraham Denial, our Arɗos group's CEO" Da sauri kuma ya ce "Yaya gamu nan" ya ce da sauri yana buɗe bayan motar Alhassan ya kalli ƙannen nasa musamman Soha ko ubanta ne ya kawo ta gidan yanzu? Ina ta bar mijin nata sai ransa ya sake ɓaci, kallo ɗaya ya yi musu ya ɗauke kai. Qasim ne ya ɗauki jakarsa ya saka a baya. Alhassan ya miƙawa Kimiyya alamar ya bashi key ɗin motar "Yaya mun daɗe a nan fa" kallo ɗaya ya yi wa kimiyya cikin sauri Qasim ya bawa Alhassan key ɗin, gaban mota ya shiga Soha na shirin buɗe motar su kaga Alhassan ya jata da gudu ya fice daga cikin airport ɗin without saying a single words. Soha ta yi gaba zata faɗi Qasim ya yi saurin riƙota suka bi motar da kallo. * Ƙarfe wajan 11:45 na dare Aafiyyah na zaune a tsakiyar gadonta tana duba ducoment ɗin da Md ya tura mata hannunta riƙe da cup tana shan fresh milk sunan farko data duba na wanda suke da hannun jari a FS WORLD taci karo da Eng Ali wali, sai wani Alhaji Boɗejo ita bata ma san shi ba, tana cikin dubawa aka buɗe ƙofa aka shiga da sauri ta ce. "Waye zai shigo mini without my permission around this time?" Shiru ta ji, sai ta ɗago kanta idanu biyu suka yi da AA MAJ yaushe rabon data ganshi ma? Ashe yana gidan a hankali ta mayar da kan, shi ɗin mijinta ne tana manta hakƙin miji da yake kanta kamar yadda shima yake mancewa ita bata san matsayinta a wajansa ba yanzu. AA MAJ ya taka zuwa bakin gado ya zauna kusa da ita sun jima haka kafin ta ce "Sannu Maj" ya yi shiru sai ta ɗago kai suka haɗa idanu ya zuba idanunsa cikin nata kafin ta ce "kana lafiya?" "You left me missing you so badly..." AA MAJ ya ce a hankali dab da kunnenta ta ce "Yaushe hakan ya fara?" Ya ɗan kame fuska sai ya murmusa kaɗan laptop ɗin ya amsa ya kashe ya kamo hannunta ya rasa me zai ce amma ya sani this is the right time daya kamata ya gina soyayyarsa a zuciyar Maamah sai ya samu kansa da faɗin "Na amince da auren ki Saffi kema kin amince mu sauya akalar mu'amala mu ok?" "In sha Allah" ta ce kanta a ƙasa. Maj ya ɗan matsa hannunta sai ta kalle shi ya ce "promise me zuwa gaba duk abin da kika ji ko ya faru ba za ki sauya ra'ayinka akai na ba, za mu zauna tare, za mu so juna a hankali, za mu ƙaunaci juna, promise me Saffi cewa you belong to me, only me Aliyu Abdul-Johar Marafa" Ya ce yana miƙa mata hannunsa ta kalli hannun ta ce "Me ya sa zan sauya ra'ayina bayan umarnin Paaahh kamar wahine a gare ni? Zan zauna da kai Maj. Safiyyerh Abdul-Johar Marafa most stay with you Maj" "Promise me,you love me. Promise you stay with me, promise you will be my side, promise you will give me a care, a support, love a cute babies like you Maamah...,!" Aafiyah ta yi murmushi ta ce "Uhm kai yaya. Babies?" Ya jinjina kai a hankali without care ya be "I want a baby, ɗana na kaina, ni dake ɗan Sofia da Aliyu" Hannunta ta ɗora saman nasa ta ce "I promised you" ta ce tana murmushi miƙewa ya yi tsaye, itama ta miƙe zata nufi bathroom sai ya riƙo ƙugunta da yafi kusa da shi ya sanya ta a jikinsa ta baya, ta yi saurin rufe idanunta domin ya yi mata bazata, a hankali ta ji ya ɗora kansa a wuyanta sai ya murza kwankwasonta tare da juyo da ita front of him, suka kalli juna a hankali ya ɗago fuskarta bayan ya ɗora tasa fuskar a saman tata cikin sauri ta ce "Where have you been all this while?" Bai ce komai ba baki ta buɗe a zata sake magana ta ji ya sauke lips ɗinsa cikin bakinta bayan ya gama sanyata a jikinsa da sauri ya rufe ido saboda feelings ɗin daya gama mamaye mata jiki tun safe he is kissing her lips romantically the halal kisses jikinta ne ya fara rawa kanta ya fara juyawa wani irin tsoro ne ya mamaye ta, tsoron wani abu ya cikin duhun idanunta take hango memories ɗin baya daya shige lokacin da Mutallab yake kissing ɗinta a gigice ta yi ƙara tare da saka hannunta duka biyun a ƙirjin AA MAJ ta tunkuɗa shi baya..... 💥Chapter 7: The Interview AA MAJ tafukan hannayensa ya saka da niyyar janyo ta zuwa jikinsa ganin yadda lokaci ɗaya ta hargitse kamar mai tsoran shi,ko sumbatar da yake mata ne bata so? Sai ya ji wani iri a gangar jikinsa duk da ƙoƙarin ganin ya saka Maamah ta nutsu da shi amma abin na neman fassakara, ya san daman it's very difficult to her ta amshe she lokaci guda domin basu da shaƙuwa da kuma jituwar da za'a yi samun fahimtar juna cikin ƙanƙanin yanayi. Auren shi da ita, ƙaddara ne wacce shi da ita ɗin, babu wata wanda ya isa ya gujewa faruwar hakan, she loves Maamah tun kafin yanzu babu wata ƙaddara da zata iya zuwa ta yi sanadiyyar rabuwar su, ko akwai wannan ƙaddarar,to; ba dai ta raba su da juna ba, sai dai wacce za ta iya ƙara kusanta zuciyoyinsu waje guda a cikin ƙirji da gangar jikinsu. Sai ya ja numfashi ta ƙirji, ya kuma ya haɗiye ta ƙirjin nasa,idanunsa na zube a saman fuskarta, yana ƙoƙarin lalubu yanayin da emotions ɗin da take ciki a yanzu, da son lalubu matsayinsa a zuciyarta ta cikin idanun nata. "Lafiya kike?" Tambayar ta fito daga bakinsa kai tsaye yana matsawa gare ta tare da riƙo hannayenta. "Yaya.. yaya... Please kar ka zo wajen, kar ka zo inda nake, yaya Please". Matse hannunta ya yi, yana riƙo fuskarta tare da tallafo gadon bayanta cikin son lallashinta wanda hakan ba ɗabi'ar AA MAJ bace, yana mamakin yadda a lokuta mabanbanta ya kan iya magantuwa a gaban yarinyar daya gama gina ƙiyayyarsa a zuciyarta tun tana rarrafe. Ya kawar da tunanin wajan sake furta "Maamah! Are you okay?" "I'm not, tsoro nake ji,bana son abin da kake yi mini kai na zai fashe" ta ce a gigice tana sake kwacewa daga riƙon da ya yi wa hannayenta. Reflection take gani, shuɗaɗɗan abubuwan da suka kasa samun gurbi na tuna su a zuciyarta a yanzu, sune suke remending kansu ta cikin idanunta sai take ganin kamar abu makamamcin hakan ya taɓa faruwa a gare ta, ita Maamah wani ya taɓa attacking yi mata kiss wanda a wancan lokacin cikin tsoro take, wannan dalilin ya saka tsoron nata ƙara girmamawa a cikin zuciyar Aafiyyah Abdul-Johar Marafa. Ta dinga girgiza kanta idanunta a rufe ruf ƙirjinta na ɗagawa tare da bugun zuciyarta wanda yake tafiya daidai da sautin fitar hucin AA MAJ. A hankali ya sake ta yana ja da baya can kuma ya yi sauri ya juya tare da barin bedroom ɗin nata yana dafe saman goshinsa. Aafiyyah ta sulale a wajan tana nishi hannunta ta saka ta daddafe kanta dake ƙoƙarin raɓewa gida biyu. Hango mutum take sanye da uniform yana ƙoƙarin sanya bakinsa cikin nata, baƙin mutum ne, duk da dishi-dishi take gani idan ta matsa kanta wajan sai taga fuskar wanda yake kissing ɗin nata, sai taji kanta ya sara musamman ta tsakiya. A hankali ta jingina da jikin bangon bedroom ɗin ta cure waje guda, har wata ramewa take wajan ƙoƙarin tuna abin da take jin tana da alaƙa da su, mene ya faru da rayuwarta? "I am sorry Maj, bana nufin ƙuntata maka i am sorry...," ta kasa ƙarasawa. Cikin sauri kuma ta miƙe tsaye kanta babu ko ɗankwali balle takalmi ta nufo downstairs tana kiran sunan J. "Yaa J Yaa J Yaa Junaid" Ta ce tana sakkowa daga stairs ɗin benen idanunta rude a kuma hargitse take kana ganinta kasam babu lafiya. Ummi dake zaune tana duba wasu kayan turaren wuta daga S Bayero wanda a lokacin shirye-shiryen tariyar Aafiyyah ɗin ake yi ba tare da saninta ba. Ummi ta ajjiye wayar hannunta tana kallon Aafiyyah kafin ta ce "Maamah" ta kira sunan Aafiyyah. "Ummi ina Yaa J?" "Maamah kina lafiya dai? Wannan kiran a gigice na magani na mene cikin ƙanƙanin lokaci?" Cewar Ummi. Aafiyyah ta girgiza kai ta ce "Kar ki damu Yaa J nake nema" "Yana cikin bedroom ɗinsa, amma...," bata ƙarasa maganar ba jin muryar Paaahh a bayanta hakan ya saka ta juyo tana kallon shi kafin ta ce "Yallaɓai meke faruwa ne?" Ya girgiza kai yana neman waje ya zauna kansa a ƙasa can ya nisa ya ce "Me zan cewa Zahiyerh ne? Me zan ce wanda zata gasgata ni ta san cewa ban rufe ta ba?" Ummi ta kalli mijin nata tana jinjina wa karamcin shi da ƙoƙarin ganin ya kyautata alaƙar shi da Ummimi jajircewar shi a matsayin uban yara biyar na sawa ta ji ta sake ƙaunar Dig Johar ya kodayaushe sosai yake da ƙoƙarin jan yaransa a jiki da kyautatawa zamantakewar shi da su, ya yi ƙoƙarin da gaske wajan bawa yaran nasa tarbiyya da ilimi da mu'amalar zama da mutane. Ya musu hani ga abu mara da muhimmancin taimakon Ɗan'adam. "Na san Ummimi ba zata fahimta a yanzu ba, domin ka tafka mata babban kuskure wajan ɓoye mata abin da ya faru da Maamah, yana da kyau ka sanar da ita koda ace bata ƙasar ne. Yanzu kam ba zata fahimta ba, bana jin zata sauraren ka ma" Paaahh ya ce "Ban ɓoye mata da nufin cutar da ita ba, saboda yanayin condition ɗinta na hawan jini kin san abu idan akan Maamah ne da Aliyu idanun Zahiyerh rufewa yake yi" "Haka ne. Ɓoyewar ma soyayya ce ta ja, amma ka yi ka je ka fahimtar da ita ko da ba zata saurara ba" Paaahh ya girgiza kai, yana ɗan kaɗa ƙafafuwansa ya ce "Amma...," "No, but." Cewar Ummi tana kallon shi. Kafin a hankali ta ce "Komai ya faru da Maamah ba laifin kowa bane sai naka, da nawa domin har gobe ba zan daina jingina laifin akan ka ba, duk da cewa a farko bamu san dalilin shigar tata ba. Amma sanda ta dawo mana gida a maye a can ƙasar da muke a ta faɗi komai. Ka yi mata al'ƙawarin da ka san cewa ba zaka iya cika mata ba, kai ne ka buɗe wannan ɓarnar Yallaɓai. Gashi ka sake yin wani laifin akan wani babu shawarar yaran data Ummimi ka haɗa Maamah aure da Aliyu, which is no good for me kenan" ita kanta zuciyarta babu daɗi ɗin. "Yanzu laifi ne don uba ya zaɓawa ɗiyar cikinsa abin da yake ganin ya dace da ita Ummi? Ban yi haka don cutar da ita ba, mene ya saka zan cutar da Maama" sai miƙe tsaye fuska babu alamun rahama ya ce "Na zama mugu ga ƴar dana haifa ko?" "Idan kai ka haifi Maamah waye mahaifina, ni kuma?" AA MAJ ya ce. Da sauri Ummi ta miƙe tsaye jikinta na rawa idanunta akan Aliyu, shi kuma Aliyu idanunsa akan Paaahh daya sunkuyar da kansa ƙasa. Aliyu idanunsa jajur zuciyarsa sai rawa take yi amma yana dakewa tare da hana kansa zaucewa, ba wai tsoron yake idan ace ba shi ne halalataccen ɗan gidan Dig Abdul-Johar Marafa ba, tsoro ɗaya bai san waye zai kasance mahaifi a gare shi ba, da hanyar sunna aka haife shi ko akasin hakan. Wannan tunanin ke sake haifar da ruɗani a zuciyar AA MAJ. Ya gyara tsaiwa ya ce "Daddy kai ne mahaifina? Ummi ce ta haife ni ko ni ne bare a cikin zuri'ar Marafa?" "Aliyu!" Ummi ta kira shi da ƙarfi. Sai ya kalli Ummi kana ya girgiza kai har yanzu yana tsaye saman ƙafafuwansa cike da jarumta irin wacce ya samu wajan hurar da sojoji da nuna rashin damuwar abin duk yadda ya kai ga ci masa zuciya. "Ummi ba zan ji babu daɗi ba idan ya zamana cewa bake ce mahaifiyata ba, domin babu wani tarihi da zai zo ya sa na sauya miki matsayin Uwa, babu lokacin da zai gabata da ba za ki amsa sunan Uwa a wajan Aliyu ba" sai ya yi shiru yana kaiwa da komowa ya furzar da iska a hankali kana ya juya ga Paaahh ya ce "Bana son a raunata zuciyar yarinyar nan da kuka bani aurenta, bana son hakan ko kaɗan. Waye ɗanka tsakanin ni, da kuma ita?" "Answer my question, kar ka bar ni cikin tunanin da zullumin rashin sanin abin da ban sani ba" "Aliyu, will you shut up?" "Why? Me ya sa zan yi shiru?" Maj ya ce yana sake ƙanƙantar da ganinsa akan Paaahh kafin ya ce "Sir. Ka san ciwon da mutum yake ji a zuciya ya rayu da mutanen da yake tunanin sune komai nasa, sune inuwar da yake zama cikinta ya ji sanyi, sune garkuwar da za su iya kare shi daga faruwar wasu abubuwan, sune katangar da zai iya jingina ya yinda ya gaza tsaiwa a saman ƙafafuwansa? Kun san raunin da mutum zai iya samu a lokacin da ya ji cewa wanda ya gama saka ran sune iyayensa kuma ace basu ne suka haifeshi ba. Sir ka faɗa mini ba komai zan iya ɗauka da gaske zan ɗauka" Paaahh ya ɗago rinannun idanunsa ya kalli Maj ya kasa magana ƙoƙarin barin wajan yake cikin sauri Maj ya tari gaban Paaahh ya ce "Junaid ɗanka, Dr ɗanka, Awais ɗanka wannan dalilin ya saka baka haɗa auren Maamah dasu ba, ka aura mini ita domin na rufa mata asiri kar abin data aikata ya fallaso ga jama'a ko? Wannan shine hujja?" "Wanne abu na aikata ni Safiyyerh? Yaya me aka ce na yi? Daddy Ummi me na yi da har za'a rufa mini asiri?" Aafiyyah ta tambaya jikinta na rawa idanunta cike da hawaye, fitowarta daga ɗakin J kenan amma yaƙi saurarta yaƙi ko kallon ta ma, yaƙi bata listing ears bai ma damu da condition ɗin da take ciki ba. Maj ya runtse idanunsa yana sake dafe saman goshinsa tare da murzawa a hankali yaƙi kallon Aafiyyah kamar yadda Paaahh ɗin yaƙi kallon ta, tuni Ummi ta haura sama idanunta cike da hawaye bata son ma Aafiyyah tayo kanta da wannan tambayar da bata da amsarta bata san me zata cewa yarinyar ba, bata ma da abin cewar kalamai sun yi kaɗan a cikin bakinta. Aafiyyah ta kalli Maj ta nufe shi tana zuwa ta kama hannunsa cikin rashin fahimta ta ce "Yaya wani abu aka maka na aikata? Da har zaka rufa asiri ka aure ni? Me na aikata a duniya da zan iya zama baƙin jini a idanun mazan dake duniya?" Zame hannunta Maj ya yi yana nufar hanyar fita. "Na san zaka faɗa mini Yaya, kar tsanar da ka yi mini a baya ta yi tasirin faɗa mini abu mai muhimmanci a rayuwata, meke faruwa?" Still Aliyu yaƙi magana. Sai ta nufi wajan Paaahh ta ce "Shekaruna nawa yanzu? Da shekarun baya dana yanzu na jin cewa akwai bambanci a cikin rayuwar Safiyyerh ta yanzu data baya, what's going on? Mene aikata me muni har haka? Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un! Daddy wace ni? Who is Safiyyerh? Don Allah...," numfashinta ne ya fara misbehaving a ƙirjinta, ta cire hannunta guda ɗaya ta ɗora a ƙirjin daidai ƙahon zuciyarta da take jin kamar ta kumbura ta cikin ƙirjin tana numfashi da ƙyar ta ce "Ka faɗa mini daddy don Allah, me na yi? Ba dai ɓata maka rai na yi ba, ba dai alƙawari na saɓa ba wacece ni?....." "Shiru haka nan Maamah" Ta girgiza kai Aafiyyah ta yi tana riƙe hannun Paaahh ta ce "Allah zan iya mutuwa idan baka faɗa mini ba" "Yadda ba ki mutu a baya ba, ki ka tsallake haka ba za ki mutu a yanzu ba, za ki rayuwa lallai za ki rayuwa" Paaahh ya ce yana riƙo Aafiyyah zuwa jikinsa ganin kamar numfashinta idan ya fita baya dawowa. Aliyu dake baƙin ƙofa ya ce "Idan ta mutu, mutuwar ta rataya ne a wuyanka Sir" ya ce yana buɗe ƙofa zai fita sai kuma ya juyo ya sake kallon Maamah da Paaahh sai kuma ya fice cikin sauri kamar zai tashi sama. Ummimi dake tsaye itama a ƙofar ɗakin da take ciki ta jingina saboda ciwon da ƙafarta take mata a hankali ta ce "Abdul-Johar ka ajjiye mini yarinya a nan, kuma idan abu ya samu Maamah da Gadanga zan yi shari'a da kai in sha Allah" Paaahh ya kwantar da Aafiyyah a saman kujera a nutse bayan ya samu jikinta ya bar rawa sai kanta data dafe da hannu biyu. Ya juya ya kalli Ummimi dake tafiya a hankali har ta nemi waje ta zauna kusa da Aafiyyah. Shima zama ya yi kansa a ƙasa ya jima kafin ya ɗago ya ce. "Zahiyerh ki....," Ummimi ta katse Paaahh wajan ɗaga masa hannunta alamar bata buƙatar jin komai kuma ya tashi ya bar mata waje. "Don Allah ki saurare ni" "Me zan saurara Abdu? Don Allah bani waje kafin na yi abin da ban niyya ba, na gode da abin da ka yi mini haka ma, zan ɗauki yarinyata. Ko kuma shi Gadanga ya ɗauki matarsa idan yaga yana buƙata kafin a kashe ta ranku ya yi fari" ganin da gaske ba zata saurare shi ba,ya saka ya miƙe jiki a sanyaye ya bar main parlour ɗin gabaɗaya. * Muhammad na tsaye gaban madubin dake faffaɗan ɗakin nasa a hankali ya dubi ƙirjinsa da yaje aka yo masa zanen Scorpion a jiki, bai gama warkewa ba amma babu mai cewa zanen sabo ne saboda yadda mai zanen ya kasance ƙwararre. Tunda ya dawo yake tunanin mutane biyun can da suke kamanceceniyya ta hanyoyi mabanbanta, muryarsa da take iri ɗaya data Kimiyya ta bashi mamaki sosai amma abin da yafi saka shi shocked ya zama wani irin statue ya samu kansa cikin difficulty in making decisions bai shige tsananin kamarsa da Mutallab ba. Su waye su? Daga ina suke? Mene haɗinsa da su? Da mai kamammin, da mai muryar? Wannan tunanin ya saka Muhammad cikin wani irin tunanin ya kasa bacci har abin da ya daɗe bai sha ba, sai daya sha jiya. Tun a lokacin yasu yi wa Mutallab magana amma sai ya rasa me zai ce masa, ga kuma mutanen da suke wajan amma lallai yana son ya kasance Mutallab, shi kuma Mutallab ya kasance Muhammad ko hakan zai saka ya san abin da yake ɓoye. Tabbas wannan yana ɗaya daga cikin abin da ya saka AA MAJ yake ɓoye shi a kodayaushe. Muhammad ya duba time da date sai yaga ba ranar zuwan Aliyu bane. Cikin sauri ya ɗauki wayarsa da key ɗin mota ya nufi waje da sauri ya faɗa motar ya yi mata key kana ya yi reverse ya nufi hanyar Federal investigation department. Da hannu ɗaya yake driving ɗaya hannun kuma yana danna wayarsa da take nuna masa lokacin ɗin Aafiyyah dana dana Maj ɗin a haka ya isa Federal investigation department ɗin. Sai ya ajjiye motar a waje fuskarsa sanye da facemask kansa a ƙasa hannunsa cikin aljihu ya nufi ciki kai tsaye, cikin sa'a ya samu ana hargitsi a cikin wajan saboda wasu kidnappers da aka kawo da ƴan fashi hakan ya bashi damar shigewa salin alin babu wanda ya gan shi. Wata sa'ar ya kuma samu ganin ƙofar ɗakin da aka ajjiye Mutallab ciki a buɗe ya sunkuya ya shiga ciki, ya zubawa Mutallab dake jingine da jikin bango idanu hannunsa ɗaure da sarƙa, jikinsa duk shatin duka hannunsa na zubar da jini. Mutallab a jikinsa ya ji cewa ana kallonsa, bai san mene ya faru ba ya dai ji kallon ya bambanta da wanda ya saba ji securities ɗin wajan na yi masa, baƙon yanayin da ya ji bai saka ya ɗago kai ba, sai tsuke fuska da ya yi kamar zai fashe alamunsa ya nuna cewa a shirye yake da barin cikin gidan saboda ya kasa jure yadda yake mafarki da bestie a kodayaushe tana kuka tana masa magiya tare da nuna masa Aafiyyah. "Hello" Muhammad ya ce yana daga tsayen da yake. “Muryar kimiyya” ita ce ya ruski Moh, sai ya fara tunanin daman har yanzu Kimiyya bai manta da shi ba? Shi kenan bai tsane shi ba? Daman kimiyya zai iya neman shi? Sai yaƙi ɗago kansa, domin ba zai so haɗa idanu da kimiyya ba, ƙila shima zai yi masa kallon ya kashe Safiyyerh ne, tunda ya san labarin mutuwar Diyna da Jaaanah sai ya sake duƙar da kansa zuwa ƙasa kamar kodayaushe. "Hey, hello" Muhammad ya sake maimaitawa yana durƙosawa daidai inda Mutallab yake zaune waje guda. A hankali ya ɗago kansa, cin karo ya yi da fuskarsa mutumin daya jima yana tunani cikin ransa, suka zubawa juna idanu alamar waye kai? Kai ma waye. Suka kasa magana kowa da tunani a ransa, a lokacin ɗaya kuma suka lumshe idanu kana suka girgiza kai, at the same time suka sake buɗe idanu suna cije lips. Mutallab ya jima da sanin shi ɗaya Ammo da Aby suka haifa ban da haka da sai ya ce wannan mutumin da yake gabansa biyuninsa ne. Muhammad ne ya fara cewa "Waye kai? Who are you? Me ya sa muke kama, me ya sa komai namu yake iri ɗaya da kai? Ka sanni ne? Ko baka da labarina kamar yadda nima bani da labarinka? Me kake yi cikin wajen nan?" Muhammad ya jero tambayoyin. Moh yaƙi magana, yaƙi kallon Muhammad, baya son ganinsa ma, saboda gabansa faɗuwa yake. "Ina son taimakon ka" cewar Muhd. Nan ma Moh yaƙi magana. Muhammad ya gyara zaman shi sosai domin ya fahimci taurin kan Moh ya danne nasa sosai da sosai. "Ban san ka ba, ban taɓa ganinka ba ko a cikin baccina amma wannan kamannin ya shige ace kawai kama ce da Ubangiji yake samar da ita tsakanin bayinsa da suke doran duniya, akwai ɓoyayyen abu tsakanina da kai da rayuwarmu. Ban taɓa faɗawa kowa ba amma yau na gamsu zan faɗa maka wani abu daya shafe ni. Sunana Muhammad, na buɗe idanu a gidan marayu ban san yaushe na kasance a gidan marayun ba, amma a can granny da sanar mini cewa a wajan su na koyi zama, rarrafe, a gurinsu na fara zuwa makaranta. Sai dai bana ji domin tun ina ƙaramin nake cin zalin yara ƴan'uwana, bani da abokai bani da kowa a gidan. Granny kawai na sani me kula dani a makarantar na koyi harkar computer, su hacking da tracking da duk wani abu daya shafi Computer. Na rayuwa cikin damuwa da ƙuncin ma rashin ahali domin na gama sawa kaina bani da iyaye, wannan dalilin ya saka na fara zuwa club ina rage damuwa har na haɗu da abokai da suka sake koya mini shan abubuwan bugawar daga ciki har giya. Na aikata abubuwa da yawa, zina ce kawai bani da tabbacin ko na aikata ko ban aikata ba, kasan sharrin giya ai" Muhammad ya yi shiru zuciyarsa babu daɗi idanunsa na sauya sosai, ya kalli Moh sai yaga har lokacin kansa a ƙasa yake ya dunƙule hannunsa waje guda. A hankali ya ce "Ban san mene ya faru ba, watarana sojoji suka shigo makarantarmu a lokacin ma koyar da ɗalibai nake musamman ɓangaren crypto su data Analyst. Wani soja mai suna Aliyu ya ɗauke ni zuwa gidansa ya bani komai na rayuwa, ya kuma kore dukkan wani kaɗaici da nake ciki ya ajjiye ni a gidansa na computer ina yi masa aiki baya taɓa fushi dani amma duk ranar daya fahimci na fita da waje sai mun yi faɗa dashi, duk bana jin haushi har raina ya fara ɓaci saboda ni mutum ne da baya son ana tauye rayuwarsa, rayuwata tawa ce, halina nawa ne haka na yarda. Sai na fara zargin akwai wani abu game dani, mene dani? Mene abun i don't know, i really don't know kuma ban damu dana sani ba. Ganinka da ganin kamanninsa da muke ya saka na ji ina son fito da abin da yake ɓoye ka bani dama Please?" "Trust me" "I never trust anyone" Moh ya ce,a daƙile. "Ban baka labarina domin ka yarda dani ba, bana cutar da kowa kamar yadda bana bari a cutar dani. Ka bani dama trust me" cewar Muhammad. Moh yaƙi magana sai juyar da kansa gefe da ya yi kawai jikinsa na ɗan rawa. Muhammad ya ce "Don Allah?" "How?" In ji Moh. "Ka zama ni na zama kai" Sai Moh ya juyo gabaɗaya ya kalli Muhammad amma yaƙi cewa komai sai kallon Muhammad yake, is he alright? Anya yana da hankali ya san azaba da raɗaɗin da yake cikin wajan nan? Shine yake son cutar da rayuwarsa ta wannan hanyar mai hatsarin gaske. Muhammad ya ce "Zaka fita daga cikin Fcid, ka koma gidan da nake ciki da zama, ni kuma zan zauna a nan wajan a matsayin kai, ba wanda zai yi tunanin ba kai bane, Allah ba wanda zai gane" "Ni ɗan'daba ne, wanda mutane da al'ummar unguwarmu suka tsana na yi tambarin da babu wani daya isa ya yi kar ka so ka zama ni" "Just to help, we can help each others" Muhd ya ce a hankali Kafin Moh ya yi magana sai ganin Abbasa sukai yi ta bayyana a gabansu, Muhammad namiji amma sai daya tsorata ya nemi tashi a gigice kallon da ta yi masa ya saka ya dake kawai. Ya baza rigar jikinta hannunta riƙe da sanda idanunta rambaɗe da kwalli ta ce "Haƙiƙa Muhammad ya zo da magana mai kyau, wannan shine lokacin da kake jira Mai dawa. Baka da cikakken lokaci, kasafin ƙaddararsu ya fara ka tashi ka je ka sake tuna wasiyyar nan dake tattare da kai, idan kana son matarka da gaske ya zama wajibi a gare ka, ka bar gidan nan, idan kuma kuskurenka ya sake sawa ka rasa ɗaya yarinyar shikenan" MOH ya kalli Abbasa kafin ya ce "Kalli fuskarsa kalli tawa" Abbasa ta kalli fuskar Muhammad da yake wasai babu tabo balle sara balle kuma ɗinki saɓanin ta MOH. Ƙyaƙyacewa ta yi da dariya sosai hayaƙi na fita daga cikin bakinta kafin ta ɗaga sandan hannunta ta nuna Muhammad da shi, wasu surutai ta fara idanunta na firfitowa waje can kuma ta buga sandan sai wani abu ya haske kana hayaƙi ya fito ya sauka a fuskar Muhammad, ɗaya hannunta ta saka ta lashe tafin hannunta da dugun harshenta kana ta shafa hannunta a fuskar Muhammad. Cikin ƙaramin lokaci tabon fuskar Mutallab ya goge tas tare da komawa fuskar Muhammad ɗin. Da Muhammad da Mutallab suka shafa fuskarsu lokaci guda cike da al'ajabi tsohuwa Abbasa ita kuma ta tsuke fuska ta ce "Baka da lokaci, wa'adin da kake da shi na cika tabon fuskarka zai dawo, ga layar zanarka ka tashi ka sauya kayan jikin Muhammad kai ma ka bashi kayan jikinka" tana cewa haka ya buga sandan hannunta a jikin sarƙar da aka ɗaure Muhammad da ita sai ga sarƙar ta rabe biyu. Cikin sauri suka sauya kaya har lokacin Moh yana riƙe da wasiyyar Safiyyerh Abdulwahab wacce yake jinta kamar Safiyyerh domin daga hannun Deer ɗinsa ta fito yana girmamata. "Ga key ɗin motata nan, ga key gidan nan ga kuma wayata nan. Password na komai da yake gidan ka saka" sai ya yi shiru a hankali ya ce ka saka "AAMAJ zai buɗe hatta na jikin laptop, computer za kaga direction na gidan a cikin motar" Sai Moh ya jinjina kai bayan ya ɗauki wayar da komai ya saka cikin aljihu kana ya ɗauki facemask da hular ya saka. "Allah Ya taimaki Mai dawa sarki me jeji, jeka abinka lokaci ya fara" Muhammad ya ce "All the best" Moh ya rufe idanunsa, ita kuma Abbasa ta juyar da kan Muhammad da sauri Moh ya danna layar bayan ya matsa jikin bango nan take ya ɓace. Kafin Muhammad ya buɗe idanu itama Abbasa ta ɓace daga wajan. Fitarsu ke da wahala Dig Abdul-Johar Marafa ya shigo ya fara tambayar Muhammad da tunanin shine Moh kuma Scorpion ɗin da suka tsare har suke ƙoƙarin zartar da hukumcin kisa ko hauka a wajansa. Wata iska mai kama da iskar ƴanci Moh ya shaƙa bayan ya fita zuwa inda motar daya tabbatar ita ce ta Muhammad, ya buɗe idanunsa ya dinga kallon sararin samaniya yana shaƙar iska da kyau amma zuciyarsa kamar ta yi bindiga kansa na wata sarawa da ƙarfi. Yaushe rayuwarsa za ta yi daidai kamar ta sauran mutane? Waye zai fahimce shi ko yaya ne? Yaushe duniya da mutanen dake cikinta zasu wanzar da adalci a gare shi? Me ya sa mutane suka kasance masu tsananin son kansu suka zama azzalumai? Me ya sa kowa ya tsane shi ne? Idan yanzu ya kasance ɗan'daba me ya sa sanda yake lafiyaye aka yi masa tsana, tsanar ma har da iyayen da suka kawo shi duniya? Shin mene laifin ɗan'daba? Shi ba mutum bane? Aka san dalilin daya saka ya zama ɗan'daba ɗin? Ya yi shiru da sauri kuma ya buɗe motar ya shiga gwargwadon yadda zuciyarsa ke bugawa ta cikin ƙirjin gwargwadon yadda yake driving motar tare da sa mata giya yana shige sauran motoci. A haka ya isa gidan ya yi parking ya shiga, kamar yadda ya ce AAMaJ shine password haka ɗinne, ya tsaya gaban computer sai tunanin recorded ɗinsa da Kimiyya ya faɗo masa. Halin da zuciyarsa take ciki ya saka ya ji zaman gidan bai masa ba, yana buƙatar ganin Goje da Mangal yana buƙatar kayan caji zama jewa yake so bana gida ba, zaman dabarsu ya fi masa komai. Zuwan shi ke da wahala AA MAJ ya shigo, Moh bai motsa ba har Maj ya ƙarasu yana faɗin "Na tura maka abu ta mail ɗinka, check" Sai Moh ya yi shiru kawai, bai san Maj sosai ma amma ya ganshi sau biyu da sanda ya cakawa Aafiyyah wuƙa da sanda ya ɗauke Aafiyyah a gaban Maj ɗin. "Muhammad" Nan ma Moh bai motsa ba. "Check ur mail aiki ne na gaggawa ka ji?" "Uhm" kawai Mutallab ya ce. AA MAJ ya zauna saman kujera sai ya ɗakko wayarsa dake ringing number Aafiyyah ya gani kuma vedio call kamar ba zai ɗauka ba sai ya ɗaga, fuskar Aafiyyah ta bayyana tana zaune saman kujerar dake office ɗinta ta yi rolling mayafin abayar jikinta a hankali ta ce "Ummimi na buƙatar ganinka, idan ka je gida" "How are you?" Cewar Maj yana sake zuba mata idanu sosai. Sai ta yi cute smile tana ɗaga kafaɗa ta ce. "Good" Maj ya jinjina kai ya ce "Wife, say hi to Muhammad" ya ce yana juya wayarsa zuwa inda Mutallab yake tsaye ya juya baya. Moh sarai ya ɗauki muryar Aafiyyah a cikin kunnuwansa kenan Maj shine mijin Aafiyyah? Da gaske daman tana da aure? Ya cije bakinsa da ƙarfi yaja numfashi yana jin to mene damuwarsa bama haka ne a gabansa ba a yanzu ɗin. "Muhammad" Aliyu ya kira Mutallab da tunanin shine Muhammad. A hankali Moh ya juyo yana kallon screen ɗin wayar Maj, idanunsa ya sauka a fuskar Aafiyyah, itama ɗin shi take kallo can ta ce "How are you?" Ɗauke kai ya yi yana barin wajan tare da nufar wani ɗaki daya gani a buɗe. * Su wajan bakwai ne a cikin gidan gonar bayan kowa ya fito daga cikin mota hankali a tashe Eng Ali wali ya ce "Wallahi akwai matsala idan Scorpion ya buɗe bakinsa a kan mu, kafin Fcid su saka shi yin magana mu yi ƙoƙarin fito da shi a ɓoye kota halin yaya ne" ya faɗa yana barin jikin motarsa tare da saɓa babbar rigar jikinsa zuwa gefe. Sharfaɗi ya ce "Ni mene haɗina da wani Scorpion da har kuka kira ni zuwa meeting ɗin nan naku?" "Kana da haɗi kowa, domin kasan mu, muma mun sanka. Yana da kyau mu nemi sulhu da shi mu ji me muka yi masa da yake ƙoƙarin raba mu da rayuwarmu a dole? Hankalina a tashe yake nine next plan ɗinsa a wanda zai kashe, wallahi ban shirya mutuwa a yanzu ba, ina da buri da muradan da nake ƙoƙarin cimmawa" Hon Maɗaita dake jingine da jikin motarsa ya yi murmushi, kallon Eng Ali wali kawai yake domin shi ba Scorpion ne a gabansa ba, idan ya tuna maganar da Alhaji Wada ya zo masa da ita akan cewa wai Ali wali ya yi tarayya da matarsa Laylerh sai ya ji ya rasa sukuni ta inda zai fara ɗaukan mataki kawai yake tunani, koda tsohuwa Abbasa bata ce ya kwanta da Sabrina Noor ba dole ya yi amfani da ita wajan ɗanɗanawa Ali wali maɗaci a baki. "Hon Maɗaita ana ta magana baka ce komai ba" "Me zai ce daman? Tunda ya san ba shi za'a kashe yanzu? Wallahi dole mu fito da Scorpion dole ne" Sai Hon Maɗatai ya kalli Ali wali ya ce "Ali wali kenan." "Ban fahimci Ali wali kenan ba? Kana nufin zan zuba idanu na mutu ne? Ai sai dai a yi mutuwar kasko" Maɗaita ya jinjina kai ya ce "Ba za'ayi hakan ba, za'a fito da Scorpion ta ɓoyayyiyar hanya amma ka bari mu kammala interview ɗin da BBC za su yi wa ƴan ta karkaku ko? Bayan wannan sai mu zauna a yi magana" Sharfaɗi ya ce "BBC ko? Ai kamar komai ne a Abuja i will be there nima" Suka amince da wannan batun, Hon Maɗatai sai kallon Eng Ali wali yake yi yana murmushi a ransa da wannan tunani kowa ya shiga motarsa suka bar gidan gonar Sharfaɗi. * A ɓangaren Aafiyyah ta samu appointment na ganawa da Dr Abraham Denial David ta dalilin I. Qasim wanda bata san yadda aka yi ya nema mata appointment ɗin ba. I. Qasim ya samu Dr Hamza a office kasancewar Dr Hamza abokin Dr Hash ne ya nemi alfarma daya sauya masa alluran wajan Dr Hash da ya kewa Aafiyyah da wanda shi kuma yake yi mata. Tunda Dr Hamza ya san komai dangane da allurar da Dr Hash ya kewa Aafiyyah. Bayan sun gama magana I. Qasim ya nufi ɓangaren da jariran suke ciki a hankali ya zubawa ɗaya idanu daya ɗan fara ƙwari kamammin da yake hangowa a fuskar macen har tsoro suke bashi, ya dinga kallon jaririyar kafin ya saka hannu ya ɗauke ta a hankali ya rungometa a ƙirjinsa wani hawaye na cika idanunsa ya jima kafin ya ajjiyeta ya ɗauki namijin Allahu Akbar kawai kimiyya ya ce sanda ya kalli kamannin namijin ya jima kana ya ajjiye shi ya fita zuwa special room ɗin da mahaifiyar tasu take ciki ya ƙarasa har yanzu bata motsi muryarsa a raunace ya ce. "Motsin ki cikin lafiya da dawowar ki cikin hayyacinki shi kawai nake buƙata, babu lokaci na kasa haƙuri zuwa sadaki da inda ya dace. Get well soon dear Allah Ya ba ki lafiya" ya ce hawaye na bin fuskarsa sai ya ji ya riƙe hannunsa da sauri ya kalle ta bata motsi sai hawaye da yake bin idanunta alama karaya. * Suna tsaye adabar tasu su kaga ya faɗo cikin sauri Mangal ya ce "Kutumar uba salatin arna, sai da kai mai gida, kai ne da gida kai ne da dawa dar yi shirunka na waje na" Goge ya bankawa Mangal harara ya ce "Ankar ɗanwahala jemamme" "Dar, a huce" cewar Mangal. Goje ya kalli Moh yana karkace bakinsa kafin ya ce "Shirwa kake baka jewar banza, na san daman dole zaka fito da iznin mai duka lillahi rabbil samawati. Dar ne wannan" "Goje" Moh ya kira sunan shi yana gyara saitwarsa kafin ya ɗago kai ya kalle shi ya sake cewa "Goje" "A lafiya mai dawa" "Ina buƙatar kayan caji" Da sauri Mangal ya ce "Sha fara kaga aljan kake so,ko ƙwayar doki ko mai zubin lemon fenta kake buƙata" "Can ji babanka Mangal zan maka tsago ƴan uwa a wuyanka. Sha fara ka ci jahilin duka yake so" "Yawane wannan Oga Goje ka faɗa mana kai kodayaushe ciki ne" Sai Goje ya juya ya amshi kayan hannun Mangal ya miƙawa Moh ƙwaya guda biyu cikin sauri ya amsa ya dannata a ƙasan harshensa a gaggauce kamar mayunwaci. "Ya aka yi kamar hannun waɗancan cinnaku? Damar na ce kar ka faɗa da yarinyar nan ta yi zubin kimini amma ka jirga da zancenta, su masu ɗankwali ba'a taɓa sirri da su gashi yanzu ta janyo ruwa ƴar wahala kawai sam ba ta yi ba" "Oga Goje da ka yi makaranta ba ƙaramin mai basira za'ayi ba, Allah Ya tarfawa garinsa nono" "Goje" "Mai dawa" "Ina matar dana ɗakko a gidan Ali wali ranar da zan bawa yarinyar can labari, ina take tana ina?" Moh ya fara jikinsa na kakkarwa da ɓari domin ƙwayar ta fara aiki, duk suka ja baya ya faki idanunsa ya fisgi wuƙa a ƙugun Mangal ya ce "Tana ina?" Cikin sauri Goje ya ce "Bamu ganka ba" kallon Goje kawai Mai dawa ya ke yi kafin ya zallaƙo harshe ya lashe gefen bakinsa sai ya juya dif dif dif ya yi kwana. * Kamar yadda Bbc ta saka musu rana bayan an fafata a interview ɗin tsakanin Eng Ali wali, Hon Maɗatai, Dr Abraham Denial David. Bayan sun fifo Dr Abraham Denial David ya ja mutanensa a lokacin mamaki ya gama cika zuciyar Hon Maɗatai ganin yadda Dr Abraham ya yi masa tawaye daman ƙarya yake yi da yake cewa ya sallama masa kujerar? Eng Ali wali ma ya kwashe jama'arsa suka bar wajan ya rage sai Hon Maɗatai. Ƴan jarida sun cika a wajan da gidan rediyo tv da ƴan media suna sun tattaunawa da Hon Maɗatai akan mene gaskiyar alaƙar shi da Dr Abraham Denial David? Ya aka yi aka haihuwa a ragaya? Hon Maɗaita ya nufi motarsa zai shiga. Jami'an tsaro ne ta ko'ina cikin kayan kaki ma bambanta, duk da cewa yammacin ranar lahadi ne a watan Fabrairu bai hana ta gane fuskarsa ba. Cikin tashin hankali jikinta na rawa da kyarma ta nufe shi tare da ƙoƙarin cakomo wuyan babbar rigarsa tana furta cewa "Shi ne, wallahi shi ne, daman na ce zan gano shi" a gigice mutumin dake ƙoƙarin shiga motarsa da aka buɗe masa ya yi baya yana mai ƙarewa matar kallo sosai sai dai ya kasa gano ko wace ita? Daga ina me kuma take buƙata. "Wace ita?" Ya furta yana tambayar zuciyarsa tare da kallon gefe. "Wallahi shi ne, mugu azzalumi sai ka yi kuka, ka wulaƙanta " Jin furucinta ya saka ƴan'jarida dawowa kan ta, suka fara tambayar "Kin san shine? Mene haɗinki da shi?" Kafin ta yi magana wani ya ce "Arrest her, ku kamata" A hankali ya jingina da jikin motar can ya numfasa yana kallon yaronsa ya ce "Wace ce? Na santa ne? To me ya sa take abu kamar ta sanni?" "Sir, da gaske ta sanka bana jin ko mutuwa ta yi ta dawo zata manta fuskarka, kuma zamanta a raye yana nufin abubuwan da yawa dole a yi wa tufkar hanci, kar a bari ƴan'jarida su samu ganawa da ita, even your securites, wannan matsalar kai da kai ce kuma zata shafi kimarka" cike da mamaki ya yi ta kallon yaron nasa na tsayin sacanni da ƙyar ya cije leɓe ya ce "To ina na santa? Me ya sa zata zama damuwata?" "Sir ita ce wacce ka saka aka kawo maka ita, wacce ka yi wa fyaɗe a lokacin.....," "Ya isa!" Ya ce yana jin jiri na neman ɗauke shi, ya dubi tarin jama'ar da suke wajan can ya yi murmushi yana ɗauke fuska sai kuma ya ƙurawa yaron idanu ya juya ya kalli matar ya gyatsine fuska ya ce "kuma ta kasance a raye ya haka? To a yi hanzarin toshe wannan ɓarnar ya zama kamar ba a yi ba" "Amma me ya kamata a yi mata?" "A yi mata allurar hauka, wacce ake yi duk shekara da wata wata kana a kaita gidan yari, life in prison har ta mutu. Bayan haukan zata mance komai, su ƴanƴan talakawa wama ya damu da su mutu ko su yi rai bata da wani mai tsaya mata kai mutuwa ma za ta yi" yana faɗin hakan ya shige mota. Tana takure a jikin ƙofar ɗakin da aka ajjiyeta idanunta ƙur a kan photonsa zuciyarta sai zafi take mata wani abu ya tsaya mata. Da sauri ta juya jin an buɗe ƙofa wani mutum ne sanye da farar riga ya rufe fuskarsa hannunsa riƙe da ƙaton sirinji iya ruwan allurar da ya yi ja abin tsoro ne, ta fara ja da baya amma a haka ya fincikota tare da yin cilli da ita,ta faɗi saman carpet bai tsaya jiran komai ba ya caka mata allurar a ƙashin bayanta wajan spinal cord ihu ta fara da birgima idanunta ya shiga ƙaƙƙafewa jikinta na sandarewa ta dinga buga kanta da jikin bango tana buge-buge a hankali jini ya fara fitowa ta cikin hanci da bakinta tabbacin allurar ta amshe ta za kuma ta yi aikin da ake buƙata a jiki da ƙwaƙwalwarta. Bayan ya yi mata allurar ya fito daga ɗakin ya dubi Hon Maɗatai ya ce "Done sir, sai a samu mai kai ta gidan yarin......," kafin ya ƙarasa maganar daya cikin redia sun ji muryar wata budurwa na faɗar cewa Hon Maɗatai ya yi mata ciki idan ƙarya take yi a tambaye shi. Sai Hon Maɗatai ya ƙyaƙyace da dariya kafin ya ce "Har abada babu mai yarda yarinya duk da ban san wacece ke ba amma zan yi maganinki" ya juya ga yaronsa ya ce "A shirya report ɗin ƙarya cewa bana haihuwa bani da cikakkiyar lafiya" Daga can gefe suka ji an ce. "Idan baka haihuwa Safiyyerh kuma ƴar wacace don banbaka?" Da sauri ya juya sai ya arba da Moh zaune saman kujera hannunsa riƙe da wuƙa. Hon Maɗaita ya ce "Wace Safiyyerh? Wacce Safiyyerh?" "Safiyyerh matata, wacce ka saka aka kashe saboda ka gano cewa ƴarka ce...... 💥Chapter 7: The Interview AA MAJ tafukan hannayensa ya saka da niyyar janyo ta zuwa jikinsa ganin yadda lokaci ɗaya ta hargitse kamar mai tsoran shi,ko sumbatar da yake mata ne bata so? Sai ya ji wani iri a gangar jikinsa duk da ƙoƙarin ganin ya saka Maamah ta nutsu da shi amma abin na neman fassakara, ya san daman it's very difficult to her ta amshe she lokaci guda domin basu da shaƙuwa da kuma jituwar da za'a yi samun fahimtar juna cikin ƙanƙanin yanayi. Auren shi da ita, ƙaddara ne wacce shi da ita ɗin, babu wata wanda ya isa ya gujewa faruwar hakan, she loves Maamah tun kafin yanzu babu wata ƙaddara da zata iya zuwa ta yi sanadiyyar rabuwar su, ko akwai wannan ƙaddarar,to; ba dai ta raba su da juna ba, sai dai wacce za ta iya ƙara kusanta zuciyoyinsu waje guda a cikin ƙirji da gangar jikinsu. Sai ya ja numfashi ta ƙirji, ya kuma ya haɗiye ta ƙirjin nasa,idanunsa na zube a saman fuskarta, yana ƙoƙarin lalubu yanayin da emotions ɗin da take ciki a yanzu, da son lalubu matsayinsa a zuciyarta ta cikin idanun nata. "Lafiya kike?" Tambayar ta fito daga bakinsa kai tsaye yana matsawa gare ta tare da riƙo hannayenta. "Yaya.. yaya... Please kar ka zo wajen, kar ka zo inda nake, yaya Please". Matse hannunta ya yi, yana riƙo fuskarta tare da tallafo gadon bayanta cikin son lallashinta wanda hakan ba ɗabi'ar AA MAJ bace, yana mamakin yadda a lokuta mabanbanta ya kan iya magantuwa a gaban yarinyar daya gama gina ƙiyayyarsa a zuciyarta tun tana rarrafe. Ya kawar da tunanin wajan sake furta "Maamah! Are you okay?" "I'm not, tsoro nake ji,bana son abin da kake yi mini kai na zai fashe" ta ce a gigice tana sake kwacewa daga riƙon da ya yi wa hannayenta. Reflection take gani, shuɗaɗɗan abubuwan da suka kasa samun gurbi na tuna su a zuciyarta a yanzu, sune suke remending kansu ta cikin idanunta sai take ganin kamar abu makamamcin hakan ya taɓa faruwa a gare ta, ita Maamah wani ya taɓa attacking yi mata kiss wanda a wancan lokacin cikin tsoro take, wannan dalilin ya saka tsoron nata ƙara girmamawa a cikin zuciyar Aafiyyah Abdul-Johar Marafa. Ta dinga girgiza kanta idanunta a rufe ruf ƙirjinta na ɗagawa tare da bugun zuciyarta wanda yake tafiya daidai da sautin fitar hucin AA MAJ. A hankali ya sake ta yana ja da baya can kuma ya yi sauri ya juya tare da barin bedroom ɗin nata yana dafe saman goshinsa. Aafiyyah ta sulale a wajan tana nishi hannunta ta saka ta daddafe kanta dake ƙoƙarin raɓewa gida biyu. Hango mutum take sanye da uniform yana ƙoƙarin sanya bakinsa cikin nata, baƙin mutum ne, duk da dishi-dishi take gani idan ta matsa kanta wajan sai taga fuskar wanda yake kissing ɗin nata, sai taji kanta ya sara musamman ta tsakiya. A hankali ta jingina da jikin bangon bedroom ɗin ta cure waje guda, har wata ramewa take wajan ƙoƙarin tuna abin da take jin tana da alaƙa da su, mene ya faru da rayuwarta? "I am sorry Maj, bana nufin ƙuntata maka i am sorry...," ta kasa ƙarasawa. Cikin sauri kuma ta miƙe tsaye kanta babu ko ɗankwali balle takalmi ta nufo downstairs tana kiran sunan J. "Yaa J Yaa J Yaa Junaid" Ta ce tana sakkowa daga stairs ɗin benen idanunta rude a kuma hargitse take kana ganinta kasam babu lafiya. Ummi dake zaune tana duba wasu kayan turaren wuta daga S Bayero wanda a lokacin shirye-shiryen tariyar Aafiyyah ɗin ake yi ba tare da saninta ba. Ummi ta ajjiye wayar hannunta tana kallon Aafiyyah kafin ta ce "Maamah" ta kira sunan Aafiyyah. "Ummi ina Yaa J?" "Maamah kina lafiya dai? Wannan kiran a gigice na magani na mene cikin ƙanƙanin lokaci?" Cewar Ummi. Aafiyyah ta girgiza kai ta ce "Kar ki damu Yaa J nake nema" "Yana cikin bedroom ɗinsa, amma...," bata ƙarasa maganar ba jin muryar Paaahh a bayanta hakan ya saka ta juyo tana kallon shi kafin ta ce "Yallaɓai meke faruwa ne?" Ya girgiza kai yana neman waje ya zauna kansa a ƙasa can ya nisa ya ce "Me zan cewa Zahiyerh ne? Me zan ce wanda zata gasgata ni ta san cewa ban rufe ta ba?" Ummi ta kalli mijin nata tana jinjina wa karamcin shi da ƙoƙarin ganin ya kyautata alaƙar shi da Ummimi jajircewar shi a matsayin uban yara biyar na sawa ta ji ta sake ƙaunar Dig Johar ya kodayaushe sosai yake da ƙoƙarin jan yaransa a jiki da kyautatawa zamantakewar shi da su, ya yi ƙoƙarin da gaske wajan bawa yaran nasa tarbiyya da ilimi da mu'amalar zama da mutane. Ya musu hani ga abu mara da muhimmancin taimakon Ɗan'adam. "Na san Ummimi ba zata fahimta a yanzu ba, domin ka tafka mata babban kuskure wajan ɓoye mata abin da ya faru da Maamah, yana da kyau ka sanar da ita koda ace bata ƙasar ne. Yanzu kam ba zata fahimta ba, bana jin zata sauraren ka ma" Paaahh ya ce "Ban ɓoye mata da nufin cutar da ita ba, saboda yanayin condition ɗinta na hawan jini kin san abu idan akan Maamah ne da Aliyu idanun Zahiyerh rufewa yake yi" "Haka ne. Ɓoyewar ma soyayya ce ta ja, amma ka yi ka je ka fahimtar da ita ko da ba zata saurara ba" Paaahh ya girgiza kai, yana ɗan kaɗa ƙafafuwansa ya ce "Amma...," "No, but." Cewar Ummi tana kallon shi. Kafin a hankali ta ce "Komai ya faru da Maamah ba laifin kowa bane sai naka, da nawa domin har gobe ba zan daina jingina laifin akan ka ba, duk da cewa a farko bamu san dalilin shigar tata ba. Amma sanda ta dawo mana gida a maye a can ƙasar da muke a ta faɗi komai. Ka yi mata al'ƙawarin da ka san cewa ba zaka iya cika mata ba, kai ne ka buɗe wannan ɓarnar Yallaɓai. Gashi ka sake yin wani laifin akan wani babu shawarar yaran data Ummimi ka haɗa Maamah aure da Aliyu, which is no good for me kenan" ita kanta zuciyarta babu daɗi ɗin. "Yanzu laifi ne don uba ya zaɓawa ɗiyar cikinsa abin da yake ganin ya dace da ita Ummi? Ban yi haka don cutar da ita ba, mene ya saka zan cutar da Maama" sai miƙe tsaye fuska babu alamun rahama ya ce "Na zama mugu ga ƴar dana haifa ko?" "Idan kai ka haifi Maamah waye mahaifina, ni kuma?" AA MAJ ya ce. Da sauri Ummi ta miƙe tsaye jikinta na rawa idanunta akan Aliyu, shi kuma Aliyu idanunsa akan Paaahh daya sunkuyar da kansa ƙasa. Aliyu idanunsa jajur zuciyarsa sai rawa take yi amma yana dakewa tare da hana kansa zaucewa, ba wai tsoron yake idan ace ba shi ne halalataccen ɗan gidan Dig Abdul-Johar Marafa ba, tsoro ɗaya bai san waye zai kasance mahaifi a gare shi ba, da hanyar sunna aka haife shi ko akasin hakan. Wannan tunanin ke sake haifar da ruɗani a zuciyar AA MAJ. Ya gyara tsaiwa ya ce "Daddy kai ne mahaifina? Ummi ce ta haife ni ko ni ne bare a cikin zuri'ar Marafa?" "Aliyu!" Ummi ta kira shi da ƙarfi. Sai ya kalli Ummi kana ya girgiza kai har yanzu yana tsaye saman ƙafafuwansa cike da jarumta irin wacce ya samu wajan hurar da sojoji da nuna rashin damuwar abin duk yadda ya kai ga ci masa zuciya. "Ummi ba zan ji babu daɗi ba idan ya zamana cewa bake ce mahaifiyata ba, domin babu wani tarihi da zai zo ya sa na sauya miki matsayin Uwa, babu lokacin da zai gabata da ba za ki amsa sunan Uwa a wajan Aliyu ba" sai ya yi shiru yana kaiwa da komowa ya furzar da iska a hankali kana ya juya ga Paaahh ya ce "Bana son a raunata zuciyar yarinyar nan da kuka bani aurenta, bana son hakan ko kaɗan. Waye ɗanka tsakanin ni, da kuma ita?" "Answer my question, kar ka bar ni cikin tunanin da zullumin rashin sanin abin da ban sani ba" "Aliyu, will you shut up?" "Why? Me ya sa zan yi shiru?" Maj ya ce yana sake ƙanƙantar da ganinsa akan Paaahh kafin ya ce "Sir. Ka san ciwon da mutum yake ji a zuciya ya rayu da mutanen da yake tunanin sune komai nasa, sune inuwar da yake zama cikinta ya ji sanyi, sune garkuwar da za su iya kare shi daga faruwar wasu abubuwan, sune katangar da zai iya jingina ya yinda ya gaza tsaiwa a saman ƙafafuwansa? Kun san raunin da mutum zai iya samu a lokacin da ya ji cewa wanda ya gama saka ran sune iyayensa kuma ace basu ne suka haifeshi ba. Sir ka faɗa mini ba komai zan iya ɗauka da gaske zan ɗauka" Paaahh ya ɗago rinannun idanunsa ya kalli Maj ya kasa magana ƙoƙarin barin wajan yake cikin sauri Maj ya tari gaban Paaahh ya ce "Junaid ɗanka, Dr ɗanka, Awais ɗanka wannan dalilin ya saka baka haɗa auren Maamah dasu ba, ka aura mini ita domin na rufa mata asiri kar abin data aikata ya fallaso ga jama'a ko? Wannan shine hujja?" "Wanne abu na aikata ni Safiyyerh? Yaya me aka ce na yi? Daddy Ummi me na yi da har za'a rufa mini asiri?" Aafiyyah ta tambaya jikinta na rawa idanunta cike da hawaye, fitowarta daga ɗakin J kenan amma yaƙi saurarta yaƙi ko kallon ta ma, yaƙi bata listing ears bai ma damu da condition ɗin da take ciki ba. Maj ya runtse idanunsa yana sake dafe saman goshinsa tare da murzawa a hankali yaƙi kallon Aafiyyah kamar yadda Paaahh ɗin yaƙi kallon ta, tuni Ummi ta haura sama idanunta cike da hawaye bata son ma Aafiyyah tayo kanta da wannan tambayar da bata da amsarta bata san me zata cewa yarinyar ba, bata ma da abin cewar kalamai sun yi kaɗan a cikin bakinta. Aafiyyah ta kalli Maj ta nufe shi tana zuwa ta kama hannunsa cikin rashin fahimta ta ce "Yaya wani abu aka maka na aikata? Da har zaka rufa asiri ka aure ni? Me na aikata a duniya da zan iya zama baƙin jini a idanun mazan dake duniya?" Zame hannunta Maj ya yi yana nufar hanyar fita. "Na san zaka faɗa mini Yaya, kar tsanar da ka yi mini a baya ta yi tasirin faɗa mini abu mai muhimmanci a rayuwata, meke faruwa?" Still Aliyu yaƙi magana. Sai ta nufi wajan Paaahh ta ce "Shekaruna nawa yanzu? Da shekarun baya dana yanzu na jin cewa akwai bambanci a cikin rayuwar Safiyyerh ta yanzu data baya, what's going on? Mene aikata me muni har haka? Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un! Daddy wace ni? Who is Safiyyerh? Don Allah...," numfashinta ne ya fara misbehaving a ƙirjinta, ta cire hannunta guda ɗaya ta ɗora a ƙirjin daidai ƙahon zuciyarta da take jin kamar ta kumbura ta cikin ƙirjin tana numfashi da ƙyar ta ce "Ka faɗa mini daddy don Allah, me na yi? Ba dai ɓata maka rai na yi ba, ba dai alƙawari na saɓa ba wacece ni?....." "Shiru haka nan Maamah" Ta girgiza kai Aafiyyah ta yi tana riƙe hannun Paaahh ta ce "Allah zan iya mutuwa idan baka faɗa mini ba" "Yadda ba ki mutu a baya ba, ki ka tsallake haka ba za ki mutu a yanzu ba, za ki rayuwa lallai za ki rayuwa" Paaahh ya ce yana riƙo Aafiyyah zuwa jikinsa ganin kamar numfashinta idan ya fita baya dawowa. Aliyu dake baƙin ƙofa ya ce "Idan ta mutu, mutuwar ta rataya ne a wuyanka Sir" ya ce yana buɗe ƙofa zai fita sai kuma ya juyo ya sake kallon Maamah da Paaahh sai kuma ya fice cikin sauri kamar zai tashi sama. Ummimi dake tsaye itama a ƙofar ɗakin da take ciki ta jingina saboda ciwon da ƙafarta take mata a hankali ta ce "Abdul-Johar ka ajjiye mini yarinya a nan, kuma idan abu ya samu Maamah da Gadanga zan yi shari'a da kai in sha Allah" Paaahh ya kwantar da Aafiyyah a saman kujera a nutse bayan ya samu jikinta ya bar rawa sai kanta data dafe da hannu biyu. Ya juya ya kalli Ummimi dake tafiya a hankali har ta nemi waje ta zauna kusa da Aafiyyah. Shima zama ya yi kansa a ƙasa ya jima kafin ya ɗago ya ce. "Zahiyerh ki....," Ummimi ta katse Paaahh wajan ɗaga masa hannunta alamar bata buƙatar jin komai kuma ya tashi ya bar mata waje. "Don Allah ki saurare ni" "Me zan saurara Abdu? Don Allah bani waje kafin na yi abin da ban niyya ba, na gode da abin da ka yi mini haka ma, zan ɗauki yarinyata. Ko kuma shi Gadanga ya ɗauki matarsa idan yaga yana buƙata kafin a kashe ta ranku ya yi fari" ganin da gaske ba zata saurare shi ba,ya saka ya miƙe jiki a sanyaye ya bar main parlour ɗin gabaɗaya. * Muhammad na tsaye gaban madubin dake faffaɗan ɗakin nasa a hankali ya dubi ƙirjinsa da yaje aka yo masa zanen Scorpion a jiki, bai gama warkewa ba amma babu mai cewa zanen sabo ne saboda yadda mai zanen ya kasance ƙwararre. Tunda ya dawo yake tunanin mutane biyun can da suke kamanceceniyya ta hanyoyi mabanbanta, muryarsa da take iri ɗaya data Kimiyya ta bashi mamaki sosai amma abin da yafi saka shi shocked ya zama wani irin statue ya samu kansa cikin difficulty in making decisions bai shige tsananin kamarsa da Mutallab ba. Su waye su? Daga ina suke? Mene haɗinsa da su? Da mai kamammin, da mai muryar? Wannan tunanin ya saka Muhammad cikin wani irin tunanin ya kasa bacci har abin da ya daɗe bai sha ba, sai daya sha jiya. Tun a lokacin yasu yi wa Mutallab magana amma sai ya rasa me zai ce masa, ga kuma mutanen da suke wajan amma lallai yana son ya kasance Mutallab, shi kuma Mutallab ya kasance Muhammad ko hakan zai saka ya san abin da yake ɓoye. Tabbas wannan yana ɗaya daga cikin abin da ya saka AA MAJ yake ɓoye shi a kodayaushe. Muhammad ya duba time da date sai yaga ba ranar zuwan Aliyu bane. Cikin sauri ya ɗauki wayarsa da key ɗin mota ya nufi waje da sauri ya faɗa motar ya yi mata key kana ya yi reverse ya nufi hanyar Federal investigation department. Da hannu ɗaya yake driving ɗaya hannun kuma yana danna wayarsa da take nuna masa lokacin ɗin Aafiyyah dana dana Maj ɗin a haka ya isa Federal investigation department ɗin. Sai ya ajjiye motar a waje fuskarsa sanye da facemask kansa a ƙasa hannunsa cikin aljihu ya nufi ciki kai tsaye, cikin sa'a ya samu ana hargitsi a cikin wajan saboda wasu kidnappers da aka kawo da ƴan fashi hakan ya bashi damar shigewa salin alin babu wanda ya gan shi. Wata sa'ar ya kuma samu ganin ƙofar ɗakin da aka ajjiye Mutallab ciki a buɗe ya sunkuya ya shiga ciki, ya zubawa Mutallab dake jingine da jikin bango idanu hannunsa ɗaure da sarƙa, jikinsa duk shatin duka hannunsa na zubar da jini. Mutallab a jikinsa ya ji cewa ana kallonsa, bai san mene ya faru ba ya dai ji kallon ya bambanta da wanda ya saba ji securities ɗin wajan na yi masa, baƙon yanayin da ya ji bai saka ya ɗago kai ba, sai tsuke fuska da ya yi kamar zai fashe alamunsa ya nuna cewa a shirye yake da barin cikin gidan saboda ya kasa jure yadda yake mafarki da bestie a kodayaushe tana kuka tana masa magiya tare da nuna masa Aafiyyah. "Hello" Muhammad ya ce yana daga tsayen da yake. “Muryar kimiyya” ita ce ya ruski Moh, sai ya fara tunanin daman har yanzu Kimiyya bai manta da shi ba? Shi kenan bai tsane shi ba? Daman kimiyya zai iya neman shi? Sai yaƙi ɗago kansa, domin ba zai so haɗa idanu da kimiyya ba, ƙila shima zai yi masa kallon ya kashe Safiyyerh ne, tunda ya san labarin mutuwar Diyna da Jaaanah sai ya sake duƙar da kansa zuwa ƙasa kamar kodayaushe. "Hey, hello" Muhammad ya sake maimaitawa yana durƙosawa daidai inda Mutallab yake zaune waje guda. A hankali ya ɗago kansa, cin karo ya yi da fuskarsa mutumin daya jima yana tunani cikin ransa, suka zubawa juna idanu alamar waye kai? Kai ma waye. Suka kasa magana kowa da tunani a ransa, a lokacin ɗaya kuma suka lumshe idanu kana suka girgiza kai, at the same time suka sake buɗe idanu suna cije lips. Mutallab ya jima da sanin shi ɗaya Ammo da Aby suka haifa ban da haka da sai ya ce wannan mutumin da yake gabansa biyuninsa ne. Muhammad ne ya fara cewa "Waye kai? Who are you? Me ya sa muke kama, me ya sa komai namu yake iri ɗaya da kai? Ka sanni ne? Ko baka da labarina kamar yadda nima bani da labarinka? Me kake yi cikin wajen nan?" Muhammad ya jero tambayoyin. Moh yaƙi magana, yaƙi kallon Muhammad, baya son ganinsa ma, saboda gabansa faɗuwa yake. "Ina son taimakon ka" cewar Muhd. Nan ma Moh yaƙi magana. Muhammad ya gyara zaman shi sosai domin ya fahimci taurin kan Moh ya danne nasa sosai da sosai. "Ban san ka ba, ban taɓa ganinka ba ko a cikin baccina amma wannan kamannin ya shige ace kawai kama ce da Ubangiji yake samar da ita tsakanin bayinsa da suke doran duniya, akwai ɓoyayyen abu tsakanina da kai da rayuwarmu. Ban taɓa faɗawa kowa ba amma yau na gamsu zan faɗa maka wani abu daya shafe ni. Sunana Muhammad, na buɗe idanu a gidan marayu ban san yaushe na kasance a gidan marayun ba, amma a can granny da sanar mini cewa a wajan su na koyi zama, rarrafe, a gurinsu na fara zuwa makaranta. Sai dai bana ji domin tun ina ƙaramin nake cin zalin yara ƴan'uwana, bani da abokai bani da kowa a gidan. Granny kawai na sani me kula dani a makarantar na koyi harkar computer, su hacking da tracking da duk wani abu daya shafi Computer. Na rayuwa cikin damuwa da ƙuncin ma rashin ahali domin na gama sawa kaina bani da iyaye, wannan dalilin ya saka na fara zuwa club ina rage damuwa har na haɗu da abokai da suka sake koya mini shan abubuwan bugawar daga ciki har giya. Na aikata abubuwa da yawa, zina ce kawai bani da tabbacin ko na aikata ko ban aikata ba, kasan sharrin giya ai" Muhammad ya yi shiru zuciyarsa babu daɗi idanunsa na sauya sosai, ya kalli Moh sai yaga har lokacin kansa a ƙasa yake ya dunƙule hannunsa waje guda. A hankali ya ce "Ban san mene ya faru ba, watarana sojoji suka shigo makarantarmu a lokacin ma koyar da ɗalibai nake musamman ɓangaren crypto su data Analyst. Wani soja mai suna Aliyu ya ɗauke ni zuwa gidansa ya bani komai na rayuwa, ya kuma kore dukkan wani kaɗaici da nake ciki ya ajjiye ni a gidansa na computer ina yi masa aiki baya taɓa fushi dani amma duk ranar daya fahimci na fita da waje sai mun yi faɗa dashi, duk bana jin haushi har raina ya fara ɓaci saboda ni mutum ne da baya son ana tauye rayuwarsa, rayuwata tawa ce, halina nawa ne haka na yarda. Sai na fara zargin akwai wani abu game dani, mene dani? Mene abun i don't know, i really don't know kuma ban damu dana sani ba. Ganinka da ganin kamanninsa da muke ya saka na ji ina son fito da abin da yake ɓoye ka bani dama Please?" "Trust me" "I never trust anyone" Moh ya ce,a daƙile. "Ban baka labarina domin ka yarda dani ba, bana cutar da kowa kamar yadda bana bari a cutar dani. Ka bani dama trust me" cewar Muhammad. Moh yaƙi magana sai juyar da kansa gefe da ya yi kawai jikinsa na ɗan rawa. Muhammad ya ce "Don Allah?" "How?" In ji Moh. "Ka zama ni na zama kai" Sai Moh ya juyo gabaɗaya ya kalli Muhammad amma yaƙi cewa komai sai kallon Muhammad yake, is he alright? Anya yana da hankali ya san azaba da raɗaɗin da yake cikin wajan nan? Shine yake son cutar da rayuwarsa ta wannan hanyar mai hatsarin gaske. Muhammad ya ce "Zaka fita daga cikin Fcid, ka koma gidan da nake ciki da zama, ni kuma zan zauna a nan wajan a matsayin kai, ba wanda zai yi tunanin ba kai bane, Allah ba wanda zai gane" "Ni ɗan'daba ne, wanda mutane da al'ummar unguwarmu suka tsana na yi tambarin da babu wani daya isa ya yi kar ka so ka zama ni" "Just to help, we can help each others" Muhd ya ce a hankali Kafin Moh ya yi magana sai ganin Abbasa sukai yi ta bayyana a gabansu, Muhammad namiji amma sai daya tsorata ya nemi tashi a gigice kallon da ta yi masa ya saka ya dake kawai. Ya baza rigar jikinta hannunta riƙe da sanda idanunta rambaɗe da kwalli ta ce "Haƙiƙa Muhammad ya zo da magana mai kyau, wannan shine lokacin da kake jira Mai dawa. Baka da cikakken lokaci, kasafin ƙaddararsu ya fara ka tashi ka je ka sake tuna wasiyyar nan dake tattare da kai, idan kana son matarka da gaske ya zama wajibi a gare ka, ka bar gidan nan, idan kuma kuskurenka ya sake sawa ka rasa ɗaya yarinyar shikenan" MOH ya kalli Abbasa kafin ya ce "Kalli fuskarsa kalli tawa" Abbasa ta kalli fuskar Muhammad da yake wasai babu tabo balle sara balle kuma ɗinki saɓanin ta MOH. Ƙyaƙyacewa ta yi da dariya sosai hayaƙi na fita daga cikin bakinta kafin ta ɗaga sandan hannunta ta nuna Muhammad da shi, wasu surutai ta fara idanunta na firfitowa waje can kuma ta buga sandan sai wani abu ya haske kana hayaƙi ya fito ya sauka a fuskar Muhammad, ɗaya hannunta ta saka ta lashe tafin hannunta da dugun harshenta kana ta shafa hannunta a fuskar Muhammad. Cikin ƙaramin lokaci tabon fuskar Mutallab ya goge tas tare da komawa fuskar Muhammad ɗin. Da Muhammad da Mutallab suka shafa fuskarsu lokaci guda cike da al'ajabi tsohuwa Abbasa ita kuma ta tsuke fuska ta ce "Baka da lokaci, wa'adin da kake da shi na cika tabon fuskarka zai dawo, ga layar zanarka ka tashi ka sauya kayan jikin Muhammad kai ma ka bashi kayan jikinka" tana cewa haka ya buga sandan hannunta a jikin sarƙar da aka ɗaure Muhammad da ita sai ga sarƙar ta rabe biyu. Cikin sauri suka sauya kaya har lokacin Moh yana riƙe da wasiyyar Safiyyerh Abdulwahab wacce yake jinta kamar Safiyyerh domin daga hannun Deer ɗinsa ta fito yana girmamata. "Ga key ɗin motata nan, ga key gidan nan ga kuma wayata nan. Password na komai da yake gidan ka saka" sai ya yi shiru a hankali ya ce ka saka "AAMAJ zai buɗe hatta na jikin laptop, computer za kaga direction na gidan a cikin motar" Sai Moh ya jinjina kai bayan ya ɗauki wayar da komai ya saka cikin aljihu kana ya ɗauki facemask da hular ya saka. "Allah Ya taimaki Mai dawa sarki me jeji, jeka abinka lokaci ya fara" Muhammad ya ce "All the best" Moh ya rufe idanunsa, ita kuma Abbasa ta juyar da kan Muhammad da sauri Moh ya danna layar bayan ya matsa jikin bango nan take ya ɓace. Kafin Muhammad ya buɗe idanu itama Abbasa ta ɓace daga wajan. Fitarsu ke da wahala Dig Abdul-Johar Marafa ya shigo ya fara tambayar Muhammad da tunanin shine Moh kuma Scorpion ɗin da suka tsare har suke ƙoƙarin zartar da hukumcin kisa ko hauka a wajansa. Wata iska mai kama da iskar ƴanci Moh ya shaƙa bayan ya fita zuwa inda motar daya tabbatar ita ce ta Muhammad, ya buɗe idanunsa ya dinga kallon sararin samaniya yana shaƙar iska da kyau amma zuciyarsa kamar ta yi bindiga kansa na wata sarawa da ƙarfi. Yaushe rayuwarsa za ta yi daidai kamar ta sauran mutane? Waye zai fahimce shi ko yaya ne? Yaushe duniya da mutanen dake cikinta zasu wanzar da adalci a gare shi? Me ya sa mutane suka kasance masu tsananin son kansu suka zama azzalumai? Me ya sa kowa ya tsane shi ne? Idan yanzu ya kasance ɗan'daba me ya sa sanda yake lafiyaye aka yi masa tsana, tsanar ma har da iyayen da suka kawo shi duniya? Shin mene laifin ɗan'daba? Shi ba mutum bane? Aka san dalilin daya saka ya zama ɗan'daba ɗin? Ya yi shiru da sauri kuma ya buɗe motar ya shiga gwargwadon yadda zuciyarsa ke bugawa ta cikin ƙirjin gwargwadon yadda yake driving motar tare da sa mata giya yana shige sauran motoci. A haka ya isa gidan ya yi parking ya shiga, kamar yadda ya ce AAMaJ shine password haka ɗinne, ya tsaya gaban computer sai tunanin recorded ɗinsa da Kimiyya ya faɗo masa. Halin da zuciyarsa take ciki ya saka ya ji zaman gidan bai masa ba, yana buƙatar ganin Goje da Mangal yana buƙatar kayan caji zama jewa yake so bana gida ba, zaman dabarsu ya fi masa komai. Zuwan shi ke da wahala AA MAJ ya shigo, Moh bai motsa ba har Maj ya ƙarasu yana faɗin "Na tura maka abu ta mail ɗinka, check" Sai Moh ya yi shiru kawai, bai san Maj sosai ma amma ya ganshi sau biyu da sanda ya cakawa Aafiyyah wuƙa da sanda ya ɗauke Aafiyyah a gaban Maj ɗin. "Muhammad" Nan ma Moh bai motsa ba. "Check ur mail aiki ne na gaggawa ka ji?" "Uhm" kawai Mutallab ya ce. AA MAJ ya zauna saman kujera sai ya ɗakko wayarsa dake ringing number Aafiyyah ya gani kuma vedio call kamar ba zai ɗauka ba sai ya ɗaga, fuskar Aafiyyah ta bayyana tana zaune saman kujerar dake office ɗinta ta yi rolling mayafin abayar jikinta a hankali ta ce "Ummimi na buƙatar ganinka, idan ka je gida" "How are you?" Cewar Maj yana sake zuba mata idanu sosai. Sai ta yi cute smile tana ɗaga kafaɗa ta ce. "Good" Maj ya jinjina kai ya ce "Wife, say hi to Muhammad" ya ce yana juya wayarsa zuwa inda Mutallab yake tsaye ya juya baya. Moh sarai ya ɗauki muryar Aafiyyah a cikin kunnuwansa kenan Maj shine mijin Aafiyyah? Da gaske daman tana da aure? Ya cije bakinsa da ƙarfi yaja numfashi yana jin to mene damuwarsa bama haka ne a gabansa ba a yanzu ɗin. "Muhammad" Aliyu ya kira Mutallab da tunanin shine Muhammad. A hankali Moh ya juyo yana kallon screen ɗin wayar Maj, idanunsa ya sauka a fuskar Aafiyyah, itama ɗin shi take kallo can ta ce "How are you?" Ɗauke kai ya yi yana barin wajan tare da nufar wani ɗaki daya gani a buɗe. * Su wajan bakwai ne a cikin gidan gonar bayan kowa ya fito daga cikin mota hankali a tashe Eng Ali wali ya ce "Wallahi akwai matsala idan Scorpion ya buɗe bakinsa a kan mu, kafin Fcid su saka shi yin magana mu yi ƙoƙarin fito da shi a ɓoye kota halin yaya ne" ya faɗa yana barin jikin motarsa tare da saɓa babbar rigar jikinsa zuwa gefe. Sharfaɗi ya ce "Ni mene haɗina da wani Scorpion da har kuka kira ni zuwa meeting ɗin nan naku?" "Kana da haɗi kowa, domin kasan mu, muma mun sanka. Yana da kyau mu nemi sulhu da shi mu ji me muka yi masa da yake ƙoƙarin raba mu da rayuwarmu a dole? Hankalina a tashe yake nine next plan ɗinsa a wanda zai kashe, wallahi ban shirya mutuwa a yanzu ba, ina da buri da muradan da nake ƙoƙarin cimmawa" Hon Maɗaita dake jingine da jikin motarsa ya yi murmushi, kallon Eng Ali wali kawai yake domin shi ba Scorpion ne a gabansa ba, idan ya tuna maganar da Alhaji Wada ya zo masa da ita akan cewa wai Ali wali ya yi tarayya da matarsa Laylerh sai ya ji ya rasa sukuni ta inda zai fara ɗaukan mataki kawai yake tunani, koda tsohuwa Abbasa bata ce ya kwanta da Sabrina Noor ba dole ya yi amfani da ita wajan ɗanɗanawa Ali wali maɗaci a baki. "Hon Maɗaita ana ta magana baka ce komai ba" "Me zai ce daman? Tunda ya san ba shi za'a kashe yanzu? Wallahi dole mu fito da Scorpion dole ne" Sai Hon Maɗatai ya kalli Ali wali ya ce "Ali wali kenan." "Ban fahimci Ali wali kenan ba? Kana nufin zan zuba idanu na mutu ne? Ai sai dai a yi mutuwar kasko" Maɗaita ya jinjina kai ya ce "Ba za'ayi hakan ba, za'a fito da Scorpion ta ɓoyayyiyar hanya amma ka bari mu kammala interview ɗin da BBC za su yi wa ƴan ta karkaku ko? Bayan wannan sai mu zauna a yi magana" Sharfaɗi ya ce "BBC ko? Ai kamar komai ne a Abuja i will be there nima" Suka amince da wannan batun, Hon Maɗatai sai kallon Eng Ali wali yake yi yana murmushi a ransa da wannan tunani kowa ya shiga motarsa suka bar gidan gonar Sharfaɗi. * A ɓangaren Aafiyyah ta samu appointment na ganawa da Dr Abraham Denial David ta dalilin I. Qasim wanda bata san yadda aka yi ya nema mata appointment ɗin ba. I. Qasim ya samu Dr Hamza a office kasancewar Dr Hamza abokin Dr Hash ne ya nemi alfarma daya sauya masa alluran wajan Dr Hash da ya kewa Aafiyyah da wanda shi kuma yake yi mata. Tunda Dr Hamza ya san komai dangane da allurar da Dr Hash ya kewa Aafiyyah. Bayan sun gama magana I. Qasim ya nufi ɓangaren da jariran suke ciki a hankali ya zubawa ɗaya idanu daya ɗan fara ƙwari kamammin da yake hangowa a fuskar macen har tsoro suke bashi, ya dinga kallon jaririyar kafin ya saka hannu ya ɗauke ta a hankali ya rungometa a ƙirjinsa wani hawaye na cika idanunsa ya jima kafin ya ajjiyeta ya ɗauki namijin Allahu Akbar kawai kimiyya ya ce sanda ya kalli kamannin namijin ya jima kana ya ajjiye shi ya fita zuwa special room ɗin da mahaifiyar tasu take ciki ya ƙarasa har yanzu bata motsi muryarsa a raunace ya ce. "Motsin ki cikin lafiya da dawowar ki cikin hayyacinki shi kawai nake buƙata, babu lokaci na kasa haƙuri zuwa sadaki da inda ya dace. Get well soon dear Allah Ya ba ki lafiya" ya ce hawaye na bin fuskarsa sai ya ji ya riƙe hannunsa da sauri ya kalle ta bata motsi sai hawaye da yake bin idanunta alama karaya. * Suna tsaye adabar tasu su kaga ya faɗo cikin sauri Mangal ya ce "Kutumar uba salatin arna, sai da kai mai gida, kai ne da gida kai ne da dawa dar yi shirunka na waje na" Goge ya bankawa Mangal harara ya ce "Ankar ɗanwahala jemamme" "Dar, a huce" cewar Mangal. Goje ya kalli Moh yana karkace bakinsa kafin ya ce "Shirwa kake baka jewar banza, na san daman dole zaka fito da iznin mai duka lillahi rabbil samawati. Dar ne wannan" "Goje" Moh ya kira sunan shi yana gyara saitwarsa kafin ya ɗago kai ya kalle shi ya sake cewa "Goje" "A lafiya mai dawa" "Ina buƙatar kayan caji" Da sauri Mangal ya ce "Sha fara kaga aljan kake so,ko ƙwayar doki ko mai zubin lemon fenta kake buƙata" "Can ji babanka Mangal zan maka tsago ƴan uwa a wuyanka. Sha fara ka ci jahilin duka yake so" "Yawane wannan Oga Goje ka faɗa mana kai kodayaushe ciki ne" Sai Goje ya juya ya amshi kayan hannun Mangal ya miƙawa Moh ƙwaya guda biyu cikin sauri ya amsa ya dannata a ƙasan harshensa a gaggauce kamar mayunwaci. "Ya aka yi kamar hannun waɗancan cinnaku? Damar na ce kar ka faɗa da yarinyar nan ta yi zubin kimini amma ka jirga da zancenta, su masu ɗankwali ba'a taɓa sirri da su gashi yanzu ta janyo ruwa ƴar wahala kawai sam ba ta yi ba" "Oga Goje da ka yi makaranta ba ƙaramin mai basira za'ayi ba, Allah Ya tarfawa garinsa nono" "Goje" "Mai dawa" "Ina matar dana ɗakko a gidan Ali wali ranar da zan bawa yarinyar can labari, ina take tana ina?" Moh ya fara jikinsa na kakkarwa da ɓari domin ƙwayar ta fara aiki, duk suka ja baya ya faki idanunsa ya fisgi wuƙa a ƙugun Mangal ya ce "Tana ina?" Cikin sauri Goje ya ce "Bamu ganka ba" kallon Goje kawai Mai dawa ya ke yi kafin ya zallaƙo harshe ya lashe gefen bakinsa sai ya juya dif dif dif ya yi kwana. * Kamar yadda Bbc ta saka musu rana bayan an fafata a interview ɗin tsakanin Eng Ali wali, Hon Maɗatai, Dr Abraham Denial David. Bayan sun fifo Dr Abraham Denial David ya ja mutanensa a lokacin mamaki ya gama cika zuciyar Hon Maɗatai ganin yadda Dr Abraham ya yi masa tawaye daman ƙarya yake yi da yake cewa ya sallama masa kujerar? Eng Ali wali ma ya kwashe jama'arsa suka bar wajan ya rage sai Hon Maɗatai. Ƴan jarida sun cika a wajan da gidan rediyo tv da ƴan media suna sun tattaunawa da Hon Maɗatai akan mene gaskiyar alaƙar shi da Dr Abraham Denial David? Ya aka yi aka haihuwa a ragaya? Hon Maɗaita ya nufi motarsa zai shiga. Jami'an tsaro ne ta ko'ina cikin kayan kaki ma bambanta, duk da cewa yammacin ranar lahadi ne a watan Fabrairu bai hana ta gane fuskarsa ba. Cikin tashin hankali jikinta na rawa da kyarma ta nufe shi tare da ƙoƙarin cakomo wuyan babbar rigarsa tana furta cewa "Shi ne, wallahi shi ne, daman na ce zan gano shi" a gigice mutumin dake ƙoƙarin shiga motarsa da aka buɗe masa ya yi baya yana mai ƙarewa matar kallo sosai sai dai ya kasa gano ko wace ita? Daga ina me kuma take buƙata. "Wace ita?" Ya furta yana tambayar zuciyarsa tare da kallon gefe. "Wallahi shi ne, mugu azzalumi sai ka yi kuka, ka wulaƙanta " Jin furucinta ya saka ƴan'jarida dawowa kan ta, suka fara tambayar "Kin san shine? Mene haɗinki da shi?" Kafin ta yi magana wani ya ce "Arrest her, ku kamata" A hankali ya jingina da jikin motar can ya numfasa yana kallon yaronsa ya ce "Wace ce? Na santa ne? To me ya sa take abu kamar ta sanni?" "Sir, da gaske ta sanka bana jin ko mutuwa ta yi ta dawo zata manta fuskarka, kuma zamanta a raye yana nufin abubuwan da yawa dole a yi wa tufkar hanci, kar a bari ƴan'jarida su samu ganawa da ita, even your securites, wannan matsalar kai da kai ce kuma zata shafi kimarka" cike da mamaki ya yi ta kallon yaron nasa na tsayin sacanni da ƙyar ya cije leɓe ya ce "To ina na santa? Me ya sa zata zama damuwata?" "Sir ita ce wacce ka saka aka kawo maka ita, wacce ka yi wa fyaɗe a lokacin.....," "Ya isa!" Ya ce yana jin jiri na neman ɗauke shi, ya dubi tarin jama'ar da suke wajan can ya yi murmushi yana ɗauke fuska sai kuma ya ƙurawa yaron idanu ya juya ya kalli matar ya gyatsine fuska ya ce "kuma ta kasance a raye ya haka? To a yi hanzarin toshe wannan ɓarnar ya zama kamar ba a yi ba" "Amma me ya kamata a yi mata?" "A yi mata allurar hauka, wacce ake yi duk shekara da wata wata kana a kaita gidan yari, life in prison har ta mutu. Bayan haukan zata mance komai, su ƴanƴan talakawa wama ya damu da su mutu ko su yi rai bata da wani mai tsaya mata kai mutuwa ma za ta yi" yana faɗin hakan ya shige mota. Tana takure a jikin ƙofar ɗakin da aka ajjiyeta idanunta ƙur a kan photonsa zuciyarta sai zafi take mata wani abu ya tsaya mata. Da sauri ta juya jin an buɗe ƙofa wani mutum ne sanye da farar riga ya rufe fuskarsa hannunsa riƙe da ƙaton sirinji iya ruwan allurar da ya yi ja abin tsoro ne, ta fara ja da baya amma a haka ya fincikota tare da yin cilli da ita,ta faɗi saman carpet bai tsaya jiran komai ba ya caka mata allurar a ƙashin bayanta wajan spinal cord ihu ta fara da birgima idanunta ya shiga ƙaƙƙafewa jikinta na sandarewa ta dinga buga kanta da jikin bango tana buge-buge a hankali jini ya fara fitowa ta cikin hanci da bakinta tabbacin allurar ta amshe ta za kuma ta yi aikin da ake buƙata a jiki da ƙwaƙwalwarta. Bayan ya yi mata allurar ya fito daga ɗakin ya dubi Hon Maɗatai ya ce "Done sir, sai a samu mai kai ta gidan yarin......," kafin ya ƙarasa maganar daya cikin redia sun ji muryar wata budurwa na faɗar cewa Hon Maɗatai ya yi mata ciki idan ƙarya take yi a tambaye shi. Sai Hon Maɗatai ya ƙyaƙyace da dariya kafin ya ce "Har abada babu mai yarda yarinya duk da ban san wacece ke ba amma zan yi maganinki" ya juya ga yaronsa ya ce "A shirya report ɗin ƙarya cewa bana haihuwa bani da cikakkiyar lafiya" Daga can gefe suka ji an ce. "Idan baka haihuwa Safiyyerh kuma ƴar wacace don banbaka?" Da sauri ya juya sai ya arba da Moh zaune saman kujera hannunsa riƙe da wuƙa. Hon Maɗaita ya ce "Wace Safiyyerh? Wacce Safiyyerh?" "Safiyyerh matata, wacce ka saka aka kashe saboda ka gano cewa ƴarka ce....... 💥Chapter 8: The hospital, Who is he "Mai dawa" Hon Maɗatai ya kira sunan Moh yana tsare shi da idanu. Moh na girgiza ƙafa ya ce "Hon Boɗejo Maɗatai" ya ce muryarsa a kumbure cike da kayan maye. "A haihuwa kasan zan iya haifar wanda ya fika, a shekaru zan iya sa'a da banbanka, saboda baka da tarbiyya kazo har cikin gidana without my knowledge, ka fara jifana da maganar banza da wofi? Saboda kasha tana faɗa maka gaskiya da ƙarya da ƙarya, banda haka har zaka kalle ni ka ce wai na kashe wata?" "Babana ba azzalumi bane irinka ɗan wahala, bana duguwar magana da ɗan asara irinka Boɗejo, ka kashe mini mata na zo wajanka domin na ɗauki fansar abin da ka yi mata, idan kaga na barka a raye ni ba ɗan babata bane, kuma zina aka yi aka haife ni, ƙarshen wani ɗan'daba mutuwa dai, dar, na shirya mata" Moh ya ce yana zaro harshe waje sai kuma ya yi saurin damƙe kunamar dake hannunsa saboda zuciyarsa a dab take, kaɗan ya rage ya sokawa Maɗatai wuƙar hannunsa. Hon Maɗatai ya kalli Moh, ya ce "Wani zance mai kama da tatsuniya, ka taɓa ganin inda uba ya kashe ƴar cikinsa bayan shi ya haife ta? Duk duniya da mutanen da suke zagaye dani sun san bana haihuwa, matata ko ɓatan wata bata taɓa yi ba. Bayan ga haka bani da cikakkiyar lafiya irin ta ɗa namiji da zan iya mu'amala da mace har ta haihu" Hon Maɗatai ya bawa Moh amsa yana zagaye cikin parlourn na shi idanunsa kamar ya zazzago amma a haka ya dake gudun kar a gano abin da yake ɓoyewa. Moh ma kallon Hon Maɗatai yake, yana girgiza ƙafarsa haf zuwa lokacin wuƙa ce a hannunsa kana ganin yanayinsa ka san cewa baya cikin hayyacinsa, sai daya samu caji ya bugu sosai yadda zai iya aikata duk abin da ya su, kuma zuciya ta raya masa kafin ya tunkaro wajan hon Maɗatai ɗin. Ya jinjina kai yana shafa wuƙar da yatsarsa guda ɗaya yace. "Kai sai ka sumar da mutum ka ke iya cin shi da yaƙi ko galaba akan shi, ni kuma ya yin faɗa da mutum ko magana dashi,sai na fara farkar dashi" ya cije bakinsa ya miƙe tsaye yana zagaye hon Maɗatai idanunsa jajur. "Hon Maɗatai zan ce? Ko Alhaji Boɗejo Maɗatai? Ko na ce Distinguish Boɗejo Maɗatai? Wanne zan kira ka ka san cewa na haifo cikin babata? Ka san cewa na yi maka farin sanin da baka isa ka raina mini hankali ba, ko kana tunanin zan yi aiki da wanda ban sani ba ne?" "Ka iya bakinka, da ɗan majalissar tarayya kake magana kuma me neman zarce wa, zan iya sakawa ka yi rayuwa ta har abada a ɗaure wallahi" Hon Maɗatai ya ce yana ɗaukan wayar hannunsa idanunsa akan Moh, zuciyarsa na girgiza da kanta mamaki yake yi ina yankan fuskarsa? Ba shi ne aka ce Scorpion ba? Idan shi ne ya aka yi ya fito? Ina yankan fuskarsa? Daman ya san cewa shi ya kewa aiki tun shekarun baya? Ko yanzu ne Jaa'afar ya faɗa masa? Kai baya jin cewa Fcid za su saki Scorpion, yanzu kuma yana tsoron yin magana reshe ya juye zuwa ga mujiya, bai kama ɓarawo ba, shi ɓarawon ya kama shi. Sai ya tattara nutsuwarsa waje guda ya ce. "Get out of my house, ban sanka ba, ban kuma san matarka, balle na kashe maka ita, kaga na yi kama da mugu ne? Ko azzalumi? Idan Boɗejo da kake magana ne ka je ka binciki tarihinsa a wajan talakawan gari ka ji, haka ma idan Maɗatai ɗinne shima ka je ka yi bincike ka ji?" "Ka kashe mini mata" cewar Moh muryarsa bata fita sosai, ji yake kamar ya caka masa wuƙa a ƙahon zuciya, amma idan ya tuna kisan wulaƙancin da aka yi wa Safiyyerh sai ya ji duk abin da zai wa Maɗatai bai huce ba, dole ya fara gana masa azaba a hankali, ya fita hayyacinsa har ya kai lokacin da zai bayyana gaskiya da kansa. Sai ya sake cewa "Ka kashe mini mata, ka kashe ƴarka, me ta yi maka? Akan wanne dalili" idanunsa na sake rinewa jikinsa ya fara rawa sosai da alama yanzu ne ƙwayar daya afa ta fara masa aiki ya ɗaga rinannun idanunsa ya kalli Hon Maɗatai dasu kafin ya lashe laɓɓansa yana fesar da huci ta cikin bakinsa wani irin abu na tsartuwa a cikin bakin, wani irin kallo yake jefawa Hon Maɗatai yaƙi magana, kamar mai tunanin wani abu ko lissafin abin da zai faɗawa Maɗatai ɗin, a hankali ya sunkuyar da kansa ƙasa maganar Deer yake tunawa da take cewa “Soyayyar nan da kake mini na gamsu, soyayyar nan da kake mini ka tabbatar ta nuna kanta, wajan ɗaukar mini fansa. Kar ka yi kuka don Allah mijina, kar ka yi kuka ka toshe kunnenka, i love you” “Ka tabbatar ka rama mini, kai gwarzo ne, kar ka yi kuka” Ya sake kallon Hon Maɗatai kafin ya ce "Ba'a ja in-ja da ni, ni a shirye nake da mutuwa da tsohuwarka, kai ne baƙwanta banƙi mu kashe juna ba" "Ai baka isa ka kashe ni ba, idan ma na kashe matarka wane ya ce ta san sirrin da nake rufewa jama'a, wane ya ce ta shigar mini sashi mafi amfani a rayuwata? Ta gano mini sirrin da babu wani ɗan'adam a duniya daya taɓa gani, kana ganin ni Hon Maɗatai zan zuba idanu asirina ya tuno? You're mistaken, na kashe matarka dai ba dai ƴata ba, domin bani da jini a duniya. Kuma da kake magana kisan shekaru uku da suka shige kai ka isa ka ɗauki mataki a kai na ne? Where is the evidence? Where is the proof? Eh? Ni ba'a sa'anka bane. Matarka dai bata raye a duniya, asirina ba zai taɓa bayyana ba kana iya faɗar adadin kuɗin da kake buƙata na ran matarka shikenan" "Boɗejo kenan" ya ce a daƙile. "Faɗi amount na ran matarka" Wuƙar ya karta a saman glasses yana jinjina kai muryarsa ta cikakkun ƴan'daba ya ce "Ko acikin ƴan'daba ni ba sakarai bane. Zan faɗa maka abin da baka sani ba, baka kashe Safiyyerh saboda taga waɗannan ƴan'matan ba, ba wannan dalilin ya saka ka kashe mini mata ba" "Idan ganin sirrina na ƴan'matan bai isa ya zama dalilin mutuwarta ba, mene hujjar da zai saka na kashe ta?" Moh ya yi feɗowa mai sauti idanunsa jajur kamar yadda suke yi a lokacin daya gama cakewa ya ce "Kana tsoron abin da ka aikatawa yaran wasu a aikatawa naka yaran saboda ba zaka jure ba, kana tsoron haƙƙin wasu yaran ya sauka akan yaranka, wannan dalilin ya saka baka son haihuwa baka taɓa sha'awar ta ba ko da wasa. Idan ganin ƴan'matan ne ai na riga Safiyyerh ganin su, me ya sa baka kashe ni ba? Duk da cewa ban san me kake yi musu ba. Ban san ya aka yi ka haifi Safiyyerh ba, amma tun ranar da naga Safiyyerh kuma naga mahafinta Professor Abdulwahab na san cewa kawai ya yi adopted ɗinta saboda shi baya haihuwa. Ka kashe Safiyyerh a lokacin daka fahimci ita jininka ce, ka kashe ta saboda kasancewa ita ce asalin Safiyyerh Boɗejo Maɗatai, ka kashe ta ne saboda ka gama faɗawa duniya baka da zuri'a kuma baka da lafiya shiyasa kake sallama dukiyoyinka ga mutane da almajirai" "Ina ka san wannan maganar? Jaa'afar ne ya faɗa maka?" "Kai ka kashe Safiyyerh?" Sai Maɗatai ya juya yaga daga shi sai Moh da mutumin da ya yi wa matar nan allura, ya yi murmushi cike da izza da taƙama sai da ya yi dariya mai isar shi kafin ya ce "Ni na kashe Safiyyerh, na kashe tabbas ko na saka an kashe ta" Sai ya yi baya kaɗan yana buɗe hannunsa ya ce "Ni ban san matarka bace ba ma. Na kashe ta saboda na lura zata iya fallasa asirin da nake ɓoyewa, wannan dalilin ya saka ni sawa a kashe ta, banda haka bani da wani business da ita wanda zai saka na rabata da duniya" Ya sake yin shiru can ya ce "Bana bawa kowa haƙuri, amma na lura kamar kana son ta sosai. I am sorry for the lost, may her soul rest in peace a aljanna cikin kabarinta" Ya sake cewa "Sorry for the lost" Kan Moh a ƙasa idanunsa ya yi jajur kamar garwashi, ƙoƙarin samawa kan shi nutsuwa yake yi, amma ya kasa wani irin juyawa kansa yake yi kamar zai tarwatse ji yake ina ma zai mutu a yanzu shima? Gabaɗaya ya gaji da duniyar tunda ya san ba zai taɓa samun farinciki a rayuwa ba, he believed in destiny, amma wannan ƙaddarar tana neman fin ƙarfinsa ta kowanne gefe da sashe bashi da wani amfani a wannan duniyar. Kunamar hannunsa tun tana motsi har ta mutu ya buɗe jajayen idanunta da suke rufe gently ya ɗago ya kalli Hon Maɗatai da mayatattun idanun nasa, wanda ya saka Maɗatai jin faɗuwar gaba, ya tsorata da yanayin Moh, kallon da yake masa wani irin kallo ne mai kama da ka raina mini hankali da wayo, baka san kuma waye ni ba. "Sai godiya..." Ya ce yana shagiɗar da bakinsa zuwa gefe yana sake yin feɗowa idanunsa kamar zai fito. "Ka kashe Safiyyerh saboda ka gano cewa ƴarka ce, ba wai don taga abin da kake aikatawa ba, kalas" "Why should i killed my daughter?" "Kafi ɗan dako sanin tasha, kana da dalilin kashe ta, bayan wannan dalilin?" "Wanne dalilin kenan Mai dawa?" "A ranar da zan faɗa maka dalilin a ranar zaka yi sallama da duniya ɗan tsinanniya. A ranar kuma za ka yi ladama mafi muni wacce baka taɓa yi ba, zaka wulaƙanta Boɗejo kafin ranar duk abin da kake taƙama da shi zai ƙare. Jaa'afar bai faɗa mini komai ba, domin ban san ina yake ba, ban kuma damu dana sani ba. Boɗejo ni na siya maka farinjinin da kake da shi a yanzu, ni na toshe bakin jama'a akan ka, ni na tabbatar da kujerarka da abin da zaka saka mini kenan? By killed my wife? Matata kisa mafi muni kai azzalumi ne, zan fara rayuwa a yanzu saboda na gana maka azabar da Safiyyerh ta ji, nagartacciyyar yarinya mai farinjinin jama'a ita ka kashe saboda dalilinka mara tushe? Ban ɗauka mace bana da amfani a rayuwata ba, bayan mahaifiyata ba, ban ɗauki soyayya da amfani ba, domin na sawa raina soyayya wahala ce. A lokacin da na gama sanyawa zuciyata ƙaunar mace na gama jin na shirya rayuwa da matata, domin ta yi mini halaccin da babu wata mace da zata iya yi wa mijinta, a lokacin da na ji cewa nima mutum ne kamar kowa, a lokacin da farinciki ya fara sama a zuciya da fuskata a lokacin kai kuma ka rabani da ita? Me ya sa?" Hon Boɗejo ya yi shiru kawai. Moh ya ce "Idan baka son ƴarka ni ina son ta, bata taɓa sawa ranta tana da wani mahaifi a duniya bayan Professor ba, why why Boɗejo?" "She is nothing to be, she can't be my daughter ka ji?" Cewar Boɗejo. Sai ya sake cewa "Mai dawa, da za ka yi haƙuri da batun nan domin ba zaka taɓa cin riba ba, baka da hujjar cewa ni na kashe ta duk da cewa ni ne, amma hukuma ba zata yarda ba, domin su ba banzaye ne irinka ba. Mu mun saba dake doka a kodayaushe kuma mu zauna lafiya, mun saba zuwa mu ɗakko mutum daga ƙauye mu sauya shi da yaranmu da suke cikin gidan yari, nothing will happen, ba abin da shari'a za ta iya akan mu, domin mu ne ita. Idan kana da mulki a ƙasar nan to kafi ƙarfin wulaƙanci, ita kan ta dokar sai yadda ka yi da ita, baka da shaidar cewa ita yarinyar ƴata ce, baka da shaidar mutuwarta balle shaidar cewa ni na saka a kashe ta" ya saki murmushi ya ce "This is the last time da zaka zo mini da wannan maganar, matar nan da kaga gani yanzu ka ɗauka baka ka ga komai ba, domin ina da iko da ita, na fika kusanci da ita, again matar da ta yi magana a gidan rediyo na san cewa sharrin siyasa ne da adawa ta siyasa kuma i will handle it,now leave my house" Wuƙar dake hannun Moh wacce ke sheƙi ya miƙar da ita ya nufi kan Hon Maɗatai, kafin ya ƙarasa P.a ɗin nasa ya nufi kan Moh, a sukwane Moh ya juya tare da durƙosawa ya ɗaga P.a ɗin sama ya buga shi da ƙasa, ya damƙi hannunsa ya ɓalla shi, ji kake wani ƙass ƙass ƙarar karyewar hannun. P.a ɗin ya kurma ihu da kururuwa ya sake neman miƙewa zai tashi zaune da niyyar kare Hon Maɗatai, cikin sauri Moh ya saka wuƙar ya datse yatsu huɗu dake hannun P.a tsananin azaba ya saka ya sako fitsari a wajan jini ya fara malala. Hon Maɗatai ya juya zai shige wani bedroom yana ƙoƙarin ɗakko bindigarsa wacce yake amfani da ita a gida, gashi securities ɗinsa duk sun yi nisa. Kafin ya shige bedroom ɗin,Moh ya saukarwa Hon Maɗatai askira a ƙeya, Maɗatai ya yi saurin dafe ƙeyarsa. Moh sai zazzaro idanu yake yana wani irin huci da fesar da numfashi gabaɗaya ya juye kamar bashi ba. Maɗatai ya juyo ya kalli Moh ya ce "har gidana kazo kake mini dabanci?" "Shi Ɗan'daba baya ɗaukan raini da ƙasƙanci baya ɗaukan cin amana, haka bama cin amana. Idan har ni mijin matata Safiyyerh ne, to ka ɗan ka gani wannan sallama ce kawai" "Me kake nufi?" Cewar Boɗejo. Sai yaga Moh ya saka tsinin harshe ya lashe jinin dake jinin wuƙar kana ya fesawa Maɗatai a fuska kana ya saka ƙafa ya danne Maɗatai, “S” ya zana masa a ƙirjinsa kana ya tsuke fuska. "Sai godiya" ya ce yana dira ta window ɗin dake bayan gidan, daman ta nan ya shigo. Hon Maɗatai ihu ne kawai bai yi shima gudun raini, ya dinga sauke ajjiyar zuciya zufa na sauka a jikinsa ya buɗe ya kalli yatsun P.a ɗinsa da aka cire sai ya ji dole ya saka a kashe Moh ko kuma a mayar da shi zuwa gidan yarin har ya mutu a can. Yana daga kwance ya ja jikinsa zuwa bedroom ɗin wayarsa ya ɗauka ya kira dr ɗinsa ya ce yana nemansa cikin gaggawa. Yana nan zaune dr ɗin ya zo, ya yi masa treatment shi da p.a. ɗinsa bayan ya kammala ya ce. "Distinguish, akwai buƙatar ka wuta sosai bp ɗinka ya hau sosai" Hon Maɗatai ya yi shiru, sai kuma ya sauke ajjiyar zuciya ya ce "Dr" "Distinguish!" "Abin da ka gani, ka yi kamar baka gani ba, ina nufin ya tsaya da cikin gidan nan ka ji ko?" "In sha Allah" "You can leave" Miƙewa dr ya yi alamar tafiya yana sake godiya ga Hon Maɗatai domin shine ya sama masa offer ta aikin, duk da level ɗinsa na matakin aikin bai kai ba. Bayan tafiyar Dr. Sai Hon Maɗatai ya kalli P.a ya ce "P.A ka shirya mini tafiya zuwa ƙasar waje na ɗan wuta kafin lokacin ya ƙaratu, ka yi hakan da nufin zan fita a duba lafiyata ne ko da zancen barin ƙasar tawa ya fita ka ji ko?" P.a Sadiq ya ce "Sir ina ganin daka haƙura da fitar ko dan tsoron abin da zai je ya dawo, kuma kaga jebi za'a rufe yin kamfel gabaɗaya elections bai fi sati biyu ba ya rage" "Sadiq!" Hon ya kira sunan P.a ɗin a hanzarce yana mai nuna masa hanya. "Tuba nake Distinguish, za'a tsara visa ta rashin lafiya zuwa gobe" "Za ka iya tafiya, ka kula da kan ka" "Godiya nake Distinguish" Bayan fitar P.a SADIQ, hon Maɗatai ya yi shiru yana tunani, ya san cewa ko a shekarun baya ya buƙaci Jaa'afar kada ya faɗawa yaron da yake masa taimako fuskarsa ko sunansa, sau ɗaya ya taɓa tsayawa ya ji sunansa kuma sai ɗaya ya gansa ranar da ya biyo Jaa'afar amsar kuɗi, ya ɗan bibiye shi har yaga sanda ya shiga Fgc shiyasa ma yake tambayata mene alaƙarsa da Fgc ɗin?. Kamat yadda Mai dawa ya faɗa ne, bai damu don taga ƴan'matan dake gidansa ba sam, domin she can't do anything, ko mutane ta faɗawa babu mai yarda duba da yadda ƙofar gidansa kullum cike yake da alamjirai da tsofaffi yana raba musu kuɗi da abinci. A sanda ƙaddara ta saka ya yi tarayya da wacce ta kasance uwar Safiyyerh maybe a lokacin ta samu cikin Safiyyerh ba tare daya sani ba, domin bai kawo ma