[4/28, 9:59 AM] khaleesat Haiydar ✍️: *If you should come across this post plss say a prayer for my late father, Allah ya sabunta masa rahama, ya gafarta masa da duk musulman da suka riga mu gidan gaskiya, Allah ya kyautata makwancinsu gaba daya, ya sa mutuwa hutu ce a garesu, Allah ya yafe masu kurakurrensu, Allah ya bamu guzurin tar da su* 🥺 **All thanks to Allah S.W.T for the chance and privilege to commence this new book, yanda muka fara lafiya Allah ya sa mu idar lafiya* _Hmm ga fa Halysaah, Allah ka bani ikon delivering babu cece ku ce_ *This first page goes to all the members of Mayraah Conversation, i love and appreciate you all*🥰 ✨✨HALYSAAH✨✨ ✍🏻 By _Khaleesat Haiydar_ 1.... Tsaye take ta jingina da trunk din bishiya a wani babban garden dake dauke da shukoki iri iri da suka kawata wajen, tsuntsaye sai shawagi suke a garden din happily making a chirping sound as the sun set slowly, the view was so beautiful and breathe taking, duk da yanda ta kafe view din da ido gaba daya hankalinta baya gun, she was just staring at the setting sun absentmindedly, tayi nisa cikin tunanin da take, daga gefenta wata ma'aikaciyar asibiti ce in her mid 40, likitar ta dafa ta tana kallonta cikin kwantar da murya tace "Magariba ya gabato mu je kiyi alwala ko" Kallon likitar kawai take babu ko kiftawa kamar bata fahimci abinda take cewa ba, sai ga hawaye ya fara taruwa idonta tana sauke numfashi a hankali, likitar ta kama hannunta ta jawota jikinta calmly tace "C'mon sweet heart, are you breaking ur promise already?" ta kwantar da kanta jikin likitan hawaye wasu na bin wasu a fuskarta, likitan ta lumshe ido tana patting dinta duk jikinta a sanyaye, a tare suka juya jin footstep a garden din, ya tsaya daga inda yake bai karaso ba yana kallonsu, likitan ta fara gaishesa cikin girmamawa, zame jikinta tayi daga na likitan ta juya masa baya alamar ko ganinsa bata son yi hawaye na zuba idonta, ji take kamar numfashinta zai dauke kamar ko da yaushe, ta fashe da matsanancin kuka ta dafe trunk din bishiyar dake gefenta, ko amsa gaisuwan likitar bai yi ba ya juya ya fice daga garden din, da sauri likitan ta kamota ganin faduwa zata yi, ta fara kokarin zaunar da ita akan lallausan carpet dake shimfide wajen trying to calm her down tace "Haba kanwata, me yasa baza ki cika min alkawarin da kika daukar min ba?" Muryarta na rawa tace "Kiyi hakuri bazan iya ba wallahi" Rungumeta likitan tayi tana bubbuga bayanta a hankali wani mugun tausayinta na shigarta, tayi attending to different cases in her career as a medical Doctor amma babu wanda ya taɓa daga mata hankali ya tsaya mata a rai irin na baiwar Allahn nan, she wish she can take away her pains, she wish she can make her happy once more, she wish she can make her forget the past and face the present, a hankali likitar tace "Halysaah...." khaleesat ta daga rinannun idonta tana kallon likitan, likitan tace "Kiyi hakuri Halysaah, kiyi hakuri" Khaleesat ta sauke idonta bata ce komai ba, likitan ta daga ta tana rike da hannunta suka bar garden din zuwa babban compound din gidan. Few years back! "Talk to Abdul about it, nasan bazai taɓa yarda da haka ba, and he will definitely find a way out for u immediately..." Khaleesat ta daga manyan idanuwanta tana kallon kawarta Safiyyah, kamar bazata ce komai ba sai kuma ta sauke idonta a hankali tace "That will be another huge burden Safiyyah, u know how expensive apartment can be in this state, gida da akwai tsada sosai, kuma na fa ce maki ni bazan sake tambayarsa komai ba, ko kuma ince yayi min wani abu...." Safiyyah tace "Cabdi, to in ba ki tambayesa ba kina da wanda zaki tambaya? Balle ma kinsan halinsa lokaci daya tsaf zai juya situation din nan against you, i think gwara kawai ki sanar masa yafi maki kwanciyar hankali" Khaleesat tayi shiru tana nazarin abinda Safiyyah ta ce, sai kuma ta sauke ajiyar zuciya tana girgiza kai tace "It's fine Safiyyah, ba sai na gaya masa ba i will cope in sha Allah, after all we have just a year and a half to go" Safiyyah na kallonta ta kamo hannunta tace "Ko zaki dawo wajena sai in gaya masu kawata zata zo ta ɗan zauna da mu zuwa wani ɗan lokaci?" Khaleesat ta girgiza kai tace "Let not inconvenience them Safiyyah, kar ki damu kawai, i will sort my self out...." Safiyyah tace "No, i will talk to Ya Musty about ur current situation khaly, nasan bazai ce a'a ba, matarsa ce dai gagarumar er iska, and do i even care? Ba ki ma san me take min ba yanxu a gidan, duk dare bata girki da ni sai dai in nemi abinda zan ci tunda kinsan Ya Musty night shift yake, ni kuma dama kin san i prefer junk food, kawai sai in hada cornflakes in sha abu na" Khaleesat tayi murmushi tace "Shine kike son in bi ki zuwa gidan a haka ko? You are very funny" Safiyya ta juya ido tace "So what? Naga ai ba kanta zaki zauna ba in kin dawo gidan, Yaya Mustyn nan fa is my cousin brother ko kin manta ne? Saboda haka ko taki ko ta so dole in zauna a gidan har in gama karatuna, very wicked and self centered woman, wallahi kar ki wani damu in dai nayi ma Ya Musty magana kawai ki dauko kayanki ki dawo gidan ko zuwa gobe ne...." Khaleesat tace "Aa gaskiya don't even start that Safiyyah, i will cope with my present situation with time, nasan zan saba gradually, beside it's something that is normal kawai dai ni ce nake damun kai na saboda addinina da culture dina da dai wasu abubuwan da baza a rasa ba, any way... it's fine Safiyyah" Tana fadin haka ta kalli wayarta dake hannunta jin shigowar notification, tace "I think my Lyft is here Sophie, sai gobe in Allah ya kai mu" Safiyya ta sauke ajiyar zuciya tace "Ohk then, take care of ur self, i will stroll home too" a haka suka rabu, Khaleesat ta nufi Lyft din da tayi ordering zai maida ta gida. Khaleesat na kitchen wajen karfe goma na dare ta gama girka Noodles da zata ci for dinner kenan taji alamar an bude kofar parlor, a hankali ta karasa juye Indomie dinta a plate ta dau fork ta saka sannan ta wanke pot din ta ajiye, ta bude fridge ta dau bottle water ta fita daga kitchen din, hanyar dakinta ta nufa direct, dai dai corridor aka bude kofar wani room that is just few steps away from her own room, ko kallon direction din bata yarda tayi ba tana kokarin bude kofar dakinta taji ance "Hi, good evening, we didn't get to meet when i was here in the morning I guess you've already left for school then, you can call me Jay, and i am ur new House mate, I moved in this morning...." Sai a sannan Khaleesat ta juya ta kallesa amma bata ce komai ba, ya gyada mata kai yace "Jay" babu yabo babu fallasa tace "I see" Ganin zata shige daki yace "A minute pls" Ta juya ta sake kallonsa da wani expression, a takaice yace "Ke bahaushiya ce?" Ta ɗan hade rai tace "I don't know what u are talking about" Yace "Oh ohk, i am asking for a permission..." Ita dai kallonsa kawai take, Ya gyara tsayuwarsa yace "As u can see it's late already now, can i use some of ur portable water and Beverages before i get mine tomorrow if you don't mind?" Khaleesat ta dauke kanta a takaice tace "Ohk" Yace "Alright" Daga haka ta shige dakinta ta kulle kofar ta saka key, ko da ta gama cin Indomie din bata ji zata iya bude kofa ta fita kai plate din kitchen ba, daga karshe kawai ta bar shi a wajen bayan ta shiga bandaki ta wanke bakinta ta dauro alwala ta fito ta zauna edge din gadon dakin ta dau wayarta, Miss calls din Abdul ta gani har biyu wanda yayi mata tun karfe shidda, ta sauke ajiyar zuciya tana duba agogon wayarta dake nuna mata karfe goma da kusan rabi, meanwhile karfe kusan biyar kenan na asuba agogon Nigeria, bude WhatsApp dinta tayi ta dubasa taga yana online, hakan yasa ta masa WhatsApp call, yana dagawa tayi kasa da murya ta gaishesa a hankali, Bai amsa ba yace "Yanzu kika ga kirana?" Ta sauke boyayyen ajiyar zuciya tace "Kayi hakuri, yanzu naga kiran wallahi" Yace "You mean tun daxu wayarki baya gun ki kenan?" Tace "Not really, tun dai da na dawo schl nake karatu, in few months time zamu fara exams" Yace "I see, shi ne yasa kika ga ban yi deserving lokacin ki ba don zaku fara exams, ta yaya ma wayarki zai yi ring ki ce baki sani ba in ba rainin hankali ba?" Rasa abinda zata ce masa tayi, don wayar a silent yake kuma ya hanata barin waya a silent on several occasions, to avoid further issues sai bata ce masa wayar a silent yake ba, a hankali tace "Kayi hakuri, wallahi ba haka bane, i am sorry..." Yace "Sorry for ur self, malama so nake ki gaya min kina ina har wayarki rang twice baki ji ba? ur lectures today terminated by 4pm Baltimore time, so ina kika je daga nan?" Ta rufe ido ta bude don ta fara gajiya da tuhumar tasa, After few seconds ta marairaice tace "Ina parlor ne ina karatu, wayar kuma na daki" Yace "Kin fara zaman parlor kenan, when did that start? House mate din taki ta dena shigowa da saurayinta ne gidan?" sai da gaban Khaleesat ya fadi, A hankali tace "Bata nan, taje LA jiya" Yace "Sau uku kenan ina kiranki a satin nan baki dagawa sai sanda kika ga dama ki biyoni, that nonsense shouldn't repeat it self again, a kanki aka fara karatu ko ni zaki gaya ma karatun Exams?" Shiru Khaleesat tayi lkci daya hawaye ya cika idonta, a ɗan fusace yace "Baki ji na ne?" Cikin sanyin murya tace "Naji, kayi hakuri hakan bazai sake faruwa ba in sha Allah" Yace "Good, you can go to bed" Tana goge hawayen da yaki tsaya mata tace "Nagode, sai da safe" Shi ya katse call din ta ajiye wayarta gefen gadon ta dora kanta a pillow hawaye na zuba idonta, after a while ta mike ta tafi bandaki ta wanke fuskarta ta dawo ta kashe wutan dakin tayi addu'an bacci ta kwanta.... Washegari Friday da wuri Khaleesat suka gama lectures dinsu, suna zaune a exact spot din jiya ita da Safiyyah dake waya, sosai Khaleesat tayi nisa tunanin da take har bata san sanda Safiyyah ta gama waya ba, dafa kafadarta da Safiyyah tayi ne ya dawo da ita duniyar tunanin da ta shiga, Safiyyah tace "What is wrong Khaleesat, ina ta magana baki ma san ina yi ba, tunanin me kike haka?" Khaleesat ta ɗan kirkiri murmushi tace "Kawai ina kewar Ummanmu ne da siblings dina" Safiyyah ta girgiza kai tace "Ban yarda ba, there is definitely something that is bothering you" Khaleesat ta kauda zancen tace "Ke da George ne ke waya ko?" Safiyyah tayi kasa da murya tace "Pls gobe weekend ki shirya mu tafi Virginia Leesat, George is throwing a party for his birthday tomorrow, kuma za mu je Beach, don Allah kar ki ce a'a, we need to take a break and rest our brain, ba ko da yaushe karatu ba kamar mu muka kawo boko duniya...." Khaleesat dake ta kallonta tace "Ke yanzu sai ki kama hanyar Virginia Safiyyah??" Safiyyah ta hade girar sama da ta kasa tace "To menene, it's just a 4 hours ride from Maryland, kamar fa ace daga kaduna zuwa kano shi ma in mota bai yi gudu ba, pls for once ki zama social mana Khaleesat, ke baki gajiya da zama guri daya ne a kasar nan? Baki gajiya da karatu? ranan Monday fa za mu dawo in sha Allah, kuma babu wanda zai san mun je wani Virginia, dama Ya Mustapha na riga na gama plan din abinda zan ce masa, ke da ba ma ki da wanda zai sa maki ido kike mis using opportunities haka, da mun koma Nigeria fa shikenan, tafiyar nan maza ne hade da mata" Khaleesat ta girgiza kai tace "Lallai... Ni dai ina baki shawara kar ki je Safiyyah" Safiyyah tace "Bana ma son shawaran, abinda mu goma za mu je" Khaleesat tace "Toh Allah ya tsare hanya ya dawo da ku lafiya" Safiyyah ta mata wani kallo tace "Baza ki je ba kenan dai?" Ba tare da Khaleesat ta kalleta ba tace "Kema kin san bazan je ba ai" Safiyyah tace "Ke kika sani, mu dai za mu je wallahi" Safiyyah na kai wa nan ta mike tace "Sai ran Monday" Khaleesat na kallonta a hankali tace "Wai tafiya za ki yi? Da sauran time fa Safiyyah" Safiyyah tace "Aa toh me za mu zauna yi a schl bamu da aji? Yau kuma kece ke cewa da sauran time duk son ki da komawa gida da wuri? Ikon Allah" Khaleesat ta kasa cewa komai, ita har ranta take jin ta tsani gidan nata yanzu, she no longer see the home as her comfort zone, and she don't think she can cope staying together with an Hausa Guy under same roof, da ma bature ne ko kadan bazata damu ba kamar yanda ta damu yanxu, har ta taho school bata hadu da sabon Housemate din nata ba da safe, Safiyyah ta ɗan buda ido ta koma ta zauna tace "Ohh now i remember, wai saboda new House mate dinki? To wai ke meye damuwarki ne da shi? Yayi harkan gabansa kiyi naki ne fa a gidan, ko magana in baki son ya maki you just call the cops a maki iyaka da shi, just dial 911 and that's all, balle nasan kilan da kyar aka kukuta masa ya taho makaranta kasar nan to kuwa ina zai tsaya bata lkcnsa akan abinda ba shi ya kawo sa ba, don dai in wani Shege ne shi bazai zauna a shared apartment ba a USA, kuma 'ya yan masu kudin nan sun fi iskanci su kuwa talakawa abinda ya kawo su kawai suke yi, kiyi ta kanki kawai shi ma yayi ta kansa, kar kiyi mamaki ta scholarship ya zo kasar ma" Khaleesat dai kallon Safiyyah kawai take, Safiyyah ta kyabe baki tace "Tashi mu je gidan, ni banda Ya Musty bazai yarda ba da ba sai in tattaro in dawo gidan naki ba mu zauna kawai" Khaleesat ta marairaice tace "Plss ki sake masa magana ko zai bar ki mana, ai sanda ya hanaki kinga bamu dade da fara makarantar ba" Safiyyah tace "Kar ma ki bata bakinki mutumin nan bazai yarda ba, tashi mu je in raka ki, in House mate din ma yaga kina wani yin abu a tsorace renaki zai yi wallahi, yi zaki yi kamar kema er gari ce kawai sai ki ga ya fara shakkar ki a gidan" Khaleesat ta mike tace "Kar fa muje kiyi ta Hausa, just pretend we are not Hausa" Safiyyah tayi dariya tace "Kece dai is not Hausa, ni kam Bahaushiya ce cikakkiya kuwa" A haka dai suka bar makarantar suka nufi gidan da Khaleesat take.... Khaleesat ta bude handbag dinta ta ciro makulli ta bude kofar shiga gidan suka shiga parlor Safiyyah na biye da ita a baya, Safiyyah na gyada kai jin wani kamshi da parlon yake tace "Da alama bai dade da fita ba ma" Khaleesat dai bin parlon take da kallo ganin duk reading materials dinsa ne saman kujera ya tula a kai, Safiyyah tace "Kinga don Allah ki saki ranki ki ci gaba da harkokin ki Khaleesat, a Maryland fa kike a Amurka ba Kano Nigeria ba, ki dinga abu irin na wayayyu mana pls" Wani kallo Khaleesat tayi mata ta ajiye handbag dinta tace "Ance maki in bature ne ko wani yare ni zan damu, kawai my issue here is about him being a Hausa Guy, har fa tambayata yayi jiya ko ni bahaushiya ce" Safiyyah tace "Ohh kun ma yi magana kenan...." Khaleesat tace "Ni ban kulasa ba kuma ban nuna masa ni Bahaushiya bace, i will just pretend i am from Morocco" Safiyyah ta dinga dariya har da saukowa daga kan kujera tace "Gashi kuwa an ma fi saninsu da fararen mata kyawawa na ajin karshe, tsaf zai yarda daga can kike, kinga da larabci ya zauna daram a bakinki sai kiyi ta zabga larabci nasan ba lallai yana ji ba, daga haka zai kama kansa yayi zaton ke balarabiyar gaske ce... sai ma Abdul yaji kuna gida daya da Bahaushe kilan Baltimore yayi maku kadan wallahi, shi sa nace ki gaya masa kika ki" Khaleesat ta ajiye jakarta bata sake kallon Safiyyah dake ta dariya ba tayi wucewarta kitchen tana tunanin me zata dafa masu dama ko breakfast bata yi ba ta fita daga gidan, tsaye tayi kitchen din tana kallon cartons din bottle water kusan bakwai wanda duk yafi tsada a state din, sai kuma ta juya ta kalli beverages masu yawa da ya ajiye kan cabinet, ta karasa cikin kitchen din ta bude babban fridge zata dau kwai da za ta dafa masu Noodles, kallon fridge din ta dinga yi ganinsa fully stocked with everything, tun daga tsadaddun drinks kala kala, fresh milk, varieties of fruits, with many eggs, muryar Safiyyah taji a bayanta tace "Kai kai kai, shi ya zuba abubuwan nan a fridge Leesah?" Khaleesat ta juya ta kalleta looking speechless, can dai ta dau eggs din da zata dauka ta kulle fridge din ta tafi inda foodstuffs dinta suke shi ma taga kayan abinci ya siyo, Safiyyah ta rike haɓa tace "Duk a kudin scholarship din yake facakan nan? Ko dai bashi da hankali ne bai san bin komai ake a sannu a kasar nan ba" Khaleesat dai ta dau Noodles dinta ta bar wajen tana kallon Safiyyah tace "Ga Indomie ki dafa mana, ina son inyi magana da Ummanmu kafin Aunty Sha'awa ta fita kasuwa" Safiyyah tace "Ohk to" Khaleesat ta bar kitchen din ta dau jakarta ta wuce dakinta, WhatsApp dinta ta bude ta shiga contact din makociyarsu Sha'awa tayi mata voice note kamar yanda ta saba a duk sanda take son magana da Ummanta. Sai kusan karfe hudu na yamma Khaleesat ta raka Safiyyah zuwa gun Lyft din da tayi ordering don tun daxu Cousin brother dinta ke kiranta ganin bata dawo gida ba, Safiyyah ta shige motar ta kulle tana daga ma Khaleesat hannu, sai da Lyft din ya bar wajen sannan Khaleesat ta juya tana tafiya a hankali ta nufi apartment dinta, dai dai apartment din taga mota yayi parking a space din da aka tanadar don parking for that apartment, bata karasa ba ta jingina jikin fence din dake inda take tsaye tana kallon motar ta little space din dake between the wooden fence din, taga ya fito daga motar ta bi sa da ido har ya shiga apartment din yana danna wayarsa, ta fi minti biyar tsaye a inda take, daga karshe tana tafiya a hankali ta karasa apartment din ta murda kofar parlon taji ya kulle, hade rai tayi tana kallon kofar, daga karshe da ta gaji da tsayuwa kawai tayi knocking, sau uku tana knocking sannan ya bude kofar, yana ganinta yace "Hi" ita dai ko kallonsa bata yi ba fuskarta babu yabo babu fallasa ta bi gefensa ta shiga parlon, direct gun wayarta dake kan kujera ta nufa ta dauka tare da reading materials dinta dake saman kujeran, har zata dakinta sai kuma ta dawo ta tafi kitchen ta dau goran ruwa daya sannan ta nufi dakin, sai da ta bude kofar tayi masa kallon gefen ido taga he is just busy sorting out some textbooks that were inside a carton he came with, har ta shiga dakin nata bai juya ba balle ya kalli direction dinta.... ✍🏻 07087865788 [4/29, 5:07 PM] khaleesat Haiydar ✍️: https://chat.whatsapp.com/KVY8hjs3iNq5ntSN4Z5g6V ✨✨ HALYSAAH ✨✨ ✍🏻 By _Khaleesat Haiydar_ 2..... Washegari har karfe sha daya Khaleesat na dakinta bata fito ba duk da yunwan da take ji, tayi tagumi don gaba daya ta ma rasa what is her problem particularly, ta dau wayarta jin shigowar WhatsApp message, tun daxu suke chatting ta VN da Ummanta ta wayar makociyarsu Sha'awa, da taji shiru ta ma zata an maida ma Aunty Sha'awa wayar nata ne, ta bude VN din tana sauraren voice din mahaifiyarta, Addu'a Ummanta ke mata tana mata fatan nasara a karatun ta, sannan kamar ko da yaushe ta sake jaddada mata ta kula da mutuncinta ta kula da kanta, daga karshe ta ƙare da cewa za a kai ma sha'awa wayarta don zata fita kasuwa, Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya ta ajiye wayar a hankali sannan ta mike ta dau hijab din sallanta ta saka ta nufi kofa ta bude a hankali ta fita daga dakin don ta gaji da horan kanta da yunwa ita da ke breakfast da wuri, kitchen ta tafi almost bumping into her new House mate shi kuma yana kokarin fitowa daga cikin kitchen din, komawa baya yayi at the same time yace "Good morning" Bata yarda su hada ido ba ta matsa gefe allowing him to pass, ya fito daga kitchen din yayi wucewarsa without looking at her, sai a sannan ta shiga ciki, tsaye tayi tana kallon littered cups da plates din da yayi amfani da su ya bari a sink din wanke wanke without washing them, ga bowl din fruit salad da shi ma ya ajiye bai sha ba, bin kofar kitchen din tayi da kallon mamaki, to wa ya bari yayi masa wanke wanke? Ta fi minti daya tsaye a inda take da tunani iri iri a ranta, wata zuciyar ta ce mata kawai tayi abinda ya kawota ta fita daga kitchen din ta bar unclean utensils din a yanda ya bar su, amma dai kawai ta jawo liquid wash da sponge fuskarta a daure ta fara wanke kayan wanke wanken kawai, bayan ta gama ta goggoge kitchen din ta hada shayi ta debi cookies a plate sannan ta fita daga kitchen din ta wuce dakinta. Wajen karfe uku Khaleesat ta fito daga dakinta, tun da ta gama breakfast take karatu sai sallah kawai ta tashi tayi da azahar, jin ko ina shiru and to be sure baya gidan ta nufi kofar parlon zata bude taji an kulle da makulli, dakinta ta koma ta dauko makullinta ta bude kofar tana duba garage taga babu motarsa a ciki, komawa cikin gidan tayi ta kulle kofar sannan ta tafi kitchen, tun shekaranjiya take son cin shinkafa da miya amma kasancewar she is not comfortable tun da ya dawo gidan yasa ta hakura da girkawa, yanzu da taga baya nan kawai tayi deciding tayi shinkafa da miyar, bayan ta daura shinkafar, ta fara hada miyar dama tana da sauran chicken thighs a fridge, fitowa parlor tayi da sweeper zata yi shara, ta ajiye sweeper din hannunta to tidy the couch first, dukawa tayi tana kallon takardun Housemate din nata da ta gani, sai kuma ta kyabe baki ta bar su nan yanda ya bari a kan kujeran, share rug din parlon ta fara yi bayan ta dauke makullin da ta gani a kasa, ta dinga juya makullin ganin kamar na Bedroom ne, kafin minti arba'in ta gama girkin da take ta tsaftace ko ina na gidan, ta debi abincinta ta tafi daki da shi, sai da ta fara yin sallahn Asr sannan ta dau wayarta tana dubawa, sosai gabanta ya fadi ganin miss call din Abdul, nan da nan taji abincin ya fita ranta gaba daya, ta zauna gefen gado a hankali tana kallon wayar, ta fi minti goma zaune a haka, she was soo worried, to yanzu me zata ce masa ma in ta kirasa, daga karshe ta daure tayi dialing number nasa, har ya katse bai daga ba, ta sake kira nan ma bai daga ba, duk da yunwan da take ji haka nan taji abincin ya fita ranta, ta tsani duk wani abu da zai sa Abdul ya daga mata hankali, haka tayi forcing din kanta ta ci abincin sannan ta kwanta side din gado, bata san sanda bacci ya dauketa ba a haka.... knocking kofar dakinta da ake yi ne ya farkar da ita daga baccin da take, ta mike zaune da kyar tana murza idonta tana kallon kofar at the same time tana mamakin me zai sa ya dinga bubbuga mata kofa haka, to ko dai bashi da kai ne?? ta jawo wayarta tana duba agogo taga karfe shidda da mintuna, bata yi tunanin ta dade tana bacci haka ba, sake knocking da aka yi yasa ta mike tsaye ta saka hijab fuska daure tace "What is that??" Ta ji yace "Ohk i think i misplaced my keys, just want to know if you saw it while tidying up the parlor?" Sai a sannan ta tuna makullin da ta gani a parlor daxu da take shara, tana tafiya a hankali ta karasa kofar dakinta ta murda key din jiki sannan ta bude door din, tuni har ya bar corridor din ya koma parlor ya tsaya yana jiranta, da alama dawowarsa gidan kenan a lkcn, ta karaso cikin parlon ba tare da ta kallesa ba, shi dai duba message din da ya shigo wayarsa yake with all his attention, ta tafi inda ta ajiye makullin sannan ta dawo ta ajiye masa kan takardunsa dake kan kujera tace "Here" Yace "Ohk" dakinta ta koma ta shiga tana mamakin wai Ohk, ba ma thank you ba kamar irin ya ajiyeta din nan, kwafa tayi ta saka ma kofarta key, bayan Khaleesat ta idar da isha ta sake kiran Abdul bai daga ba, sau hudu kenan tana kiransa tun karfe bakwai bai yi responding ba, yanzu dai tafi tunanin yana bacci don dare ne sosai a can kasar, even at that tasan she is in soup, mikewa tayi ta dau plate din da ta ci abinci daxu ta nufi kofa ta fita daga dakin, a parlor ta ga sabon Housemate dinta yana tattara takardunsa at the same time yana answering phone call taji yana cewa "I am on my way now" Daga haka ya katse wayar ya mayar aljihunsa ya dau takardunsa da makullin mota ya mike tsaye, ido hudu suka yi for the first time tunda ya dawo gidan, ita dai ta dauke kai kamar bata ma gansa ba ta karaso cikin parlon zata tafi kitchen taji yace "I ate a little out of the food you cook, and...." Yayi pointing takeaway din da ke kan kujera yace "I am taking some to my frnd too" duk wannan abun bai kalli inda take tsaye ba yake magana, sai ita ce ma da ta dinga kallonsa da mamaki babu ko kiftawa, ya dau takeaway din ya nufi kofa cikin hanzari, yace "Good night" Ta bi sa da kallo har ya fita ya kulle gidan da makulli ta waje, mamaki yasa ta kasa karasawa kitchen din, after some seconds ta tafi kitchen din, da plate din da ya ci abincin, da cup din da ya sha coffee, da bowl din da ya sha fruits salad duk suna ajiye a sink babu wanki, ta jingina da kofar kitchen din ta rungume hannu tana kallon sink din kamar zata fashe don bakin ciki, can ta karasa ciki tana duba shinkafar da ya bar mata, taga da kyar in zai yi spoon uku, gashi duk yayi littering din wajen da shinkafar wajen diba kuma ya bar shi haka, haka nan ta juye er shinkafar da ya rage a karamin bowl, ta wanke duk utensils din, ta gyara ko ina ta goge sannan ta hada shayi ta koma daki da bowl din sauran abincin, zaunawa tayi gefen gado ta dau wayarta tayi dialing number Safiyyah, sai da ya kusa katsewa Safiyyah tayi picking daga daya bangaren tace "Allah da gaske baki da kirki Khaleesah, to ko baki kira ba dai na isa Virginia cikin koshin lafiya" Khaleesat ta ɗan yi murmushi tace "Dama nasan kin isa lafiya ai, hope you are doing good?" Safiyyah ta tabe baki tace "Oho dai, wannan ba matsalar ki bane" Khaleesat tace "Amma don Allah ina kika ce ma Ya Musty za ki?" Safiyyah tace "Ahaf tsaya wasa, sai kace baki san ni ba, munafukar matarsa da yake ba son zamana a gidan take ba ita ce ma ta kara convincing dinsa, duk zatonsu ina gidanki muna group reading with some of our Coursemate" Khaleesat tayi murmushi tace "To ai shikenan, yanxu yaushe zaki dawo?" Safiyyah tace "Gobe ne birthday din ai, in sha Allah i will be back on Monday" Khaleesat tace "Toh Allah ya kai mu, kinsan mene?" Safiyyah tace "Aa" Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya tace "Wallahi in gaya maki Abdallah ne ya kirani nayi missing call dinsa as i am speaking to you now tun daxu nake kiransa yaki picking, nasan fushi yayi sosai, ni kuma...." Safiyyah ta dakatar da ita tace "Ke kuma me? Shikenan rayuwa babu uxuri dama?" Khaleesat tayi kasa da murya tace "He warned me times without number kar in sake missing call dinsa Safiyyah, kuma wallahi ina kitchen sanda ya kira wayar kuma na daki ba da gangan nayi missing kiransa ba" Sounding so pissed off Safiyyah tace "Wai don Allah me yasa kika dauki tsoron duniya kika dora ma mutumin nan ne Khaleesat? For how long will things continue this way? Yaushe za ki fara nuna masa ke fa mace ce? yanzu haka za ku yi auren ya maida ki slave a gidansa tunda kin nuna masa kina mugun tsoronsa tun a waje? wannan wani irin gantalallen relationship ne? Gaskiya ina jinjina maki Khaleesat, don wallahi in nice bazan iya ba Allah ma ya gani sai dai duk abinda zai faru ya faru" Cikin sanyin murya Khaleesat tace "I have no choice nor option Safiyyah...." Tana fadin haka hawaye ya fara gangarowa idonta, a ɗan fusace Safiyyah tace "To wai ke kadai ce mace a gidanku ne da ya gani? Naga ga Labibah da Lamisah, ina ce sati biyu kika ba Labibah a shekaru, ita kuma Lamisah wata daya, ga kuma yayyinki Samira da salamatu, to wai halan su ba mata bane sai ke??" Khaleesat dai bata ce komai ba tana goge hawayen dake zuba idonta, Safiyyah ta sauke ajiyar zuciya tace "Ai shikenan, but u really need to speak up for ur self Khaleesat, ni dai nasan their worst mistake is sending you to school abroad, aje dai zuwa, ke kuma in har baki waye kin kwatar ma kanki 'yanci daga karshe ba to sorry to say this, wallahi u will live a miserable life in the nearest future Khaleesat, this is just the fact i am saying, na gaji da lamarin so called Abdul din ki" Cike da karfin hali Khaleesat tace "Ki daina cewa haka pls Safiyyah, ke me tayani addu'a ce kan Allah ya kawo min komai da sauki amma ba ki dinga fadin wa ennan maganganun ba...." Safiyyah ta taɓe baki bata dai ce komai ba, a hankali Khaleesat tace "Pls ko zuwa gobe da safe ki masa magana ta Whatsapp ki tayani basa hakuri cause nasan bazai daga kirana ba no matter what..." Safiyyah tace "To naji, Allah ya kai mu goben" Khaleesat tace "Ameen" Sallama suka yi, Khaleesat ta ajiye wayarta. Karfe goma saura na safe Khaleesat ta fito daga dakinta rike da wayarta don kar ma Abdul ya kira by mistake tayi missing call dinsa, tun jiya take makale da wayar duk don kar ya kira bata sani ba, kuma sau uku tana kiransa bayan da tayi sallan asuba bai daga ba still, yanzun ma da ta tashi sae da ta kirasa sau daya nan ma no answer, zaune taga new Housemate dinta a ɗan reading nook da aka tanadar a living Room din studying with a huge textbook dake gabansa, she had no idea ma ya shigo gidan, don bayan da tayi sallan asuba ta fito ta hada shayi ta sha da cookies a nan parlon sannan tayi karatu har zuwa bakwai na safe, daga nan ta shiga daki ta kwanta sai kuma yanzu da ta tashi feeling hungry, sau daya ya kalleta yana ci gaba da duba Textbook din gabansa yace "Good morning" Ta karaso cikin living room din a takaice tace "Ok" Ajiye wayarta tayi kan 1 sitter ta nufi kitchen, Ya daga kai yana kallon direction din da ta bi da harshen turanci yace "In baki yi breakfast ba, ga wani nan ki dauka....." Tsayawa tayi sai kuma ta juya ta kalli Centre table da yake nuna mata, ledan abinci ne kan table din duk da bata san wani kalan abinci bane a ledan, ta kallesa taga ya ci gaba da karatun da yake, girgiza kai tayi with no interest tace "No, tnx" Daga haka tayi wucewarta kitchen, ta fi minti uku tsaye kitchen din tana tunanin me zata yi, seeing her House mate sitted in the living room yasa ta zama uncomfortable to cook anything, hakan yasa kawai ta dauko kwalin cereals da bowl zata hada cornflakes, wayarta ta ji yana ring a parlor don tun jiya ta cire wayar a silent, bata san sanda ta saki both d bowl and the Cereal din hannunta ba ta fito daga kitchen din within few seconds, House mate dinta ya bi ta da kallo har ta nufi gun wayarta ta dauka da sauri, sai da gabanta ya fadi ganin Abdul ne ke kiranta, babu bata lokaci ta daga call din, zuciyarta na bugawa tayi masa sallama, jin shiru tace "Hello" kallon wayar tayi ta sake maidawa a kunnenta har sannan bata daina cewa Hello ba, House mate dinta dai ya ajiye Textbook dinsa gefe ganin yanda ta rude ya maida duk concentration dinsa akan ta, Khaleesat ta sake kallon Screen din wayar jin shiru Abdul ya ki ce mata komai kuma tana jin maganar mutane a background, marairaicewa tayi ta duka nan kasan living room din ta saka wayar a handsfree tace "I know u can hear me pls, don Allah kayi hakuri, i am making u this promise hakan bazai sake faruwa ba wallahi, don girman Allah kayi hakuri" Sai a sannan yayi magana da husky voice yace "Hold on to ur promise malama, sau biyar kenan kina missing call dina within a short period, are you out of ur senses or is anything wrong with ur brain?" Da sauri ta girgiza kai kamar zata yi kuka tace "Wallahi ina kitchen ina girki san da ka kira jiya, kuma...." Cutting dinta yayi yace "ke, bana bukatar jin komai daga gare ki, none of ur lies and excuses will convince me, naga kamar u are beginning to take me for granted this days.... Kinsan Allah kika sake missing call dina zaki sha mamakina wallahi cause it will take me nothing to be in America...." Hawaye ya cika idonta cikin sanyin murya tace "Amma me yasa baka min uxuri?" Yace "Baza ayi uxurin ba, ni za ki gaya ma uxuri? A kanki aka fara karatu?" Shiru tayi bata ce komai ba, yace "Wato ke kin fi karfin ki bude baki ki bada hakuri ko" Kasa cewa komai Khaleesat tayi don tun da ta daga kiransa ta fara basa hakuri bata kuma san wani hakurin yake nufi ba, A takaice yace "Anyway, i called to warn you to stop disturbing me with unnecessary calls, na biyu kuma ki ja ma kawarki kunne she should never come into my DM and tell me nonsense again don zan dau mummunan mataki a kanta, ke kuma duk sanda yayi suiting dina i will call you, don't try calling my line again" Yana kai wa nan ya katse wayar, Khaleesat ta dinga kallon screen din wayar hawayen dake makale idonta ya gangaro, House mate dinta ya ɗan yi murmushi wanda iyakarsa lips after paying attention to their conversation, mikewa Khaleesat tayi tana share hawayen dake sauka idonta, sai a sannan ta lura da shi a parlon, dauke kai tayi da sauri bayan sun hada ido, gaba daya ta ma mance yana parlon, taji yace "Is that ur Father?" Wani kallo ta jefa masa tayi wucewarta dakinta wasu sabbin hawayen na zuba idonta, ruf da ciki tayi kan gadonta tana kuka har da shessheka, ta kusa minti arba'in kwance a yanda take, zuwa sannan ta dena kukan da take kawai ta lumshe ido, knocking din kofar dakinta da taji anyi at the same time aka bude ne yasa ta mike zaune da sauri don bata san bata kulle kofar ba, hada ido suka yi da new Housemate dinta, yayi dropping ledan hannunsa ya jingina jikin kofar dakin ya rungume hannu yana kallonta da kyau, calmly yace "Like seriously, Namiji kika kwanta kike yi ma kuka?" Ta wani hade rai ta kauda kanta zuwa wani direction din daban, how did he even know she understands Hausa?? yana juya counter din hannunsa as if counting his words yace "It's... funny" Ta juya ta kallesa har sannan fuskarta a daure tace "Excuse you, why will u barge into someone else's bedroom just like that?" Ya daga kafadarsa yace "Zan yi shisshigi in baki shawara ni dai, run for ur dear life cause u are dating a monster as a boyfriend" Yana kai wa nan ya juya ya fita daga dakin closing the door behind him, Khaleesat ta dafe kanta da yayi mata nauyi, daga karshe ta mike ta kulle dakinta da makulli sannan ta shiga bandaki, karfe sha biyu da yan mintuna ta gama shiryawa don wanka tayi, kallon ledan da ya ajiye mata tayi ta dauke kai sannan ta nufi kofa ta bude ta fita, satan kallon kofar bedroom dinsa tayi ta karasa living room, tana tafiya a hankali ta tafi kofar parlon ta murda taji a kulle an sa makulli, leka windon parlorn tayi taga babu motarsa a garage alamar ya fita, tana tafiya a hankali ta shiga kitchen, ta jingina da kofa tana kallon Cereal da bowl din da ta dauko daxu an ajiyesu kan cabinet din kitchen din, juyawa tayi ta fita daga kitchen din ta koma dakinta, ledan da ya ajiye mata ta dauka ta zauna kan kujeran dake dakin tana duba abinda ke cikin ledan, Breakfast Sandwiches ne sai fresh fruit smoothie a ledan..... ✍🏻 07087865788 [4/30, 5:36 PM] khaleesat Haiydar ✍️: https://chat.whatsapp.com/KBwGIidDZY683SzzudJ0zc ✨✨ HALYSAAH✨✨ ✍🏻 By _Khaleesat Haiydar_ 3..... Bayan magrib Khaleesat ta fito living room saboda yunwan da take ji, har sannan bata ji alamar House mate din nata ya dawo gidan ba, gaba daya haka ta wuni ranan babu walwala, all of a sudden yau ta ji a zuciyarta ta fara gajiya da attitude din Abdul da abubuwan da yake mata, da ta tuna Housemate dinta overheard all her conversation with Abdul da kuma maganar da ya gaya mata sai taji wani bakin ciki da takaici ya tokareta at the same time tana wishing that never happened, zaunawa tayi kan kujera ta jinginar da kanta jikin kujeran ta afka duniyar tunanin rayuwarta, after a while ta sauke ajiyar zuciya ta mike tana tafiya a hankali ta shiga kitchen tana tunanin abinda zata dafa ta ci, absently ta fara wanke few utensils din da yayi amfani da shi ya bari a sink sannan ta kunna gas, stir fry pasta ta girka, bayan ta gama ta debi kadan da zata ci ta fita daga kitchen din, dai dai corridor din dakunan ta kusa cin karo da House mate din nata, a firgice tace "Innalillahi...." Sai kuma tayi shiru ta hade rai, ya koma gefe yana kallonta, har ranta taji tsoro don bata san yana gidan ba amma tayi pretending ta hanyar daure fuska, ya daga kafada ya bar wajen ta bi sa da kallon gefen ido.... reading nook dake cikin living room din ta ga ya nufa yana kwashe takardunsa dake kan table, ta dauke kanta ta shiga cikin dakinta ta kulle da makulli, karfe takwas da few minutes ta gama duk abinda zata yi ta dauro alwala sannan kwanta don gobe Monday tana da aji da safe, tana lumshe ido bacci ya dauketa. Cikin bacci Khaleesat taji ana knocking kofar dakinta, ta mike zaune da kyar tana murza ido ta jawo wayarta tana kallon agogo taga karfe goma saura minti biyar, kallon kofar tayi da mamakin dalilin da yasa yake mata knocking by this time, can dai ta daure fuska tace "Waye wannan?" Taji yace "I could use ur help if u don't mind" Bluntly tace "I beg ur Pardon?" A takaice yace "Nayi misplacing makullina again" Da farko rasa ma me zata ce masa tayi don mamaki, she was mute for almost a minutes, taji yace "Hello" Sosai ta hade rai tace "I don't understand kayi misplacing makullin ka?" Yace "Look, ni fita zan yi yanzu idan na fita sai ki kulle gidan" Bata san sanda tace "Idan fita zaka yi ka fita mana, me yasa zaka tambayeni makulli? ko makullinmu a hade yake?" Shiru yayi at first, sai kuma yace "Ta yaya zan fita nace maki ban ga makullin kofa ba" Tace "But our keys are separate isn't it?" Yace "Sai yanzu da kika fada na sani ai, fito ki bude min kofa zan fita" Wani bakin ciki taji ya tokareta, yace "I am waiting at the parlor" Bata tanka sa ba, can tayi tsaki ta sauka daga kan gadonta ta dau hijab ta sa, ta bude handbag dinta ta dau makullinta ta nufi kofar dakin, fuskarta a daure ta bude ta fito ta karasa living room ta gansa tsaye bakin kofar parlon yana jiranta, ko kallonsa bata yi ba kamar yanda shi ma din wayarsa yake dannawa bai kalli inda take ba, ta karasa ta bude kofar parlon da makullin hannunta tace "You weren't given a needle as key da zai dinga ɓata kullum, and i shouldn't be responsible always for someone else carelessness" Shi dai bai ce mata komai ba ya fita without looking at her yace "Na zata ai needle aka bani Housemate" Da ido ta bi sa har ya isa inda motarsa take, wato godiyar da zai mata kenan? Ta gyada kai ta kulle kofar parlon a ranta kuma tayi vow bazata sake masa amfani da makullinta ba sai dai kar ya fita, banda ma rainin hankali me yasa baya misplacing makullin motarsa sai na gida, next time sai dai ya fasa zuwa inda za shi don bazata sake sharing key dinta da shi ba, fuska daure ta koma cikin parlor, sai kuma ta tsaya tana kallon plate din da ya ci abinci ya bari a parlon da container din soft drink ga goran ruwa, tsabar mamaki bata san sanda ta nemi waje ta zauna ba, is this guy okay? After fetching her food without asking for permission he still have the mind to leave the plate for her at the parlor, anyway... she believe he didn't leave it for her, he left it for himself instead, don ko sati daya zai yi bai dawo gidan ba zai dawo ya tarar da plate din at that same spot don bazata daukesa ba, tashi tayi ta tafi daki fuskarta a daure. Da safe Khaleesat ta gama shirin fita makaranta, har a lkcn bata dauke plate din da ya bari a parlon ba, amma fa zuciyarta kawai ta kai nesa don ta tsani ganin abu ba inda ya kamata ba, zata kai cup din da ta sha shayi kitchen taji ta taka makulli a kan ash carpet din parlon, dukawa tayi ta dau makullin tana kallo taga nasa ne, he is just careless, tabe baki tayi ta mike ta ajiye makullin nan kan kujera, ta kalli plate din jiya da ya bari, tsaki tayi ta dauke tare da gwangwanin soft drink din da na ruwa, ta hada da cup din hannunta ta tafi kitchen, bayan ɗan lokaci ta dawo parlor ta dauki handbag dinta tana duba wayarta, ganin Lyft din da tayi order ya kusa isowa ta nufi kofa ta fita. Wajen karfe sha biyu Khaleesat na zaune tare da Safiyyah warce shigowarta makarantar kenan, Khaleesat na kallonta tace "Kun sha birthday" Safiyyah tace "Oho dai tunda ke baki je ba, yau me ku ka yi a aji?" Khaleesat tace "Nothing much" Safiyyah ta bude handbag dinta ta ciro cake tana mika ma Khaleesat tace "Gashi ba don halin ki ba" Khaleesat tayi murmushi ta amsa tace "Nagode" Safiyyah tace "Kun yi waya da Abdallan ne?" Khaleesat ta sauke idonta a hankali tace "Sophie me kika ce masa ta chat?" Safiyyah ta dau wayarta tayi unlocking cikin few seconds ta shiga DM din Abdul sannan ta mika ma Khaleesat wayar, Khaleesat ta amsa tana duba chat din, it was nothing worth taking personal Safiyyah ta gaya masa a chat din, Khaleesat dai tayi shiru bata ce komai ba tana kallon wayar hannunta, Safiyyah tace "Me yace maki halan?" Khaleesat ta mika mata wayarta tace "Nothing, kawai yace min kin masa magana" Safiyyah ta tabe baki tace "Kin dai ga yanda yake amsa min chat din ma kamar wani ɗan sarki, wallahi Abdallah bai yi deserving dinki ba, u are too good to be Abdul's or to end up with him, Allah ya maki sauyi cikin ruwan sanyi ya kawo maki mafita" a hankali Khaleesat tace "Ki tashi mu je aji" Safiyyah tace "Oh baza ki ce Ameen ba??" Murmushi Khaleesat tayi tace "Wani mafita kenan Safiyyah? Cewa zaki yi Allah ya canza min halayyarsa kawai...." Safiyyah ta tabe baki ta mike tace "Mu je" Khaleesat ta mike suka bar wajen a tare... Khaleesat na sauka Uber din da ya dawo da ita gida ta nufi apartment dinta, dai dai sanda Co-tenant dinta ya fito daga cikin motarsa dake inda aka tanadar domin parking, sau daya ta kallesa ta dauke kai tana ci gaba da tafiyarta toward their apartment, ya bi bayanta yace "I've waited all day long, i forgot some paperwork a cikin gidan gashi zanyi Submitting tun daxu" Ba tare da ta juyo ba tana ci gaba da tafiya tace "Serves you right" Kallonta yake yana biye da ita, ta ciro makulli a jakarta ta bude kofar ta zare makullinta sannan tayi shigewarta ciki ta nufi dakinta da makullin... Bayan Khaleesat ta idar da sallah ta sauya kaya ta fito parlor don daura girki, bata gansa a parlon ba, kuma bata ji alamar ya shiga dakinsa ba, ta nufi tagar living room din tana leka parking space, ganin babu motarsa ta karasa gun kofa ta murda taji a kulle, kallon inda ta ajiye makullinsa daxu da safe tayi taga ya gani har ya dauke, wucewarta tayi zuwa kitchen. Wajen karfe tara na dare Khaleesat ta gama karatun da take ta jawo wayarta ta bude WhatsApp dinta don ganin ko Neighbor dinsu Aunty Sha'awa tayi replying sakon da ta tura mata amma sai taga bata yi reply ba har sannan kuma ta bude message din, ajiye wayar tayi ta mike ta dauke darduman da take zaune kai, ta dau hijab ta saka sannan ta fito parlor zata debi abinci, Zaune taga House mate dinta a parlon yana operating laptop dinsa, without looking at him ta tafi kitchen, after some minutes ta fito, ya daga kai yana dubanta yace "Can i have some of ur food if you don't mind?" Mamaki ma ya bata, har da baza ta tanka sa ba sai kuma ta tsaya tace "Duk na baya da kake diba gaya min kake halan?" Ya ɗan buda ido yana gyada kai yace "Haka ne kuma fa, i just decided to ask politely today" Bata sake bi ta kansa ba tayi tafiyar ta daki, in har sai tace ya diba to ashe bazai ci ba. Washegari da safe Khaleesat na kitchen tana ma kanta snacks da zata kai school don har yamma suke da Lecture gashi suna da er jarabawan da za su yi ranan da safen, Housemate dinta ne ya shigo parlon, tun jiya da daddare da ya fita sai a sannan ya dawo gidan, har zai tafi dakinsa sai kuma ya tsaya yana kallon Handbag dinta da makulli dake ajiye gefen jakar, karasawa yayi ya dau makullin sannan ya juya ya fice daga parlon gaba daya closing the door gently ya kulle da key, Khaleesat tafi minti sha biyar tana duba makullinta bayan ta fito daga kitchen, tun daga dakinta har parlor zuwa kitchen babu inda bata duba ba amma bata ga alamar makullin ba, she can't even tell ko ta fito da shi parlor, she was so confuse gashi tayi latti, daki ta koma sai da ta birkice ko ina amma babu alamar makullin, how comes will her keys disappear just like that, tunda ta fara karatu a kasar bata taɓa misplacing makulli ba banda wani lkci da Safiyyah ta yar mata guda daya, ko gyara dakin da ta birkita bata yi ba ta dawo parlor looking so frustrated, tsaye tayi trying to calm her brain ko Allah zai sa ta tuna inda ta ajiye keys din, ta ɗaga kai da sauri tana kallon kofar parlon jin ana budewa, House mate dinta ne ya shigo living room din da wasu takardu a hannunsa, sai da ya kulle kofar ya zare makullinsa sannan ya karasa cikin living room din ya ajiye takardunsa kan kujera without looking at her yace "Good morning Housemate...." Bai tsaya yaji amsarta ba yayi wucewarsa daki yana cire jacket din jikinsa, Khaleesat ta bi sa da kallo har ya shige daki ya kulle, zaunawa tayi gefen kujera ta dafe kanta da taji har ya fara ciwo, yanzu ina ta jefar da mukullin nan for God sake gashi lokaci na ta wucewa, after few minutes sai gashi ya sake dawowa parlon, har sannan bai yarda ya kalli direction dinta ba, taga yayi wucewarsa kitchen ya fito rike da ruwan gora ya sake komawa dakinsa ya kulle, wayarta dake jaka ne ya fara ring ta bude jakar ta ciro wayar taga Safiyyah ce, dagawa tayi ta kai kunne Safiyyah tace "Ya baki shigo schl ba har yanzu, duk latti na yau na riga ki shigowa makaranta, ko kin manta muna da test ne" Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya tace "Ina sane Safiyyah" Safiyyah tace "Na fa ce akwai tutorial da zaki min kafin mu shiga test din" a hankali Khaleesat tace "Zan taho yanzu" Safiyyah tace "Don Allah ki taho, wallahi ba abinda na sani a course din kema kin sani" Khaleesat ta ajiye wayar bayan Safiyyah ta katse, agogon wayarta ta kafa ma ido, bayan wasu yan mintuna ta mike after gathering courage to do what her mind is telling her, walking slowly ta nufi dakinsa, tsaye tayi tana facing kofar, a hankali ta kai hannu kofar tayi knocking tana turo baki, Yana jin knocking din ya kalli kofarsa, gyada kai yayi letting out a grin, sai da ta sake knocking din sannan yace "Waye wannan?" Exactly yanda take yawan fada, Shiru tayi bata ce komai ba ta kara turo baki, ya mike ya tafi gun kofar ya bude yana kallonta daga sama har kasa da alamar mamaki, tuni ta kauda kai, still keeping a surprise face yace "Madam hope nothing??" Trying to sound a little polite tace "I need you to open the door for me" ya gyara tsayuwa yace "I don't understand, dama a hade makullinmu suke? Where is ur key?" A takaice tace "It's fine, no long talk" Juyawa tayi zata bar wajen, yace "Ko baki ga naki bane?" Ta wani kallesa tace "Banda haka ai da ban zo nan nace ka bude min kofa ba" Yace "Ohh i see, does this mean u are careless too?" Barin wajen tayi ta koma parlor ta zauna, ya gyada kai with smile of satisfaction sannan ya koma daki ya dauko makullinsa ya fito, sai da ya shigo parlon yace "Ta yaya ma zaki yi misplacing a whole bunch of key sai kace allura, this is kind of weird" Daukar handbag dinta tayi ta nufi kofar yana budewa ta fice daga parlon tayi wucewarta without turning her back, ya gyada kai yace "Zaki dawo ai, zan ga ta inda zaki shigo gidan" Kulle kofar parlon yayi still smiling, ko ba komai ya rama abinda ta masa jiya. Safiyyah na kallon Khaleesat tace "To ko ya shige cikin Couch ne makullin?" Khaleesat tace "Ta yaya zai shiga kujera?" Safiyyah tace "Kuma har kitchen din kin duba?" Khaleesat tace "Babu inda ban duba ba fa" Safiyyah tace "Toh kawai kiyi ma agent din gidan magana su baki wani makullin mana" Khaleesat tace "Gani nake kamar dogon process ne hakan, kuma ai biyu ne makullin kika yar min da daya shine na dauko spare key din nake using, to shima gashi ban gansa ba yanzu" Safiyyah tace "Kar ki wani damu kanki, makullin na nan zaki gansa, kawai kin mance inda kika jefar ne, amma definitely it's either in ur room ko kuma parlor, yanzu jira zaki yi sai sanda housemate dinki ya dawo ki koma gidan kenan?" Khaleesat tace "Wani housemate? Shi da ba kwana ma yake a gidan ba, kuma ba shi da exact time da yake zuwa" Safiyyah tace "Kai haba, to a ina yake kwana?" Khaleesat ta zaro ido tace "Kin ji ki da wani tambaya, ta yaya ni kuma zan sani? what is my business with him da zan san inda yake kwana" Safiyyah tace "To kawai mu je gidanmu ki kwana" Khaleesat tace "Kina ganin babu matsala hakan?" Safiyyah tace "Wani irin matsala? To gidanta ne ko na ubanta da za a samu matsala? ta shi mu tafi jare" Safiyyah na gaba Khaleesat na biye da ita a baya suka shigo parlor da sallama, Surayya matar cousin brother din Safiyyah dake zaune parlorn ta daga kai tana kallonsu, Safiyyah tace "Sannu da gida Mom Aslam" Surayya ta ci gaba da danna wayar hannunta tace "Yauwa" Khaleesat ta zauna kan kujera ta gaisheta, Surayya ta amsa without looking at her tana danna wayarta, Safiyyah tace "Ai kin ganeta Mom Aslam, kawata ce kuma Coursemate dita Khaleesat" Surayya tace "Ohk" Safiyyah tace "She will be passing the night here, makullinta ne ya ɓata" Surayya ta daga wayarta da ya fara ring ta kai kunne hade da amsa sallama ta mike ta bar masu parlon, Safiyyah ta kalli Khaleesat tace "Tashi mu je ciki" Mikewa Khaleesat tayi ta bi bayan Safiyyah zuwa dakinta, Safiyyah na idar da sallah ta canza kayan jikinta tana kallon Khaleesat dake zaune saman darduma tace "Bari in samar mana abinda za mu ci a kitchen" Kai kawai Khaleesat ta gyada mata, Safiyyah ta fita daga dakin... Khaleesat was so uncomfortable a gidan cause it's a home that she is not welcome, ko daga irin tarban da aka mata tasan she isn't welcome, karatun da take ta yi na boko ne ke while din mata lokaci, Safiyyah kuwa tun da suka ci abinci take ta bacci har yanzu da magrib yayi, Khaleesat tayi alwala sannan ta fito ta tasheta, bayan sun idar da sallah Safiyyah tace "Bari in je in ga me waccan matar ta girka" Ita dai Khaleesat bata ce komai ba tana ci gaba da azkar dinta, Safiyyah ta fita daga parlon, Surayya na parlor tana ba yaronta Cereal da ta hada masa, Safiyyah ta karasa parlon tace "Aslam yanzu ya tashi ne, ban gansa tun daxu ba" Surayya tace "Ehh" Safiyyah ta ɗan masa wasa sannan ta wuce kitchen, abinci ne iya cikinta taga Surayya ta ajiye mata a kitchen din, Safiyyah ta fi minti biyu tsaye kitchen din tana kallon abincin, can tayi kwafa ta dau plate ta juye ma Khaleesat kawai ita idan ya so ko cornflakes ne sai ta sha anjima, ta fito kitchen din kenan sai ga Cousin brother dinta ya shigo parlor, gaishesa tayi ta amshi ledan hannunsa yace "Leave it, kije ki ci abincin ki" Tace "Ai ba nawa bane ba ma, kawata zan kai ma, ni sai dai in sha cornflakes tunda abincin iya wannan ya rage" Surayya dai kallonta kawai take, Musty yace "Wace kawarki?" Safiyyah tace "Khaleesat, she lost her house key shine ta zo zata yi spending night din a nan" Musty yace "Oh Allah sarki, ba ayi abincin da yawa bane?" Safiyyah ta karkace masa plate din sosai tana nuna masa tace "Iyakarsa kenan aka bari a kitchen, tun da rana muka dawo kuma" Musty yace "Ohk, me ku ke son ci let me get it yanzu a restaurant" Safiyyah ta ɗan yi murmushi ta ajiye plate din saman center table kusa da Surayya tace "Bari in tambayi Khaleesar abinda zata ci" Surayya ta bi ta da wani kallo har ta shige daki, Safiyyah na shiga dakin tace "Khaleesat ki fito ku gaisa da yaya Musty nace masa kina nan" Khaleesat ta daga kai ta kalleta tace "Is it necessary Safiyyah?" Safiyyah tace "Ban gane is it necessary ba, yayana ne fa, kuma nace masa kina nan, ai ya kamata ki gaishesa dai ko" Khaleesat tayi shiru, can ta mike suka fito daga dakin tare, tana tsaye daga jikin kujera ta gaida Musty ba tare da ta kallesa sun hada ido ba, ya amsa da fara'a yana kallonta, Surayya dai fuskarta babu yabo babu fallasa take tura ma yaronta Cereal a hanci maimakon baki ba tare da ta sani ba, Khaleesat ce kadai ta lura da hakan, Safiyyah na murmushi ta kalli Khaleesat tace "Wai yaya yace me za mu ci zai fita yanzu ya siyo mana" Khaleesat taki cewa komai, Safiyyah tayi fari da ido ta fara lissafo masa abubuwan da zai siyo masu, Surayya ta ajiye bowl din Cereal din hannunta kan Centre table ta ciro Aslam daga kekensa tace "Mu je in maka wanka Aslam" Daga haka ta bar parlon tayi wucewarta daki, Khaleesat dai ta sunkuyar da kanta, Muryar Musty da taji yana mata magana yasa ta daga kai ta kallesa, yace "Su kenan iya abinda Safiyyah ta lissafo za a siyo maku Khaleesah?" Kai kawai Khaleesat ta gyada masa, bayan nan ta juya ta koma dakin Safiyyah jiki a sanyaye. ✍🏻 07087865788 [5/1, 5:20 PM] khaleesat Haiydar ✍️: ✨✨ HALYSAAH ✨✨ ✍🏻 By _Khaleesat Haiydar_ 4..... Khaleesat ta zauna gefen gadon dakin Safiyyah duk jikinta a sanyaye, jawo wayarta tayi tana duba agogo taga karfe bakwai har da rabi, sam bata ji zata iya kwana gidan nan ba, tasan probably yanzu House mate dinta na gida, to ya ta iya? Hakan dai zata koma gidan tayi masa knocking, the thought of this made her weak, shigowar Safiyyah dakin yasa ta daga kai, Safiyyah ta rike haɓa tace "Kinsan kuwa shegiyar matar nan bata ajiye mana abinci ba, ai ko sai ga yaya Musty kamar an jefosa kuma night shift fa yake yi wallahi, kinga ko ba komai sai ta hadiyi zuciya ta mutu don bakin ciki yau, abincin da na lissafo masa ko rabinsa baza mu iya ci ba kuma kwalelenta sai dai in har shi yayi dubaran siyo mata nata daban, ban taɓa ganin me tsinannen hali kamar matar nan ba tirr, ni ai na zata in mutum zai taho wata kasar barin baƙin halinsa yake a gida, to ita dai da nata ta taho wallahi" Khaleesat tayi murmushin karfin hali tace "Lallai kam, kinga ni kuma tafiya zan yi fa, da ma bai siyo abincin ba, yanzu Housemate dina ya kirani yace he is back home" Safiyyah ta bude baki da mamaki tana kallonta, can tace "Ban gane ba, yaushe kika samu number Housemate dinki har ya kira ki? Wallahi ban yarda ba kawai so kike ki tafi, bari ki ji in dai don Surayya ce nima fa zaman hakuri nake da ita a gidan nan Khaleesat, mugun halinta bai da part 2, gwara kawai kiyi zamanki in ma shekara zaki yi a nan babu yanda ta iya tunda ba gidan ubanta bane kuma warmly Ya Musty zai yi welcoming din ki" Khaleesat tace "Sophie ni fa tunda Housemate dina ya dawo bazan kwana a gidan nan ba, dama bani da kayan da zan canza sannan na ma manta na bar kaya a washing machine kin ga bani kadai bace a gidan, may be zai yi laundry shi ma" Safiyyah ta hade rai tace "A takaice me kike nufi kenan? Kina ji ina lissafa ma Ya Mustapha abinda zai siyo mana don walakanci ki ce ke zaki tafi? shima ai bazai ji dadi ba idan ya dawo da abincin yaga kin tafi kuma saboda ke ya fita ya siyo don in dan ta nice sai dai yunwan ya kasheni in bai ga dama ba" Khaleesat ta ɗan yi murmushi tace "Zan jira ya dawo, sai in tafi da abincin gida kawai" Safiyyah da har ranta ya ɓaci tayi mata banza ta tafi ta dau wayarta tana dannawa, Khaleesat dai bata sake cewa komai ba, komin fushin Safiyyah ita kam baza ta kwana gidan nan ba, after a while Ya Mustapha ya dawo gidan da abincin da ya siyo masu, Safiyyah ta mike ta nufi kofa bayan ya kirata a waya, Khaleesat ta bi ta da kallo har ta fita sannan tayi murmushi, Safiyyah ta karasa dinning table ta dau abincin da Cousin din nata ya ajiye masu ta koma daki, iya wanda zata ci ta cire ta bar ma Khaleesat duk abincin, Khaleesat tace "Ya zanyi da abincin nan me yawa Sophie?" Ba tare da Safiyyah ta kalleta ba tace "Wannan kuma ke kika sani" Khaleesat bata son jan maganar yayi tsayi kawai ta mike ta dau veil dinta da handbag sannan ta dau ledan abincin tace "Sai mun hadu gobe, thank you so much dear" Safiyyah tace "Kinyi order din ride ne?" Khaleesat tace "Sure" Mikewa Safiyyah tayi suka fito dakin a tare, dai dai fitowar Mustapha parlor shi ma, yana kallonsu da mamaki yace "Ya aka yi kuma?" Safiyyah ta langwabar da kai tace "Her Housemate is back, shine kawai zata tafi gida wai" Yace "Isn't it late?" Safiyyah ta kyabe baki tace "Nima dai haka nace mata" Ya kalli Khaleesat da ta sunkuyar da kanta, yace "Kiyi hakuri ki bari gobe mana Khaleesah, yanzu ai dare yayi...." Khaleesat ta ɗan yi murmushi ta dago kai cikin sanyin murya tace "Akwai abinda nake son zan yi ne idan na koma gida" Mustapha ya daga kafada yace "While, if you insist...." Ta gyada masa kai tace "Nagode" Safiyyah ta wani harare ta, Mustapha yace "Zan koma aiki ne dama, mu je sai inyi dropping din ki ko" Khaleesat bata yi expecting offer din nasa ba, ta ɗan kallesa tace "Na riga nayi order din Lyft ai...." Safiyyah ta mata wani kallo tace "Haka kuma you can cancel it ai ko...." Kasa cewa komai Khaleesat tayi, lkci daya ta zama uncomfortable, Mustapha dai kallonta kawai yake, after few seconds a hankali tace "Ohk" in response to Safiyyah, Kofa Mustapha ya nufa, Safiyyah tayi kasa da murya tana kallonta tace "Ke in zaki saki jiki ki saki jiki, a ko da yaushe sai kin nuna ke er.... Ya ma sunan wannan unguwan naku a kano?" Khaleesat ta dinga kallonta, can ta juya ta nufi kofa tana tafiya slowly, Safiyyah ta fara dariya kasa kasa tace "Good night girlfriend" Ko tankata Khaleesat bata yi ba. Yana zaune cikin motarsa yana jiranta har ta karaso, ta bude gaban motar ta shiga, sai kallon entrance din gidan take tana fatan kar matarsa ta fito ta gansu, ya tada motar suka bar garage din, sai a sannan ta sauke boyayyen ajiyar zuciya tayi fastening seat belt dinta a ranta ta dau alwashin wannan shine zuwanta na karshe gidansu Safiyyah, bayan sun hau saman hanya taji yace "Where do u stay?" Idonta na kan titi ta gaya masa, yace "Co-living kike yi kenan?" Tace "Um" Yace "Menene yasa baki dawo ku zauna gidana tare da Safiyyah ba instead of living alone with a stranger?" Ko rufe baki bai yi ba tace "Ai yawanci ni kadai ce a gidan, my Housemate is not always around" Yace "Ok then" After almost a minute yace "Kema er kano ce?" Tace "Um" Yace "Wani anguwa?" Tayi shiru, sai kuma ta ɗan kallesa ta gefen ido taga kallonta yake at the same time yana tuki, ta sauke idonta kasa ta gaya masa, she is so uncomfortable with him, Yana gyada kai yace "Ohk, i am also from kano, Sharada to be precise" Ita dai tayi shiru bata ce komai ba, cikin minti 13 ya kawota gida, ya juya yana kallonta bayan yayi parking, daukar ledan abincin tayi tace "Nagode sosai, Allah ya saka da alkhairi" Wayarsa taga ya mika mata, ta daga kai ta kallesa, yace "Ki sa min digit dinki sai mu dinga gaisawa, in kina bukatar wani abu kuma feel free to ask me anytime" Khaleesat ta sauke idonta, ita da ta sani babu abinda zai kai ta gidansa yau, da kawai dawowarta tayi ta zauna bakin apartment dinta ta jira har sanda Housemate dinta ya ga daman dawowa ya bude mata kofa, muryarsa ya dawo da ita duniyar tunanin da ta tafi ta daga kai da sauri ta kallesa, bata ma san me yace ba taga dae yana kallonta, da kyar tayi stretching hannu ta amshi wayar ta sa masa digit din nata, yayi dialing, ita dai kanta na kasa, wayarta dake cikin jaka ya fara vibrate, yace "Kiyi saving nawa digit din" Tace "Um" Yace "Good night, take care Khaleesah" Tayi karfin halin cewa "Nagode" Daga haka ta bude motar ta sauka, kallon window din kitchen na apartment dinta tayi ganin wuta a kunne, sannan taga mota a Garage, she felt relieved sanin cewar her Housemate is around, ta zaga zuwa gaban apartment din tana jin sanyi na shigarta sosai don sanyi ya fara shigowa kasar, knocking din kofar parlor tayi gently, sai da ta kwankwasa sau uku sannan taji muryarsa yace "Who is there?" Ta kauda kai a takaice tace "Somebody" Yace "Somebody? I am not expecting somebody this late" Ta wani hade rai tace "Ni ka bude min kofa in shiga gida" Yace "Ke wa zan bude ma kofa?" Kin cewa komai tayi cause she is already provoke, yace "Ohk then, i am going back to my room after all i am not a door keeper" Tana jin haka a fusace tace "Don Allah ka bude min" Yace "Ke wa?" Tace "Ban gane ni wa ba?" Yace "Ohh, tsawa ma kike min?" Ta kara marairaicewa tace "Don Allah ka bude mana" Yace "To ai ni ban san wacece ba, baki da suna ne?" Shiru tayi tana kallon kofar kamar zata fashe da kuka, Yace "Ke zan fa yi tafiyata daki in baza ki fadi sunanki in san wa zan bude ma kofata ba cikin daren nan" Ta sauke idonta kasa, after a few seconds ta dake tace "Khaleesat" Yace "Halysaah..." Wani harara ta zabga ma kofar, Kamar yana counting harufan sunan yace "Ha.. lee...saah" A fusace kamar zata yi kuka tace "Sanyi fa nake ji ka ki bude min kofa, ko don ba kai bane tsaye cikin sanyin?" Bude kofar yayi yace "Baki san da sanyin ba kika je kika yi dare a titi?" Ko kallonsa bata yi ba ta kusa bangajesa ta shige parlon fuskarta a murtuke, yace "Wajen saurayinki kika tafi kenan kika yi dare, naga ma shi ya ajiye ki a mota, Allah sa ba me sa ki kukan nan bane dai" Direct dakinta ta nufa without even looking at him abinda ya fada na sinking zuwa cikin kanta, ya bi ta da kallo yace "Ok.... ga Door keeper dinki ya bude maki kofa ko? Tomorrow is another day, better look for ur lost key in ba so kike ki kwana a waje ba next time" Tuni ta bude kofar dakinta tayi shigewarta ta sa makulli tare da jan dogon tsaki. Da safe tunda Khaleesat ta tashi take zaune tana tunanin how today will be like, taje schl din ne ko ta hakura kawai tunda bata da makulli yanzu, zaro ido tayi bayan ta tuna lecture din da za su yi ranan, she just can't miss that class don course din is a bit complicated, mikewa tayi ta shiga bandaki, wajen karfe tara ta fito parlor hoping house mate dinta bai fita ba, don jiya wajen karfe sha biyu da rabi na dare ta fito don saka abincin da bata iya ta ci ba a fridge ta gansa kwance a parlor yana bacci, har ta gama abinda zata yi a kitchen ta fito bai farka ba, tun zuwansa gidan ranan ne rana na biyu da taga ya kwana a gidan, babu kowa parlorn ta karasa kusa da tagan parlon tana leka Garage ko zata ga motarsa taga motar na nan alamar he is around, ajiyar zuciya ta sauke don da ya fita shkkn babu tafiyarta makaranta kenan, kitchen ta tafi ta hado shayi ta debi cookies ta dawo parlon, har ta gama breakfast bai fito parlor ba, sai kallon agogo take don goma ta kusa gashi bata son tayi latti, kuma ita dai bazata taɓa masa maganar ya bude mata kofa zata fita ba, goma saura minti goma ya fito parlorn, ita dai bata dago kanta ba tana ci gaba da danna wayarta, taji yace "Good Morning, Halysaah" Without looking at him tana ci gaba da danna wayarta kamar tana ma kanta magana tace "Ok" Ta gefen ido ta bi sa da kallo ganin ya nufi kofa ta mike ta bi bayansa, yana lura da ta biyosa sai ya fasa bude kofar, ya juya yana kallonta keeping a serious face yace "Me ya faru?" Ta kauda kai taki cewa komai, mayar da makullin yayi aljihunsa zai bar wajen ta wani kallesa tace "Ni dai ka bude min kofa zan tafi makaranta" Yana gyada kai yace "Ohhh, ohk kin boye makullinki ne don in zama door keeper dinki dama?" Taki kallonsa don bata ma san me zata ce masa ba, ganin da gaske barin wajen zai yi ta marairaice tace "Makaranta zan tafi fa" Ya juyo yace "Be a good girl and beg politely first....." Shiru tayi tana bin sa da kallo har ya koma cikin parlor ya zauna kan kujera, Ta dake da kyar tace "Please ka bude min. i am going to school" Yace "Ban ji ba" Takaici yasa ta dauke kai taji ranta ya kara ɓaci, ganin lokacinta kawai take ɓatawa ta sake juyowa trying to be calm tace "Plss ka bude min kofa i am going to school" Ɗan murmushi yayi ya mike ya dawo bakin kofar ya ciro makullin a aljihunsa yace "Never knew u can be this Obedient" Ita dai bata kallesa ba, ya bude kofar yace "In kika sake yin dare baza ki shigo gidan nan ba sai dai ki kwana bakin ƙofa ko kuma a Garage..." Bata tankasa ba ta fice daga parlon with annoyance almost brushing his shoulders, ya bude baki yana bin ta da kallon mamaki yace "Ohh, is this ur thank you??" Tuni har ta kusa titi abun ta, ta ja tsaki feeling so fed up with him. Bayan Khaleesat sun fito daga aji Safiyyah tace "Kinsan me Khalee?" Khaleesat ta juya ta kalleta, Safiyyah tayi dariya har da kyakyatawa tace "Wai Ya Musty ke tambayata ko kina da saurayi" Sai da gaban Khaleesat ya fadi, Safiyya bata fasa dariyar da take ba tace "Wallahi kuwa, he chatted me up yesternight wajen karfe sha biyu, bari ma in nuna maki ki ga, ni ko nace masa baki da kowa wallahi" Sai a sannan Khaleesat ta kalleta tace "Ban gane bani da kowa ba Sophie?" Safiyyah tace "To kina da shi ne? To in kallon saurayinki kike ma Abdul to ni wallahi kallon ɗan daba nake masa, ni dai nace ma Ya Musty bakya kula kowa saboda karatu don haka baki da saurayi, kema kin dai san da Ya Musty na da mugun hali da tuni na fesa maki ni da bakina baya shiru, ai ko don wannan er banzar matar tasa zan so ya kara aure, kuma ace kawata ya aura huhuhu za a ga rashin nasiha da jahilci wajena" Khaleesat ta mike tana gyara Veil din jikinta tace "Zan tafi gida sai gobe" Safiyyah ta tsuke fuska tace "Ban gane zaki tafi gida ba daga na kawo maki maganar arziki" Khaleesat tace "Wallahi da na sani babu abinda