zata samu cikin ba, a sanda Jaa'afar yake yi masa maganar DNA test bai ɗauki abin very serious ba, ko daya matsa ba sai kawai ya amshi result ya ajjiye inda ba zai sake gani ba. Ranar da hankalinsa ya tashi a ranar da idanunsa ya gane masa Safiyyerh ta cikin CCTV camera, ya san cewa da idanunsa kawai ƙofar ke buɗewa sai gashi ƙofar ta buɗe da idanun yarinyar da bai ba sani ba, sai ya fara tunanin maganar Jaa'afar tabbas idan babu rami babu abin da zai kawo dalilin buɗewar ƙofar da idanun Safiyyerh, ya ji a ransa dole akwai ƙwayar halittarsa a jikin Safiyyerh. A lokacin ya miƙe da sauri ya samu kansa da duba result ɗin. “Safiyyerh Boɗejo” shi ya gani raɗau jikin test ɗin dake nuna positive alamar ƴarsa ce, ba don ta kasance ƴarsa bace kaɗai ya kashe ta, hanyar da aka samar da ita ne, ya sake ƙarfafa masa qwwia wajan kashe ta, domin a lokacin ya gama yi wa Ali wali tawaye ya shirya zama ɗan majalisa don haka yake toshe dukkan wata ɓaraka da zata iya hana shi hawa mulkin da Ali wali ke kwaɗaita masa, yasan idan Safiyyerh ta kasance a raye tabbas akwai ranar da gaskiya za ta yi halinta, baya son asan cewa ita ƴarsa ce balle a san cewa ita ƴar zina ce, ba aure ne ya samar da haihuwar ta ba kamar kowanne yaro. Wayarsa ya sake ɗakko wa ya kira wata number ana ɗagawa ya ce. "Sp Ghali Gaddafi meet me at my house right now" ya ce yana kashe kiran, da kashe wayar gabaɗaya. * Moh na kwance saman tagar kangon da suke ciki ƙafarsa ɗaya kan ɗaya, sigari yake zuƙa a hankali yana bawa samaniya ajjiyar hayaƙinta idanunsa rufe, domin wannan shine last abin da yake iya yi ya samu nutsuwa, duk da cewa babu sukuni a ransa nutsuwar ma ba samun ta yake ba, duniya yake jin tana yi masa zafi da girma idan yaga wani ya yi murmushi ko dariya abin har mamaki yake bashi, domin shi a yanzu bashi da wani dalili na yin murmushi balle dariya, ba zai iya yafewa kansa ba idan hakan ya faru ko da kuskure ne, ko murmushi ya yi sai dai ya yi da niyyar ƙeta ko idan ya tabbatar ya shuka abin tsiya. Kara wajan goma ya zuƙe a cikinsa ya sake ciro wata sai Goje ya ce. "Sai godiya, a dinga sararawa ciki ko dan lafiyarmu" Moh ya yi shiru. "Sarki" Goje ya sake kiran Moh. "Sarki!" "Ehemm" Moh ya ɗan yi gyaran murya kaɗan tare da buɗe idanunsa ya kalli sama iska na ɗan busa shi kaɗan. "Sarki wannan abubuwan da kake yi babu abin da zai amfane ka da shi sai cutarwa, madadin ɗaukan fansa sai ka kassara kan ka a banza. Na san akwai ciwo a zuciya saboda an zalunce ka, ina yin kamar bai san komai bane akan idanun mutane na san wacece Safiyyerh domin na taɓa mu'amala da ita dalilinka ba dai sosai ba, ina da yaƙinin bata jin daɗin abin da kake yi, dole ka samawa kan ka nutsuwa ba zaka iya komai ba a haka" Goje shi kaɗai yake maganarsa Moh bai tanka ba, idanunsa sama kawai yake kallo yana busa hayaƙi. Bayan ya shanye sai ya ciro jar ƙwaya ya cilla a cikin bakinsa, ya ɗauki mintina sai ya ji sam ba ta yi masa aiki, ya sake watsa biyu a baki cikin sauri Goje ya ce "Wai kai wacce irin zuciya ce da kai? Ka san adadin ƙwayar da kake sha? Haukata kan ka kake son yi ne ko yaya?" Sai ya diro daga saman tagar yana muzurai yaƙi kallon Goge gabaɗaya ya nufi hanyar barin kangon. "Ina zaka yanzu? Ka baro hannun kwalawan can da ƙyar shine zaka sake fita? Kai baka damu da rayuwarka ba ko? Me ya sa kake haka" nan ma Moh bai magana ba ya sake ɗaukan hanya zai fita Goje ya tare ya ce "Ba inda zaka malam" "Goje" ya ji ya kira sunan Goje saman kan shi jikinsa na rawa. "Sai dai duk abin da za ka yi mini ka yi fa,amma babu inda za ka" "Goje" "Mai dawa" "Zan saka maka sakata a baki, zan maka maka gulando" "Yi, ban hana ba" Sai Moh ya ɗago kan shi ya kalli Goje, sai kuma ya girgiza kai kawai tare da komawa ciki ya kwanta a ƙasa. Ajjiyar zuciya Goje ya sauke yana rufo ɗakin ya nemi can saman dutse ya zauna kan shi a ƙasa yana tunani. * Aafiyyah na zaune a office ɗinta tana danna laptop a hankali hannunta ɗaya dafe da haɓarta a hankali ta yi baya tana rungume hannayenta a ƙirji. Knocking ƙofar office ɗin aka fara yi, tana ji ta yi shiru can a hankali ta ce "In" buɗe ƙofar aka yi tare da shigowa ɗauke da sallama. "Good morning Maa" "Yakake Accouter?" "Couldn't be better" Ta nuna masa kujerar dake gabanta fuska a ɗan sake ta ce "Have a seat" Accounter Wazeer ya ce "Thank you" Waje ya nema ya zauna hannunsa riƙe da file ya miƙa mata ya ce "Ga file ɗin nan na sabuwar shinkafar da aka kawo, na shigar a ducoment na yi sharing nasa to your mail" ta jinjina kai kawai haryanzu bata kalli Accouter ba. Ya sake cewa "Md ya yi mini sharing mail na invited da aka yi wa Fs world, akan taron dukkan wasu manyan Companies da suke Kano, ya ce ki duba mail ɗinki" "I saw it" ta ce silently. "Maa naga a list ɗin har da Arɗos group, da sauran manyan kamfanin" "Wazeer" "Yes Maa" Aafiyyah ta ɗago kanta tana kallon Accouter kafin ta ce "What are afraid of? Na ga invited, so we'll be there" "Maa wai daman ƙarfin Arɗos group ne sai a hankali bamu san invited ɗin kan mene ba, dole mu shirya we have to be very careful, kinga har yanzu bamu san su waye Arɗos group ba" "I don't care Wazeer. Ka bani information na binciken da ka yi" Laptop ɗin gabanta ya janyo ya fara danne danne sai sunaye suka fito sama da mutane hamsin ya ce "Wannan sune mutanen da suke da hannun jari a FS WORLD INVESTMENT, yadda suke a jere haka matsayin hannun jarin kowa yake, ba zan iya tantance mutane biyar ɗin da ake zargin cewa sune masu asalin kamfanin ba. Mutum na farko a sunan ke ce Safiyyerh A Marafa, na biyu akwai wani wai M.A, akwai Eng Ali wali, akwai Alhaji Boɗejo, akwai Alhaji Haladu, akwai Alhaji Lawwalli da Alhaji Saduƙu akwai Professor Abdul-Johar Marafa e.t.c" "Accouter ji nake Alhaji Haladu da Saduƙu da Lawwalli sun rasu" "E, an ce wani wai Scorpion ya kashe su kamar yadda gidan jaridar VOA suke sanarwa a labaransu" Aafiyyah ta yi shiru, Scorpion ya kashe Alhaji Haladu da sauran mutane biyu da suke da hannun jari a FS WORLD, yanzu yana harin Ali wali da Maɗatai, anya wannan abin babu wani abu a ƙasa? Abin da yake faruwa bashi da alaƙa da wannan kamfanin? Amma ai Maɗatai bashi da hannu jari dole ta sake bincike sosai. Ta sauke ajjiyar zuciya ta ce "Waye M.A kuma?" Accouter ya ce "Ban sani ba" "Take your time Wazeer" "Thank you maa" Bayan fitarsa Aafiyyah ta kira Md ya kashe ta ya ce "Manager ya aka yi?" Murmushi Aafiyyah ta yi na dole kafin ta ce "Md kenan" "Manager akwai labari ne?" "Nop" ta ce tana miƙewa tare da tattara kayanta ciff ta ce "Akwai wata sister ta da take da matsalar ƙoda, mun nemi wacce za'a iya saka mata mai kyau da za'a iya dacewa, ina son sister ɗita sosai ko zaka iya taya ni nemo ƙoda Please?" Md ya yi shiru yana tunani Aafiyyah ta ce "Ko nawa ne zan biya, ka san kuɗi ba matsalata bace in sha Allah" sai ya yi saurin miƙewa ya ce "Manager ai ko a wannan kamfanin za'a iya samun ƙoda, ko nawa kike so, mu je na raka ko ɓangaren amma za ki bani wani abu" ya ce cike da fara'a. "Faɗi abin da kake so" "500k ma ya wadatar dani" Aafiyyah ta ce "i will add you another 500k, 1m kenan ka yi farinciki" "Thank you Maa" Fita suka yi Aafiyyah ta ce "Amma ka yi shiru kaga basa son a san ana sabgar nan, be quiet ok?" Azumi take yi, amma kuzarinta na nan ma sha Allah gata da tsayi a hankali take tafiya Black ɗin jallabiya ce a jikinta mai ɗan faɗi ta saka wani baby hijab, wannan karan cat eye ne a idanunta, sai jakar L&G dake hannunta, yanayin tafiyarta kamar catwalk haka take yi tana tafe tana lumshe idanunta, kafin su ƙarasa can sashin da yake kamar asibiti ta saka facemask a fuskarta. A bakin ƙofar suka tsaya I.d cards ɗinta ta nuna security ɗin da aka saka Safiyyerh A Marafa. Manager ta Fs world cikin sauri ya buɗe mata ƙofa ta shiga,cak tsaya saboda wani irin sanyi daya ratsa mata jiki ga wani irin warin acid da ƙyar ta yi ƙoƙarin ƙarasawa har office ɗin wanda yake kula da ɓangaren asibitin cikin sauri ya tarbeta ya ce "Wclm Maa, Dr Ganash my name how can i help you" "Sannu Dr Ganash, ina buƙatar Kidney for my sister's health" Dr Ganash ya ce "Oh I'm so sorry ma, Allah Ya sauwaƙe ok" Ta jinjina kai kawai. "Ina tunanin akwai sabbin ƙoda ma, zan ba ki information ki duba lafiyar kowanne kidney sai ki yi zaɓa" Aafiyyah ta ce "Aikin ka ne, kawai me lafiya nake su. Nawa ne kuɗin?" Dr Ganash ya ce "10m each" "Ok. Details na biya?" Dr Ganash ya yi ɗan shiru sai kuma ya ce "But ba'a nan zan ba ki ba, zan faɗa miki inda zamu haɗu na ba ki ok? Saboda abin namu akwai risk" "Allah Ya taimaka. Yau ne farkon zuwana yana da kyau a zaga dani naga yanayin aikin naku" Fita suka yi ya fara nuna mata komai zuciyarta na bugawa da ƙarfi har sashin operation ya nuna mata wai a nan ake wa mata aiki da sauran mutane sai ta sawa ranta cewa aikin cire ƙoda ne kawai. Ta dinga kallon jariran da suke kwance akan baby bed kyawawan gaske, ta tsaya akan wani baby sai ta dinga ganin kamar Hon Maɗatai a fuskar babyn, idanunta ya cika da ƙwalla amma ta yi saurin dakewa saboda Dr Ganash sunayen Allah kawai take kira a ranta. A haka suka gama ta fito bata saurari Md ba ta nufi motarta tana shiga ta ɗora kanta a saman kan motar ta saki wani irin kukan tashin hankali ta yi mai isarta kana ta yi shiru, amma kamar jaririn da hon Maɗatai ta tsaya mata a zuciya ainun ta ji dole ta nemo gaskiya. "Why Ashraf?" Ta ce a hankali. Da yana raye da tuni ta shige wajan, da ace ya faɗa mata da tuni ta kawo ƙarshen matsalar sai ta ji lallai Ashraf ba mutuwar Allah da Annabi ya yi ba, kashe shi a ka yi, sai kuma gabanta ya faɗi idan ta tuna a daren mutuwar Ashraf ya ce daddy ya je, for what reason kuma?. A hanya ta dinga yi sadaƙar kuɗi ta fanshi kur'ani da yawa ta kai masallatai. Tana zuwa gida ana kiran sallar magariba, a gurguje ta yi wanka ta yi sallah ta jima tana addu'a tare da kaiwa Ubangiji kukanta kafin ta sakko jikinta sanye da jalbab hannunta riƙe da counter ta yi zuru-zuru. A parlour ta same su tana murmushi ta zauna ta ce "Barka da dare Ummi, my brothers" sai suka yi shiru suna kallon ta musamman Junaid ta watsa hannunta sama ta ce "Kamarya? Me na yi?" "Maamah kin ga idanunki?" Cewar Dr Hash. Sai Awais ya ce "Wallahi kamar idanunki mage, ba kifi kilo ɗaya ba little sis are you okay" Kallon su kawai take tana bubbuɗe idanunta saboda da gaske bata gane ba. Dr Hash ya ce "Ƙarya muka yi ne?" Kamar jira take yi ta fara watsa hannu tana nunnunasu ta yi turanci idan ta yi ta gaji sai ta koma German language. "Quiet!" J ya furta yana miƙewa tsaye Awais ya ce "Baturiyar gidanmu, gaskiya an yi kuskuren kai Maamah Germany maganar gaskiya, saboda Allah kina Hausa Fulani amma Hausa cikakkiya bata wadace ki ba? Muma sai ki tsare mu da wannan turancin naki dake kaɗai kike ganewa? Huh!" "Kuma azumi ta yi fa, dake yau ƴan maganar na kusa shine zata dame mu, sai ki je wajan abokin ko mijinki" Aafiyyah ta cillawa Awais harara ta ce "Maganarka ne zai hanaka yin budurwa wallahi" ya yi dariya sosai ya ce "Lallai ƴa, kar ki so kiga yadda ake rushing akai na wallahi mamas boy ne ni fa, be careful" Ummi ta ce "Ki rabu da shi ki je ki buɗe cikin nan naki dake maƙale" "Kai kai Ummi wannan cikin nawa watarana baby zai ajjiye fa,zan haifar miki jikoki masu kyau irina" Awais ya ce "Au kenan wani kyau ne dake? Or poor Maamah sorry fa" Tana nufar bedroom ɗin Ummimi ta ce "Wallahi ina son babies sosai musamman maza kyakkyawa masu halina, Allah ina ƙaunar baby ji nake kamar na je na ɗakko kyautar baby na raine shi Allah Ummi" Ummi ta riƙe baƙi ta ce "Mun shiga uku, anya kanki ɗaya kowa? Bama ki haifi naki ba?" Aafiyyah ta ce "Ai na yi ƙarama da samun ciki Ummi" ta ce tana shigewa cikin ɗakin Ummimi. Gaban Ummi ya faɗi kamar yadda na J ya faɗi a lokaci guda, anya sun kyauta kowa ita da Paaahh? Anya basu ɗauki hakƙin Aafiyyah ba?" Jikinta ne ya yi sanyi ta miƙe ta nufi part ɗin Dig Johar. Aafiyyah na shiga bedroom ɗin Ummimi ta ce "I so much miss you love...," saurin yin shiru ta yi ganin AA MAJ kwance a cinyar Ummimi ya kifa kansa, magana take yi masa a hankali cike da nutsuwa, a fuskarta zaka hango zallar so da ƙauna a yayinda da takewa Maj magana, ta riƙe hannunsa cike nata ɗaya hannun nata tana shafa kansa, Aafiyyah mamaki ya cikata dama Maj yana irin wannan sangarta wani ƙato da shi, me ya sa baya sakin jiki da kowa sai da Ummimi? Juyawa Aafiyyah ta yi zata fita Ummimi ta ce "Ina za ki kuma? Ko maganar ɗakko babyn ce ba ki kammala ba?" Zaro ido Aafiyyah ta yi kenan duk sun ji? Kunya ta kamata domin bata yin rashin kunyarta akan idanun Ummimi yanzu zata ci ubanta kana ta rarrashe ta. Zama ta yi gefen Ummimi ta ce "Ansha ruwa lafiya?" "Allahamdulillah" Ummimi ta amsa tana kamo hannun Aafiyyah ta haɗa tana Maj ta riƙe cikin nata ta ce "Shi ba ki yi masa sannu" sai Aafiyyah ta marairace fuska tana ɗan tura bakinta gaba ta ce "Ai baya azumin Alhamis da juma'a" Ummmi ta ce "Injiwa? Tun kafin a haife ki Gadanga ke yin azumi, ban da zamani gudanawa kike ma Maamah?" Sai Ummimi ta yi murmushi ta ce "Uhm, na daina raina matar Maj kar a saka mini bindiga kodayake ai na ji kina maganar jikoki Allah Ya nufa na gansu idan muna raye" Maj ya miƙe tsaye ya ce "Bari na je, a kawo mini part ɗina" Ummimi ta jinjina kai. Ta dawo kan Aafiyyah ta ce "An faɗa miki gobe za ki tare a gidan mijinki ko?" Aafiyyah ta yi shiru. "Sha wannan" zumar S Bayero ce da sauran haɗin wasu maganganu musamman na sanyi ta bawa Aafiyyah da ƙyar Aafiyyah ta shanye ta sake bata haɗin wata dafaffiyar kazar amare wacce ta yi ordered daga wajan S Bayero. Da ƙyar Aafiyyah ta ci kazar tana yi wa Ummimi rigima hadda kuka, ita dai Ummimi bata kula Aafiyyah ba bayan ta gama ta ce "Ki ɗauki warmers ɗin nan ki kaiwa Gadanga" "Uhm'uhm Love wai komai ni" Carbi Ummimi ta ɗauka da gudu Aafiyyah ta ɗauki warmers ɗin ta nufi part ɗin da ɗan guntun hawayenta. A zaune ta same shi yana shan coffee bayan ta ajjiye zata juya ya yi saurin riƙo hannunta ya zaunar da ita saman cinyarsa yana ajjiye wayar hannunsa ya ce "Muhammad nake kira yaƙi ɗagawa" sai ta yi shiru a hankali kuma ta juyo tana daga kan cinyar tasa ta kalle shi ta ce "Ka san me Maj?" Ya girgiza mata kai yana bin fuskarta da kallo ta ce "Muhammad ɗin nan kamar na san irin fuskarsa ba, da voice ɗin haka nake ji" ya yi ta kallon ta, sai ya tuna cewa Muhammad ya taɓa faɗa masa cewa ya san Aafiyyah ya ganta da ciki a hankali Maj ya ce "How?" "Haka nan fa" ta ce tana ɗaga kafaɗa. Game ya kunna a screen ɗin t..v dake cikin parlournsa, ya miƙa mata handle ɗaya ya ce "Play" super mario suka fara shi Maj bai wani iya ba, Aafiyyah tuni ta manta damuwarta idan taga ta ci game ɗin sai ta yi ihu ta juya ta rungume Maj ta faɗin "Yes yes I'm the winner hooo" ta yi masa gwalo, shi Maj kallon ta kawai yake yi domin baya ma fahimtar game ɗin, sai ya ji nutsuwa ya fara samun hanyar shaƙuwa da ita cikin sauƙi. A wannan karan bayan ta rungume shi ta buɗe baki za ta yi masa gwalo ta ji saukan harshensa mai laushi cikin bakinta ta yi saurin rufe idanunta, jikinta na fara amsawa saboda abubuwan data gama sha, wani irin kissing ɗinta yake slowly slowly kuma romantically, a hankali tafin hannunsa na yawo a wuyanta, saurin rufe idanunta ta yi jin hannun Maj a wani wajan, ta yi saurin riƙe hannun kafin ya yi abin da ya yi niyya, ta fara ƙoƙarin ta shi ya yi saurin rungumeta sosai a ƙirjinta a hankali ya ce "You want a baby right?" "Uhm" ta girgiza kai. Sai ya cigaba da sumbatar bakinta a lokacin daya gama cire hijabin jikinta, da kyau ya riƙeta yana janta zuwa saman bed, ita Aafiyyah kasa jurewa ta yi, abin da take ji na fusgarta zuciyarta na buɗe, sai ta fara responding kisses ɗin zuwa back to Maj, a lokacin Maj ya nunawa AAFIYYAH ƙauna a zahiri duk da bai bayyana ba, sun ɗauki minti uku suna kissing juna tare da ajjiye wani good memory a lokaci. "Do you love me?" "I have to ask Yaya, kana so na?" Sai ya nuna mata ƙirjinsa ya ce "Nan" Hannunta ta miƙa zuwa ƙirjinsa ta ɗora hannu idanunta na sauka a gargasar ƙirjinsa kansacewar fari ne shi tas, ya saka sumar ƙirjinsa bayyana sosai madadin ta ji bugun zuciyar tasa, sai ta samu kanta da shafa sumar ƙirjinsa a hankali ya ce "Waya saki?" Ta yi saurin rufe fuskarta a ƙirjinsa tana murmushi ta ce kan uba ashe haka auren yake za ta yi wasarere ai zama za ta yi ta ɓarje guminta da lokacinta zuwa nan da wata tara ta samu cute baby boy. A daren dai a tare suka kwana tana kwance a jikin Maj tana bacci hankali kwance, shi kuma idanunsa biyu lokaci zuwa lokaci sai yaga ta ɗan zabura tana surutai, ko kuma yaga ta shafa cikinta har hawaye yake gani a idanunta, sai ya yi mata addu'a ya sake shigar da ita jikinsa yana shafa sumar kanta sai a lokacin ya samu damar ƙarewa fuskarta kallo shi bai sai dame zai kwatanta fuskar Aafiyyah ba sam, kawai ya san idan har mutum namiji idan ya kalleta sau ɗaya zai sake juyawa ya kalle ta, duk da hasken da take da shi sosai. A zuciyarsa ya ce “I'm already crazily in love with you & you're making me more crazy” * Morning. Aafiyyah ta haɗa team a ɓoye ta shirya tsaf cikin Black suit for girls ta yi mata kyau sosai, ta shiga motarta ta ce team su bita a baya, tana ƙoƙarin fara driving ta hango AA MAJ ya fito zai fita training ta cikin motar suka kalli juna, murmushi kawai ta yi shi kuma kallon yake kafin ta ji notification ta duba taga saƙon shi ne "Ina za ki?" Replied ta yi da "Aiki, good morning" “Be careful bby ga” Dariya Aafiyyah ta yi jin ya ce baby sai ta sake replied da “I have a gun with me” sai taga ta turo emojin na dariya ya ce "Allah Ya ji ƙan wanda ya yi arba da matar Maj" "Ni staff ɗin Fcid ce, ina da Paaahh and you too husband" Wayarsa ya mayar kawai cikin aljihu yana danne murmushinsa. Motarta taja zuwa waje. Map ta dinga nuna mata direction ɗin da Dr Ganash ya bata, team ɗinta na Fcid na biye da ita, tashin hankalin da Aafiyyah ta gani bai shige ganin gawar Dr Ganash ba kwance cikin jini, kamar ba'a jima da kashe shi ba, a gigice ta zaro bindigar aljihunta ta fara kewaye wajan. "check the roads guys" dubawa suka fara yi, ita kuma ta kutsa kanta cikin wani lungu ai kowa tana shiga ta hango wani da bindiga kafin ta ƙarasa wani ya shigo suka zama su biyu. Saita bindigarta ta yi, tana zuwa ta saka ƙafa ta taɗe wani ya faɗi ƙasa, ya yunƙura zai tashi ta buga masa ƙasan bindiga a kansa wajan ya fashe, bai ɗauka mace nada ƙarfi haka ba, bai san cewa ƙarfin zuciya bane. Wanda yake tsaya da bindiga fuska rufe ya saurin yin baya, Aafiyyah ta fara yi wa team ɗinta inkiya, mutumin yaga asiri zai bayyana sai ya faki idanun Aafiyyah ya harbe wanda ta kama. "What, kana da hankali?" Bai saurare ta ba, ya sha kwana ta bisa da gudu kafin ta ƙarasa ya shiga wata mota ta aka cire number motar kafin ta ƙarasa tuni ya gudu ta yi saurin komawa. Shi kuma gudu kawai yake yi a titi sai da ya yi nisa sosai ya buɗe fuskarsa, a hankali Hon Maɗatai ya sauke numfashi gani ya tsira, yana mamakin halin yarinyar bata da tsoro ko kaɗan. * Moh na zaune gaban computer yana kallon ikon Allah, domin daman Muhammad ya gama yin connected na motar Aafiyyah da computer idan har ta fita da motar yana iya ganinta da duk inda zata. A hankali Moh ya miƙe tsaye yana sake kallon abin da yake faruwa sai ya ɗan taɓe bakinsa da sauri kuma ya kashe computer ɗin jin motsi alamar ana shigowa. AA MAJ ya shigo cikin sauri yana faɗin "Muhammad kana ina, how many times zan kira ka ne?" Moh ya juya ya kalli AA MAJ kallon tsaf, shi mamakin yadda har kamminsa suka ɓaci da wanda bai ba sani ba haka, har ake iya kasa gane cewa shi ba Muhammad bane. Ya ɗauke idanunsa daga kan Maj, sabon rainin da Muhammad ya tsira yana bawa AA MAJ haushi sai ya juya yana cewa "Follow me Muhammad" Tsoron magana Moh yake saboda muryarsa ba iri ɗaya bace data Muhammad sai kawai ya jinjina kai ya bi bayan Maj a mota ya same shi yana cewa "Wanne hospital ɗin? An samu jinin ko yaya?" Can ya ce "Ok, i am coming ku jira ni" Moh ya shiga gaban motar, tunda suka ɗauki hanya bai magana ba, gari kawai yake kallo fuskarsa rufe da facemask a haka har suka ƙarasa babban hospital ɗin, a nan ya fahimci kamar accident aka yi. Gaban Moh ya faɗi lokacin da idanunsa ya sauka akan I. Qasim kimiyya dake jikin Jeddah idanunsa ya yi jajur, a hankali ya fara bin mutanen wajan da kallo, sai ya sake jin faɗuwar gaba lokacin da idanunsa ya sauka akan Alhassan da fuskarsa ta fi ta kowa nuna tashin hankali, sai kuma yaga Mimi dake sanye cikin babban hijabi,harɗe hannu a ƙirji sai Moh ya ji he feels comfortable here da mutanen wajan, gabansa nata faɗuwa, musamman idan ya sake ganin kimiyya daman har yanzu Kimiyya yana nan yana raye?" Innalillahi. Suka mimmiƙe lokacin da su kaga AA MAJ shi da wani wanda ya fi Maj ɗin jiki da buɗewa har tsayi yafi Maj. Kansacewar fuskarsa a rufe take sai suka kasa sanin waye, Qasim bai motsa ba yana rungume jikin Jeddah da take rarrashinsa. "Daman Dr Abraham tafiya ya yi? Hatsari garin yaya?" Cewar Maj. Jeddah ta ce "Za shi Lagos ne, duba aikin da aka fara na kamfani wai daga gida zuwa airport akace sun samu accident shi da Alhassan. Cikin ikon Allah Alhassan ba abin da ya same shi sai bugawa aka yaƙi bari ma a yi treatment ɗinsa, Dr kuma ya zubar da jini sosai gabaɗaya an gwada jinin Alhassan dana Qasim bai yi daidai ba, Al Hussaini baya garin shima balle a gwada nasa, ana buƙatar jini urgently" "Where is doctor?" "Yana laboratory" Maj ya juya ga Alhassan, kafin ma ya yi magana Alhassan ya miƙe ya bar wajan. Sai Maj ya ce "Mu je Muhammad" Mutallab kasa motsi ya yi, kallon Alhassan kawai yake yi ya ji kansa na sara masa sosai, sai a lokacin Qasim ya lura da wanda suke tare da Maj amma bai damu ba, hankalinsa naga mahaifinsa da kuma Mimi da haryanzu ba ta yi magana ba tun faruwar abin ko saboda Jeddah dake wajan ne?. Laboratory AA MAJ ya nufa, Mutallab da Maj yake tunanin Muhammad ne na biye da shi, suna zuwa Dr ya shigar da Mutallab aka gwada jininsa da sauri Dr ya ce "Waye kai?" Sai Moh yaƙi magana, haryanzu fuskarsa a rufe sai kawai ya miƙe ya fito. Dr ya fito shima ya kalli Maj ya ce "Thank God, jinin ya yi daidai bari a ɗauka a saka masa" "Shi waye da jininsa ya yi daidai dana mahaifina? Babu jinin wani bare da aka isa a sawa Papi" Cewar Alhassan yana ƙarasu wajan. Dr ya kalli Maj ya kalli Alhassan kana ya kalli Moh da yake tsaye hannunsa zube cikin aljihu, sai wani shocked ya kama Moh jin irin muryarsa sak a tattare da Alhassan. "Who is he? Waye shi?" Maj ya yi shiru yana kallon Muhammad can ya ce "Dr je ka ɗauki jinin Please" "I meant it, ba za'a sakawa Papi jinin wani ba" Moh zuciyarsa na harzuƙa shi baya tolerating irin wannan abubuwan yanzu sai sakawa Alhassan askira a ciki ko ya yi masa ɓalli-ɓalli ina ruwansa da su ma?. Dr ya ce "Alhassan waye wani ɗin?" Alhassan ya yi poiting Mutallab ya ce "He" Dr ya ce "Wannan ɗin?" "Yes, shi" sai Dr ya yi murmushi ya ce "shi ɗin ai ba wani bane, shi ɗin Abraham's son ne, ɗan Abraham ne"......... 💥Chapter 9: Complex Tension Alhassan ya tsare dr da sexcy eyes ɗinsa da ya ɗan lumshe su ya buɗe, ba tare daya juya ya kalli Moh yana poiting ɗin shi da yatsa ya ce "liar, you're a liar ta ya wannan zai zama jinin mahaifina? Never ƙarya ne" Alhassan ya ce "Dr ka faɗa mini waye ya baka wannan kwangilar aikin? Waye ya saka ka ce shi ɗan babanmu ne? Saboda kawai jininsa ya zo ɗaya dana Papi? Are you stupid?" "Be respectful Alhassan" cewar AA MAJ. Domin shi baya son mutum mara kunya, zai iya sanya ƙafa ya tattaka Alhassan yanzu, ya lura sarai yaron bashi da kunya duk da cewa shi ne babban ɗa a wajan Dr Abraham ɗin, amma ya kasa nutsuwa till now, ya kasa ginawa kan shi kyakkyawar makoma ko aure ya kasa yi, sai son girma, da shegen girman kai da izza, kodayake dole ya yi izza idan aka duba asali tarihi akwai jinin sarauta a tattare da shi, haka ma izza ɗin bai ɗauka a ƙasa ba, ko wajan kakansa an sha fama haka mahaifinsa. Yana da kishi sosai. Alhassan bai kalli Maj ba ya cigaba da magana with Spanish language "Ko saboda ya shiga siyasa ake son yi masa wani sharrin? Shi ya sa bani da wani interest akan wata siyasa, shima Papi i told him ya bar wannan siyasar kawai me ya rasa a rayuwa? Dr wannan plan ɗin waye? Mene tabbacin cewa shi ɗin jininmu ne? Wani mutum can wagairahun yana yawo a duniya za'a ce wai jininmu ne? No no no please, this is complicated, set up ne kawai" Haryanzu Moh bin Alhassan yake da gajiyayyun idanunsa, da suka soma juyewa yana riƙe kansa da kyau, da ƙoƙarin ganin ya bar wajan cikin kwanciyar hankali bai yi ɓarna ba, amma baya jin za su kwashe lafiya dole ya saitawa wannan ɗan wahalar nutsuwa, sai ya saka masa tsini zai nutsu ko ya yi masa ƴan uku-uku da askira. Ya fesar da numfashi ta cikin facemask ɗin tare da cije bakinsa kawai. Alhassan ɗin ma kallon idanun Moh yake kafin ya ce "Dr DNA test ka yi kaga ya fito as positive? Ko ra'ayinka kawai ka faɗa?" Dr ya girgiza kai ya ce "A'a" "Kenan me ka yi?" "Blood ɗinsu ya nuna matching, blood group, da genotype are the same" "Oh! For real?" Cewar Alhassan. Daidai nan Qasim ya ƙarasu wajan shi da Jeddah, da Mimi da Soha, Mimi idanunta akan Alhassan domin tunda ta ji kanta na sarawa ta san Alhassan ke yin wata rigimar, da fararen idanunta cikin babban hijjabinta kawai take kallon shi, itama Jeddah Arabian jallabiya ce a jikinta mai kyau da tsada hannunta cikin na Qasim ita kuma Moh ɗin take kallo, tsaiwarsa da cikin idanunsa tana sake gasgata tunaninta a kan shi kafin ta tausasa kalamanta ta ce "Meke faruwa tawaye? Wannan ɗaga muryar cikin asibiti akan menene?" "Gashi nan, ku kalle shi" Ya ce yana nuna Moh. Suka juya gabaɗaya suka kalli Moh ban da Mimi, Qasim ya dinga kallon shi sai Jeddah ta ce "Mun gani, mene?" "Suna claiming wai ɗan'uwanmu ne" "Pardon! Ban fahimta ba?" Soha asked, tana sake kallon Moh da kyau da idanunta masu kaifi cikin nutsuwa kuma. Alhassan bai kalle ta ba, ya yi wa Jeddah bayani komai sai ya ɗora da cewa "Rainin wayo kawai ne wannan bai san aikin shi ba" Qasim ya yi gyaran murya ya ce "Dr wanne bincike ka yi ne? Aikinmu ɗaya maybe i can help you" "Dr Qasim ba bincike na yi ba, kamannin dana gani a fuskar yaron da kuma kamannin Alhassan shine ya saka na ce haka, da kuma yadda jinin Dr Abraham ya yi ɗaya dana wannan yaron da suka zo tare da Maj" cewar dr yana nuna Alhassan da Moh da hannunsa yana sake jaddada kamannin sosai, domin da suka shiga wajan ɗaukan jini Moh ya zame fuskarsa kaɗan wanda hakan ya bawa dr damar ganin kamar. "I am sorry, wannan ba hujja bace dr, domin Ubangiji kan samar da kamannin mutum har sau bakwai a gari, ƙasa, ko unguwa wannan kaɗan daga cikin girma da kaɗaitar Ubangiji, kamar yadda hadisi da fatawar malamai suka nuna haka. Baka haɗa komai da mutum ba amma jininku na blood group kan iya zuwa daidai, ƙwayar halitta ce kawai zata nuna ainahin gaskiyar da kake ƙoƙarin nuna mana, sai mu yi DNA test to find out the truth ko?" Alhassan ya ce "Ba wani DNA test da za'ayi, hatsarin Papi set up ne, kawo wannan yaron ma set up, useless boy" ya ce yana ɗaga kafaɗa sama. A hargitse Moh ya yi kan Alhassan, dif dif dif zuciyarsa na buɗewa cike da damuwa da takaici, da ya san nan za'a kawo shi wallahi da bai zo ba, har cikin ran shi shi ya ji cewa bashi da haɗi da su, ko a baya bai jure wulaƙanci da ƙasƙanci ba balle yanzu da zuciya ke ribatar shi, da yake jin shi daban a cikin sauran mutanen tabbas shi useless ne, bashi da wani amfani ga kowa, iyayen da suka haife shi ma basa ƙaunar shi balle wasu dangi daban?. Idanunsa rufe ya damƙi wuyan Alhassan ya haɗa shi da jikin bango, jikinsa na kakkarwa idanunsa na buɗe tare da watsa su a fuskar Alhassan ɗin, ƙoƙarin kwacewa Alhassan yake daga hannun Moh, amma ya kasa, duk da training da yake yi morning and night amma ƙarfin Moh a ƙirjinsa ya saukar masa. Idanunsu cikin na juna yana sake sake shaƙe Alhassan da ƙarfi, Qasim baya ya yi tare da harɗe hannu, AA MAJ kallon Moh kawai yake yi da tunanin cewa Muhammad. Mimi kuma Alhassan da Moh take bi da kallo, haka kawai ta ji gabanta ya faɗi, kamar yadda zanen tattoo yake a gefen wuyan Alhassan daga sama, haka ta hango zanen tattoo a ƙirjin Moh daya buɗe saboda rigar jikinsa buɗaɗɗiya ce wasu daga cikin kayan Alhassan ya ɗakko ya saka. Ɓacin rai da yadda zuciya ke angiza Moh ya saka ya falle Alhassan ya faɗi wanwar a ƙasa, ya bisa da ƙafa ya danne murya a kumbure da yadda baka iya tantance sautin ta ya ce. "I hate you, i hate myself, i hate your family, i hate my own family" Ya ce yana ƙoƙarin ciro askira sai kuma ya dakata saboda ya tuna Muhammad baya faɗa da makami ya faki idanun mutanen ya cillawa Alhassan kunama a cikin wando kamar walkiya kuma ya tashi ya yi wata kwana cikin wata tafiya da buɗawa irin babu wani shege da ya yi saura sai shi. Da sauri Alhassan ya tashi jin wani abu na gasa masa cizo a jikin mazantakarsa, zafi da raɗaɗi ya saka ya fara haɗa uwar zufa amma ya dake gudun raini daga wajan ƙannensa ya bi bayan Moh da sauri cike da zafin zuciya kuma. "Alhassan!" Mimi ta kira shi da ƙarfi. Cak, ya tsaya bai juya ba ta ce "Idan ka bi bayansa sai ka gane baka da wayo" magana zai yi ta yi saurin ɗora hannunta a bakinta ta ce "No agreement" sai jinjina kai ya yi gaba yana buga ƙafa. Mimi ta juya kan Qasim ta ce "Kai daman ba namiji bane ko? Kana gani ana faɗa da ɗan'uwanka idan anji masa rauni fa?" Qasim ya ce "Mimi wanann faɗan na majiya ƙarfi ne, matata nake lallaɓawa kai na gaskiya" "You're right dear" cewar Jeddah. Mimi ta sake kallon AA MAJ ta ce "Aliyu ya gida? Idanunka kenan kwana da yawa? Fatan komai lafiya?" "Alhamd, ya mai jiki" Ta ce "Alhamd" Ta ɗan yi shiru sai ta ce "Meke faruwa ne Aliyu? Waye wancan ɗin?" AA MAJ ya shafa kai ya ce "Kamar yadda dr ya yi faɗa ne, sunan yaron Muhammadu a wajena yake zaune kuma da gaske shi jinin Sir ne halataccen ɗan shi, domin na jima da yin DNA test shi ya sa da aka ce an rasa jinin da za'a sawa Yallaɓai na yi tunanin kawo Muhammad ɗin ko za'a dace, and thank God ya yi" "Unbelievable!" In ji Qasim. "Ya aka yi hakan ta faru? Jeddah bata taɓa haihuwa ni kuma ga iya yaran dana haifa nan, dr bashi da wasu matan sai mu balle na yi tunanin ɗan wata ne, i trust my husband ba zai bi matan banza ba, balle na ce garin haka aka samu Muhammad ne. Mene yake faruwa mene gaskiyar lamarin?" Cewar Mimi tana ƙoƙarin faɗuwa domin a gigice take, musamman da ya ji muryar Moh wacce iri ɗaya ce sak data Alhassan tsananin kiɗima da tu'ajjuji ya saka ta kasa motsawa gashi yaron a tsaye yake babu alamun tsoro tamkar Dr Abraham yana matashin saurayi, meke faruwa? Whats going on? Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, subuhanallahi! Shi kawai take maimaitawa a zuciyarta da fili. AA MAJ ya ce "Zan yi bayani amma ki bari Sir ya ji sauƙi a bar hospital ko" Ta jinjina kai kawai. Qasim ya juya ya bar wajan, hankalinsa tashe abubuwa da yawa sun yi masa yawa a zuciya ya fara rasa ta inda zai fara ina kuma zai tsaya me kuma ya kamata ya yi? AA MAJ ya bar asibitin shima Soha ta shiga motarta ta nufi gida domin ba'a zama a asibitin Mimi ta kasa motsawa, Jeddah kuma na jingine da jikin bango tun ɗazo tsoro da fargabar bankaɗo gaskiya ne ya cika mata zuciya ya hanata kuma sukuni. Cikin ƙaramin lokaci yanar gizo ta ɗauki trending akan hatsarin Dr Abraham Denial David ɗan takarar ɗan majalissar tarayya a ƙarƙashin jam'iyyar NNY New Nigerian Youth. * A can federal investigation department. Muhammad na zaune idanunsa a ƙasa jikinsa ya yi jina-jina da jini yadda kwana biyu suka tisa shi a gaba wajan faɗin dole sai ya amsa cewa shi ne Scorpion kuma ya faɗi dalilinsa na kashe mutanen da yake kashewa, mene ya saka yanzu yake harin kashe ƴan siyasa hon Maɗatai da Eng Ali wali?. Ya faɗi komai yadda za su sassauta masa idan har akwai gaskiya akan abin da yake yi, idan babu kuma za su kashe shi nan take ne ko su yi masa allura ya je can ya ƙarata sannu a hankali zai haukace. Dig Johar na tsaye ya ce "Scorpion kenan" ya ce yana jan kujera ya zauna ya girgiza kai ya ce "Za ka yi magana kai sai na saka an cire maka yatsa guda ɗaya ne?" A hankali ya ɗago kan shi, cikin kwanakin da ya yi har ya fara fita hayyacinsa yana neman gazawa amma ya daure da ƙyar numfashinsa ke fita saboda wahala ga wani zazzaɓi da ya yi mai zafin gaske kwana biyu, baya iya cin abincin wajan ya saba da abinci mai daɗi, kwanciya a makeken gado, ga ac komai a wadace. Ya ja numfashi mai zafi ya fesar kafin ya ce "Za ka iya faɗa mini mutane nawa na kashe?" "Uhm ka kashe Alhaji Saduƙu ka kashe Alhaji Lawwalli da wani Alhaji Lamiɗo kuma kana shirin kashe Maɗatai da Eng Ali wali" Muhammad ya dinga kallon Dig Johar, yana tuna maganar tsohuwa Abbasa data zo ɗazo take faɗa masa sai ya ce "Mene aikin su?" "Ina ruwanmu da sanin aikin su? Mu jami'ai ne masu kare hakƙin rayukan mutane da dukiyoyinsu kuma su ɗin manya ne su a ƙasar nan da jihar, haifaffun ƴan ƙasa Nigeria ne da cibiya Kano, suna da hannun jari a FS WORLD INVESTMENT" Wani killer smile Muhammad ya jefawa Dig Johar ya ce "Ka je ka tambayi Hon Maɗatai da Eng Ali wali, ina ne asalin mahaifarsu? Daga ina suke, a ina aka binne cibiyarsu" "Silly questions! Kowa ya san ƴan Kano ne su wanann a zahiri yake" Muhammad ya ce "Sai yanzu na tabbatar Fcid basu iya aikinsu ba, ko suma dai cin hanci ake basu? Daga taskar su Maɗatai ɗin?" "Be careful yaro" Dig Johar ya ce yana zaro bindiga tare da saita kan Muhammad. Sai Muhammad ya ƙyaƙyace da dariya, sai ya ɗauki abin kamar yana playing game ne, yana son funny abu yana bashi nishaɗi bayan ya gama dariya ya ce "Su ɗin duka Bafullatanai ne, ka je ka tambaye su mene dongantakar su da garin RANO, sai ka dawo na baka amsar tambayar da kake mini" Yana faɗin hakan ya tsuke bakinsa, Dig Johar ya dinga magana amma ya yi shiru suka dinga dukan Muhammad har suka karya masa hannu nan take suka sumar da shi, da sauri Dig Johar ya fice daga cikin ɗakin yana shiga motarsa ran shi ɓaci saboda wahala kawai yaron ke bashi, gashi daga sama har yanzu an dagatar dasu daga kashe Scorpion. The following days. Sama-sama Muhammad ya ji ana matse hannunsa, cikin sauri ya buɗe kumburarrun idanunsa da sukai masa jajur idanunsa ya sauka akan tsohuwa Abbasa da kuma Moh dake zaune fuska kame, ya yunƙura ya miƙe zaune sai yaga tuni ta gyara masa karayar hannunsa amma ya kasa tsohuwa Abbasa ta ce "Na ji komai, duk abin da za su ce ka yi shiru har sai na baka damar magana ka ji ko? Mu yi ƙoƙarin ka fita cikin salin alin kuma kamfani ya dawo hannun Mutallab ka ji?" Ya jinjina mata kai. Sai ta juya kan Moh da idanunsa ke gefe ɗaya ta ce "Za ka je can Fs world, matsayin Muhammad tunda Manager ta san Muhammad a tare da mijinta, zaka je matsayin taimaka mata ka faɗa mata cewa Hon Maɗatai shine Alhaji Boɗejo dake cikin jerin mutanen da suke da hannun jari a kamfanin, kuma ta yi ƙoƙarin gano asalin mai kamfanin sai ka yi amfani da wannan damar wajan ɗakko photon mutane biyar ɗin dana faɗa maka, ka bincika mana asalin su" "Me ya sa kike so dole a amshi kamfanin?" Moh ya ce yana zare ido "Dole zan faɗa muku musamman kai, amma akwai lokaci kaɗan da abin da nake jira, ya zama dole mu kawo ƙarshen abin nan cikin wannan lokacin kun ji?" Suka yi shiru dukkansu kowanne akwai abin da yake tunani, Moh tunaninsa naga rikitaccen al'amarin can daya baro, ya san cewa gaskiyar abin da Muhammad yake neman sani ce idanu rufe, amma shi kansa ƙullin ya yi masa wahalar kuncewa, muryar Muhammad iri ɗaya data Kimiyya, shi kuma kamarsa ɗaya da Muhammad da Alhassan, again muryarsa ɗaya da Alhassan. Ya san cewa Maj Aliyu tunaninsa Muhammad ne shi, yanzu idan aka ce za'ayi gwajin jini ya zai yi?" Gyaran murya ya yi. Muhammad ya ce "Baka da gaskiya" Ya sake gyara muryar yana tunanin me zai ce domin maganar ta yi masa tsayi sosai sai ya ce "Iyayenka na raye" da rashin fahimta Muhammad ya ce "Iyayen wa?" Da yatsa Moh ya nuna Muhammad. Sai Muhammad ya yi murmushi ya ce "Ai sai iyayen mutum sun mutu ake kai shi gidan marayu, iyayena basa duniya" "Ok" kawai Moh ya ce. Muhammad ya juya gefe yana cewa "Amma me ya sa ka ce haka?" Sai ya ji shiru babu amsa, ya sake cewa "akwai wani abu daya faru ne?" Nan ma shiru babu amsa yana juyuwa yaga wayam, babu Moh babu tsohuwa Abbasa a wajan ya lumshe idanunsa da suka cika da hawaye, shi bashi da rabon ganin iyayensa a duniya haka ƙaddara ta wanzar da rayuwarsa kuma ya amsa ya san cewa ba zai taɓa mutuwa ba sai lokacin da Ubangiji ya iyakance masa na rayuwa a duniya. * A gidan Malam Abdullahi yau Ammo tun safe bata fito daga cikin ɗaki ba, ko motsinta ba'a ji. Malam ne ya shigo yana sababi hannunsa riƙe da butar da ya yi alwalar sallar asar tun ɗazo. Ya dubi murhu a bushe babu komai sai ya nufi ɗakin Mama Zaituna ya ɗaga labule ya ce. "Yau babu abin da aka samu ne? Ba abin da za mu sawa cikinmu?" Zaituna dake juya kwaki a kofi ta saka masa hashfatin data amso bashin na ashirin a maƙota ta cira kai ta kalli Malam kafin ta ce "Meka kawo balle mu ɗora?" Ta ce tana ɗauke kai kanta tare da miƙawa Zaituna kwakin gabanta ta ce "Sha, sai ki ɗora da ruwa" Malam ya ce "Ba shakka, sai na kawo za'a ɗora? Duk mene amfanin yaran dana tara da ba za su je su nemo ba? Kai Allah wadaran naka ya lalace ga yara mata can nata neman kai suna taimakawa iyaye amma nawa yaran basa neman albarka, kai Allah wadarai ni Abdullahi ina ganin tijararriyar rayuwa mara albarka" "A'a,kul! Kar ka fara kar ka soma yarana duka mata ne kar ka ja musu jarfa da wannan bakin naka na shiga uku, wallahi ba zan ɗauka ba idan kana ganin ka yi wa ɗanka baki ya bi duniya ni daidai nake da zamaninka wallahi, hakkin waye ya fita ya kawo a ɗora kowa ya ci? A wacce aya ko hadisi aka miji ya tanƙwashe ƙafafuwa yaransa mata su fita su nema masa? Ba burinka auri saki ba? Burinka tara yara babu tarbiyya babu kulawa banda Ubangiji ya rufa mana asiri ai da duka yaran ne zasu lalace mu shiga uku" Mama Zaituna ta dinga sababi ta ce "Ashe shi ya sa ake cewa ka yarda ta faɗar malam amma kar ka yadda da abin da yake aikatawa wallahi dai malam ka salala makaronin asara". Carbi ya ɗakko ya zai cauɗa mata ta yi saurin matsawa gefe. Ya kalli Saudat dake can gefe guda ta takure cikin hijjabi ya ce. "Saudala ƴar baba me zan samu" Da kumburarrun idanunta take kallon mahaifin nata, bata ce komai ba ta ciro ɗari biyu ta bashi, ya yi caraf ya amsa ya ce "Yawwa ƴar baba" bai tambayi ina ta samu kuɗin ba, tunda ba sana'a take yi ba, haka kuma bai tambayi mene dalilin kumburin idanunta ba ya baza riga ya fice daga cikin ɗakin. Saudat ta mayar da kanta ƙasa ta ci-gaba da kuka a hankali mai cin zuciya. Mama Zaituna ta ce "Saudat kukan nan ya fara damuna, na ce me aka yi miki kullum kina cewa babu komai, kukan yau daban na gobe daban, idan zama da yunwa ne idan da sabo ai kun saba" a hankali Saudat ta ce "Mama babu inda za ki nemo mini aikatau ne? Ko wanki ne ko shara da wanke-wanke ana biyana?" "Cab, Saudat shi kan shi wannan ai sai mutum yana da hanya komai na rayuwar nan sai da sanayya fa, da ina da hanyar samu da tuni na nema" Miƙewa Saudat ta yi, ba tare da ta ce komai ba ta nufi waje tana goge idanunta zuciyarta na mata zafi. Ammo bata ji shigowar Malam ba, sai ganinsa ta yi kawai a kanta, sai ta yi sauri ta ɓoye abin hannunta ya dube ta ya ce "Na ce miki aure zan yi ko? Idan kin girka wani abu kuma ki zuba mini kin ji?" Bata kula shi ba ta bawa banza ajjiyarsa. Ya daka mata tsawa ya ce "Ba dake nake ba? Daman kin fara isata wallahi zunubinki ya ja mana komai, da halin muke ciki" Ya yi ƙwafa ya ce "Daman saura igiya biyu na aurena da yake kan ki, zan tsinke sauran ki fita ki yi naki wajan, kin san Allah ne gatanki a duniya sai ni Malam Abdullahi, ba ki da inda ya shige gidana zama dani dole" "Idan ka sake ni sai me?" Ta ce tana miƙewa tsaye, idanunta yayo waje tana jifansa da wani irin hargitsatstsen kallo, sai gabansa ya faɗi saboda abin da ya fara hangowa a cikin idanunta, a hankali tausayinsa yake warware daga cikin idanunta, tsana ta maye gurbin so da tausayin da take nuna masa tsayin shekaru, dukkan wani hijabin kunyar dake tsakaninsa da ita ya kau daga cikin idanunta, wannan kyautatawar babu, wannan tausayin babu, wannan biyayya da alkunyar babu, wannan soyayyar da mace kewa mijinta gabaɗaya ya kau daga cikin idanunta. Bugawar da zuciyarta take yi ta cikin ƙirjinta a dalilin malam babu, soyayyar da ta yi mata ƙatutu da ƙawanya a zuciya yanzu ta marmashe ƙirjinta ya yi mata wasai, soyayyar ta zama murgayya. Ta matsa dab da shi ta ce "Idan ka sake ni, na ce sai me Abdullahi? Ko kana tunanin zan mutu ne? Kana tunanin ba zan iya komawa wajan dangina bane? Wallahi ba aurenka a kaina baya gabana bai daman ba" "Ni kike faɗawa haka?" Cikin ƙaraji ta ce "Na faɗa, waye kai? A kayan miya wane Abdullahi? Ni wacce na buɗe ƙofar wulaƙantani da cin zarafina na gaza gane cewa daman haka halin maza yake, mace zata ja namiji inuwa idan ya tashi gwanya mata ya kai ta cikin tsakiyar rana mai azabar zafi, ya ɗora mata garwashin azaba, na yi ladama na yi dana sani, i regretted it, regretted everything, wallahi na tsanai kai na i failed as a mother,I failed as a daughter....," Sa'adah dake bakin ƙofa ta yi cak, jin turanci na fita daga cikin bakin Ammo, turanci bana wasa ba, tana wani acting like a queen, muryarta na fita saɗara bayan saɗara ta ce "Kai ba masoyi ne bane mugu ne, kai ba malam bane shaiɗani ne, naga irin naku riƙon auren na Hausawa DAMA SUN FAƊA MINI, na ɗauka cikakken mai hankali na aura, Malami musulmi wanda zai tayani riƙe amanar da Ubangiji ya ɗora mini na yara, zai taimaka mini wajan gyara kuskurena ashe ANA MUSLIM na aura, ashe mugu azzalumi na aura, wanda bai san darajar aure da hakƙin da yake cikin shi ba, bai darajar yaran da Ubangiji Ya azurta shi da shi ba, wallahi Allah Ya...," Sai ta yi saurin yin shiru kawai tana buɗe hannunta ta ce "Enough is enough, I'm scarred,na gaji na gaji" Ta ce idanu cike da hawaye. Cikin sauri Malam ya ɗaga hannu zai mare ta, kafin ya ƙarasa Ammo ta sauke masa lafiyayyun maruka a fuskarsa sai kuma ta yi baya