zai sa in bi ki gida jiya Safiyyah, haba fisabilillah, put ur self in the wife's shoe in kece aka ma haka zaki ji dadi?" Safiyyah tace "Godforbid, her shoes will never size me sef kafin in sa kafata ciki Khaleesat, ai ni bani da mugun hali kamar ta, kina ga fa ko tsayawa ta amsa gaisuwarki bata yi ba ta wani ƙara waya a kunne ta wuce daki ita er iska, sannan bari kiji jiya iya cikina ta ajiye abinci a kitchen bayan nace mata nan zaki kwana kuma ta sani, ni dai wallahi in kika ce baki son yayana nice kawai baki so, Ya Musty bai da wani aibu wallahi, ga arziki ga Ilimi ga kyau, baza ma ki ce ya taɓa auren wata er iska ba wai ita Surayya, ɗan saurayi da shi" Khaleesat tace "In matarsa kike son tura ma haushi ai kema zaki iya aurensa tunda he is ur cousin brother kuma da aure tsakanin ku" Daga haka Khaleesat ta bar wajen tayi wucewarta, Safiyyah tace "Oho dai wallahi ce masa zan yi kin amince sai dai ki mutu, haka kawai kin makala ma kanki ɗan daba kina kiransa da wanda zaki aura, ki auresa ki ci uwar me da shi, wannan har duka sai ya dinga nakada maki babu me kwatarki in ku ka yi aure" Khaleesat na isa gida taga babu motar Housemate dinta a parking space, jingina tayi jikin entrance din apartment din nasu, gashi ta gaji sosai ga yunwar da take ji, babu wanda ta saba da shi a Neighborhood din balle ta shiga gidansa, balle su turawa basu yarda da hakan ba ma, ta kusa twenty minute a tsaye sai ga motarsa ta hango, sunkuyar da kanta tayi har yayi parking ya karaso kofar entrance din, gefe ta koma without looking at him, tun kan ya karaso kofar apartment din ya sa hannu a aljihunsa yaji babu makullin, ya ɗan bude ido still yana laluba duk aljihunsa, sai a sannan ta daga kai tana kallonsa, juyawa yayi ya koma motarsa ta bi sa da ido, ya gama dube dubensa a motar bai ga makullin ba, ai tana ganin yanda yake dube dube tasan kilan ya yar da makullin, shikenan ta shiga uku, she is soo tired, har wani jiri take ji a tsayen da take, dawowa yayi yana kallonta yace "Look Halysaah, i think i left the key at where i am coming from" Ita dai bata ce komai ba kuma bata bari ta hada ido da shi ba, yace "Ko zaki shiga apartment din Neighbor dinmu kafin in dawo" Sunkuyar da kanta tayi still keeping mute, yace "Or ain't you familiar with them?" A takaice tace "Eh" Yace "Ok i will be back as soon as possible" Juyawa yayi ya koma gun motarsa ta bi sa da wani kallo.... Khaleesat na ta tsaye har bayan wani minti sha biyar sai gashi ya dawo, yana kallonta yace "Allah ya taimake ki na gani" Wani kallo tayi masa wato ita Allah ya taimaka ma, yana bude kofar tayi shigewarta ciki ta nufi dakinta ba tare da ta juya ba, sai da ta kwanta na kusan minti sha biyar sannan ta mike a hankali ta shiga bandakinta, bayan Khaleesat tayi wanka tayi sallah tana zaune kan darduma taji yayi knocking kofar dakinta, kallon kofar take bata ce komai ba kuma bata amsa ba balle ta tashi, taji yace "Halysaah" Bluntly tace "Me ya faru?" Jin ya murda kofar dakin ta zaro ido ta mike tsaye da sauri tace "What?" Tuni ta isa gun kofar ta bude tana masa kallon tuhuma, ledan hannunsa ya ajiye mata yace "I got you food, naga kin yi laushi" Ta kalli ledan, ya juya ya bar wajen ta bi sa da kallo har ya koma parlor, sauke idonta tayi, bayan few seconds ta duka ta dau ledan ta juya ta koma dakin. Khaleesat ta bude abincin da ya kawo mata ta fara ci kenan wayarta ya fara vibrate, mikewa tayi ta bude handbag dinta ta ciro wayar, sosai gabanta ya fadi ganin Abdul ke kiran ta, zaunawa tayi gefen gado tana kallon screen din wayar har sannan gabanta na bugawa, kafin kiran ya katse tayi karfin halin dagawa ta sa handsfree sannan tayi sallama cikin sanyin murya, maimakon ya amsa sai ji tayi yace "Wato all this While ni kike jira in kiraki ko Khaleesat?" Ta sauke idonta a hankali tace "To ai cewa kayi duk sanda kake son magana da ni zaka kirani amma kar in sake in kira ka" Yace "Don nace kar ki kirani sai ki ki kiran nawa? Me yasa baki reason ne?" A sanyaye tace "Kayi hakuri" Yace "In ban hakura ba ya zan yi da ke? Ai saboda baki damu da ni bane yasa kika zama comfortable without calling me all this while, ko da bazan daga ba ai kamata yayi ki kira" Cikin sanyin murya tace "Kayi hakuri" Yace "Yaushe za ku fara jarabawa?" Tace "Probably nan da 6 to 7 weeks" Yace "I can't wait har zuwa nan da sati bakwai ban gan ki ba Khaleesat, idan na samu lokaci zan shigo anytime from now in sha Allah" Shiru Khaleesat tayi as if trying to process what he just said, yace "Hello" Da sauri ta kifta ido tace "Na'am ina ji" Yace "Me yasa kika yi shiru? Ko baki son in zo ne?" Tayi yake tace "Aa ban yi shiru ba network ne, ban ji me kace ba" Yace "Ohk, nace you should expect me any moment from now" A hankali tace "Toh Allah ya kai mu" Yace "Ameen, me kike yi yanzu?" Tace "Abinci nake ci" Yace "Ohk switch to video call" A hankali tace "Toh" Mayafinta ta jawo sannan tayi yanda yace mata. ✍🏻 07087865788 for more info [5/2, 5:50 PM] khaleesat Haiydar ✍️: ✨✨ HALYSAAH ✨✨ ✍🏻 By _Khaleesat Haiydar_ 5...... Wajen karfe biyar na yamma Khaleesat ta fito parlor daga dakinta, window ta nufa tana leka garage ta ga motar Housemate dinta alamar yana gidan, juyawa tayi ta tafi kitchen zata yi disposing takeaway din da yayi mata daxu, ta window din kitchen din ta hangosa zaune a Lawn din dake bayan kitchen din waya ƙare a kunnensa alamar he is making a phone call, komawa baya tayi don kar ya hangota ta window din kitchen din, ta ajiye ledan hannunta a hankali ta juya ta fita daga kitchen din ta dawo parlor, tsaye tayi tana kallon handle na kofar living room din, sai kuma ta tafi gun da ya ajiye takardun karatunsa ta hau bincika Books din da sauri, har ta gama dube dubenta bata ga abinda take nema ba, ta koma kitchen din tana kara lekansa, seeing he is still on call ta dawo da sauri ta tafi corridor din dakunansu, tsaye tayi gabanta na faduwa as if contemplating on whether to do what is on her mind or just forget it, ganin she is just wasting time ta runtse idonta ta bude, sai kuma ta kai hannu handle din kofar dakinsa a hankali ta bude ta shiga ciki zuciyarta na bugawa, bin dakin that was neat and tidy ta fara yi da kallo kafin ta karasa can ciki da sauri, har sannan tana kallon ko ina na dakin, ta ma rasa daga inda zata fara duba abinda ta shigo nema, zagaye dakin ta fara yi tana dube dube with confusion, daya wayarsa dake gefen gado yayi haske alamar shigowar sako, kallon screen din wayar take yi ganin wani matashi kamarsa a shekaru ne a fuskar wayar, ta juya ta kalli Trouser dinsa, gabanta na faduwa ta dauka ta kai hannu aljihun wandon, Dollar ta ciro masu yawa tayi saurin ajiyesu gefen gado, sannan ta duba daya aljihun, zaro ido tayi jin makulli da Counter a ciki, ta ciro da sauri tana kallon makullin taga makullin kofar parlor ne, bata san sanda tayi murmushi ba ta ajiye wandon a inda ta dauka sannan ta juya da sauri, ƙamewa tayi a spot din da take ganinsa tsaye bakin kofar dakin ya rungume hannu yana kallonta daga sama har kasa, kawai ta juya masa baya zuciyarta na bugawa taji kamar ƙasa ya bude ta shige ta huta, after some seconds taji yace "Sannu da aiki" Ita dai ta kasa juyowa, she felt so ashame at that moment, she wish this never happened, sai juya makullin hannunta take with shame, Calmly yace "Give me the key" Ta wani turo baki taki juyowa tace "To ba amfani zan yi da shi ba" Yace "Dama in bana nan bincike kike shigowa ki min a daki?" Bata san sanda ta juyo tana kallonsa babu ko kiftawa ba jin abinda yace, sai kuma ta ajiye makullin a gefen gado ta nufi kofa ta bi gefensa ta fice daga dakin ta shiga nata ta tura kofar, nan da nan taji hawaye ya cika idonta ta zauna gefen gado, sai kuma ta ɗora kanta saman pillow hawaye na sauka idonta har da shessheka. Karfe bakwai da few minutes Khaleesat na zaune kan darduma, tun da ta idar da sallah take zaune wajen, da ta tuna abinda Housemate din nata yace mata sai taji hawaye ya cika idonta, gaba daya taji ta tsani zaman gidan, kuma bata jin zata iya ci gaba da zama as far as he is here, ta yanke shawaran kawai zata gaya ma Abdul ya canza mata gida kamar yanda Safiyyah ta bata shawara tun farko taki dauka, wayarta dake gefen gado ta dauka jin ana kira, tana dubawa taga Mustapha ne ke kiranta, ajiye wayar tayi gefenta taki dauka har ya katse, ya sake kira nan ma taki dagawa, bayan ɗan lokaci aka sake kiranta kallon wayar tayi a bit fed up thinking it's still Mustapha sai taga Abdul ne ke kiranta this time around, ta jawo wayar a hankali tayi picking ta kai kunne, sallama tayi masa sannan ta gaishesa, yace "Ya naji muryarki haka?" Tayi shiru tana tunanin ta inda zata fara sanar masa the situation at hand, muryarsa ya dawo da ita tunanin da take, a ɗan tsawace yace "Ke, baki ji na ne zaki min shiru?" Kasa gaya masa tayi don bata ma san yanda zai fara daukar lamarin ba barin yanda taki gaya masa tun farko, Ta ɗan yi yake tace "Ina jin ka, kawai muna da wani jarabawa ne gobe, kuma ina jin ciwon kai, and I haven't covered up, shi yasa nake damuwa" Yace "Na ce ki dena stressing kanki da karatu, u are not dull to be studying as if ur life depends on it, read a little and get enough rest, nasan za ki yi passing ko ma me za kuyi gobe" Tana murmushin karfin hali a hankali tace "To" Yace "Kin ci abinci ne?" Ta girgiza kai tace "Ban ci ba" yace "Ohk get something to eat, idan kin gama sai ki kirani ina jiran ki" Tace "Toh" Katse wayar yayi, ta bude WhatsApp dinta tana duba ko Neighbor dinsu ta mata reply taga ta hau WhatsApp din amma still bata yi reply ba, yau kwana uku kenan basu yi magana da Ummanta ba, Dialing din Number Sha'awa tayi ta direct call, har ya katse ba a daga ba, sai da ta sake kira aka daga, sallama Khaleesat tayi mata sannan ta gaisheta, Sha'awa ta amsa tace "Lafiya lau Khaleesah, ya karatu?" Khaleesat tace "Alhamdulillah ya gida ya su Kamilu?" Sha'awa tace "Duu lafiyansu lau wallahi" Khaleesat tace "Su Ummanmu suna lafiya..." Sha'awa tace "Kwana biyu kinyi magana ta wassap kinji shiru ko, to Ummanku dai bata da lafiya amma da sauki yanzu" Nan da nan Khaleesat taji hankalinta ya tashi don dama tun da taji shiru for days tasan ba lafiya ba, don ko bata yi ma Ummanta magana ba ita zata mata ta wayar Sha'awa taji ko tana lafiya, Hankalinta a tashe tace "Aunty Sha'awa tun yaushe?" Sha'awa tace "Ina jin yau kwana uku, ai an ma ce kar a gaya maki, shi yasa ko mayar maki da sakon da kika yi ta wassap din ma ban yi ba, yanzun ma kar ki wani ce zaki kira kowa kiyi ta mata addu'a kawai Allah ya bata lafiya" Khaleesat taji hawaye na sakko mata ta kasa cewa komai, Sha'awa tace "Wai daga ta tashi zata fito daki tayi alwalan magariba shi ne fa ta yanke jiki ta fadi a bakin kofar dakin, duk kwanan nan ina rabata da saka ma kanta damuwa tunda tasan matsalarta na hawan jini, to kinga ai irin haka ake gudu gashi kuma ya faru, Farida ma ta taho daga legas tun jiya ta iso, kar ki wani tada hankalinki don jikin da sauki" Cike da karfin hali Khaleesat tace "Suna asibiti ne yanzu?" Sha'awa tace "Wani asibiti? To har sai da Farida ta zo sannan ta kai ta asibiti jiya in gaya maki, amma duk kwanakin nan tana gida gashi ko taɓata kika yi a daya barin jikinta bata ji wai, ko magana ma in tayi sai kin sa kunne sosai zaki ji, ke abun fa ba kyau, har yanzu hankalinmu a tashe yake, an dai ce kar a gaya maki kar hankalinki ya tashi...." Khaleesat in hankalinta yayi dubu ya tashi a lkcn, ta kalli Screen din wayarta jin kiran ya katse alamar katin ta ya kare, ajiye wayar tayi ta fara rera kuka kamar an sanar mata da mutuwa... Har karfe goma na dare Khaleesat ta kasa tashi daga kan darduman da take, sosai ta shiga damuwa ba kadan ba, a inda take zaune Abdul ya kirata sau biyu amma ta kasa picking call din nasa, karfe goma da rabi taji anyi knocking kofar dakinta, ta juya ta kalli kofar tana share hawayen dake idonta amma bata tashi ba sai ma hade rai da tayi, after a while ya sake knocking still dai bata tanka ba, sai kuma taji yace "Assalamu alaikum" kawai ji tayi ya bude kofar dakin ta juya da sauri daga inda take zaune suka hada ido, daga nan bakin kofar ya tsaya yana kallonta, ita dai taki yarda ta sake hada ido da shi, ya karasa ciki ya tsaya still leaving enough distance between them, calmly yace "Maganar da na maki yasa kike kuka? But i was only pulling ur legs Halysaah, i am sorry about that, was just joking" Wasu hawaye suka cika idonta sai kuma ta fara kuka, bude ido yayi alamar mamaki sosai yana kallonta, can dai ya kwantar da murya yace "Look, do not take my words serious Halysaah ni wasa nake maki wallahi" Ta rufe fuskarta da Hijab din jikinta tana kuka a hankali, dukawa yayi da mamaki sosai yana kallonta ya ma kasa cewa komai, after few seconds da taji shiru ta ɗan bude fuskarta don tunaninta ya fita daga dakin, suna hada ido ta daure fuska tace "Ni saboda kai nace nake kuka?" Yace "Toh why are you crying?" Shiru tayi bata ce komai ba wasu sabbin hawayen na cika idonta, Yace "Tell me Halysaah, what is making you cry?" Kamar bazata ce komai ba sai kuma tace "My mother is sick" Yace "Hasbunallah, what's wrong with her?" bata sake ce masa komai ba tana goge idonta, After few seconds ya sauke ajiyar zuciya yace "Amma ai ba kuka zaki zauna kina yi ba, addu'a zaki mata Allah ya bata lafiya" Nan ma dai bata ce komai ba, ya mike yace "Allah ya bata lafiya" Sai a sannan tace "Ameen" Yace "Are you going back home to check on her?" Ta daga kai ta kallesa amma bata ce masa komai ba, yayi shiru shima, can yace "Are you from kano?" Ta gyada masa kai, Yace "Allah Ubangiji ya bata lafiya, and try getting something to eat for Dinner" Ta sunkuyar da kanta kawai, ya juya ya fita daga dakin ya kullo mata kofar gently. Wajen karfe sha biyu na dare Khaleesat na kwance taji ya sake knocking kofar dakinta, juyawa tayi ta kalli kofar, bayan wasu yan sakwanni ta mike zaune tana kallon kofar, sai da ya sake knocking sannan ta sauka daga saman gadon ta dau hijab dinta ta saka ta nufi kofar ta bude, yace "Are you still crying?" Ta hade rai ta girgiza kai without looking at him, yace "Ok naga baki fito kinyi dinner ba and it's past 12, ki nemi abinda za ki ci kar ki kwanta haka" Ita dai bata ce komai ba, yace "Hello" Daga kai tayi ta kallesa tace "Naji" Yace "Good" Kullo kofar dakin nata tayi ta nufi kitchen tana tafiya a hankali, sai da yaga ta shiga kitchen din sannan ya shiga dakinta yana bin ko ina da kallo, after a while Khaleesat ta fito daga kitchen din with a cup of tea and some cookies, tsaye ta gansa corridor, bayan ta karaso yace "Kin ga nima Ummi na bata da lafiya amma ban zauna ina kuka ba kamar yanda kika yi" Khaleesat bata kallesa ba ta shige dakinta ta kulle kofa, tana gama shan shayin ta koma saman gado ta kwanta, tasan yau da kyar ta iya bacci, she wish she can just see herself in Nigeria, but how?? Wasu hawaye ne suka zubo idonta ta lumshe ido, after a while ta jawo wayarta a hankali tayi dialing number Abdul bayan ta tuna ya kirata har sau biyu daxu bata iya tayi picking ba, har kiran ya katse bai daga ba, ta sake kiransa nan ma bai daga ba, tasan as usual yayi fushi kenan, ko uxuri bazai mata ba, ajiye wayar tayi ta juya zuwa daya side din gadon. Washegari da safe Khaleesat na zaune daki tana ta kokarin kiran Aunty Farida amma baya shiga, har Sha'awa sai da ta kira ita ma wayarta baya shiga, ta rasa wa kuma zata kira, ta kalli agogon wayarta dake nuna karfe goma sha daya ta ajiye wayar tayi tagumi, tun daga daren jiya har yau bata da sukuni, ko schl din ma yau tasan bazata iya zuwa ba, juyawa tayi jin knocking a kofar dakinta, tana dai zaune har sai da ya kwankwasa kofar sau uku sannan ta sauka daga saman gado, walking slowly ta tafi ta bude kofar, Yace "Good morning Halysaah, how was ur night?" Without looking at him tace "Fine" Yace "Ya jikin Mama? Kun yi communicating da su?" Kai kawai ta gyada masa bata ce komai ba kuma bata kallesa ba, Paper da pen din hannunsa ya mika mata yace "Can i get ur Email Address?" Ta daga kai ta kallesa da mamaki tace "I don't understand" Yace "I mean ur Email Address" wayarsa ne ya fara ring ya mika mata takardan da pen ya daga kiran sannan ya juya ya bar wajen, ita dai ta bi sa da kallon mamaki, can ta juya ta koma daki ta ajiye takardan da pen da ya bata, after some minutes sai gashi ya dawo yayi knocking yace "Can i get the paper" Tasowa tayi ta bude kofar bayan ta dau pen da takardan tace "Why are you asking for my Email Address?" Yace "Ki dae rubuta ki bani" Shiru tayi, sai kuma ta jinginar da paper din jikin kofa ta rubuta sannan ta mika masa ya amsa ya juya ya bar wajen, yana fita da few minutes taji message ya shigo wayarta, ta dau wayar ganin E-mail ne ya shigo ta bude, kallon Image din da ta gani as Email din ta dinga yi babu ko kiftawa, she look shocked and confused at the same time, ta daga kai tana kallon kofar dakinta babu ko kiftawa, dai dai sanda taji sallamarsa, kasa tashi tayi daga inda take zaune, har sai da yayi knocking sau biyu tayi karfin halin mikewa ta isa kofar ta bude tana kallonsa, Yace "I don't know if you find this okay and a good idea" Ita dai bata fasa kallonsa ba looking speechless, Yace "Hope they won't be Mad at this back home Halysaah?" Jin bata basa amsa ba ya gyada kai yace "I guess it's a bad idea, I should have ask for ur opinion first before doing this" Nan da nan hawaye ya cika idonta ta sunkuyar da kanta, yace "Ok it's fine, i will get the ticket cancelled" Daga kai tayi da kyar tana kallonsa hawaye na zuba idonta tace "Thank you so much, i appreciate" Yace "Sure??" Ta gyada masa kai, yace "Ohk, u can order a Lyft that will be taking u to the airport later, ur flight is at 3pm today" Sauke idonta tayi cause she is totally speechless, ya mika mata travelling documents dinta, amsa tayi cike da mamakin how he got them, ya juya ya bar wajen, komawa cikin daki tayi ta kulle kofar tana kallon inda take ajiye travelling doc din nata a dakin, did he come to her room to check ne, to ai throughout babu inda taje, ta karasa gefen gado har sannan jikinta a mugun sanyaye ta zauna, kallon screen din wayarta ta sake yi tana kallon ticket din don ganin abun take kamar a mafarki, tana kara duba taga tun daren jiya ya siya ticket din and kamar yanda yace the flight is by 3pm today, ta ma rasa ko farin ciki zata yi ko kuma wani reaction zata yi, amma da ta tuna she is going back home to see her Mom which was her wish since yesterday sai taji wani farin cikin da tunda take bata taɓa jin irinsa ba a rayuwarta, 80% a cikin dari na damuwarta ya ragu cikin lokaci kankani, kallon agogo tayi taga sha daya ya wuce sosai, the weakness she is been feeling since this morning immediately vanished, mikewa tayi tana share hawayenta ta dau medium box din kayanta.... Karfe biyu Khaleesat ta gama duk abinda take, har sallan zuhur tayi, Lyft din da tayi ordering kawai take jira, tana zaune gefen gado xuciyarta fal da tunani kala kala, babban burinta a yanzu bai wuce ta ganta kusa da mahaifiyarta ba, in yaso koma me zai faru daga baya sai ya faru, kallon wayarta tayi taga Safiyyah ce ke kiranta, tun daxu da safe ta kirata amma sbda damuwar da take ciki ko picking bata iya tayi ba, Khaleesat ta daga kiran ta kai kunne, Safiyyah tace "Khalee me yasa baki shigo schl ba yau? Are you okay?" Khaleesat ta sauke boyayyen ajiyar zuciya tace "Ummanmu ce bata da lafiya Sophie" Safiyyah tace "Subhanallah, amma ya jikin yanzu?" Khaleesat tace "Da sauki" Safiyyah tace "To Allah ya bata lafiya, plss nasan ki kar ki sa ma kanki damuwa kawata addu'a kawai zaki dinga mata, nasan kilan kina nan kina ta kuka ko?" Khaleesat dai tayi shiru bata ce komai ba, Safiyyah tace "In sha Allah in mun gama lectures zan taho" Khaleesat tace "I am sorry ban kira ki na gaya maki ba i will be leaving for Nigeria by 3pm" Da mamaki Safiyyah tace "Zaki tafi Nigeria? Abdul ne ya siya maki flight ticket?" Khaleesat ta sauke idonta tace "Uhm" Safiyyah tace "Is it that critical Khaleesat?" Khaleesat tace "To da sauki dai, amma kinsan bazan samu rest of mind ba in ban je ba" Safiyyah tace "To kina airport yanzu ne?" Khaleesat tace "Aa ina jiran Lyft ne yanzu zan tafi" Safiyyah tace "Toh shikenan mu hadu a can kawai sai mu yi sallama, bari in nemi Uber nima" Khaleesat tace "To nagode Sophie" Da haka suka gama wayar, Khaleesat ta mike bayan Lyft dinta ya iso, tana rike da trolley dinta da handbag ta fito daga dakin ta kulle kofa, sanye take da Maroon Abaya sai veil dinta, tana tafiya a hankali ta karaso cikin parlorn, ya ajiye wayar da yake yace "Kin shirya?" Without looking at him tace "Eh" yace "Kin yi ordering ride ai?" Tace "Eh" yace "Ohk" Mikewa yayi ya ciro 1000 Dollars ya mika mata yace "Sort ur self out with this" Girgiza masa kai tayi tace "Aa Nagode" Yace "C'mon, u didn't beg me Halysaah" Ƙin kallonsa tayi kuma taki amsan kudin, ya dau handbag dinta da ta ajiye saman trolley din gabanta ya bude zip din jakar ya sa mata kudin tare da wani farin takarda, ta ɗaga kai tana kallonsa, ya koma ya zauna yace "Allah ya tsare, my regards to ur Mom and everyone back home, Allah ya bata lafiya" Da kyar tace "Ameen nagode" Yace "Zaki ga digit na rubuta maki a takarda, idan kun sauka Airport sai ki kira number kice masa kun sauka" Ta kasa cewa komai, after few seconds ta dau handbag dinta cikin sanyin murya tace "Nagode " Yace "U are welcome, wishing u a Safe trip" Tana jan trolley dinta a hankali ta nufi kofa, tana bude kofar ta fita ta daga kai tana kallonsa taga Idonsa na kan wayarsa da yake dannawa, kulle kofar parlon tayi, taga Lyft din dake jiranta ta nufi wajensa. A Airport Khaleesat suka hadu da Safiyyah, Safiyyah na rike da hannunta tace "Tun yaushe ne Umman bata da lafiya?" Khaleesat tace "Jiya Aunty sha'awa ke gaya min" Safiyyah ta sauke ajiyar zuciya tace "To Allah Ubangiji ya bata lafiya" Khaleesat tace "Ameen" Safiyyah tace "Lallai Abdul ya fara hankali da yayi tunanin biya maki jirgi kije ki duba Umma, nayi mamaki sosai wallahi" Khaleesat ta ɗan yi murmushi da iyakarsa lips, Safiyyah tace "Yanzu kwana nawa za ki yi?" Khaleesat tayi shiru at first, sai kuma tace "Sai dai naje tukunna in sha Allah" Safiyyah tace "Toh Allah ya kai ku lafiya, don Allah ki gaida min Umma da jiki" Safiyyah na fadin haka ta jawo handbag din Khaleesat ta saka mata dala dari tace "Plss manage this kawata" Khaleesat ta ɗan bude baki tace "Haba meye haka Sophie" Sophie bata tsaya ta saurareta ba ta daga mata hannu tana murmushi ta bar ta tsaye wajen, Khaleesat dai ta bi ta da kallo. Khaleesat was more than shock bayan ta amshi boarding pass dinta ganin ticket din Business Class ya siya mata, Business class fa? Kikkifta ido tayi ta sake kallon ticket din sosai to confirm, taga Business class din dai ne still, sosai jikinta yayi sanyi, tana jan kafa da kyar ta shiga jirgin, this is the first time she will be traveling Business class, wata Flight Attendant that gave her all the maximum attention ta yi leading dinta har zuwa Seat dinta a cikin jirgin da fara'a tana welcoming dinta, bayan wani ɗan lokaci jirgin ya tashi, Khaleesat ta ajiye Amenity kit da aka bata ko duba abinda ke ciki bata yi ba tana bin ko ina na Business class din da ido, the Flight from Baltimore Washington International to Amsterdam Schiphol Airport in North Holland for Layover was smooth and comfortable, duk zuwanta Amurka bata taɓa tafiya feeling so comfortable like this ba, bayan few hours aka sauya masu jirgi zuwa Nigeria a nan North Holland, Khaleesat tayi shiru da mamaki jin announcement na cewar Lagos Nigeria jirgin ya nufa, ticket dinta ta sake dubawa taga ashe haka ne a jiki, bayan tafiyar kusan awa bakwai jirgin nasu ya sauka a MMI Airport Lagos. [5/3, 6:15 PM] khaleesat Haiydar ✍️: ✨✨HALYSAAH✨✨ ✍🏻 By _Khaleesat Haiydar_ 6..... Bayan Khaleesat ta dau trolley dinta a cikin airport after going through custom ta tsaya cikin airport din tana tunanin yanda zata yi cause karfe shidda saura ne na asuba, should she check for available flight to Kano? To nawa ne ma a account dinta before she think of doing so, ko dai kawai ta tafi Motor park ta hau mota zuwa kano, dollars din da Housemate dinta ya bata ne ya fado mata a rai don gaba daya ta ma mance, ta bude handbag dinta ta ciro kudin tana kallo, takardan da ya saka mata hade da kudin a jaka ya fadi kasa, ta duka ta dau takardan tana kallon numbers din jiki sai kuma ta mayar cikin jaka tare da Dollars din, masallacin dake cikin Murtala Muhammad International airport ta tafi don yin sallan asuba, tana ta zaune cikin masallacin bayan ta idar da sallah tana azkar dinta, can ta ciro wayarta a handbag ta duba agogo taga karfe bakwai da minti goma, dollars din jakar ta sake cirowa ta kirga taga dala dubu ce, kallon kudin ta dinga yi jiki a sanyaye don bata yi tunanin har haka ya bata ba, ta dau white paper din dake dauke da digit tana tunanin to ko digit dinsa ne wannan din, kati ta siya ta Ussd sannan tayi dialing number a wayarta, sai da ya kusa katsewa aka daga, daga daya side din aka yi sallama ta amsa, amma sai taji kamar ba muryarsa bane, ta dai ce "Ina kwana?" Yace "Hajiya ko kece kika taho daga America?" Tace "Eh" Yace "To barka da isowa Hajiya, ina ta sauraren kiran naki dama tun daxu, kina cikin airport din ne yanzu?" Tace "Eh" Yace "Ohk to gani nan tahowa ba da dadewa ba in sha Allah" Bayan ya katse wayar ta kalli screen dinta, to waye kuma wannan, maida kudin tayi jaka ta ciro nose mask dinta ta saka sannan ta mike ta fito daga Masallacin da trolley dinta with handbag, bayan wasu mintoci sai gashi ya sake kiranta, ta fito outside of the airport, yana hangota ya nufota ya gaisheta da ladabi har da bowing kansa yace "Ya hanya Hajiya?" Ta sauke idonta tace "Lafiya Alhamdulillah" With respect yace "Ga mota can Hajiya, zaki je hotel ki huta zuwa karfe daya na rana don Flight dinki zuwa kano na karfe Biyu ne in sha Allah..." Khaleesat was speechless ta dinga kallonsa babu ko kiftawa cike da mamaki, can kuma ta kalli lafiyayyen motar da ya nuna nata, tuni ya karasa ya amshi trolley dinta ya tafi ya bude booth ya saka, sannan ya bude mata bayan mota yace "Bismillah Hajiya" Sauke idonta tayi kasa taji kafafuwanta sun mata nauyi amma a haka tana tafiya a hankali ta tafi ta shiga back seat sannan ya kulle motar, ya zaga ya shiga driver seat, Hotel me tsada sosai that isn't far away from the airport ya kai ta, sai da ya tabbatar tayi check in har zuwa dakinta sannan ya bar hotel din, tana shiga babu jimawa wata ma'aikaciyar hotel din ta kawo mata lafiyayyen Breakfast, ita dai Khaleesat ba um bare um um, gaba daya kanta ya gama kullewa, tashi tayi ta bude trolley dinta ta dau Shower gel zata yi wanka. Khaleesat na bacci wajen karfe daya da minti ashirin vibration din wayarta ya tasheta, ta jawo wayar a hankali tana duba me kiranta taga mutumin da ya kawota Hotel ne, ta mike zaune sannan tayi picking call din ta kai kunne tayi shiru, daga daya bangaren yayi mata sallama sannan yace "Hajiya fatan kin shirya in taho in dauke ki, flight din naki nan da minti talatin ne in sha Allah" a hankali Khaleesat tace "Toh" Yace "Gani nan tahowa yanzu da izinin Allah" Yana katse wayar Khaleesat ta sauka daga saman gado taje tayi alwala a bandaki, tana idar da sallan Azahar sai ga kiransa, ta dau trolley dinta da handbag ta bar dakin hotel din ta sauko downstairs, yana hangota a Reception din hotel din ya tafi da sauri ya amshi trolley din hannunta, ya karbi makullin dakin ya kai ma Receptionist, sannan suka fita haraban hotel din ya bude mata back seat bayan ya saka trolley dinta a booth, cikin mintuna kadan suka isa MMI Airport, sai da ya tabbatar ta amshi boarding pass dinta sannan yayi mata sallama da murmushi fuskarsa yace "Toh Allah Ubangiji ya tsare Hajiya, idan kun sauka kanon za a karasa dake gida in sha Allah... We will keep in touch" a hankali Khaleesat tace "Toh Nagode, Allah ya saka da alkhairi" Yace "Ameen Hajjaju, nagode kwarai, Allah Ubangiji ya kai ku lafiya" A haka suka rabu ta nufi Departure lounge walking slowly, bayan kusan minti ashirin jirginsu ya tashi zuwa garin kano. Suna sauka kano Khaleesat ta fito daga cikin airport gabanta na faduwa, sai gyara nose mask din fuskarta take tana waige waige, yanzu ina ma ta nufa tukun, tasan ko da wasa bazata nufi gida ba dai, wayarta ya fara ring ta duba da sauri gabanta na ci gaba da faduwa, wata lamba ce ke kiranta tayi picking tayi shiru, taji an mata sallama ta amsa, mutumin ya gaisheta yace "Hajiya Hamisu ne ya aiko min lambarki, naga jirgin ku ya sauka yanzu, yace za a karasa dake gida, kina ta ina yanzu?" Tace "Na fito outside of the airport" Tahowa taga mutumin yayi zuwa inda take tsaye bayan ya hangota, nan ya kai ta har motar dake jiranta, motar shigen wanda ta shiga a Abuja ne, mutumin ya bude mata back seat ta shiga tace "Nagode" Yayi bowing kansa yayi mata sallama yace "Allah ya kai ku lafiya" Tace "Ameen Nagode" Drivern dake mazaunin driver ya gaisheta yana tambayarta ya hanya sannan ya tada motar suka fita daga airport din yace "Ina muka nufa Hajjaju?" Khaleesat ta ɗan yi shiru kamar me nazari, sai kuma tace "Hotoro zaka kai ni" Yace "To Allah ya kai mu lafiya" Suna isa dai dai kofar gidan da ta nuna masa ya tsaya, ya bude motar ya sauka don fiddo mata Trolley dinta a booth, bude motar tayi ita ma ta sauka tana gyara facemask dinta, ta amshi akwatinta a hannunsa sannan tayi masa godiya ta shiga cikin gidan da sauri, Baaba Gaje dake zaune tana tankade garin tuwo ta daga kai tana kallonta, Khaleesat ta ɗan sauke Facemask dinta tana murmushi tace "Baaba sannu da aiki" Baaba Gaje ta ajiye rariyar hannunta tace "Khaleesatu? Daga ina kuma haka?" Khaleesat ta duka nan gabanta har sannan tana ɗan murmushi tace "Makaranta" Baaba Gaje tace "Ikon Allah, to ai ko minti ashirin banyi da dawowa daga gidanku ba kuma ba ace min kina hanya ba" A hankali Khaleesat tace "Baaba ya jikin Ummanmu fa?" Baaba Gaje tace "Kaddai ba a san kin biyo hanya ba kika taho Khaleesatu?" Khaleesat ta gyada mata kai kawai, Baaba Gaje tace "Ikon Allah, to ai jikin nata da sauki er nan, shi Awdul din ne ya biya maki kudin jirgi kika dawo?" Khaleesat ta girgiza kai gabanta na faduwa tace "Bai san na dawo ba Baaba" Baaba Gaje tace "Ikon Allah, to bari in kira Parida, ko kuma ke ki kirata da kanki, Gwara da kika yi dubaran zuwa nan kada Salubabben uban nan naki ya sa ki a bakin duniya mu shiga uku, Ga tabarma taho ki zauna ki huta, irin wannan tafiya me nisa haka, naji ance Amurkan har yapi legas nisa ko? Kira Paridan mu ji yanda za ayi" Khaleesat ta zauna gefenta ta bude handbag ta ciro wayarta, duk da yanda gabanta ke faduwa haka tayi dialing din lambar kanwar Ummanta Aunty Farida, Baaba Gaje tace "Auu to ai Parida ba waya a hannunta wai an sace a mota" Khaleesat ta daga kai tana kallonta, Baaba Gaje tace "Abinda zai faru kawai ga garin tuwon nan ki karasa tankade min ga can murhu na dora ruwan tuwo in yayi ki min talgi ki tuka tuwon in ya silala ki kwashe, ga kuma kayan miya can bai dai da yawa ki jajjaga ki kada min miyar kuka, ni kuma sai in koma can Mariri yanzu in sanar ma Ummanku kin zo" Khaleesat tace "Toh Baaba" Mikewa Baaba Gaje tayi ta figi yakunennen gyalenta a igiyar shanyan dake ɗan karamin tsakar gidan ta yafa tace "Bara inje, dama ina da canjina dari da hansin sai in roke masu ɗan sahu su kai ni ko Farawa ne sai in karasa Maririn da kafa ta" Khaleesat ta bude handbag dinta amma sai taga Dollars kawai, ta daga kai ta kalli Baaba Gaje tace "Wallahi bani da kudin Nigeria a nan Baaba, amma bari in ciro a POS yanzu sai in baki kudin adaidaita sahun" Baaba Gaje tace "Aa yi zamanki kiyi aikin da na sa ki, minti nawa ne nan da Mariri, kawai dai ga wanke wanke can bakin kwararo ki wanke min har su, ki share tsakar gidan nan, in yaran nan suka dawo islamiyya ki dauraye masu Uniform dinsu, dakin ma na nan sunyi kaca kaca da shi babu kyan gani" Daga haka ta fice daga cikin gidan bayan ta saka slippers dinta, Khaleesat ta cire mayafin abayan jikinta ta dora kan