tare da durƙushewa saman ƙafafuwanta ta rushe da wani irin raunataccen kuka tana cewa "It's over, between us" Sa'adah waje ta yi itama tana kuka sosai kamar ranta zai fita, hankali tashe babu abin da yake bata mamaki da ɗaure mata kai jin turanci a bakin Ammo, duk yadda suke so da ƙaunar karatun book ashe ta iya ta yi musu burus bata ko ganin gabanta a haka take tafiya idanu cike da hawaye. * I. Qasim kimiyya ne tsaye cikin ɗakin asibitin hannunsu riƙe da baby boy ɗin dake cilla ƙafafuwa gwanin sha'awa suma fal kan yaron, ya dinga jin so da ƙaunar babyn a zuciyarsa, a hankali ya kalli macen da take buɗe ido da ƙyar,data ga haske take rufe ido ita haryanzu bata yarda cewa ta zo duniya ba ta takure jininta waje guda cikin lallausan shawel ɗin da Qasim ya siyo sumarta har wajan goshi,a duk sanda zai ɗauki yarinyar fargaba ce take cika masa zuciya da tsoro ya rungometa a jikinsa ya ce "Matsoraciya, kar ki yadda ya fiki wayo" ya ce idanunsa cike da hawaye. Ya daɗe ciki kafin ya ajjiye su kusa da mahaifiyarsu wacce har yanzu bata motsa ba, kullum abu ɗaya * Paaahh ya kalli Zahiyerh kafin ya ce "Junaid ya ce kina nema na" Ta jinjina kai, bata kalle shi ba ta ce "Faɗa mini komai na abin da ya faru da Maamah, completely" Ya yi shiru yana tunani bai sani ba ko zata fahimta ko kuma zata gasgata shi? Wannan dalilin ya sa ya kasa magana sai ta ɗago kanta daga saman wayarta ta ce "Abdul-Johar" "Afuwa Zahiyerh" Ya gyara zama ya ce "Kamar yadda kika sani sanda Safiyyerh ta kammala primary school ɗinta na yi ƙoƙarin ganin mun koma ƙasar waje ta yi karatu secondary school a can, amma ta kafe ta ce dole ita a Nigeria za ta yi karatu a nan ɗinma akwai makarantun masu kyau, kuma a Nigeria aka haifeta me ya sa zata gujewa ƙasarta? Daga baya na fahimci ashe dalilin wata ƙawarta ko na ce aminiyarta ya saka Maamah ƙin ƙasar waje, ta kafe ta nace naje wajan mahaifin yarinyar kin ma santa ai Safiyyerh sunanta, na buƙaci ya bani dama na haɗa Safiyyerh da Maamah na kai su ƙasar waje karatu, sai ya nuna rashin amincewar hakan bai kamata ba, na faɗawa Maamah kin san yaro duk sanda ka yi ƙoƙarin yi masa abin da baya so sai an samu matsala, na yi tunanin ko ta je ƙasar wajan ba lallai ta yi karatun ba, na ce ta zaɓi makaranta sai ta ce Fgc na cike komai ta fara zuwa, kullum tana ɗaukan first position, amma sai ta sauya result ɗinta dana Safiyyerh ƙawarta, ta kawo mini matsayin ta ɗauki 2nd position,a tunaninta ban sani ba, ta manta cewa da handwritten ɗinta dana ƙawar ba ɗaya bane, ban damu ba, domin na san a information na makaranta dole ita ce a gaba, a haka ta yi jss 1 da 2 duk hutu bama yi a ƙasar. Kwatsam sai ta zo mini da zancen wai taga wani yaro tana son shi, don Allah na aura mata shi, na ce ya sunan yaron ta ce bata sani ba, sai na ɗauki maganar a shashanci, a take kuma ta ki ai Maamah bata taɓa zuwa da magana makamancin hakan ba, tabbas da gaske take magana ɗaya take yi, gudun kar ta saka soyayya a ranta ya sa na yi saurin ce mata na amince amma sai ta yi first graduation,ta kawo first certificate ɗinta, a ranar kuma zan yi maganar aurensu amma da sharaɗin kar ta yadda ta bari yaron ya gane yana son ta, kuma kar ta sake yi mini maganarsa, she agreed and she accepted, a lokacin ta ce tana son zama kamata na ce kowa zata zama. Bayan haka kullum tana cikin rashin lafiya sai na ɗauka ko ciwonta ne, bata taɓa ce mini ga abin da yake damunta ashe ciwon soyayya ne ban sani ba. Har na gaji na ɗauke ta muka bar ƙasar, a can komai ya lalace ta kasa dauriya duk da tsananin tawakkalin Maamah, yanzu za ka yi mata abu yanzu zaka manta, soyayya a lokacin ta ci ƙarfinta duk da bai kamata a wannan shekarun ace ta faɗa soyayya haka ba, lokacin ƙuruciya ce matakin teeganer, na gaza tunanin cewa a lokacin adolescence stage yara sun fi ɗaukan abu very serious ta zaɓi da kuma sanyawa a rai, kuma ban taɓa kawowa har yanzu yaron yana zuciyarta ba. Ranar data zo mini tana kuka akan ina alƙawarin da na yi mata, sai na ce ba gaskiya bane, wasa nake mata domin ta nutsu ta yi karatu, ba har zuciya ba, kuma ko babu haka aure ita da yaron ba zai yiwu ba, saboda na yi alƙawarin aurenta da ga Ashraf ɗan wajan Sharfaɗi asalin sunansa Alhassan tagwaye ne shi. Kuma idan har ni na haife ta kar ta sake yi mini maganar wacan yaron, ta yi mini biyayya. Again she agreed, she obeyed, bata sake yi mini maganarsa ba, kullum zata nuna she is ok bata da damuwa, ashe idan ta ware kanta kuka take yi, zuciyarta kullum cikin ƙunci take damuwa ashe har sadaƙa take yi Allah ya yafe mata, amma tana da sanya abu, ta kasa controling na zuciyarta, ashe damuwa ya yi mata illa mun ɗauka aljanu ne ma da ita, ban taɓa nutsuwa na fahimci cewa cutar damuwa depressed ne ya kamata ba, saboda ina zarya daga ƙasar da muke zuwa Nigeria akan wani case da nake dubawa. Ta fara zuwa makaranta ashe bata ma zama a makarantar ta haɗu da wata muguwar ƙawa, ta fara bata maganin shaye-shaye da yake sata baccin da take kasawa, ina da tabbacin da a zahirin kwalbarsa Maamah taga maganin ba zata sha ba, sai ƙawayar ta yi amfani da lemo wajan bawa Maamah, na san Maamah ta son abin kwaɗayi ban kawo wani abu ne a cikin lemon ba, a haka har ta saba da sha, daga nan abubuwa suka faskara ta dinga ihu tana cewa zata mutu ga mala'ikan ɗaukan rai nan, sai na fara rufe ta a ɗaki, har lokacin kuma bata faɗa mini cewa akan yaron bane, kwatsam watarana muka nemi Maamah a ƙasar da muke muka rasa, daman a lokacin ta tsani a dinga ce mata Safiyyerh sai Aafiyyah haka dai muka fi ra'ayinta...," Paaahh ya yi shiru, kan shi a ƙasa idanunsa jawur kamar yanzu komai ke faruwa. Ummimi kallon Paaahh take yi da wani irin expression looking daga cikin idanunta. "Abdul-Johar" Ya kalli Ummimi ya ce "Ashe lokacin ne mafarin ƙaddarar Maamah, ban san cewa ƙaunar da nake yi mata ta yi girman haka ba, sai dana wayi gari naga bata tare dani, yanke jiki na yi na faɗi, nan take Ummi hawan jini ya kamata har ya nemi kashe mata idanu, na fara nemanta ido rufe, har Nigeria na koma babu Maamah. Abin da ya bani mamaki bincike daya nuna mana cewa tana Lagos, a Lagos ɗin muka sameta cikin jini an caka mata wuƙa an yi mata fyaɗe, Ubangiji ne ya ƙaddara dani da ita zamu cigaba da rayuwa, na karaya sosai, ban taɓa jin cewa za ta yi rayuwa ba, na san dai hakan ƙaddararmu ce da kuskure na, na yi mata al'ƙawarin dana gaza cikawa. A lokacin na samu ciwon zuciya har yanzu kuma matata da yarana babu wanda ya sani sai yanzu dana ke faɗa miki. Mun jima a asibiti hankalinta ya tashi jin cewa an yi mata fyaɗe, ita bata san ya aka yi ta tsinci kanta a Lagos ba, tun kafin mu bar asibitin ciki bayyana a jikin Maamah hankalina ya sake tashi, ciwon zuciyata ya kuma tsananta ya kai matakin da ba lallai na iya cigaba da rayuwa ba, a haka muka tattara na nemana gida a Germany muka zauna, na tattara yaran na yi musu bayanin komai banda Aliyu domin yana can wajan aikin soja, Junaid muna tare da shi always, Hashim da Awais suna karatu, na ce kar na sake na ji maganar a bakin wani, kuma da ace na san wanda ya yi wa Maamah fyaɗe ko komai nawa zai ƙare muddin yana raye wallahi sai na ɗauki mataki a kan shi, ko a yanzu ban haƙura ina ta addu'a kullum ina bada sadaƙa. Bamu faɗa mata tana da ciki ba sai sanda ta fara jin motsi a cikinta, dake cewa ita dai maciji ne a jikinta, domin tattara ta mance maganar fyaɗe bama taɓa yi mata maganar hakan, a lokacin nakan ce mata shikenan wata zata haifi maciji, sai ta fara kuka ta ce tana shiga uku mutuwa za ta yi, ko bacci take yi cikin ya motsa sai ta fara ta sakko ƙasa tana ƙwala mana ihu da kiran sunan mu, ciki bana halak ba, amma kyawun da ta yi a lokacin ɓata baki ne, gashi yaro cikin ƙoshi lafiya yake, da ina da iko zubar da cikin zan yi wallahi, Ashraf ya amince zai aureta haka saboda yana son ta sosai, sai na fara tunanin komawa Nigeria muka gama shiri tsaf, a nan nake cewa ai ciki ne da ita haihuwa za ta yi, ga mamakina sai naga kamar fuskarta ta faɗaɗa da murmushi, murmushin da har yanzu na gaza gano ma'anarsa har muka sauka a Nigeria kuma Kano bata sake cewa komai ba, ni da ita motar mu ɗaya, sauran kuma motarsu daban, hanyarmu ta zuwa gida daga airport Ubangiji ya saukar mana da mummunan hatsari, wanda ya yi sanadiyar da ya saka Maamah ta yi loosing memory, tunaninta na baya ya goge daga cikin ƙwaƙwalwarta, a lokacin data farka da naje wajanta cikin idanuna ta kalla ta ce Who are you? Hankalina ya tashi sosai fiye da sosai sai na sake yanke jiki na faɗi, babu wanda ta iya ganewa cikinmu a lokacin kuma Dr Hash ya yi mata aiki, kafin a fito da ita ma daga ɗakin operation ɗin na ɗauke ta muka bar asibitin, a gida aka gama yi mata treatment, na ce nine mahafinta kowa na faɗa mata matsayinsa har ke da Aliyu, sai na ji daɗi Ubangiji ya kawo mana sauƙin abin, ta manta komai a har makarantarsu na nuna mata Kinal na ce ƙawarta ce bayan na gargaɗi Kinal ce, haka na nuna mata class mate ɗinta Kimiyya na ce abokinta ne sunansa Qasim kuma duk ta yarda a lokacin muka daina ce mata Aafiyyah sai Safiyyerh, lokacin kuma na fahimta lossing memory ɗin ba mai nisa bane, sai ka buƙaci dr hash yana yi mata allura wannan dalilin ya saka duk sanda ta yi yunƙurin tunawa sai a yi mata allura, lokacin na samu damar cika mata muradinta da take cewa tana son zama kamata, na fara bata horo a ɓoye na musamman kuma ta fara online classes ɓangaren business ta ƙware sosai akan harkar kuɗi, sai Sharfaɗi yazo da buƙatar ɗaukanta aiki a Company kuma matsayin Manager ban yi musu ba domin ai ɗansa zata aura" Shiru ya yi alamar ƙarshen maganar kenan sai Ummimi ta ce "Ina yaron data haifa? Mene amfanin rabata da shi? Duk wahalar data sha ta haifo amma duk bata san cewa tana da yaro a duniya ba?" Ya yi shiru. Tana ƙoƙarin magana AA MAJ ya shigo ya ce "Sai ka faɗa mini waye shege tsakanin ni da Maamah, waye ba ɗanka ba?" Paaahh ya kalli Aliyu, sai kuma Aafiyyah ta shigo bata ji komai ba sai maganar Aliyu don haka ta ƙarasa kusa da Maj ta tsaya itama tana kallon Paaahh kamar yadda Aliyu ya tsare shi da idanu ta ce "Paaahh don Allah ka faɗa mana waye ba ɗanka ba?" Sai ya yi murmushin takaici yana miƙewa tsaye ya juya baya ya ce "Ko baku tambaya ba, yau na shirya zan faɗa muku waye ɗana a cikinku waye kuma bani na haife shi ba" Ummimi ta miƙe da sauri ta ce "Ka kar soma Abdul-Johar ban goyi bayan ka faɗa musu gaskiya a yanzu ba" "Me ya sa?" Junaid asked yana shigowa cikin parlourn. Dr Hash da Awais ma suka shigo haka Ummi. Itama Ummi kuka ta fara ta ce "Don Allah Dig ka yi shiru da maganar nan, ka bar maganar nan kar ka faɗa " Dai Paaahh ya yi murmushi ya ce "Me ya sa? Bani lokacin, kwanakin da suka rage mini a duniya kaɗan ne, kuma baku san komai ba, idan na mutu ban faɗa musu gaskiya ba ya kuke so na yi da hakƙinsu dole na faɗa" a gigice Ummimi da Ummi suka yi kan Dig Johar ganin yana tarin jini "I most telling you the truth, time is not our side ba wani lokaci" "No please, babu abin da zai faru ka yi shiru ba sai ka faɗa ba don Allah" Cewar Ummi tana riƙe Paaahh sai kuka take, Aafiyyah tuni hankalinta ya tashi ta gigice jikinta ya fara rawa da ɓari sai ajjiyar zuciya take saukewa ta kasa yin kuka, AA MAJ ne ya kama hannunta ya damƙe cikin nasa. Junaid ya ce "Daddy ka faɗa mana gaskiya muma mu fita daga cikin shakku da kokwanto" "Junaid zan faɗa zan faɗa" Sai ya yi kasa da kai a hankali kuma ya ɗago ya kalli AA MAJ ya kalli Aafiyyah sai ya ce "I am sorry, ba kowa bane wanda bani na haife shi ba a cikin ku face.............. 💥Chapter 10: The Evidence "Aliyu shine wanda ba ƙwayar haihuwata ya samar da shi ba, Aliyu ne wanda ba jinina ke gudana a jikinsa ba, Aliyu ne wanda ba fito daga cikin tsatsona ba, Aliyu ne wanda na rufewa duniya asalin matsayinsa da nasabarsa ga Marafa family, Aliyu is not my son, but he is blessing to me, ya yi mini abin da ko jinina ba zai iya yi mini ba, ya yi mini biyayyar da ko su Junaid sai haka" ya yi shiru da maganar, yana jan numfashi a hankali kuma ya juyo gabaɗaya yana ƙarewa kowa dake cikin parlon kallo, musamman Maamah domin ya kasa kallon direction ɗin da Maj yake tsaye, muryarsa na ɗan rawa duk da dauriyar da yake da ita ya ce. "Is that what you want?" Ya ce a hankali. "Shikenan shikenan. Na faɗa muku gaskiya, gaskiyar da nake son a binneta a nan wajan kar na ji komai a waje, jininka wuya za shi" Ummimi ta ce "Sai dai, gurbin ido, ba idon bane Abdul-Johar" "What do you mean? Kina son daƙile Aliyu daga kallon uba da yake mini ne, saboda kin san kina da ikon hakan, kina son farraƙa tsakaninmu Zahiyerh? Haka kike so?" "Ko kaɗan, ban taɓa barranta Aliyu da kai ba, ka sani abin da ka yi zunubi ne ba kuskure ba, kar dokin zuciya ya jaka zuwa turbar halaka Abdul-Johar ka gyara wannan shaci-faɗin naka, ka yi ƙoƙarin lashe aman da ka yi domin anyway ban ga alfanu da tasirin wannan abin ba" ta ce idanunta jawur har yanzu kuma ta kasa fidda hawaye, abubuwan da suka yi mata tsaye a zuciya idan ta ce kuka za ta yi musu to akwai buƙatar ta ajjiye bokiti domin tissue ko hanky ya yi mata kaɗan wajan tare gudanar hawaye daga cikin idaniyyarta, bata isa ta iya kaucewa wannan cukurkuɗaɗɗiyar ƙaddarar, she believe in fate, ta kuma yi accepting hakan a matsayinta na cikakkiyar musulma, cikar imanin mutum shine, yar da da ƙaddara, bata son dai kawai Abdul-Johar ya yi ladamar abin da ya aikata, domin hakan kamar an kashe maciji ne ba'a sare wuya ba, bata so buɗe gaskiyar ta wannan hanya da tsigar ba. Maj tunda furucin Paaahh ya sauka a kunnensa ya ji bugun zuciyarsa ya tsaya na shuɗewar wasu daƙiƙo, shuuuu! Shuuuu! Shuuuu! Kamar saukan ruwan sama haka yake jin sautin amon muryar Paaahh, sai ya ji wani sanyi a gaɓɓansa, sai ya ji nutsuwa, nutsuwarsa data saukar da rauni a zuciyarsa mazan jiya. Hamdala, ya yi a zuciyarsa ya godewa Sarki Ubangijin talikai, daya wanzar da gaskiya a kan shi, ba'a kan ta ba, damuwar da zai shiga idan ya kasance Maamah ce ba jinin Marafa family ba, ya fi gaban kwatance, wani miki ne wanda kan iya zama maroro a zuciyarsa mai wahalar samun magani. Daɗi, farinciki, gamsuwa, nutsuwa, sune suka mamaye shi, da maye gurbin wasu-wasi da taraddin da zuciyarsa take ciki, amma hakan bai hana ɗaya zuciyarsa faɗa masa tare da tambayarsa cewa; "Waye mahafinka Aliyu?" A fili kuma Junaid ne mai ƙarfin halin cewa "Waye mahaifin Yaya? Me ya sa aka rufe mu, mene dalilin ɓoye gaskiya, wanne irin hali kuke tunani Yaya zai iya shiga? Haba daddy!" Paaahh ya juya ya kalli Junaid sai ya jinjina kai ya yi shiru, a hankali kuma ya ƙarasa zuwa gaban Maj, ya miƙa hannunsa ya riƙo na Aliyu, cikin kwantar da murya ya ce "Kar ka hau majajjawar son zuciya,ta ingiza ka zuwa tubalin danasani, komai ya faru da Ɗan'adam, Ubangiji ya rubuta faruwar hakan a zanen allon lauhil Mahfouz, alƙalamin da baya taɓa rubutu ƙarya. Aliyu, kar ka karaya kar ka ji kamar bani da iko da kai, kar ka ji kuma kamar kai ba daga jikina ka fito ba, ka ɗauka Ummi ta yi dakwan cikinka, kuma ta yi naƙudarka, ka cigaba da kallon mu matsayin one big family, we love each others, support, care don Allah kar ka bari ia raunata. Hashim, Junaid, awais duka ƙanenka ne, babu wani tarihi da zai sauya hakan...," Paaahh ya tsahirta da maganar, sai juya ya kalli Maamah, dake tsaya ta kasa motsi sai rarraba idanunta take yi fuskarta ta yi jajur musamman karan hancinta hakan ya nuna tashin hankalinta a fili, jikinta sai rawar yake yi,kamar wacce ake tsaka da busawar hunturun sanyi ko gittawar jaura, gaf gaf gaf haka fararen haƙoranta suke haɗe kansu waje guda, suna bada sauti kamar jinin turawa haka take acting ta kasa zama waje guda, sai jujjuya kanta kawai take yi, tana fesar da iska daga cikin bakinta, data lumshe idanunta irin samun nutsuwa sai kuma ta buɗe idanunta, da sauri. Ya kamo kyakkyawan hannunta, ya damƙa a hannun AA MAJ. "And you have Maamah, na bar maka Maamah duniya da lahira, na baka ita halak malak, ka ɗauke matsayin komai na rayuwa, kamar yadda ta nuna mini kai ne inuwar data gamsu ta shaƙi iska a cikinta" ya ce a nutse. "Huhhh...!" Ta fitar da iska daga cikin bakinta, idanunta na cika da hawaye. "Yes Aliyu, Safiyyerh ta rubuta cewa kai ne next of kin ɗinta tun kafin na san cewa ƙaddara zata iya haɗaku aure. Na je kamfanin da take yin aiki, a lokacin da aka sace ta, na je wajan Alhaji Baihaƙi Sharfaɗi, Ceo na Fs world, da burin ya bani ya bani gabaɗaya hannun jarin Safiyyerh, sai ya ce me zan yi da dukiyar Safiyyerh? Ko saboda bata nan tunina za'a kashe ta, shine ya saka zan amshe dukiyar yarinyar? Sai na ce masa, what ever Sharfaɗi kuɗi kawai nake nema dole ka bani, sai ya nuna sam ba zai bayar ba, idan ma zai bayar sai an yi cike cike, shima idan ya tabbata cewa Safiyyerh ta saka sunana matsayin next of kin ɗinta, unfortunately, sai aka sakko file ɗinta, unbelievable na ce a zuciyata ganin sunan Aliyu Abdu Marafa matsayin next of kin ɗinta, ba ƙaramin jinjina wa basirar Safiyyerh na yi ba, kowa ya san basa ga majici, kamar Annabi Musa da fir'auna haka suke rayuwa, babu wanda zai kawo cewa zata saka sunan Aliyu. A lokacin shocked ne ya kama ni, at the same time kuma farinciki, reaction ɗina sai ya nuna wa Sharfaɗi kamar ban ji daɗi ba. Ni kuma na yi acted da misbehave like ban damu da rayuwar da Safiyyerh ba, at that time, na san cewa Eng Ali wali zai iya neman information, wannan dalilin na yi saurin daƙile hakan" Ya shafa kan Aafiyyah ya ce "Ina alfahari dake Safiyyerh Abdul-Johar Marafa, ke kyauta ce daga Ubangiji" Ya damƙe hannunta dana Aliyu ya ce "Don Allah ku so juna, ko ƙaunaci juna ina buƙatar ganin jikoki daga gare ku Aliyu, kafin wa'adina ya yi" "Daddy!" Aafiyyah ta ce, very loudly. Tana girgiza kan ta, ta yi saurin saka hannunta ɗaya tana rufe bakinta da hancinta saboda kukan dake shirin ƙwace mata. Paaahh ya yi mata murmushi ya ce "Of course, of course" Ya ɗora da "Ina son ganin ƴan dagwai-dagwai ina son ganin jininki don Allah Maamah, ki mini wannan alfarmar favourite, autar Abdul-Johar" jikinta na rawa ta zame hannunta daga na Maj ta faɗa jikin Paaahh, jinta a jikinsa ya saka ta saki wani irin kuka, jikinta na rawa da kyarma idanunta ruf, bata gani, ƙafafuwanta suka gaza ɗaukan jikinta, luuu! Ta ja Paaahh ƙasa zuwa saman haɗaɗɗan Italian carpet ɗin dake shimfiɗe a parlourn, suka durƙushe da shi, da ita, wani irin gunjin kuka take kamar wacce komai ya ƙarewa a rayuwa ta ƙanƙame Paaahh tana girgiza kai sai kuma ta fara fitar da numfashi da ƙyar. "I am sorry daddy, i am sorry daddy ka yafe mini ka yafe mini don Allah" "Me ki kai mini?" "I don't know, na ji kamar a rayuwa na taɓa maka rashin kyautatawa ka yafe mini saboda darajan shugaban halitta Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallam, ka tauysawa ka yafe....," her voice was sharking, fuskarta ta jawur ta riƙe Paaahh sosai. Sai ya yi murmushi yana danne ciwon da zuciyarsa take yi masa ya ce "Ba ki yi mini komai ba, idan ma kin yi kuskurena ne, na kuma ya fe miki" "Oh, i promise you, i promise you i won't do that again" Sai ta riƙe cikinta ta shafa da kyau, sai ta yi shiru thinking kamar ta taɓa ajjiye baby a cikin nata da sauri ta ce "zan haihu, zan haifa maka grandchildren masu kyau Paaahh, in sha Allah Safiyyerh za ta haihuwa Daddy, zan haihu" ta ce hawaye na bin fuskarta jikinta na rawa. Da sauri J ya juya ya fita, zuciyarsa na ingiza shi zuwa ga faɗawa Maamah gaskiyar abin da ake ɓoyewa mata, how long za'a ɗauka ana rufe wannan abin? Idan Maamah ta mutu ba tare data san cewa tana da ɗa a duniya ba, mene ribar su? Me za su faɗawa Ubangiji wajan raba uwa, da ɗan da bata san ta haife shi ba? He can't take it anymore, wannan secret ɗin yana ƙoƙarin tarwatsa masa zuciya. Wannan dalilin ya saka Paaahh haɗa auren AA MAJ da Maamah, saboda a yi dakan ɗaka, tuwona mai na, tunda da ruwan ciki ake jan na rijiya, shi zunubi romo ne, ƙirjin mutum kuma hijabin sirrinsa. Dole watarana Aliyu ya goranta wa Maamah cikin shegen da ƙaddara ta sanyata yin shi, domin kamar yadda Ummimi ta faɗa ne, gurbin ido, ba idon bane, Aliyu idan bai samu budurci daga wajan Maamah ba, that means he gonna divorce her immediately? “No!” Junaid ya ce. Awais ma bayan J ya bi zuciyarsa a dame, da tunani ashe kallon biri a kewa rogo, ashe Maj ne ba jinin Paaahh. Dr Hash ma fita ya yi, domin daman a ganiye ya dawo gidan saboda operation ɗin da ya yi. AA MAJ ma a sukwane ya juya zuwa sashinsa dake cikin gida, Ummimi ta sulale saman kujera ta zauna tana dafe kan ta, Ummi kuma har yanzu kuka take yi bata san da wanne idanu zata kalli Aliyu ba. On the night. Juyi kawai Aafiyyah take yi, kan ta na yi mata wani irin ciwo sosai, yanzu bata iya tunanin komai bacci take yi sosai, Ummimi ta hana yi wa Dr Hash yi mata allura wannan dalilin ya saka Dr Hash bawa Dr Hamza alluran, shi kuma dr Hamza ya kwashe alluran ya basa Dr I. Qasim kimiyya ya sauya su da wasu na ƙarin lafiya. Wayarta ce ta fara ringing kamar ba zata ɗauka ba, sai kuma ta janyo wayar idanunta rufe ta ɗaga muryarta can ƙasa ta ce kamar dole Ta ce "Assalamu Alaiki" "How are you Safiyyerh?" "Allahamdulillah. Kinal" Kinal ta ce "Lafiya kike kowa? Your voice....," "No, lafiya nake ya sana'ar ƙarya wacce ƙarya kike shimfiɗawa kuma?" "Uhm, hahahaha" Kinal ta yi dariya ta cikin wayar ta ce "Ba ko da kirki sam, sana'ar tawa ce ƙarya ya miki kyau" Luuu! Aafiyyah ta lumshe idanunta ta buɗe tana yi farfar da su ta ce "Of course, waƙa dai ƙarya ce, dani kikaiwa waƙar ma, daba kwaɗo ba in ji gaya wallahi" Kinal ta ce "Yaushe kika ji Hausa? Abin mamaki, na ji mamaki" "Kinal Aberdeen Awaya kenan, kina wasa dani ne kodayake ai an ce al'ƙalamin ya fi takobi ko?" Kinal ta ce "Ƙwarai ma kowa ta wajena matar soja mazan fama" "Faɗi da ihu ki ƙara da wai, yarinya Safiyyerh matar mijinta Aliyu" Wani ihu Kinal ta buga ta cikin wayar "wayyoo, unbelievable. Yaushe hakan ya faru? Wait daman kina son shi ne Aafi.... Safiyyerh? Do you love him" Aafiyyah ta yi shiru, can ta ce "Na taɓa ce miki na tsane shi ne? komai a rayuwa jarrabawa ce in ji Daddy. Bamu muke faɗawa soyayya ba, so ke faɗawa kan mu da sarƙafe zuƙatan masoya waje guda, har suka dinga jin inda babu juna ba za su iya rayuwa ba, so akwai daɗi matuƙa ban fahimci hakan ba sai dana rasa Ashraf. So gaskiya idan ka yi dace da masoyin ƙwarai, so azaba ne idan ka kamo da son masu wani, Ubangiji kan yi azaba da iya so" ta ce with full of emotional. Kinal ta ce "Oh Allah! Sannu malamar soyayya" "You're mistaken, kin san i love reading English novels akwai favourite writers ɗin da nake following stories ɗinsu on wattpad, so na san abubuwa da yawa akan so. Allah yana gani ina son kulawa a soyayya, ina son a nuna mini so, ina son a nuna an damu dani... And ina son romantic guy haka, kin san irin mijin da nake so ai, na faɗa miki, ni bani da wata kunya ga abin da zuciyata ke so, kuma wanda zan rayu da shi har abada no" "Wanne kalar miji kike so?" Kinal Asked muryarta ɗauke da fara'a. Aafiyyah ta ce "Bawai don ina karanta novels ba, shi kin san creating ideas ne, but most of the time can be reality. Kamar wani littafi dana karanta ANA MUSLIM na yi kuka sosai, na yi baƙin ciki sosai, akan so mace ta yi Ridda daga Muslunci uhm. Ina son namiji miskili, wanda idan na ce kai, zai ce ke, wanda gangar jikinsa zata nuna abin da yake zuciyarsa ban damu da cewa i love you ba, wannan duk yayin da ne, reality nake son a nuna mini, bana son mutum wanda aka raina shi koyaushe tsare gira, ina son baƙin namiji sosai kinga ni yanayin kalar da Ubangiji ya yi mini" "Uhm haka ne. Gashi kuma Soja fari ne ya za ayi kenan?" Aafiyyah ta ce "Haka ƙaddara ta zaɓa mini, daman imagination ne, mafarki kuma bai taɓa zama gaskiya, abin da kake so daban abin da Ubangiji yake baka daban, i love Maj" Jira suka cigaba da yi saboda yau ƴan mutumcin Aafiyyah suna kan ta daga ƙarshe ta ce "Ɗan cillo mini waƙar soyayya da WhatsApp kin motsa mini zuciyata Allah zai saka mini" "Hehehe ke da kike da miji?" * The following weeks. Aafiyyah bata sake saka idanunta akan AA MAJ ba, ashe baya ma Kano ya je Abuja ne, ta dinga tunanin kiran shi amma ta kasa to ta ce masa me?. Tana zaune a office ɗinta a hankali take juya kujerar da take zaune hannunta ɗaya ta dafe haɓarta ɗayan kuma tana danna laptop, ƙafarta ɗaya kan ɗaya flat shoe ne a ƙafarta mai igiya ya fiddo da farar ƙafarta simple bubu ta saka mai faɗi sai siriryar sarƙa a wuyanta mai ɗan ƙaramin stone. Hannunta ta miƙa ta ɗauki fanice ɗin data saka aka kawo mata a hankali tana sha tana duba abin da aka tura mata. Ƙarar buɗe ƙofa ta ji, sai ta yi mamaki waye zai shigo mata kai tsaye? Ranta a ɓace ta ce "Out of my office" Ba'a amsa ba, kuma ba'a juya ba, ranta a ɓace ta ɗago tana cewa "Wanne hauka ne wannan da....," haɗiye sauran maganar ta yi, sanda idanunta ya yi arba a kan shi, yana tsaye saman digadigansa biyu, tsaiwa irin ta cikakkun maza wanda koyaushe a shirye suke da ko ta kwana, hannunsa zube cikin aljihu, wando ne iya qwwia a jikinsa sai t.shirt a jikinsa wacce ta kama jikinsa sosai, damtsen hannunsa da buɗaɗɗan ƙirjinsa six pack na jikinsa ya bayyana, ya rarrabe musamman brest ɗinsa, ya rufe fuska da facemask sai wata p.cap daya saka. Wani waje can yake kallo kamar baya son kallon ta. A hankali ta sauke ajjiyar zuciya a ɓoye tana miƙewa tare da komawa saman 3seater ta zauna tana harɗe ƙafarta "Na san sai kai musulmi ne, da zaka shigo babu sallama ba haka Maj ya baka tarbiyya ba ok" Still bai motsa ba, bai kalle ta ba, walking majestically ya fara zuwa wajan windown office ɗin, a bank ya ɗan leƙa lullumin hadari ne ƙasa-ƙasa da yake haɗuwa saman gajimare iska mai daɗi na kaɗawa, iskar ta bashi damar tuna besty da yawan lokaci cikin dare yana tarfata tana kallon sama sai ya dinga murmushi idan ta ji iska na kaɗa ta. Ya rufe ido ya buɗe yana sake kallon girman kamfanin yama manta office ɗin wata ya shigo. Aafiyyah ikon Allah kawai take kallo, tana kuma bin bayansa da ido ganin duk motsin da ya yi sai hannunsa ya motsa asalin American guy. "Idan Maj ya baka saƙo ka faɗa mini and leave my office" Moh ya ji muryar Aafiyyah raɗau a kunnensa ya yi jim, sai ya juyo ya kalle ta, a duk sanda zai kalle ta ya kan ji cewa inama ya ƙarasa kashe ta? Gently yake tafiya ya zaga zuwa kujerar da yake zama ta matsayin Manager, ba ki ta buɗe sosai ta ce "Hy Blackman, office ɗin Manager kake fa, ka san wacce ni?" Ya ji ta, ya share, laptop ya janyo ya fara danne danne kana ganinsa ka san cewa ya kware wajan dannawa, sai ya yi tsaki kuma yana jin idanunta na yawo a kansa ya saka hannunsa ya a aljihu ya fito sigari da leta ya kunna, baki Aafiyyah ta saki saboda mamaki, a tunaninta ta ce daman haka Muhammad ɗin yake mara tarbiyya? Ɗan shaye-shaye? Ga wata shegiyar izza ta girman kai, ya zame facemask ɗin zuwa ƙasa a hankali ya dinga zuƙar sigarin yana fesar, ta zuba masa ido kamar mai study ɗin shi. Bayan ya gama danne danne sai ta ji wayarta ya yi ƙara, jerin sunaye ta gani. Boɗejo, Ali wali, Lawwalli, Saduƙu da wani ya ce mata dukkan su a garin Rano suke, kuma Boɗejo shine Hon Boɗejo Maɗatai. Tana gama dubawa ta miƙe tsaye jikinta na rawa tashin hankali da warin sigari suka taimaka wajan hautsina mata ciki, ta nufi wajan deep freezer da sauri ta durƙusa ta ɗakko ruwan gora, juyawa ta zo ta ji kanta ya daki ƙirjinsa ashe yana tsaye hannunsa cikin aljihu cikin masifa ta ce "Wai dame kake taƙama ne, ko Maj ne ya baka lasisin shigo mini kana abu kamar baka da..," ta yi saurin yin shiru saboda idanunsa daya saka cikin nata a ransa ya ce "Ba ki da hankali Aafiyyah" A fili kuma fuskarta yake kallo ta ce "Muhammad ko?" Ya sake yin shiru idanunsa akan tafin hannunta da yatsun ƙafarta. "Ya aka yi ka san wannan? Ta ya ya waɗannan mutanen za su kasance ƴan gari ɗaya? Bayan dukkansu ƴan Kano ne? Ta ya ya Hon Maɗatai zai kasance Boɗejo? How? Me ka sani game da wannan kamfanin?" Madadin ya bata amsa sai ya sake zuƙar sigarin ya fesa mata a fuska, ta fara tari, ya damƙi ƙafafuwanta ya matsar da ita daga wajan, gorar ruwa ya ɗauka sai ya samu kan shi da zubawa chocolates ɗin cikin freezer ɗin ido, ruwan ya ɗauka ya nufi waje da sauri ta tari gabansa ta ce "babu inda zaka, wallahi kuma sai na faɗawa Maj ka fita, who are you?" "Uwar Maj" ya yi niyya faɗa. Ya sake matsawa zai fita, ta sake shan gabansa sai ya bubbuɗe idanunsa a kanta rai ɓace kuma ya saka hannu ya damƙo gaban rigarta, ya ɗakko har breziyar cikinta yatsunsu na kartar fatar ƙirjinta idanunsa ya zazzago kamar zai faɗo. Aafiyyah ma hannunta ta saka ta damƙo wuyan rigarsa har tana shafo sumar ƙirjinsa tana ƙifta idanu ta ce "Har kake tunanin zaka shigo office ɗina ka yi abin da kaga dama ka fita? Ba'a yi mini haka Blackman ba'a mini wannan shirman" Mai dawa da jajayen idanunsa yake dubanta ya ciko bakinsa da hayaƙin sigarin daidai sanda ta buɗe bakinta za ta yi magana ya busa mata cikin bakin maganar da hayaƙin sigarin ya shige cikin maƙoshinta, sai idanunta ya yi ja kanta ya fara juyawa sosai da kyau Moh ya damƙo gaban rigarta da kyau da ƙarfi ƙitttt! Ta ji ƙarar yagewar sabuwar rigar, tana tari tana ƙoƙarin ganin itama ta yaga masa riga ta ji ya cilla ta saman kujera inda ya tabbatar ba zata ji ciwo ba, kafin ta yunƙura tuni ya fice da sauri ta fito tana tambayar securities amma suka ce basu ga kowa ba, rai ɓace ta ɗauki waya zata kira Maj sai ta fara tunanin kar ta haɗa su faɗa, gwara ta rama da kyanta ko ta saka a ɗaure mata sakarai mara amfani, ɓacin rai da takaicin rashin ramawa da ba ta yi ba ya saka idanunta cika da ƙwalla zuriyarta na tafarfasa sosai ta ji zaman office ɗin ma ya ishe ta sai ya nufi office ɗin Ceo ta same shi zaune saman kujera bayan sun gaisa cike da ladabi ta ce "Daman Sir tambaya ce dani" Sharfaɗi ya ce "To daughter ya akai?" Da yake da yawan lokaci daughter yake ce mata tun sanda suka fara soyayya da Ashraf har yanzu kuma bai daina faɗa ba. Ta ce "Abba me ya saka aka bani Matsayin Manager a wannan kamfanin? Su waye Boɗejo, Ali wali, da Lawwalli da Alhaji Saduƙu?" Zufa ce ta fara yankowa Sharfaɗi ya dake ya ce "Saboda kin cancanta ki zama Manager ne, sauran kuma suna da hannun jari a FS WORLD ne ai kin sani ma" "Boɗejo shine Madatai?" Ta sake jefa masa tambayar sai ya miƙe tsaye ya ce "Ban fahimta ba? Boɗejo daban Maɗatai ba, Maɗatai ai bashi da hannun jari a nan" Aafiyyah ta yi murmushi ta ce "To mene haɗinsu duka? Mene ya haɗa su da Rano? Ashe Fulani ne?" "Who told you that?" Ta ce "Abba ka san komai, don Allah ka faɗa mini gaskiya, ina ganin girma da mutuncinka kallon uba nake maka, kuma don Ashraf baya raye ba zai zama hujjar da zata saka na daina yi maka wannan kallon ba, me ya sa aka bani kujerar Manager?" Ya shiga zagaya wajan can ya ce "Amsa ɗaya zan iya ba ki Safiyyerh, bani ne da ra'ayin ba ki kujerar ba, buƙata ce aka zo mini da ita, kuma aka ce ke ake buƙata, sanin hujjar ni kai na ban sani ba, bani da amsar hakan ki yi haƙuri kar ki ƙara mini wata tambayar daughter" ya ce yana fita daga office ɗin Aafiyyah ta dafe kanta ta ce "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, meke faruwa ne haka? Ashraf don Allah ka faɗa mini ko a mafarki ne Please" ta ce a sanyaye. Da ƙyar ta miƙe ta nufi motarta tana zuwa ta shiga kai tsaye gida ta nufa, zuciyarta fal baƙin cikin abin da Muhammadu ya yi mata ga damuwar da Sharfaɗi ya saka ta. A lokacin ta samu labarin wai a daren ranar zata tare a gidan AA MAJ, aka dinga shiryata Ummimi ta yi mata faɗa da nasiha sosai, tana cikin lafayar da aka naɗa mata jikinta sai ƙamshin haɗin S Bayero yake mai narkar da zuciyar masoyi ƙamshi ne na musamman yake tashi a jikin nata. Sanda ta durƙusa gaban Paaahh kuka ta saka masa harda buri ita ta fasa auren, ya dinga mata dariya can kuma ya kama hannunta da kan shi ya nufi hanyar fita, daidai nan J ya yi saurin barin wajan ta ce "Paaahh bari na yi wa Yaa J magana" Ya jinjina mata kai, a can bayan gidan ta ganshi ya sunkuyar da kai. "Kuka kake yi?" Ya ji saukar muryarta Cikin sauri ya ɗako yana kallon ta sai ta yi murmushi ta ce "Kamar kana jin haushina bayan ban san laifin da na yi maka ba, idan na maka abu a ƙa'ida kana faɗa mini ni bani da wani aboki sai kai, kana haɗe mini fuska kamar kaga maƙiyarka, kamar ka tsane ni haba Yaa J, i love you fa" "Where is the love?" Ya ce a hankali. "A nan" ta ce tana nuna masa ƙirjinta, ya kalli ƙirjin sai ya ɗauke kai a hankali ya ce "show me" "Allah ina son ka yaya" Ya ji zuciyarsa da gangar jikinsa ta motsa, yar yar tsigar jikinsa je zubawa wani abu mai kama da feelings, kuma feelings ɗin Aafiyyah ta gudana a jinin jikinsa ya kasa motsi, kar kar kar haka zuciyarsa ke rawa idanunsa suka juye, sanda ta kama hannunsa kamar dalma haka J ya ji jijiyoyin kan shi suka mimmiƙe idanunta cike da hawaye ta ce "Ko babu komai ka yi mini addu'a a gidan aurena, ina sane ko murnar aure ba ka yi mini balle ka bani gitfs,, wannan sauyin na mene? sauyin lokaci ɗaya?" "Sauyin ki ne, laifin ki ne" ya samu kan shi da faɗa a fili ta ce "Kamarya?" Sai ya ce "I love you" farfari ta yi da idanunta ta ce "And i love you too J" sai ta nufe shi zata rungume shi, ya yi saurin ja da baya ta madaidacin sai kuma ta ce "Ina ta son na yi maka gulma, Yaa J kaga wanda Paaahh ya saka na yi arrested ɗin shi" J dai baya uhm baya uhm'uhm ta miƙa masa wayarta ta ce "kaga picture ɗin shi, dana ɗauke shi yana shaye-shaye da haukan shi" ta ce tana murmushi. Dam! Zuciyarsa J ta buga sanda yaga photon, a gigice ya ɗako ya kalli Aafiyyah a kiɗime ya ce "Kin tabbatar shi kika kama?" Ta ɗaga masa gira. "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un. Maamah kin san wa aka saka kika kama? Kin sani? Ko dai daddy yana sane ya saka kika kama shi?" "Kamarya? Ba kowa bane Scorpion me mai kashe mutane mana ɗan ta'adda" Wani irin kallon tausayin Aafiyyah J ya bita da shi, ita kuma sai murmushi take yi, shi sam bai yarda shi ta kama ba, yaron data rayu da soyayyarsa? Yaron data shiga matsala da dama saboda shi, shine yanzu ta kama? Aafiyyah ta ce "Kuma kasan cewa kashe shi za'ayi? Yana da kwarjini sosai ni kowa har kwaɗa masa mari zan iya" ta amshi wayar ta ta ce "bye" Paaahh ya ce "Ya aka yi kika zauna?" Ta yi dai murmushi sai kuma ta yi sak ta ce "Daddy jini a hancinka" ya yi saurin buɗe ido sai ya ce "Oh haɓo na yi" ya ƙarasa wajan motar ya bubbuga, a nutse aka buɗe bayan motar ƙafar Maj ta fito sai ya ƙarasa fitowa yana sanye da wani yadi fari tas mai laushi da taushi, ya ɗora hula a kan shi ya fito a asalin ango iya kyau da haɗuwa Aliyu ƙarshe ne. "Aliyu ga amanata" ya ce yana damƙa hannun Aafiyyah ana Aliyu "Ka dinga haƙuri da ita don Allah, ban ce karka hukuntata ba, amma ka kula da ita" "In sha Allah. Thank you Sir" Sai Paaahh ya ji tsoron wani iri da Aliyu ya ce Sir akan idanunsa ya buɗewa Aafiyyah bayan mota ta shiga, shima ya shiga Sergeant Timo ya ja motar suka ɗauki hanya zuwa gida AA Maj Aliyu Abdu Marafa. Ƙamshin Aafiyyah ya nutsar da zuciyar Aliyu ya kasa daurewa abinka da soja kuma tsohon gwauro anjima babu aure uwa uba haɗin S Bayero daya gama gigita masa zuciya. Ya saka hannunsa ya kama nata ya ɗan matsa, a hankali ya janyota zuwa jikinsa, ta yi saurin ɗago kai ta kalle shi sai taga ya yi mata murmushi,a hankali ya sumbaci goshinta yana zame lafayar muryar can ƙasa ƙasa daidai kunnenta yana sake matse hannunta ya ce "Barka da zuwa duniyar ma'aurata, barka da zuwa gidan soja halaliyyar matar soja" "Ina ne gidan?" Ta ce a hankali. "My cheek?..," ya ce yana kwantar da kanta a ƙirjinsa ta yi luff tana sauke numfashi ta zaga hannayenta ta baya ta rungume shi. "Thank you" "For?" He said. "For being your wife" Bai ce komai ba, domin yanayinsa bana magana bane ya sake rungumeta very tight a jikinsa a hankali kuma ya ɗago fuskarta ya yi covering suka kalli juna. "Aliyu loves Safiyyerh so much ok?" "And Safiyyerh loves Aliyu for life" Kissing ɗin juna suka fara,.with full of love and care romantically. * Abubuwan da yawa sun faru. Muhammad har baya iya motsi domin an ƙara tsananta bincike akan Scorpion saboda labarin harin da aka ji ya kai wa Hon Maɗatai duk da yana tsare a wajan Fcid ɗin. A kuma asabar ɗin da zata zo ne aka tsayar ranar da za'ayi zaɓen Ɗan Majalisar tarayya da kuma Gwamna, sai duka jam'iyyu ukun suka shiga cikin ruɗani musamman Eng Ali wali, Hon Maɗatai kuma ko a jikinsa saboda shirun da ya ji kwana biyu matar da ta yi magana akan shi bata sake yi ba, sun karɓi votes card ɗin talakawa aka jefe su da kuɗi da sabulu da omon wanda suka amsa ta hannun woman leaders a ɓangaren mata, suka shirya ƴan daba tare da basu kayan caji da makamai na musamman saboda fasa akwati kuma da satar akwatin kamar yadda aka shirya kafin akai su zuwa ga inec. Babban parlourn gidan Dr Abraham Denial David a cike yake da family ɗin. Alhassan da Al Hussaini da Arjun da suka dawo jiya saboda zaɓe sai kuma Soha da abokiyar haihwurta, sai Qasim da Mimi da Jeddah kana AA MAJ sai Oga Mutallab da yake tsaye yaƙi zama wanda a tunaninsu Muhammad ne shi. Dr Abraham ya gyara zama ya ce "Muhammad ko? Nemi waje ka zauna" sai ya ji maganar Abraham kamar umarni ce a gare shi kawai ya nemi armchair ya zauna yana duƙar da kan shi zuwa ƙasa, Qasim sai kallon shi yake yana tuna maganar da suka yi da Jeddah. "Aliyu ya aka yi Muhammad ya zama jinina? Ba musu nake ba, domin kallo ɗaya na yi masa na san jinin Abraham na gudana a jikinsa" AA MAJ ya ce "Sir ka san cewa kai ne ka shige mini wajan ganin na yi nasara a aikin soja ka mini komai ta ya zan wofintar da abin da na fahimci yana da alaƙa da kai? Akwai watarana muna neman ƙwararre a fannin computer aka kai mu wata makaranta, kai tsaye aka nuna mana Muhammad ne zai iya yi mana abin da muke so, lokacin baya nan saboda an ce baya son zama waje guda, kuma lokacin wai kamar ya je Lagos wani interview da makaranta ta tura shi, ina ta bibiya har muka samu ya dawo lokaci daga club ma yake yana warin giya, kallo ɗaya na yi masa naga kamannin Alhassan da kuma kamanninka" Qasim da Jeddah suka kalli juna Aliyu ya ce "kai tsaye na ce ya sunanka? Sai ya yi mini shiru sai dana nuna masa bindiga da id card ya ce Muhammad na ce ka san dr Abraham? Ya nuna bai taɓa jin sunan ba, na koma wajan nanny ɗin data rai ne shi domin a gidan marayu ya taso na dinga bincike ta ce ai wata mata ce ta kawo shi yana zanin goyo haka na dinga bincike har muka samu matar ita kuma ta kai mu wajan wata nurse wacce ta amshi haihuwar Malama" ya nuna Mimi dake zaune ya ce "Ba iya Qasim ta haifa ba, yara maza tawaye ta haifa kafin ta san cewa tagwaye ta haifa aka ɗauke jariri guda ɗaya aka bar mata ɗaya, na saka nurse ɗin a gaba ta ce ai ita wallahi sata aikin satar aka yi, kuma bata san matar ba, domin fuskarta rufe yake da niƙab kuma kuɗi ta bata mai yawa, kuma tana ɗakko jaririn ta bawa matar ta fice da shi daga cikin asibitin, har gashin kan ka sir na cira a lokacin da na yi maka waya cewa wasu sun biyo matata a hanyarka ta tafiya wajan meeting, na ciri gashin Muhammad na kai aka yi DNA test results ya nuna positive. Muhammad da Qasim twins ne" Waje ya yi shiru, Jeddah dai kanta na ƙasa zuciyarta na bugawa da matsanancin ƙarfi idan ta kalli Moh dake zaune wanda sukewa kallon Muhammad sai ta kalli Qasim. Wayar Qasim ce ta fara ringing da sauri ya ɗauka ya ce "Dr Hamza ya aka yi? Lafiya dai?" Ta cikin wayar dr Hamza ya ce "Kimiyya komai kake yi ka bari ka zo asibiti yanzu, mara lafiyar ka ta farfaɗo allahamdulilah amma sai ihu da kuka take yi tana kiran sunan wani ko yaran taƙi gani sai mutumin take kira" wayar a speaker take hakan ya saka kowa jin abin da ake cewa, Moh ya yi saurin kallon kimiyya haka kawai ya ji gabansa ya faɗi, jikinsa ya yi sanyi zuciyarsa na bugawa ta cikin ƙirjinsa ta ƙarfi ya ji yana son bin kimiyya zuwa asibitin, sai ya miƙe tsaye ya yi waje "Muhammad Muhammad" Maj ya shiga kiran shi, shima Kimiyya miƙewa ya yi ya fita zuwa waje, yana fita Moh har ya shiga Moh ya kunna, daidai nan kuma Aafiyyah ya shigo da motarta saboda tana ta kiran wayar Qasim bai ɗauka ba, kuma tana buƙatar zuwa wajan Dr Abraham har yanzu bata san shine mahaifin Qasim ba, kafin ta fito daga mota Kimiyya ya yi saurin shiga motar ya ce "Yawwa kin zo a daidai dear, kai ni asibiti don Allah" Ganin yadda jikinsa ke rawa ya saka bata tsaya tambayarsa ko lafiya ba, daman tasan asibitin don haka ta kunna motar ta yi reverse ta fita daga gidan da wani irin gudu, kafin mai gadi ya rufe gate shima Moh ya yi waje da gudu a cikin motar Maj ya bi bayan su Aafiyyah da I. Qasim kimiyya zuwa asibitin da suka nufa. Not edited 💥Chapter 11: Fake love, Internal love Gudu sosai Aafiyyah take yi akan titi idanunta cikin sunglasses, sarai taga motar dake biye da tata, bata fahimci dai motar waye ba, sai ba ta yi zargin su ake bi ba. Juyawa ta yi kaɗan ta kalli Qasim sai ta lura baya cikin nutsuwarsa hankalinsa kuma a tashe, giyar motar ta rage ta fara tafiya slowly sauran motoci na shige ta. Qasim ya juyo ya kalle ta ya ce "Maamah please" ya faɗa da sauri. "Please what?" "Drive faster" "Uhm" kawai ta ce tana sake rage gudun motar, har sai da motar Moh ta yi daidai da tasu suka fara jerawa, har lokacin kuma Qasim bai lura da motar Moh ɗin ba, domin ya tattara hankalinsa kwacokan zuwa ga asibitin da kuma abin da yake jiran shi a can ɗin, don haka sai ya sake duban Aafiyyah ya ce "Kina ji" Ta girgiza kai, sai ya ce "Tsaya a nan ki bani kan motar wallahi ji nake kamar na ari fuka-fukai na tashi sama, da kin san abin da yake gabana da ba ki yi wannan iyayin naki ba Maamah" sai ta kalle shi kawai, still kuma ba ta yi magana ba, shiru ta yi na wani lokaci, kafin ta juya su sake haɗa idanu da Qasim a hankali ta ce "Qasim waye kai?" Cikin rashin fahimta Qasim ya ce "ban fahimce ki ba, bangane waye ni ba, wanne irin question ne haka?" "Abu ɗaya na tambaya, ka yi magana ya kai 10 words. Qasim who are you? Waye kai Please?" "Safiyyerh" Qasim ya kira ta da mamaki sosai a fuskarsa sosai. Sai ta saki kan motar gabaɗaya tana ɗaga hannu sama, da sauri ya ce "Safiyyerh lafiya kike? Kashe mu za ki yi ne? Kin saki motar fa" sosai ya ruɗe musamman daya lura a tsakiyar titi suke kuma suna gab da zuwa asibitin. Bata riƙe kan motar ba, sai ta yi murmushin tana rufe ido ta ce "Oh oh oh, na san driving nake, na san akan titi muke, ina sane" Sai ta riƙe motar tana sauke numfashi a hankali "Huh, it's okay, zan sake maimaitawa waye kai?" "Qasim Ibrahim" ya bata amsa. "Kana son raina mini hankalin tabbas. Qasim na san na taɓa rayuwa da kai mai tsayi, we spend time together, we know eachother, ban san yaushe bane ban san wacce kalar rayuwa na yi da kai ba, muryarka na damuna cikin bacci sometimes, ina ganinka cikin idanuna, Qasim who are you?" Ta ce shortly. Qasim duk da a ruɗe yake, damuwa da tashin hankali bai hana shi jin wani daɗi na saukar masa ba, tambayoyin Aafiyyah a gare shi ya nuna masa cewa a kowanne irin lokaci zata iya recovering daga Anemia ɗin data shiga, wanda kuma dalilin BDNF Brain-Derived Neurotrophic Faction injection da yake mata ne ya taimaka wajan dawowa da tunaninta daya shuɗe na wasu shekaru, kuma daman memory loss ɗin under AA ne Anterograde Amnesia wanda hatsarin mota ke haddasa ce a kuma Severe cases recovery can take months to years average 1-2 years or more. Aafiyyah kuma dalilin allurar da dr hash ke yi mata ya sake taimakawa wajan daƙulewar farfaɗuwar tunaninta akan lokaci. Sai ya share ya ce "still, ban fahimta ba, me kike nufi da kina ganina a baccinki? Daman dole ki ganni mana, tunda ni abokinki ne, kuma akwai amana ana tare ko ya?" "Makamancin haka. Bayan kai akwai wanda nake gani, na damu da isan ko waye idan na zurfafa tunani kai na ciwo yake sosai. Qasim muryarka tana amsa mini cikin kunne, muryarka iri ɗaya data wani, shi kuma wanin yana yi mini shige data wani ni kam na kasa fahimtar komai a wannan lokacin, Safiyyerh ta rasa ƙwarin zuciyar fahimtar abu" "No, ba ki rasa ba, as long as muna tare kuma kin yadda dani zan taimaka miki in sha Allah" "Qasim when?" Ta ce tana buɗe hannunta tare da yin corner, ta manta da batun motar Moh tuni. "Ki bani lokaci" Bata ce komai ba. Asibitin suka shiga, ta yi parking jikinsa duka rawa yake kamar mai jiran wani gagarumin abu ko wanda aka yi wa bushara da samun aljanna kai tsaye babu hisabi haka ya saka hannu ya buɗe murfin motar ya fito, itama buɗewa ta yi zata fito sai ya zaga inda take zaune, kafin ta fito ya kalle ta sun haɗa ido sai ta tsaya tana binsa da idanu a hankali ya ce "Za ki jira ni a nan ai?" Kamar yarinya ta ɗan rausayar da kanta gefe ta ce "Kamarya to?" "Ki jira ni" "Ba zan bika ba?" Ya girgiza kai ya ce "Laaaah, yanzu zan fito ki kunna waƙa ki yi game i am coming bani five minutes?" "Bari na tafi gida to" "No please ki jira" Sai ta yi sak, sai kuma ta ɗaga kafaɗa ta ce "Ok, zan jira" Cikin motar ta koma ta zauna, Qasim ya juya kuma zuwa cikin asibitin tun a reception Dr Hamza ya tare shi, bayani yake yi masa yanayin data farfaɗo ɗin, yana shiga wani room us ɗauki korayen kaya ya saka a jikinsa, takalmi da hula da safar hannu yana kammala sawa ya nufi room ɗin da take ciki, tun kafin ya shiga na'urorin dake room ɗin suke bada sauti, da sauri ya ƙarasa bakin gadon da take kwance idanunsa a kanta, itama ɗin tunda aka buɗe ƙofa ta samu nasarar buɗe idanun nata da ƙyar saboda nauyin da suka yi mata, ga wani irin ciwo da kanta yake mata, kallon shi take yi babu ko ƙiftawa, wani irin kallo mai kama da ashe da ikon cigaba da rayuwa? Ashe numfashina da takuna gami da shan ruwana a duniya bai ƙare ba, ina da sauran lokacin da zan iya rayuwa da mutanen da suke so na. Tun daga sama har ƙasa take bin Kimiyya da kallo, ta lumshe idanunta sai ta buɗe su tar a kan shi har ya gama shigowa cikin room ɗin ya daidaita tsaiwar shi a kanta. Qasim wani irin farinciki ne ya lulluɓe masa jiki musamman ganin kallon da take yi masa, wanda yake nuna masa jikin nata ya samu ƙwarai, amma tana jifansa da kallon tuhuma ne, kallo ne, mai kama da ka yi mini laifi madadin kuma ta juyo ta kalle shi sai ta rufe idanunta ruf hawaye na bin gefen idanun masu zafi kuma. Qasim ya yi ƙasa da murya ya ce "Allahamdulillah. Kin farfaɗo jiki ya samu mun gode Allah" ya ce a tausashe yana duba computer da ya yi connected ɗin ta da nunfashinta, ya yi disconnected ya cire komai a hankali ya miƙa hannu ya kamo hannunta, sai ya ji hannunta laushi lumus har wani tsantsi fatar take, a lokacin yaga ta juyo da ƙyar ta kalle shi a hankali, sai ta mayar da idanunta zuwa ga hannunsa daya riƙe hannunta da shi. Da sauri ya sake ta yana faɗin. "Oh oh afuwa" Ta dai tsora masa ido, da idanunta ya sake cewa "Afuwan, ina ƙokarin cire miki wannan abin ne so that za ki iya jingina da jikin gadon" "Ya jikin? Ya kike ji yanzu?" Ta ɗaga idanunta da ƙwalla ta gama cika su sosai, sai gently ta ɗauke kanta ta zubawa bakin ƙofa idanu kamar jiran shigowar wani, kamar mai kiran tsammanin warabbuka zuciyarta na wani irin bugawa da ƙarfi ta cikin ƙirjinta, ko kallo na nutsuwa ka yi mata sai ka fahimci rashin nutsuwar da zuciyarta take ciki, ta kasa jure rashin ganin wanda take tunanin gani a yanzu ɗin. Laɓɓanta suka fara rawa ta fara ƙoƙarin yin magana amma ta kasa, ko ɗazo ma, taimakon Ubangiji ne ya sahale mata yinta, sai ta ɗaga yatsarta guda ɗaya ta juya ta kalli Kimiyya ta fara nuna masa bakin ƙofar da take buɗe, bai fahimci me take nuna masa ba, ita kuma kamar a mafarki taga shigewar Moh da wannan tafiyar tasa kamar jumuna, ƙokarin tashi ta fara amma ta kasa saboda bata da ƙarfi da nauyi nan da nan hankalinta ya tashi ta dinga nunawa kimiyya bakin ƙofa, da wani irin hanzari ta yunƙura da dukkan ƙarfinta zata tashi, sai ta yanke jiki ta faɗi. Takaici da damuwa da ƙuncin zuciya da ya yi mata yawa ya saka ta kwanta a wajan ta saki wani irin kuka mara sauti saboda har yanzu wuyanta a tokare yake abu,kuka take sosai idanunta da fuskarta sun yi jawur dasu, kukan baya fita sosai. Ganin hankalin data shiga ya saka Qasim kimiyya saurin fita daga cikin room ya fara duddubawa amma babu kowa, dr Hamza ya kira ya taimaka masa suka yi saurin mayar mata da kayan aikin ganin ciwon na neman dawowa ruwa. Ta kasa nutsuwa dai kuka take yi dr Hamza ya ce "Wai wani abu ne ya faru ne?" "Actually, i don't know Dr Hamza, waje kawai naga tana nuna mini" "Kuma ba wani ta gani ba? Ba ka yi mata al'ƙawarin kawo mata wani ba" Qasim ya yi shiru yana nazari cikin sauri kuma ya tafi windown ɗakin ya leƙa can baya wajan following na asibitin motar Aafiyyah ya hango har yanzu tana inda ta yi parking, ya dinga kallon mutanen wajan da nazari cikin sauri ya juyo yana kallon Dr Hamza ya ce "Na yi al'ƙawari tabbas ba kuma mantawa na yi ba, lokacin al'ƙawarin ne kawai bai ciki ba, akwai abin da nake jira, ita kanta a yanzu ba zata ji daɗin ganin abin da take buƙatar gani ba, ba zata so ganinsa a yadda yake ɗin ba, akwai sauran lokaci yana nan zuwa in sha Allah, in sha Allah" "In sha Allah" Dr Hamza ya maimaita "Ka ɗakko mini babies ɗin" "Ok" cewar dr Hamza yana fita. Qasim ya dawo da ganinsa gare ta, ya runtse idanunta jikinta har yanzu rawa yake yaja kujera ya zauna a tausashe ya ce "Ki yi haƙuri, ki yi haƙuri, ki yi haƙuri da rayuwa da kuma yadda kika tsinci kan ki, ki yi haƙuri da karya miki alƙawarin da na yi miki, na san ban kyauta ba, amma ki yafe mini ba haka na shirya haɗuwarku ba, ba haka nake so ya ganki ba, kema kuma ban shirya ki ganshi a yadda yake a yanzu ba, ki yi mini alfarma zuwa lokacin daya dace, idan har ya san cewa kina raye kuma ba ki mutu ba, to akwai matsala don Allah ki bani ƙarfin qwwia ka bani haɗin kai" Muryarta na rawa bata fita sosai da ƙyar take jan numfashin daya tsaya mata iya ƙirji hawaye na fita a idanunta ta ce "I want to see him" "Za ki ganshi, not now" Ta sake cewa "Ina son shi, ina son shi, ina son ganinsa don Allah" "Nahhhh, ki sake haƙuri kan haƙuri kin ji? Dom Allah za ki iya" Laɓɓanta na rawa ta ce "Zafi ina ji" "A ina?" Sai ta nuna masa saitin zuciyarta, alamar nan yake mata ciwo ɗin, kuma da gaske zafi da raɗaɗi take ji a zuciyarta kamar ana rura mata garwashin wuta haka take jin zafin da ƙirjinta yake mata. Da ƙarfi kamar wacce aljanu suka shafa ta ce "Ina son ganin shi, i want to see him ka tausaya mini don Allah, don Allah" sai wani irin rauni ya mamaye zuciyar Qasim, da yana da ikon yin hakan tabbas da ya yi, da kuma yana da damar hakan da ya yi, amma wannan damar ba'a hannunsa take ba, dole ya yi taka tsantsan akan lamarinta. Sai ya sunkuyar da kan shi ƙasa idanunsa cike da hawaye wanda ya kasa fitar dasu a kan idanun nata, yana jin yadda take ta haɗa shi da girman Allah ya kalle ta sai yaga ta yi murmushi ta ce "Allah Ya shirya ka, ai shikenan ni ko? Ni ɗin ko?" "I am sorry" ya ce a hankali. Dr Hamza ya shigo da baby a hannunsa, da wata nurse da take biye dashi hannunta riƙe da ɗaya jaririn. Qasim ya ɗauki baby girl ɗin ya miƙa mata ya ce "Ga abin da kika haifa nan, kyautar da Ubangiji ya yi miki" ta zubawa jaririyar idanu musamman idanunta da ɗan ƙaramin bakinta, laɓɓan jaririyar jajir sai tsotsar yatsa take yi alamar tana buƙatar nono, sai buɗe ido take yi tana rufewa a tsorace kana ganinta kaga farar kura, ko yaya abu ya yi sauti sai ta razana. Mahaifiyar kuma kallon yarinyarta ta kawai take yi, ta rasa me take ji zuciyarta game da yaran ta rufe idanunta ta bawa hawayen idanunta damar zuba a saman fuskarta. Qasim ya amshi baby girl ɗin, ya ajjiye mata baby boy ɗin, sai da ta firgita da ganin kamar yaron ta ƙanƙame shi a ƙirjinta kamar zata mayar da shi ciki. Sai Qasim ya yi murmushin jin daɗi ya ce "Yaranki ne duka, suna buƙatar zafin jikinki da kuma abincin su" Kamar bata gane ba ta ce "Da gaske yarana ne? Har wannan cute babyn?" Ta ce, tana nuna baby boy ɗin hannunta "Allah ne ya ba ki kyauta" "Allahamdulillah" ta ce. Ta yi shiru for a while kana ta ce "Kuma ya san da su? Ya san ina da babies? Ya san na haifa masa yara?" "A'a, tukunna" ya bata amsa. Sai ta haɗe fuska kamar yarinya ta saurin cillar da yaron dr Hamza ya yi saurin tare babyn ya faɗo hannunsa, da tuni ya faɗa ƙasa dake namiji ne sai ya kwakkwaɓe fuska ya fara cilla hannu da ƙafa kamar zai yi kuka. Ita kuma ta takure jikinta waje guda taƙi magana, lokaci zuwa lokaci taka kallon ƙofa tana ganin kamar zata sake ganinsa ya zo shigewa. Allurar bacci ya yi mata wacce zata sake sawa ta nutsu sosai kuma ta dawo nrml kamar yadda take baya. Kayan jikinsa ya cire yana sake yi wa Sarki Ubangijin talikai godiya a zuciya da sarari daya farfaɗo da ita a lokacin da ake buƙata,ya wanzar da nutsuwa na ɗan wani lokaci a zuciyarta tare da sanya mata dangana na taƙin lokacin kafin ta sake birkicewa. "Ranki ya daɗe a yi mini alfarma, a yafe mini" harara ta watsa masa tana ajjiye wayarta ta yi wa motar key. Allah Ya gani Ubangiji shine shaidar zuciyarsa yana tsananin so da ƙaunar Aafiyyah kamar rai, shekaru nawa? Tun soyayyar ƙuruciya abu kamar wasa ya kasa dating ɗin kowacce yarinya saboda Aafiyyah, bai taɓa tunanin akwai watarana da zata iya yi masa shamaki da Aafiyyah sai yanzu, yana shirin faɗawa mata yadda yake jinta a zuciyarsa, sai kwatsam ta tare shi da batun wai tana son MUTALLAB, so bana wasa ba, son da take jin watarana shi zai iya ajalinta a wannan lokacin sai ya ji, jinin dake yawo a jikinsa ya daskare ya nemi dukkan wani nutsuwa da sukuni a zuciyarsa ya rasa, tashin hankalin da bai taɓa shiga a rayuwa ba, shi ne ya shiga a yanzu tun bayan ranar da ya yi tozali da Mutallab, that's the comfortable day for him, idan ya tuna ranar da yaga Mutallab zaune akan tudu sai ya ji mikin abin ya taso masa, har tuntubar ya yi wajan zuwa ya shaidawa Jeddah abin da ya gani, a lokacin tana zaune a parlour bayan maid ɗinta ta ajjiye mata jarida tana dubawa tana sanye wani da dakakken lace wanda ya gaji da haɗuwa Kimiyya ya faɗo cikin parlourn yana nishi. "Jeddah Jeddah Jeddah" Ya dinga kwaɗa mata kira jininsa duka rawa yake, Jeddah ta juya ta kalle shi kana ta ajjiye abin hannunta ta ce "Qasim" ta kira shi. "Qasim sau nawa zan shaida maka bana son shigowa waje babu permission Ubangiji ya yi hani, ko ka nemi izini sai an baka dama haka Ubangiji ya koyar da bayinsa musulmai ka ji? Saboda gujewa ganin haramun ka gane?" Ya rusina ya ce "Ki yi haƙuri Jeddah" Ta jinjina kai. Shi dai ya kasa yin shiru ya ce "Jeddah i just saw my brother" ta kalle shi ta ce "Your brother?" "Eh, naga ɗan'uwana Allah yanzu a ɗan unguwar dake gabanmu zaune saman tudu" I bit of scared take kallon Qasim a hankali a nutse ta ce "Alhassan ko Al Hussaini? Ko kuma Arjun ko Yaa K?" "A'a babu ko guda, wani mai kama da Papi da Alhassan" "Kimiyya wanne rubishh ne haka?" Idanunsa ya yi rau-rau "Allah Jeddah da gaske nake, wani mai kama da Papi sosai na gani mai kama da Alhassan i saw him, da gaske nake" Jeddah was about to confuse na maganganun Kimiyya cikin dabara ta ce "Jeka ɗakko mini photonsa a wayar da Papi ya siya maka, go Qasim" da sauri ya fita jikinsa na rawa, Jeddah kuma ta yi shiru bayan tabi shi da idanu, thinking of kimiyya ko dai ya samu matsala ne? Ko aljanu sun buɗe masa idanu? Ban da ta san cewa babu wani ɗan Hajia Majeederh dake zaune a Nigeria duk suna Germany, ita daman tun sanda ƙaddarar aure ta haɗa ta da Dr Abraham, ranar da suka fara haɗuwa ta ke Arɗos group tun kamfanin na ƙarami taje da nufin siyasa sai suka haɗu, bata taɓa aure ba, ita da kanta taje wajansa bayan ta sha wahala kafin ta samu appointment da shi, ita ta yi requested soyayya daga gare shi, duk da cewa ta ji tsoro ƙwarai kar ya wofintar da ita, luckily ya amince ba tsangwama balle yarfe na wasu mazan, uwargidansa dai ce ta bada matsala amma daga ƙarshe ta amince domin cewa ya yi sai da yardar Malama Majeederh. Bayan sun yi aure ya ce ta zauna a Nigeria tana kulawa da kamfaninsa dake Kano a lokacin kuma ko ɓatan wata bata taɓa yi ba har aka haifi su Qasim. "Jeddah Jeddah kin ganshi" Qasim ya katse mata tunanin da take yi, wata majajjawar hajijiya ce ya ɗauke ta lokacin da idanunta ya sauka akan Mutallab, dake zaune yana kallon gefe guda, kallon farko ta fahimci yaron yana cikin damuwa da baƙin ciki bashi da mafita, kamannin da Mutallab yake yi da Dr Abraham da Alhassan har ya ɓaci ainu, lallai duk inda wanannan yaje ya dawo akwai ƙamshin gaskiya ta jinin Abraham ke yawo a jikinsa dole zata binciko. "Jeka wajansa ya zo ka ƙulla abota da shi, kar ka yadda ka ce masa yana kama da mahaifinsa, kar kuma ka yadda ka nuna masa photon Papi da Alhassan, go and meet your brother Qasim, jeka wajansa" "Jeddah ina son shi" "Dole ka so shi, ni da kaina na ji ina son shi, bana son kowa ya san maganar nan keep it as secret" "Secret" Kimiyya repeated the word. Aafiyyah ce ta kira shi da ƙarfi hakan ya haddasa dawowa daga duniyar tunanin abin da ya shuɗe dawo masa, ya yi shiru, who is Muhammad? And who is Mutallab? Ya tambaya a zuciyarsa cike da mamaki da kokwanto ya kuma rasa meke faruwa. Wannan dalilin ya yi sacrificed na soyayyar da yake yi wa Aafiyyah zuwa ga Moh, domin ya jima da fahimtar ina tunanin Moh yake yana yawan ganinsa yana satar kallon Aafiyyah most of the time har pictures ɗinta yake ɗauka a wayar daya bashi, kasancewar ƙaddara zane ce, inda muke tura zuƙatanmu daban inda take kai mu daban, ƙaddarar Buddy ta Safiyyerh bestie ce, baya wulaƙanta mata saboda duka yan'uwansa mata ne, yana kuma jin tsoron kula mace gudun abin da ya faru da Jaaanah da Diyna ya faru da wani wannan shine ɓoyayyiyar ƙaddarar kowanne bawa dake rayuwa a duniya. Aafiyyah bata sake kula shi ba, har suka fita daga asibitin. Moh dake cikin motarsa zaune yana zuƙar sigari ya bi motar Aafiyyah da kallo, shi dai haka kawai ya ji zuciyarsa ta alaƙantu da wannan asibitin, a sanda ya shigo bayan motar Aafiyyah ta yi parking ƙin fitowa ya yi, har kimiyya ya fito cikin sauri ya fito ya bi bayan kimiyya yana gyara zaman facemask ɗin fuskarsa zuciyarsa sai rawa take yi a cikin ƙirjinsa, kafin ya kai zuwa ga ciki har Kimiyya ya ɓacewa ganinsa, sai rasa wanne room ɗin kimiyya ya shiga, ya dinga buɗe rooms one by one amma ba kowa a ciki,gudun kar a zarge shi ko ayi tunanin satar yara yake yi ko ta mutane ya saka ya yi lungu dab da wani room 23 da yake buɗe, a daidai lokacin ya ji gabansa ya faɗi zuciyarsa ta yi tsalle tare da dokawa ta cikin ƙirjinsa bugun da bata taɓa yi masa ba, tun bayan ranar da Safiyyerh ta ce ya bata takardar saki ta fasa auren, ya ji ƙafafuwansa na rawa suna neman gaza ɗaukan gangar jikinsa, kamar walkiya haka ya shige ta ƙofar ɗakin ƙafafuwansa na harharɗewa idanunsa jajur jijiyoyin kansa sun fito sun yi dara-dara tare da kwanciya a saman goshinsa, cikin sauri ya shige mota ya kifa kan shi da sitiyarin motar a gaggauce kuma ya fara jan sigari ya shanye sama da kara shida yana daga zaunen. Ya bi motar da kallo har su Aafiyyah suka fice kana ya tayar da motar ya nufi gidan computer ɗin AA MAJ. * Ummeyh na zaune ita da Professor ta yi wata iriyar ramewa ta zabge ta lalace idanunta ya faɗa ya jeme, shi kan shi Professor ɗin kamar bashi ba. Abba Nasim da Haydar na zaune dai Nahyan da Waheebah da Uncle Musbah. Uncle Musbah ne ya ce "Dr da za ki yi haƙuri ki daina wannan kukan don Allah" Tana sake matsar hawaye ta ce "Ta ya ya zan iya controling zuciyata daga hana kaina zubar da hawaye, na cancanci kuka Musbah na cancanta da kai na na yi Safiyyerh gwaji da naga duk ta sauya gwaji ya tabbatar da tana ɗauke da ciki" ta sake rushewa da wani irin kuka ta ce "Yanzu da ciki a jikinta ta tafi lahira? Da ciki a jikinta aka gwada mata wannan rashin imanin? Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un wallahi ban ɗauka baya son ta ba, ko a labaran littafai dana film mata na ji tana kashe mijinta, amma yau tarihi ya kafo a kan ƴata mijinta ya kashe ta, me Safiyyerh ta yi masa a gidan duniya? Waye shi a wannan garin da duniyarmu ta kasa ɗaukarwa Safiyyerh fansar abin da aka yi mata? Wayyo Allahna wayyo zuciyata wallahi mutuwa zan yi muddin babu Safiyyerh" Kuka take kan jiki kan ƙarfi. Waheebah ta ce "Ummeyh Allah yana son ta, sai dai a lokacin ko ya fara shaye-shaye ne tunda yanzu na ji labarin ya zama riƙaƙƙen ɗan'daba" "Haka so yake? Allah ya tsinewa so idan haka yake ya kashe mini gudaliya" Uncle Musbah ya ce "Kina da tabbacin shine ya kashe ta?" "Evidence? A proof haba Musbah" Ta kasa yin magana sai kuka. Professor daban bai fiya magana ba ya yi dangana cewa babu gudaliyarsa a duniya babu ita kuma ba zata dawo ba, amma dole ya sadaukar da komai wajan ganin ta samu adalci a hukumance a kuma tsarin shari'a. Nahyan baya cewa komai, domin har yanzu kan shi a kulle yake baya taɓa sawa ran shi cewa Mutallab zai kashe Safiyyerh baya taɓa wannan tunanin. Daga bakin ƙofa aka shigo tare da faɗin "Ai gurbin ido ba idon bane, tsintacciyar mage bata taɓa zama mage, na faɗa muka cewa yarinyar nan TSINTACCIYA ce ku nemi haihuwa tun da wuri kuke ɗaukata matsayin sauna shasha wacce bata san abin da take yi ba, gashi nan yarinyar da kuka dogara da ita an samu wani matsiyacin la'ananne ya kashe ta, tsinuwar Ubangiji data Mala'iku ta tabbata akan shi" "Haba Hajiya" cewar Uncle Musbah. "Haba hajiyar uwarka, ji yaro ɗan nema nifa shi ya saka duk wani ɗan'daba nake Allah wadai da haihuwarsa domin irin masifa ne a duniya, gashi nan duk sun hana ƴan unguwarmu sakat da shegiyar satar waya kamar ɓeraku" Rai ɓace Uncle Musbah ya miƙe ya fice sai Nahyan ya bi bayansa. * Maamah da AA MAJ zuciyoyinsu tuni sun manne waje guda, sun aminta da juna fiye da tunanin Dig Johar da Ummimi wata soyayya suke shimfiɗawa a nutse da kuma cike da zakwaɗi da shauƙin juna. Har yanzu AA MAJ bai san Aafiyyah matsayin mata ba, domin ko kiss ya zurfafa da ya yi yanzu numfashinta zai fara sama-sama tana dafe kanta, idan ya ɗauki hanyar zuwa babban fada saboda tsoro da gigita sai ta fasa ihu ko ta suma, shi kuma yana Allah wadai da dukkan abin da zai taɓa lafiyar matar Maj sai ya haƙura. Dinner ta shirya tana duba agogo taga wajan 9:30 na dare lokacin ana ta sanarwa cewa a kula da yara da matasa, a yi siyasa bada-gaba ba, a gudanar da zaɓe cikin nutsuwa da kwanciyar hankali a guji bangar siyasa a kuma kula da yara, ana kira ga kowa akan ya fita zaɓe domin kaɗawa shugaba na gari kuma adali, a je a zaɓi mai taimakon al'umma ban da siyar da ƴan cin kai. Haka ɗan'jaridar yake ta faɗa daga gidan yari rediyon Idon mikiya goma daidai kuma za'a fara program domin matasa wanda za'ayi da Professor Abdul-Johar Marafa. Short skirt ne a jikinta sai wata ƴar riga iya ƙirji ko cibiya bata rufe ba, ta tufke gashin kanta kasa jiran shi ta yi ta miƙe ta nufi ƙofar bathroom ɗin. Bubbugawa ta fara a shagwaɓe ta ce "Ni dai ka fito" Buɗe ƙofar ya yi, ba tare daya fito ba cikin cold voice ɗin shi ya ce "My towel" ta fahimci manta shi ya yi a saman bed sai ta koma ta ɗakko ta ce "Gashi" kyakkyawan farin hannunsa ya fito da shi alamar ta bashi, sai ta miƙa masa ya yi caraf ya riƙe hannunta ya janyota cikin banɗakin da ƙafarsa ya saka ya tura ƙofar, jikinta ya ɗauki rawa tana ƙifta idanu ta ce "Wasssh It's so cold here" A tausashe ya rufe ta da jikinsa sai ya saki ruwan dake zuba wanda ya kasance warm water, ta yi saurin rufe fuskarta a ƙirjinsa tana zagaya hannunta wajan riƙe ƙugunsa a daidai kunnenta ya sauke numfashi yana fesa masa ruwa ya ce "Soldier' wife, aliyu's wife, Maj's baby" "Uhm Yaya" Ya saka tafukan hannunsa ya tallafo haɓarta ya ɗora kan shi a kan fuskarsa ta yana ɗan fiddo tongue ɗinsa wajan zagaye lips ɗinta da shi yana mata wasa romantically. Ta zubawa fuskarsa idanu a hankali ya matse ta da ƙirjinsa da yake buɗe ruwa na sauka ɗis ɗis ɗis, cikin nutsuwa ya sutale ƴar rigar jikinta, ƙirjinta ya bayyana ta yi saurin haɗe ƙirjinta da nasa saboda kunyar da ta ji, tudun ƙirjin Aafiyyah ta shige tunanin Aliyu, numfashinsa ya fara neman ɗaukewa daga ƙirjinsa, idan akwai wani abu da AA MAJ yake tsoro bai shige lossing Aafiyyah a rayuwarsa ba, ya tabbata Maamah ita ce rauninsa a matsayinsa na soja, mata kan iya ribatar maza musamman sojoji da aka yi musu wannan shaidar, amma shi dukkan ƙuruciya da balagarsa da mazantakarsa bata kowa mace sai ta Aafiyyah, wa ita kawai ya adana kwaɗayinsa tsayin shekaru. Ya ja numfashi ya dire idanunsa cikin nasa ya ce "waye ni wajanki" "My husband" Ta ce itama tana fiddo tongue ɗinta ta fara lasar nasa tongue ɗin da yake waje, hannunta ɗaya a saman mararsa tana shafawa tare da murzawa slowly slowly. Sai ya ji tana neman kunce masa notikan kan shi ya sake mannewa da jikinta suka ƙarasa har wajan sink madubi na hasko su ya ce "Waye ni?" "Mijina" "Again?" Ya ce yana zuƙar harshenta. "Mijin Safiyyerh" "Uhmm again Please" "My husbbyyy" Sai ya ƙara gudun ƙarfin ruwan, jikinsu ya jiƙe jagab dukkan jikinsu rawa yake yi alamar sun shirya amsar juna da buƙatar kasancewa da juna a lokacin. AA MAJ ya damƙi sumar kanta idanunsa rufe kamar yadda nata idanun yake rufe ya manne mararsu waje guda ya ce "Maa....mahhhh.... Who am i to You?" Ta yi shiru, ya sake goga mata mararsa da ƙarfi sai ta yi saurin ƙanƙame shi tana fitar da numfashi kamar zata mutu kayan S Bayero na motsa kansu a lokacin da ƙyar ta ce "My cubbyy my husbbyyy" "Oh i got it" ya ce. Sai ya buɗe idanunsa da suka sauya launi sosai yana mata wani irin killer smile mai narkar da zuciya ya zaro harshe ya kaɗa mata yana sake manneta da kyau sai ya shinshina wuyanta ya manna lips ɗinsa a wajan ya ce "You know i love you?" Kaf kaf kaf jikinta ke rawa saboda sarawar da kanta ya yi ta fara hangowa wani yana mata kwatankwacin abin da AA MAJ ke mata ta fara hango lokacin da yake gana mata azaba mai tsananin gaske ta fara hango sanda yake caka mata wuƙa, bata son rana Maj abin da yake so sai ta ji dole a wannan karan ko zata mutu ta bashi hakƙin shi "Matar Maj" "Mijin Manager" ta furta a lokacin da take sanya hannunta a.... Ba'a nan nasu na tsaya ba, lokacin ne ya ƙure a yi Manager a yi mini uziri kuma tausayin AA MAJ ne ya cika mini zuciya ƙila dai yau ya angwance ras😝 💥Chapter 12: Ume-kalsom "Yaya stop please!" Ta ce a ruɗe. A ƙirjinsa ta sauke hannunta tana numfashi sama-sama. A nutse ya riƙo ta cikin kwantar da murya a narke cike da wani irin fitinannan shauƙin so ya ce "ki kalla, ni mijinki ne, ke matata ce me kike tsoro?meke firgitar dake ne haka Madam? Are okay?" Ta girgiza kai idanunta a ƙasa cike da hawaye ta ce "Ka yi haƙuri, amma ba zan iya ba, ba zan iya ba mikam" ya dinga kallon bakinta da yake maganar, laɓɓanta sun yi jawur da su tare da yin wani pech yirrr musamman da ruwa ya jiƙa su, daman koyaushe kamar ta shafa jambaki haka lips ɗinta suke anytime. "Me ne ba za ki iya ba?" Ya tambaye ta, a lokacin da yake sanya tafukan hannayensa ya riƙo ƙugunta zuwa kusa da shi, yana sauke mata numfashi a fuska tare da sanya yatsa guda ya shiga zagaye fuskarta da shi, idanunsa ciki. "Ba zan iya abin da kake so ba" "Still dai, Maj bai fahimta ba" "I can't sleep with you" Sai ya ja numfashi ya ce "No need, ni zan iya ai, kar ki ji ɗar" Ta girgiza kai, tana ƙoƙarin yin baya, sai ya kasa bata damar yin hakan saboda wani irin azababben shauƙi dake fisgar zuciyarsa zuwa ga Maamah, shauƙin da bai taɓa nutsuwa ya fahimci cewa yana da shi ko babu ba, bai ɗauka yana da cikakkiyar lafiya da kuzari mai zafin har hakan ba, yana zargin kansa a lokuta mabanbanta idan ya ga mace bai ji yana developing any feelings a kan ta ba, bai taɓa jin sha'awar wata ɗiya mace a duniya ba, abokan shi sojoji sun sha attempted haɗa baki da mace ko zata ja hankalinsa amma ba su yi nasara ba, lokaci da yawa su kan kalle shi su ce. "Baka da cikakkiyar lafiya Maj" sai kawai ya yi gyatsine idan ya so, idan bai so ba, ko kallon su ba yayi, har blue films sukan sawa ya ji sounds ɗin a kunnensa amma bai taɓa damuwa ba. A duk sanda zai dawo gida ya ɗora idanunsa a kan Aafiyyah a lokacin ya ke sanin cewa shi rayayye ne, da numfashi a jikinsa har yanzu bai gama macewa ba, a ranar yini zai yi yana kallon picture ɗin Aafiyyah har ya ji nutsuwa, irin relief ɗin da Aafiyyah ce kawai ke samar da shi a zuciyarsa, ya jure zaman gida ba mace, ya jure zaman jeji babu mace, ya jure zaman barrack ba mace, tsayin kwanaki, tsayin satuttuka, tsayin watanni, tsayin shekaru sama da talatin da biyar ko bakwai, yana namiji kuma mai lafiya ya kasa tarayya da kowacce mace, sai ya ji cewa ba macace baya so ba,wacce ya bawa dukkan zuciyarsa ita yake buƙata a jikinsa, ita yake buƙatar ya sanya girmansa cikin duniyarta wacce sunna ta bashi dama, bai taɓa mafarkin samun Aafiyyah a matsayin matarsa ba, domin ya gama amanna cewa ita lil sis ɗinsa ce, amma zuciyarsa ta kasa hango masa kowacce ɗiya mace sai Maamah, wannan dalilin ya saka baya ƙaunar dawowa hutu domin yana shiga tsakanin azabar da baya iya jurewa sai ya shigo cikin bedroom ɗin Aafiyyah ya zuba mata idanu, ya raya daren hannunsa sarƙafe cikin nata yana kallon yadda take bacci peacefully. Tunaninsa ya dawo gare shi lokacin da ya ji tana cewa "Yaya...," Sai ya dube ta, duba na tsanaki wani abu na sauka a jikinsa ya ce "Ko dai ba ki yi na'am da auren bane?" "Kamarya?" Ta ce cikin raunin murya. "Look Maamah, ke ba yarinya bace kin fahimci me nake nufi ok?" Ta jinjina kai, hawaye na cika idanunta ita bata san me ya sa take tsintar kan ta a cikin wannan yanayin ba, ba auren ne bata so ba, ba kuma Aliyun bata so ba, ita birninta ma a yanzu bai huce taga sun zama abu ɗaya ba, ta cikawa Paaahh burinsa na ganin tsatsonta, amma ta gaza ta rasa meke going a cikin kwakwalwarta, tana da wayewa daidai ita wacce ta isa ta san mene aure me kuma ake nufi da aure, amma tsoro yana mata shamaki da abin da Maj yake buƙata, dole ta ji tsoro saboda tana yawan jin yadda dararen farko da ake yin huka dasu, amma nata tsoron na musamman ne, bata san abin ba bata san ya ake yi ba, amma reflection ɗin da take tsintar kan ta ciki shine yake ƙoƙarin tarwatsa tunaninta da nutsuwar da take ƙoƙarin sama musu ita da Maj ɗin, itama tana buƙatar mijinta. Rau-rau idanunta ta yi ta ce "Kana jin zafina a cikin zuciyarka ko? Kana jin kamar bana ƙaunarka?" Ta girgiza kai "Ba haka bane, amma ka bani lokaci ka ji?" Maj ya kasa magana, shi maganarta ma azaba ce a ckin zuciyarsa kamar ana yayyafin wuta haka yake ji a jikinsa ta marairace fuska ta ce "Please Yaya, give me some time" "Why Yaya?" Ya tambaya. Sai ta langwaɓar da kan ta zuwa gefe, tana yarfe hannunta cike da shagwaɓa wacce daman halin Maamah ce ta ce "I am sorry Hubby" "Uhm.... Huh..." Ya ja numfashi ya sauke sai kawai ya jata zuwa cikin jikinsa ya rungume ta, a ƙoƙarin samawa kan shi nutsuwa, fat fat fat haka zuciyarsa da tata suke bugawa at the same time, bugun zuciyar Maj dai har tsoro yake bata. Suna rungume da junan ta ji yana yi mata wani abu, ta fara jurewa jin ya tsananta ya saka ta yi saurin ɗago kai ta kalle shi tana faɗin "Washh" "Sorry, i never hurt you" Ta yi shiru a kunnenta ya raɗa mata "I want to..... I want to" ya rufe ido da ƙyar ya ce "I want to be okay with you, ba abin da kike tunani bane, kawai mu yi sharing warm ɗin jikin juna, agree?" Sai ta ɗaga masa kai, ya sumbaci goshinta ya sake sakar musu ruwa. Ya rigata fita daga cikin bathroom jikinsa sanye da bathrobe yana tsane kan shi da towel, ta bi bayansa da kallo bayan ya fita ta dawo da tunaninta ta zubawa madubin dake banɗakin idanu, ba tunani take ba, kan ta take kallo ba, ta sauya, wanne irin sauyi? Ita dai tabbas ta san cewa ta sauya, akwai kuma abin da ta yi missing a rayuwarta, abu mai tsananin muhimmaci a rayuwarta da duniyarta, what is this? Mene haka daya rabu da rayuwarta? Ta yi believing cewa idan babu abin, to babu ita, babu Safiyyerh without abin no Safiyyerh, nutsuwarta shine fahimtar me ta rasa a rayuwarta? Murmushi ta yi mai sanyi wanda ya haddasa lomawar dimples ɗinta, sai kuma ta ɓata rai wata kunya ta kamata sanda ta tuna ashe Maj ya kalle mata ƙirjin da take matukar ji dasu kamar rai, daurewa kawai take yi amma mu'amala da mutumin da take tunanin yayanta ne, mahaifa ɗaya ta samar dasu It's very difficult to her, nauyi take ji, girman abin take gani. Sai da ta shafe tsayin lokaci a banɗakin kafin ta yi wanka ta fito sanye da towel jikinta na ɗigar da ruwa, da sauri ta shirya bayan ta shafa oil ɗin S Bayero da haɗin humura da kwalacca masu sanya nutsuwa a zuciyar mutum, ta gyara sumar kanta ta ɗaure da ribbon. Sallah ta gabatar harda shafa'i da wutiri tana idarwa ta fesa turare ta fesa mouth mint, wardrobe ta je ta ɗauki rigar bacci D&G couples iya cinyarta ta sauka ba bacci take ji ba, sai ta ɗauki laptop ɗinta ta ɗauka da kuma wayarta ta nufi parlour ta zauna sai taga Maj baya ciki, program ɗin rediyon aka fara har ta fara danne-danne a laptop ta ajjiye saboda muryar mahafinta da ta ji wanda mutane da yawa sukewa kallon Professor Abdul-Johar Marafa madadin Dig Abdul-Johar Marafa. Bayani yake yi sosai akan zaɓen da za'a gudanar na ƙananan hukumomin da suke jagorantar Kano/Nigeria yana kira tare da gargaɗi ga matasa akan su guji tayar da husuma a wajan zaɓe kowa ya yi zaɓe ya koma gida cikin iyalansa, masu kula da harkokin zaɓe suji tsoron Allah wajan kula da hakƙin al'umma na daga abin da suka zaɓa, a kare musu ƙuri'unsu har zuwa inec a guji tayar da fitina kar a sake kuɗi ya rijiyi mutum wajan siyar da kimar shi ta ɗan adam a kiyaye shaye-shaye ko shan abin da zai gusar mak da hankali har ka aikata ɓarna.... Haka Dig Abdul-Johar ya dinga bayani yana janyo hankalin mutane cikin siga ta siyasa. Aafiyyah wayarta ta ɗauka ta kunna network ta shiga Facebook, sai a lokacin ta ha followers ɗinta har sun je 1.m, ta jima rabon da ta yi rubutu. Sai ta shiga wajan da aka saka what is on your mind? Photon Dr Abraham Denial David ta ɗakko ta yi posting tare da caption ɗin “Cikar mafarkin kowanne matashin ɗan Kano” Within 2 minutes, sai comments sama da 200 a lokacin gudu. Wani kira yake who be this? Wani ya ce shima har da shi a masu neman takarar, wani kuma ya ce bayan ubansa Denial David ya mulki Germany matsayin shugaban ƙasa, shine mu kuma zai mulke mu? Wani ya ce, ai sun saba satar kuɗin jama'a, ka sani ko karayar arziƙi ce ta same shi? Wani ya sake replied da "An ce fa Abraham ɗin ba musulmi bane" Ta dinga duba comments ɗin sai ta ji ta karaya, amma akwai matured people da suke comments tare da reposting. Wani suna ta gani Alhassan Abraham Denial, ya yi liked posting ɗin, ta yi saved sunan a kanta, sai taga Ibrahim Qasim ya yi like ya kuma yi comment da "support" wani mutum ya ce "Ni dama mai kamfanin Arɗos group aka bawa mulkin nan, saboda yana da tausayin talakawa da ƙoƙarin taimako ga sauƙaƙawa mutane wajan siyan kayansu, ni kam hundred percent zan yi supporting nasa."Who is the owner of the company?" A new person a conversation ɗin ya tambaya. "Ban sani ba, ba wanda ya san shi ai" daga nan aka dinga comments yawancin mutane ra'ayinsu akan Hon Maɗatai yake sai masu Eng Ali wali, da yawan matasa kuma ra'ayinsu goes to Dr Abraham Denial David. Highlighting ta shiga, sai taga just now posted ɗin Alhassan photon Arɗos group ya saka da caption ɗin "Kuna son sanin me kamfanin?" Mutane suna ta faɗin Yes, yes sai wani me suna Ibrahim Khalil ya ce "Don't do this Alhassan" Ta ji ranta na ɓaci, sai ta nufi X nan ma ta yi posting Instagram ne da Tiktok ne daman bata yi bata ra'ayin shi. Bayan ta gama ta ajjiye wayar ta samu kan ta da yin addu'a sosai ita kawai tana buƙatar Dr Abraham Denial David ya samu nasara haka kawai Hon Maɗatai da Eng Ali wali ba su yi mata ba. Kashe Laptop ta yi ta miƙe ta nufi bedroom, har lokacin Maj baya ciki sai ta damu ga lokacin ya ja, kawai ta kwanta abin ta. Cikin dare ta juya kaɗan sai ta ji wayam babu shi ta duba 3:20 na dare, ga gidan ya yi mata girma miƙewa ta yi ƙafarta cikin bedroom slippers, a hankali take tafiya ta zo tsakiyar parlour ta ji an rungumeta ihu za ta yi ya saurin cewa "Shiiii" "Hubby" Ya yi shiru, sai ta kunna haske suka haɗa ido ta dinga kallon shi from head to toe, baƙaƙen kaya ne a jikinsa hannunsa riƙe da bindiga "Aiki cikin dare?" Ya ɗaga mata gira, bai bata damar magana ba ya ja hannunta zuwa cikin makeken bedroom ɗinsa ya ce "ki kwanta nan, zan duba abu ok" Ta jinjina kai, idanunta cike da bacci tana kwanciya bacci ya ɗauke ta, cikin baccin ta jita a jikinsa da kuma abin da yake mata, ta yi saurin buɗe ido tas, ƙirjinta na bugawa subhi ya kusa, sunayen Allah take kira da ƙoƙarin ganin ta jure, again wannan reflection ɗin take gani, ta yunƙura a gigice jin yana ƙoƙarin shigar ta duk da bai ma ɗauki layi ba. "Yaya Please, don Allah ka bari wayyo" take faɗa jikinta duka ɓari yake yi. Muryarsa na breaking ya ce "Ki cire tsoro Safii, ina buƙatar ki?" Girgiza kai ta shiga, sai yaga jikinta ya saki zufa ta jiƙata sosai ya zare jikinsa ya mirgina ya janyo jikinsa bayan ya ƙara gudun ac, ya dinga shafa kanta cike da kulawa yana matsa hannunta da danna ƙirjinta. "Hmmmmmm" Ta ja numfashi sai kuma ta yi saurin razana "Ban so, ban so" ta ce a gigice. "Shhhh, na bari ok?" Sai ta buɗe ido suna haɗa ido gabanta ya faɗi taga idanunsa jawur jikinsa zafi zau sai ta fashe da kuka sosai ta ce "Ka yi haƙuri don Allah, don Allah Maj" bai magana ba sai bayanta kawai yake bubbugawa yana jin kamar ana tsaga masa mararsa, kamar mararsa za ta yi bindiga saboda ciwon da take yi masa. Shiru ta yi saboda abin da take tunani "Are you ok?" Ya yunƙura ya jingina da ita a frame ɗin gadon. "When you are with, am completely ok" ya ce silently. "To yaya, gobe zan bari ka yi kaɗan ka ji? Ina jin tsoro ne" "To zan jira a bani kaɗan ɗin" ya ce yana lakace karan hancinta. "Kaɗan fa?" Ya ɗage mata gira, sai ta ji tausayinsa sosai ganin kallon da take yi masa ya ce "To ƴar Dig Abdul-Johar" "Are you ok?" "Maybe..." "How can i help you?" Ya ce "Sleep with me" "Zan yi, amma banda...," sai ta yi shiru sai ya kwanta kawai bai ce komai ba, domin nauyi bakinsa yake masa daman sharrin soyayya ce da kan iya juya mutum da sauya masa ɗabi'a shi ya sa har ya iya buɗe bakinsa da zuciyarsa ga Maamah. A hankali ta bi jikinsa ta kwanta ta shige sosai, sai ta ji ya kama hannunta a kunne ya ce "And help me with this...," ya ce yana ɗora hannunta a mararsa ta runtse idanunta saboda tsananin kunya ya ce "Common matar maj" * Morning/news Kamar kodayaushe VOA sune suka fara bayyanar da harin da aka samu da aka kaiwa Hon Maɗatai again, amma ba'a yi nasarar kashe shi ba, kuma aka bada tabbacin Scorpion ne ya kai harin saboda shaidar da yake bari a kodayaushe. Nan take sanarwa ta fita dasa hannun gwamnati akan janyo hankalin jami'ai na ganganci da rayuwar manyan mutane da suke yi, kuma gwamnati ta yi Allah wadai da rashin iya aiki daga jami'ai da suke da alhakin kare rayukan ƴan siyasa da dukiyoyinsu kai tsaye kuma da Fid ake, domin an daina batun SSS tunda daga cikin SSS aka ware team guda masu matsayin Federal investigation department alhakin kama Scorpion ba'a kan DSS ko SSS yake ba, ba kuma akan National security Organisation (NSO) ba kuma hakƙin hukumar NSA bane ba kuma hakƙin NIA bane balle kuma DIA ba, ba kuma gabaɗaya aikin akan FCID ne wannan dalilin ya saka tun 7:00 Aafiyyah ta bar gida lokaci AA MAJ na bacci bai san meke faruwa ba. Aafiyyah ta zubawa Muhammad idanu wanda yake numfashi a hankali saboda wahalar da aka gama gana masa a yanzu, fitar Dig Abdul-Johar kenan da shi da sauran team ɗin ita kaɗai ta yi saura. Black ɗin Suit ce a jikinta mai riga da wando ta yi rolling kanta da red ɗin vail takalmin ƙafarta ma red ne, black shade glasses ne a fuskarta lips ɗinta sun yi wani yirrr dasu sai glowing suke yi. Ta harɗe ƙafafuwanta tana study ɗin Muhammad wanda suke tunanin Scorpion ne kuma Mutallab cikin nutsuwa ta ce "waya taimaka maka ka fita daga wannan wajan har ka kaiwa Hon Maɗatai hari?" Bai kulata ba, kan shi ƙasa ƙirjinsa na ɗagawa a hankali. "Har yanzu jikinka bai gama laushi ba ko?" "Leave!" Ya ce a ruɗe duk sanda zai ji muryarta zuwan shi Lagos yake tunawa. "Scorpion" ta ce, cikin sweetness voice ɗinta sai ta miƙe tsaye ta dawo kusa da shi, ta duƙa dab da shi ya yi saurin rufe idanunsa ya haɗe fuska tamau "Kawai na ji ina jin tausayin ka yau, ka bani amsa ya aka yi ka fita? Akwai munafukai ne cikin team ɗin mu ko ya?" Ya share ta. "Me ya sa kake son kashe Hon Maɗatai da Eng Ali wali?" "Dalilin daya saka na kashe Alhaji Lawwalli da Alhaji Saduƙu" ya bata amsa. "Me dalilin?" Ta tambaya, tana bin zagayayyiyar baƙar fuskarsa da kallo, tana mamakin yadda take jin muryar Kimiyya a cikin bakinsa, sai ta fara tunanin ai Muhammad ta sani da Kimiyya's voice, me ya sa ta ji muryar yanzu a wajan Scorpion? Bayan haka kamannin Scorpion yana mata kamar wani, ta yi shiru tana tunani. Sai ta katse tunanin saboda kan ta daya fara ciwo "mene dalilin?" "Ki je ki tambayi Hon Maɗatai da Ali wali, ki ce musu dalilin daya saka na kashe Alhaji Lawwalli da Alhaji Saduƙu shine dalilin daya saka nake neman rayuwarsu, wannan dalilin daya faru a garin Rano har suka sauya mahaifa saboda wannan dalilin, kuma suka sauya daga fulani zuwa zalla Hausawa, sun san dalilin sai su faɗa miki komai, daga nan sai ki zo wajena ki gani, akan gaskiya nake bibiyar rayuwarsu ko akan ƙarya, daga nan zan ga kalar naki adalcin za ki sake ni ki kama su ne ko za'a ba ki cin hanci" ya ce yana fesar da numfashi sai ga jini ya fita daga cikin hancinsa. "Ka faɗa mini waya fitar da kai jiya daga cikin wajan nan" "Hon Maɗatai" ya bata amsa. Da sauri ta miƙe tsaye jikinta na rawa ta ce "What? Hon Maɗatai akan wanne dalilin, mu da muke kare rayuwarsa shine ya fitar da kai? Akan wanne dalilin kenan kuma?" "Gudun kar na fallasa asirin su" Bata saurari Muhammad ba, ta miƙe da sauri tana ciro. Id card ɗinta, da bindigoginta guda biyu ta soka cikin aljihu ta saka shade glasses ɗinta, saƙo ta turawa Dig Johar, kana ta yi waje. Muhammad ya bi bayanta da kallo musamman hips ɗinta yana lumshe idanunsa ya furta "Sophie" Tana fita mota ta shiga bata tsaya jiran sauran team ɗin ba, cikin ƙwarewa a driving ta shiga kwarara gudu saman kwalta, tana ta kiran number Kimiyya amma baya ɗauka. Daman duk wani waje da Hon Maɗatai ke zama Fcid sun sani, a ƙofar gate wasu securities suka tsayar da ita, id card ta nuna musu sai suka sara mata ta shiga, ko gama daidaita parking ba ta yi ba ya fito cikin sauri-sauri tana catwalk haka ya shiga cikin parlourn idanunta rufe bata lura da mutanen da suke wajan ba ta nufi wajan Hon Maɗatai ta ce "You are under arrest Hon Boɗejo Maɗatai" ta ce tana ɗorawa Maɗatai bindiga saman kan shi. "Waya ba ki permission na kama shi? Akan wanne dalilin? Ina arrest oder?" Ya ce yana zaro bindiga. Without looking at him ta ce "Sp Ghali Gaddafi, shut up" Domin sarai ta ɗauki muryarsa a cikin kunnenta ta dubi Hon Maɗatai ta ce "Alhaji Boɗejo ko?" "Waye haka?" Maɗatai asked. Tana sake daidaita bindigar akan Maɗatai ta ce "Kodayake a Fs world kake matsayin Alhaji Boɗejo ko? A siyasa kuma Hon Maɗatai? Good nice one. Safiyyerh A Marafa bata zo a matsayin Manager ta Fs world ba, yanzu ina matsayin Safiyyerh Abdul-Johar Marafa staff a Federal investigation department, bana jira wajan bani permission domin ina da hujjar kamaka akan abin da ka aikata" "Safiyyerh cire bindigar nan" Cewar Sp Ghali. Sai ta zaro ɗaya bindigar ta ce "Sp Ghali Gaddafi shut up or else....," ta taune lips ɗinta ta ce "Matsayinka daban, nawa daban, kuma ina sama da kai wallahi ka sake yi mini magana zan harbeka tabbas" Hon Maɗatai kallon Aafiyyah kawai yake yi idanunsa jajur ya miƙe tsaye ya ce "Dame kike taƙama? Jami'an FCID bamu suke bawa tsaro ba, yanzu kira ɗaya zan saka a cire ki gabaɗaya stupid girl, ke ba ki da ɗa'a ko? Kina crossing limit ɗinki? Akan wanne dalilin ma za ki zo mini gida?" Ta ce "Ka saka a fitar da Scorpion saboda kada ya faɗi gaskiyar abin da kuka aikata kai da sauran mutanen? Saboda kada ya fallasa asirinku na abin da kukai a garin Rano? Me kuka aikata a Rano?" Ras! Gaban Hon Maɗatai ya bada sauti ya buga sosai ta cikin ƙirjinsa, ya nemi yawo a bakinsa ya rasa. Ya dinga nanata Rano a zuciyarsa jinin jikinsa ya tsinke ya dinga gudu kamar yadda gudun bugun numfashinsa ya ruɓanya