akwatinta sannan ta ci gaba da tankaden da Baaba Gaje ta bar mata, Baaba Gaje makociyarsu ce a can unguwansu Mariri kafin 'ya yanta su siya mata wani ɗan kararramin gida a nan Hotoro Tsamiyar boka ta dawo tana zaune da jikokinta biyar tana dubasu, zaman mutunci da amana Baaba Gaje suka yi da Mahaifiyar Khaleesat da ta dauki Gajen tamkar uwa. Wajen karfe shidda saura Khaleesat ta gama duk aikin da Gaje ta loda mata sannan ta dora ruwan da zata yi wanka a sauran rushi, zaunawa tayi kan tabarma ta jingina da bango don ta gaji likis, Housemate dinta ne ya fado mata, ta dai yi shiru staring into space, after a while ta sauke idonta a hankali ta mike ta shiga da kwanukan da ta wanke cikin dakin Gaje, dai dai nan Gaje ta shigo cikin gidan da Aunty Farida, Khaleesat ta tafi da gudu ta rungume Aunty Farida cike da murnan ganinta, Aunty Farida na kallonta tace "Ke kuma da wa kika yi shawara kika biyo hanya Khaleesah? Abdul din ne yace ki taho?" Gaje ta daga hannu sama da sauri tace "Aaaa tace bai ma sani ba" Aunty Farida na kallon Khaleesat da mamaki tace "Ban gane bai sani ba??" Khaleesat ta marairaice ta kauda zancen ta hanyar cewa "Aunty ya jikin Ummanmu?" Aunty Farida ta kamo hannunta suka zauna saman tabarma tace "Ai jikin Umma da sauki sosai Khaleesat, gashi har an sallamemu a asibiti, wa yace maki bata da lafiya ne ma tukun?" Khaleesat da har hawaye ya ciko idonta tace "Aunty Sha'awa" Gaje tace "Lahh ha ila, wato Sha'awa bazata dena munafurci ba ko? Wato bazata canxa hali ba ko? Da kaina fa sai da na jaddada mata kar ta gaya maki ko kin mata sako ta wassol don kar hankalinki ya tashi, ashe sai da munafukar ta zaga ta fada maki" Aunty Farida tace "Toh Allah ya kyauta, kwata kwata Sha'awa bazata canza ba" Khaleesat da hawaye ke cika idonta tace "To Aunty ta yaya zan ga Ummanmu yanzu?" Aunty Farida tace "Kar ki damu kiyi zaman ki nan wajen Baaba Gaje, gobe da safe in za mu tafi asibiti sai mu fara biyowa ta nan da Umman tunda asibitin Malam Aminu kano ne" A hankali Khaleesat tace "Toh Allah ya kai mu Aunty" Sai bayan Magrib Aunty Farida ta bar gidan bayan ta ci tuwon da Khaleesat tayi ma Gaje, sosai Khaleesat taji ta samu rest of mind bayan taji jikin Ummanta da sauki, bayan Isha Gaje ta gyara mata ɗan lungun da zata kwanta a dakin ta daura mata net din sauro tace "Allah dai ya rabaki da cinnaku" ita dai Khaleesat tayi murmushi kawai bata ce komai ba, ita matsalarta ma zafi, ko ya zata yi da zafi yau gashi karamin dakin wani ɗan mitsitsin window ne kawai ke garesa, su bakwai kuma zasu kwana a ciki, Khaleesat ta gama shirin kwanciya don tayi wanka sannan ta shiga net din ta kwanta, ta amshi maficin da gaje ke mika mata ta cikin net din, tun dawowarta sai a sannan tayi subscription ta shiga WhatsApp dinta, Message din Safiyyah dake tambayarta ko ta isa lafiya kadai tayi ma reply, bata yi mamakin rashin ganin message din Abdul ba don she isn't even expecting his message, ajiye wayar tayi ta gyara kwanciyarta ta lumshe ido, Housemate dinta ne ya fado mata, she have no access to him balle ko godiya ma tayi masa, bata yi tunanin da ta fito zata tafi airport bazai tambayeta phone number dinta ba, ko Airport din ma bata yi tunanin bazai yi offering yace zai kai ta ba, juye juye kawai take yi a net din idonta a rufe, after a while of thinking bacci ya dauketa. Washegari Khaleesat ta gama yi ma Baaba Gaje duk aikace aikacen gidan, ta hura gawayi ta daura ruwa tayi ma kananun jikokinta wanka sannan ta dama kunu, Baaba Gaje ta fita siyo masu kosai a titi, har karfe goma Khaleesat bata ga Aunty Farida sun zo gidan da Ummanta ba, gaba daya ta damu taga Ummanta, Baaba Gaje tace "To ke sai ruwan ya salance zaki je kiyi wankan? Ba fa wani gawayin" Khaleesat tace "Zan yi" Daga haka ta mike ta tafi yin wankan, tana fitowa daga wanka taga takalmin da Aunty Farida ta zo da shi jiya a bakin kofa da wani takalmin daban wanda ko ba a fada ba tasan na Ummanta ne, da sauri ta shiga dakin Baaba Gaje taga Ummanta da Aunty Farida a zaune, tsallake Aunty Farida tayi ta tafi gun Ummanta da gudu cike da farin cikin ganinta ta durkusa gabanta ta rungumeta, Aunty Farida tace "Ko dai baki da hankali ne?" Baaba Gaje tace "Toh da sauki dai kam" Ita dai Umman sai kallon Khaleesat take, gaba daya Khaleesat ta ma mance wai Umma bata da lafiya tsabar farin cikin ganinta, a hankali Umma tace "Meyasa zaki biyo hanya Khaleesah? Abdul din ne yace ki dawo?" Khaleesat ta kamo hannunta cike da damuwa tace "Umma ya jikin?" Umma tace "Naji sauki Alhamdulillah" Khaleesat tace "Aunty Sha'awa tace min ko magana fa baki yi" Baaba Gaje ta rike haɓa tace "Oh ni 'ya su, kun ji er iska ko? Wallahi Sha'awa da kyar taga annabi, babu yanda bamu yi da ita ko da wasa kar ta gaya maki ba ashe sai da ta zaga ta fada, har ce mata nayi tace maki tayi tafiya ko da zaki buga nata wassol" Khaleesat ta daga kai ta kalli Baaba Gaje tace "Ni ce na kirata don ina ta magana bata min reply ba" Aunty Farida tace "Ai tsabar munafurci yasa ta gaya maki ba wani abu ba" Khaleesat ta ɗan yi murmushi ta gaida Aunty Farida, Aunty Farida ta amsa tace "Amma shi Abdul yasan Umma bata da lafiya shine ko kira ya dubata bai yi ba?" Khaleesat ta sauke idonta kasa tace "Ni fa bai san na dawo ba Aunty" Aunty Farida tace "Wai ban gane bai san kin dawo ba, wa ya biya maki kudin jirgin?" Khaleesat ta daga manyan idanuwanta tana kallonsu, Sai kuma a hankali tace "Wani ne ya biya min ba Abdul ba" Umma ta kalleta da sauri tace "Wani?" Da mamaki Aunty Farida tace "Wani a ina?" Khaleesat na kokarin mikewa tace "Neighbor dina ne" Umma ta bude baki tana kallonta, sai kuma tace "Ko baki da hankali ne, waye ya biya maki kudin jirgi Khaleesah?" Khaleesat tayi shiru bata ce komai ba, Gaje tace "Bude baki zaki yi ki mana bayani dalla dalla, waye shi zai biya maki zunzurutun kudi na jirgin da naji ance ya fi miliyan daya? A ina kika san sa?" Still dai Khaleesat taki cewa komai, Aunty Farida tace "Ke bana son rainin wayo uban wa zaki ma shiru ana maki magana? Ko baki ji tambayar da ake maki bane?" Umma dai kallon Khaleesat kawai take da mamaki, Khaleesat ta koma baya ta ɗan sunkuyar da kanta a hankali tace "Ni fa nace makocina ne ya biya min, kuma ai gani yayi ina ta kuka Ummana bata da lafiya shine ya biya min jirgi in dawo in dubota" Cikin sanyin murya ta kare maganar, Baaba Gaje tace "Atoh dama ai ko ina ana samun na Allah, Allah ya masa albarka, Bature ne ko?" A takaice Khaleesat tace "Um" don bata son ma a ci gaba da zancen, Baaba Gaje tace "Ko da naji, ai sai baturen dama, wani baƙin fata ne zai biya maki jirgi don yana makocinki, ai ko mutuwa uwar taki tayi iyaka ya maki gaisuwa ya kama gabansa, to Allah ya saka masa da alkhairi, abinda ma baturen kudin jirgin ba wani kudi bane a wajensa, ji zai yi kamar naira dubu goma ya kashe fa" Khaleesat na kallon Aunty Farida tace "Aunty yanzu za aje asibitin ne?" Aunty Farida tace "Aa mu har mun dawo daga asibiti sai kuma na gobe in Allah ya kai mu" a hankali Umma tace "Toh da ya biya maki kudin jirgin zuwa wa zai maki na komawa yanzu? Kinsan dai ko hauka kike baza ki bari Abdul yaji wannan batun ba ki ja mana masifa ko?" Sai da gaban Khaleesat ya fadi, a hankali ta sunkuyar da kanta, ita gaba daya ta ma mance ashe biyan jirgi za ayi a koma, nan da nan jikinta yayi mugun sanyi, yanzu ina zata samu kudin ticket din komawa, she became so weak at once, Aunty Farida tace "Toh shi Abdul din baki ce masa Umma bata da lafiya bane?" Khaleesat da har sannan jikinta yake a sanyaye ta girgiza kai tace "Baya nan ne" Daga haka ta mike ta tafi zata shirya don zanin da tayi wanka ne daure jikinta har a lkcn, Khaleesat na cikin saka kayanta da ta fiddo a akwati 1000 dollar din da Housemate dinta ya bata suka fado mata a rai, ta zaro ido lkci daya taji hankalinta ya kwanta har sai da ta sauke ajiyar zuciya, tasan probably in ta canza har da 100 dollar din da Safiyyah ta bata kudaden za su iya maidata Amurka, she felt so relieved, nan da nan walwalarta ya dawo, tana jin Baaba Gaje na tambayar Aunty Farida ko kishiyoyin Ummanta sun shiga dubata yau, Aunty Farida tace "Jiya ma basu shigo dubata ba sai yau Baaba Gaje" Baaba Gaje tace "Shegu matsiyata, so fa suka yi ace ta mutu, to shi Malam Alin ya ku ka ƙarke da shi? Ya bada kudin?" Aunty Farida tace "Aa ni fa ban bi ta kansa ba Baaba Gaje, dama me ya tsinana kafin in zo kanon? daxu ma aka turo min sauran kudin adashina da nake jira, duk na siya sauran magungunan" Baaba Gaje tace "Atoh dai bai taɓuka komai ba a takaice, shi ma da zaki basa yanxu tsaf zai amshe" Har aka yi azahar su Umma da Aunty Farida na gidan, Umma har tayi bacci ta tashi saboda maganin da take sha, har a sannan da kyar take taka kafarta daya, hannunta dai ya sake ya dawo normal tun a jiya, Khaleesat ta shigo dakin da shinkafa da waken da ta dafa, Baaba Gaje kuma ta shiga makota dubiya, Aunty Farida dai sai bin Khaleesat take da kallo, sosai taga ta kara kyau tayi fresh, duk da dai tana nan a yanda take babu kiba, komawa tsakar gida Khaleesat tayi ta dauko man gyadan da ta soya ta dawo dakin, ta fara zuba ma Umma da Aunty Farida abincin, Umma dake zaune kan darduma tana kallonta tace "Kun fara jarabawan ne?" Aunty Farida tace "Haba dai sun fara jarabawa zata taho? Ai bazai yiwu ba, ko ana haka ne?" Khaleesat dake sauraronsu ta girgiza kai tana ɗan murmushi tace "Da sauran lokaci bamu fara ba tukun" Aunty Farida tace "To yanzu dai tun kan wani munafukin yasan kina garin nan mu shiga uku yaushe za ki koma Khaleesah?" Khaleesat ta daga kai a hankali tace "Cikin satin nan in sha Allah" Aunty Farida tace "Toh inji dai Abdul din ya rage abubuwan nan nasa da yake maki?" Khaleesat ta ajiye masu abincin a gabansu kamar bazata ce komai ba sai kuma tace "Babu abinda ya fasa, ni na gaji da halinsa ma yanzu" Umma ta daga kai tana kallonta, Aunty Farida ma kallonta take don bata taɓa cewa ta gaji da halin Abdul ba, Aunty Farida ta sauke ajiyar zuciya ta fara cin abincin gabanta tace "Na dai gaya maki babu me canza maki shi sai ke da kanki, ke macece ya kamata ace zuwa yanzu kinsan wanene Abdul kinsan kuma yanda zaki zauna da shi" Mikewa Khaleesat tayi without saying anything don ita yanzu taji ko zancen nasa ma bata so har cikin ranta, tun shekaranjiya da yayi fushi har yau bai kirata ba ita kuma as far as tayi masa miss calls har biyu to bata ji zata iya sake kiransa ba unlike before da ta dinga kiransa kenan ko da bazai daga ba, ko kuma tayi ta masa magana ta WhatsApp, to yanzu kam bata ji zata iya ba..... ✍🏻 07087865788 *Still on free pages* [5/4, 8:14 PM] khaleesat Haiydar ✍️: ✨✨HALYSAAH✨✨ ✍🏻 By _Khaleesat Haiydar_ 7..... Kwanan Khaleesat hudu yau a garin kano, kuma har a sannan babu wanda yasan da zuwanta a cikin yan gidansu, ko nan da can bata fita a gidan Baaba Gaje don ma kar tsautsayi ya sa ta hadu da daya daga cikin yan gidan nasu, a kwanaki hudun nan sau biyu Ummanta da Aunty Farida suka zo gidan Baaba Gaje dominta, zuwa sannan Umma ta warware gaba daya tafiyarta ya dawo normal, tun kwanaki biyu da suka wuce ta gama amsan treatment dinta a hospital sai magunguna da take sha kawai, har zuwa ranan kuma Abdul bai kira Khaleesat ba, ita kuwa kawai taji ko a jikinta da ya kira da kar ya kira, there wasn't an atom of disturbance a tattare da ita, ko ta WhatsApp bata yi gigin yi masa magana ba Unlike before da bazata iya hakuri ba sai ta masa, tana bakin murhu tana dafa shinkafa da wake ga turmi gabanta tana ɗaka yajin da za ayi amfani da shi wajen cin shinkafa da waken, Su Ummanta da Baaba Gaje kuma na can uwar ɗaka, tunanin yanda zata fara shirye shiryen komawa USA take don suna da wani presentation nan da kwana uku, daxu da safe ta duba available flight da farashinsu online and she is hoping in ta canza dollars din da Housemate dinta ya bata zai isheta ta koma, Khaleesat ta bar daƙan yajin da take yi bayan taji Aunty Farida na kwalo mata kira, mikewa tayi ta wuce dakin tana amsawa, tun da ta zo gidan Baaba Gaje ta sakar mata aikin komai, hatta jikokinta ita ke masu wanka kan su tafi makaranta, ita taga kamar har ta ɗan yi duhu tsabar girki cikin rana da take yi tun zuwanta, Aunty Farida tace "Ana kiran wayarki" nan da nan mood din Khaleesat ya canza ta karasa gun wayar without much interest, duk tunaninta Abdul ne cause she isn't expecting any call from anybody, Number mutumin da ya tarbeta a Airport din Lagos ta gani a gaban Screen din wayarta, ta dinga kallon number bata ko kiftawa, duk da bata yi saving ba amma ta gane nasa ne, daukar wayar tayi ta fita daga dakin ta koma bakin murhun sannan tayi picking ta kai kunne, sallama yayi ya gaisheta da ladabi, tace "Ina yini?" Yace "Alhamdulillahi Hajiya, ya jama'ar gidan?" Tace "Alhamdulillah" Yace "To maa sha Allah, dama na bugo ne inji ko zaki kara kwanaki nawa nan gaba kan ki koma America?" Khaleesat tayi shiru trying to understand why he is asking her that, yace "Hello?" Tace "Ina jin ka, ban gane tambayar bane" Calmly yace "Aa so nake in san ranan da zaki koma ne Hajiya, in ya kama ayi rescheduling din ticket dinki sai ayi hakan in sha Allah" Khaleesat was speechless, a ranta tace Ticket kuma? Kasa cewa komai tayi with surprise, taji ta ma kasa ci gaba da tsayuwa, jin ya sake cewa "Hello" ta kifta ido da kyar ta duka kusa da turmin da take daka yaji tace "Ina ji" Yace "Ina ga a bari duk sanda kika shirya zaki nemeni ta waya ko Hajiya?" Sauke idonta tayi kasa, lokaci daya jikinta yayi sanyi sosai, cikin sanyayyen murya tace "Ranan Lahadi nake son zan koma idan Allah ya yarda" Yace "To Maa sha Allah, dama booking din ranan aka maki da zaki taho, flight din karfe daya ne, za ku tashi ta Airport din Abuja in sha Allah" Ita dai Khaleesat ta kasa cewa komai, yace "Sai kin ji ni in sha Allah Hajiya" A hankali Khaleesat tace "Nagode" Khaleesat na zaune dakin Baaba Gaje tana jujjuya shinkafa da waken dake gabanta da cokali, gaba daya ta kasa cin abincin, ita kanta ta rasa dalili, ko tsabar yanda jikinta yayi sanyi ne tun bayan da suka yi waya da mutumin daxu da ya sanar mata da ticket dinta na komawa America sannan tana gama aikin da take ta bude WhatsApp taga ya aiko mata da Flight Ticket dinta which was also business Class kamar dai yanda ta zo, this made her so weak, gaba daya ta ma rasa gane feeling din dake ranta a lokacin, bata taba tunanin Housemate din nata zai mata ticket din komawa ba, Duk Ummanta na lura da sauyawanta lkci guda, Aunty Farida ta gama shafa powder din da take zata leka gidan wata kawarta Maman Fu'ad a nan hotoron, ta dau jakarta da mayafi tana kallon yayarta tace "To sai na dawo Umma" Umma tace "Amma kar ki dade don Allah Farida" Aunty Farida tace "Haba ai yamma tayi bazan zauna ba Umma" Daga haka ta fita daga dakin tayi ma Baaba Gaje dake waje tare da bakuwarta sallama sannan ta fita daga gidan, Umma ta daga kai tana kallon Khaleesat tace "Menene kika saka abinci a gaba kika kasa ci Khaleesat?" Khaleesat ta daga kai da sauri tana kallon kyakkyawan fuskar Ummanta, babu wanda zai ce Umma ce ta haifeta sai dai ma yayi tunanin yayarta ce don kama suke ba na wasa ba kamar an tsaga ƙara, Khaleesat tayi murmushin yake ta kai shinkafa da waken baki tace "Babu komai fa Umma" Umma tace "Yaushe za ki koma? Kuma yaya za ayi da batun kudin jirgi? Har yanzu Abdul din bai san kina nan ba?" Khaleesat ta girgiza kai tace "Umma ai nace baya nan kuma ba a samunsa ta waya, ranan lahadi zan koma in sha Allah" Umma tace "Ranan Lahadi? To ina za ki samu kudin komawa?" Khaleesat ta gyara zamanta tace "Makocin nawa ai tare ya biya min na zuwa da dawowa" Kallonta Umma ta dinga yi da alamar tuhuma ga mamaki kwance fuskarta, Khaleesat taki yarda ta bari su hada ido sai tura abincin gabanta take, Umma tace "Khaleesah" Da kyar Khaleesat ta daga kai gabanta na faduwa, Umma tace "Meye tsakaninki da wannan mutumi da ya biya maki kudin jirgin zuwa har da na komawa?" Khaleesat ta hadiye sauran shinkafar da ya makale a throat dinta da kyar tace "Wallahi Umma babu komai, makocina ne kawai shi, kuma don yaga yanda na daga hankali baki da lafiya shi ne yasa yayi hakan, ni kaina sai bayan da ya biya min na sani, amma ki yarda dani Umma babu komai tsakanina da shi" Kamar zata yi kuka ta kare maganar, Ummanta ta sauke ajiyar zuciya tayi shiru, bayan some seconds tace "Toh shikenan, amma dai kinsan in Abdul ya samu labarin nan da matsala ko?" Khaleesat ta sunkuyar da kanta bata sake cewa komai ba, jin Umma tayi shiru alamar ta fada duniyar tunani Khaleesat ta daga kai a hankali tace "To ai Umma babu wanda yasan na zo kano har yanzu, don haka bazai sani ba" Umma ta sauke wani ajiyar zuciyar tace "To gudun kada hakan ya sake faruwa kar ki sake yarda ko wata mu'amula ta hadaki da shi makocin naki Khaleesat, ki rufa mana asiri" Khaleesat bata ce komai ba sai kuma ta jawo handbag dinta ta ciro dala dubu dayan da Housemate dinta ya bata ta nuna ma Umma cikin sanyin murya tace "Wannan ma shi ya bani da zan taho" Umma ta dinga kallon kudin duk da bata san ko nawa bane ta dai ce "Ki kula don Allah Khaleesat kar ki ja mana magana kin dai san wanene Abdul kin san kuma waye Babanki" Khaleesat dai tayi shiru, tasan Umma bata san har nawa bane Dollars din in an canza zuwa Naira, ita dai tayi shiru bata gaya mata ba kar ta kara daga mata hankali. Washegari da wuri Khaleesat ta shirya ta saka Nikab dinta ta fita don zata je canza dollar din nata ta dan yi siyayya, bayan ta canza dalolin taga har ya wuce yanda take tunani a Naira, nan ta fara zuwa inda zata siyi waya, ta siya ma Ummanta da Aunty Farida sabbin wayar Android iri daya na dubu dari da hamsin each, Ganin Baaba Gaje ma bata da waya kuma ba iya amfani da Android zata yi ba ta siya mata karamar waya na dubu ashirin, daga nan ta karasa kasuwa tayi siyayyar yan abubuwan da zata koma USA da shi, ta siya ma siblings dinta twins mata sabbin school bag da schl shoe da socks, ta siya masu atamfofi kala uku each da mayafai da takalma masu kyau da inner wears, jikokin Baaba Gaje ma ta siya masu takalma da inner wears gaba dayansu, pharmacy ta shiga da takardan da aka rubuta magungunan Ummanta ta siya mata na wata biyu duk da tsadar magungunan, kusan Azahar ta koma gidan Baaba Gaje ta tarar su Ummanta basu zo ba. Washegari asabar Khaleesat na shanya kayan jikokin Baaba Gaje da ta wanke, Baaba Gaje kuma na shirin fita kasuwa Ummanta suka shigo gidan tare da Aunty Farida da Siblings dinta yan biyu Islam da Noor that are just 11 years old, da gudu suka tafi suka rungumeta suna mata oyoyo, sosai kannin nata ke kama da ita, Khaleesat was so happy seeing her twins Siblings wanda su uku kawai Ummansu ta haifa, Baaba Gaje tace "Basu tafi islamiyya bane?" Umma tayi kasa da murya tana kallon Gaje tace "Sun ma kwana biyu rabonsu da zuwa, ba a biya kudin wata ba" Baaba Gaje tace "Ikon Allah to Alin ca yayi bazai biya ba kenan?" Umma tace "Cewa yayi in dora masu talla kamar yanda yan uwansu ke yi tunda su ba 'ya yan Gwal bane, dama ba fa shi ke biya masu ba wannan karan ne bani da kudi duk jarin ya lalace shine nace su tambayesa" Baaba Gaje tace "To Allah ya kyauta, amma Ali dai haƙƙin 'ya ya da kyar ya bari ya jiyo kamshin aljanna balle yaje kusa da ita" Ita dai Khaleesat a sanyaye ta kama hannun kannin nata zuwa dakin Baaba Gaje, tana jin Baaba Gaje na cewa "Amma de suna zuwa bokon?" Umma ta sauke ajiyar zuciya tace "Ina fa, islamiyya ma da ya zama dole ba aje ba sae wani boko" Aunty Farida ta girgiza kai cike da takaici tace "Allah de ya kyauta, shi fa bakin cikin bata dora ma yaran talla kamar yanda sauran matansa ke dora ma nasu 'ya yan talla ba yake" Sosai jikin Khaleesat yayi sanyi don duk sanda ta tambayi Ummanta ko kannen nata na zuwa boko da Islamiyya ta wayar Sha'awa sai tace mata eh suna zuwa, ashe basa zuwa, Umma dai bata ce komai ba suka shiga dakin gaba daya, Baaba Gaje tace "Kun ga bari inje kasuwa in dawo" Su Umma suka mata Allah ya kiyaye ta figi gyalenta ta fita daga gidan, Khaleesat ta fiddo duk siyayyan da tayi jiya, daga Ummanta har Aunty Farida kallonta suka tsaya yi, Aunty Farida ta rike haɓa tace "Haka kudin suke da yawa da kika canza? Kuma wa ya aike ki kashe kudi haka mu da muke da sabga a gabanmu Khaleesat? Maimakon ki bada a ajiye maki ko kujeru da setin gado ne da kudaden? Kin de san ko tsintsiya mahaifinki ba lallai ya siya maki da sunan a kai ki dakinki da shi ba ko?" Khaleesat tayi murmushin karfin hali bata ce komai ba, Umma dai ta ma rasa abun cewa, Aunty Farida tace "Ni da kin yi shawara da ni duk baza ki yi wannan siyayyan ba, iyaka ki siyi abinda zaki koma can Amurka da shi, in suka tado da maganar aure me garemu da za a kai ki da shi Khaleesah?" Khaleesat na murmushi tace "Allah zai rufa asiri zuwa sannan Aunty" Aunty Farida tace "Yanzu duk kudin sun kare kenan?" Khaleesat ta girgiza kai tace "Aa, saura dubu dari biyar" Daga Aunty Farida har Umma bude ido suka yi sosai suna kallonta with shock, Aunty Farida ta gyara zama tana zaro ido tace "Har nawa ya baki haka? Ko dai baki da hankali ne" Khaleesat ta kauda zancen ta hanyar cewa "Har fa da kudadena duk na canxa" handbag dinta ta jawo ta bude ta ciro sauran kudaden da suka rage don har wanda Safiyyah ta bata ta canza, ta kirga dubu dari a ciki ta ware, sannan ta kirga dubu dari da hamsin shi ma ta ware, kallonta kawai Umma da Aunty Farida suke, ta ba Aunty Farida dubu dari tace "Aunty kiyi kudin mota da wannan idan zaki koma Lagos sannan ki kara jari" Ta ajiye ma Umma 150k tace "Umma ki rike wannan a biya kudin makarantar su islam da Noor a kuma canza masu Uniform" Umma tace "Ko dai baki da hankali ne Khaleesah? baki ji shawaran da Farida ta kawo bane halan?" Aunty Farida ta mayar mata da 100k din tace "Aa gaskiya ban ga alamar da kan nan ba Umma, ina ga hakoranmu za mu je mu jera mata a gida idan bikin ya tashi...." Khaleesat bata san sanda tayi dariya ba tace "Akwai fa kudade a account dina wanda Abdul ke bani kuma suna da yawa za su isa ayi duk abinda za ayi sannan Aunty" It took Khaleesat almost an eternity to convince her Mother and aunt akan su rike kudin da ta basu, nan kuma bata da wani kudin a zo a gani a account dinta sai miliyan 10 na Abdul da ya ajiye a account din wanda nashi ne ba nata ba, iya kudin foodstuff kawai yake tura mata duk karshen wata sai kuma kudin Uber na zuwa makaranta, sai house rent dinta da yake biya at due time, iya abinda kawai yake mata kenan amma naira biyar dinsa baya bata a matsayin kyauta, instead sai dai ya siya mata kaya masu tsada, monthly kuma yake mata subscription a waya, apart from this bai bata kudi da sunan kudin kashewa, a haka dai ta samu tayi convincing Umma da Aunty Farida suka amshi kudin da ta basu, Aunty Farida na kallon Umma tace "To kinga sai kiyi kaffa kaffa da wayar nan kar su sace maki tunda sun saba maki haka, kin dai ga ba dan karamin kudi aka siyo wayar da shi ba" Umma na kallon Khaleesat tace "To shi Malam din me kika siya masa?" Aunty Farida ta wani kalli yayarta, Khaleesat ma dai kallon Ummanta tayi bata ce komai ba, Aunty Farida ta kyabe baki ta kauda kai, Umma ta kalli Aunty Farida tace "Wai saboda hakki, naga ta siya min waya shima da sai ta nemi abinda ta siya masa kwatankwacin wayar, kuma bashi da wayar shi ma wallahi" Aunty Farida na kallon yayarta da kyau tace "Umma in kinsan zuwa za kiyi ki kyautar da wayar nan da ta siya maki to gwara dai ki bar mata kayanta, ina ce kwanaki can matansa ya siya ma Atamfa yar gadagalle lkcn bikin Salisu ke ya siya maki?" Umma tace "Aa ba ruwanta da wannan Farida, ai ubanta ne, kuma don ta siyi abu ta basa ai ba faduwa tayi ba" Aunty Farida bata sake tanka Umma ba ta fara harhada ma Khaleesat kayayyakin abinci da ta siyo waje daya, Sai kusan la'asar su Umma suka bar gidan kuma har sannan Baaba Gaje bata dawo ba, a boye Khaleesat ta ba Siblings dinta 50k wanda ta saka a karamin jakar Islam tace masu in sun je gida su ba Umma kuma ta ja masu kunni sosai kan daukan sabon wayar da ta siya ma Umma kar su lalata mata. Washegari da safe Khaleesat ta fito wanka wayarta ya fara ring tana dauka taga mutumin nan ne dai, bayan ta daga suka gaisa sannan yace "Hajiya nan da karfe tara da rabi wani driver zai kiraki sai kiyi masa kwatancen inda zai zo ya daukeki ya kai ki airport, don flight dinki zuwa Abuja na karfe sha daya ne, in kun iso Abuja kuma jirgin da zaki bi zuwa Amurka jirgin karfe biyu saura ne" Khaleesat tace "To ba damuwa Nagode" Aunty Farida kadai ce ta zo gidan Baaba Gaje yi ma Khaleesat sallama, Khaleesat bata ji dadin da Umma bata biyo ta ba, duk jikinta yayi sanyi sosai, a haka drivern da zai kai ta airport ya iso, Baaba Gaje ta dinga sa mata albarkan wayar da ta siya mata da abubuwan da ta siyo ma jikokinta, bayan an kai akwatin kayanta cikin mota su Aunty Farida da Baaba Gaje suka rakata har bakin motar, bayan Khaleesat ta shiga motar ta daga masu hannu a sanyaye tana murmushin karfin hali, har cikin ranta bata ji dadin da bata yi sallama da Ummanta ba, a haka suka kama hanyar airport da drivern da ya zo daukarta, suna sauka Abuja karfe daya da minti 40 jirgin su ya tashi. The flight to the United state was so comfortable for Khaleesat in her business class seat, don throughout bacci tayi, karfe hudu saura na asuba jirginsu ya sauka Maryland, It was soo cold in Maryland gashi bata da sweater a kayanta, bayan ta fito da luggages dinta tana duba Uber da zai kai ta gida tana rike da wayar kamar ance ta daga kai taga motar da yayi parking, kallo daya tayi masa sai kuma ta sauke kai kasa, ya karaso har inda take yace "Jirgin ya dade da sauka ne?" Sai a sannan ta kara kallon Sleepy face dinsa, sai kuma ta girgiza kai tace "Aa" Yace "Ohk let me drop you home" Daga haka ya koma gun motarsa ta bi bayansa with both of her luggages, ya bude booth ya amshi daya trolley dinta ya sa a booth, ita ma ta sa dayan, ya zaga ya shiga driver seat, tana jan kafa ta karasa front seat ta bude motar sannan ta shiga tana kallonsa da gefen ido, jinginar da kansa taga yayi da kujeran motar idonsa a lumshe, ta kulle motar gently, after few seconds ta sake kallonsa ga mamakinta sai taga kamar fa bacci yake, kallonsa ta dinga yi, and they seated for almost 3 minutes a haka ita dai bata tashesa ba kuma bata ce komai ba, Vibration din wayarta ne ya sa ya bude ido, ya wara ido ya fara kokarin tada motar, bude jakarta tayi to stop the alarm din da ya sa wayarta ke vibrate, bayan ya ja motar sun bar wajen, still not sounding normal yace "Ya jikin Mama?" Ta sauke idonta tace "Alhamdulillah, You shouldn't have bothered coming tunda akwai Lyft ko Uber" Without looking at her yace "The house key is with me, shi yasa na taho, cause i estimated when u are arriving" Bata sake ce masa komai ba shi ma haka, a haka har suka iso gida yayi parking, ya sake jinginar da kansa da kujeran motar, ita dai ta bude motar gently ta fita, jin fitarta ya sa ya bude ido, shi ma ya sauka daga motar, Entrance din shiga gidan ya nufa ta bi bayansa, Pajamas ne jikinsa sai Jacket da ya saka saboda sanyi, yana isa kofar ya kai hannu aljihu alamar zai ciro makulli, still taga yayi a bakin kofar, ita dai kallonsa kawai take, after some seconds ya juya yana kallonta, zuwa sannan his eyes are very clear gaba daya baccin ya gudu jin babu makulli jikinsa, ko bai gaya mata ba ta fahimci baya tare da makullin gidan, ya ɗan sosa kai yace "I think.... I think, i left the key at where i am coming from, i am sorry about that Halysaah" Sauke idonta tayi without saying anything, ya juya ya nufi motarsa ta bi sa da kallo, sai da ya isa gun motar ya juyo, da sauri ta dauke kanta daga kallonsa, yace "Mu je in dauko makullin, ba wani nisa zuwa can, kinga it's cold out here baza ki iya tsayawa cikin sanyi ki jirani in dawo ba" Bata yi musu ba ta koma gun motar don yanzun ma sanyin take ji sosai, sai da ya shiga sannan ita ma ta shiga, his car was so warm, ya tada motar suka bar garage din, inda yace mata babu wani nisa taga sunyi tafiyar kusan 15 mins basu kai ba, nan taji gabanta ya fara faduwa, lkci lkci take ɗan satan kallonsa ta gefen ido, wani unguwa suka shigo wanda ko wani gida da gate dinsa unlike some houses in US, daga karshe taga yayi parking ba tare da ya kashe motar ba yace "Let me get the keys" Bude motar yayi ya sauka ta bi sa da kallo taga gate din kusa da su ya bude ya shiga, tsaf take iya kallon hadadden gidan dake ta cikin gate din don ba irin gate dinmu na gida bane, ita dai sai bin unguwan take da kallo wanda ko ba a fada maka ba kasan na masu hannu da shuni ne a Amurka din, ba a wani dau lokaci ba sai gashi ya fito da wani Huge Dog dake biye da shi yana shisshige masa, wani faduwa gabanta yayi don a duniya tana mugun tsoron kare, ya duka yana patting Dog din yana masa magana at the same time, wani matashi ne dogo just like him ya fito daga cikin gate din gidan sanye da Pajamas shi ma, Khaleesat ta dinga kallonsa as if ta taɓa saninsa amma kuma bata san sa from anywhere ba, tana kallonsa tana gyara mayafin kanta kar ma ya kalli direction dinta su hada ido da shi, gabanta kuwa sai faduwa yake kamar mara gaskiya, matashin ya jingina da gate crossing his both legs yana kallon Housemate dinta taji yace "Daga ina kake?" Ƙin basa amsa Housemate din nata yayi instead ya mike yana tura masa ƙaton karen don karen tsaf zai ce zai bi sa, Calmly matashin yace "Ina za ka?" Housemate dinta ya kallesa yace "You have any issue with that?" Matashin ya ɗan kalli motarsa calmly yace "Is that a lady in ur Car?" Housemate dinta yayi kamar bai ji sa ba still pushing the Dog to him, Matashin ya sake kallon motar, Khaleesat tayi saurin kauda kanta, tabe baki yayi yace "Enjoy" Daga haka ya ja karen suka koma cikin gidan, Khaleesat da duk taji conversation din nasu taji ranta ya baci, House mate dinta ya dawo cikin motarsa ya kulle without looking at her yace "Sorry for keeping u waiting Halysaah" Yana fara driving ta hade rai tace "Mene yasa bazaka gaya masa i am just ur housemate ba da kuma dalilin da yasa ka kawo ni nan din?" Housemate dinta yace "Never mind, ba wai yana da hankali bane" ✍🏻 07087865788 [5/5, 6:00 PM] khaleesat Haiydar ✍️: ✨✨HALYSAAH✨✨ ✍🏻 By _Khaleesat Haiydar_ 8....... Har suka isa gida babu wanda ya sake cewa komai a cikinsu, yana parking a garage ya bude motar ya sauka, ita ma ta sauka tana satan kallonsa, kofar entrance din parlor taga ya nufa without looking at her, hakan yasa tana tafiya a hankali ta bi bayansa, ya bude kofar parlon ya juya ya kalleta, ita ta fara shiga parlorn sannan shi ma ya shiga ya kulle kofar, dakinta ta tafi bayan ta bude kofa ta juya ta kallesa, kwanciya taga yayi a kan 3 seater ya lumshe ido, ta shiga dakinta kawai ta kulle. Washegari da safe karfe takwas da 'yan mintuna Khaleesat ta fito daga dakinta, zaune ta gansa da text books a gabansa alamar he is studying, yana daga kai tayi saurin dauke idonta daga kallonsa, har ta karaso cikin parlon ta tsaya jikin kujera tana wasa da edge din mayafin jikinta, a hankali tace "Ina kwana" Ya ajiye pen din hannunsa yace "Good morning Halysaah" Still bata dago kanta ba kuma bata fasa wasa da gefen gyalenta ba, yace "How was ur trip?" Ta ɗan kyafta ido tace "Alhamdulillah" Yace "Sorry jiya ban tambayeki jikin Mama ba, i was sleepy hope she is better now?" Sai a sannan ta daga kai ta kallesa, tace "She is fine Alhamdulillah" Yace "Hope ur mind is now at rest?" Sunkuyar da kanta tayi bata ce komai ba, sai kuma ta ɗan gyada masa kai, wayarsa ne ya fara ring ya dauka sannan yayi picking ya kai kunne, ta ɗaga kanta tana kallonsa, taga shiru yayi alamar yana sauraron abinda ake gaya masa a wayar, after few seconds yace "It should be upstairs then" Daga haka ya katse wayar ya ajiye ya daga kai, da sauri Khaleesat ta dauke kanta daga kallonsa, Yace "Hope nothing Halysaah?" A hankali tace "Kawai, i want to appreciate you, thank you so much, Allah ya saka da alkhairi...." Cikin calm voice yace "No, You need not to Halysaah, iya abinda zan yi ma kanwata na maki ai" Cikin sanyin murya tace "To Nagode Allah ya saka da alkhairi" Ya