tashin hankali ƙarara ya bayyana ta cikin zuciyarsa sai kuma ya shanye ya ce "Rano?" Ta ce "I can repeated the word in capital latters RANO" "Bani da haɗi da Rano" "Ok haka ka ce?" Ya faki idanunta ya ƙwace bindigar, Sp Ghali ya matsa zai kwace ɗayar ta yi saurin saka masa ƙata tare da juyawa ta ɗauke shi da mari, cikin zafin nama kuma ta daki ƙirjinsa ta hannunta ta kwarfe shi ya faɗi ƙasa tana poiting ɗin shi da hannu ta ce "Kai ne karan ƴan siyasa ko? Irin kune kurɓatattun jami'an tsaro? Useless ka yi asara wallahi" ta dawo kan Hon Maɗatai ta ce "Zan cigaba da bibiya a yanzu na ji zan fara bincike akan ka, da Rano wataƙila Scorpion yana da gaskiya ranar dana samu shaida a fili wallahi ranar a wajena zaka kwana. Na tsaneka tun kafin yanzu wallahi sai ka wulaƙanta baka da gaskiya Allah Ya hanaka mulkin da kake nema" tana cewa haka ta ƙwace bindigar ta yi waje. Ajjiyar zuciya ya sauke zufar da yake ɓoyewa ta shiga gangaro masa a jiki ya jiƙe jagab, baya iya bacci duk ranar da zuciya ta bashi damar tuna RANO ya dubi Sp Ghali ya ce "Ya aka yi Scorpion ya fita?" "Ban sani ba" "Sp Ghali Gaddafi waye Scorpion ɗin nan ? Wace Safiyyerh?" Sp Ghali Gaddafi ya ce "Muhammad Mutallab Abdullahi tare muka yi makarantar Fgc da shi, aji biyu ne tsakanina da shi zuwa ɗaya na manta, yana da ƙwazo sosai fiye da tunani baya kula kowa karatu kawai yake yi,da mutum ɗaya yake mu'amala shine Qasim Ibrahim. A lokacin kuma Safiyyerh Abdulwahab ta shigo rayuwarsa, baya son kula mata domin mazan ma baya kula su, ya yi mata wulaƙanci sosai ko'ina ta ce bestie ita dai bestie a kan shi ta daina fahimtar komai, har faɗa da duka ake yi mata a gida, kamar da wasa kuma aka ɗaura auren su a makarantar mahaifinta ya ce bai yadda ba sam ita kuma ta bijire a haka har ya fara kulata Mutallab kuma aka kore ta a makaranta saboda faɗuwa exam da ta yi har sau uku Fgc kuma basa jure zama da daƙiƙin ɗalibi. Ni kuma a lokacin hankalina a tashe yake" "Me ya sa hankalinka ya tashi?" "Saboda duk duniya babu wacce nake so a rayuwa sama da Safiyyerh Abdulwahab ina son ta kamar rai, gashi kwatsam Mutallab ya raba ni da ita, ya hana ni cikar muradina" "Ita kuma wannan yarinyar fa?" Hon Maɗatai ya tambaya. Sp ya ce "Safiyyerh Abdul-Johar Marafa shine cikakken sunanta da ita da murgayiya Safiyyerh Abdulwahab aminan juna ne, a lokacin ba'a iya banbance su saboda kowacce da Safiyyerh Abdu take amfani, sai aka sauyawa Safiyyerh Abdul-Johar Marafa suna zuwa Aafiyyah tun bayan hutun da muka yi na daina ganin ita Aafiyyah da Safiyyerh har zuwa sanda aka ce Mutallab ya kashe Safiyyerh na yi kuka sosai na shiga tashin hankali, kuma a lokacin na ji dukkan wata soyayyar da nakewa Safiyyerh ta koma kan Aafiyyah na ji duk duniya yanzu ita nake so, kamar yadda na ɗauki alwashin ba zan taɓa barin wanda ya kashe Safiyyerh ba" Hon Maɗatai ya dinga kallon Sp Ghali sai ya yi shiru can ya ce "Kuma akwai tabbacin shi ya kashe ta?" "Sosai" cewar Sp Ghali. Hon Maɗatai ya kalli amintattun mutanen nasa hadda Musbah ya ce "Ku je zamu tattauna zuwa dare tunda gobe da safe ne ya kama asabar kuma ranar zaɓe" Fita suka yi sai da suka je bakin a hankali Musbah ya juyo ya kalli Hon Maɗatai sai ya yi murmushi ya fita. * Ko ƙarasa buɗe motar bai yi ba a sukwane ya fito ya nufi motar Eng Ali wali yana zuwa ya damƙi wuyan Ali wali ya ce "Kai ne ka je ka fitar da shi ko? Saboda ya kashe ni ya samu mulki kai ne?" Zuciyar Ali wali na kusa shima ya damƙi wuyan hon Maɗatai ya ce "Kar ka raina mini wayo Boɗejo idan na fito da shi mene ribata tunda har ni zai kashe?" "Ƙarya kake yi" "Na ji ɗin, ni na fito da shi" Dambe suka fara yi suka daki juna babbar riga ta dinga tashi sama da ƙyar aka janye su hon Maɗatai ya ce "Sai ka shirya bada bayanin abin da ya faru a Rano don mai cin uwarka" A hargitse Ali wali ya ce "Don me nanawa ubanka dai, kuma bani kaɗai zan yi wannan bayanin ba" Huci suka yi shi dai Sharfaɗi ya yi shiru kawai sai kuma Ali wali ya ce "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un! Wane ya fito da maganar Rano muna cikin kwanciyar hankali wallahi da ƙyar idan gudawa bata ɓata mini wando ba, cikina sai kaɗawa yake yi" Hon Maɗatai dake jingine da mota ya juyo ya ce "Daga mutanen Rano har na Kano babu wanda ya isa ya faɗi shaida akan haka, duka shaidon sun mutu, mutum ɗaya ya ji maganarmu mistakenly shi ne Ashraf ɗan wajan Alhaji Baihaƙi Sharfaɗi kuma Ashraf is no longer alive, baya raye kenan har gaban abada babu wanda zai ji tarihin garin Rano" "In sha Allah" cewar Eng Ali wali. Sai Sharfaɗi ya ce "Zan tafi ni" "Minti biyu Sharfaɗi, ina buƙatar 1B a yau ɗin nan, domin zan sallami mutane da su, zan yi harkar zaɓe a daren yau zan fasalta komai" in ji Eng Ali wali yana duba wayar hannunsa. "Tabɗin" cewar Sharfaɗi. "Bangane tabɗin ba" Sharfaɗi ya ce "Dole sai Manager ta saka hannu kafin ya je wajan Accouter kuma yarinyar nan bana jin zata saka hannu a fitar da kuɗi har biliyan ɗaya ba tare da an faɗa mata abin da za'ayi dasu ba" "Ban fahimta ba, kuɗinmu ne fa ina jin saboda haka muka ɗora ta matsayin Manager ko? Me kake nufi Sharfaɗi? Ban fahimta ba" "Aliyu ka fahimta mana, ka san yarinyar nima dai ba komai nake fahimta zan bin cika mu ji, amma a shawarce ka cire kuɗin daga cikin kuɗin hannun jarinka" Rai ɓace Ali wali ya ce "Sharfaɗi ba zan cire daga cikin kuɗin hannun jarin nawa ba, ana kamfani zan cire" Sai Sharfaɗi ya ce "Ok Aliyu, i will try my best amma idan ta hana dole a bari fa, idan aka matsanta a bin ɓoye ne zai fito fili" "Ka faɗa mata cewa kaya za'a kawo" "Jiya muka fitar da dukkan list da jadawalin abin da kamfani yake buƙata mun tura kuɗin tare da jagorancin masu kawo mana kaya, kaga wannan ma ba zata yarda ba" Ƙwafa Ali wali ya yi "Ni fa sai na kashe yarinyar nan akan wannan kuɗin tsaf wallahi" A lokacin Hon Maɗatai ya ce "Allah Ya baka sa'ar kashe ta, saboda kai dauɗa ne shine zaka kashe ta idan ka kashe ta to gabaɗaya mu ka kashe" Sharfaɗi ya ce "Ka yi rancen kuɗin ta ƙarƙashin Arɗos group mana" "What? Ina na san suwaye masu kamfanin?" Sai Maɗatai ya ce "Kamfanin Dr Abraham Denial David ne" Da mamaki duka suke kallon shi * Ƙarfe 4:00 media ta ɗauka cewa Arɗos group kamfanin mai neman takarar kujerar ɗan majalissar tarayya ne ƙarƙashin jam'iyar NNY New Nigerian Youth wato Dr Abraham Denial David sai mutane suka dinga mamaki mene haɗin Abraham da sunan fulani kuma Arɗo? Kafin wani lokaci ko'ina ya ɗauka facebook, Instagram, X aka dinga cewa babu wani nargatacce daya kamata ya samu wannan kujerar sama da Dr Abraham Denial David. Aafiyyah na office ɗinta a lokacin take duba komai nan take ta sake posting na supporting ɗinta tare da kira ga matasa a lokacin Kinal na online itama ta yi reposting na posted ɗin Aafiyyah aka fara yaɗa munafa ko'ina poster ɗin Dr Abraham Denial David ne shi yana can ba tare da ya san meke faruwa ba. Number Qasim ta kira yana ɗagawa ta hau faɗa sai ta ji ya ce "I slept off early yesterday, was feeling a severe headache" "Allah Ya sauwaƙe ina jiran ka" "Right now my dear" A lokacin Kimiyya na cikin asibiti zaune hannunsa riƙe da baby gal ɗin yana jijjigata yake waya da Aafiyyah. Har zuwa lokacin da ya ce "Masifaffiyar yarinya kawai" ta cikin wayar ta ce "Qasim ni ce yarinya?" "A'a ni ne" ya ce yana dariya. Raɗau ta ji muryar Aafiyyah a kunnenta dake a speaker ya saka, a hankali ta ɗago ta kalli Kimiyya da kuma wayar. Ya ajjiye wayar jin idanu a kan shi suna haɗa ido ta zaro masa idanu ya yi murmushi ya ce "To ya? Zan tafi" ta jinjina kai. Ya ajjiye jaririyar ya nufi waje sai ya ji ta ce "To ba za ka yi fira dani ba?" "Ke da kike zaro mini ido?" Ta ce "Ai laifin idona ne ko?" Ya tuntsire da dariya ya ce "gaskiya kam, ai bakya son hira ko tunda ni kaɗai nake magana kullum" Ta zubawa fuskarsa ido shi bashi da wata damuwa kenan sai ya ɗaga mata gira ta ce "Ai ina ji maganarka fa, Allah da gaske ina ji" "To kin kyauta" "Zaka dawo ba?" Ya jinjina kai ya ce "E, gobe zaɓe maybe jibi" "To ka tafi dani" Ya zaro ido ya ce "Kai, na saka ki a ina? Bayan kisan matsalar dake tare dake ko?" "Ai ni ba ƙatuwa bace sai ka ɓoye ni a riga ko? Go with me" Ya yi dariya ya ce "E kuma kin kawo shawara bari na ɗakko babbar rigata ko?" Ta kalli babyn ta ce "Ka taho da zani ka goyata a bayanka ka ji?" Ya dubi jiriyar kyakkwa ajin ƙarshe ya ce "Iya ita zan goya ko har ke?" Sai ya ga ta yi murmushi ta ce "Allah Ya shirya ka, Allah kowa Allah Ya shirya ka" Yana yin waje ya ce "shirin carbi ko na jigida? Bari na ɗakko zanin goyan da babbar rigar a bayana babba ne duka zai ɗauke ku" ta bi bayansa da kallo tana yin dariya ƙasa-ƙasa. * Aafiyyah na shan tea taga ya faɗo office ɗin kamar daga sama ta juyo ta kalle shi sai bai kalle ta ba, yana ta muzurai idanunsa jajur sai warin sigari yake yi. "You again?" Ta ce tana kallon Moh da tunanin Muhammad ne. Ya ƙarasa wajanta ya duƙa fuskarsa dab da tata ya zuba mata rinannun idanunsa yana fesa mata numfashi, sai ta ji gabanta na faɗuwa sosai domin yi ya yi kamar zai haɗe fuskokinsu sai kuma ya yi baya ya zauna saman table yana yi yana duba agogon hannunsa da kuma wayar hannunsa kamar mai gadinta ko mai bata tsaro, almost 20 minutes ya sake miƙewa ya nufi bakin window ya leƙa ita kuma ta zubawa bayansa ido, a hankali ta miƙe ta nufin leƙawa taga me yake kallo, sai ta samu kan ta da zubawa wuyansa ido a hankali ta miƙa yatsa ta taɓa wuyansa tare da shafowa, ya jita sarai bai kula ta ba, sai taga ya ɗakko waya yana dannawa can ya mayar, ta sake miƙa hannunta zata shafo gefen fuskarsa ya yi saurin juyawa. Suka haɗa ido kallo ɗaya ya yi mata ya ɗauke kai. "wai dame kazo?" "Biyo bayana, babu buƙatar maimaita miki don zan iya kwaɗa miki mari" haka taga ya turo mata ta wayarta ta ɗago ta kalle shi fuskar nan kamar ta yi bindiga babu annuri, sai ya nufi waje ta bi bayansa motarta zata shiga ta ji ya yi gyaran murya da yatsa ya nuna mata motar da yake ciki, ji ta yi kawai tana bin umarninsa tamkar shi ne AA MAJ, ta shiga motar ya ja ta a guje suna tafe yana busa sigari Aafiyyah kamanninsa kawai take kallo can ta ce "Baka damu da lafiyarka ba ko?" Ya share ta, har ƙofar gidan Dig Johar ya sauke ta tana fita ya juya daidai nan motar Kimiyya ta ƙarasu shiga ta yi ya jasu zuwa gidan Dr Abraham Denial David da yake amsar baƙi. Bayan sun gaisa ta ce "Sunana Safiyyerh Abdul-Johar Marafa, wannan kuma abokina ne Qasim Ibrahim" ta ce tana nuna kimiyya. Sai Dr Abraham ya kalli Kimiyya tamkar bai san shi ba ya ce "Allah sarki, sannu yaro ko?" "Good evening sir" cewar Qasim yana kashewa Dr Abraham ido, shi kam ko ƙara kimiyya bai yi ba. Aafiyyah ta faɗawa Dr Abraham Denial David komai na buƙatar taimakawa a tafiyarsa ya ce "To Abraham na godiya, how can i help you?". Ta ce "Addu'a da goyan baya" ya dinga kallon ta kawai bai ce komai ba, ana haka Alhassan ya shigo yatsun ƙafar Aafiyyah kawai ya kalla ya ji gabansa ya faɗi, sanda na a kalli fuskarta neman ƙwarewa ya yi da sauri ya juya yana dafe ƙirji, Qasim da Abraham suka bi bayan Alhassan da kallo Aafiyyah kuma bata san ma waye ba. Sai ta yi masa godiya ta miƙe ta fita, Qasim yana ƙoƙarin fita ya ji an murɗe masa kunne ya ce "Auchhh Papi" Abraham ya ce "Baka da gaskiya Qasim tabbas" ya rungume mahaifinsa ya ce "I love you Papi" Suna tafe a hanya shi kuma sai kallon Aafiyyah yake yi cike da ƙauna ta ce "Daina kallo na" "Naƙi" ya ce. "Me ya sa kake kallon matar Maj" "Uhm" kawai ya ce. Sai ta juyo sosai kamar baturiya zata kama hannunsa ya yi saurin cewa "Sannu sannu kar ki taɓa ni to, naga ke da sauran ki sosai da sosai" "Dame zan saka maka ne Qasim?" Bai kalle ta ba, bai kuma ce komai ba har suka yi nisa can ya sauke numfashi ya ce "Ba duk abin alkhairi ake buƙatar mutum sai ya saka ba. Idan nace miki ina so ki saka mini da wani abu gani nake kamar ban miki adalci ba. Adalci shine na bari lokaci ya zo da abin da za ki saka mini da shi. Idan ma hakan bai yiwu ba, na tabbata idan Allah ya ga sahihancin son da nake miki zai saka mini. Domin duk abin da za'a yi shi da zuciya ɗaya yana da sakayya komin daren daɗewa" * Aafiyyah ce ta fito daga cikin kitchen hannunta riƙe da bowl na fruit wata riga ce a jikinta mai kama da bra sai wando iya cinyarta skin ɗinta sai ɗaukan idanu take ƙirjinta ya cika sosai a tsattsaye ga mazaunanta tubarakallah tun daga nesa take murmushi ganin ya fito daga shi sai gajeren wando alamar ɗakin motsa jiki zai shiga ta ƙarasa ta shige jikinsa tana rungume shi ta ce "I miss you hubby" hugging nata back ya yi, kana ya zare ta a jikinsa yana amsae bowl ɗin ya caki pineapple ya kai bakinsa ta ce "Yaya don Allah yau ɗaya ka ɗan goya ni wallahi na gaji da yawa" Ya buɗe ido ya ce "What?" "Uhm goya ni" Ta ce tana zagaye waist ɗin shi ta ce "Ina son Maj,ina son mijina" "You are not serious Saffi" Sai ta marairace masa tuburan hadda kuka sosai tana neman kwanciya ta yi masa bori, bai ɗauka sangarta ya kai haka ba ya yi sak yana jin wani irin shauƙi na musamman sai ya duƙa ƙasa ya ce "to hau" ya nuna mata bayan nasa, ƙoƙarin hawa ta yi sai ta ji ya sunkuce ta yana juyi da ita a parlourn ta ƙanƙame shi tana dariya, ya nufi training room ɗin da ita ita kuma ta fara shafa ƙirjinsa ya kunya ya kalle ta "No one, but u" "I love you Maj Aliyu Abdu Marafa" "Maj Aliyu Abdu Marafa loves Sofia" Sai ya ji ta fara kissing ɗin shi tana masa wani irin abu romantically suka fara kissing juna * A daren dukkan mazaɓar da za'ayi zaɓe a cikinta ƴan'daba sun bi sun manne bana da posta ɗin Hon Maɗatai da Eng Ali wali ko'ina sune. Don haka Moh ya sulale ya nemo posta ɗin Dr Abraham Denial David ya ajjiye wuƙaƙe da kayan caji yadda zai ji daɗin rashin kirki so yake tsakiyar dare shi da su Mangal da Goje su fita ko'ina babu wani shege. Tana sanye cikin zumbulelen hijjabin Mama Zaituna tana ɗaga ƙafa da ƙyar ta nufi banɗakin kamar koyaushe bata ma da lafiya zazzaɓi take yi jikinta babu ƙwari wata yunwa take ji, yau ya riga ta shigowa domin tana shiga ta samu Ɗan'yaro tsaye a banɗakin suka haɗa ido ya yi mata murmushi yana rufo ƙofar ya saka sakata, domin yau har wani tsumi ya sha na musamman ya zame jallabiyar jikinsa yana karkaɗa kugu ya ce "Wclm habibaty madarar zuciyata na yi kewarki ƙwarai tamkar yaron daya rasa nonon mahaifiya" ya ce yana riƙota zuwa jikinsa ya rungometa "Yaya ina yini?" Saudat ta ce a hankali idanunta a ƙasa Ya riƙo fuskarta ya ce "Haba zuciyar Ɗan'yaro ɗan almajirin Malam Abdullahi, yaushe za ki daina ce mimi yaya kina hukunta mini zuciya da sunan yaya nan, ni ba yayanki bane kin ki Saudena?" "To me zan ce?" "My suger za ki ce, ni ai abin da ɗinki ne ko Saudat ɗina?" "To my suger" Ɗan'yaro ya tallafe zuciyarsa ya ce "Kin ji sunan nan a bakin ki? Subuhanallahi! Sake faɗa na ji" Ta yi murmushi ta ce "My suger" "Saudat da kin yi ilimi ba ƙaramar mai ƙwazo za'ayi ba, kin ci abinci?" Ta girgiza kai ta ce "ai kasan kai ne kake bani bacci har na ragewa Zaituna, Malam baya ciyar damu, Mama bata da kuɗi kuma bata aiki" "Sorry agwalumata, yau ai ke amarya ce harda gasasshen nama, hope ba ki faɗawa kowa abin da yake tsakaninmu ba? Kuma ba'a san ina shigowa banɗakin gidanku ba" "Ba'a sani ba" Ya lakato wuyanta da bakinsa sanda yake zare mata hijjabin ya ce "Yau sauri nake mu fara shan iska mu ji daɗinmu sai ki shiga ciki ko?" Ta jinjina kai, abin da ya saba yi bata shine yake mata yanzu, sai ta ju babu zafi ta saki jiki ta sakankance waro idanu ta yi jin yana mata shigar sauri ta yi saurin cewa "Wassh yaya bana so ka bari don Allah" ya ce "Bakya son me? Ai ba ki isa ba Saudat ina ciyar dake a lokacin da iyayenki suka gaza ciyar dake kina ganin haka zata dakon wahala da shuka ki a banza? Ba salallammme bane ni, dole a yi mini ramako sabgar ban gishiri na baka manda ce" bata ƙarasa magana ba ta ji ya cusa mata tsumma a cikin bakinta, ta kasa kuka sai hawaye da harbe-harbe amma haka ya banƙare ta kamar kaza, shi ma ɗin a tsorace yake amma yadda ake labarta masa sabgar ya ji dole yau ya ɗanɗana, giyar ƙuruciya ke ɗiban Ɗan'yaro idanunsa jajur wata ashar ya danna ya ce "Kut, kambu" a lokacin daya samu nasarar tura taɓarya zuwa cikin turmi sai ya ji wani zafi da ɗumi na musamman jikinsa ya hau rawa da ɓari kamar bashi da wani aiki sai wannan ya dinga zaga yazo a cikin samaniya bai farga ba sai da yaji jini caɓa-caɓa a jikinsa ya zare ido ya ɗago Saudat amma ina sharaf bata motsi ya kara kunnensa a kunnenta nan ma babu numfashi, jikinsa ya dinga rawa sai ga hawaye a idanunsa "Saudat kar ki mutu don Allah" ya ce a gigice ganin jini na yawo a wajan bata ko motsi. Ta shi ya yi ta fita da sauri da niyyar guduwa ya bar garin. Daidai nan Ammo ta fito daga cikin gidan Malam in sha Allah wayewar gari a cikin gidan iyayenta za ta yi mata, hankalinta ya karkata zuwa ga danginta da guliyan ɗanta Tayo, suka ci karo da Ɗan'yaro ya tsaya zare ido bata bi ta kan shi ba ta ɗauki hanya idanu rufi har ta je titi, ana ta yi mata horn bata ji ba sai aka yi parking cikin faɗa driver ya fito ya rufe Ammo da masifa ita dai bata saurare shi ba tana tsaye cak, a hankali Jeddah ta fito daga cikin motar lokacin wajan 11:45 na dare cikin wata lafiyayyiyar abaya kana ganin zubin Jeddah kaga jinin sarauta da ƙyar take ɗaga ƙafa tana mayarwa. .."Ya da faɗa?" Ta cewa driver tana ɗan shafa goshinta ta rufe ido ta kalli Ammo ta ce "Baiwar Allah a titi kike" "Na sani" cewar Ammo. "Kamarya kin sani?" "E, so kawai nake na mutu" Ammo ta ce tana juyuwa zuwa ga inda Jeddah take, Jeddah ta zaro idanunta a ruɗe a gigice ta nufi wajan Ammo tana cewa "Ume-kalsom"....... 💥*MUTALLAB* Chapter 13: Election Day "Ume-kalsom" Jeddah ta sake maimaitawa da mamaki ganin wacce ke gabanta, ta sake saka hannunta a nutse tana murza idanunta domin gani take yi shi yake gwada mata ba daidai ba, yaushe rabon duniya da ayyaraye yau ita take gani? Gaske dai ko mafarki? Irin wanda ta saba yi kodayaushe? Zuciyarta bata gasgata ba ta sake matsawa cikin kiɗima ta ce "Omo-Oba" Ammo da jikinta ke rawa tana kallon Jeddah ta ce "Ayoola!" Ta ce da ƙarfi idanunta na sauyawa tare da cikowa da ƙwalla, Jeddah ɗin ma jikinta rawa yake tana rusunar da kan ta alamar girmamawa ta ce "Da gaske Omo-Oba ce? Da gaske ke nake gani?" Sai ta tafi da ɗan sassarfa tana ƙoƙarin durƙosawa a gaban Ammo, Ammo ɗin ta yi hanzarin saka hannunta ta kama hannayen Jeddah tare da ɗagota zuwa tsaye, sai ta samu kanta da kasa magana kawai ta kuma ɗauke kanta zuwa gefe a hankali ta numfasa ta ce "Kina lafiya Jeddah?" Murmushi Jeddah ta yi, har zuwa lokacin ta gaza kallon cikin idanun Ammo kafin ta ce "Cikin amincin Ubangiji Ume-kalsom" "Allahamdulillah" cewar Ammo. Juyawa Ammo ta yi zata cigaba da tafiya da sauri Jeddah ta tare ta tana faɗin "Ina za ki cikin dare? Ga shi lokacin zaɓe babu abeben hawa, mu shiga na sauke ki" Ammo ta girgiza kai a hankali ta ce "Ki je kawai Ayoola" Jeddah ta girgiza kai ta ce "Ta ina kike tunanin zan tafi na barki a nan wajan? Ai na zalunci kai na idan na yi hakan, Ubangiji kuma ba zai taɓa barina ba, dole na ji kunyar haɗa idanu da....," da sauri Ammo ta ce "Ya isa, stop" Jeddah ta jinjina kai kawai, tana sake kallon Omo-Oba ganin kamar ba ita ba, babu wannan jar fatar babu jikin nan, babu taƙama, da jin kimar nan, kyawun fuskarta ne kawai ya yi saura, ban da ta yi wa Ume-kalsom mugun sani kuma ta san labarin aurenta da a yanzu ba zata taɓa cewa ita ce ba, ta fige ta lalace ta fita hayyacinta, komai nata ya ƙare sai iliminta da ya yi saura. Cikin girmamawa Jeddah ta ce "Ki zo mu je" "Kin san in da zani ne?" "Bani da masaniya, umarni kawai nake jira ki faɗa mini yanzu, ko gidan za ki je, gidan aurenki?" "Daga gidan auren nake, kuma bana buƙatar na koma" cewar Ammo. Jeddah ta yi jigum na rashin fahimtar furucin Ammo, itama Ammo ɗin shiru ta yi tana ƙure Jeddah da idanu wanda daman ɗabi'arta ce idan ta so jin abin da mutum zai ce, sai taga da gasken cewa Jeddah bata fahimci maganar ba wannan dalilin ya saka ta yi ɗan murmushi ta ce "Zan koma Ogun state in sha Allah" "Ogun? Da gaske Ogun za ki koma?" Ta jinjina kai tana sake yin murmushi, sai Jeddah ta ɗaga hannayenta sama ta ce "Allahamdulillah, Allahamdulillah Ya Allah what a good news, kai ma sha Allah fatabarakallahu ahsanul kali'ƙin" idanunta cike da hawaye farinciki sai kuma ta ce "Babu hanya yanzu, ko jirgi za'a bi ba za'a samu ba, saboda an yi blocked abubuwa da yawa musamman shiga da fita, ina tunanin mu je inda nake bayan komai ya lafa sai a nemo ticket babu mamaki mu tafi tare" sosai walwala da farinciki ya wanzu a fuskar Jeddah. Ammo ta ce "Jirgi? Kayya ina ni ina jawa jirgi na motar ma bani da shi" cewar Ammo "Allah zai kawo in sha Allah" "Jeddah, da dai kin bar ni na je duk ina Ubangiji ya nufa please" "Haba Omo-Oba, kina tunanin da na san kina garin nan zan yi shiru na yi rayuwar aure ban neme ki ba? Ai the last think i can do, shine wofintar da ke da dukkan abin da ya shafi palace, ina mai roƙan ki da girman Allah kar ki ja maganar da nisa ki zo muje, Ubangiji ya ƙaddara haɗuwarmu kuma shi kaɗai ya san nufin hakan ok?" Muryarta har rawa take yi na tausayin Omo-Oba da yadda ta koma. "Ƙaddarorina masu zafi ne Ayoola bana son ƙaddarata ta shafe ki, ko ta raunata aurenki, ki fahimta" Jeddah ta ce "Fahimta ɗaya zan yi shine ki zo mu je, bayan wannan babu wata sauran fahimta da zan yi" Bisa dole ta shiga mazaunin baya, itama Jeddah ta shiga mazaunin baya driver ya ja da sauri ta ce "Khamis, mu je gidana zan saka a yi replacing nawa wajan taron, Asia za ta iya yin dukkan abin da zan yi ko fiye da haka" cewar Jeddah tana danna waya. Khamis ya ce "Anya Madam? Ai wani kaya sai amale, gurbin idon baya zama ido, kuma hangen dala ba shiga birni bane ramin kura sai ƴaƴanta" Ta dai yi shiru kawai. Khamis ya ɗora da faɗin "Kin san Asia da shegen bacci kamar ta ci naman kasa babu mamaki bacci take yi, a shawarce dai ki je da kan naki" Murmushi ta yi ta ce "Khamis kuma kamar ya ci naman aku kuturu" Number Asia ta kira ta ɗaga da sallama da girmamawa, Jeddah ta ɗauki daƙiƙo kafin ta amsa ta ce "Ina Asia?" Ta cikin wayar Asia ta ce "Gani ranki ya daɗe, Allah Ya ja kwana" Jeddah ta ce "Ki ware adadin matan da zasu zama agent gobe,ki tabbatar da cancanta da nutsuwarsu da iliminsu, kar su yi forcing kowa wajan voting Yallaɓai gobe, su dai bawa mata da tsofaffi ƙwarin qwwia, kuɗin dana bayar bana cin hanci bane, na siyan ruwa da lemo ne ga masu buƙata a wajan har wanda ba ɗan jam'iyyar NNY bane suna iya taimakon su, kin gane?" "In sha Allah Hajiya, na gane na fahimta za kuma a yi komai in sha Allah" cewar Asia murya na rawa. Jeddah ta numfasa tana jinjina kai cike da gamsuwa kafin ta ce "Bama buƙatar bawa kowa komai a wajan, kar na ji labarin an yi rabon wani abin kar aja hankalin mutane da kuɗi ko kayan abinci ko suttura, za'a kawo dafaffen abinci in sha Allah" Tana gama wayar ta ajjiye a cinyarta, ta yi shiru tana tunanin yadda electios ɗin gobe zai gudana, za su yi nasara ne ko za'ayi nasara a kan su? Za'a bawa talakawa abin da suke buƙata ne ko kuma za'a bi son zuciya ne? Tinani ya koma ga cakwkiyyar gidansu, musamman akan MUTALLAB wanda ta yi wa farin sani tun yana yaro, ga wannan daya bayyana mai suna MUHAMMAD wanda ake da tabbacin jinin Abraham ne, banda kullum tana tambaya ana ce mata Mutallab na tsare da babu abin da ba zai saka ta ce Muhammad shine Mutallab ba, idan Muhammad ɗan Mimi ne Mutallab kuma ɗan waye? Tunaninta ya zurfafa dole bayan zaɓan nan ta kawo ƙarshen komai kowa ya tsaya a level ɗin shi gaskiya ta fito. * Ajjiyar zuciya Ɗan'yaro ya sauke lokacin da Ammo ta shiga mota, ya yi hamdala da bata ganshi ba, ya diriri ce ya rasa ma yadda zai yi idan ya yi niyyar guduwa ya san ba hanya kuma zuciyarsa na gargaɗinsa da rashin hakan, ko zai gudu ya tsaya ya fara taimakawa Saudat. Ya shiga shagon da Mutallab ya yi rayuwa ciki, ya ɗakko jallabiya baƙa ya saka, har lokacin alamjirai na bacci malam ma haka, cikin sassarfa ya shiga banɗakin yana yashe inda ya barta bata ko motsi ya tattaɓata "Saudat, Saudat Saudat" shiru ba amsa. Sai kawai ya ɗauke ta ya azata bisa bayansa ya ɗauki ruwa a buta ya kwara a banɗakin kana ya rufe ƙofar ya fita. Tafiya ya dinga yi a saman ƙafafuwansa kasancewar babu abin hawa ga kuma jami'an tsaro da yawa sai ya dinga yanka da lunguna ya shafa ya ji ba kuɗi a jikinsa kuma asibiti ɗaya ya rage, ya ci sa'a da sauran ma'aikata amma nurse ne. "Likita likita likita" Ɗan'yaro ya dinga ƙwalla sunan likita sai wata ma'aikaciyar jinya ta fito jikinta sanye da uniform ta ce "Malam ya zaka shigo kana ƙwallawa mutane kira bayan kasan babu aiki, kuma ga patients muna da su?" Cikin kame fuska ya ce "Kuma naga asibitin bai yi kama dana gwamnati ba, balle ace babu aiki ko? Kuɗi zan biya ba kyauta za'a duba ta ba" Wata nurse ta ce "Ko private hospital ne dai yau babu aiki daga nan har Monday" ta ce cikin ɗaure fuska. "Basshi Nurse Kamila, let him talk" Nurse Kamila ta ce "A'a sister Bara'a gwara na faɗa masa, idan Hausa ce baya ji sai na faɗa masa da yaran da zai gane ya fahimta" "What is going on?" Suka ji murya Dr I. Qasim ta ratsa kunnuwansu wanda ba su yi tsammanin zai shigo night duty ba, ya ci kuma su fahimci cewa a kwana biyun nan ya mayar da asibitin gidansa ya kwana kuma ya yini hatta abinci order ya ke yi. Jikinsu ya hau rawa, a nutse Qasim ya ƙarasu ƙafarsa cikin white sandals hannunsa cikin blue black ɗin long sleeve trousers daya saka, sai wata white sport t.shirt daya saka, ya ɗora p.cap a kan shi buɗaɗɗiya sai ƙamshi yake yi fuskarsa ba yabo babu fallasa ya kalli nurse Bara'a ya ce "Ya dai?" Tana inda-inda tare da shafa kai ta ce "Kai zuwa ya yi ya hau mu da faɗa, daga cewa sai dare zai kawo mara lafiya" Ɗan'yaro ya juya da sauri ya kalli Bara'a takaici ma ya hana shi magana, sai kawai ya yi ƙwafa yana gyara goyan Saudat dake bayansa tana bleeding har lokacin. Qasim ya fahimci ƙaryar nurse Bara'a a fuskarta da bakinta, don haka bai kulata ba sai ya juya zuwa ga Ɗan'yaro ya ce "Biyoni" ya yi gaba ɗan yaro na biye da shi ya nuna masa wani room mai kyau yana cewa "I am coming sir" ya ce yana juyawa da nufar ɗakin special patient ɗin shi, ya tura ƙofar a hankali ba tare daya shiga ba ya leƙa kan shi sai ya hangota tsakiyar gado ta tura kanta tsakanin cinyoyinta ga jaririn namijin nata kuka ta yi burus da shi, baya son ɓata lokaci wajanta sai ya fara duba mara lafiyar da aka kawo, kuma daman domin ita ya shigo asibitin ba tare da an sani ba a gida. Sai ya saka key ya bubbuga ƙofar a hankali ta ɗago kanta idanunta jage-jage da hawaye ya buɗe idanunsa da mamaki, zai yi magana yaga ta zabga masa harara tana turo baki tare da langwaɓar da kai ta juya masa baya. Murmushi ya yi yana girgiza kai ya ja ƙofar ya rufe. "Ɗan bani waje" Qasim ya cewa Ɗan'yaro ganin yanayin yadda jikinsa ke rawa sosai kamar ya yi kisan kai. Ya daɗe tsaye a wajan kafin ya ji Qasim ya buɗe ƙofa ya fito, kallo guda ya yi wa Ɗan'yaro ya ɗauke yana cewa "Biyo ni" ya ce yana cire safar hannunsa ya nufi office Ɗan'yaro ya bi bayansa. Zaune ya tarar da Qasim yana ɗan juya kujerar da yake kai, ya dafe haɓarsa da hannu ɗaya a haka ya same shi jikinsa na rawa ya zauna. "ya sunan yarinyar daka kawo?" "Saudat" ya bashi amsa. "Matarka ce?" Qasim asked yana nazartar Ɗan'yaro da kyau. Gaban Ɗan'yaro ya tsananta faɗuwa, tsoran ya ce a'a dr ɗin ya yi arresting na shi ko ya yi reporting cases ɗin as physical violence or sexual violence apart from violence against humanity. Don haka sai ya saita kan shi ya ce "E, matata ce" "Sabon aure ko tsoho?" "Yau ne first time ɗin mu" Qasim ya ce "Shi ya baka lasisin shigar ta, ta wannan sigar kenan? Saboda sabon aure ne kana murna da zumuɗi zaka kassara musu yarinya, kasan cewa abin da ka yi bai yi kama da auratayya ba sai fyaɗe? Ka san ƙarfin daka gwada a kanta kan iya sawa ta samu yoyon fitsari" Ɗan'yaro ya yi shiru a zuciyarsa yana salati sosai, lallaɓawa zai yi ya gudu kawai hankali ƙwance idan an kammala zaɓe. Qasim ya cigaba da cewa "Ba faɗa zan yi maka ba, i just caring about her ne, iyayenta sun baka ita amana shine za ka ci mutuncinta ta wannan sigar? Ka kyauta kenan? Anya kana son ta ma? Duk macen da kake so ba zaka bi da ita ta wannan hanyar ba wallahi, Allah ya saka ba auren haɗi bane ko na ƙuruciya domin kai kan ka baka kai minzalin aure ba" ya ce yana jan tsaki. "Ya take yanzu?" "Are you care? Ban sani ba to" Sai ya yi ƙasa da kai ya ce "kuskure ne, hakan ba zai sake faruwa ba" "Better for you. Domin aure ɗan soyayya ne, tausayi da jin ƙai, kyautatawa juna da fahimtar juna, kiyaye ƙarya da shiga haƙƙin juna. Yarinyar nan ba guduwa za ta yi ta barka ba, sannu a hankali ake yin komai cike da soyayya da ƙaunar juna. Ka jira farkawarta muga abin da hali ya yi, amma maganar gaskiya sai na yi reporting case ɗin nan" Qasim ya faɗa saboda nuna gargaɗi ga Ɗan'yaro. Aikowa hankalinsa ya yi masifar ta shi ya dinga bawa Qasim haƙuri "don Allah, don Allah yaya" "Who is your yaya abeg?" Sai ya yi shiru. Qasim ya miƙe tsaye ya ce "za'a buɗe mata file, mene sunanka?" "Ɗan'yaro" Ya ɗago ya kalle shi ya ce "Ɗan babba dai, domin aikin ka bai nuna na yara ba. Sunanka na gaskiya" "Jaheed" "Sai a saka Saudat Jaheed?" He asked. Ɗan'yaro ya jinjina kai ya ce "Sunana na gaskiya kenan Jaheed a saka mata Saudah Jaheed Sada" Qasim bai ƙara magana ba, bayan ya yi rubuce-rubuce ya danna laptop ya ce "Jeka reception wajan nurse Bara'a" "Na gode Yallaɓai" Ya fita tun a hanya ya dinga zabga godiya ga Ubangiji bayan ya je wajan nurse Bara'a ta ce "Angama komai, kuɗin gado dana magani da komai 150k amma an rage maka ka biya 100k" ya zaro ido ya ce "Dubu ɗari? Ina zanga dubu ɗari kuma?" Ta ce "ok a fito da matar taka kenan?" "A'a ina zuwa" ya ce yana fita daga asibitin jiki a sanyaye tare da tunanin ta inda zai samu dubu ɗari dai ya fara tunanin hon, daman kwana biyu gajiya ya yi ya daina zuwa sam, saboda wahalar da yake sha sai ya ji bari kawai ya je can ya san zai samu in sha Allah, domin haka kawai tausayin Saudat da ƙaunarta ya zauna a zuciyarsa duk da bai gaba tabbatar da soyayyar ba, amma zai iya yin komai domin sama mata lafiya, amma da farko dole ya fara zuwa gida ya yi musu wata ƙaryar dama kuma ya roƙi Dr Qasim akan ka da ya yi musu bayanin komai saboda mistakenly za su iya zuwa. Kai tsaye ya nufi gidan hon ba tare da tunanin komai ba, bayan yau ɗin ba lallai ya isa samun shi ba saboda zaɓe. Walking slowly I. Qasim ke tafiya har zuwa bakin room ɗin ya saka key ya buɗe ya tura, tana jin shi ta yi saurin rufe idanunta hakan kuma akan idanunsa sai ya yi murmushi, bayan ya ƙarasa ya nufi wajan computer ya dudduba komai ya tarar drip ɗin ya ƙare ya cire mata shi. Temperature ɗin jikinta zai gwada ya ja kujera ya riƙo hannunta a hankali, laushin hannun mamaki yake bashi kamar audiga ya yi shiru yana kallon hannun fara tas, sai ya ɗaga kai suka haɗa ido ta yi saurin tura bakinta, ya ce "Ya jikin naki?" Ta yi shiru. "Me kama da Angela ya jikin?" Ta sake yin shiru. Ya saka hannunsa ya juyo da fuskarta zuwa gabansa bai magana ba, ya saka yatsu biyu ya buɗe bakin ya saka tsinken gwajin for some minutes, yaga har yanzu akwai zazzaɓi ya cire ya ajjiye ya sake dube-dube bayan ya gama. Zata juya fuskar zuwa gefe ya riƙe fuskar a tafin hannunsa yana ɗaga gira biyun sama ya ce. "Ya Angela mun yi faɗa ne? Ba magana ba gaisuwa? Na ce mun yi faɗa ne Madam?" Ta kalle shi sosai idanunta na cika da ƙwalla fuskarta a marairace. Ya saki fuskarta ya saka hannunsa biyu ya ɗagota zaune ya jingina mata pillow yana daga right side ɗinta ya ce "A faɗa mini laifina" Ta maƙale kafaɗa ya langwaɓar da kai cikin kwaikwayon muryarta ya ce "to a bar hukunta ni haka nan" Sai kawai yaga ta kifa fuskarta a cinyarsa ta fashe da raunataccen kuka, wanda sautin baya fita sosai ya fahimci yau kuma jikinne bata jin daɗinsa sosai domin ga zazzaɓi nan yana damunta, ya dinga jan astagafirulla a zuciyarsa saboda ya san matar aure ce ita ɗin, amma yana da tabbacin Ubangiji ya ba zai tuhume shi ba, saboda lafiyarta yake yin komai ta dinga kuka ganin bamai ƙarewa bane ya ɗago ta a hannunsa ya ce "To raɗa mini na ji" "To kawo kunnen" Kunnensa ya saka mata a baki a hankali ta ce "Allah, Allah Ya shiryaka" ya yi murmushin jin tana zarara masa yawu a kunne ya ce "Amin, sai me?" "Ka faɗi magana ba daidai, Allah ka nemi ya fiyata kada mala'iku su jika" "Allah na tuba, ka yafewa Qasim" Ya cire ta a jikinsa, ta ce "zaka kwana a nan ko, babies sai kuka suke yi shine nima na yi ai ban san me suke so ba, da kana nan sai ka tambaye su" ta ce a hankali tana kallon baby girl ɗin ya kama hannunta tana watsa dana yarinyar. Ya tsare ta da idanu for a while ya ce "shine kike kuka kema?" "E, kuka na dinga yi don ka ji" Sai ya durƙusa zai ɗauki macen ta girgiza kai ta nuna masa namijin sai ya ɗauke shi ya ce "ai yunwa suke ji, ba ki basu abinci ba?" Sai ta ce "To ina abincin yake? Ai ba'a nuna mini ba, where is the food" A rikice ya ce "don't tell me ba ki taɓa shayar da su ba, haba Angela" Ganin ta kafe shi da kallo sai ya juya ya fita ta ɗauka haushi ya ji sai ta fashe da kuka, ya dawo ya same ta a hakan tana da kuka ya kwantar da baby boy ɗin ya ce "mene kuma" Ta dinga kuka ita dai sai ya duƙa daidai fuskarta ya ce "Ya aka yi" Taƙi magana ya gane rigima ce gashi sai kiran shi Mimi take yi baya son ya ce baya gida, sai ya fara rarrashinta ta ce "Ni dai ka tafi dani" ya girgiza kai ya ce "bakya iya tafiya, ba'a son ki ki hayaniya kinga ina son ki samu lafiya sosai na matso na kai ki wajan shi ko?" Ta maƙale kafaɗa ta "sai ka goyani, ni na goya baby girl, ita kuma ta goya wancan" ta ce tana nuna baby boy ɗin. Qasim ya ce "To haka za a yi kowa ba ki da case teddy" ya faki idanunta ya yi mata allura ta riƙe hannunsa gam kanta a cinyarsa, ta dinga masa surutu yana ya amsata tare da yi mata bidiyo ya san zazzaɓi ne da giyar allura, a haka ya ji jikinta ya saki ta fara sauke numfashi a hankali tana riƙe da hannunsa, cikin dabara ya gyara mata kwanciya ya rufe ta da duvet ya saita baccin nata, ya kwace babies ɗin zuwa wajan Nurse Bara'a. Ya bata su. Bara'a ta ce "Dear Allah ya bada sa'a" "For?" "Zaɓen gobe" Ya jinjina kai yana cewa "Amin, ina mijin Saudat ɗin?" "Ya fita kawo kuɗi" Cikin faɗa Qasim ya ce "Wanne kuɗi? Ni na ce miki ki amshi kuɗin shi ne Bara'a ba ki dubi yanayinsa bane, ke komai kuɗi kuɗi are you ok?" Ta ce "I am sorry my love" Ya ja tsaki yana kiran number Jeddah. Bara'a ta ce "I love you" Da wani kalar yanayi ya dubi Bara'a ta ce "Qasim i love you, ina son ka" Bai bi ta kanta ba ya yi waje abin shi, lokacin da yake cewa "Allah Ya ja da ran amaryar Papi, don Allah ko Mimi zata kira ki ce ina wajanki Please" ta cikin wayar ta ce "Mimi ba zata kira ba, kana ina ne?" Ya bata amsa da "Asibiti, ina tunanin a can kwana zuwa subhi zan dawo" ta yi shiru. "Don Allah Jeddah" "Qasim come back" Ya marairace mata ya ce "Haba mana Jeddah don Allah kin ji" "Allah Ya tsare ya kiyaye ka kula ka saka securities a asibitin ka ji?" Ya ce "In sha Allah bye i love you" "I love you my son" Ya kashe kira ya leƙa ɗakin yaga bacci take yi sosai ya yi mata addu'a ya fita, ya leƙa ɗakin Saudat itama bacci take yi sai ya nufi bedroom ɗinsa dake cikin asibitin. * Hon Maɗatai yana zaune ana ta tsare-tsare duk a cikin daren wannan ganawa ta wajan biyar ce da su Sp Ghali da su Musbah su p.a da sectary. Da agent na zaɓe a goben. Ya jingina yana harɗe ƙafarsa ya ce "a zaɓen gobe idan muna raye, hukuncin Ubangiji ne kawai zai saka naƙi samun nasara domin nasara a jinin Maɗatai take kuma zan same ta in sha Allah. Kamar yadda kuka sani su talakawa har yanzu basu san kansu da ƴanci su ba, muddin za'a ka janyo su inuwa ko yaya ne wajan cimma buƙatarka do zasu bada kai bori ya hau. Mun tanadi atamfofi mai suna atamfar Maɗatai, da taliya da makaroni sabulu da omo dubu biyar-biyar dukkan wanda ya yi zaɓe akan idanunku kuma ku kaga alamar jam'iyyar NPL New people life ya zaɓa, ku bashi atamfa ɗaya makaroni ɗaya komai ɗai-ɗai. Idan a kaga zaɓe yana kyau kuma an kusa kammalawa kawai a saka yaranmu ƴan'daba su fara sare-sare a wajan kunga mutane za su ji tsoro su bar wajan, ku saka faɗa sosai har masu kayan zaɓen kar ku bari ta yadda za ku je ku yi ta dongwala mana, jami'an tsaro baza su je wajan ba sai komai ya lafa, a ɗauki dubu bibbiyu a bawa ƴan'daban idan sun gama wanda kuma aka kama ka da ku sake su yi mentioning sunana, a basu kayan caji sosai ta yadda ƙwaƙwalwarsu za ta tsaya da aiki ko?" Sectary ya ce "Duk mun kammala shirya komai lokaci kawai muke jira" Ya ce "Good, za ku iya tafiya" Musbah ya ce "Ranka ya faɗa kuɗaɗen da za'a bawa woman leaders fa?" hon Maɗatai ya ce "Musbah P.a zai baka 2m" Duk suka watse daga wajan. Bayan tafiyar kowa ya miƙe a hankali yana murmushin jin daɗi hannunsa cikin aljihu yana tafiyar izza har ya isa bakin ƙofa, yana shiga ta same ta zaune ƙasan carpet tana ta barbaza gashinta ya saka ƙafa ya zungure ta, ta yi zumbur ta miƙe tsaye tana yarfe hannunta ya ce "mahaukaciyata" "Allah Ya isa, mugu sai ka wulaƙanta" Ya ɗaga kafaɗa ya ce "Daman Allah ai isasshe ne, ni ma zai saka mini tunda asirina za ki tuna, nama fasa kai ki gidan yarin kina nan tare dani" Ta dinga ja-da-baya tana mannewa da jikin bango jikinta duka rawa yake yi da ɓari, ya saka hannunsa ya fisgota zuwa jikinta domin yana sawa kullum a yi mata wanka a gyara mata jikinta sosai. Ya zuba mata ƴan iskan idanunsa masu kaifi, yana nazarinta tare da tunanin wani abin ta dinga kowa da shi ganin yana shirin kamo bakinta, tana da ihu-ihu ya haɗe bakinsu da sauri jikinsa na rawa ya fara kissing ɗinta a gaggauce yana shafo mazaunenta jikinsa duka rawa yake, tunda ta da 💥Chapter 14: Betrayer "Kana nufin wannan mahaukaciyar ta samu ciki, kuma abin data haifa yana raye, kana nufin ku ce mini Safiyyerh ƴar wajan Abdul-Johar ita ce ƴar mahaukaciyar nan, kuma Safiyyerh ƴa ta ce?" Hon Maɗatai ya tambaya yana yin baya tare da buɗe idanunsa sosai cike da shocked ɗin daya gama ratsa jikinsa ya ji ya fara hooking jikinsa ya ɗauki mazari. Ya fara sunturi a parlourn, Uncle Musbah da Moh basu motsa, suna tsaye inda suke tun zuwan nasu, mahaukaciyar dake zaune saman kujerar asibiti ta marasa lafiya waɗanda ba za su iya tafiya ba, kuma aka tanada domin irin su. A hankali take kallon fuskar Hon Maɗatai cike da tsantsar tsana da tsoron shi wanda ya dasa mata a zuciya, ta wanzu da wannan tsoron tsayin shekaru. Da kyakkyawan fararen idanunta kamar na turawa haka take binsa da idanu, fara ce tas kamar jini ya yi magana a jikinta, tana da manyan idanu,da tsayayyen hanci sai zagayyen baki mai ɗauke da siraran laɓɓa duguwa ce sosai domin tsayinta Aafiyyah ta ɗauka tana yawan haɗe yatsun hannunta waje guda, kallo ɗaya ta kewa abu ta kau da kai, amma Hon Boɗejo Maɗatai ya zama tarihi a gare ta da kuma rayuwarta, ko sunansa ta ji bata iya numfashi mai kyau, balle ta gan shi tsaye a gabanta, numfashin ne gabaɗaya yake ɗaukewa. Ya yi mata azabar da babu wani rai da za'a yi wa wannan azabar tunaninsa bai goshe ba, ya ɗauke ta tamkar matar da aure ya halasta masa ita, ya shayar da ita wata rayuwa da dabbobi ne kawai suke yin irin ta, ko ƙara ta ce zata kai shi gani take dukkan wani hukunci da za'a iya ɗauka akan shi bai kai kwatan abin da ya dasa mata a zuciya ba, babu wani hukunci da zai iya faranta mata rai sai hukunci da Ubangiji zai ɗauka akan shi. Sa kayyar Allah take nema. Ta ɗauke idanunta tana rufe su. Hon Maɗatai ya girgiza kai da ƙarfi ya ce. "Impossible, ba zai ta taɓa yi yuwa a ce Manager ita ce ƴar mahaukaciya ba, ba kuma zai yiwu ace ƴar wajan Laylerh ita ce wacce ta rasu ba" Ya fesar da huci yana hargitsa sumar kan shi idanunsa sun firfito waje ya ce "Dole murgayiya ita ce shegiya ita ce ƴar wajan wannan taɓaɓɓiyya, na yarda Manager ƴa ta ce, amma ta wajan Laylerh kuma ƴar sunna. Domin ni Maɗatai na rufe dukkan wata hanya da zata iya kawo mini cikas a siyasata, na rufe dukkan abin da nake zargin zai iya tuzarta ni a idanun jama'a da talakawansu da suke shirin zaɓena, abubuwa da kan iya kawo mini tsako kowa ya haɗa harda murgayiya Safiyyerh wacce ta rasu, wannan dalilin na toshe wannan damuwar tun kafin na fara siyasa a domin haka wannan maganar da kuke yi ta ƙanzon kure ge ce mai kama da tatsuniya ko almara da irin labaran nan masu kama da labaran hikaya" Uncle Musbah idanunsa ya gama rinewa ya ce "To da gaske ka kashe Safiyyerh? Ka kashe mana gudaliya?" Moh kan shi a ƙasa hannunsa a dunƙule baya son yin misbehaving a gaban matar dake gabansa gudun kar ya ƙara razanar da ita, wannan dalilin ya saka ya yi ƙasa da kan shi, muddin yana kallon Maɗatai za'a iya samun Madam bai kuma san iyakacin inda matsalar zata tsaya ba. Hon Maɗatai ya yi murmushi yana ja-da-baya tare da ɗaga hannayensa zuwa sama ya ce "bani na kashe ta ba, amma tabbas ni na saka a kashe ta, ni ne dalilin mutuwarta. Ni Boɗejo Maɗatai bana tsoro ko shakkar aiwatar da dukkan abin da na san zai kawo mini nasara ko faɗuwa. Ina da matata mai suna Laylerh, bawai juya bace tana haihuwa amma ni na daƙile haihuwarta ta, akan ra'ayin kai na, na san ina aikata abubuwa da yawan gaske bana fatan na haifi yara musamman mata zuciyata ba zata jure hakƙin yaran da na yi mu'amala dasu ya faɗa kan zuri'ata ba, zuciya da gangar jikina ba zai ɗauki yanayin ba, ina da tsananin son ka na, to ba zan iya ɗauka watarana ace an yi wa ƴar gidan Hon Boɗejo Maɗatai fyaɗe ba, zan iya mutuwa da wannan mikin zai iya zama ajalina lashakka. Hakan ya saka na hana Laylerh haihuwa, kwatsam na same ta da ciki lokacin na yi tafiya ashe ta samu ciki ta ɓoye mini, sanda na ruski cikin kuma ya shige matakin zubarwa sai na haƙura da niyyar zan ɗauki ƙaddarata zan yi ƙoƙari naga na ajjiye jinina a duniya ko ɗaya ne. Har cikinta ya isa haihuwa muka je asibiti bayan ta sauka lokaci suka tabbatar mana cewa babyn bai zo a raye ba, har kyautar kuɗi na yi saboda tsananin murna da farinciki, ban damu da sanin mace ta haifa ko namiji ba, tun kafin ta farfaɗo na ɗauke matata muka bar ƙasar, daga wannan ranar kuma bata taɓa samun ciki ba. Game da wannan mahaukaciyar kuma....," Ya yi wani lalataccen murmushi yana cije baki na cikakkun ƴan duniya ya ce "Ina da tsari, dukkan wacce aka bani umarni na yi mu'amala na kan yi ƙoƙarin ganin na bi hanyar da ba zai taɓa samun ciki ba, wannan ya saka na fi mu'amala da yaran da basu fara al'ada ba, tunda nake abuna babu wacce ta samu ciki, so ba za'a fara akan wannan matar da bata da wani ƴanci ba, ba kowa bace ita sai talakawa irin ku" ya yi taku ɗaya zuwa biyu ya ce "lalala, point of correction, ba zan haihuwar ɗan zina ba, wacce na tabbatar ƴar zina ce kuma ƴata tuni ta bar duniya. Sanda naga idanun matarka ya buɗe ƙofar nan ba ƙaramin gigita na yi ba, ban ji muryarta ba, kuma ban damu da ganin kamanninta ba, domin ta bawa ƙofa baya duk da ina ganin gefen fuskarta, idanunta kawai ya wadatar, na riga na san abin da Laylerh ta haifa baya duniya, sai jikina ya bani duk inda yarinyar take ƴata ce kuma yarinyar ɗaya daga cikin matan da na yi mu'amala dasu" "Allah Al'hakkamu Sarki zuljalalu, Ubangiji daya samar da duniya kuma ya wanzar da ikon shi akan wanda ya su, Ubangijin da yake wanzar da adalci akan bayinsa yake bayyanar da gaskiya, yake nuna ikon shi akan gafalallun bayinsa irin ka. Allahu Akbar, Allahu Allahu, Allah mun tuba, Allah kar ka tuhume mu akan zunubin wasu, Allah mu bayinka ne masu biyayya da kiyaye hakkoƙinta kar ka dulmiyar damu akan kuskuren wasu daga cikin mu" ya ƙarasa maganar hawaye na bin samar fuskarsa idanunta sun yi jajur, jikinsa ya ɗauki rawa ƙafafuwansa suka gaza ɗaukan jikinsa, gaɓɓansa na rawa ya durƙushe bisa kan duga-dugansa, kar kar kar haka zuciyar uncle Musbah ke rawa ta cikin ƙirjinsa, wani irin rauni da bai taɓa jin shi ba, wani tsoron Allah, wani tsoron mutuwarsa ya koma ga mahaliccinsa, da zaman kwanciyar kabari tsoron ya dinga ratsa zuciyar uncle Musbah da ƙyar yake fitar da numfashi, wata kewar Safiyyerh yake ji tana ratsa jinin jikinsa tausayin ɗan'uwansa Professor Abdulwahab da tausayin matarsa sune suka cika zuciyar Musbah, uwa uba tausayin Mutallab ya rasa wanne irin tunani zai yi, sai ya baje, tare da yin zaman dirshen a wajan wani irin raunataccen kuka na suɓuce masa. "Allah Ya ji ƙan ki gudaliya, Ubangiji ya haskaka kabarinki ya ba ki ikon kwanciya a gidanki cikin nutsuwa da sallama, Ubangiji kada ka hukunta baiwarka akan zunubin mahafinta Allah ka bawa Safiyyerh ikon bacci a kabarinta cikin nutsuwa ka yi mata sakayya da aljannar Fiddausi ta kasance cikin amintattun bayinka. Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, innalillahi wa'inna ilaihirraji'un wayyo Safiyyerh Ubangiji ya ji ƙan ki, Ubangiji ya yi miki sakayya da abin da zato bai taɓa zata ba, haƙurinki, sanyin halinki, da ƙaunar Allah data ManzonSa da kike yi su zame miki tukuici. Rabbi rahamhuma" Kuka yake yi sosai, zuciyarsa na girgiza mutuwar ta dawo masa sabuwa fil a zuciya, idan ya tuna yadda Safiyyerh ke ƙaunar Allah da Manzonsa har tsoron imaninsa shi yake yi sau tari idan ta ziyarci gidansa, cikin dare yana samunta a waje guda inda babu kowa zaune a saman ladduma ta kifa kan ta ƙasa, har zama yake yi yaga me take bata taɓa sanin yana ganinta, har watarana ya gaji ya fito ya ƙarasa gare ta, tare da durƙusawa ya taɓa kafaɗarta amma bata motsa ba, ya sake taɓa ta bata motsa a lokacin a sanyaye ya kiranyi sunanta. "Gudaliyar Prof" "Safiyyerh....!" Ta ɗago a gigice sai yaga hawaye yana gudana daga cikin idanunta yana sauka saman farar fuskarta mai tsananin kyau da haske idanunta jawur ya dubi sama hadari sama- sama, ya dubi balcony ya rasa meke kawota wajan sai ya tsinci kan shi da cewa "Me kike yi a nan wajan, all the day? Cikin duhuwar dare lokacin da dare ya raba kowa ke buƙatar nutsuwa da samawa kan shi hutu? Me kike yi Safiyyerh?" Itama saman ta kalla tana jin yadda iska ke ratsa ta, tana jin nutsuwa na sauka a ƙirjinta. Sai ta yi shiru, domin bata san me zata faɗawa uncle Musbah wanda zai fahimce ta ba. "Kina da matsala ne?" "E, ina da ita, ga Ubangijina uncle Musbah" ta ce a hankali. Uncle Musbah ya ce "Safiyyerh, wacce matsala meke damunki?" Murmushi ta yi masa, tana ɗauke hawayen fuskarta ta ce "Ina son Allah da Manzonsa, ina jin tsoron Allah da haɗuwa da shi, ban sani ba ko ina da tarin zunubai, Ya sayyadi ya ce, babu wata soyayya kamar ta Muhammadur Rasulullah sallahu Alaihissalam. Uncle ina tsoron haɗuwa da Ubangijina, zuciyata zafi take yi mini ina ƙaunar Allah da Manzonsa uncle, ina son ganawa da ma'aiki ko a cikin baccina ne, ina son komawa wajan Ubangijin al'ajabi" Ɗib, Uncle Musbah ya ɗauke wuta ya zubawa Safiyyerh idanu ganin yadda take kuka saboda soyayyar Manzon Allah. Ya kasa furta komai ta ce "Uncle babu wani hutu a wajan bayin Allah wanda ya shige bautawa Allah, bani da tabbacin sallolina suna amsuwa, Ya sayyadi ya ce dukkan wani abin lada da gulamai wanda basu fara mafarki ba suka aikata to ladan na iyayensu ne, kaga Daddy baya samu hutu sosai shi ya saka nake ta yin abubuwa domin Allah ya kai ladan ga Abbana, ya kuma yafe masa, ina roƙan Allah ya dubi raunin zuciyar wanda ya kasance mahaifina ya yafe masa, ya gafartawa wanda ya haifan ni tsoran duniya nake uncle" Ta rushe da kuka sosai. "Uncle ina son ganawa da ma'aiki, yadda lahira take ga yara da yadda Ya sayyadi yake kwaɗaita mana aljanna ya saka bana son zaman duniya, aljanna akwai daɗi akwai abubuwan ƙawa, wanda ya rabauta da ita ya ji daɗi" Ta ɗan tsagaita sai ta yi murmushi ta ce "Ina son wannan rabautar" sai ta yi sauri ta miƙe tana naɗe laddumar ta yi gaba sai murmushi take yi, uncle Musbah ya yi sak yana jin kamar imaninsa da saura. *Uncle Musbah ya sake tsananta kukan shi sanda ya gama tuna wasu memories, abin da bai taɓa faɗawa Professor ba kenan, ya sha kama Safiyyerh tana rubuta ƙasidu tana rerawa ita kaɗan. Dab da zata rasu ta same shi suna ta hira da tsokanar shi sai ya yi mata murmushi ya ce "Drop out zan ce ko out of school, ƴar love?" Sai ta ƙyaƙyace da dariya tana fari da idanunta ta sakko daga saman kujera ta dawo wajan ƙafafuwansa ta ce. "Ka san me uncle?" Ya ce "A'a, ina zan san me ni ba akuya ba?" Ta yi smile ta ce. "Wai ku haushi kuka ji an kore ni daga makaranta ko? Ni wallahi ban damu ba, kawai i feel bad saboda Professor, amma ni makarantar bokon nan bana so, na mawaƙiyar yabon Annabi Sallallahu alaihi Wasallama nake so na zama, ina son shauƙin ya kasance dani, ina son ƙasidun fadar bege sosai shi zai zama role model ɗina" "Gudaliya fadar bege ai ya rasu ko?" Ta buɗe idanunta ta ce "Subuhanallahi ban sani ba, Ubangiji ya ƙaddara saduwarmu cikin ƙanƙanin lokaci, Allah Ya yafe mana Allah ya yafewa Abbana" "Sannu mai Abba, yau ki ce Abba gobe ki ce daddy, gata ki ce Professor" "Uncle su iyaye a duk yadda suke garkuwarmu ne, duk lalacewar iyayena ba zan iya wofintar dasu ba, balle Ubangiji Ya yi mini liɗifi da iyayen bugawa a jarida, i love them, i love them for the sake of Allah, ina son iyayena" ta miƙe tsaye sai uncle Musbah ya ce "To a fasa auren kawai ki dawo wajan iyayen naki" Kamar bata fahimta ba, haka ta juyo kalli uncle Musbah ta ce "Ina son mijina ai uncle, ƙaunar Mutallab a jinin jikin Safiyyerh take zan ta haƙuri da shi Ubangiji yana sane dani" tana cewa haka ta fice tana ɗan tsalle kamar ba matar aure ba. *Uncle Musbah ya kalli Hon Boɗejo Maɗatai ya ce "Rasuwar Safiyyerh hujja da dalili ne, rasuwar Safiyyerh manufa da ishara ne, rasuwar Safiyyerh buɗewar wani sirri ne, kai ne dalilin mutuwarta kamar yadda kai ne za kaga ishara amma Ubangiji da kan shi ya so ya ɗauke Safiyyerh ta dawo gare shi, wallahi Ubangiji ya fi mu ƙaunar Safiyyerh shi ya sa ta koma gare shi kamar yadda take roƙa kullum, kai sanadi kawai ka zama amma soyayyar Ubangiji ce ta janye ruhin Safiyyerh daga duniya. Abin mamaki bata waye ubanta ba har ta bar duniya, kuma bata taɓa sanin Professor da dr ba sune iyayenta ba, Professor ba mutum banza bane amma Safiyyerh bata da magana sai ta Ubangiji ya yafewa Abbanta, ya shiryi Abbanta, tana yi wa mutumin da shi ya kawo ƙarshen shan ruwanta addu'a ina da tabbacin addu'arta zata bika saboda ita tsarkakkiyar yarinya ce" Uncle Musbah ya miƙe tsaye ya kalli Mutallab da ya saurin juya baya, alama ya nuna baya son aga fuskarsa amma yanayin hawa da saukar ƙirjinsa ya bawa uncle tsoro sosai musamman daya lura da hatta gargasar da suke jikin Mutallab sai da suka mimmiƙe tsaye. "Maɗatai ka yi kuskure, su yaran da zina ta samar dasu ba yara bane ko? Mene laifinsu? Me ya sa ka aikata zina bayan ka san bashi ce dole zaka biya, ko ta biya kan ta a yanayin da baka taɓa sani ba, wallahi wallahi saboda Ubangiji ya nuna maka ikon shi ya nufeka da kashe ƴar cikinka kuma ƴar sunna da kan ka, sai ya bar maka ƴar zina ɗin wacce ma baka taɓa sanin da samuwarta a duniya ba, domin Ubangiji ya ɗauke tunaninka ya saka Maamah bata ɗakko kammaninka ba, kuma bata ɗakko kamannin mahaifiyarta ba, Ubangiji ya wanzar da kamanninta daban domin akwai tabbaci idan kaga kamar ka saka a kashe ta. Kamar Yadda Maamah ta ɗakko muryar mahaifiyarta, haka late Safiyyerh ta ɗakko muryar Laylerh matarka sak,.haka kuma ta ɗakko zubin ƙwayar idanunka, kuma da ace ka nutsu sosai wannan zafin zuciyar da ɗagawa da jinkimar, da rashin tsoron Maamah bata kowa bace face taka Hon Boɗejo Maɗatai, amma take idan kana lissafi baka komawa gidan ɗaya shi ya saka lissafinka baya cika, hatta wayon Maamah naka ne bana Dig Abdul-Johar ba. Kaga inda jini yafi ruwa kauri ko? Blood is thicker than water" Boɗejo dai na tsaye kamar saƙago har yanzu ya kasa gasgata maganar Musbah baya jin kuma zai yarda ɗin. "Wannan dalilin ya saka ka shigo cikin siyasata saboda ɗaukan fansa?" Sai uncle Musbah ya ɗan yi shiru sai kuma ya ce "Is that what you are thinking? Nop! Actually no!" Ya ce "Ni ai na san waye kai, duniya kuma nake son ta sani, ta san cewa Boɗejo shine Maɗatai, Maɗatai shine Boɗejo. Ranar da Safiyyerh zata rasu i received a message from her, ta numberta abu ɗaya ta rubuta mini shine; Alhaji Boɗejo Maɗatai" ya juya sosai ya ce "Tun a lokacin na saka idanuna a kanta domin babu wani furuci da Safiyyerh take faɗar shi a banza, wannan dalilin ya saka na shigo jikinka kuma i knw a lot of you, kuma in sha Allah Mutallab zai wanke tas zai fita daga zargin jama'a nan nan kusa ma kowa, kai ka san yadda ka samar da cikin Maamah, kamar yadda baka san yadda aka haife ta ba kuma baka san yadda aka yi ta je wajan Dig Abdul- Johar ba. Ina roƙan Allah akan cewa, kada Maamah ta san cewa kai ne ubanta domin zata iya haɗiyer abubuwa, kuma in sha Allah sai tafi ƙarfinka kuma daga kanta zaka gane cewa suma shegu ƴaƴa ne" Ya juya zai fita sai ya tsaya ya ce. "Mutallab saboda darajar da Allah Ya yi wa ManzonSa kar ka ɗauki mataki a hannunsa, ka bar Ubangiji Ya hukunta shi kuma ka har doka ta yi aikinta a kan shi in sha Allah zai gani, iya fitowar gaskiya kawai ka cika wasiyyar Safiyyerh kuma na gasgata son da kake mata daga nan duniya har lahira Ubangiji Ya saka mana" Keken matar ya tura har yanzu taƙi sake kallon kowa kan ta a ƙasa, ya tura a hankali suka nufi ƙofa, Mutallab dai na tsaye domin a yanzu baya fahimtar komai ko taɓa Boɗejo ba zai iya ba wani irin abu yake ji a zuciyarsa. "Babu mai iya janyo Boɗejo zuwa rana, zan cigaba da samun nasara zan ta yin nasara kuma gaskiya iya ko ne kawai kuka santa kuma zan kawo ƙarshen ku. Zan yi bincike akan ita Manager ɗin idan na tabbatar da gaskiya zan kashe ta tabbas zan kashe ta wallahi" Da wani irin speed Moh ya ɗago kan shi saboda jin furucin Maɗatai, zai kashe Maamah! Maamah dai? Jikinsa na rawa ya yi kan Maɗatai ya ce. "To don babanka jeka jeka maza hanzarta ɗan ta shegiya" Ya cilla masa paper ya ce "Take it, ranar daga shigo gidan nan na yanke ka na ciri gashin kan ka, kamar yadda na ciri nata gashin, na je aka yi DNA test kuma ya tabbatar kai ubanta ne, kamar yadda na sake yin gwaji dana mahaifiyarta. Ka yarda ko akasin hakan idan na amsa sunan Muhammad Mutallab Abdullahi wallahi ba zan taɓa bari Mayh ta gano cewa ba Dig Johar bane mahafinta ba, idan har ba zina uwata ta yi ta haifan ba wallahi baka isa ka cutar da jinin matata ba, hakƙin kula da MAYH a wajena yake darr ne don uwarka kimini ni da kai shega kafasa kai iskanci kake da rashin ilimi ni kuma taƙadiri ne mai cikakken ilimi, rayuwar MAYH tawa ce, numfashin MAYH nawa ne, kukan MAYH nawa ne, dariyar MAYH bata kowa bace face ta Mudallabi na Ammo ganin Sa'adah da Hamida jinin Bafullatana, ɗan gidan Malam mijin matarsa Safiyyerh bestie" Moh ya shagiɗar da baki yana yin wani ɗan iskan taune harshe ya ce. "Dar, da babban wasali nake goga maka idan ka taɓa MAYH sai ka yi danasin zamanka a duniya a lokacin zaka tabbatar da sunan mai dawa don sai na kai jeji ka yi kwanan zaune" ya juya zai fita sai Maɗatai ya ce "Scorpion ko? Zan saka a kashe ka" "Ka je Federal investigation department za kaga Scorpion a can, ka faɗawa jami'an tsaro kuma hakan ya tabbatar kuna son taimakon Scorpion saboda kar ya fallasa asirinku na garin RANO da kuke ɓoyewa" Ya ɗaga hannayensa sama ya ce "Sai godiya" Suna fita Hon Boɗejo Maɗatai ya saki wata ajjiyar zuciya wacce yake ta riƙe da ita, zufa ta dinga yanko masa tamkar babu ac ya fara ƙoƙarin kiran Ja'aafar da Sp Ghali Gaddafi. Baya son tayar da maganar sai an faɗi makomar zaɓan ya fara ƙoƙarin ganin an nemo jaririn da aka photonsa da nashi wanda suke tsananin kama kwabo da kwabo da kuma uwar jaririn duk inda aka gansu kawai a kashe su kamar yadda ya kashe Dr Ganash. Uncle Musbah na tsaye jingine da jikin mota yana duba wayarsa da sakamakon mazaɓun da aka fara saki yaga Mutallab tsaye hannunsa zube cikin aljihu, ya mayar da wayar cikin mota ya tsaya kallon Mutallab ganin yadda ya rame ya yi zuru-zuru yaro tun yana ƙarami yake gwagwarmayar da rayuwa tun bai kai ya kawo ba ya rabu da iyayensa rayuwar daba da shaye-shaye suka yi masa mara ba, cikakken matashi wanda duniya take neman irin su, gashi tsayayyen namiji da kakke mai kyau da nutsuwa da tarin haiba da kwarjini amma ƙwaya ta birkita shi, ƙaddara kenan! "Ba zaka daina shan abubuwan maye ba? Ba zaka daina ba ashe?" Moh ya yi shiru. "Mutallab" "Mutallab yana ji" ya ce yana sake cakewa waje guda. Uncle Musbah ya ce "Ba zaka dai na ba? Rayuwarka kake gurɓatawa" "Allah Ya ban ikon, zan doƙa zuwa jewa" cewar shi. "Shikenan Allah Ya kiyaye, kana lura kar ka yi misbehaving ɗin da zai nuna ba Muhammad bane kai, domin sanda naga Muhammad ɗin na firgita da kamanninku. Anya ku ba jini ɗaya bane?" Kafaɗa kawai Moh ya ɗaga yana ƙoƙarin juyawa ya ji ta kama hannunsa ya yi saurin juyawa, sai yaga ta yi masa murmushi ta ce "How are you?" Ya ɗan yi jim, sai ta buɗe idanunta ta ce "Kamarya? Is there any wrong?" Ta ce tana kallon uncle Musbah da shima kallon ta yake yi sai ta sake buɗe ido tana watsa hannunta ta ce "Na yi wani abu ne?" Ya girgiza kai ya ce "You did, nothing" "He is my son right?" She asked. Uncle Musbah ya ce "Ɗanki ne mana,.halak malak" Sai ta yi murmushinta sak irin na Aafiyyah ta ce "To ni ma na bar bashi babyna halak malak Ubangiji ya shaida" "Mun gode kowa sosai, kuma mun amsa Mutallab ka yi godiya mana an baka ƴa" sai Moh ya kasa cewa komai, shi dai matar yana ganin girmanta da nauyinta sosai a zuciyarsa magana take yi a hankali amma yanayin sakin maganar sam babu hankali a ciki a hakan ma kuma da sauƙi a kowanne lokaci tsoron zai iya sakinta. Da ƙyar ya zame hannunsa ya sulale ya bar wajan. Mota uncle Musbah ya saka ta a ciki ya ja suka bar wajan. * Ɗaiɗaikun waje ne ba'a kammala zaɓan ba, kuma duk inda aka irga ƙuri'a Dr Abraham Denial David ne gaba da kowa sai hon Maɗatai. Ba'a maganar Eng Ali wali ma, aka dinga posting cewa Taliya bata zaɓe duk da dai ta ja ra'ayin wasu, sun amshi kaya wanda kuma suka zaɓa daban hakan ya sake tunzura zuƙatan magoya bayan Hon Maɗatai, daman shi uncle Musbah dukkan woman leaders ɗin daya bawa kaya cewa yake su amsa kawai amma su saka a zaɓi Dr Abraham Denial David. An samu rikici, yawanci na faɗan daba ne kuma sai an gama jami'an tsaro suke zuwa aka dinga bada rahotanni daban daban daga kowacce gidan rediyo musamman inda Yakasai yake aiki. Har dare ya yi aka fara kai ƙuri'un gwamna zuwa inec shi kuma ɗan Majilisar tarayya ya tsaya a ƙaramar hukumar da zai wakilta wanda kuma yawanci tun dare aka sake hayar ƴan daba wanda aka shirya set up ana cikin shirin faɗar sakamako za su tayar da tarzoma a ɓangaren Dr Abraham Denial David, nutsastsun mutane ne suke tsaye a kan komai da kuma jajir cewa wajan ganin an bawa al'umma abin da suka zaɓa, suka hana idanunsu bacci. Har wajan uku na dare an tattara samako kuma har lokacin Dr Abraham Denial David ne gaba da kowa sanarwa kawai ya rage ace ga wanda ya saci ama abu ya gagara, dab da asuba aka kawo wasu jami'an tsaro na abin mamaki duk wannan abin a idanun Mutallab yana saman bishiya ya haɗe ƙafafuwa yana kallon komai shi da Goje Mangal kuma sun tura shi cikin jama'ar Eng Ali wali. * Morning. Bugawar 7:00 na safe ya yi daidai da farkawar Aafiyyah daga baccin dolen daya ɗauke ta. A hankali take buɗe idanunta tana mayarwa saboda haske ta kasa buɗe su gabaɗaya tana jin hannunta na mata zugi hannunta ta ji an kama tare da cewa. "Maamah, You are awake?" Jin muryar Paaahh ya saka ta riƙe hannunsa da kyau gefen idanunta na zuba da hawaye ya saka hannunsa ya goge mata hawayen ya ce "Ke da za ki yi godiya ga Allah daya ba ki ikon farkawa lafiya? Kuka kuma haba Maamah" sai ta fashe da kukan tana buɗe idanunta muryarta na rawa ta ce "Paaahh na yi mafarki mai munin gaske, zuciyata ta tsinke Paaahh" "In sha Allah, ba komai" Ya ce yana goge mata hawayen. "Mrs crying" aka faɗa a hankali. Ta juyo suka haɗa idanu da shi yana zaune hakimce yana kallon ta yana murmushi da jin daɗin ta farka lafiya ya tasu a hankali ya duba drip ɗin hannunta ta yi saurin tsuke fuska ta ce "Qasim!" Ta kira shi a gaggauce. "Ba allura zan miki ba ƴar nan" "Wace ƴar taka?" Ya yi dariya ya ce "To, mata" Miƙewa Paaahh ya yi yana ɗaga waya tare da faɗin "shi Scorpion ɗin? Gani nan ina hanya yanzu" Aafiyyah ta yi saurin kallon Paaahh ta ce "Daddy me ya yi?" Ya juyo ya ce "Wa kenan?" "I had his name, Scorpion" Ya ce "Ohh umarnin yi masa allura muka samu yanzu" yana faɗin haka ya fice. A gigice Aafiyyah ta miƙe zaune jiri na ɗaukanta ta kalli Qasim wanda shi ma tashin hankali ƙarara ya bayyana a saman fuskarsa ta ce "Qasim na shiga uku" ya yi kamar bai fahimta ya ce "Maganin shiga uku Allah Maamah. Mene?" "Ka san allurar da ake nufi za'ayi masa?" Sai ya girgiza kai ya ce "Laaa, koma wacce kala ce ai murna za ki yi bake kika kama shi ba? Kamar za ki fi kowa murna ai Maamah" Ta lumshe idanunta ta ce "kawai yau na ji faɗuwar gaba, na ji bana son a cutar da shi sam" sai ta yi maza ta sakko daga saman gadon ta ce "Qasim arama mini key ɗin motarka" kafin ya yi magana ta zari key ɗin motar dake gaban rigarsa yana ƙoƙarin dakatar da ita ta daka masa tsawa tana nuna shi da tsaya cikin sauri ta yi waje, tana fita kuma J na shigowa cikin asibitin na I. Qasim ya hangota ta shiga mota jira na ɗaukarta, wannan dalilin ya saka yaƙi fitowa motarta na fita yabi bayanta shi kuma Qasim ya fito da sauri jin ƙarar motar ya bi bayanta kawai da addu'a gabansa na faɗuwa jiki a sanyaye ya koma cikin asibitin can part ɗin da special patient ɗinsa take ya nufa. Tana kwance idanunta na kallon sama ƙamshin turarensa ya yi mata sallama ta ɗan juyo ta kalle shi sai ta yi masa murmushi ya ƙarasu yana haɗe hannunsa ya ce "Good morning" Murmushi ta yi a hankali ta ce "Kana lafiya dai? Ina ta jin hayaniya yau" Ya ja kujera ya zauna ya ce "Oh! sure; na yi sabuwar patient ne wasu ƴan daba ne suka sare ta wajan zaɓe" Ta rausayar da kanta gefe ta ce "Ayya ƴan daba kuma?" Qasim ya ce "Eh" "Ubangiji Ya shirya su, Allah Ya yafe musu Ubangiji kar ka yi fushi dasu" "Amin" Sai ta ce "To kai ni na yi mata sannu?" "Saboda me?" Ta ce "I I'm just worried about the patient, to kai mata baby girl su gaisa ko? Ko na bar mata ita?" Kimiyya ya dinga kallon ta sai ya amshi yarinyar ya ce "Kuma kin san za ta yi murna idan kika bar mata ita? Zata riƙe ta kamar ita ta haife ta" Murmushinta ya faɗaɗa sosai har white teeth ɗinta ya bayyana ta rungume hannayenta a ƙirji ta ce "Allah na bar mata" ya yi mata shiru ta ce "To ita baby girl ɗin da waye take kama ne?" Sai ya dube ta ya sake duban jaririyar ya ce "Da Safiyyerh take kama sosai" ta washe haƙoranta cike da jin daɗi ya ce "Me ya sa bakya ɗaukan namijin ne?" Ta ɓata fuska ta ce "Da shi yake kama, baya ji, na nuna masa so sosai, ya wofintar Allah baya jin magana saka alheri yake da sharri amma ina son shi haka nan, kawai fushi nake da shi, ai zaka kai ni ko?" Ya jinjina mata kai ta ce "when?" A hankali ya ce "jibin gobe" "Gobe?" Ya ce "jibin gobe" Ta marairace fuska ta ce "To bangane ba ni dai, ka yi kyau sosai?" Sai ya ce "Ah haba? Taɗi na je" Cikin rashin fahimta ta ce "Me?" "Zance na je wajan budurwata" Ta ɗauke fuska sai bata sake magana ba, ya dinga janta da hira amma ta yi ɗib daya matsa mata daga baccin ƙarya sai na gaske ya ɗauke ta. Ya zuba mata idanu yana rungume da babyn da take ta tsotsar fatan wuyansa tana cilla ƙafafuwa gwanin sha'awa. Riƙe da babyn ya fita suka ci karo da AA MAJ ya ce "Wclm uncle" AA MAJ ya tsare Qasim da idanu sai Qasim ya yi saurin cewa "Oh Maamah ta je Fcid wajan Scorpion" sai zuciyar AA MAJ ta motsa, shi sam baya ƙaunar yadda take yawan zuwa wajan Scorpion ɗin nan bai ga hujjar zuwa ba tana matar aure kishinsa ya bayyan tare da son ta fil a zuciya. Ya juya ya fice daga cikin wajan. Qasim ya nufi ɗakin da Saudat ke ciki ya samu Mama Zaituna da Inna Binta zaune ya ce "Ya mai jikin?" Caraf Inna Binta ta ce "Da sauƙi ɗan nan, ai a gigice muka zo sanda almajirin Malam ya zo yake cewa ya tsinci Saudat a ƙofar gida yashe cikinta yana ciwo ya kawota asibiti. To ashe jikin ma da sauƙi sai dai kamar ciwon ya tafi da bakinta taƙi yin magana sam sai kuka tambayar duniya ta yi shiru, ai da ko kunun tsamiya an yi mata ta kurɓa tunda dai yau ma hannu wayam muka wayi gari wallahi tallahi" "Allah Ya sauwaƙe" Ita dai Mama Zaituna jaririyar hannunsa kawai ta ke kallo ta kasa jurewa ta ce "Ma sha Allahu ƴarka ce wannan?" Murmushi Qasim ya yi ya ce "E, yarinyata ce" Ya ce yana miƙa mata ita, ta amsa ta zubawa jaririyar idanu sak Safiyyerh kamar an tsaga kara, ban da Safiyyerh ta rasu babu shakka da ta ce wannan jinin Safiyyerh ce, idanunta ya cika da ƙwalla Allah Ya gani ta ƙaunaci Safiyyerh musamman dab da rasuwarta "Ina Maman babyn ya sunanta?" Ya ce "Maman baby na gida, baby ke kewar Abbanta sai Abbanta ya taho da ita nan, sunan matata umm baturiya ce sunanta akwai wahalar faɗa kawai ina ce mata Angela shikenan" "To Allah Ya raya, amma ka mayar da ita jikin mahaifiyarta ta yi ƙanƙantar da shaƙar iskar nan ka ji?" "In sha Allah" * Aafiyyah ta riga Dig Abdul-Johar Marafa zuwa FCID ɗin, cikin sauri ta fito daga mota hankali tashe ta nufi ɗakin da Scorpion yake ciki, J na biye da ita an ɗauka tare suke sai babu wanda ya kula shi ita kuma bata san yana biye da ita ba a haka ta buɗe ƙofar ta shiga ciki idanunta zube a kan shi, yana zaune jingine da jikin bango hannunsa dafe da cikinsa saboda yuwar da yake ji sosai. Ta ƙarasa ta tsaya a gaban shi, sai kuma ta durƙusa daidai fuskarsa, ya ji saukar numfashinta da ƙamshin da take fitarwa mai sanyi. Ya juyo tare da buɗe sexcy eyes ɗinsa zuwa kan fuskarta, idanunsa ya sauka a kan jajayen laɓɓanta sai ya lumshe idanunsa ya ja numfashi ta ƙirji kuma ya shanye numfashin ta ƙirjin nasa gudun kar ta ji, suka kalli idanun juna ita ta fara cire idanunta daga cikin nasa ganin bashi da niyyar zare idanunsa a hankali ta ce "An yi maka allurar?" Aafiyyah asked. Ya ji ta sarai sai ya share, he want hear her voice again and again kuma again sai ya dinga binta da kallo da musamman cikinta. "Malam a hannun hukuma kake, ka daina jinka kai wani ne babu abin da za ka iya yi, ina magana Dig Johar ya shigo nan?" Ya yi shiru, tana ƙoƙarin magana taga ya yunƙura kamar zai tashi zaune ta yi baya sai taga ya riƙo hannunta, za ta yi magana ya ɗora yatsa a bakinsa alamar shiru, ai kowa shirun ta yi, bandejin dake hannunta wanda ya cire ya kama ya fara naɗa mata a hankali ita kuma idanunta akan fuskarsa, sai kuma tunanin Muhammad wanda ya taimaka mata ya faɗo mata ta kasa tantance komai sai ƙirjinta da yake bugawa, ya gama gyara mata hannun ya koma ya jingina ya sake zuba mata narkakkun idanunsa. Ta ɗauke idanunta ta ce. "Kawai ina jin tausayinka ne" Ya yi shiru bai fiya son magana ba gundirarsa take yi. Za ta sake magana ya yi saurin marairace fuska ya ce. "Wassh cikina, Wassh Sophie yunwa" "Sophie!" Ta maimaita sunan a cikin zuciyarta da ƙwaƙwalwarta. "Sophie yunwa" "Yunwa Sophie" Ya sake nanatawa yana narkar da fuska, nan ta nan ya rikice kuma ya rikitata ta miƙe da sauri ta nufi waje da niyyar nemo masa abinci tana fita Junaid ya shigo da yake tsaye, he saw everything komai akan idanunsa. Suka haɗa idanu da Muhammad sai Junaid ya ja kujera ya zauna ya ce "Sunana Junaid Abdul-Johar Marafa, yayan Safiyyerh wacce ta kama ka, ka bani minti biyu mu yi magana don Allah" Sai Muhammad ya kalli J ya tuna labarin komai da Mutallab ya bashi a hankali ya jinjina kai. J ya ce "Sunanka Muhammad Mutallab? Kuma ka yi makarantar Fgc tare da su Safiyyerh su Qasim kimiyya? Haka ne? Kuma ka auri mata mai suna Safiyyerh haka ne?" Kamar Muhammad ba zai magana ba sai kuma ya ce "E" J ya ce "To na gode shikenan, kar ka faɗa mata na zo" yana faɗin hakan ya fice yanzu kam yana da tabbacin da gangan Paaahh ya saka Aafiyyah ta kama Mutallab, domin a labarin da Paaahh ya bawa su Ummimi akwai abubuwan daya cire wanda bai faɗa musu ba, amma ya aka yi Paaahh ya gane Mutallab me ne ya saka ya yi amfani da Aafiyyah wajan kama abin da take ƙauna a duniya? Wanne dalili ne wannan? Dole ya sanarwa da Aafiyyah komai duk abin da zai faru ya jima bai faru ba, ɗaukan hakƙin yarinyar ya isa haka nan. * Kowanne ɓangare suna tsaye dasu da jama'ar su kowa yana jiran jin sakamako saboda saura minti biyar a faɗa. Hon Maɗatai na tsaye a parlournsa da sauran mutanensa haka ma Eng Ali wali. Dr Abraham Denial David da shi da sauran family suna babban parlour. Qasim sai tsokanar Papi yake yana cewa "Papi congratulations in advance" "An faɗi samako ne?" Qasim ya ce "Haba Papi ina lissafai da samakon kowacce mazaɓa kai ne a gaba mutane nata celebration faɗa ne kawai ba'a yi ba, amma kai ne wanda ya ci zaɓe wallahi" "Qasim Shut up!" Alhassan ya faɗa cikin tsawa domin gab ake faɗa sai suka mayar da hankalinsu kan redio daidai nan kuma tv dake haska wajan faɗar samakon aka samu matsala daga can wajan, sai a redio suka cigaba da saurara sun dai ji ana hayaniya daga baya kuma aka tsaya. Ritanin ofisa ne ya fara magana "kamar yadda kuka sani kuke lissafe jam'iyar NNY ita ce gaba kuma yanzu zamu faɗi wanda ya haye..." Muryarsa ta fara rawa ta rediyon. Dr Abraham ya miƙe tsaye Alhassan ma haka Mimi sai murmushi take yi, Jeddah ma miƙewa ta yi tana kallon Qasim tare da yin murmushi ƙiris take jira a faɗa ta rungume mijin nata ta yi masa murna. Kamar daga sama suka ji an ce "Wanda ya lashe wannan zaɓe na Ɗan Majalisar tarayya ba kowa bane face Hon Maɗatai dake jam'iyyar New people life congratulations Distinguish" Baya Qasim ya zai faɗi Jeddah ta yi saurin riƙo shi zufa ba yanko mata. A daidai wannan lokacin kuma Aafiyyah ta dawo hannunta riƙe da takeaway na lafiyayyen ta ƙarasa wajan Muhammad ta ajjiye abin cikin ta ce "gashi nan" sai ya yi shiru ta saka hannu zata taɓo shi ganin kamar bacci yake yi caraf ya riƙe hannunta ya juyo da rinannun idanunsa ya fisgota da ƙarfi muryarsa a sama a tausashe kuma ya ce "Ina ɗana? Ina ɗana?" Jikinta ya fara rawa ta ce "kar ka raina mini wayo kaga na yi kama da wacce ke satar yara ne? Dilla sake ni" ya sake damƙo ta ya haɗe ta da ƙirjinsa ya ce "Ɗana wanda kika haifa a cikinki, ɗana wanda ya fito daga cikin mahaifarki shi nake magana, ki faɗa mini inda ɗana yake ko na yi miki wani cikin yanzu a nan wajan wallahi" Aafiyyah was shocked ta ce "Kai wanne irin mutum ne? Wanne ɗa kake magana, do I know you before? Who are you?" "Good, great!" "Who are you?" Ta sake maimaitawa. "Me ya sa kike pretending kullum me ya sa kike son nunawa mijinki ba ki san waye Muhammad ba? Ina cikin? Ina babyna zan dalla miki mari na sake maimaita kai ne" sai ta zama kamar statue ta kasa tunanin komai kan ta ya fara juyawa tare da yi mata ciwo dum! Kamar an doka mata guduma ta sauri buɗe idanunta tana riƙe Muhammad muryarta na rawa ta ce "Yaa Muhammad" "Sophie" Muhammad ya kira ta silently. Sai ta shafa cikinta ta ce "A baby? Bani da baby babu baby" ta faɗa a hargitse ya sake doka mata wata razananniyar tsawar wacce take motsa mata tunani ya ce "betrayer, ina ɗana? Sophie my son?" Bata fahimtar komai sai Yaa Muhammad da take cewa ta ce "Babu baby" ya damƙota ya ce "Ok kafin ki samu cikin Maj bari a yanzu ki sake ɗaukan cikin Yaa Muhammad.... 💥Chapter 15: Critical condition Kalaman Muhammad ta ji suna juya mata kai da hargitsa mata tunaninta. Ya sake riƙo hannunta ya ce "Sophie ki faɗa mini ina yarona da kika haifa? Ina abin da kika haifar mini? Shi kaɗai ya rage mini, shi nake kallo matsayin jinina, abin da ya fito daga tsatsona, ina mai sake nanata miki, kuma zai zama magana na ƙarshe da zan yi miki ita ina yarona da muka sabar da cikin shi a Lagos?" Ya ce da ɗan ƙarfi yana buɗe mata idanunsa. Jikinta ne ya fara ƙoƙarin bada ita, saboda tsananta bugawa da zuciyarta ta yi a cikin ƙirjinta, tashin hankali ya bayyana ƙarara a saman fuskar Aafiyyah, ta kasa kwakkwaran motsi tunaninta ya tsaya cak, ƙwaƙwalwar ta yi hooking kamar zata fahimci wanne ɗan yake nufi sai kuma ta kasa ta fara janye jikinta daga gare shi da hanzari ta yi baya ta ce "Kai baka da tarbiyya ko?" Ya ɗage gira ya ce "When it comes to you, ni kam bani da wata kunya" Hannu ta saka ta ture shi amma ko gezau sai kawai ya sake ta idanunsa a ƙanƙance ya ce "To inda za ki, ki dinga hakƙin wani dana ɗan da kika haifa a kan ki. Sophie kan ki yana rawa, kan ki yana fisga, kan ki yana kai ki zuwa ga halaka, idan kin mance cewa kina da ɗa a duniya, amma ba za ki manta rayuwarki ta Fgc ba?" Ya yunƙura ya miƙe tsaye, jikinsa sanye da sarƙar da aka ɗaure shi da ita, ya ɗaga hannunta ya kaɗa sarƙar ta bada sauti, kacaaa! Ya yi baya kaɗan sai kuma ya sake juyawa ya kalli Aafiyyah dake zaune zaman dirshen da lulu eyes ɗinta masu sheƙi idanunta ya yi wata kala tamkar ruwa ya kwanta a cikin su, sai ya miƙa mata hannunsa alamar ta kama ta riƙe wajan miƙewa tsaye, ta zubawa tafin hannunsa idanu wanda suke jajur dasu, ta kasa motsi balle kama hannun, ita kan ta, ta rasa wanne tunani take ta san cewa ita dai bata kai arahar haka ba a wajan wasu mata balle namiji, namijin ma a criminal person wanda ake ƙoƙarin kashewa ko haukatawa, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane wajan uku, mashayi, ɗan'daba, mara cikakken ilimi da kuma asali, amma ta kasa sanin taƙamaimai abin da ya saka ta kasa hukunta shi a hannunta har ya kai hannunsa zuwa jikinta, is he alright? Is he even okay? "Oh, common Sophie hold my hand" Muhammad ya ce yana ɗauke kai zuwa gefe kamar bashi ya yi maganar ba. Aafiyyah ta ja numfashi kana ta yunƙura ta miƙe tsaye fuskarta babu walwala a dole bata son raini daga gare shi, a dole tana jin samun girmamawa daga wajan shi. Ta juya idanunta sai taga ya juyo zuwa gare ta, ya buɗe ido ya ce "Oh! know, kika ƙi riƙe hannun nawa?" Ta yi shiru. Ya taka gabanta ya ce "A ƙalla ki tuna makarantar da ta zame miki ƙaddara, yana da kyau ki tuna Fgc da mutanen cikinta, idan ma ba za ki iya tuna su kimiyya ba, ki yi ƙoƙarin tuna Fgc, ki tuna Fgc AAFIYYAH!" "AAFIYYAH?" ta nanata sunan a cikin zuciyarta, ta kuma ji sunan yana nanata kan shi a saman kanta da kwakwalwarta, ina ta taɓa jin suna Aafiyyah? Wa ta taɓa gani ko ji da irin wannan sunan? Oh Allah, who is that Aafiyyah? Mene alaƙarta da sunan ko mai sunan? Mene haɗinta da Fgc ɗin da yake magana? Ita da ba'a ƙasar nan ta yi secondary school ba, gabaɗaya bata taɓa shiga makarantar Fgc ba, but Fgc ai makarantar su Kinal ce. Sai ta fara zarya a cikin ɗan ƙaramin ɗakin, yatsarta ɗaya tana shafa kanta da jan numfashi da saukewa tunani take yi da niyyar ko zata samu hanya ɗaya da zata iya fahimtar meke faruwa da rayuwarta da kuma duniyarta? Ta jima da sanin cewa ita ɗin ba ita bace, to ita tana ina? Mene ya samu ainahin ita ɗin? Ita a yanzu wacece? Ita kuma a baya wacce, mene alaƙarta da ita da baya da kuma ta yanzu? Mene ya saka ta zama abin da ta zama yanzu? Me ya sa take tunanin wasu mutane a baya wanda suka taka rawa a rayuwarta, where is the old Safiyyerh? Kuma wace Safiyyerh ta yanzu? Wani abu yana tafiya ba daidai ba, akwai abin da bata sani ba, gabaɗaya ta yi missed kan ta, ta baro ainahin kan ta a baya. Jikinta na rawa ta yi waje, hankali kuma tashe bata ganin ko gabanta saboda duhun daya cika cikin idanunta da kuma tension ɗin da yake ƙoƙarin jikkita tunaninta da lafiyarta gabaɗaya, dole ta samu amsoshin da wasu suke jifanta da shi. Muhammad ya bita da miskilayen idanunsa yana taune harshensa, ya ja baya ya jingina da jikin bango ya rufe idanunsa yana sake tunanin zuwan shi Lagos da abubuwan da suka faru, ba zai taɓa mance Sophie da muryarta ba, muryarta a nutse cikin sanyin murya yanayinta mai sauya mutuwar jiki da kassara jiki gabaɗaya, sparkle eyes ɗinta masu motsa zuciyar mutum tare da tunasar da mutum yana da lafiyayyiyar zuwa. Motsi ya ji a bayansa da kuma gyaran murya sai ya yi saurin buɗe idanunsa da sukai masa laushi lumus a saman fuskarsa. A tsaye yaga Moh, kwana biyu da bai ganshi ba sai yaga kamar ya sauya musamman cikin idanunsa, idan ka nutsu ka kalli Mutallab za kaga ƙwayar idanunsa bata normal mutane bace, kamar yadda ƙwayar idanun Aafiyyah suke sometimes. "Kar fa su shigo su ganka" cewar Muhammad yana sake kallon Moh ɗin da kyau da kuma reactions ɗin shi, amma ya kasa hango komai a fuskar ta Moh ba zai iya tantance abin da fuskar tasa take faɗa ko nunawa ba. Ya gyara murya ya ce "Kana ji ko, ka faɗi abin da ya kawo ka wajan nan ka tafi, a kowanne lokaci wani daga cikinsu zai iya shigowa wajan nan" Moh ya juyo ya tsaya saman ƙafarsa da kyau, hannunsa zube a ƙugunsa ya buɗe jirkitattun idanunsa ya dinga bin Muhammad dasu sosai ya kuma yi shiru bai tanka ba. Muhammad ya fidda ran Moh zai yi magana sai ya tsinkayi muryarsa a saman kan shi yana cewa "za ka fita yanzu" "Ban fahimta ba, wai na fita daga wajan nan? A saboda me?" "Saboda baka da hankali" Moh ya ce a fisge kuma a daƙile. Murmushin gefen baki Muhammad ya yi ya ce "Saboda na taɓa wancan yarinyar? Shine ya saka na zama mahaukaci? Shine dai dalili?" Moh yaƙi magana sai kallon Muhammad da yake yi. Muhammad ya juya ya kalli hanyar da Aafiyyah tabi wajan fita sai ya ce "Ba abin da kake tunani bane" Ya ɗaga kafaɗa yana murmushi sosai ya ce "Ka yi haƙuri na taɓa maka kayanka, na taɓa maka ajjiyarka, na taɓa maka yarinyarka" ya sake tuntsirewa da dariya yana lumshe idanunsa da girgiza kai ya ce "Na ɓallo ruwa, da ƙyar idan ba ta yi recovering ba yau ko gobe" shi kaɗai yake ta magana Moh ya yi shiru. "Me ka yi?" Muhammad ya ji tambayar da Moh ya yi masa da muryarsa a kumbure sai ya juyo ya kalle shi ya ce "Na yi mata maganar ɗanka ne, da kuma makarantar Fgc da su kimiyya da kuma sunanta na makaranta Aafiyyah, ina sane da labarin ban manta komai ba, ina son wasa da hankalin mutane, ina enjoying kai na idan naga na ruɗa mutum, tsoro ɗaya dai kai ta yi tunanin ni ne kai, kar ta fara takura mini domin akwai matsala wallahi" ya ce yana jinjina kai tare da haɗe hannunsa. Moh ya ce "Matsala ta me?" "Yarinyar zazzafa ce, bana jin zan iya bar maka ita idan har na kamo, tsaurin idanunta ya yi mini" jin Moh ya yi shiru ya saka Muhammad cewa "Naga baka damu ta dawo hayyacinta ba, shi ya saka na taimaka maka wajan yin wannan abin, sorry kawai na riƙe hannunta ne bana nufin abin da na furta a harshena. Idan da gaske kana son late Safiyyerh ya zama dole ka cika wasiyyarta, ba neman wanda suka kashe ta bane kawai wasiyyar har da kusanta Aafiyyah gare ka, ta yi lossing memory wannan dalilin ya saka take zaune Uncle AA, bana son ta fara tara zuri'a dashi gwara a kawo ƙarshen aurensu tun kafin ma ta dawo hayyacinta, domin definitely idan ta dawo hayyacinta ba zata zauna dashi ba, zuciyarta da ƙwaƙwalwarta ta baya suna tare da kai, ta yanzu kuma tana wajan AA MAJ. Uncle AA ba zai rabu da matarsa ta sauƙi bana jin ma zai sake ta, ita kuma ba zata zauna dashi" "So gwara a yi ending abun nan" Moh ya ce "Zaka bar wajan nan yanzu" yana buɗe ido. A hargitse Muhammad ya ce "Wai meye kake ta damuna na fita na fita akwai wani jin daɗi a wajanne? Mene damuwata da fita wajan, gwara kai idan ka fita za ka iya ganin wanda ka sani kuma zaka tuna kana da iyaye ni waye nake da shi ne? Ka fara takura mini da fita ɗin nan, ga maganar hankali data yarinyar nan ina maka kana basarwa, irin you don't care?" "Mene business ɗina da wacce kake magana eh? Ina business ɗina a shirman ku? Da kai da ita hankali ne baku da shi, idan kana da interest a kan ta je ka kashe mata auren nata sai ka aure ta ok? Ka daina damuna" shima Moh ɗin ya ƙare maganar a fusace yana yin kan Muhammad sai Muhammad ya jinjina kai ya ce "Goodness, kai kana son faɗa mini baka da wani feelings akan ta ne? Ina first kisses ɗin makarantar? Ina kwanciyar da kuka yi a Lagos, kai ne ka fara saninta a matsayin mace, kai ne namijin data fara sani, kai ne wanda ta ɗauki cikinsa har ta haifa masa yaro....," ya yi ƙwafa ganin jikin Moh na rawa shima jikin nasa rawa yake yi zuciyarsu duka ta motsa ya sake yin ƙwafa ya ce "Aafiyyah ce first love ɗinka not Fiyya, Aafiyyah ka fara ƙauna not Fiyya, Aafiyyah ka fara gani not Fiyya so wannan jinkimar da nuna baka damu ba duk na mene? Mene ya kawo haka?" "Liar.....," Moh ya ce silently. Muhammad ya jinjina kai ya ce "Liar? Ni da kai kar ta san kar ne tun ranar daka fara ganin Aafiyyah ranar weekend ɗin da kuka je makaranta ka fara son ta, kana jin cewa tafi ƙarfinka ne shi ya sa ka ɗauke tunanin hakan a zuciyarka, soyayyar bestie nufi ne na Allah, na kuma yarda kana son ta amma a second choice ɗin ka, bestie plan B ɗinka ce kawai, kuma da Aafiyyah ce ta nuna maka soyayyar da bestie ta nuna maka da tuni ba wannan maganar ake yi ba, shi Ubangiji da ikon shi yake tsara komai" Kau! Kau! Moh ya ɗauke Muhammad da maruka ya kasa magana sai huci yake yi, duk da sarƙa ce a jikin Muhammad bai hana shi kai wa Moh duka ba, cikin hanzari Moh ya damƙi wuyan Muhammad ta haɗa shi da bango ya shaƙe shi, kokawa suka fara a cikin cell ɗin tamkar idanun Moh zai faɗo ƙasa, ya zaro harshensa da niyyar mugunta da kuma sawa Muhammad kunama a jiki, sai ya runtse idanunsa haka nan ya ji ba zai iya cutar da shi ba, ya lanƙwasa harshen ya kaɗa shi kana ya mayar da shi cikin bakinsa, da murya tamkar bata shi ba ya ce "Kar ka kuskura ka aibata ruhin matata, zan maka illa" da sauri shima ya ce "Me ya sa? Bayan matar taka ta yi kuskure, ita da kanta ta san ta yi kuskure shi ya saka ta baka wasiyyar auren Sophie, dole ka yi ƙoƙarin cika umarninta ka kuma neme mata yafiya wajan Sophie" "Quiet!" Moh ya ce yana kaiwa Muhammad duka sai kuma ya fasa. Muhammad ya ce "Ba zaka iya ba, ai ba zaka iya cutar dani ba, kuma sai dai mu cutar da juna wallahi" Ya ce yana yin ƙasa da kan shi, ɗagowa ya yi da nufin sake yin wata maganar sai yaga wayam babu Moh sai wata ƙaramar paper daya bar masa. Ya ɗauki paper ɗin ya buɗe. "Ka shirya barin wajan nan, iyayenka na raye daga mahaifiyarka da mahaifinka. Sunanka Muhammad Abraham Denial, Dr Abraham Denial David shine mahaifinka. Kimiyya da kake magana jininka ne ɗan'uwanka ne, kai da shi tagwaye ne shi ya saka muryarku take iri ɗaya" Ya gama karanta rubutun yana jin zafi a ƙirjinsa, shi bashi da wasu iyaye a duniya, idan har yana dasu suna ina? Suka bar shi ya yi rayuwa a wulaƙance ya taso cikin marayu aka haɗa shi da yaran da zina ta samar dasu, ya jima da yaƙinin shima ba ɗan halak bane shi ya saka suka cillar dashi, idan ma da gaske sune iyayensa ba zai taɓa accepting nasu matsayin iyaye ba zai ta yin rayuwarsa haka. Ya yi shiru yana tunani, tabbas muryarsa data Kimiyya iri ɗaya ce, idan kimiyya jininsa ne shi kuma Mutallab fa? Kamar da suke yi dashi ya shige ace kama ce kawai da kan iya zuwa ɗaya, dole akwai alaƙar jini, kama, hali, ra'ayinsu kusan duk iri guda ne. This is completely! Ya rufe ido a hankali kuma ya nemi waje ya zauna yana shafa wuyansa inda Mutallab ya shaƙe shi, har yanzu ya kasa hango soyayyar Sophie a idanun Moh, ko da gaske ne baya son ta? Bai taɓa son ta ba? Ba'a fahimtar zuciyarsa akan abin da yake so ko yake ƙi. * Qasim ya kasa zama ya kalli Jeddah ya ce "fake result, wannan set up ne akwai zaƙon ƙasa a cikin abin nan" Soha da idanunta yake cike da hawaye ta ce "Wallahi akwai abin da yake faruwa, ka duba muryar mai faɗar sakamakon, akwai tsoro a tattare shi, ba zamu yarda ba" sai ta fashe da kuka sosai tana babbuga ƙafa. Al Hussaini ya ce "Nima irin tunaninki nake Soha, Papi suwaye a wajan ne? A mutanenku?" Mimi ta watsawa Al Hussaini harara ta ce "tashi ka je ka gano Al Hussaini" "I am sorry Mimi" Jeddah ta sauke numfashi ta ce "Mimi yaran nan suna da gaskiya, akwai abin da yake faruwa, ga rashin gaskiya ƙarara ya bayyana" Mimi ta yi wa Jeddah kallo ɗaya ta ɗauke kai can kuma ta ce "Ni daman bana son wannan siyasar, tunda haka abin ya zama a bar su kawai" "A bar su? A hana talakawa abin da suka zaɓa? Bayan ana ta faɗa musu cewa vote for the right and freedom, Dr Abraham al'umma suka zaɓa ba Hon Maɗatai ba, bana goyan bayan cewa a rabu da su dole mu taya talakawa faɗa kar wahalarsu ta tashi a banza gaskiya" Qasim ya ce "I support you Jeddah" Alhassan ya miƙe tsaye daman shi baya jure zama waje guda, kamar ya rufe Qasim da duka haka yake ji, walking slowly ya fice daga parlourn. Yaa K ya ce "To me kuke so a yi?" Jeddah ta ce "za mu shiga court dasu, court zata amsar mana hakƙinmu" Sai a lokacin Papi ɗin ya ɗago kai ya kalli Jeddah da take ta ɗan latsa wayar hannunta alamar tana son yin kira amma maganar privacy ce sai ya yi murmushi ya ce "Presidency za ki kira ko?" Ta juya idanun rashin gaskiya ta ce "bangane ba?" Da sauri Qasim ya miƙe zai fita sai Papi ya ce "Kai, dawo" Bisa dole ya koma ya zauna yana sunkuyar da kai ƙasa. Dr Abraham, ya miƙe tsaye ya ce "Jeddah dake da Qasim baku da gaskiya, kun kuma raina mini wayo, sai dai tunanina da naku ba ɗaya bane kamar yadda kuke zato" Mimi tana ji ta yi shiru sai counter take ja hankalinta baya ma kansu haka ta nuna. Da rashin fahimta Jeddah ta ce "Ban fahimci bamu da gaskiya ba, saboda na nuna a nemawa talakawa hakƙin su?" Sai ya tunzura ya ce "Zan miki abin da ba ki yi zato ba, zan watsa miki yatsu a fuska Jeddah" ta jima tana haɗiye abubuwa a zuciyarta saboda haka ta gyara tsaiwa ta ce "Allah ko? To mare ni Ibrahim, idanunka ya rufe akan soyayya? Abin da matarka take so shi kake so? Na tabbatar da ita ta ce aje court da tuni ka yi magana da jam'iyya shine yanzu za ka yi mini faɗa saboda na zama tuwon tushe ko? Na nuna ina son ka na zama abin wulaƙantawa daman kuma alfarma ka yi mini, ya yi kyau na gode sosai" ta ce idanunta na sauyawa, Qasim ya ji tausayin Jeddah ba kuma zai iya jure ganin abin da mahaifin nasu yake ƙoƙarin yi ba cikin sauri ya bar wajan, sauran yaran ma suka tashi tare da ficewa. "Ni na ɗauka soyayyar dana nuna maka da kuma yadda nake son jininka zai saka ka dinga mini kara, ko taƙamar kana ganin ni juya ce bani da mamora ko?" "Silent!" Ya ce cikin ɗaga murya. Ya ce "Point of correction Jeddah, duk wannan ba shi ne ya damu Abraham ba, ni kuma ba mijin tace bane. Sai nunawa kike kamar ba ki gane akan me nake magana ba, ki jinki mai gaskiya kuma you have a right to talk, the whole me ina magana kina magana ta ƙamar kina da connection da presidency ko? Kafin wanda kike magana ya zama abin da ya zama ubana ya yi mulkin daba kowa zai iya irin shi ba, bama irin mulkin Nigeria ba" ta girgiza kai ta ce "Uhm" ta ce tana shirin barin wajan ya janyo ta, ta yi baya ya ce "Explain" "Explain what?" Ta ce tana tsare shi da ido, hawaye na sauka a fuskarta "Kin yi waya a Presidency, kin saka an saki mai laifi, waye shi? Mene haɗin ki da mai laifin da har za ki bi ta sama ki saka a sake shi" Sai ta ware ido ta ce "Oh" "Za kiga Oh a fuskarki" Ficewa kawai ta yi ta bashi waje, ya biyo bayanta kafin ya fito ta shiga mota ta ja a guje ta nufi gidanta. * Jama'ar Hon Maɗatai suka fara celebration na cin zaɓe musamman Sp Ghali Gaddafi da yake tunanin dama ta samu da za'a ƙara masa matsayi. Daga gefe guda kuma al'umma sun hargitse da zanga-zanga ana ta yage fastocin Hon Maɗatai ana ba'ayi kuma ana cewa justice for us, a bamu abin da muka zaɓa. Sai faɗa ya rikice wannan dalilin ya saka daga Government house aka baza jami'an tsaro kuma aka saka kafiyu na wani lokaci. Shugabanni jam'iyya suka ce basu yarda ba, NNY aka buga ƙara court kai tsaye aka yi accepting ƙarar aka saka ranar da za'a fara saurare. Social media aka dinga yaɗa photon jariri dana Hon Maɗatai ana cewa ai mutumin banza ne ya yi wa wata maɗe har ta haifi mai kama dashi. Cikin ƙaramin lokaci mutanen Hon Maɗatai suka ce sharri ne daga mutanen adawa ake son lalata masa suna, Hon Maɗatai baya haihuwa bashi da lafiya kamar kowanne namiji akan wannan dalilin ne ma matarsa Laylerh ta guje shi duk da irin son da yake yi mata, amma ta kasa haƙuri ta ƙaddarar da Ubangiji ya ɗora masa ta tursasa sai ya sake ta, shi kuma yaƙi sakinta wannan dalilin ta gudu daga gidansa. Nan da nan bloggers suka fara yaɗa labaran ƙanzan kurege wanda aka samu daga bakin PA ɗin Hon Maɗatai. Zantuka suka fara fitowa aka dinga cewa tabbas Hon Maɗatai bashi da ɗa balle jika ashe bashi da lafiyar haihuwa ne? Daga nan aka ƙara sakin magana cewa ai Alhaji Boɗejo mai taimakon alamjirai da kuma marasa ƙarfi yake raba abinci da kuɗaɗe shine HON BOƊEJO MAƊATAI. Sai hankalin jama'a ya karkata suka daina batun neman adalci ga Dr Abraham domin tarihi ya nuna Alhaji Boɗejo mutum ne mai tausayi da jin ƙai suna da kyakkyawan yaƙini a kan shi. Sai aka ce photon jaririn ma edited ne kuma set up ne irin yarfe na siyasar nan da akewa mutane. "Hahaha, second round dole" Boɗejo ya ce yana miƙewa tsaye Alhaji Wada shima ya miƙe yana tsiyaya lemo a cup suka haɗa alamar cheers. "Congratulations Hon Boɗejo Maɗatai congratulations once again" "Alhaji Wada nawa" "Boɗejo ikon Allah, congratulations Distinguish wannan karan ka nemo matsayin Speaker a majalissa" cewar Alhaji Wada yana kai cup bakinsa. Boɗejo ya yi murmushi yana tuna sanda suka yi shigen tattaunawar nan da Eng Ali wali, Ali wali ya yarda da shi amma ya yi masa zaƙon ƙasa, shi kuma sam bai yarda da kowa ba. Sai ya yi murmushi ya ce "Alhaji Wada mun yi nasara, mun yi nasara" Alhaji Wada ya ce "Nasara daman taka ce, yanzu mutumin yana nan jininsa ya kai 200 ina tunanin kaɗan ne ya rage bai samu bugawar zuciya ba" ana haka kuma sai ga notification ta wayar Boɗejo daga number Jaa'afar wanda ake tunanin ya koma tsagen Ali wali. Ta WhatsApp ne, sai ya shiga ya buɗe Eng Ali wali ne ya yi zaman dirshen ana yayyafa masa ruwa, ga jama'arsa sai salati suke yi. Nan take Boɗejo ya tura bidiyon zuwa ga Alhaji Wada, shi kuma ya turawa drivensa, drivern kuma ya turawa abokinsa, abokin kuma yana da aminin blogger sai ya bashi bidiyon nan take ya ɗora a internet. "Amma Dr Abraham zai iya shiga court fa" In ji Alhaji Wada. Boɗejo ya ce "To ya shiga mana? Mu ma sai mu je court muga me zai faru" * Cikin sauri Accouter yake driving motarsa zuwa wajan matar data haifi jaririn wanda Aafiyyah ta haɗa su, sanda Aafiyyah ta je asibitin dake cikin Fs world, taga jaririn dake tsananin kama da Hon Maɗatai sai hankalinta bai kwanta ba, ta nufi ɓangaren da take gani a rufe tana shiga taga wata budurwa tana ta kuka bata jima da haihuwa ba an ɗauke jaririn za'a siyar dashi, ta samu damar ɗauke yarinyar mai suna Yasmin, ta ɓoye a nan take faɗa mata cewa ga yadda aka yi ta samu cikin, sai AAFIYYAH ta yi amfani da wani mutum ya je ya siyi jaririn, yana siya ya kaiwa Aafiyyah ita kuma ta bawa Yasmin ta siya mata gida ta ɓoye yarinyar a ciki. Wazeer ya ƙarasa gidan da Yasmin take ciki tana zaune tana shayar da jaririn idanun nan nata jajur, ta yi saurin miƙewa ta ce "Yaa Wazeer" "Yasmin sako hijabi da takalmi ba lokaci" ya faɗa yana duba agogo. "Ina zamu?" Ya ce "Gidan t.v zamu a haska ki live ki faɗi dukkan abin da ya faru ok?" Ya sata a gaba suka nufi gidan t.v bayan ya yi waya da ƴan jaridu. * Sanda Aafiyyah ta shiga gida akan idanun AA da Dig Abdul-Johar, daman ba gidan mijinta ta nufa ba idanunta a juye kamar gauta ya rine sosai. Babu wanda ta kula ta nufi ɗakinta dake gidan message ta yi wa Kinal akan tana son ganinta. Babu jimawa Kinal ta shigo Ummi ta ce "Yau Kinal ce a gari?" Tana murmushin ta ce "Wallahi Ummi, ina mutuniyar ne?" "Tana ciki, daga asibiti ta gudu ai kin ji mene ya faru da ita ko?" Kinal ta ce "Abu babu daɗi Ummi, na gani a social media Allah Ya tsare ya kiyaye gaba" Ummi ta ce "Amin, amm don Allah ki riƙe alƙawari kin ji?' "In sha Allah Ummi" cewar Kinal ta faɗa tana nufar ɗakin Aafiyyah. Durƙushe ta samu Aafiyyah a tsakiyar bedroom ɗin ta ce "Madam wannan kiran na gaggawa fa?" Ta ce tana cilli da handbag ɗinta. "Matar AA ya aka yi?" Ta sake tambaya. "Kinal wacece ni?" Aafiyyah ta faɗa tana miƙewa tsaye ta juya ta kalli Kinal, gaban Kinal ya faɗi sosai ganin yadda idanun Aafiyyah ya rikiɗe ya yi jawur kamar garwashin wuta ƙirjinta kamar zai yi magana saboda ɗagawa da yake yi. Ta kasa magana. Aafiyyah ta buga mata tsawa ta ce "Kinal wacece ni?" Kinal muryarta na rawa ta ce "ummm amm ban fahimta ba" "Ƙarya kike yi Kinal, kin fahimta, kin gane abin da nake magana. At least ko kowa zai rufe ni ban dake, na ɗauka ke aminiyyata ce ko?" "E haka ne" cewar Kinal. Aafiyyah ta ce "Good, yaushe amintarmu ta fara? Ni dai kawai Paaahh ya nuna mini ke ya ce ke aminiyyata ce, Kinal don Allah don girman Allah saboda ƙaunar da kikewa Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama ki faɗa mini wacece ni? Wacece Safiyyerh me ya saka aka kira ni da Aafiyyah, Kinal ki faɗa mini na taɓa yin Fgc ne, ki faɗa mini waye Kimiyya" ta saki kuka tana durƙushewa tare da riƙe ƙafafuwan Kinal ta ce "Ki tausayi mini, ki tausaya zuciyata ki tuna ban taɓa cutar da kowa ba, ban taɓa cutar dake ba kada a haɗa baki dake a cutar dani, ni ba wani abu zan yi ba kawai ina son sanin kai na ne, wallahi wannan Safiyyerh da ki kaga tana magana ba asalin Safiyyerh bace" ta sake tsananta kukanta ta ce "ki taimakawa aminiyarki, ki dubi ƙarfin amintarmu ki faɗa mini wacece ni mene ya faru dani, ni ba karayayyi bace zan ɗauka zan jure" Kuka Kinal ta saki itama ta durƙushe a wajan jikinta na rawa ta rasa me zata cewa Aafiyyah, gashi ko yanzu an sake gargaɗinta. "Zuciyata zata buga, gab nake da zaucewa Kinal ki taimaka mini" Da sauri Kinal ta miƙe tsaye ta na yin baya, itama Aafiyyah ta miƙe tsaye tana ƙoƙarin kama Kinal sai ta ji ta ce "I am sorry Safiyyerh ban san komai ba, maybe you should ask Qasim" Tana cewa haka ta juya da gudu ta yi waje, da sauri Aafiyyah ta biyo bayanta tana kiran sunanta sai Awais ya tare Aafiyyah ta yi masa wani irin kallo sai ta juya wajan Paaahh dake ƙoƙarin shigewa part ɗinsa, Ummimi na zaune haka Ummi da AA suna bin Aafiyyah da kallo. "Daddy who is me? Who is Safiyyerh Abdul-Johar Marafa, daddy waye Kimiyya, wace Aafiyyah, mene ya faru a Fgc, daddy wanne abu ne ya kai ni Lagos? Daddy ina da ɗa?" Ta jera masa tambayoyin hawaye na bin fuskarta ta buɗe masa manyan idanunta kuma. Kafin ya yi magana an hasko labarai matsayin breaking news fuskar Yasmin da jaririn hannunta da aka ɗan rufe gefen fuskarsa ya bayyana, inda ake tambayarta "Malama Yasmin da gaske yaron hannunki ɗanki ne? Da gaske kuma ɗan Hon Maɗatai ne kamar yadda jita-jita ta bayyana, da gaske Hon Maɗatai ne ya yi miki fyaɗe har kika haihu?" Wannan tambayar ya dakatar da Aafiyyah ta mayar da hankalinta kan t.v. tana kallon Yasmin da babyn hannunta da kuma Wazeer dake tsaye yana saurare. "Malama Yasmin ke muke saurare" Sai Yasmin ta fashe da kuka ta ce "Wallahi ƙarya ne sharri aka yi wa Hon Maɗatai, ni ban ma taɓa sanin shi ba tunda nake a rayuwa" Aafiyyah ta buɗe ido, ta ɗauki wayar Ummimi da niyar yi wa Wazeer messages jikinta duka rawa yake yi kamar daga sama ta ji Yasmin ta ce. "Wannan mutumin shi ya yi mini fyaɗe shi ya yi mini cikin" Yasmin ta faɗa tana nuna photon Dig Abdul-Johar Marafa ta fashe da kuka sosai ta ce "Sunansa Dig Abdul-Johar Marafa shine wanda ya yi mini fyaɗe, domin rufa masa asiri ƴar shi mai suna Safiyyerh Abdul-Johar Marafa Manager of FS WORLD INVESTMENT ta taimaka mini ta siya mini gida, ashe itama akwai ƙudirinta tana son Dr Abraham ya samu kujerar ɗan majalissar tarayya shi ne take ƙoƙarin ɓatawa Hon Maɗatai suna saboda suna ganin an sanar da sakamakon zaɓe akan Hon Maɗatai ya ci, ina tunanin azaman court da za'ayi suke son su yi nasara tunda akwai yiwuwar court ta ƙwace kujerar ta bawa Dr Abraham, amma wallahi Dig Johar ne ya yi mini fyaɗe, ba zan iya wannan rayuwar ba" Tana cewa haka ta buɗe wata kwalba mai ɗauke da fiya-fiya ta ɗorawa jaririn nata itama ta sha. Moh dage can gidan da yake zaune yana kallon komai ya yi shiru yana tunani, Dig Abdul-Johar mahaifin Aafiyyah dai? Akwai lauje cikin naɗi. Mutane sukai kan Yasmin ana jijjigata a daidai lokacin kuma Qasim ya shigo gidan t.v. ɗin yana tura mara lafiyar dake zaune saman wheelchair hannunta riƙe kyakkyawar jaririya sai nurse Bara'a dake riƙe da baby boy ɗin. Qasim ya ce "Idan an rasa wata shaidar to ga wata" ya faɗa yana ƙarasa tura wheelchair ɗin daidai nan aka hasko fuskar matar. A kusan lokaci ɗaya Moh da Aafiyyah suka yi wata zabura jikinsu na kyarma da ɓari suna nuna screen ɗin t.v tsananin shock ya saka Moh kasa motsi sai zuciyarsa dake motsawa tana raya kanta a cikin ƙirjinsa a zabure ya ɗauki key ya yi waje gani yake duk wata daƙiƙa da take shigewa kamar da numfashinsa take tafiya,gangar jikinsa da zuciyarsa na fuskarsa zuwa gare ta, har ya tafi ya sake dawowa domin tabbatar da abin da yake gane, ya zubawa fuskarta idanu sai ya ji ƙafafuwansa na rawa sun gaza ɗaukar gangar jikinsa kawai ya sulale ya zube saman ƙafafuwansa yana kai hannunsa saman t.v tare da shafa fuskarta idanunsa na cikowa da ƙwalla...... 💥Chapter 16: Amsh Gani ya yi zaman da yake yi ma sake ɓata masa lokaci yake yi, sai ya miƙe tsaye naman ƙirjinsa duka rawa yake, ya nufi hanyar fita sai ya sake dawowa ya durƙusa ya ɗauki p.cap da facemask ya saka bai ɗauki key ɗin mota ba, cikin sauri ya yi waje. Kasancewar har yanzu ana cikin hargitsin zaɓe ga kuma rashin abeben hawa da babu saboda zanga-zanga da ake yi ya sa ya nufi takawa da ƙafafuwansa cike da kuzari tare da mazantakarsa, kallo ɗaya za ka yi wa Moh kasan ba irin lusarin namijin nan bane, shi ɗin tsayayyen namiji ne, kuma senior man he is always serious bashi da wani hujja na yin murmushi balle dariya, kamar yadda bashi da hujjar zama ya yi fira, hakazalika bashi da cikakken lokacin ɓatawa wajan gulmar wani, sabgarsa ya fiye masa komai a rayuwa, he is a caring person akan abin da ya shafi mace, shi ma ba tattali ko rasshi ba, duk bai iya wannan ba, a yanzu ma bashi da nutsuwa da fahimtar wata mace baya tsofaffin feelings ɗin da suka gama mutuwa a zuciyarsa, kamar dama a dalilin Barewarsa ya fahimci yana da wannan nagartar ta ɗiya mace. A yanzu da yake jin kamar ya rasa komai zai yi wahala idan ba haka zai rayu babu mace a gefensa ba, idan ma batun sha'awa ne shi baya jinta gabaɗaya ko tsirara zai ga mace baya jin akwai abin da zai iya fisgarsa, yadda yake jin zuciya da gangar jiki da ruhinsa ba zai iya zama da mace watan SAFIYYERH bestie ba, nutsuwarta ta kai, haƙurinta ya yi yawan da ba za'a iya kwatanta shi ba, haƙurinta tamkar wani dinare haka yake jinsa za'a tara mata sama ɗari ba'a samu mai nutsuwa haƙuri da gudun duniyarta fa, baya fatan ƙaddara ta bashi ikon kasancewa da wata mace domin zai iya yi mata dukan mutuwa zai iya casa ta kamar yadda ake casar shekararriyar fawa, gani zai yi kamar dalilin wata Safiyyerh ta rasu, bai san dalilin faruwar hakan ba, but Allah knows everything! Tafiyar yake yi amma gani yake kamar baya yake komawa, Allah Allah yake ya isa ga gidan jaridar, yana cikin tafiya sai ga mai napep ya tsayar dashi yaƙi tsayawa, zai ja napep ɗin Moh ya yi saurin riƙe kan napep ɗin cikin ɓacin rai mai napep ɗin ya kalli Moh ya ce "Malam wanne irin shirme da shashanci ne haka? Na ce ba aiki na fito yi ba, akwai inda na nufa ka bani hanya kafin jami'ai su ƙarasu ka ji ko?" Yatsu biyu Moh ya saka ya zare facemask ɗinsa zuwa ƙasa, ya zaro tsinin harshensa wanda har biyu yake ɗan ramewa ya ja huci ya fesar ya ce "Malam na gida, wannan ɗan'daba ne" ya ce a kumbure yana muzurai da manyan idanunsa masu sawa bugun zuciyar mutum tsayawa na wani lokaci. "Ah ah to Allah Ya baka sa'a ɗaukan ka ne dai ba zan iya ba" mai napep ɗin ya bawa Moh amsa cike da gadara. "Ka bani hanya" Ya sake maimaitawa. Sai Moh ya ɗaga rigarsa ya zaro wata shafceciyar wuƙa mai bakin zarto yana tsartar da ruwa daga bakinsa ya ce "To ya? Mu huce ko ka farka a barzahu" Jikin mai napep ɗin ya fara ɓari domin babu alamun imani a tattare da Moh babu fuskar rahama ya kunna napep ɗin ya ce "Oga shi ga, shiga mu je Allah Ya kaimu lafiya" gidan jaridar Moh ya faɗa masa suka nufa, shi dai mai napep ta madubi kawai yake kallon Moh har suka ƙarasa ko gama daidaita napep ɗin bai yi ba, ya fito da sauri ya nausa cikin gidan jaridar. Mai napep ya girgiza kai ya ce "Allah ka shirya mana zuri'a, ji yadda yake shagiɗar da bakinsa gefe sai warin sholi yake yi wai ni ɗan'daba bane" ya ce yana karkatar da bakinsa zuwa gefe. Har zai juya ya ce "Kai ina, gwara a yi komai a gabana idan ma rahoto ake nema zan faɗi komai daya faru domin kana gani kasan cewa ba abin arziƙi zai yi ba, zan jira nan, dama mai rake ko gyaɗa marau-marau zasu zo gittawa sai tsaiwar yafi mini daɗi" Dif dif sautin tafiyarsa yake badawa, yanayin tafiyar kamar ɗawisu yadda yake ajjiye ƙafa ɗaya bayan ɗaya saurin da yake yi kuma shine zai nuna zarihin ƙirarsa. Ya dinga ganin jami'an tsaro ta ko'ina baya raba ɗayan biyu duk a dalilin wannan abin aka sako jami'an tsaron, baya son yin wani abu da zai nuna bashi da gaskiya akwai abubuwan da yake son aiwatarwa idan suka kama shi kuma akwai aiki, sun jiƙa masa aiki sai ya yi baya-baya ya kama katanga hannunsa ya sauka akan kwalba wacce aka jera a saman katangar gidan jaridar matsayi kariya, jini ya fara zuba saboda sosai kwalbar ta ratsa cikin hannunsa da ƙyar ya fisge yana jin raɗaɗin har tsakiyar kan shi ya dunƙule hannun jinin na cigaba da zuba da sauri ya yi wata kwana yana haɗe zufa da gwama numfashi. A can ɓangaren Qasim ya durƙusa a gabanta ganin ta ɗan firgice tana neman sakin babyn hannunta a hankali cikin kwantar da murya ya ce "Nutsu Angel, ki nutsu kin ji?" "Ina jin tsoro" ta furta cikin ƙasa da murya alamu ya nuna tsoron mutanen wajan take yi ma. "Ke jaruma ce angel, ba ki da wani dalilin jin tsoro idan ina gefenki kin ji?" Ya ce yana rarrashinta "You told me za ka kula dani ko?" Ya jinjina mata kai alamar eh, ta saka farin hannunta ta riƙe nasa ta sarƙe su waje guda idanunta cike da hawaye ta ce "Ka yi ɗawainiyya dani sosai, ka kula dani a lokacin da nake hanyar mutuwa,ka jani jikinka a lokacin da bani da kowa, ka zame mini bangon jikina a lokacin da nawa bangon ya gaza ɗaukan al'amurana, ka zamewa yarana uba na duniya da lahira basu da uban daya shige kai...," Ta yi shiru sai ya ce "Madam ba lokaci ki bar duka wannan mu yi abin da yake gabanmu, wannan ita ce ranar da kike jira, ranar da zan sadaki da wanda ya dace kuma ga wannan ranar ta kasance yau Ubangiji Ya bamu ikon ruskar ta" "Madam.... Maaa" ya kira ta, ganin kamar ta ɗan fara yin daidai ta dai na wannan misbehaving ɗin like a child. Ta sunkuyar da kanta zuwa ƙasa, camera duka an saita a kanta ita kawai ake jira tunda daman live ne ya sake numfasawa zai kira ta ji ta ce "Al'Qasim!" Ba sunan ne bai saba ji ba, sai ya ji shi wani iri musamman data kira shi da Al'Qasim ɗin wanda Mimi kawai ke kiran shi sai Aafiyyah idan taso tsokanar shi. Ya kasa amsawa sai ya riƙo hannunsa ta miƙa masa jaririyar ta ce "Riƙe ƴarka" ya amsa ya riƙe babyn da take ta bacci cikin nutsuwa da ƙyar ya ce "Maaa, how do you knew my name?" Ta watsa masa harara ta ce "Me ka ce?" Ya girgiza kai kawai. "Kin shirya?" "Dr ba zan iya ba, ba zan iya ba ina jin nauyin hakan a ƙirjina" Shima ɗin kai ya girgiza ya ce "Me zai hana? Ki ƙarfafa zuciyarki ki tuna al'ummar da za ki ce ceto, ki tuna cewa bake kaɗai aka zalunta ba, rayuka da rawa sun ta gayyara dalilin shi, Madam ko a wajan Ubangiji fa ba ki da laifi, mara gaskiya kika tunawa asiri rayuka za ki ceto, ki tuna abubuwan da kika faɗa mini kafin ki shiga coma, ki zama mai confidence, kuma mun yi magana as confidentiality don Allah kar ki rusa yardar da na yi miki Madam, please!" Ta yi shiru, idanunta na cika da hawaye a hankali ta ce "I think, zan bar shi da Ubangijin Al'arshi zan bar shi da Sarkin da baya bacci, ni na san addu'ata ba zata tafi a banza ba domin ya zalunce ni, ya mini miki a zuciyata fiye da yadda baka tunani Qasim, ka ɗauke ni a wajan nan" ta ce a raunace muryarta na rawa. "Yanzu me kike so?" "Take me out of the country" "No, no Madam ki yi magana" Ta girgiza kai tana cewa "Do you think it's easy for me na tuna masa asiri? Kasan waye shi?" "Na sani tunda kin yi mini bayani maybe kin manta ne. Kina ji ko babu wani ɗan'adam daya kamata a ji tsoro a duniya muddin azzalumi ne shi, Ubangijin daya halicce mu shi kawai ya kamata mu ji tsoro, bayyana asirin mutane irin su Hon Maɗatai alheri ni, Madam don Allah ki yi saboda Allah da kuma al'ummar Annabi" "Uhmm" ta ce kawai. "Ba Uhmm nake son ji ba, ki dubi wannan matar yanzu da muke shigowa yadda ta sha fiya-fiya ta kashe kan ta, ta kashe jaririn data haifa ki duba yadda aka ci zarafin babban mutum irin Prof Marafa, har abada an ɓata masa suna, ɓacin da zai yi wahala a gyara shi idan har bake kika buɗe baki kikai magana ba, yana da nartacciyar zuri'a maza yana da ƴarsa mace kina ganin ba za su iya samun matsala a cikin mutane da zuciyarsu ba, don gane da abin da akaiwa mahafinsu na cewa ya yi wa, wata fyaɗe har ta haihu?" "Al'Qasim zan yi, but in one condition" "Mene shi?" "Will you marry me?" Ta ce tana juyawa a hankali tare da zuba masa idanu tana murmushi a hankali. Qasim ya ji maganar ta sauka a tsakiyar kan shi, zuciyarsa ta bada bugu dum! A cikin ƙirjinsa ya ji kalmar will you marry me ɗin tabbas, amma ya kasa fahimtar abin da kalmar take nufi baya son ma fahimta burinsa kawai ta yi abin da ya dace don haka sai ya jijjiga mata kai ta ce "Allah Ya shirya ka Qasim" ya yi shiru ta ce "Answer me" "I.... I... I will" he gave her an answer "To na shirya" ta ce a hankali. Ta gyara zamanta akan wheelchair ɗin ya damƙa mata babyn a hannunta aka gyara komai, conversation ɗinsu da Qasim daman iya su ne amma ya nunawa jama'a kamar argument suke yi a tsakanin nasu. Bayan ta daidaita ɗan'jaridar ya ce "kin shirya?" Ta ɗaga ya ce "Action...!" "Sunana Laylerh Abdulmaleek, ni kuma matar Alhaji Boɗejo ce wanda a yanzu duniya ta san shi da Hon Maɗatai asalin sunan shine Alhaji Boɗejo Maɗatai...," ta yi jim sai kuma ta juyo fuskar jaririn hannunta namiji ta ce "Dukkan wanda ya san Hon Maɗatai ko ya taɓa ganin photonsa ko poster ɗinsa zai ya zallar kamar da suke yi da wannan jaririn na hannuna, kamar copy and paste aka yi kamar kakin jaririn Boɗejo ya yi, ya tofar. Na haifi yara tagwaye a lokacin da ban taɓa tunanin samun rabo na ɗa a duniya ba, ban taɓa kawowa zai kasance cikin mata masu rabon ganin jininsu da zuri'arsu ba. Zai yi wahala mace ta zaɓi bayyana asirin mijinta ta wannan sigar saboda ko babu komai dole a ce Boɗejo mijin Laylerh ne, batun Boɗejo baya haihuwa ba gaskiya bane shi ne ya zaɓi kada ya haihuwa da kan shi gudun wani abu da yake ɓoyewa. Kafin na faɗa muku abin da nake son faɗa ku fara ganin wannan...," pictures ɗin bikinsu da Boɗejo take haskowa jama'a wanda adadin mutanen da suke kallon live ɗin Allah Ya yi yawa dasu, Boɗejo tun yana matashi ya yi aure kusan na ƙuruciya yana da jiki da suffar jan hankalin ƴan'mata ya iya ɗaukan wanka da tarin jinkima da ɗagawa shi ɗin tamkar wahainiyya haka yake ya iya tako wajan cimma manufarsa kamar ɓauna. Daga pictures na biki ta fara hasko wasu hoto sanda take da ciki fuskarta ba walwala shi kuma ya rungumo ta jikinsa. "Wannan ni da mijina kenan gani kuma aka ce ya kore ji. Ina son faɗa muku...," ɗif hasken wajan ya ɗauke akai disconnecting gidan jaridar gabaɗaya na wannan lokacin kamar daga sama suka fara ganin shigowar mutane masu ɗauke da baƙaƙen kaya jikin Laylerh ya fara rawa ta rikice domin ta gane mutanen irin mutanen da suka dinga mata allura a gidan Boɗejo jikinta na rawa ta yunƙura zata tashi ta kasa ta ƙanƙameta baby girl ɗin a ƙirjinta laɓɓanta na haɗewa ta ce "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un! Allahumma ajirni fil musibati, wa'aklifni khairan minna" Da ƙyar take addu'ar tana saki gani ta yi suna dumfaro ta ya saka ya kurma ihu tana sake riƙe babyn a ƙirji. Qasim ya yi saurin amsar jaririyar ya damƙawa Bara'a ta yi waje da gudu kafin su ƙarasu daidai nan Moh ya samu zarafin shigowa kamar wakilƙiya idanunsa ya sauka akan mutanen nan take ya gane guda biyu, sanda ya je wajan Jaa'afar da Safiyyerh ya ce kar ta shigo bayan ya gargaɗe ta suna zaune ya jiyo ihun Safiyyerh da gudu ya tashi daya fita babu ita sai ya yi waje a lokacin ya hango su suna jan wata mata zuwa cikin gidan tana ihu tana ɗago masa hannu sai ya yi kamar bai ga komai ba ya fice daga cikin gidan a lokacin daya fita ya samu Bestie jikinta na rawa sai kuka take yi, har suka shiga napep tana kuka yaƙi tanka mata sai ta marairace tana kwantawa gefen ƙirjinsa cikin kuka ta ce "Allah Ya shirya ka kana ji ina kuka ina ta maka kuka don ka rarrashe ni" Da ƙyar ya daƙile fuska ya ce "Na aike ki? Kukan daɗi yake miki" "Ni ɗin ko?" Ya ɗage mata girarsa biyun da suke cure yana lashe jajeyen laɓɓansa da suka tattare suka fiddo asalin sexcy ɗinsa da yanayinsa na Yoruba boy. Ita kuma ta yi shiru ta tsuke fuska ya saka hannu ya zungure ta, taƙi motsawa ya sake zungurinta taƙi motsi bai damu da mai napep ba ya zura hannunsa ta cikin hijabinta ya zura cikin riga, jikinta ya motsa da abin da yake mata amma ta ci mur taƙi bada kai ta haɗe fuska, sai ya ji rashin walwalarta na sokan naman ƙirjinsa bawai damuwa ya yi ba amma hakan ya taɓa shi ya cire hannunsa ya yi shiru. Ganin ya mata banza ya saka ta cire takalmanta ba zato ya ji tana kai masa duka a ƙirji hawaye na biyo fuskarta ya ware hannayensa biyu ya zura ta cikin ƙirjinsa ya rufe ta, ta dinga motsi har ta gaji ta fashe da kuka tana rungume shi cikin kuka ta ce "Allah Ya yafe wa mijina, Allah ga mijina ina son shi ko baya so na, Allah ka so shi, ka sanya Mala'iku so ƙauna ce shi, ina son shi haka" Ya matse a ƙirjin ya ɗora bakinsa a kunnenta ya fara ja mata fito cikin husky voice ya ce "Love me more Bestie" "I love bestien bestie" Ya cire ta a gefensa yana zuƙe harshe kamar mai shan ya ji ya ce "Ya miki kyau da kukan banza" "Uhm Mai dawa kenan" Sai ya ƙanƙantar da idanunsa ciki jin sunan da ta ce masa sai ta kyalkyale da dariya tana ɗaga hannu sama ta ce "Oh! Laaaa tuba nake ranka ya daɗe mijin Safiyyerh kai na ƙasa kar na zama rest in peace yanzu da hukuncinka" sai ya juya yana danne murmushinsa ya ce "Barewar Mai dawa" ta ce "In sha Allah" Da ƙarfi ya ce "Subuhanallahi napep zai kife" salati ta yi da ƙarfi ɗaraf ta haye cinyarsa cikin napep ɗin tana salati "Allah kar ka ɗauki raina ban bar baya mai kyau na haifawa bestie babies ba" yana mamakin yadda gabaɗaya sokuwa ce bata da wayo sam sai ya sake cewa "ka mata ƙadangare" ta kalle shi kamar bashi ya yi maganar ba waje ma yake kallo abin shi ta harare shi ta ce "Zan rama. Ka san me wata mata na gani tana kuka na taimaka mata shocked da tsoro ya hanani motsi kasan na taɓa jin kukanta a cikin baccina, na ji ina son matar da taimakon ta. Idan Ubangiji bai bani dama da ikon hakan ba to don Allah ka taimaka mata ka ji botsararren mijin deer?" Ya share ta sai ta ce "ka tuna mini ma, don Allah yau ka faɗa mini yadda ka cirewa Aafiyyah lizards ɗin nan, Aafiyyah bata son lizard ko kaɗan" sai taga yana murmushi shi kaɗai nutsuwarsa ta bayyana ya lumshe idanunsa ya buɗe shi yama manta amma shi da kan shi idan ya tuna yadda ya cire ƙadangarun daga cikin ƙirjinta sai ya yi murmushi. Baki ta buɗe za ta sake masa surutu ya yi saurin zura matsa yatsarsa cikin bakinta ya ce "Silent, quiet deer ko ki zama abin farautata yau da daddare?" Ta tsotsi yatsar ta fito dashi ta ce "jeji zaka dani? Farauta za ka yi yau?" Ya ɗage mata gira ya ce "Farauta mai kyau ma, Allah Ya kai damo da harawa?" "Ina Allah zai kai so?" Ya cije lips ya ce "Ba ki da kai, nikam na auri mara wayoo" Ya sake yin dariya yana gyara mata zama a napep ɗin saboda wata data shigo sai kawai ya bar fiyya a cinyarsa ya ce "Allah Fiyya ba ki da kai" bata kula shi ba tana ji yana mata cakulkuli sai ta take masa ƙafa *Ganin Laylerh ya saka Moh tuna abubuwan da suka faru a lokacin sai ya kasa motsi shikam a rayuwa ya yi Bestie abubuwa da yawa na rashin ɗa'a. Qasim ya durƙusa ya ce "Madam come with me?" Ta girgiza kai ta ce "Al'Qasim bana bar maka yarana ba? Jeka kula dasu ka bari su ƙarasa kashe ni" bai tsaya sauraranta ba, ya tattare hannun rigarsa ya yi Astagafirulla ya sunkuceta tare da saɓa ta a wuyansa ya nufi waje bai kula da Moh ba. Yana fita samudawan suka yi kan Qasim cikin zafin nama Moh ya cire wuƙar hannunsa ya yi wani shaɗi da ita, cikin sauri wanda aka yanka ya yi baya ya ce "Waye kai?" "Sai godiya" Moh ya ce yana shata layi da jinin daya lakata da jinin mutumin daidai nan hasken wutar ya kawo gaban mutumin ya faɗi mijin wanda suka kashewa mata ne ai? Wanda da ace ya san cewa sune suka kashe masa mata, to tabbas yau sai dai buzunsu. "Ka bani hanya" "zan yi maka bille" "Kai wuƙa ce hannunka ni bindiga ce a hannuna wake da riba.....," Kafin ya ƙarasa maganar Moh ya ɗaga shi ya buga shi da ƙasa ya damƙi hannunsa ya karya ya sake karya hannun ya ɗaga ƙafarsa ya daki gaban mutumin cikin sauri sauran mutanen suka dinga yin baya shi kuma Moh ya damƙi ɗayan ya ja shi waje ya cilla shi cikin napep ɗin wanda ya tsaya jin gulma. Bara'a na tsaye taga mutum gabanta kafin ta yi magana ya amshi jaririyar hannunta ya zubawa fuskar jaririyar idanu da wani irin yanayi mai wahalar fassara wa yake bin fuskarta da kallo, tunda aka hasko fuskar jaririyar a t.v kamanninta da Deer suka firgita shi, suka saka tunaninsa ya tsaya cak ya fara zargin duk inda babyn nan take to akwai Bestie a wajan, haka zuciyarsa take faɗa masa, har ya fita amma domin ya sake tabbatar da kamannin jaririyar data babyn daya gani ya saka ya dawo ya yi zaman dirshen a gaban t.vn zuciyarsa na bugawa da ƙarfi. "Malam waye kai?" Bara'a ta tambaya tana ja baya, domin wani irin kwarjini Mai dawa ya yi mata, a hankali ya miƙa yatsarsa ya riƙe tafin hannun babyn ɗis ɗis take buɗe idanunta ya zubawa cikin idanunta ido, komai nata iri ɗaya ne dana bestie da tsotsar yatsa da lumshe idanu da tsotsar lips komai har ɗan ƙaramin bakin, ji ya yi idanunsa sun yi masa duhu kamar abu ya cika su. "Bara'a me kike jira?" Qasim ya ce yana ƙarasawa wajan cak ya yi ganin Muhammad sai ya dake ya ce "Muhammad me kake yi a nan?" Moh ya share, cikin sauri Qasim ya ce Muhammad ina magana kana share ni?" Ya faɗa yana tsayawa gaban Moh. "Ke.... fece" Moh ya cewa Bara'a ba tare daya ɗago kai ba. Cikin sauri ta bar wajan Qasim ya ce "Bani babyn nan, sai ka yi ta zama a nan Muhammad" "Sunana Muhammad Mutallab Abdullahi inkiya MOH, wata inkiyar Mai dawa ko ka ce Scorpion" "Buddy!" Kimiyya ya ce da ƙarfi sai ya jujjuya ganin ba kowa ya ce "Mutallab bana son wasan banza, ina Muhammad waye kai waye Muhammad" "Da Hausa, da mayan wasali na karta maka ai Muhammad Mutallab" Qasim ya ce "Ka san me nake nufi, na san cewa Fid sun kama ka kuma basu sake ba, ba kuma za ka iya barin wajansu ba saboda tsaron da wajan yake dashi, me kake shiryawa? Ya akai ka zama Muhammad jinjina har ka shigo gidanmu, ko kai ne Muhammad kuma kai ne Mutallab?" "Ina Safiyyerh?" Moh ya ce a daƙile yana sake kallon jaririyar hannunsa. "Wacce Safiyyerh?" "Wacce nake da ikon tambaya, ina matata? Ina aka kai ta?" Anya Mutallab nada hankali yake tambayar wacce ta yi shekaru uku a ƙasa da rasuwa tana neman shiga shekara ta huɗu. "Subuhanallahi ka fi kowa sanin matarka ta rasu" "Liar, ƙarya kake yi kimiyya ka fito mini da matata duk inda yarinyar nan ta fito to daga jikin deer ta fito, ni nasan Safiyyerh ba zata taɓa mutuwa ba, tana nan a raye kawai cutata akai da aka rufe ni, ko wani abu na aikata ba za ta yi fushin da zata hukunta ni ta wannan hanyar. Qasim where is my wife ina Barewata?" Su Goje da Mangal ne suka zo wajan Goje ya ce "Sarki ya aka yi ne?" "Ka faɗa masa da yaran da zai gane, ya fito mini da matata" Ya ce yana juyawa tare da ƙoƙarin barin wajan da jaririyar data fara kuka a hankali tana razana. Cikin saurin Qasim ya ce "Ku dakatar dashi daga tafiya da ƴar mutane, kun taɓa ganin mamaci ya mutu ya dawo ne?" Ya yi maganar kamar da muryar rashin gaskiya. Goje ya nufi wajan MOH yana zuwa ya cake ya ce "Kawo yarinyar nan" "Goje" "Mutallab" Goje ya kira shi. "Ka bani waje, idan ban tafi da ita ba baza su taɓa dawo mini da mahaifiyarta ba, ja jiki" "Kana da nonon bata kenan?" Mangal ya ce "Kambu au nono ake basu? To na sai a tatso na akuya ba?" "Ji ɗan mahaukaciya kai yaron nan mugun daƙiƙe ne, shege kowa ma nonon akuya yake sha kamar ka?" Mangal ya buɗe ido ya ce "Nima da na sha na akuyar ai mugunta ce, kuma gashi ban mutu ba ina raye sai na zama Sadam-Hussain" ya juya ya kalli Mutallab ya ce "Sarki, mu ware kawai da ƴar babyn nan zan kwalo wata akuyar ta dinga shayar da ita, ko kawai ka dinga bata nonanka tunda naga manya ne ko ya?" Ya yi maganar tsakani da Allah har cikin ran shi. Moh ya ɗago ya kalle shi sai ya ɗauke kai ya ce "Salman" Mangal ya ce "Sai godiya, ka dake Sarki yau ranar sa'a tace Sarki ya kira sunana" ya faɗa yana busa sigari "Ko ka yi shiru, ko kuma dai yanzu na saka ka bacci" Goje ya ce "Ka bani yarinyar nan mu fece nan ba wajan zaman mu bane saboda ɗankoki idan cinnaku suka dafe mu akwai matsala gwara mu gara yanzu a tayoyinmu" "Sultan, za k bar wajan nan" Ya cewa Goje shi tunda ya ji Moh ya kira sunansa na gaskiya ya san akwai Matsala domin bai ɗauka ya san sunan nasa ba da gaske. Qasim ya ce "Mutallab ka bani yarinyar nan" Moh ya yi ƙirmishi sai ya nufi waje Qasim zai yi magana Goje ya girgiza kai da sauri Mangal ya je ya faki idanun Moh ya caka masa sirinji a wuya, Moh ya tsaya cak jikinsa ya ɗauki rawa jijiyoyin jikinsa suka saki ya kasa motsi ko yunƙurin tafiya kuzarinsa ya kau idanunsa sukai jawur sai numfashi yake fesarwa cikin tsananin azabar da allurar take ratsa shi. Goje ya amshi jaririyar yana ji yana kallo ya damƙawa Qasim, shi kuma Qasim ya nufi mota ya bubbuga aka buɗe ya bawa Bara'a ya ce su shige gidan Jeddah kar su koma asibiti yanzu zai zo. Goje da Mangal suka ja Moh zuwa napep suka nufi Camber ɗinsu. * Saudat na zaune saboda yau suke saka ran sallama ba kowa a ɗakin sai ita idanunta jajur ta yi kuka har ta gaji ciwo sosai zuciyarta ke yi mata na baƙin ciki. A hankali ya turo ƙofar room ɗin hannunsa riƙe da baƙar leda yadi ne a jikinsa ruwan ƙasa ya yi kyau sosai sai ƙamshi yake yi yana ƙaunar tsafta ya kuma zani ƙazanta sam. Saudat na jin motsin shi ta yi saurin rufe fuskarta saboda tsoron shi take yi sosai gani take yi kamar zai kuma nanata azabar da ya yi mata. Ya ƙarasa tare da kallon ta yaga bacci take yi sai ya duƙa daidai fuskarsa yana fesa mata numfashi ya ɗora hannunsa a kanta ya ji da zazzaɓi sai ya koma ya zauna kan kujera wayarsa ya ɗakko ya fara dannawa a hankali cikin nutsuwa. Saudat ta buɗe ido, ta zubawa Jaheed jajeyen idanunta ashe yana da kyau sosai ya iya gayo gashi a nutse yake sai ta zabga masa harara, duk yana jin abin da take yi a jikinsa sai ta turo bakinta tana murguɗawa "Damn it" Jaheed ya ce yana miƙewa tare da saka wayarsa cikin aljihu. "Kar ka ƙarasu mini nan" ta ce a shagwaɓe idanunta fal hawaye. "Kina da inda yafi ƙirjin Jaheed Sada ne?" Ya ce yana nuna ƙirjinsa da hannunsa yana ɗaga mata gira da ƙarasawa sai ta yi sauri zata juya ya riƙo fuskarta yana sakin lallausan murmushi ya ɗora kanta a cinyarsa ya ce "Ya Saudah mun yi faɗa ne?" Ta yi shiru taƙi magana. "Oh common Saudah, Jaheed miss you alot my tom" Still taƙi magana sai shassheƙar kuka, ya ɗagota ya ɗora a cinyarsa kokawa ta fara dashi tana dukansa da ƙarfi idanunta rufe ya tattare hannun rigarsa ya riƙota ya jirkito da ita jikinsa kan ta a ƙirjinsa, ya dinga shafa kanta ya yi shiru a hankali ta fara magana "mugu, azzalumi ka cuce ni ka zalunce saboda bani dashi, ka yaudare ni saboda ina neman abincin ci a wajanka ashe ba don Allah kake yi mini komai ba, wallahi ba zan yafe ba na tsane ka...," "Please Saudah kar ki hukunta ni ta haka kin ji? Na yi kuskure ki bani dama na goge kuskure na, kin ji Tom?" "Na tsaneka" "Saboda na miki fyaɗe?" Ta kuma cewa "Na tsaneka" "Ƙaddara ta haddasa komai" "Bana son ganinka" "Ni ina son ganinki" "Ka fita daga rayuwata" "Yanzu na ji na shirya rayuwa domin ki Saudah" Jaheed ya ce a hankali. "Na tsaneka, na tsaneka, na tsaneka" "Ina son ki, zan soki, ina kan son ki" Kuka ta saki sosai ya rungumeta ya ce "Idan kika tsane ni to waye zai so ni? Ba kisan meke damuna ba ko? Ba ki san yadda nake samu abincin da nake ba ki ba ko? Yadda kika tsane ni haka na tsani iyayena, domin a karkararmu akwai tsangayoyi kala-kala amma sukai burus suka ƙi sani a can, ina kuka ina cewa bana son zuwa almajiranci amma Baffa yaƙi wai su kamar gado haka zuwa almajiranci yake abin kunya ne ka haifi ɗa yaƙi zuwa neman karatu wani wajan, don haka dole zance gashi Baffa yana yin noma muna da abinci sosai baya yanke mana amma ya kawo ni nan garin daba uwa ba uba, ba wa ba ƙani, ba mai cewa bari ko ka yi. Ni kam Saudah ki yi mini uziri, ki yafewa Jaheed Sada" "Ba zan taɓa yafe maka ba, kuma sai na faɗawa Malam ka yi mini iskanci, ina cewa kar ka yi, kar ka yi amma....," "Mene kar na yi?" "Saka abin...," "Uhmm Saudah kenan. Ki rufa mini bargon asiri mu magance matsalar tsakaninmu mu zama abu ɗaya tamkar kabejin dake cikin kofensa. Give a chance zan goge laifina kin ji? Idan kika faɗawa Malam cewa almajiransa ya yi wa ƴarsa fyaɗe da matsala ba kaɗan ba" magana za ta yi ya saurin haɗe bakinsu waje guda ta yi shiru tana ji yana kissing nata smoothly. Bacci ya ɗauke ta a jikinsa ya dinga danna mata ƙafa a hankali yana yi mata pictures masu kyau. Saƙo aka turo masa. "Dukkan wata Eng Ali wali ya taɓa mu'amala dashi da namiji ya nemi wajan ɓoyewa domin ya saka a kashe su ko kama su a kai su gidan yari a musanya su da masu laifi, Ɗan'yaro ka bar garin nan yanzu na turo maka wannan saƙon saboda wani abu mai muhimmanci kuma ina som gyara kuskure ne, kabar garin nan" Da sauri Jaheed ya miƙe tsaye jikinsa na rawa ya juya ya kalli Saudah sai ya sake kallon saƙon da aka tura masa cikin tashin hankali ya yi waje, ya fice tare da barin Saudah ƙwance a gadon asibiti bayan ya yi mata fyaɗen da babu wanda ya sani daga shi sai ita, sai Allah daya halicce su * A can gidan Dig Abdul-Johar Marafa kowa sanda Yasmin take wannan jawabin tun kafin ta ƙarasa Paaahh ya yi saurin sanya hannunsa yana dafe ƙahon zuciyarsa ya fara yin baya tare da soma tari a hankali ya saka hannunsa ya rufe bakinsa a gigice Aafiyyah ta yi cilli da wayar hannunta duk da shocke na ganin jaririyar hannun Laylerh. "Daddy, Daddy!" Ta ce a gigice tana nufar wajan Paaahh kafin ta ƙarasa ya yi saurin zubewa a wajan saboda wata bugawa da zuciyarsa ta yi a ƙirjinsa wani gudan jini ya yi fitar gurbi daga cikin bakinsa ya sauka a tafin hannun Aafiyyah zaro ido ta yi jikinta na rawa ta fasa ihu tana yin kasa kamar zata kifa cikin sauri AA MAJ ya riƙota ta faɗa jikinsa a sume kwantar da ita ya yi a kan kujera. Junaid da Awais da Dr Hash suka yi kan Paaahh gabaɗaya a ruɗe suna kiran sunan shi amma baya ji komai nasa ya ɗauke. "Take him to the hospital, yana ciwon zuciya" cewar Ummimi Ummi tashin hankali da fargaba ya saka ta sulale ƙasa ta yi zaman ƴan bori sai ajjiyar zuciya take saukewa. "Ciwon zuciya? Daddyn?" Dr Hash ya furta a kiɗime yana ɗora hannunsa a ƙirjin Paaahh tare da ɗan dannawa a hankali. Paaahh ji yake kamar ana fisgar ranshi zuciyata ya ji ta daina bugawa wani duhu da gilmawar abu yake gani a cikin idanunsa, ya san idan wani abu ya same shi tamkar Maamah ya samu, an san cewa babu wani abu da yake zama raunin Aafiyyah sai an taɓa Dig Abdul-Johar shi ya saka aka zaɓi wannan hanyar wajan ganin an kashe Aafiyyah da ranta bashi ake so ya mutu ba, Aafiyyah ake son ganin bayanta. "Maamah, Maamah" Yake cewa a hankali yana miƙa hannunsa AA MAJ ya miƙe ya ƙarasa ya ce "Sir you'll be fine in sha Allah" "Zafi nake ji a nan ɗina Aliyu" "Sannu sir" Ya nuna musu Aafiyyah ya ce Ina Junaid, Hashim, Awaisu, Aliyu?" Ya kira su, su huɗun ya kama hannunsu ya riƙe cikin nasa ya nuna musu Aafiyyah wacce ta ja numfashi a fisge kamar mai aljanu tana zabura, daidai lokacin Anty Turai da Wahee da Zahiderh suka shigo gidan daman daga wajan malami suke aka ce suyo nan mai tsaye su yi aikinsu akan Aafiyyah. "Subuhanallahi gida ya rikice meke faruwa a nan?" Ta ce tana nufar wajan da zaratan samarin suke Wahee ta yi jigum Zahiderh kuma ta kafe AA MAJ da idanu wanda ya ɗora kan Paaahh a cinyarsa. Ummimi ta miƙe ta nufi ɗaki zata ɗakko wayarta cikin rashin sani ba tare da kowa ya ankare ba Aafiyyah ta zabura kai babu ɗankwali ba takalmi ta yi waje idanu rufe mai gadi baya nan sai ya nufi bakin gate ta fice daga cikin gidan gabaɗaya idanu rufe. A can gidan kuma Paaahh ya damƙe hannayen yaran nasa ya ce "Aliyu ga Junaid da Awais nan ga dr Hash nan, Aliyu ga Ummi nan, Aliyu ga Zahiyerh nan, Aliyu ga Turai nan wannan nauyin naka ne na bar maka" ya yi shiru jini yana cigaba da fita daga hancinsa da bakinsa idan ya tuna cikin Aafiyyah sai ciwon ƙirjinsa ya ƙara zafi, idan ya tuno maganar ɗazo ta Yasmin sai ya ji ya sallamawa rayuwa da duniya. Ya numfasa ya ce "Safiyyerh" "Me ya samu Safiyyerh?" Cewar J "Ku tabbatar ta yi dariya a rayuwarta, ku tabbata babu abin da zai ƙara sanyata kuka Aliyu ka zama uban Maamah na bar maka wannan matsayin" sai ya fara salati jikinsa ya saki ihu Anty Turai ta saka AA MAJ ya runtse idanunsa hawaye na sauka a idanun Dr Hash Awais kuma kifawa kan Dig Johar ya yi yana sakin kuka tare da faɗin "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un innalillahi!" Miƙewa AA MAJ ya yi jiri na kwasar shi da nufin ɗauke Aafiyyah daga gidan gabaɗaya kar ta farko taga wannan tashin hankali kar kuma a yi biyu babu sai dai babu Aafiyyah a rikice ya haura upstarts. Aafiyyah ta yi nisa ƙarfarta futu-futu tana tafiya a tsakiyar hanya kamar mahaukaciya wata mota dake bayanta ta fara yi mata horn din din din amma bata ji. Wanda ke baya hakimce a motar ya ce "Mene ya faru ne?" Driver ya ce "Sir wata mahaukaciya ce akan titin ita na kewa horn bata ji amma" Barrister ya ce "Mahaukaciya kuma?" Ya faɗa yana kallon Amsh dake tsalle akan kujerar motar. "E, mahaukaciya sir" "Ikon Allah, ka yi parking muga wacece ta ya zamu taimaka mata" "Ok sir" ya yi parking a kusan tare Barrister da Alhassan da shima ya hango Aafiyyah suka fito daga mota Barrister ya fito yana cewa "Come with me Amsh" ya ce yana ɗakko cute babyn yana nufar wajan Aafiyyah data durƙushe a wajan....