ɗan yi murmushi yace "To Ameen, so u can be this calm?" Ta wani kallesa, yace "Makarantar zaki tafi baza ki bari ki huta from ur long journey ba?" Ta sauke idonta tace "I am having presentation today" Yace "Ohk then, Allah ya bada sa'a" A hankali tace "Ameen" Ya nuna mata Trolley dinta da ya shigo mata da shi parlon yace "Ga boxes dinki can" Ta kallesu tace "Thank you" Yace "You are welcome" Daga haka ya ci gaba da abinda yake, Sai da ta kai su dakinta sannan ta dawo ta nufi kitchen, Tea kawai Khaleesat ta sha da Cookies sannan ta dauko jakarta zata wuce makarantar, makullin gidan ya mika mata yace "The house key...." Ta tsaya tana kallonsa, sai kuma tace "Ain't u using it?" Ya daga kafada yace "Will sort my self out" Shiru tayi at first, can kuma ta nufesa ta amshi makullin tace "Thank you" Yace "You are welcome" Daga haka ta fita daga gidan ta kullo masa kofar. Khaleesat na tafe tare da Safiyyah dake mata mitar Ya Mustapha yace bata daga kiransa, ita dai Khaleesat tafiyarta kawai take bata ce komai ba, Safiyyah ta tsaya tace "Ohh ga gantalalliya na maki magana ko?" Khaleesat ta tsaya tana kallonta tace "To me zan ce Sophie? Ke kanki kinsan ina da wanda zan aura to menene amfanin in daga wayar Yaya Mustapha? Beside wallahi ko da bani da wanda zan aura ni bazan kulasa ba, ai ana barin halaq ko don kunya" Da wani expression Safiyyah tace "Ban gane ba, as per cewar Surayya cousin sis dinki ce ko kuma kawarki ce? Where did u know her from? Meye hadinki da ita da har za a bar halal don kunya? Can you hear ur self pls? If you are not interested in my cousin brother ba sai kin ta corner corner ba kina kawo zancen da hankali ma bazai dauka ba, meye hadinki da wata Surayya da zaki bar halal don kunya?" Khaleesat tace "Ni dai don girman Allah ki ma bar wannan zancen, Ya Mustapha kuma kiyi ma Allah ki gaya masa i am engage, ni bazan daga kiransa ba" Safiyyah tace "Wallahi bazan fada ba ai kina da baki ki gaya masa da kanki, ke da wa aka yi engaging da zance masa u are engage? Ai as far as i am concern ni ban san wannan batun ba, kawai nasan kina da wanda baki da wani option sai na aurensa, but as time goes on ke kanki zaki san kina da option, za kuma ki ji baza ki iya auren ba sai dai duk abinda zai faru ya faru" Khaleesat ta taɓe baki tace "Kin ga ni yunwa nake ji zan tafi gida, sai gobe in mun hadu" Safiyyah bata tanka ta ba ta ci gaba da tafiya ta bar ta tsaye a wajen, Khaleesat ta bi ta da kallo, to wai ma ta yaya zata daga kiran Ya Mustapha, ita a rayuwarta abinda tasan in an mata bazata ji dadi ba ko by mistake ne bata yi ma wani, ita Safiyyah in ita ce a shoe din Surayya ya zata ji, wannan ai son zuciya ne ma kawai, bin bayanta Khaleesat tayi tace "Ni dai tunda ba mu da aji mu je gida pls ki mana girki i am very hungry and at the same time tired from yesterday's journey" A haka ta samu ta lallaba Safiyyah dake jin haushinta suka kama hanyar gidanta, suna sauka daga Uber ta nufi apartment dinta tana kallon Garage taga babu motar Housemate dinta, does this mean a bude ya bar kofar tunda makullin na hannunta, tana murda kofar taji sa a kulle, to ina ya samu key? ko dai magana yayi aka basa wani makullin, bude jakarta tayi ta ciro key ta bude kofar suka shiga cikin living room din tare da Safiyyah dake biye da ita, Safiyyah ta dinga bin parlon da kallo ta lumshe ido tace "Kai amma wannan turaren Housemate din naki ba dai dadin kamshi ba, the perf is so cool" Khaleesat dai bata ce mata komai ba, ta ajiye jakarta da mayafi ta zauna saman kujera tana ciro wayarta a jaka, Safiyyah ta zauna ita ma kan kujera tace "To kun hadu da Abdul din a Nigeria?" Khaleesat tayi shiru cause kawai taji ita ko maganar Abdul ma bata son ana mata yanzu, ganin yanda Safiyyah ta tsareta da ido, a takaice tace "Eh... me zaki dafa mana pls, wllhi yunwa nake ji" Safiyyah ta mike tace "Toh bari in je in ga what is available in the kitchen" Daga haka ta mike ta nufi kitchen, tana shiga bayan few minutes sai ga ta ta fito, tana kallon Khaleesat da mamaki tace "Kee wai Housemate din naki ne ke maku restocking abubuwa a kitchen haka? Look how ur kitchen is stocked up with costly food items, where is he getting the money to buy all this from?" Khaleesat tace "Baza dai kiyi girkin ba kenan in zo inyi?" Safiyyah tayi dariya tace "No wallahi mamaki nake naga abubuwa masu tsada yake siya, don ni dai nasan kudin da Abdul ke turo maki bazai taɓa siya maki wnn uban abubuwa dake kitchen din nan ba, anya bazan dawo gidan nan ba kuwa Khaleesat? Kinga wasu tsadaddun cookies da drinks da na gani, even the table water in this kitchen ba na yara bane wallahi, the fridge is full to the brim" Khaleesat taki tanka ta tana danna waya, hakan yasa Safiyyah ta juya ta koma kitchen tana kara jaddada anya bazata dawo gidan ba kuwa, Lafiyayyen girki Safiyyah ke yi a kitchen din komai baja baja malam, Sallah kawai Khaleesat tayi a daki ta dawo ta kwanta kan 3 seater tana danna wayarta waiting for the food to be ready, kiran Abdul ne ya shigo wayar hannunta, sosai gabanta ya fadi lkci daya mood dinta ya canza ta hade rai, ta dinga kallon screen din wayar fuskarta babu fara'a tana jiran sai ya kusa katsewa kafin tayi picking call din, dai dai nan taji alamar ana bude kofar parlon, ta mike zaune tana gyara scarf dinta sai ga Housemate dinta ya shigo parlon, sallama yayi ganinta zaune living room din, ta ajiye wayar hannunta ta fasa picking call din Abdul din ta amsa sallamar House mate din nata, yana cire takalman kafarsa yace "Good evening" Ta sauke idonta tace "Ina yini" Yace "Alhamdulillah, bakuwa kika yi?" Double foot wear da ya gani bakin kofar yasa yayi tambayar, tace "Um she is my course mate" Yace "Good" Daki ya nufa, sai a sannan ta kalli wayarta taga kiran Abdul har ya katse tuntuni, she wasn't bothered at all kuma bata yi attempting bin kiran nasa ba ta ajiye wayar kawai, mikewa tayi ta wuce kitchen, tare suka fito kitchen da Safiyyah bayan Safiyyar tayi dishing masu abincin a plate daya, Safiyyah na bin parlon da kallo tace "Ko dai Housemate din naki ya dawo ne kamshin turaren nake kara ji a parlon" Khaleesat ta dau spoon ta fara cin abincin tace "Ko dai kin san sa ne Safiyyah?" Dariya Safiyyah tayi tace "Ina kuwa na san sa, kawai so nake in gansa ne wallahi, irin wannan kayan alatu a kitchen haka, where is he even getting the money shi da ya zo ta scholarship" Khaleesat dai cin abincin gabanta kawai take taki ce mata komai, Safiyyah ta dau spoon ta fara cin abincin ita ma, basu jima da fara cin abincin ba sai ga shi ya fito daga dakinsa, bai kalli direction din da suke ba ya nufi kofa rike da laptop dinsa, Safiyyah ta bi sa da kallo kamar idonta zai fita ya bi sa, ita dai Khaleesat kallo daya tayi masa ta ci gaba da cin abincinta har ya fita daga parlon ya kulle masu kofa, Safiyyah ta ajiye spoon din hannunta tace "To fa, shi kuma haka yake? Ji wani ɗaga shoulders da yake ko kallon inda muke bai yi ba, haka yake maki a gidan dama?" Khaleesat tace "You can be funny Safiyyah" Safiyyah ta hade rai tace "No like seriously haka yake feeling kansa? Ko don abincin da yake ajiye maki na yan gayu a kitchen ne ya ja haka? Ta yaya zai wani wuce mu babu ko Hi, ni fa bana son harkan walakanci" Khaleesat tace "Look Safiyyah ni ba shi ya ajiye min duk abinda kika gani a kitchen ba, shi baya ma zaman gidan nan, jifa jifa kawai nake ganinsa, beside ai mun gaisa da ya shigo kina kitchen, to kuma kallon me zai yi mana don zai fita?" Safiyyah zata yi magana wayarta ya fara ring, mikewa tayi ta dauko wayar, ta ɗan buda ido tana kallon Khaleesat tace "Ke Abdul ne ke kirs" Sosai gaban Khaleesat ya fadi ta ajiye cokalin hannunta ta dinga kallon wayar Safiyyah, Safiyyah ta rike haɓa tace "Ikon Allah, ko ya kiraki baki daga bane? Let me pick dai inji me zai ce" Da sauri Khaleesat ta kamo hannunta zuciyarta na bugawa tace "Safiyyah kar ki ce masa naje Nigeria plss cause bai sani ba wallahi" Safiyyah ta saki baki tana kallonta hangangan, da mugun mamaki tace "Ban gane bai sani ba? To wa yayi sponsoring tafiyar taki? Ina kika samu kudin tafiya" Sosai hankalin Khaleesat ya tashi a lkcn, tana girgiza ma Safiyyah kai tace "Just don't tell him pls, nace maki bai sani ba" Safiyyah da mamaki ya kasa barin ta tace "Ai kiran nasa ma ya katse" Khaleesat taji gaba daya abincin ya fita ranta, sai ga kiransa ya sake shigowa wayar Safiyyah, Safiyyah ta gwalo ido tace "Abdul ne da kirana har sau biyu? Anya lafiya" Khaleesat tayi gathering courage tace "Just pick, in ya tambayeki ni kawai kice masa bani da lafiya yanzu ma kika baro gidana" Safiyyah tace "Ohk" Picking call din tayi ta saka handsfree, ita ta masa sallama ya amsa yace "Ya kike?" Safiyyah tace "I am good" yace "Are you together with Khaleesat?" Babu bata lkci Safiyyah ta sanar masa exactly abinda Khaleesat tace ta gaya masa, ya dan yi shiru at first, sai kuma yace "Tun yaushe ne bata da lafiya?" Safiyyah ta kalli Khaleesat, da sauri Khaleesat tayi mata alamar sati daya da fingers dinta, Safiyyah tace "Yau ina jin sati daya kenan" Daga daya bangaren yace "Sati daya? Me yasa ba a gaya min ba, and what's wrong with her?" Safiyyah tace "Oh ni na zata ai ta gaya maka" Abdul yace "Wani irin rashin lafiya take haka dake hindering dinta from picking calls?" Safiyyah ta wani yamutse fuska jin useless question din da yake yi taki basa amsa tana kyabe baki, ita dai Khaleesat gabanta sai faduwa yake, Yace "Where is she now?" Sounding uninterested with the conversation Safiyyah tace "Tana gidanta mana" Da sauri Khaleesat tayi typing a wayarta sannan ta nuna ma Safiyyah, bayan Safiyyah ta ga abinda Khaleesat ta rubuta tace "Jikin nata dai da sauki sosai fa" A takaice yace "Thanks" Daga haka ya katse wayar, Safiyyah ta ajiye wayarta tace "Tirrrr, ki ji wani magana gatsau gatsau kamar dan daba, ko tashi hankalinsa fa bai yi ba, ni wallahi da ina da yanda zanyi ku rabu rabuwa na har abada da Abdul din nan wallahi yi zan yi, ko kadan bashi da features din miji na gari, babu caring babu tausayi babu affection, so pompous and full of himself always, nonsense and ingredient, wallahi in wani mutumin kirki ne da yanzu hankalinsa ya tashi duk ya birkice min a waya amma kiji yanda yake magana a tsattsaye kamar ubana daga karshe wai Thanks, kamar wanda nayi ma albishir me dadi wai Thanks, ke ki ji fa wai thanks" a hankali Khaleesat tace "Baza ki gane ba Safiyyah, nima naji i am fed up with him, na gaji da halinsa yanzu" Safiyyah ta rike haba da sauri tace "Ke Khaleesat, anya kece ke fadin haka kuwa?" Khaleesat ta wani taɓe baki ta jawo abinci ta fara ci tace "Kawai naji na gaji all of a sudden wllhi" Safiyyah ta sako baki tana mata kallon mamaki, can tace "Ni ba wannan ba ma, Khaleesat wa yayi sponsoring flight dinki zuwa Nigeria?" Khaleesat ta daga kai tana kallonta amma tayi shiru, Safiyyah tace "Kin yi shiru, waye ya biya maki kudin jirgi?" Khaleesat ta sauke idonta kamar bazata ce komai ba sai kuma tace "Housemate dina ne ya siya min Ticket" Safiyyah ta gwalo ido da wani expression na mamaki sosai tace "Ban fahimta ba Khaleesat, Housemate dinki as how?" Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya tace "Eh shi ne ya biya min ticket din jirgin...." Khaleesat bata boye ma Safiyyah duk yanda aka yi Housemate din nata yayi sponsoring tafiyarta ba, Safiyyah was totally speechless and Surprise, after few seconds tace "Did you know what flight ticket is saying from USA to Nigeria Khaleesat?" Khaleesat tace "I went to Nigeria in business class and came back in Business class Sophie" Buda baki Safiyyah tayi ba tare da ta san tayi hakan ba tana kallon Khaleesat kamar idanuwanta za su fito, a hankali tace "Business class fa kika ce Khaleesat?" Khaleesat ta gyada mata kai, Safiyyah ta fara bin gidan da suke ciki da kallo that is for the average here in America, da wani Expression tace "Business class? To me yake yi a wannan gidan if he is doing this well that he can afford to pay for business class to and fro? Dama ni tun daga irin abubuwan da na gani a kitchen nasan wannan mutumi might be trying to disguise himself for a reason best known to him, idan ba haka ba why share an Apartment bayan zai iya affording shi kadai ya zauna a gidan, beside zai iya samun wanda ma yafi wannan in a more better area" Ita dai Khaleesat kallon Safiyyah kawai take ganin yanda tayi concluding lokaci daya, Safiyyah ta wani juya ido tace "Or did he have any mission here da bamu sani ba?" Khaleesat ta girgiza kai tace "Daga sanda nayi misplacing makullina ne ya fara kwana gidan nan tunda yasan bani da makulli, amma tun da yayi move in zuwa gidan nan i can count sau nawa ya kwana if i remembered well, baya kwana nan wallahi, ba har na gaya maki ba...." Safiyyah tayi dariya tace "But i am trying to understand me yasa yake zaune a gidan nan, ko dai ya sanki from somewhere ne shine ya dawo nan saboda ke?" Khaleesat tace "Ji fa wani magana, bai san ni a ko ina ba wallahi, ni bamu taɓa haduwa da shi ba, ranan da suka fara zuwa gidan i overheard him asking if his housemate is a Male or female, lkcn ina dakina, kilan he is in a haste to settle down ne shi yasa kawai he opt for this, amma bai san ni ba wallahi" Safiyyah dai tayi wani murmushi tace "Ae shikenan we shall see" Sai kusan karfe bakwai Safiyyah ta bar gidan shi ma saboda azababben kiran da Ya Mustapha ke mata ne, tana mita haka ta bar gidan, bayan Khaleesat ta rakata ta dawo tayi sallahn magarib a nan parlon tana zaune saman darduma bayan ta gama azkar ta dau wayarta don dubawa ko Ummanta tayi mata reply, tun Safiyyah na nan suke Voice chat da Ummanta da kannenta, ganin Umma bata yi reply ba ta gane wayar ya mutu don dama Umma tace mata babu caji wayar ta kusa mutuwa, mamakin Abdul kawai Khaleesat ke yi a ranta, duk da ce masa da Safiyyah tayi bata da lafiya amma har yanzu bai kira wayarta ba, ko ta Whatsapp bai mata magana ba, tana cikin wannan tunanin taji an bude kofar parlon, juyawa tayi Housemate dinta ya shigo, sallama yayi ganinta a parlon, ta dauke idonta ta amsa, ya karaso cikin parlon without looking at her ya tafi inda Books dinsa suke yace "Kawar taki ta tafi kenan...." Khaleesat tace "Ina yini" Yace "Good evening Halysaah" Bayan ya gama daukan text books da zai dauka ya dawo cikin parlon yace "Alright Good night" Ta bi sa da kallo, sai da ya nufi kofa ya sake juyowa yace "Sai da safe" Ta sauke idonta tace "Allah ya kai mu lafiya" Daga haka ya bude kofar ya fita tana jin ya kulle kofar da makulli daga waje. Washegari Khaleesat bata da karatun da za su yi a makaranta, don haka har karfe goma bata fito parlor ba tana kwance, ita har sannan fa ta kasa daina mamakin Abdul don har sannan bai kirata ba, tashi tayi daga karshe ta shiga bandaki tayi wanka ta shirya, wajen karfe goma da minti arba'in ta fito daga dakinta, kwance taga Housemate dinta saman 3 seater yana bacci, kulle kofar da tayi ne yasa ya bude ido a hankali, walking slowly ta karaso cikin parlon, juyawa yayi bayan ya sake rufe idonsa as if murmuring yace "Good Morning Halysaah" Tace "Ina kwana" Bai bude ido ba bai kuma amsa ba alamar ya ci gaba da baccinsa, ita dai ta wuce kitchen. After an hour Khaleesat ta fito daga kitchen bayan ta gama girkin da take, zaune ta gansa a parlon ya dafe kansa, tsayawa tayi tana kallonsa, ya daga kai suna hada ido ta ɗan koma baya tace "Is everything okay?" ✍🏻 07087865788 [5/6, 4:37 PM] khaleesat Haiydar ✍️: ✨✨HALYSAAH✨✨ ✍🏻 By _Khaleesat Haiydar_ 9..... Still bai dago kansa ba yace "Tashi na kika yi" Ta ɗan bude ido tana kallonsa tace "How?" Ya koma ya kwanta ya rufe ido yace "With the noise ur utensils were making in the kitchen" At first kamar bazata ce komai ba, sai kuma tace "To ai ba nan ya kamata ka kwanta kana bacci ba" Ya bude ido yace "Ok u intentionally woke me up kenan?" tace "Ni ban ma san kana parlon ba ai..." Murmushi kawai yayi bai ce mata komai ba, tana ɗan kallonsa a hankali tace "I made some breakfast, you can have some" Yace "Ok thanks, baki je schl yau ba?" Tace "Ba mu da lectures" Yace "Ohk, wani school kike?" Shiru tayi tana kallonsa, ya mike zaune yace "University of Maryland Baltimore? Loyola University Maryland? Morgan state University? Stevenson University? Johns Hopkins University?" Tace "Duk kuma a nan garin su ke?" Yace "Ohh, kina gari baki san makarantun dake garin ba?" Ta girgiza masa kai kawai still looking at him, shi dai bai kalleta ba yace "To ke wanne kike zuwa a cikinsu?" Ta sauke idonta tace "Na karshen da ka kira" Ya ɗan yi murmushi yace "John Hopkins kenan? Buh ni ban taɓa ganin ko me kama dake a schl din ba ai" Yayi dariya yace "Just joking kafin ki fara min kuka" Ta wani kallesa, duk wannan abun bai kalli direction dinta ba yana magana ne yana kallon agogon wrist dinsa, yace wani course kike yi?" Tace "Pharmacology" Sai a sannan ya kalleta yace "Really?" Ta gyada masa kai, yace "That's a very good course, year what kike yanzu?" Calmly tace "Year 3" Ya gyada kai yace "Good, Allah ya bada sa'a" Ta sauke idonta tace "Ameen" Yace "Ban yi tunanin makarantar kike ba da na dinga dropping dinki in zan je ai, ko da yake ba lallai sanda zan je kina da Class ba...." Sunan wani lecturer dinsu ya kira mata, kawai ta ɗan yi murmushi tana kallonsa cause he is one of her favourite lecturer, yace "He took us during our Undergraduate Degree, and Master's degree also, that was 3 years back, and he is still among my Supervisors currently...." Khaleesat dai sai kallonsa take, ta kasa hakuri har sai da tace "And you are still a student till date?" Ɗan murmushi yayi yace "I am a Medical Dr, pursuing my PhD on Cardiology" Khaleesat couldn't stop staring at him, Yace "I have been studying since i was a baby" Tace "Amma lecturer kake son zama?" Er dariya yayi yace "Not at all Halysaah...." Khaleesat dai tayi shiru bata ce komai ba tana kallonsa, ya dau wayarsa da ake kira ya mayar ya ajiye yace "Kin ci abincin ne a kitchen naga ban ganki da plate ba as usual?" Ta wani kallesa bata ce komai ba ta juya tayi wucewarta daki, shayi ta sha da cookies a kitchen sanda take girki, bayan ta gama girkin kuma taji bata ma jin yunwan shi sa bata zuba abincin ba, Khaleesat ta koma dakinta da kusan 45 minutes tana duba wani course dinsu ta laptop taji kamar ana knocking din kofar parlor, ta mike ta fito parlorn, tsaye taga Housemate dinta bakin kofar living room din har ya bude kofar, Safiyyah ce ta shigo parlon tana kallonsa tace "Hello" Ya dauke idonsa yace "Hi" Komawa daki Khaleesat tayi, Safiyyah tace "Pls is Khaleesat around?" Yace "Sure...." Dakin Khaleesat ta nufa, shi kuma ya tafi ya ci gaba da karatun da yake a parlor, Khaleesat ta mike tana kallon Safiyyah bayan ta shigo dakinta tace "Why are you looking this way Sophie?" Safiyyah tace "Wallahi kwanan nan zaki ji nayi ma matar can duka a kasar nan" Khaleesat tayi murmushi tace "Me kuma tayi maki again?" Gefen gado Safiyyah ta zauna kana ganinta kasan ranta a bace yake tace "Tun fa da kika je gidan mugun halinta ya ninku akan wanda take min a baya Khaleesat, she is trying all possible best to make the house miserable for me, dama yanzu ta dena ajiye min abinci kwata kwata, cornflakes da Golden morn sai ta boye a dakinta da sunan taje hada ma yaronta ne duk don kar in sha...." Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya tace "To Allah ya kyauta, ko zaki dawo nan?" Safiyyah tace "In dawo nan for what reason? ashe ma riba ta ci kenan idan na bar mata gidan, ai we die together with her in that house, babu inda zan dawo wallahi, kawai rabon ta ci duka ne ba wani abu ba" Lkci daya expression din Safiyyah ya canza daga bacin rai ta kamo hannun Khaleesat tana washe baki tace "Kee naga Housemate dinki ido da ido yau, dama haka yake gayen? Wallahi he is so well flavoured komai yaji, ina masa magana ma ko kallona bai yi ba amma ya amsa min cikin girmamawa, wallahi ya burgeni" Tana blushing ta karasa maganar nata, Khaleesat dai ta saki baki ta kasa cewa komai, can ta kalli kofar dakinta da sauri don ta tabbatar a kulle yake kar ace yana jiyo Safiyyah, sai kuma tayi kasa da murya fuska daure tace "Meye haka Safiyyah what if yana jin ki?" Safiyyah tace "Wallahi raina a bace yake amma yana bude kofar kawai na mance da abinda er iskar matar can ta min, a very calm gentleman, yace min Hi nace Hello... kuma kuna Hausa da shi ko turanci ku ke? Ni sai nake ga kamar ba bahaushe bane ba fa" Khaleesat ta hade rai sosai tace "Don Allah ki rufa mana asiri Sophie, What's all this?" Safiyyah tayi dariya tace "Ni dai kinyi girki? Don wallahi yunwa nake ji" Khaleesat ta mike ta nufi kofa ta fita daga dakin, a corridor ta gansa zai shiga dakinsa, bai kalli ma wanda ya bude kofa ba yayi shigewarsa daki, Khaleesat ta tafi kitchen ta dibar ma Safiyyah abincin da ta girka, jin alamar har ya fito daga dakin nasa ta dawo parlor ta tsaya sai gashi ya shigo parlon, makullin motarsa taga ya dauka da wani littafi, ya daga kai suka hada ido ta fara kame kame tace "Ain't you eating the food?" Yace "Oh, ok na manta" Kitchen din taga ya nufa ta bi sa da kallo, sai da ya shiga sannan ta bi bayansa zata gaya masa kar ya bar mata plate bai wanke ba, tsaye ta gansa kusa da abincin ya dau spoon ya bude tukunyar sannan ya debi shinkafar kadan ya kai baki, kallonsa kawai take da mamaki, ya juya ya kalleta yace "Bad habit right?" Sake dibar abincin yayi ya kai baki, daga haka ya rufe tukunyar yace "Kinga ni ba yunwa nake ji ba, I am full" Ta dinga kallonsa, bata san sanda tace "Ko in zuba maka ka tafi da shi?" Ya bude fridge ya ciro bottle water yace "Aa in na dawo anjima zan ci" Daga haka ya fita daga kitchen din ya nufi kofar living room ya bude, sai a sannan ya juya, ta dauke idonta, yace "See yah" Fita yayi ya kulle kofar daga waje. Sai wajen karfe shidda na yamma Khaleesat ta raka Safiyyah zata hau Uber da tayi ordering, Safiyyah na kallonta tace "Ya Mustapha dai ya hakura dake, jiya nake gaya masa gaskiya kina da wanda zaki aura a gida, don nima na gaji da damuna da yake yi shi sa kawai na gaya masa, ai ko ina gaya masa yace to shikenan dama tun farko ai da kin gaya masa he will understand" Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya tace "To ai kinga gwara haka" a haka suka rabu Khaleesat ta koma cikin gida, har goma na dare bata ji shigowar housemate din nata ba hakan yasa ta gane bazai dawo gidan ba ranan. Washegari da safe ta shirya ta tafi makaranta, bata dawo gidan ba sai kusan karfe hudu na yamma, tana shiga living room ta gane ya dawo gidan da bata nan, bedroom dinta ta wuce bayan tayi wanka tayi sallah ta canza kaya ta fito kitchen zata yi ɗan wake don shi ne a ranta, bayan ta gama hada duk ingredients din taji an bude kofar parlor, ta dai ci gaba da abinda take, kitchen din ya shigo ya ajiye ledan hannunsa yace "Good evening Halysaah" Tace "Ina yini?" Yace "Lafiya lau, Are you baking?" Ta kalli flour din da take kokarin kwabawa tace "No" Yace "What are u using flour for?" Bata yarda su hada ido ba tace "Dan wake" Da mamaki yace "Meye shi?" Ta wani kallesa ganin da gaske jiran amsarta yake tace "Dan waken ne baka sani ba?" Yace "Ban san shi ba" Tace "Toh zaka gansa" Turning stick ta dauko ta fara kwabin danwaken shi dai yana tsaye yana kallo, yace "Hey, why did it change to that color? Ko dai ba flour bane?" Ta ɗan kallesa amma taki basa amsa, yana ta kallo with astonishment har ta gama kwabin, sannan ta wanke hannu ta fara saka dan waken a ruwan dake tafasa kan gas, shi dai kallonta kawai yake, can yace "To haka ake cin sa?" Tace "Aa da bread ake ci" Sounding amused ya kalli sauran bread din dake a kitchen din yace "Really?" Bata san sanda tayi murmushi ba batare da ta sake ce masa komai ba don taga da gaske ya yarda da Bread za a ci ɗan waken, he couldn't stop looking at her and the food har ta gama, ya ga ta soya man gyada, sannan tayi dishing din abincin a plate, ta saka eggs din da ta bare a gefe, ta dauko roban yaji, yace "Dama wai wannan abincin ne? To ai na san sa when i was a kid, idan munje wajen Grandma dinmu tana mana" Without looking at him tace "Da ka girma ne ka dawo America ka mance sa kenan" Dariya yayi ya karasa cikin kitchen din yace "Ohk, Can i taste some inji yanda yake?" Komawa gefe tayi bayan ta saka cokali a danwaken, ya dau cokalin ita dai kallonsa kawai take har ya ɗan juya ɗan waken ya debi seed biyu ya kai baki, she couldn't stop looking at him yana tauna abincin gently as if trying to figure out the taste, can ya karyar da kai yace "It's nice, i like it, i still remember the taste, it's nice" Murmushi kawai tayi, ya sake diban abincin ya kai baki, tace "To kaje da shi, i will make another one" Yace "Aa bazan iya cinyewa ba ai" Yana fadin haka ya dauko wani plate din ya debi ɗan kadan a ciki yace "Thank you" Ta karasa ta amsa cokalin a hannunsa ta kara masa ɗan waken ta saka masa kwai daya, ya kalleta ya ɗan bude ido yace "Thanks Halysaah, but seriously I can't finish all this" Tace "Eat and remain" Ruwa ya dauka a fridge ya fita daga kitchen din. Khaleesat na idar da sallan Isha'i ta fito parlor zata dafo black tea don tana son tayi karatu har zuwa karfe dayan dare, tunda ta shiga daki daxu da yamma bata sake fitowa ba sai lkcn, bacci ta tarda Housemate dinta yake yi a 3 seater, da mamaki take kallonsa ganin wai bacci yake bayan Isha'i, ita bata ma san yana gidan ba sai yanzu da ta fito, kallon wayarsa dake gefensa tayi ganin yana haske, ta leka screen din taga an rubuta A-jay, kiran na katsewa taga 5 miss calls aka yi masa, kamar ta tashesa sai kuma dai bata yi hakan ba, ta dau wayar kawai tana dubawa taga babu password balle pin a jiki, cire wayar tayi a silent mode sannan ta mayar inda ta dauka tayi wucewarta kitchen, ta gama dafa shayi ta fito parlon kenan taji wayar ya fara ringing loudly, da kyar ya bude idanuwan sa, ita dai ta koma kusa da kofar kitchen din ta makale a jiki, ya ɗan kalli wayarsa ya jawo yana duba screen din, ɗaga kiran yayi ya kai kunne yayi shiru har sannan yana lullumshe ido, can ya ja tsaki ya ajiye wayar sannan ya mike zaune, har sannan bai ganta ba ita ma bata bar jikin kofar da ta makale ba, mikewa tsaye yayi daga karshe yana lumshe ido, gani tayi kamar baccin yake yi a tsayen, ta wara ido tana kallonsa with shock , sai da yaga ya kusa faduwa sannan ya bude idonsa sosai, ta kai hannu bakinta saboda dariyar da taji ya taho mata, tafiya yayi ya isa jikin pillar dake parlon ya jingina ya rufe ido, kasa daina kallonsa tayi da mamaki, he stood there for almost 3 minutes yana bacci, ringing din wayarsa ne yasa ya bude ido da sauri as if frightened, kitchen ta shige don bata son yin dariyar da ya taho mata a wajen, sai a sannan ya ganta bayan ta shige kitchen da sauri, ya fara bin parlon da kallo as if trying to understand what was happening, lkci daya idonsa yayi clearing gaba daya ya fara sosa kai, at first bai yi niyyar bin ta kitchen din ba, can kuma dai ya nufi kitchen din, ta ajiye kofin shayin hannunta ta dafe cabinet tana dariya ciki ciki, tana ganinsa ta hade rai tana juya shayinta da cokali as if nothing happened, fridge ya bude ya dau ruwan gora yana kallonta yace "You are still awake?" Ta ɗan kallesa tace "To karfe nawa ne yanzu da zan yi bacci, as if i am you" Bai ce komai ba ya fita daga kitchen din, murmushi tayi ta bi sa da kallo, daukan shayin tayi ta bi bayansa, taga ya dau makullin motarsa da waya without looking at her yace "Good night Halysaah" Bata san sanda tace "To kar fa kaje kana driving bacci ya dauke ka a kan steering" Bai kalleta ba sai murmushi da yayi kawai ya nufi kofa, ta bi sa da kallo har ya fita sannan ya kulle kofar ta waje, karasawa kusa da window tayi ta ɗan bude curtain kadan tana kallonsa har ya shiga motarsa a garage yayi reverse, sai da ta daina hangen motarsa sannan ta sake curtain din a hankali, tafi minti uku a tsaye wajen ta jingina da window, daga karshe tana tafiya a hankali ta wuce dakinta bayan ta kashe wutan parlon..... Washegari Khaleesat na sauka daga Lyft bayan ta dawo school taga motar Housemate dinta heading toward the garage, kafin ta karasa apartment din nasu har ya shiga ciki, murda kofar tayi taji a bude ya bar mata alamar ya ganta shi ma, tana shiga parlon yana fitowa daga kitchen rike da Lemon gwangwani me sanyi, ya karaso cikin parlon yace "Are you just coming back from school?" Gaishesa tayi, yace "Good evening Halysaah" Bedroom dinta ta wuce ta bar sa a parlon, it's almost 6pm na yamma kuma Safiyyah ce ta bata masu lkci tana mata bayanin wani course dinsu da tace bata ganewa, wanka Khaleesat tayi ta sauya kayan jikinta zuwa kananun kaya sannan ta saka hijab ta fito parlor, yana parlon har sannan yana operating laptop dinsa, ganin zata shiga kitchen yace "Ki bari ki hutu, zan fita sai na siyo abinci" Khaleesat ta kallesa tace "I am cooking noodles" Yace "Ohk then" Tana fadin haka ta wuce kitchen, Ya mike ya wuce dakinsa da laptop dinsa, cikin mintunan da basu da yawa Khaleesat ta gama dafa noodles din da take, ba da yawa ta dafa ba don bata san ko zai ci ba, zata yi dishing din abincin a plate taji ana knocking kofar parlor, ta ajiye plate din hannunta sannan ta fito daga kitchen din, Housemate dinta ta gani har ya fito shi ma to check on who is at the door, amma ganinta kawai ya juya ya koma dakinsa, karasawa tayi ta bude kofar, lkci daya taji komai ya tsaya mata cak ta dinga kallonsa babu ko kiftawa kamar ranan ta fara ganinsa, Yana kallonta daga sama har kasa yace "Meye kike kallo na haka Malama?" Tayi wani yake zuciyarta na bugawa tana in-ina da kyar tace "Ya Abdul, I.. I.. was surprised, san..nnu da zuwa" Da sauri ta juya ta koma parlon, ya bi bayanta yana duba wayarsa dake vibrate a hannunsa alamar ana kiransa, ita dai ta koma bayan kujera ta tsaya kamar munafuka tana kallonsa zuciyarta na bugawa sosai, kana ganinsa kasan ba a lkcn ya shigo America ba, probably tun daxu ya shigo ya sauka hotel, ya ɗaga kiran da ake masa ya kai kunne, tana ganin haka ta juya ta nufi corridor din dakunan apartment din tana waige waige, ganin attention dinsa na kan wayar da yake ta bude kofar dakin Housemate dinta ta shiga da sauri ta kulle kofar, Housemate dinta ya juya yana kallonta da mamaki, gaba daya a rude take ta nufesa tana yarfe hannu ta duka kusa da shi, ya mike still looking at her with surprise yace "Are you alright Halysaah?" ✍🏻 07087865788 [5/7, 6:25 PM] khaleesat Haiydar ✍️: ✨✨ HALYSAAH ✨✨ ✍🏻 By _Khaleesat Haiydar_ 10..... Khaleesat ta gyada masa kai tana rufe bakinta da hannunta murya can kasa tace "Plss i have a visitor, i want u to plss pretend you are not staying here, just pretend u came to drop some books for ur Female friend living here plssss" Kamar zata yi kuka ta kare maganar tana kallonsa, yayi shiru shima yana kallonta at first, sai kuma yace "As in how Halysaah?" Ta marairaice masa tace "Kawai dai kayi kamar ba a gidan nan kake ba don girman Allah ka rufa min asiri, u know my former housemate mace ce, act as though u are her friend, kayi kamar wajenta ka zo pls, don Allah ka taimake ni" Bata jira cewarsa ba ta mike ta juya da sauri ta fice daga dakin kafin Abdul ya biyo ta, ya bi ta da kallon mamaki baya ko kiftawa, can kawai yayi murmushi ya zauna ya ci gaba da abinda yake yi a Laptop dinsa, parlor Khaleesat ta dawo suka kusa cin karo da Abdul da ya nufo corridor yace "Me kika je yi a ciki? You didn't even get me something to drink" Ta ɗan yi murmushi a hankali tace "Why didn't you let me know u are coming? Me yasa baka gaya min zaka zo ba?" Yace "Sai na gaya maki in zan zo? Ko ke zaki biya min ticket din jirgin?" Ta girgiza kai cikin sanyin murya tace "Aa ba haka nake nufi ba, ya hanya?" Yana kallonta daga sama har kasa yace "What is wrong with you, why were you sick?" Ta sauke manyan idanuwanta kasa a hankali tace "I don't know too, but i am much better now, naji sauki Alhamdulillah" Yace "Rashin lafiyar ne yasa kika dena daga kirana all this while?" Ta marairaice masa tace "Don baka san yanda nake ji bane a sannan, let me get you water to drink" Daga haka ta wucesa da sauri, ya bi ta da kallo har ta shiga kitchen, Khaleesat ta jingina jikin cabinet din kitchen din ta dafe kirjinta that was heaving so fast, after few seconds ta sauke numfashi sannan ta dau tray ta bude fridge ta dauko ruwa da lemo da glass cup sannan ta fito daga kitchen, zaune ta gansa a parlon yana danna wayarsa, ta karasa ta duka gabansa ta ajiye masa ba tare da ta bari sun hada ido ba, shi dai tunda ta fito kitchen din yake bin ta da ido, ta zauna kan carpet ta tankwashe kafarta ba tare da ta bari sun hada ido ba tace "Ya su Mumy da Daddy?" Jin yayi shiru ta daga idanuwanta ta kallesa taga kallonta kawai yake, a hankali ta sauke idonta kasa, yace "Duk kwana biyun nan kin canza Baby, you don't look critically ill da har zaki kasa daga kirana, menene yasa kika dena kirana kuma idan na kira ki ki dagawa? Common WhatsApp kin dena min magana yanzu" Ta kasa kallonsa, tana wasa da gefen hijab dinta a hankali tace "To kwanan nan sai kayi ta min fada ta waya baka considering dina, ga kuma course dinmu da wahala ka sani" Ita kanta ta rasa dalilin da yasa hawaye ya cika idonta, He let out a sigh har a sannan yana kallonta, sai kuma ya dagota sitting her down by his side, gabanta ne ya fara faduwa, in da akwai abinda ta tsana kuma take fargaba a rayuwarta bai wuce Abdul ya zo America wajenta ba, duk da yawanci zuwan da yake it's either tare da Mom dinsa or his Dad, amma duk da haka a dar dar take da shi saboda wasu abubuwan da ya tsira wanda a baya baya mata haka, duk zuwansa kasar sai ta kirko wani abu da zai maidata unhealthy wani lkcn har sai an kai ta hospital, ita da tasan zai kamo hanya ya taho da bata fara ce ma Safiyyah tace masa bata da lafiya ba, yana caressing fingers dinta yayi kasa da murya yace "But you know i love you Khaleesah, ke ce kike jawowa nake maki fada a ko da yaushe" Ita dai bata ce komai ba hawayen dake makale idonta ya gangaro bisa kuncinta, ya kai hannu yana goge hawayen a hankali yace "Ohk, but you know i love you so much right?" ta gyada masa kai kawai, a hankali yace "Housemate dinki fa? Is she around?" Sosai taji gabanta ya fadi, taki barin su hada ido tace "No ban sani ba, i saw she had a visitor daxu ya zo nemanta, probably her friend...." Yana kallonta yace "Friend? Namiji kenan?" Khaleesat ta gyada masa kai, lkci daya ya hade girar sama da ta kasa yace "Yaushe ta fara kawo namiji gidan? When did that start?" Khaleesat tayi karfin halin cewa "Dama tana kawowa time to time ai but not frequently, sai in kilan sun kawo mata reading materials ko bata da lafiya sun zo dubata" Yace "Kuma mazan na kwana a nan?" Khaleesat ta hadiye wani abu da kyar tace "Ni ban sani ba gaskiya, tunda ina dakina always a kulle ai" Kallonsa tayi to cut short the conversation tace "Na dafa noodles yanzu bari in kawo maka kar ya huce" Tana fadin haka ta mike da sauri zuciyarta na bugawa, dai dai nan Housemate dinta ya fito daga dakinsa, Khaleesat taji zuciyarta ya kusa shigewa cikinta tsabar kidimewa, tayi saurin dauke kai tayi hanyar kitchen, Abdul ya juya jin an bude kofar daki, hada ido suka yi da Housemate din nata da ya shigo parlon yana tafiya slowly waya kare a kunnensa duk da ba magana yake a wayar ba hannunsa daya rike da wani Textbook, idonsa kuma na kan Abdul, hannu ya daga masa calmly yace "Hello" Abdul ya bi sa da kallo babu ko kiftawa without replying to his Hello, shi dai Housemate din nata yana tafiya calmly ya nufi kofa ya fita daga parlon, tuni Khaleesat har ta shige kitchen hankalinta a tashe ta dafe kirjinta tace "Na shiga uku....." A haka dai ta fara zubo noodles din a plate, cike da karfin hali ta dawo parlon, Abdul dake ta kallonta yace "Who is he Baby?" Khaleesat ta ɗan yi fari da ido tace "Ni ban ma taɓa ganinsa ba sai yanxu, Nancy ya kawo ma littafi ina ga" Abdul ya mike yace "Ta yaya zaki dinga rayuwa under same roof da wani gardi Baby? Yaushe Nancy din ta fara shigo da samari gidan nan? All this while dama yana cikin gidan nan?" A hankali Khaleesat tace "Na fa ce maka ban taɓa ganinsa ba, i have never seen him before sai yanzu" Ajiye abincin hannunta tayi cike da karfin hali tace "In dafo maka black tea?" Komawa yayi ya zauna yaki cewa komai, kana ganinsa kasan he is boiling inside, ita dai ta juya tana tafiya kamar munafuka ta koma kitchen, mikewa yayi ya bi bayanta har zuwa kitchen din yace "Ta yaya wani banza can zai dinga shigowa yana kalle min ke anyhow Khaleesah?" A hankali Khaleesat tace "Ya Abdul kar ka manta communal living muke a gidan nan, this is America.... this isn't my apartment alone, bazan iya cewa ga wa enda za su shigo gidan ba tunda ba gidana ni kadai bace" Tsawa ya mata yace "And so what??? An gaya maki bazan iya kama maki hayar gidan ke kadai bane? Banda kince kina tsoron zama ke daya a gida do you think u will be sharing an Apartment with anyone in America? Do u think I can't afford a full apartment for you??" Har jikin Khaleesat ya fara rawa ganin how fiercely he was speaking to her yana huci, ga idanuwansa sun fara sauya launi, sosai take jin tsoron Abdul ita kam, hawaye ya fara gangarowa idonta muryarta na rawa tace "Ka fara kuma ko?" Kamo hannunta yayi fuskarsa a murtuke suka fito daga kitchen din, ta fashe masa da kuka a hankali har suka dawo cikin parlon, cike da fada yace "Ya bazan fara ba naga wani katon banza under same roof with you? Me yasa tun tuni baki gaya min Housemate dinki na shigowa da gardawa cikin gidan nan ba in samar maki other alternative? Me yasa baki da hankali baki da tunani ne ke a rayuwarki?" Zaunawa tayi ta fashe da kuka sosai ta hade kanta da kujera, ya zauna yana huci, ita dai kuka kawai take tana shessheka, after few minutes ya koma kusa da ita ya dagota drawing her closer to him kamshin turarensa ya cika mata hanci, nan da nan ta hadiye kukan da take tana zare ido, Gently yake caressing dinta murya can kasa yace "I am sorry Baby, amma da kin gaya min da na samar maki wani apartment din ai...." Ta fara kokarin komawa baya tana son kwace kanta daga hannunsa, kin saketa yayi a fusace yace "Why do u always act like a Bush gal Khaleesah? Har yanzu rayuwar Ghetto bazai fita a kanki ba? What is the meaning of this nonsense?" Ta ki barin su hada ido, da kyar tace "To ai... This is a promise you made, amma kuma sai ka dinga..." Cikin tsawa yace "So f what if i break the promise? Ko ance maki tsoronki nake ne? Ko kuma wani ne zai aure min ke dama?" Ta marairaice masa kamar zata yi kuka tace "Ni dae bari in kawo maka black tea" zata mike ya fixgota har sae da fado kansa, ya fige hijab din jikinta yace "Naga alamar kin ma maida ni wani gara don kinga ina biye ki" Ta takure waje daya wasu hawayen na taruwa idonta taki yarda su hada ido tana kokarin kwatar kanta daga grip dinsa, skirt karami ne sosai jikinta sai half vest shi sa ma take ta yawo da hijab tun daxu da ta dawo schl, ya sake fixgota sosai jikinsa, kuka ta fara yi muryarta na rawa tace "Don Allah ka bari plss, this wasn't our deal, you are not keeping to ur promise" Kallonta ya dinga yi saboda yanda tayi provoking dinsa, duk da shi bai yi niyyar mata komai ba da ya wuce ya lallasheta amma tsabar yanda ta hasala shi sai ya fara kokarin kissing dinta, ƙin yarda tayi tana kiciniyar kwace kanta tana kuka, House mate dinta ne ya shigo parlon a lkcn, ya kalli yanayin da suke da kuma yanda take struggling din kwatar kanta daga jikinsa, direct ya nufi cikin parlorn har inda suke without a second thought ya cakumo Abdul yana kallonsa da kyau "Hey, this is America guy, what sort of molestation is this??" Mikewa Abdul yayi yana kallonsa da wani irin Expression na mamaki, bai yi wata wata ba kawai ya sauke masa fist dinsa a kirji har sau biyu, ya wani cakumosa yace "Are you insane? How dare you??" Khaleesat ta zaro ido ta mike cikin tashin hankali ta riko Abdul tana zaro ido with shock, lkci daya ta kalli Housemate dinta da ya tsaya yana kallon Abdul baya ko kiftawa kuma bai yi attempting rama abinda yayi masa ba, da kyar tace "He is my boyfriend, I don't think u have any problem with this, who are you? And where do you know us from? You have no right to intrude!" Housemate dinta dake kallonta ya sauke idonsa kamar bazai ce komai ba, sai kuma calmly yace "My bad! And i am sorry, i thought u were in danger, i am only here to drop some books, sorry about that plss" Khaleesat ta wani kallesa tace "Do i know u from anywhere that warrant u intruding?" Ya girgiza kai yace "Not at all... I am sorry" Kallon Abdul yayi, bowing his head gently at the same time yace "I am sorry, dude" Daga haka ya ajiye book din hannunsa ya juya ya nufi kofar parlon ya fita waje, that was when Khaleesat realized she was half dressed all this while, dukawa tayi ta fara kuka a hankali ta hade kanta da kujera tana jin kanta na wani irin sara mata, wani kallo Abdul yayi mata yana huci, kawai ya dau wayarsa ya nufi kofa ya fice daga parlon kamar zae tashi sama, ta bi sa da kallo hawaye na sauka idonta, mikewa tayi da sauri ta nufi window tana duba waje taga babu motar Housemate dinta har ya tafi, sae Abdul da ta hango yana tafiya down the street, dawowa parlon tayi tana goge hawayen dake sauka idonta ta dau Hijab dinta ta wuce daki da sauri, har wajen karfe tara na dare Khaleesat ta kasa tashi daga saman darduman da take zaune ga wani ciwo da kanta yake mata, jawo wayarta tayi a hankali, tun daxu take son kiran Abdul amma ta kasa kiransa saboda tsoro, daga karshe tayi gathering courage tayi dialing numbersa har ya katse bai daga ba, ta sake kira nan ma bai ɗaga ba, tasan ba lallai ya ɗaga ba dama, ajiye wayar tayi ta kwanta gefen gado wasu sabbin hawayen na zuba idonta. Da safe duk da yanda Khaleesat ke jin ta wani iri kamar zata yi rashin lafiya haka nan tayi shirin makaranta ta saka Facemask dinta sannan ta bar gidan, ta kusa awa daya a makarantar kafin Safiyyah ta shigo, Khaleesat ta zauna gefenta tana kallonta tace "Why are you sitted here Khalee? Is the lecturer not around?" Khaleesat ta sauke idonta bata ce mata komai ba, Safiyyah ta sauke Facemask dinta ganin swollen eyes dinta cike da damuwa tace "Subhanallahi, what is wrong Khaleesat? Kukan me kika yi? Ko jikin Mama ne?" Khaleesat ta girgiza mata kai hawaye na taruwa idonta, hankalin Safiyyah ya tashi tace "Innalillahi, don Allah me ya faru? Is everything ok?" Khaleesat ta girgiza mata kai tana goge idonta a hankali tace "Abdul ne ya zo" Safiyyah ta gwalo ido tace "Abdul kuma?? Yaushe? Kuma me ya maki kike kuka?" Khaleesat tace "He came yesterday evening" Safiyyah tace "Ji jaraba, to me ya zo yi? Kuma me ya faru da ya zo din?" Safiyyah na jefa mata wannan tambayar taji hankalinta ya tashi lkci daya, let it not be what just crossed her mind now, tunda tasan ko wanene Abdul, ta kamo hannun Khaleesat da sauri cikin tashin hankali tace "Ko ya maki wani abu ne? A gidanki ya kwana???" Khaleesat ta girgiza mata kai a hankali tace "A'a" Safiyyah bata san sanda ta sauke wani ajiyar zuciya ba, can tace "Toh meye kuma na kuka don ya zo, ko rashin mutuncin da ya saba ya shuka maki?" Khaleesat na shessheka a hankali tace "He met my Housemate" Safiyyah ta bude baki tace "Kai don Allah, cikin gidan ya gansa? To ke ma dai wallahi baza ki iya karyan kare kanki ba kice masa kawai baƙon Housemate dinki ne shi tunda bai san Nancy ta tashi a gidan ba, to sai kika ce masa me?" Khaleesat na gyada mata kai tana goge hawayen da yaki tsaya mata tace "Haka nace masa, amma ai kin sansa kinsan halinsa, he even fought with my Housemate" Safiyyah ta zaro ido tace "Fight? To akan wani dalili?" Khaleesat tace "Kema kinsan yanda yake yi ai Sophie, kawai wai zai yi kissing dina ni kuma naki yarda sai ga Housemate dina ya shigo shine yayi approaching dinsa seeing what he was doing to me, hakan da yayi ne yasa Abdul yayi fada da shi, he hit him so hard" Safiyyah tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, to Housemate din ya rama ne?" Khaleesat ta girgiza kai a hankali tace "Bai rama ba, kawai hakuri ya basa" Safiyyah tace "Wallahi in ance min Abdul na shan giya ni bazan musa ba, cause his actions portray that, kawai daga ganin mutum ka fara fada da shi kamar wani ɗan daba, kuma in banda rainin wayo zai zo me yasa bazai ce maki zai zo ba kawai sai dai ki gansa kamar an jefosa a gidan?" Khaleesat tace "Wai fa ce masa da kika yi bani da lafiya shine yasa ya taso ya taho, da na sani da ban ce kice masa haka ba" Safiyyah ta bude baki tana kallon Khaleesat don ita ma sai a sannan taga da basu ce masa haka ba tunda ba isasshen hankali ke garesa ba, Safiyyah ta sauke wani ajiyar zuciya tace "To yanzu Housemate din naki fa? Hope he didn't hurt him?" Khaleesat ta fara goge wasu sabbin hawayen idonta tace "Kinsan menene ya dameni?" Safiyyah ta girgiza kai, a hankali Khaleesat tace "Maganganun da na gaya ma Housemate din nawa, meanwhile he was just trying to be protective ganin kamar Abdul molesting dina zai yi, ni kuma abinda yasa nayi masa haka don kar Abdul din ya zargi mun san juna da Housemate din nawa, cause i told him frnd din Nancy ne kuma ni ban taba ganinsa ba" Safiyyah da ta kasa rufe baki tace "Wasu irin maganganu ki ka gaya ma Housemate din naki?" A hankali Khaleesat ta gaya mata duk bakaken maganganun da ta gaya ma Housemate din nata, Safiyyah ta dinga mata wani kallo cike da takaici, can tace "To shi katon banzan da kika fadi bakaken maganganun a kansa hope yayi considering dinki at the end of everything?" Khaleesat ta girgiza kai tace "He walk out on me, na kirasa sau biyu jiya yaki dagawa, kuma har yanzu bai kirani ba" Safiyyah ta ja tsaki tace "In ma ya ɗaga shi babban ɗan iska ne, kada Allah yasa ya daga, kuma shi Housemate din naki kun sake haduwa bayan abinda ya faru jiya?" A hankali Khaleesat tace "Shi ma tunda ya bar gidan jiya har yanzu bai dawo ba" Safiyyah tace "To wallahi ki kirasa don mutumin nan yafi karfin walakanci a wajen ki" Khaleesat ta fara wani hawayen tace "I don't have his Number" Safiyyah tace "Ban gane baki da lambarsa ba?" Khaleesat tace "Wallahi, even when i was going to Nigeria kawai hadani yayi da wani mutum ya bani number mutumin amma bai bani lambarsa ba" Safiyyah tayi shiru, can ta sauke ajiyar zuciya tace "Ki tashi kawai ki koma gida kilan Allah zai sa ya dawo sai ki basa hakuri, Abdul kuma kar ki kuskura ki sake kiransa in ba haka ba in tsine maki wallahi" Duk da bakin cikin da Khaleesat ke ciki sai da ta ɗan yi murmushi, a haka ta koma gida ta bar Safiyyah a school din bayan Safiyyah tace ta kirata duk abinda ake ciki, in ma Abdul din ne ya sake dawowa gidan ta kirata zata taho..... Throughout ranan Khaleesat bata ga Housemate dinta ya dawo gidan ba har karfe takwas na dare, ta rasa me yasa ta kasa samun nutsuwa hankalinta yaki kwanciya, ko tunanin Abdul bata saka a ranta ba tun bayan barin ta school daxu da safe da Safiyyah tayi encouraging dinta kar ta sake kiransa, but she was so restless ganin Housemate dinta bai zo gidan ba, she wish she had his number ta kirasa, wajen karfe goma saura wayarta ya fara vibrate ta jawo a hankali tana duba screen din taga Safiyyah ce, Safiyyah ta kirata yayi sau 6 daga barinta school da safe har zuwa yanzu, Safiyyah tace "Is he back Khaleesat?" Khaleesat ta girgiza mata kai a hankali tace "A'a bai zo ba" Safiyyah ta sauke ajiyar zuciya tace "Kilan sai gobe zai zo gidan, ki kwantar da hankalin ki pls" Khaleesat dai tayi shiru bata ce komai ba, Safiyyah tace "Plss kar ki wani damu kanki da yawa kawata, hope kin ci abinci?" Khaleesat tace "Na ci" Safiyyah tace "To kiyi kwanciyarki, good night" A haka suka rabu, Khaleesat ta ajiye wayarta ta lumshe ido duk da tasan ba baccin zata yi ba....... *Continue making your payment before the end of free pages fanss, in ba haka ba aji shiruuu...*😃 ✍🏻 07087865788 [5/8, 6:48 PM] khaleesat Haiydar ✍️: ✨ ✨HALYSAAH✨✨ ✍🏻 By _Khaleesat Haiydar_ 11..... Tun da gari ya waye Khaleesat ta kira Safiyyah tace mata bazata shigo school ba don tana son tayi bacci, Safiyyah tasan sarai bata yi baccin kirki ba kenan daren jiya, har mamakin yanda Khaleesat ta iya saka abu a rai ya dameta take, Safiyyah tace "Shikenan kawata, after our classes zan zo ko da yamma ne in sha Allah" a hankali Khaleesat tace "To Allah ya kai mu, Nagode" Daga haka suka yi sallama ta ajiye wayar ta koma ta kwanta. Wajen karfe hudu na yamma Khaleesat ta tashi daga baccin da take, bandaki ta shiga ta wanke baki sannan tayi wanka ta dauro alwala ta fito, tun wayewar gari babu abinda ta ci har zuwa sannan, rabonta da abincin kirki zae yi kwana uku yau tun dai faruwar incident din few days ago, bayan ta idar da sallah ta shirya cikin kaya marasu nauyi ta fito parlor ta tafi kitchen ta hada shayi kawai sannan ta koma dakinta, laptop dinta ta jawo ta kunna zata saka movie ko zata ɗan samu nutsuwar abubuwan dake damun ta a rai ta hanyar kallon film, daga karshe ma ta fasa kallon ta dauko takardunta ta fara karatu, nan ma taji bata fahimtar komai a karatun, rufe takardan tayi ta kwantar da kanta gefen gado ta lumshe ido with different thoughts running her mind, it's not as if she is disturb don Abdul bai daga kiranta ba ko bai kirata ba, kawai dai bata ma san abinda ke damunta bane in particular, bayan lokaci me tsawo ta sauke ajiyar zuciya ta bude idonta ta jawo wayarta ta bude WhatsApp, status taga Abdul yayi updating few hours ago, ta bude hoton da yasa taga har ya ma koma Nigeria cause a field din kwallo yayi hoton da abokansa dukkansu sanye da jersey, ko kadan bata yi mamakin komawarsa Nigeria ba don zai ma iya abinda yafi hakan, da taji shiru har kwana uku dama ta zargi ya koma, dai dai nan taji an bude dakin that is opposite her's, sosai gabanta ya fadi don tun ranan sae yau Housemate din nata ya zo gidan, ta kalli agogon wayarta taga karfe biyar har ya gota, ta ajiye wayar ta dago kanta, tana ta zaune har bayan 15 mins da shigarsa daki sai kuma ta mike tsaye tana jin jikinta ba karfi ta dau gyalenta tana tafiya a hankali ta nufi kofarta ta bude ta fito corridor, sai kallon kofar dakin nasa take gabanta na faduwa, ta rasa courage din karasawa bakin kofar, she stood der for some minutes daga karshe ta lumshe ido ta bude tana tafiya slowly ta isa bakin kofar nasa ta tsaya, ta kai hannu tayi knocking a hankali kamar tana tsoron kofar, komawa gefe tayi kamar mara gaskiya waiting for his response, jin shiru bai amsa ba ta sake knocking din a hankali, ta jira for like a minute again taga dai ba a amsa ba, babu abinda yayi crossing mind dinta sai ko yana bacci ne, but bacci da yamma haka? handle din kofar ta kai hannu gently without thinking twice ta bude kofar tana kallon cikin dakin with throbbing heart, a edge din gadon dakin ta gansa a duke yana operating laptop dinsa da alamar abinda bai gama ba ranan da ya bar gidan yake karasawa, ya daga kai ya kalleta sai kuma ya ci gaba da abinda yake yi, she felt really really bad, ashe yana ma jin tana knocking din, da tasan yana ji ya kyaleta da bazata fara bude kofar dakin nasa ba, ya mike tsaye yace "Good evening Halysaah" Taki amsawa kuma taki yarda ta kallesa, da kyar tace "Dama kana ji kaki amsawa?" Har muryarta ya fara rawa, ya ɗan bude ido yace "To na sani ko saurayinki ne Halysaah?" Nan da nan hawaye ya cika idonta ta juya ta bar bakin kofar ta kullo masa dakin ta koma nata, dukawa yayi ya ci gaba da abinda yake yi a laptop, tana komawa daki ta fara kukan da bata san dalilinsa ba, she felt really hurt kuma tayi da ta sanin zuwa dakin nasa, tana nan a yanda take har shidda saura sannan taji yayi knocking kofar dakinta gently, daga kai tayi tana kallon kofar sai kuma ta hade rai, lkci daya ya bude kofar tare da sallama, sai dai daga nan bakin kofar ya tsaya yana kallonta yace "I was trying to finish a power point Housemate, how are you doing?" Ta sauke idonta a takaice tace "It's fine" Yace "Baki je makaranta ba yau?" Ta gyada masa kai looking toward a different direction, yace "Why?" A takaice tace "Ba komai" Yace "Ok, hope everything is okay?" Sai a sannan ta daga kai ta kallesa sai kuma ta dauke kai don kar ma ta fara kukan dake taruwa idonta, bayan like 10 seconds yace "Saurayin da ke maki fada a waya ne guy din nan ko?" Ta kasa cewa komai at first, sai kuma muryarta na rawa tace "Kayi hakuri da abinda ya faru" Ya ɗan buda ido yace "No it's fine Halysaah, ai ba ma abinda ya faru, but where did you know him from?" Tayi shiru ta kasa cewa komai tana share hawayen idonta, yace "I am intruding ko?" Ta girgiza masa kai kawai, yace "Ohk can we talk if you are comfortable Halysaah" She kept mute Kamar me nazari, can kuma a hankali tace "Ohk" yace "Then meet me at the parlor" Daga haka ya juya ya fita, ko da Khaleesat ta fito parlon bata tarda sa ba a ciki, ta zauna kan kujeran parlon tunani iri iri na yawo a kanta har ta rame a kwana ukun nan, bayan some minutes sae gashi ya fito daga kitchen with a cup of coffee, ya karaso cikin parlon ya zauna yana kallonta yace "You look pale Housemate, are you okay? Ko ya maki wani abun ne?" Khaleesat ta daga kai ta kallesa, sai kuma ta girgiza masa kai a hankali tace "He left immediately u left too" Yace "Oh really? That's weird" Ita dai tayi shiru, ya ɗan yi murmushi ya ajiye coffee din hannunsa yace "Amma baki ci abinci ba" Nan ma tayi shiru tana kallonsa, yace "Naga kamar its been a while da kika yi girki a kitchen, so me kike ci a gidan?" Ta sauke idonta, he could see tana cikin damuwa sosai, yace "Tun ranan da ya tafi bai dawo ba kenan?" Tace "Um" Ya kalli agogon wrist dinsa yace "Do u mind me taking u out for dinner?" Kallonsa Khaleesat take babu ko kiftawa kuma bata ce komai ba, ya mike yace "Get ready, let me get my car key" Yana fadin haka ya mike ya tafi dakinsa ta bi sa da ido, Khaleesat ta fi minti uku zaune parlon tana contemplating on weather to go out with him or not, what if Abdul bai bar kasan ba kawai old picture yayi uploading a status dinsa? The thought of this sent her quivers all over, Tana cikin wannan tunanin sai gashi ya fito daga dakinsa, yana shigowa parlor ta mike ba tare da ta bari sun hada ido ba ta wuce dakinta, canza kaya tayi ta dau veil dinta ta yafa sannan ta zauna gefen gado tana tunane tunane iri iri, bayan 15 mins da shigowarta dakin taji yayi knocking yace "Baki shirya ba Halysaah?" A hankali ta mike ta dau wayarta ta nufi kofa ta bude ta fita, ta samesa har ya koma parlor yana jiranta, tana isowa parlon yana kallonta yace "Where u contemplating inside the room?" Bata san sanda ta dan yi murmushi ba bata dai ce masa komai ba, yace "To mu je, this is after 6 already" Shi ya fara nufar kofar fita living room din sannan ta bi bayansa, yana tsaye bakin kofar bayan ya fita ya jira har ta fito daga parlon sannan ya kulle kofar yana kallonta yace "Why this much Deodorant Housemate?" Ta wani kallesa tace "Ni nace maka na sa?" Bai bata amsa ba ya nufi garage tana biye da shi a hankali, ita dai bata sa turare yanzu ba sai tun wanda ta saka da tayi wanka daxu, sai in ko kamshin kayanta yaji amma ba dai ita ba, bude mata motar yayi tun bata karaso ba sannan ya zaga ya shiga motar yana jiranta, bayan ta shiga suka bar Garage din, wani babban restaurant sananne ya kai ta a Baltimore, bayan yayi parking ta dinga kallon restaurant din da ta ga an rubuta The Capital Grille, sai da ya fara sauka daga motar sannan ita ma ta sauka, tana biye da shi suka shiga ciki, shi yayi offering dinta seat bayan ta zauna shi ma ya zauna ya dau food Menu dake saman table yana nuna mata na kusa da ita yace "Ki duba abinda za ki ci" Ita dai bata dau Menu din ba, yace "I am talking Halysaah" Without looking at him tace "Ko ma meye zan ci" Yace "Ohk" Tana danna wayarta yayi masu ordering abincin, mamaki Khaleesat ta dinga yi ganin amount of different type of foods that he ordered kamar za ayi karamin feast a wajen, abinci kuma masu tsadan gaske, da yawa cikin abincin da aka kawo masu sai a ranan ta fara ganinsu, duk da dai abincin turawa ne, drink ma ya kusa kala hudu ya siya masu, ta daga kai ta kallesa a karo na farko tace "Su waye za su cinye duk wannan?" Orange Crush ya dauka yana sha bai ce mata komai ba, after a while ganin bata fara cin abincin ba shi kuma sai cin abinda zai ci yake ya daga kai ya kalleta yace "Ko babu abinda kike so a nan ne?" A hankali ta dau Tacos daya, shi ko ya ci gaba da cin abincinsa, ƙasa ƙasa Khaleesat take kallonsa, ta lura yanda baya wasa da bacci haka baya wasa da abinci, because he didn't even mind she was in front of him abincinsa kawai yake ci sosai, ganin ko kallonta baya yi ta abincin gabansa kawai yake yasa ta ɗan saki jiki kadan ta fara cin abincin duk da ba sosai ba, ta ci iya abinda zata iya ci ta dau drink tana sha a hankali, sai a sannan ya daga kai ya kalleta after almost finishing his food yace "Ko dai a maki packaging abincin ki ci a gida, naga kamar kina kunyan ki ci abinci cikin mutane, or should i give u privacy?" Tana kallonsa a hankali tace "Privacy in an open restaurant? Ni nace ina kunyan in ci abincin?" Ya ɗan bude ido yace "Naga u ate just the Tacos bayan ga abinci da yawa a gabanki" Ta sauke idonta tace "Nafi son sa ne" Yana goge lips dinsa da tissue alamar ya koshi yace "Ohk, so now can i talk to you?" Shiru tayi na few seconds, sai kuma ta kallesa a hankali tace "Ohk" Ya karasa shanye drink dinsa yace "A nan America kika hadu da saurayin naki ko a Nigeria?" Khaleesat was silent, sai kuma ta sauke idonta tace "Nigeria" Yace "Ohk, but me kike tunanin yake janyo maku matsala tsakaninku?" Ta girgiza kai tace "Nima ban sani ba" Yace "Saboda ke ya taho nan daga Nigeria or he have a business here?" Ta gyada masa kai tace "Saboda ni ya zo" ya gyara zama yace "Kinga yana sonki kenan, sosai ma kuwa yake sonki, he left everything he was doing and came over just to see you, in na fahimta bai son kiyi sharing apartment da namiji a kasar nan ko?" Ita dai Khaleesat bata ce komai ba tana wasa da gefen mayafinta, yace "Sure... yana da gaskiyarsa, don ko ni bazan bar budurwata tayi communal living ba" Khaleesat ta daga kai ta kallesa, Yace "Yanzu dai kiyi kokari ki basa hakuri ku dai daita kanku, ni kuma i will think of another alternative for peace to reign between u and ur boyfriend, sannan shawaran da zan baki shine try all possible best ki dinga nuna masa abinda baza ki yi tolerating ba tun kafin kuyi aure, ya kamata ace akwai mutual understanding tsakanin ku, he look cool though kawai yana da hot temper ne and i notice insecurity na daya daga cikin matsalarku da shi, but you can definitely change him gradually Halysaah, so last maganar da zan maki ina ga ba abinda ya shafeni bane, kawai dai zan tunatar da ke Do's and don't din addininki ta bangaren relationship tsakanin mace da namiji" Khaleesat dai sauraronsa kawai take without looking at him, kuma taki ce masa komai tana kokarin fahimtar abinda zancensa na karshe ke nufi, shirun da taji yayi yasa ta daga manyan idanuwanta ta kallesa, at the same time ta kalli wa enda yake kallo a cikin restaurant din, 3 Guys ne suka shigo restaurant din gaba dayansu yan Africa, amma daya ne ɗan Nigeria a cikin su, guys din da ba yan Nigeria ba suka daga ma Housemate din nata hannu alamar girmamawa, and he waved back at them with smile on his face, Khaleesat ta dinga kallon daya mutumin da ya nufo su don ta ma ganesa, su sauran biyun kuma suka tafi yin abinda ya kawo su restaurant din, Mutumin na isowa kusa da table dinsu yana kallon Housemate dinta yace "Done with the power point?" Tuni kamshin turarensa ya cika wajen, Housemate dinta ya daga kai ya kallesa yace "Yau kuma har da kai za a ci abinci a nan kenan...." Yace "Not at all, i am getting some Steak for legend, meanwhile ashe kana nan" Housemate dinta yace "Yea, i came with my friend for Dinner" Khaleesat dai danna wayarta kawai take don mutumin yi yayi kamar bai san da Allah yayi ruwanta a wajen ba, ita ma ko kallon direction dinsa bata yi ba, Housemate dinta ya nuna masa bill dinsu yace "Get the bill cleared" juyawa mutumin yayi ya bar wajen yana tafiya irin ta ƙasaita, Khaleesat ta bi sa da kallon gefen ido, he was wearing a Jogger and a white Polo, ta dai ci gaba da danna wayarta, muryar Housemate dinta taji yace "That's my gee Halysaah, we share the same name with him...." Khaleesat ta daga kai without interest tace "Ohk" Yace "Sorry about his attitude, he isn't friendly, but i promise you he is good" Khaleesat tace "Likewise myself" Murmushi housemate dinta yayi sannan yayi excusing kansa ya mike ya nufi gun wanda ya kira da gee dinsa, daga inda take zaune taji mutumin na cewa "Kai kuma ina ka samo waccan yarinyar dake zaune kamar gunki bata iya gaisuwa ba, duk wani harkar raini ka iya ja ma mutane, that was how the other day da ka kawota karfe ukun dare a mota ta dinga kallon mutane kamar statue da aka dasa a gaban motar" Definitely yayi maganar ne ta yanda zata ji, Housemate dinta dake kallonsa yace "Ban gane bata iya gaisuwa ba, ba kai ka sameta a wajen ba, kayi mata magana ne kaga bata amsa maka ba?" Maimakon ya ba Housemate dinta amsar abinda yace sai taji yace "Na kai Legend gun Veterinary daxu" Taji Housemate dinta yace "Hope he is better now?" Mutumin yace "Let me get the bill cleared mu tafi gidan Mike yanxu...." Housemate dinta yace "No kayi tafiyarka zan yi dropping frnd dina first" Taji mutumin yace "Like seriously kai ko wani irresponsible being sae kace friend dinka, why are you stooping your self soo low Jay" Taji Housemate dinta yace "C'mon Ajay, come off it, this is so harsh..." Mutumin da ya kira da Ajay ya tafi ya bar sa gun a tsaye, Dawowa Housemate din nata yayi inda take, tuni ta mike tana gyara gyalenta without looking at him tace "Thanks for the dinner, kawata na kirana zan tafi gida" Housemate dinta yace "Ke kika kawo kanki da za ki koma ke kadai?" Taki kallonsa tace "Ae naga ur responsible frnds are here, so let me get going" Yace "Halysaah" ta daga kai ta kallesa, yace "Jira ni inyi clearing bill dinmu in yi dropping dinki gida" Yana fadin haka daya daga masu aiki a restaurant din ya nufosa da ladabi ya sanar masa anyi clearing bill din su, ya bi A-jay da ya fita daga Restaurant din da kallo, wa enda suka shigo tare na biye da shi a baya. Khaleesat bata yarda ta hada ido da Housemate dinta ba har suka fito daga Restaurant din zuwa inda yayi parking motarsa, sai da ya shiga motar sannan ita ma ta shiga ta zauna tana danna wayarta, bai tada motar ba ya kalleta, speaking calmly yace "Hope you are not offended Halysaah?" Without looking at him tace "Offended at what?" Yace "I don't really know" Ta kada baki tace "Ai ni ban yi kama da someone that isn't responsible ba balle in zama Offended at what a random stranger spew out, out of his ignorance, shi dai da bashi da manner shi ne babban irresponsible being, ai da ya fada a gabana yaji abinda zan gaya masa" Housemate dinta ya bude baki yana kallonta da mamaki looking completely speechless, bai yi tunanin taji abinda Ajay din ya fada ba, bai kuma yi tunanin tana ma da baki haka ba, after few seconds yayi kasa da murya yace "Pls kiyi hakuri Halysaah, bana son wannan yasa ranki ya bace, i purposely brought you out to cheer you up and make you lively don naga kamar kina cikin damuwa, amma ba don a kara bata maki rai ba, plss ignore Ajay's attitude, wani lkcn yana da problem i think today is one of those days" Khaleesat bata sake cewa komai ba but she is trying hard not to cry, ya ci sa'a ba yana tsaye gabanta ya fadi haka ba da tsaff zata mayar masa da baƙar magana dai dai da abinda ya gaya mata a wajen, Housemate dinta ya tada mota suka bar Restaurant din, hakuri ya dinga bata kamar shi ne yayi mata laifi har suka isa gida, direct dakinta kawai ta wuce, after like 40 mins ta fito wanka tana duba sleeping dress din da zata sa taji yayi knocking kofar dakinta, hijab din da tayi sallah ta dauka da sauri ta saka, bai bude kofar dakin ba har sai da taje ta bude tana kallonsa, yace "Sae da safe Halysaah, pls ki kwantar da hankalinki and get some rest, gobe kuma ki je school" ta sauke idonta bata ce komai ba, taji yace "Take care" Sai da ya juya ya bar wajen sannan ta daga kai ta bi sa da kallo cikin sanyin murya tace "Thank you so much, for..." Sai kuma tayi shiru, ya juya yace "For?" Ta langwabar da kai tace "The Dinner" Ya ɗan buda ido yace "My pleasure Halysaah" A hankali tace "But.... i don't... know, ur name" Yace "Oh really, amma ranan da na fara zuwa gidan nan ai nayi introducing kaina sai dai in kin manta, I am Ahmad Jawwad Yusuf, my frnds call me Jayy" Kallonsa Khaleesat ta dinga yi without blinking, yace "Are you okay with that?" Ta sauke idonta tace "Alright, i really appreciate you" Ya sakar mata murmushi yace "See yah tomorrow" daga haka ya bar wajen ta bi sa da ido har ya fita daga gidan gaba daya sannan ta juya a hankali ta koma dakinta ta kulle kofar. *Make ur payment before the end of free pages, kar a ji shiru* ✍🏻 07087865788 [5/9, 4:49 PM] khaleesat Haiydar ✍️: ✨✨HALYSAAH✨✨ ✍🏻 By _Khaleesat Haiydar_ 12..... Washegari da safe Khaleesat ta gama duk abinda zata yi a gida ta shirya ta tafi makaranta, tana zaune favourite spot dinsu ita da Safiyyah bayan sun fito daga aji, Safiyyah na facing dinta tace "Tsakaninki da Allah ina kika je jiya da yamma da naje gidan baki nan? Ni dai nasan babu inda kike zuwa a garin nan, ba kuma frnds gare ki ba, So where did u go?" Khaleesat da idonta ke kan jotting da tayi a aji tace "To ke meye na zuwa da yamma likis, i was expecting you around 5pm not 7pm" Safiyyah ta amshi takardan hannunta tace "Ina maki tambaya kina min tambaya, ko akwai abinda kika fara boye min ne Khaleesat?" Tagumi tayi tana kallon Khaleesat din da tuhuma, sai a sannan Khaleesat ta daga kai ta kalleta, dariya ta bata amma bata yi ba, kamar dai bazata ce mata komai ba sai kuma ta bude baki tace "Mun fita zuwa restaurant ne da Housemate dina" Safiyyah ta buda baki tana kallonta with surprise, can tace "Waw, really? Housemate dinki fa kika ce?" Sai kuma tayi dariya tana gyara zama idanuwanta kamar za su fito tace "Anya Khalee babu magana a kasa kuwa? Restaurant fa kika ce? How did he convince you har kika bi sa zuwa restaurant?" Khaleesat ta tabe baki tace "Toh meye kuma a kasa? Daga dai ya kai ni restaurant mu ci abinci? Kinsan yaushe rabon da inci abincin kirki a gidan?" Khaleesat ta sauke idonta a hankali tace "He notice i haven't been eating shi ne yasa har ya kai ni restaurant" Safiyyah ta sauke ajiyar zuciya tace "Ai kece da dora ma kanki abinda Allah bai dora maki ba kawata, akan Abdul din da naga yayi updating status da jersey jiya alamar har ya koma Nigeria ya ci gaba da harkokin gabansa ke kina nan kina neman kashe kanki, wallahi in zaki ajiye lamarin gayen nan a gefe da zai fi maki alkhairi a rayuwarki, very very heartless guy with no conscience, dubi tsabar zuciyarsa ta dutse ne ya gwammace ya kara siyan ticket yayi juyawarsa ya koma Nigeria, Allah ma yasa yayi maki ya jiki zuwan da yayi" Khaleesat dai tayi shiru tana kallon Safiyyah, Safiyyah ta daga kafada tace "Ga dai Housemate din nan naki duka duka yaushe har ma ku ka san juna? Amma ya gane kina cikin damuwa har da kai ki restaurant for dinner, to this is how a caring and understanding Boyfriend and a Gentleman should be" Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya a hankali tace "Ni babban damuwata kar ya sake dawowa kasar ban sani ba Sophie, ce masa nayi Housemate dina frnd din Nancy ne fa, kinsan bai san Nancy bata gidan ba ai har yanzu, to kar ya sake dawowa unexpectedly ya gansa" Safiyyah tace "Abinda zai faru kawai kiransa zaki yi ta yi har sanda ya ga daman daga kiranki, ki basa hakuri ki samu ku shirya, in har ku ka shirya duk wani movement dinsa zaki dinga sani, yanzun ma ai don baku communicating ne all this while shi yasa kawai ya taho kamar an jefosa, banda haka ai duk sanda zai zo yana gaya maki" Khaleesat tace "Haka ne, amma kin san irin zuciyarsa wallahi zan iya kiransa sau goma ma bazai daga ba, ko na masa magana ta WhatsApp bazai yi reply ba" a sanyaye ta kare maganar, Safiyya tace "Bari in kirasa ta wayana yana picking zan ce ya kirani, daga nan in ya kira sai in baki wayar ku yi settling dispute din karyan ku" Khaleesat tayi shiru bata ce komai ba, amma tasan hakan kadai shi ne way out, Safiyyah ta ciro wayarta ta fara kiran Abdul, har ya katse bai daga ba, ta sake kiransa sai gashi ya daga, sallama tayi masa ta gaishesa tace "Pls in ba damuwa ka kirani" Katse kiran yayi sai gashi ya kira tayi picking sannan ta mika ma Khaleesat wayar, Khaleesat ta amshi wayar gabanta na faduwa ta kai kunne, Safiyyah ta tashi ta bar ta a wajen ta koma wani waje ta zauna, a hankali Khaleesat tace "Don Allah kayi hakuri ka saurareni..." Shiru yayi da yaji muryarta, nan da nan hawaye ya cika idonta muryarta na rawa tace "Pls kayi hakuri da abinda ya faru, i promise you hakan bazai sake faruwa ba" Yace "Dama akwai abinda ya faru ne?" Tayi shiru bata ce komai ba, yace "I am asking you, akwai abinda ya faru ne dama?" Ta sunkuyar da kanta tace "Don Allah kayi hakuri, i am truly sorry plss" Yace "Look i am super busy now, idan kin shirya gaya min abinda ya faru kike ban hakuri sai ki kirani ta layin ki anjima" Cikin sanyin murya tace "Toh Nagode" Katse wayar yayi, ta juya tana kallon Safiyyah, Safiyyah ta kyabe baki ta dawo kusa da ita ta zauna tace "Ya ku ka yi da shi?" Khaleesat ta ja tsaki tana tattara reading material dinta tace "An gaya masa banda ina tsoron kar ya dawo without notice ni zan sake magana da shi ta waya ne" Safiyyah ta bude baki tana kallon Khaleesat tana tunanin yaushe bakinta ya fara budewa haka akan Abdul ne wai, Dariya Safiyya tayi tace "Shi Abdul din naki Khalee?" Khaleesat ta ki bata amsa, har ranta ita fa yanzu tana jin bazata iya ci gaba da tolerating abubuwan Abdul ba, ita kanta bata san daga inda wannan liver din yake zuwa mata ba, sai dai duk abinda zai faru ya faru but she is not tolerating anymore. Wajen karfe biyu ta koma gida, bayan tayi wanka tayi sallah ta sauya kayanta ta kwanta, sai bayan da tayi la'asar ta shiga kitchen ta jingina da cabinet tana tunanin abinda zata girka, tuwo taji take son ci, kawai daga karshe tayi deciding tayi tuwon since tana da duk ingredients din girka tuwon, kan kace me ta gama girka tuwo da miyar kuka with enough obstacles a ciki, ta gama goge gogen kitchen din sannan ta fito parlor wajen karfe biyar, dai dai shigowar Housemate dinta gidan, ita dai tana tsaye kusa da kitchen, ya juya ya kalleta bayan ya kulle kofar parlon yace "Good evening Halysaah" Tace "Good evening" Yace "What are you cooking with such a nice Aroma" Tace "Tuwo ne" Ya karaso cikin parlon yace "Really, it's been long na ci tuwo fa" Tana kallonsa tace "In kawo maka?" Ya dan buda ido yace "Ok thank you" Juyawa tayi ta koma kitchen din, ya zauna saman kujera hoping ba da yawa zata saka masa ba, ba a dau lokaci ba sai ga ta ta dawo parlon da plate dauke da tuwo with a diff bowl of soup, tun da ta duka ta ajiye abincin yake kallon bowl din miyan babu ko kiftawa, can dai ya daga kai ya kalleta yace "Wani miya ne wannan Halysaah?" Ta koma gefe tace "Miyar kuka ce" Lkci daya yayi yaƙe yana shafa kansa yace "Wow, but bana cin irin miyan, i thought vegetable soup ne, baki yi stew ba?" Ta wani kallesa, a takaice tace "Babu, kuma kayi tasting miyan ne kafin kace baka cin irin sa?" Ya jingina da kujera ya sauke ajiyar zuciya yace "Na ma ci abinci few minutes ago fa" Dukawa tayi ta dau bowl din ta mika masa miyan tace "Taste it first before concluding" Ya dan kalleta yana murmushin dole yace "Ok, where is the spoon?" Tace "Shi ba a cin sa da cokali ai, da hannu zaka sha" Yayi shiru sai kuma yace "Then bari in wanke hannu" Yana fadin haka ya mike, ta koma gefe don basa hanya sannan ta bi sa da kallo har ya tafi bandakin dake parlorn ya wanke hannu sai gashi ya dawo, bayan ya zauna ta mika masa miyan tana kallonsa, shi dai bai yarda ya hada ido da ita ba, tun da ya kai finger ya lasa miyan ya kai baki ya kasa dago kai, ita dai kallonsa kawai take bata ko kiftawa, can dai yana murmushi da kyar ya dago yace "It's sooo nice amma na ci abinci wallahi Halysaah" Duk da dariyar da ya bata ta dake tace "To ai tunda ka sa na zuba sai ka ci ko kadan ne cause i am not throwing it away" Bata jira cewarsa ba ta juye masa miyan a kan tuwon dake plate ta dau plate din ta mika masa tana kallonsa, he was totally speechless and confuse at the same time, tana kallonsa da kyau tace "Karba" Ya kai hannu a hankali ya amsa plate din tuwon, in ya debi tuwon sai ya dangwala miyar kamar yana tsoronsa sannan ya kai baki, sosai ya bata dariya amma fa bata yi ba, instead sai murmushi take, sau uku yana diban tuwon yana ci kuma har sannan yaki yarda su hada ido da ita, kana ganinsa kasan da kyar yake cin abincin, his facial expression says it all, wayarsa ne ya fara vibrate, ya ajiye tuwon da sauri ya fiddo wayar yana kallon screen, sai kuma ya kalleta yace "This is an urgent call Halysaah bari in shiga daki in daga" Kasa basa amsa tayi don kar ma tayi dariyar da take dannewa, ya mike ya nufi dakinsa da sauri don ko jiran jin abinda zata ce bai yi ba, tana ji ya sa ma kofar dakin makulli bayan ya shiga, sai a sannan ta zauna gefen kujera ta rike kanta tana dariya, after some minutes ta mike ta dau plate din tuwon still smiling ta wuce dakinta. Khaleesat na Voice call ta WhatsApp da Ummanta wajen karfe tara da rabi na dare taji Housemate dinta na knocking kofar dakinta, bayan tace ma Ummanta tana zuwa ta ajiye wayar sannan ta sauka daga kan gado ta saka hijab ta tafi ta bude kofar, yana jingine jikin bangon opposite din dakinta idonsa a kulle, yana jin bude kofa ya bude idon da sauri, kana ganinsa kasan daga bacci ya tashi, tun da ya shige daki daxu yace ana kiran wayarsa bata sake ganinsa ba sai yanzu, yace "Zan tafi sai da safe Halysaah, but pls ki dan kulle kofar i can't find my key" Ita dai bata ce komai ba tana kallonsa, he look so sleepy, ya ciro wayarsa dake ta vibrate a aljihu, tsaki yayi after picking yace "Kai dalla ina hanya" Daga haka ya mayar da wayar aljihu ya sake yi mata sai da safe ya juya ya fara tafiya, ta bi sa da kallo har ya isa parlor, jingina taga yayi ta bayan kujera ya rungume hannunsa ya rufe ido, Khaleesat ta sauke idonta sannan ta fito daga dakinta tana tafiya a hankali ta tafi parlon, bude ido yayi da sauri jin tafiya, sai kawai ya nufi kofar fita daga parlon, tace "Since u can't control ur self a ko ina ka samu bacci kake, be it standing, sitting, driving and even walking, then why not sleep over?" Ya dan kalleta jin abinda tace, nan da nan kuwa yaji baccin ya bar idonsa gaba daya, yana mata kallon mamaki at the same time yana sosa kai yace "Yaushe kika ga nake yin duk wannan da kika lissafa Housemate?" Ita dai ta rungume hannu tana kallonsa bata ce komai ba, ya dauke kai yace "I was only meditating ba wai bacci nake ba, in dai kika ga na rufe ido to i am meditating" Yana fadin haka ya nufi kofa ya bude yace "Good night, kar ki manta ki kulle kofar" Daga haka ya fita ya tura mata door din, ɗan murmushi tayi tana tafiya a hankali ta isa kusa da window ta dan bude curtain din tana lekansa, parking space taga ya nufa ya bude motarsa ya shiga, she is just hoping yana shiga bazai fara wani baccin ba a cikin motar, after few seconds taga ya fara reverse, ta sauke ajiyar zuciya tana kallonsa har ya bar Garage din ya dau hanya, sake curtain din tayi slowly, ta dan tsaya for few minutes sai kuma ta tafi daki ta dauko key dinta ta kulle kofar ta wuce dakinta, sake kiran Ummanta tayi ta WhatsApp, bayan Umma ta daga Khaleesat tace "Ko kin fara bacci ne Umma?" Umma tace "Aa idona biyu ina jiran ki, Abdul ya maki wata magana ne?" Khaleesat tayi shiru jin abinda Umma tace, ta girgiza kai tace "A'a bai ce min komai ba, me ya faru Umma?" Umma tace "Daxu Hasiya Matar Malam Saleh ta zo gidan nan" Sosai Khaleesat taji gabanta ya fadi, Malam Saleh aminin mahaifinta ne, yawanci abubuwa da yawa a bakin matarsa Ummanta ke ji tunda ba gaya mata baban nasu ke yi ba, abu da yawa ma sai dai taji a duniya ba dai a bakinsa ba, Khaleesat tayi karfin halin cewa "Me tace Umma?" Umma tace "Wai ko an tsaida maganarku da Abdul, haka dai tace min" Khaleesat was short of words, lokaci daya jikinta yayi sanyi, sosai maganar ta zo mata a bazata, she could feel her self tearing up, hankalinta yayi mugun tashi cikin lkci kadan, Umma tace "To ina jira dai in ga ko Malam din zai yi min magana, in ba ayi hankali ba kuma in ji a bakin matansa tun da su zai gaya masu ai, kuma kin ce Abdul din bai ce maki komai ba har yanzu ko?" Khaleesat ta goge hawayen da ya gangaro idonta, tana gyada kai da kyar kamar Umma na ganinta amma ta kasa cewa komai, Umma tace "Khaleesah?" Da kyar Khaleesat ta bude baki ta amsa don bata son Ummanta tasan kuka take, Umma tace "Naji kinyi shiru ne" Khaleesat ta dake tace "Ba komai Umma, ina duba wani karatu ne a takarda" Umma tace "To shikenan, kiyi karatun ki ma yi magana washegari ko?" A haka suka rabu, Khaleesat ta ajiye wayar hannunta ta kwantar da kanta saman pillow hawaye na sauka idonta, bata san menene ya sa all of a sudden taji she can't marry Abdul ba unlike before da har cikin ranta tasan bata da option dole ne aurenta da shi, tana kuma masa fatan ya canza wataran, yanzu kam bata jin haka a ranta, instead ji take bazata iya aurensa ba ma, Khaleesat bata yi wani baccin kirki ba daren ranan nan fargabanta daya kar ma yace a daura auren nan take, tasan in har suka ce ma iyayenta haka babu abinda zai hana a daura auren nan sai wani ikon Allah. Da safe Khaleesat ta tashi da ciwon kai sosai, kana ganinta kasan tana cikin damuwa ba kadan ba, haka dai ta shirya ta fita zuwa makaranta, warce take son tayi ma magana ta dan ji saukin abinda ke damunta sai bata shigo school ranan ba, wayarta ta ciro kawai tayi dialing number Abdul cause she can't hold it anymore, kiran na shiga ya katse ya kirata, ta daga ta kai kunne a hankali ta gaishesa, amsawa yayi yace "Ya aka yi?" At first tayi shiru, sai kuma tace "Ba komai i only called to greet you" Yace "Which side of the bed did you wake up from today da kika kirani ki gaisheni?" Tayi masa shiru, yace "ke dai fadi abinda kike so Malama, foodstuffs din ki ne ya kare ko me?" Ta hade rai tace "Yaushe ka siya da har zai kare?" Yace "Bazai kare ba dama mana tunda baki wani cin abinci sai cookies da kayan kwadayi" Ta wani turo baki bata ce masa komai ba, after few seconds tace "Kawai naji a jikina ne kamar da wani abu dake shirin faruwa shi sa na kira ka" Yace "Wani abu kamar me fa?" She was mute bata basa amsar tambayarsa ba, yace "Anyway, ko ma me kika ji a jikin ki haka ne, zan shiga meeting yanzu sai anjima" Katse wayar yayi a nan take, ta dinga kallon screen din wayarta wani tsanarsa na yawo a zuciyarta, a baya duk abubuwan da yake mata bata taba jin tsanarsa ba sai dai haushinsa yanzu kuwa kawai ji tayi ta tsanesa, ta ja tsaki ta mayar da wayarta jaka tana jin wasu hawaye na cika idonta, rashin zuwan Safiyyah makaranta ya sa bata tsaya su gama karatun ranan ba ta kama hanyar gida kawai cike da damuwa, tana jiran Lyft din da tayi ordering sai ga kiran Safiyyah ya shigo wayarta, tun daxu ta kirata bata daga ba sai yanzu ta biyo ta, Khaleesat ta daga ta kai kunne tana jin muryar Safiyyah tace "Baki da lafiya ne?" Da kyar Safiyyah tace "Tun jiya da daddare, na ma zata rasuwa zan yi kawata" Khaleesat ta ɗan bude ido tace "Me ya sameki?" Safiyyah tace "To ina ma na sani Khaleesat, Allah sa ba poison dina matar nan tayi ba don tun jiya sai yanzu nasan mutanen dake kaina" Khaleesat tace "Subhanallah, kina gida ne yanzu?" Safiyyah tace "Har da karin ruwa kuwa" Khaleesat tace "To bari in taho gidan yanzu" Khaleesat na maida wayarta jaka ta nufi gidansu Safiyyah, bayan tayi knocking kofar Surayya ta bude mata, Khaleesat ta sauke ido ta gaisheta, in ba kasa kunne sosai ba ma baza kasan Surayya ta amsa ba, Khaleesat taji muryar Mustapha na tambayar matar tasa wanene, ji tayi kamar ta juya ta fasa shiga cikin gidan, amma kasancewar a bude Surayya ta bar kofar yasa ta karasa ciki walking slowly, without looking at Mustapha dake parlor ta gaishesa, ya amsa yace "Ya karatun Khaleesat?" Khaleesat tace "Alhamdulillah, ya jikin Safiyyah?" Yace "Alhamdulillah, she is inside her room" Khaleesat ta juya ta nufi dakin Safiyyah, da gasken ruwa ta tarar ake kara mata don ta zata kawai tace mata haka ne don ta zo, Khaleesat ta zauna gefenta da damuwa tace "Sannu Sophie, ya jikin?" Safiyyah tace "Ba sauki Khaleesat, wallahi kilan abu matar nan ta saka min a abinci" Khaleesat tace "Don Allah ki dena cewa hka, kin ga yayanki ai bazai ji dadi ba in kina wnn magana" Safiyyah tace "Wallahi ita ce don lafiya na dawo gida jiya, ni na zata ma na rasu, sai da na farfado naga ba haka ba" Khaleesat tace "Allah dai ya baki lafiya, kin ci abinci?" Safiyyah tace "Ni bazan ci abincinta ba gaskiya tun daxu sai fruit kawai nake ta sha da lemon kwali" Khaleesat tace "Ko in je gida in maki girki? Me kike son ci?" Safiyyah tace "Ko tuwo da miyar kuka ne ki min in kina da ingredient, kawai shi naji nake so wallahi" Khaleesat tace "To ba damuwa, bari inyi sallah sai in tafi in maki girkin" A haka Khaleesat tayi sallahn azahar ta bar gidan bayan tayi ma Surayya da mijinta sallama, Mustapha ne ma ya tambayeta har zata tafi, Shine tace masa zata dawo anjima, Khaleesat na isa gida taga motar Housemate dinta a Garage, tana bude kofar ta shiga parlor ta gansa kwance kan 3 seater yana bacci, har ta kulle kofar bata ga ya bude ido ba, ta nufi dakinta ta shiga ciki ta canza kaya sannan ta fito ta shiga kitchen, tuwon ta dora har zata fara hada ingredient na miyar kukan sai kuma ta fasa taji gwara tayi vegetable soup kawai, ita kanta bata san menene yasa take son yin vegetable soup din ba duk da bata wani son cin miyar ganye she prefer slimy soup, sai da ta gama tuwon sannan tayi ordering lyft da zai kai ta nearest African store da zata iya siyan ingredients din miyan Vegetable. *Make ur payment before the end of free pages* _Halysaah is just 500 naira_ ✍🏻 07087865788 [5/10, 10:07 AM] khaleesat Haiydar ✍️: Read My Book "HALYSAAH" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=681294ff01c6bd900451c8e6 ✨✨ HALYSAAH✨✨ ✍🏻 By _Khaleesat Haiydar_ 13.... Har Khaleesat ta fita daga gidan zuwa Supermarket Housemate dinta bai tashi ba, bayan ta dawo sai bata gansa a parlor ba alamar ya shiga dakinsa, kafin karfe hudu da rabi na yamma Khaleesat ta gama miyan da take, tayi dishing ma Safiyyah abincin a warmer din da zata kai mata, kan kace me aroma din girkin ya cika gidan, ko tuwon bata ci ba ta tafi dakinta tayi wanka tayi alwala tayi sallan la'asar sannan ta shirya, fitowa parlor tayi ta nufi kitchen, tsaye ta ga Housemate dinta ya jingina da cabinet din kitchen din idonsa a lumshe, ya dora lipton a gas, tace "Bacci kake a kitchen din?" Bude ido yayi ya juya ya kalleta yace "Not at all" Tace "To me kake yi?" Ya dan shafa kansa yace "I am having a terrible headache" Tayi kasa da murya tana kallonsa tace "Ka sha magani?" Ya kashe gas din yace "Zan sha" Tace "To in sa maka abinci?" Yace "What did you cook?" Tace "Tuwo...." Bai jira ta karasa ba da sauri yace "A'a, Alhamdulillah, am full" Murmushi tayi tace "To ai ba miyar kuka bane, vegetable soup ne" Tana fadin haka ta bude masa tukunyar miyar tana kallonsa, bayan ya ga miyar a hankali yace "Ohk, but let me dish the food my self" Ita dai bata ce masa komai ba ya dau plate ta nuna masa inda tuwon yake, kallon dan tuwon da ya zuba ta dinga yi, sai kuma tace "Wannan dan kadan din?" Without looking at her yace "Zai isheni" bata sake cewa komai ba ya zuba miyar a gefe with just one protein ya saka spoon a gefe, sannan ya dau mug ya debi lipton da ya dafa ya dau plate din tuwon yace "Thank you" Bin sa tayi da kallo har ya fita daga kitchen din. Ko da ta fito parlor da abincin Safiyyah ta samesa zaune kan kujera bai fara cin abincin ba, ya daga kai ya kalleta, ta dau handbag dinta dake saman kujera, yace "Are you going out with food?" Tace "Yea, kawata zan kai ma abinci she is sick" Yace "Ohk Allah ya bata lafiya" Tace "Ameen" Daga haka ta fita daga gidan. Har kusan Magrib Khaleesat na tare da Safiyya, sosai jikin Safiyyah yayi sauki sai labari take ma Khaleesat da tayi shiru hankalinta baya kan hirar, da ta tuna maganar da Ummanta tayi mata jiya da kuma abinda Abdul yace mata da ta kirasa daxu sai taji duk duniyar tayi mata zafi babu abinda ke mata dadi a rai, Safiyyah da ta kula da yanayin Khaleesat tace "Wai me ke damun ki ne kawata?" Khaleesat ta kalleta, sai kuma ta dan yi murmushi tace "Bakomai Sophie, kawai na gaji ne sosai har na fara jin bacci" Ba don khaleesat bata son gaya mata damuwarta bane yasa tace mata haka sai don bata son fadin damuwar tata a wnn lkcn, but tasan dole zata gaya ma Safiyyah abinda ke faruwa, Safiyyah tace "To ki kwana a nan mana tunda bamu da lectures gobe, it's already pass 7 yanzu" Khaleesat ta dan bude ido tace "In kwana a ina? A'a ni dai kin ga tafiyata" duk yanda Safiyyah ta so convincing Khaleesat ta kwana gidan, khaleesat ta ki sauraronta tayi sllhn magariba ta kama hanyar gida, dama tun da ta kawo tuwon da tayi ma Safiyyah daxu Mustapha ya shigo har dakin ya diba ta zama uncomfortable zama a gidan, matarsa kuwa ta kasa ta tsare a parlon gidan, ko da ta fito parlorn ita kadai ta samu zaune fuska a murtuke, Khaleesat tayi mata sallama ita dai har ta fita daga gidan bata ji ta amsa mata ba. Khaleesat na isa gida ta kulle kofar parlon ta karasa ciki tana kallon plate din dake saman kujera da yayi covering with another plate, mug din shayin ma na ajiye bai sha ba, ta tafi ta bude plate din tuwon taga bai ci ba, abinda ya fada mata a kitchen ne daxu ya fado mata that he is having headache, ta juya tana kallon kofar dakinsa, tana tafiya a hankali ta nufi dakin tayi knocking gently, sai da ta sake knocking jin bai amsa ba ta ɗan bude kofar slightly, bacci ta gansa yake yi saman gado, ta sauke idonta kasa, lkci daya ya bude ido yana kallonta, ta ɗan koma baya kamar mara gaskiya tana kame kame tace "Are you okay?" Kansa kawai ya nuna mata ta karasa cikin dakin ta duka ta side dinsa da damuwa tace "Baka sha maganin bane?" Bai yi responding ba hakan yasa ta kai hannu kusa da forehead dinsa sai dai bata taɓa sa ba, amma she could feel he is running temperature, a hankali tace "Should i order an Uber ride sae kaje asibiti?" Ya girgiza mata kai idonsa a lumshe, rasa abinda zata yi tayi, lkci daya taji hankalinta ya tashi, mikewa tayi ta fita zuwa dakinta ta dau karamin towel tayi soaking dinsa da ruwa bayan tayi squeezing ta dawo dakin, ta nufi inda yake kwance ta duka kusa da shi ta dora karamin towel din da ta linke saman forehead dinsa, ya bude idonsa, cikin sanyin murya tana kallonsa tace "In yi ordering ride din?" Ya dafe towel din da ta dora masa a forehead yace "Don't worry Halysaah" ita dai kallonsa kawai take, can ta tuna tana da pain reliever a daki, mikewa tayi dai dai nan taji kamar ana kwankwasa kofa a parlor, ta juya ta nufi kofar ta fita zuwa parlorn, tsaye tayi bakin kofar parlon tana tambayar waye at the same time tana bude kofar, ta ɗan koma baya tana kallonsa with surprise, shi ma daga sama har kasa yake kallonta hannunsa rike da wayarsa, su biyu ne tsaye bakin kofar, lkci daya ta hade rai tace "How may i help you?" Kai tsaye shi wanda yake mata kallon sama da kasa ya shigo parlon har sai da ta matsa gefe da sauri kar ya bangajeta, shi dayan mutumin dake tsaye bakin kofar calmly yace "Hello, plss is Jay in here? Ahmad Jay...." Mutumin da ya shiga parlon ya juya yana masa wani kallo yace "Kaii wajenta ka zo halan?" Shi wanda ke waje ya ɗan yi murmushi ya shiga parlon ya sauke kai kasa, amma sai ya tsaya daga bakin kofar bai karasa can cikin parlon ba, shi ko wanda ya fara shigowa har ya nufi hanyar dakunan dake apartment din, da sauri Khaleesat ta nufesa a fusace tace "How will you just barge into someone's apartment without excuse or an explanation?" Juyawa yayi ya kalleta from head to toes, ita kanta bata san me yasa ta tsaya ɗan nesa da shi ba taki ci gaba da bin sa ba amma bata fasa masa kallon da take masa ba fuska a daure, ya gyada kai ya ci gaba da tafiyarsa kamar yasan dakin, kawai taga ya bude ya shiga ciki, ta juya ta kalli mutumin dake tsaye har sannan a parlor tace "Ku haka ake yi daga inda ku ka fito?" Cikin nutsuwa mutumin yace "We are sorry Madam, location shi Jay din ya tura masa wai bashi da lafiya and here is the location sannan mun ga motarsa a garage din apartment din nan, hope we are in the right place?" Khaleesat tace "Sai bayan kun shigo za ka tambayeni ko kuna right place din?? Where Is it done this way?" Mutumin ya hade hannunsa biyu alamar bada hakuri yace "Kiyi hakuri dai" Yana fadin haka ya bi bayansa ya shiga har cikin dakin shi ma, bin su tayi amma ta tsaya a corridor, ji tayi wanda ya fara shiga dakin da farko na cewa "Jay me kake yi a gidan nan da wannan karamar yarinyar da bata da manners? Is this the reason why ka dena zama 24/7 a gida yanzu? When did u start this useless life? First of all who is the little brat i want to know?" Da wani expression yake kallon Jay dake fama da kansa a kwance yaki basa amsa, shi dai mutumin da ya shigo a karshe na tsaye daga daya gefen Jay yana masa sannu, sai kuma ya kalli Ajay calmy yace "Kaga dai bashi da lafiya yanzu Ajay, all this question isn't necessary now" Da kyar Jay yace "Ka kyale ɗan iska mana, laifina ne da na tura masa location" Ajay dai sai bin dakin da kallon mamaki yake yi ganin property din Jay duk a dakin, can ya kallesa yace "To ma menene yasa za ka kirani? in baka da lafiya ita yarinyar ta kai ka hospital mana, ba tare ku ke zama a gidan ba" Mikewa zaune Jay yayi yace "Kai wai did you know how i am feeling? Ka wani zo nan ka isheni da unnecessary surutu, pls get out Ajay, gerrout pls" Khaleesat dake sauraron conversation dinsu ta wani taɓe baki ta juya ta koma parlor ta zauna wani mugun haushin mutumin da taji ana kira da Ajay take ji a ranta, taga Abdul ma balle shi, Salem ya mika ma Jay hannu zae taimaka masa ya tashi, Jay yace "Pls kace mata ta kawo min bottle water, or you check the kitchen ka dauko min" Salem ya juya ya fita, Ajay dake taɓe baki ya juya ya fice daga dakin shi ma, direct ya nufi kofar fita daga apartment din yayi ficewarsa ya koma can waje ya tsaya jikin motarsa, Salem dai ya bi sa da kallo ya sauke ajiyar zuciya ganin fita yayi, sannan ya kalli Khaleesat ya gaya mata ta dauko ma Jay ruwa, ta mike ta tafi kitchen ta dauko ruwan ta basa, ba a dau lokaci ba sai ga shi sun fito tare da Jay, mikewa tsaye tayi tana kallonsa, Jay ya zame hannunsa a na Salem ya zauna saman kujera ya jinginar da kansa da kujeran ya lumshe ido, a hankali Khaleesat tace "Amma hospital zaku je ko?" Da kyar yace "No, gida za mu je ya min treatment" Khaleesat tace "To Allah ya sauwake, Allah ya baka lafiya" Ya gyada mata kai sannan ya mika ma Salem hannu ya mike tsaye, Khaleesat na son tambayarsa abu amma ta kasa, ganin za su fita daga parlon ta dake tace "Can i get ur digit so i can be checking up on you?" Salem dai ya juya ya kalleta da ɗan mamaki jin tambayar da tayi, does this mean basu san juna ba kenan tunda har bata da lambarsa, Housemate din nata ya juya ya kalleta yace "Ai zaki gane gidan da muka je ranan da na mance makulli da daddare bayan kin dawo Nigeria, that's our home, zaki iya zuwa at anytime...." Khaleesat dai ta dinga kallonsa, sai kuma yace "Salem give her my digit, ko kuma ka bata nata kar ta kira bata sameni ba" Salem yace "Ohk bari in bata nawa" Khaleesat ta dauko wayarta sannan ta amshi number Salem, bayan ya gama bata suka fita daga parlon tare da housemate din nata, tana tafiya a sanyaye ta karasa gun window ta bude labule tana kallonsu, sae da suka fito Ajay ya shiga motarsa, bayan sun shiga yayi zoom off. Khaleesat ta sauke idonta sannan ta juya a hankali ta koma cikin parlon. Bayan kwana uku Khaleesat sun fito daga aji tare da Safiyyah dake waya, ita dai Khaleesat na tafiya ne amma gaba daya hankalinta na wani gun daban, Safiyyah tace "Wai ya jikin Housemate din naki yanzu? Ko ya dawo ne baki gaya min ba?" Khaleesat ta kalleta tace "Har yanzu ai bamu yi magana da shi ba" Safiyyah tace "To wanda ya baki number sa fa ko har yanzu bai daga kiran naki ba?" Khaleesat tace "Aa ya daga jiya, amma sai yace min he is much better, da na tambayesa ko yana kusa sae yace min a'a yana bacci, kawai ni dai i hope da gasken jikin nasa da sauki..." Safiyyah tace "Shegen mutumi in ba kinibibi ba me yasa zai wani ƙi baki lambar Housemate din naki sai na shi, me za kiyi da lambarsa when u have no business with him, in ni ce ke cewa zanyi a'a ba nasa zai ban ba gaskiya, amma fa har yanzu abun na ban mamaki ace duk mutuncin Housemate din nan naki bai taɓa requesting phone number din ki ba ko sau daya, ji ma sanda kika je Nigeria, to ko me yasa oho" Ita dai Khaleesat kallonta kawai take bata ce komai ba, Safiyyah tace "To wai ma ba kince har cewa yayi ki je gidan nasu ba, tun jiya nake ce maki mu shirya mu je kin ki, in baki je kin dubasa ba ta yaya zai san kema kin damu da halin da yake ciki, ai ance gaida me gaisheka, beside da bakinsa ya maki kwatancen gidan nasu ai, to me yasa baza ki je ba, da Nigeria muke sai mu ce ai bai kamata ba saboda yan sa ido da yan fassara lamari but this is USA Khaleesat, kuma abu ai kamawa yake for 3 days baki san halin da mutumin nan yake ciki ba gashi ke kanki kina testifying kyawawan halayyarsa, wallahi ki shirya in rakaki mu je ki dubasa da jiki, kuma kafin nan mu fara biyawa ta shopping mall kiyi masa shopping da zaki kai masa, shi ma sae yaji dadi wallahi" Khaleesat tace "Kawai sai in kama tafiya har gidan nasu duba shi? Ai bai ma dace ba sai kace wasu marasa kamun kai Safiyyah, be it in USA still bai dace ba, mu mata ne fa" Safiyyah ta mata wani kallo, can tace "Ai da naki matsalar ya taso haka ya cire kudadensa sama da miliyan goma sha biyar ko fin haka if i am not mistaken yayi solving maki matsalar ki, shi kuma bai da lafiya rai kwakwai mutu kwakwai kince zuwa dubasa rashin kamun kai ne, to rashin dacewa ya wuce zaman da ku ke yi gida daya? Shi wannan me za ki ce masa? Wani lokacin baki ma nazarin maganar dake fitowa bakin ki Khaleesat, in zuwa dubasa bai dace ba to zamanku gida daya ma ai bai dace ba be it in USA" Khaleesat dai sai kallonta take ta kasa cewa komai, can dai tace "Ban gane ba, Miliyan goma sha biyar for what??" Safiyyah ta mata wani kallo tace "Ohh for what ko? da yake business class ticket din da ya siya maki an gaya maki na wasan yara ne ai, to bari ki ji Business class ticket kusan 5000 dollars ne base on Airline, ki lissafa 5000 ko 4000 dollars kudin Nigeria kiga nawa zai baki" Khaleesat was speechless after realizing Safiyyah is saying the truth, banda dala dubu dayan da ya bata da zata tafi, sannan ga kuma domestic flight ticket from lagos to kano, and from kano to Abuja, bata mance irin hotel din da ta zauna na few hours a garin Lagos ba, sauke idonta kasa tayi bata sake cewa komai ba, Safiyyah ta ja tsaki tace "Wallahi ki ajiye wnn kauyancin naki ki zama wayayyiya ki dinga yin abun da ya dace, komai a rayuwar nan kamawa yake Khaleesat, to wai ku ka zauna apartment daya ba ace rashin kamun kai ba sai don zaki je dubasa bai da lafiya? ni abinda ke daure min kai kenan" Khaleesat dai taki cewa komai with many thoughts running her mind, a haka dai suka rabu kowa ya tafi gida... The next day sai da Safiyyah tasan duk yanda tayi convincing din Khaleesat da dadin baki da masifa da bacin rai, daga karshe Khaleesat ta yarda su je can inda Housemate dinta yace gidansu ne su dubosa amma fa don babu yanda ta iya da Safiyyah ne don har cikin ranta tsoron zuwa anguwan take don unguwa ce na masu kudi a kasar, to in ma sun je su ce me ya kai su? What if iyayensa ko wasu yan uwansa mata na gidan sai su yi yaya kenan? Kasa hakura tayi har sai da tayi ma Safiyyah wannan tambayar, Safiyyah tace "Dai dai kenan in ma iyayensa na gidan, ai ba Nigeria bane nan USA ne, kuma tsaf za su amshe mu hannu bibbiyu su yi farin ciki da zuwan mu don duba ɗan su muka je yi bai da lafiya" Khaleesat ta sauke wani boyayyen ajiyar zuciya, Safiyya tace "Amma ni har raina ina son sanin dalilinsa na dawowa apartment dinki ya zauna bayan ga nasu gidan can, nace da wani abu a kasa kince min ba haka ba, wallahi kilan ya san ki from somewhere Khaleesat" Khaleesat tace "Sai kuma kiyi ai, nace maki bamu taɓa sanin juna da shi ba" Safiyyah tace "Ma ji ma gani dai" Sai da Safiyyah ta fara jan Khaleesat zuwa inda za su siya kayan ciye ciye sannan suka yi ordering Uber da zai kai su unguwan, tun da suka shigo Safiyyah ke kallon manyan Gidaje with fascination, Khaleesat kuwa gabanta sai faduwa yake sai addu'a take a ranta, ita banda Safiyyah tayi insisting da babu abinda zai kawota wai duba Housemate dinta, dai dai kusa da gidan Uber din ya tsaya duk suka sauka, Safiyyah dake zaro ido tana kare ma Glass house din kallo tace "Ke kin tabbata nan ne kar mu shiga gidan mutane a kira mana 911 mu shiga uku Khaleesat" Khaleesat bata san sanda tayi dariya ba amma bata tanka ma Safiyyah ba, Khaleesat ta ciro wayarta tayi dialing number Salem ita kanta zuciyarta bugawa yake gaba daya she is afraid, sai da kiran ya kusa yankewa ya daga, sai gashi a mota zai fito daga cikin gidan, sauka yayi daga motar ganinsu, yana kallon Khaleesat da mamaki yace "Ohh you are here, sannu da zuwa...." Gaishesa tayi ta sauke idonta kasa kamar munafuka, ya amsa da fara'a, Safiyyah ma ta gaishesa sannan tace "Dama ta zo duba jikin Housemate dinta ne shi ne na rakota" Yana gyada kai yace "Ohh that's so thoughtful of her, mu je ciki to...." Suna biye da shi suka shiga cikin katon gidan, Safiyyah dai sai gwale ido take tana bin gidan da kallo ta gefen ido, ita dai Khaleesat gabanta sai faduwa yake sosai ko daga kai ta kasa, after walking briefly sai gasu sun iso entrance din shiga parlon gidan, kofar shiga parlon ma kadai sai ka kalla ka sake kalla, Safiyyah ta saci kallon motoci uku dake compound din kuma masu tsada, suna shiga parlon gidan Khaleesat ta hada ido da Ajay dake zaune kan kujera ga different fruits daga gefensa yana kallon abu a wayarsa at the same time yana cin apple dake hannunsa, 3 quarter ne baƙi a jikinsa with gray polo, tuni ta dauke idonta tsabar yanda ta rikice bata ma san sanda ta bude baki ta gaishesa ba tana makale bakin kofa, hade rai yayi ya dauke kai ya ci gaba da kallon abinda yake a wayarsa. ✍🏻 07087865788 [5/11, 5:06 PM] khaleesat Haiydar ✍️: ✨✨HALYSAAH✨✨ ✍🏻 By _Khaleesat Haiydar_ 14.... Safiyyah ma dake kallonsa kamar munafuka tana in-ina tace "Good... good evening sir" Without looking at Safiyyah ya amsa yana cin apple dinsa, Salem na kallonsa speaking calmly yace "Ajay sun zo duba jikin Jay ne" Ajay ya ajiye apple din hannunsa, sai kuma ya kai wayarsa kunne alamar bashi da lkcn basa amsa, ganin haka Salem ya juya ya kalli su Khaleesat yace "Bari in masa magana a sama, za ku iya zama ku jira ni, have a sit pls" Daga haka ya nufi stairs, ko haurawa saman bai yi ba Khaleesat ta zaro ido tace "Innalillahi" da sauri ta koma bayan Safiyyah ganin wani jibgegen kare ya nufo su yana haushi, Safiyyah ta dinga buga ma karen jakar hannunta tana koransa ita ma a tsorace, Salem ya dawo parlon da sauri ganin haushin da karen ke yi zai yi attacking dinsu, Ajay ya mike ya nufi karen yana kiransa yace "C'mon Legend" Karen ya juyo da gudu ya dawo gun Ajay da yayi patting din kansa, Salem ya dawo kusa da su yana murmushi yace "Mu je saman kawai tunda tsoron kare ku ke, ai ba abinda zai maku kawai yaga baƙin fuskoki ne shi yasa" Khaleesat da jikinta ke rawa ta bi bayan Salem da sauri Safiyyah na biye da ita, a haka Salem yayi leading dinsu har sama zuwa Bedroom din Jay, knocking yayi yana tsaye bakin kofar, Khaleesat sai waige waige take tana ganin kamar karen zai sake biyo su saman, sai da Jay ya amsa ma Salem knocking din da yayi sannan ya kallesu yace "Bari in sanar masa yana da baƙi" Daga haka ya bude kofar dakin ya shiga ciki ya kullo, Safiyyah ta rike haɓa ta kalli Khaleesat murya can kasa tace "Ke wani tantirin ɗan iska ne wannan muka gaida a kasa ya mana walakanci haka?" Khaleesat bata tanka ta ba, har sannan kuma bata daina waige waigen da take ba don gani take fa karen nan zai iya biyo su har sama, sai ga Salem ya fito daga dakin yana kallonsu yace "Za ku iya shiga, ni zan ɗan fita sai na dawo" a hankali Khaleesat tace "Ohk mun gode" Bude kofar dakin tayi still gabanta na faduwa ta shiga cikin massive room din da sallama Safiyyah dake gwale ido na biye da ita a baya, wani ɗaddadan kamshi hade da sanyin Ac ne yayi welcoming dinsu a cikin babban dakin, Housemate din nata na zaune saman makeken gadonsa alamar Salem just woke him up, his room was just something else wajen tsaruwa da haduwa, Khaleesat taki yarda ta hada ido da shi zuciyarta na bugawa ta zauna nan ƙasan lallausan carpet din dakin, a hankali yace "C'mon Halysaah, ga gefen gado ku zauna, ko ku zauna kan kujera" Khaleesat bata dago kanta ba tace "I am comfortable here" Ya lura kamar she is frightened, ya kalli Safiyyah dake kallonsa bayan ita ma ta zauna, dan murmushi yayi mata yace "Hello...." Kana jin muryarsa kasan he is still recovering, Safiyyah ta gaishesa da fara'a tana tambayarsa jikinsa, yace "Alhamdulillah, ya karatu?" Tace "Alhamdulillah" Ya kalli Khaleesat yace "Ya kwana biyu Housemate? Hope you are doing good?" Sai a sannan ta daga kai ta kallesa tace "Ya jiki?" Yana murmushi yace "Da sauki, Alhamdulillah" A hankali tace "To Allah Ubangiji ya sauwake ya kara lafiya" Yace "Ameen ya Allah" Safiyyah ta ajiye ledan hannunta kusa da gadon dakin tace "She got you this" Khaleesat ta kalleta, godiya yayi masu gaba daya, sai kuma ya fara kokarin sauka daga saman gadon yace "Bari in kawo maku ruwa" Edge din gadon ya zauna kamar bazai iya tashi ba, Khaleesat tace "Aa mun gode, we are okay" Ya kalleta a hankali yace "To ai ba ke kadai nayi offering ba Housemate" After some seconds ya tashi ya bude portable Fridge din dake dakin ya dauko masu ruwa da tsadaddun lemuka duk ya ajiye masu sannan ya fita daga dakin walking slowly, exactly irin kayan jikin Ajay ne a jikinsa shi ma, Safiyyah ta rike haba tana kallon Khaleesat bayan ya fita, sai kuma tayi kasa da murya tace "Khaleesat kin dai ga arziki ko? Gidansu kenan fa a Amurka ina ga Nigeria kuma?" Khaleesat ta hade rai tace "Pls stop this Safiyyah" Safiyyah ta rufe baki da sauri, sai kuma tayi kasa sosai da murya tace "Kuma haka fa, kar ace da Cctv a dakin mu ji kunya" Khaleesat ta wani kalleta tace "Ki ji kunya dai, tun da mun gaishesa ki tashi mu tafi kawai" a hankali Safiyyah tace "Gaskiya Housemate din nan naki is more than nice and calm, ni har naji yana burgeni wallahi, look how he welcomed us warmly duk da bashi da lafiya" Khaleesat ta daga ido ta kalleta sai dai bata ce komai ba, ita dai Safiyyah sai bin katon dakin take da kallo with fascination, tayi kasa da murya tace "In na samu irin wannan dakin ai mance me ya kawo ni kasar ma zan yi gaba daya, anya ma kuwa student ne Housemate din nan naki" Khaleesat ta hade rai tace "Tashi mu tafi tunda mun dubasa Safiyyah" Safiyyah tace "Amma ai kya jira ya shigo mu yi masa sallama ko, dadina dake a ko ina sai kin nuna halin ki, kamar ana koranmu daga shigowa gida kice mu tashi mu tafi" Budewar kofar dakin ya sa duk suka yi shiru, Housemate dinta ya shigo da sallama ya zauna kan kujeran dakin ya jinginar da kansa da kujeran, sai ga wani chef din gidan ya shigo da wasu tsadaddun cookies ya ajiye masu kusa da su, sannan ya juya ya fita, Jay na kallon Khaleesat yace "Naga kina son cookies sosai Housemate, here are some for you and ur frnd" Bata yarda ta kallesa ba tana wasa da gyalenta tace "I am okay, tafiya ma za mu yi" a hankali yace "So soon? Amma sai kun ci cookies tukun" Khaleesat ta ɗan kallesa suka hada ido a karo na farko tun shigowarsu dakin, sosai taji gabanta ya fadi tayi saurin sauke idonta, ya kalli Safiyyah yace "In bazata ci ba ke ki ci abunki... Amma ban san sunanki ba kawar Housemate" Safiyya tayi murmushi tana bude cookies din ta dau guda daya tace "Sunana Safiyyah Adam" Yace "Maa sha Allah, it's nice meeting you Safiyyah, i am Jawwad Ahmad, or you call me Jay" Safiyyah tace "Nice meeting you too Jay" ita dai Khaleesat wasa da gefen veil dinta kawai take kanta a kasa, Safiyyah ta bude handbag dinta saboda kiran wayarta da ake yi, tana dubawa taga Cousin brother dinta ne, ta mike tace "Let me pick a call pls" Jay yace "Alright Safiyyah" Kofa ta nufa ta bude ta fita sannan ta kullo masu kofar, ledan da suka shigo dakin dashi ya ɗan bude yace "You got me all this Halysaah" Khaleesat ta ɗan kallesa tace "Um" Yace "Ohk thank you so much i really appreciate" Tana kallonsa a hankali tace "Ya jikin?" Yace "I am getting better gradually, daxu sai naji ina sha'awar wannan tuwon da kika yi some days back" Tana kallonsa tace "Na vegetable soup?" Yace "No, wannan da na kasa ci, the dark soup, I can't remember the name" Bata san sanda tayi murmushi ba tace "Ok miyan kuka?" Yace "Shi... kawai naji shi nake son ci sincerely" a hankali tace "Ohk zaka je can gida anytime soon ne?" A hankali yace "Idan na samu lafiya in sha Allah" Ita dai Khaleesat kallonsa kawai take, shi kam idonsa na gun different direction, Ajay ne ya bude kofar dakin, kai tsaye ya shigo ya nufi Jay yana mika masa wayar hannunsa yana kallonsa, ita dai Khaleesat ta sunkuyar da kanta bata kalli inda yake ba, Jay ya amshi wayar yana duba screen din, sauke ƙafafuwansa yayi daga kan kujeran da yake zaune ganin wanda ke kan layi, ya kai wayar kunne da ladabi yayi sallama hade da gaisuwa, sai kuma yace "Alhamdulillah Abba da sauki, wayar a silent yake ne shi yasa" Sai kuma ya daga kai ya kalli Ajay jin abinda Abban ke ce masa, a hankali yace "A'a ba haka bane Abba, i do eat... but not much, ba gaskiya ya fada ba" Daga haka yayi shiru bai sake cewa komai ba, after a minute yace "To in sha Allah Abba, Allah ya kara girma" Sai da ya jira Abba ya katse wayar sannan yayi wurgi da wayar saman gadonsa yana kallon Ajay, wani kallo Ajay yayi masa ta gefen ido ya juya ya tafi ya dau wayarsa a kan gadon sannan ya fice daga dakin, Khaleesat ta gama tura ma Safiyyah text din da take na cewa tayi masu ordering Lyft su tafi gida, sai kuma ta daga kai ta kalli Jay, ganin mood dinsa ya canza, a hankali tace "Baka cin abincin ne ko?" Yace "Ki kyalesa mana, i took cereal daxu da safe kuma a gabansa, shi in bai bata min rai ba baya jin dadi a rayuwarsa" Khaleesat tayi shiru kamar bazata ce komai ba, can dai tace "To ai Cereal ba abinci bane, ka dai dinga ci ko kadan ne" Ɗan murmushi kawai yayi bai ce komai ba, tace "Shikenan, za mu koma, Allah Ubangiji ya baka lafiya" Yace "Baza ki bari Salem ya dawo yayi dropping din ku ba?" Tace "Aa, Safiyyah nasan brother dinta ne ke kiranta a waya, kaga tun daxu muka gama lectures bata koma gida ba" Yace "Ohk ni bari in ajiye ku" Khaleesat ta zaro ido tace "Aa kai da baka da lafiya, za mu yi ordering Uber do not worry about us pls" Khaleesat ta mike, yana ganin haka shi ma ya tashi, amma sai da ya dafa kujera for sometime saboda juya masa da kansa ya fara yi, A hankali Khaleesat tace "Pls kar kayi stressing kanka, just lie down and rest" Ya dago kansa yace "No, let me see you downstairs" Juyawa tayi ta nufi kofa, ya bi bayanta, ga mamakinta sai ta ga Safiyyah tsabar samun waje tana zaune parlon dake upstairs tana kallo tana cin cookies ga lemo a gabanta, to a ina ta samo lemun da cookies, Safiyyah ta washe baki ganin Khaleesat sannan ta mike tace "Shikenan mu tafi?" Jay da ta hango ne yasa tayi tsit, Khaleesat ta nufeta suka fara sauka downstairs a tare amma gabanta faduwa yake kar su kara ganin karen daxu, hakan yasa ta bari Safiyyah ta shiga gaba, Jay na biye da su a baya har suka sauko downstairs, ai ko karen na ganinsu ya nufo su da gudu yana haushi, Khaleesat ta juya a tsorace zata koma sama ta ci karo da Housemate dinta dake bayanta, ya rikota da sauri yace "C'mon, are you afraid of dog Halysaah?" Bayansa ta koma zuciyarta na bugawa, Safiyyah kuwa sai kora karen take da jakar hannunta fuska daure, shi dai Ajay na zaune parlor tun da ya kallesu sau daya ya dauke kai ya ci gaba da kallon Football da yake, sai da Jay ya kori karen sannan ya juya da gudu ya koma gun Ajay ya zauna saman kujeran kusa da shi, Jay ya juya ya kalli Khaleesat da ta marairaice ita ma tana kallonsa, ya ɗan yi murmushi yace "Ba abinda zai maku ai, bai san ku bane shi yasa...." ita dai bata ce komai ba, Jay ya jufi Ajay yace "Ajay ina makullin motana?" Ajay yace "Me zaka yi da makullin mota?" Khaleesat dai tuni ta nufi kofar fita parlon da sauri don ko kallon Ajay bata son yi, Safiyyah kam tana kallon Ajay tace "To sai anjima, Nagode sosai" Yace "Allah ya tsare" sallama tayi ma Jay shima sannan ta bi bayan Khaleesat, Jay yasan bazai basa makullin ba, hakan yasa ya duba aljihun Ajayn ya zaro few dollars sannan ya juya ya bi bayan Safiyyah, duk yanda yayi da Safiyyah ta amshi kudin taki amsa, Khaleesat tuni ta kusa fita daga gidan gaba daya, a haka Safiyyah ta bi bayanta. Safiyyah na kallon Khaleesat bayan sun shiga Lyft har sun fara tafiya ta rike haɓa tace "Ke ashe wannan gayen da muka yi misunderstanding da farko da muka shigo gidan yana da kirki sosai, in gaya maki da na zauna parlon nan na sama ni kadai ya zo wucewa ya ganni sai ya tsaya yayi powering min TV, har da kunna min wutan parlon, ya kuma nuna min fridge in dau lemo in sha, wallahi i never expect such kind gesture from him duba da yanda ya amsa mana gaisuwanmu da muka shigo parlon da farko, ashe mun yi misperceiving dinsa ne" Khaleesat tayi kamar ma bata ji abinda Safiyyah ke cewa ba. ✍🏻 07087865788 [5/12, 6:46 PM] khaleesat Haiydar ✍️: Read My Book "HALYSAAH" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=681294ff01c6bd900451c8e6 ✨✨HALYSAAH✨✨ ✍🏻 By _Khaleesat Haiydar_ 15..... Wajen karfe takwas na dare Khaleesat na zaune parlor tana duba wani reading material dinta wayarta ya fara vibrate, daukan wayar tayi taga number Salem, ita dai kallon screen din kawai take at first, after some seconds ta daga ta sa Hands-free tayi shiru tana saurare, daga daya bangaren aka mata sallama, muryar Housemate dinta ta ji, ta amsa sallamar tare da gaishesa, yace "Ya kika je gida Halysaah?" Tace "Lafiya lau" Yace "How about Safiyyah?" Tace "Tana can gidansu" Yace "Good, thank you so much for the visit" a hankali tace "Allah ya kara lafiya" Yace "Ameen Housemate" Daga haka yayi mata sallama ya katse wayar, bata kai ga ajiye wayar ba wani kiran ya sake shigowa ta ga Abdul ne, sai a sannan ta tuna damuwar da take ciki for days now, nan da nan mood dinta ya canza, tayi picking call din ta saka hands free sannan ta ajiye a gefenta tana ci gaba da duba reading material dinta a hankali ta gaishesa, yace "Didn't you see the money i sent to you?" Ta girgiza kai tace "Ban kula ba" yace "To ki duba" Katse wayar yayi ta jinginar da kanta jikin kujera with many thought running her mind.... Washegari da yamma bayan Khaleesat ta idar da sallah tana zaune tayi dialing number Salem, yana fara ring ya daga, bayan sun gaisa tace "Dama abinci ne zan ma Housemate dina yace min yana so, ban san ko zaka iya zuwa karfe biyar sai ka tafi masa da shi ba, that's if you are available and u don't mind doing so pls" Yace "Oops naje Pennsylvania daxu da safe, but za ki iya zuwa gidan ki kai masa ai, he is at home" A hankali Khaleesat tace "Ohk" Yace "Yeah, ki kai masa kawai can gidan" Tace "To nagode" a haka suka yi sallama ta ajiye wayar, Allah ya so bata dora girkin ba don ta san babu abinda zai sake maida ta gidan nan dai, tayi zuwan farko tayi na karshe. Khaleesat na zaune tare da Safiyyah bayan sun gama lectures din su na ranan, Safiyyah tace "Are you checking on ur Housemate even if ta waya ne kuwa Khaleesat?" Khaleesat ta kalleta tace "I don't have his number ai" Safiyyah ta dinga kallonta da mamaki, can ta girgiza kai tace "Ni ban san me yasa kike haka ba, why won't u ask that guy Salem ya baki? It's almost 10 days now da muka je gidan dubasa tunda kika ga har yanzu bai zo apartment dinku ba kinsan kilan ko bai ji sauki bane" Khaleesat tace "There was a time da muka yi waya da Salem din yace zai turo min lambarsa kuma bai turo ba shi sa har yau ban sake masa magana ba naga kamar baya son tura lambar ne, sannan kawai i assume kilan wannan arrogant guy din ne na gidan yayi stopping dinsa from coming to the house, i suspect they are kind of related or something like that" Safiyyah ta tabe baki tace "To ko in raka ki mu sake zuwa dubasa ne?" ko rufe baki bata yi ba Khaleesat tace "I am going no where, sai dai in ke zaki je sai in masa tuwo ki kai masa, dama ranan da muka je yace min yana son tuwo da miyar kuka, but for me babu abinda zai sake maidani gidan nan wallahi" Safiyyah ta dinga kallonta, can tace "Gaskiya zuciyarki kamar dutse yake Khaleesat, wato har ce maki yayi yana son cin tuwo amma kika kasa yi ki kai masa saboda wani banzan dalilinki, gaskiya you are not nice at all sorry to say" Khaleesat ta mike tace "Ki kirani ko ma me zaki kirani amma wallahi bazan koma wannan gidan ba as far as that bossy Man is in the house, kawai sai in kama hanya in sake komawa don yaji dadin kara raina min hankali ya walakanta ni, in dai ke zaki je zan yi girkin in baki, after all kince the arrogant guy is nice to you ai" Safiyyah bata tanka ta ba ta fara danna wayarta kawai, a haka suka rabu ko sallaman kirki basu yi da juna ba, har Khaleesat ta isa gida a lyft bata san sun iso ba, a duk kwanakin nan Allah ya sani Housemate dinta na ranta don babu ranan da zai zo ya wuce bata tunasa a zuciyarta, ba willingly taki zuwa gidan ta dubasa ba kawai wannan mutumin ne bata son ta sake haduwa da, sannan she is afraid of the huge dog in the house, kar ma taje mutumin ya sakar mata karen ta shiga uku, amma a ko da yaushe Housemate dinta yana ranta tana kuma son sanin how he is feeling, a hankali ta bude motar ta sauka duk jikinta a sanyaye ta nufi apartment dinta ta bude kofar ta shiga, turus tayi a living room din ganinsa kwance kan 3 seater yana bacci, juyawa taga yayi with his eyes still close yace "Good evening Halysaah" Sauke idonta tayi daga kallonsa, walking slowly ta karasa cikin living room din ta nufi can kusa da single sitter ta tsaya still looking at him, a hankali ya bude ido ya fara bin parlon da kallo alamar he is looking for her, suna hada ido calmly tace "Good evening" Mikewa zaune yayi trying to recover fully from his sleep yana shafa fuskarsa yace "How are you?" Tace "Alhamdulillah, ya jikin?" Yace "Naji sauki ai" Shiru tayi kamar me tunanin abinda zata ce, can kuma dai tana rike da edge din gyalenta cikin nutsuwa tace "Naga baka zo bane, i thought jikin ne har yanzu...." Ya girgiza kai without looking at her yace "Abbana ne yasa na je Nigeria, we spent 6 days in Nigeria, jiya muka dawo" Yana fadin haka ya daga kai yaga kallonsa take, da sauri ta kauda kanta tana nodding tace "Ohk" Daga haka ta juya ta nufi dakinta kamar munafuka, ya koma yayi kwanciyarsa. After almost an hour Khaleesat ta fito parlor, ta samesa zaune ya gama baccin yana danna laptop dinsa, kanta a kasa ta karasa cikin living room din ta dan kallesa suka hada ido tana kame kame tace "Dama tambayarka zan yi in maka tuwon ne yanzu zaka ci?" Yace "Tuwo kuma? Aa kinga you just came back from school, ki bari next time in sha Allah" Tace "Ohk" Daga haka ta tafi kitchen to make a light dinner, bayan ta gama girkin ta fito parlor, har sannan yana nan zaune, ta ɗan kallesa tace "You care for some?" Ya kalli hanyar kitchen din sai kuma yace "Let me dish it my self" Daga haka ya ajiye laptop dinsa ya mike ya tafi kitchen din, ita dai tana tsaye ta bi sa da kallo, bayan few minutes ya fito da bowl din pasta din ya zuba very little quantity, with another plate of the pasta, ita dai kallonsa take, ya mika mata na plate din ta sauke idonta ta amsa, ya zauna ya ajiye bowl din nasa, a hankali tace "Wannan ne zai isheka?" Yace "Eh" juyawa tayi zata bar wajen, yace "Bedroom za ki je ki ci abincin kenan" Ta gyada masa kai tayi tafiyarta daki. Wajen karfe tara na dare Khaleesat ta saka hijab dinta jin yana knocking kofarta sannan ta tafi ta bude kofar, yace "Sai da safe Halysaah, i am going home" at first shiru tayi, can kuma a hankali tace "Why are u having two home?" Ya ɗan buda ido yayi murmushi yace "One is a home, the other... a comfort zone" Ta langwabar da kai tace "U said two same thing ai, A Home is also known as a comfort zone" Dariya yayi yace "Not in my case Halysaah, they are two different thing to me" Shiru tayi kafin tace "So now, which is home and which is comfort zone?" Yayi murmushi yace "Kema dai kamar er jarida, how is ur frnd?" Tace "She is fine" Yace "And ur Bossy boyfriend, hope ya daina saka ki kuka dai yanzu?" Ta wani kallesa zata kulle kofarta da sauri yace "Wait, it's just a harmless question Halysaah" Tace "To da nace maka kuka yake sa ni?" Yace "Ohk, Allah sa kar in zo ina baki hakuri kwanan nan bayan ya saka ki kukan, and before i forget me yasa baki cin cookies dake kitchen?" Tace "Nawa ne da zan ci?" Yayi shiru kamar bazai ce komai ba, can kuma yace "To ki dinga ci daga yau duk abinda kika ga na siya ki dauka idan kina bukata, I didn't buy them all because of my self alone, ko da namiji ne a gidan nan ko wata mace daban in zan siya abu in ajiye zan siya ne in surplus not for only me, kin gane ko? Har bottle water ina siya mana ne mu biyu ba ni kadai ba, after all there is love in sharing" Ita dai idonta na kasa bata ce masa komai ba, Yace "Good night" juyawa yayi ta bi sa da kallo har zuwa parlor, sai kuma ta kulle kofar dakinta a hankali. Washegari Asabar Khaleesat ta gama laundry da take a kitchen, tayi tidying din duk gidan sannan taje tayi wanka ta fito parlor tana tunanin abinda zata girka kafin ta fara karatu cause it's almost 12pm, tun karfe goma Housemate dinta ya shigo gidan ya wuce Bedroom dinsa, ta ma san bacci, ita kam mamakin yanda baya gajiya da bacci take, knocking kofar parlon aka yi, she is expecting Safiyyah dama amma bata yi tunanin da wuri zata zo ba, ta karasa gun kofar ta bude a bit relieve ta samu me taya ta girki, da mamaki ta bi sa da kallo bayan ta koma gefe don da ta ci gaba da tsayuwa wajen taga alamar bangajeta zai yi ya shiga parlon, direct taga ya nufi dakin Jay ya bude ya shiga, kasa rufe baki tayi tsabar mamaki, tana jin sa yana ma Jay bala'i a dakin, ita dai bata ji muryar Jay din ba, Jay ne ya fara fitowa daga dakin, kamar yanda ta zarga kuwa baccin yake, laptop din da ya bari kan kujera da ya shigo daxu ne ya dauka, Ajay na fitowa ya mika masa laptop din, a mugun fusace Ajay yace "What the hell should i do what with it again bayan lokaci ya kure? Kasan implications din da abin nan da kayi zai ja min kuwa?" A karo na farko Jay yace "Kai dalla wayar a silent yake, kuma ni ban san akwai recent aikinka a ciki ba, da bazan taho da shi ba ai" Ajay dai kallonsa kawai yake kamar ya shaƙo sa, Jay ya zauna kan kujera ya jinginar da kansa tare da lumshe ido, banda hararan Ajay babu abinda Khaleesat da ke tsaye parlon take yi, lkci daya Jay ya mike yace "Hey let me see you off, wanka zan yi" a takaice Khaleesat tace "And pls Housemate warn him not to ever barge into someone else's apartment like this again, this isn't a shopping Mall da zai shigo kai tsaye" A tare suka juya suna kallonta gaba dayansu, Ajay yayi facing dinta calmly yace "Ke, da ni kike wannan maganar ko wa?" Ta wani kauda kai fuskarta a daure tace "In baka son ayi da kai kar ka sake shiga gidan mutane babu Excuse, after all ba tare muke renting apartment din ba da zaka shigo min gida without notice, idan wajen abokinka ka zo maturely sai ka jirasa a waje, you don't have to push ur way into people's apartment like it's a shopping complex" Ajay that was speechless ya kalli Jay, Jay ya shafa kansa yace "Why didn't u knock and wait for me outside, after all she is saying the truth" Khaleesat tace "Ni in ya sake shigo min gida haka wallahi 911 zan kira masa..." Ajay ya ciro wayarsa a aljihu yana mika mata yace "Call them immediately" Ta jefa masa wani kallo tayi hanyar dakinta, Yana kallonta da kyau yace "I will definitely deal with you" Ita dai tuni ta shige dakinta ta kulle kofar da makulli, Jay na kallonsa yace "Me yasa zaka shigo mata gida kamar tsohon barawo?" Ajay yace "Za kayi bayanin me kake yi da mace under the same roof in America, macen ma da ka kusa haifa, i promise to report you back home, ita kuma i will teach her the lesson of her life" Yana kai wa nan ya fixge laptop dinsa a hannun Jay, Jay dake murmushi yace "Babu abinda ka isa kayi mata don ta gaya maka gaskiya Malam, kai waye da baza a gaya ma gaskiya ba" Tuni Ajay ya fice daga parlon, Jay ya zauna kan kujera ya dafe kansa yana dariya, the incident was just funny to him, kallon kofar dakinta yayi yana mamakin dama wai haka yarinyar nan take amma take ma saurayinta kuka? Mikewa yayi ya nufi dakin nata yayi knocking kofar yace "Halysaah" sai da ya kirata sau uku sannan ta bude kofar a hankali tana leka parlon kana ganinta kasan a tsorace take, dariya yayi yace "Kinsan waye shi da kika masa rashin kunya Halysaah?" Ta wani turo baki tace "To ni ina ruwana da koma wanene shi, saboda me zai shigo min gida kamar wani barawo, where is it done that way? Ni dai wallahi kar ya sake zuwa min gidan nan in ba haka ba in kira 911" Jay dai sai sauraronta yake, can yayi murmushi yace "So dama kina da baki haka amma kike ma saurayin ki kuka?" Khaleesat ta wani kallesa ta hade rai tace "Ni bana son haka" still smiling yace "Ok, sorry" keeping a straight face tace "Ya tafi?" Jay ya juya zai bar wajen yace "Ya tafi mana" Da sauri tace "Plss ni dai kayi masa magana kar ya sake zuwa, if there is anything ai sai ya kira kaje can gidanku ka samesa kawai ba sai ya zo nan ba" Jay dai murmushi kawai yake yace "Ohk" parlor taga ya tafi, ta koma dakinta ta zauna bakin gado, har sannan gabanta faduwa yake, ita kanta bata san inda ta samu courage din gaggaya masa abubuwan da ta gaya masa ba, ko don dama tana jin haushinsa ne yasa ta samu irin wnn courage din oho, bata fito daga dakinta ba sai da tayi sallan zuhur, a hankali take tafiya ta shigo cikin parlorn, gani take kamar zai sake dawowa gidan at anytime, ai ko wallahi yan sanda zata kira masa, Zaune taga Jay a parlon yana danna wayarsa, tana tsaye bayan kujera tace "Did u warn him not to come back plss?" Jay yace "To ke meye damuwarki ba kin masa warning kar ya sake dawowa ba, ai bazai dawo ba" Kamar zata yi kuka tace "Wallahi zai iya dawowa, kuma in ya dawo baka nan ya zan yi?" Dariyar da yake dannewa ne ya taho masa yace "Ina kuwa zan san yanda za ki yi, ke wa ya aike ki yi masa rashin kunya? Da sai ki yi shiru da bakinki har in fitar da shi daga gidan, Laptop dinsa na dauko daga can gida yana bacci ban san akwai aikinsa da zai yi put foward ta email ba, yana ta kiran wayana kuma ina bacci na sa wayar silent, that was what brought him here" Zaunawa tayi kan kujera tace "That doesn't still warrant him ya shigo gidan mutane kai tsaye, ko magana bai min ba ina bude kofa ya kusa bangajeni fa ya shigo parlon, am i a joke to him?" Dariya Jay yayi yana gyada kai yace "This energy u used in attacking him Allah ya baki irin energy din kiyi using ma Boyfriend din ki" Wani kallo Khaleesat tayi masa, shi dai murmushi kawai yake still not looking at her yace "Naga kamar kin damu da abinda kika masa, ko in kirasa ki basa hakuri ta waya komai ya wuce?" mikewa tayi a takaice tace "Allah ya kiyaye" Daga haka tayi wucewarta kitchen, shi dai murmushi kawai yake looking at a different direction, yasan yau da kyar Ajay yayi bacci akan abinda tayi masa. Bayan Khaleesat ta gama girkin da take ta fito parlor tana kallon Jay ganin fita zai yi don har ya shirya yana saka agogon wrist dinsa without looking at her yace "I think sai gobe zan dawo in sha Allah" Ta marairaice amma bata ce masa komai ba, har cikin ranta ta fara jin tsoron kasancewarta ita kadai a gidan, ya ɗan kalleta yace "Any problem?" Ta hade rai tace "Toh ka bani makullinka idan ka zo goben sai kayi knocking in bude maka kofar" Da mamaki yace "Why?" Tace "So that baza kaje ka ajiye key din recklessly ba wannan mutumin ya gani ya dauka" Yayi dariya yace "To ya dauka yayi me da shi?" Ta nufesa tace "Bani" ba musu ya bata makullin ta amsa sannan a hankali tace "To abincin fa?" Yace "Abinci? Wani iri?" Bata tanka sa ba ta juya ta koma kitchen din, after some minutes sai ga ta ta dawo da plate din rice and stew, ya ɗan bude ido yace "Wa zai cinye duk wannan?" Tace "Kai mana" Ya zauna sannan ta mika masa abincin, yana girgiza kai yace "It's very plenty" tace "Should i get you water?" Yace "I will appreciate that" kitchen din ta koma ta dauko masa ruwan gora da drink din gwangwani, yace "Thank you Halysaah" dakinta ta wuce, after a while taji yayi knocking kofar dakinta, bayan ta bude yace "Zo ki bude min kofar zan tafi" Makulli ta dauko ta tafi ta bude masa kofar yace "Thank you, see yah tomorrow" ita dai bata ce komai ba ya fita daga parlon ya nufi garage, a hankali ta kulle kofar da makulli sannan ta tafi window ta ɗan bude labulen tana kallonsa har ya bar garage din after some minutes, Sake curtain din tayi, walking slowly ta tafi kitchen, bude abincin da ya rufe tayi taga kadan ya ci a ciki, Allah yasa yayi spoon hudu, naman ma kawai daya ya ci, kulle abincin tayi ta dawo parlor ta zauna, dai dai nan taji anyi knocking kofar parlon mikewa tayi da sauri tana kallon kofar a tsorace, da kyar tace "Waye??" Muryar Safiyyah taji, lkci daya ta sauke ajiyar zuciya sannan ta tafi ta bude kofar, Safiyyah tace "Har kin gama laundry din?" Khaleesat tace "Na gama" Safiyyah tace "Housemate din naki ya fita kenan?' Khaleesat tace "Eh" Safiyyah tace "Jiya da daddare da kika gaya min ya zo gidan ta chat wallahi nayi farin ciki, don mutumin na da kirki sosai" Khaleesat bata tanka ta ba, ta koma cikin parlon ta zauna tace "Ban gan ki da laptop dinki ba" Safiyyah tace "Abeg i will use urs, bani da strength din dauko laptop, kin yi girki kuwa? Don yunwa nake ji, wancen er iskar matar faten wake tayi saboda tasan ba na ci, hegiya dama bayerabiya ce ta wajen uwarta ai" Dariya kawai Khaleesat tayi ta mike ta tafi kitchen, abincin ta zubo ma Safiyyah, ita kuma ta dau wanda Housemate dinta ya rage, ta dauko masu ruwan gora da lemon kwali daya.... ✍🏻 07087865788 [5/13, 6:21 PM] khaleesat Haiydar ✍️: ✨✨HALYSAAH✨✨ ✍🏻 By _Khaleesat Haiydar_ 16..... Ko da wasa Khaleesat bata ba Safiyyah labarin abinda ya faru tsakaninta da Ajay ba, amma fa bata da rest of mind gani take kamar zai iya dawowa gidan at anytime, upon all her restlessness bata ji tayi da ta sanin abinda tayi masa ba, dama haushi yake bata, Safiyyah na kallonta tace "Ke kwana biyu shiru banji kince ga abinda Abdul yayi maki ba ko dai ya fara canzawa ne? This is so unusual, ko baki gaya min ba in dai ya maki wani abu you are always moody in school, ta haka nake ganewa" Khaleesat na powering laptop dinta ta tabe baki tace "Ni ina naga wannan time din yanzu ga exams a gabana" Safiyyah tace "Atoh dai, wallahi naji dadin da kika fara daukar shawarata kina fita sabgarsa, sauranki abu daya yanzu" Khaleesat ta daga kai ta kalleta, Safiyyah ta gyara zama tace "Saura ki fara mayar masa da magana, in ya gaya maki daya ki gaya masa biyar" Ita dai Khaleesat bata sake ce mata komai ba tana neman softcopy na course din da za su yi studying tare da Safiyyah. Bayan tafiyar Safiyyah... Khaleesat ta wanke utensils da suka yi amfani da sannan ta wuce dakinta, wayarta ta dauka ta shiga WhatsApp don ganin ko Ummanta tayi mata reply din message da ta ajiye mata daxu, wajen karfe goma da rabi tana shirin kwanciya wayarta ya fara ring, dauka tayi taga Abdul ne ke kiranta, ta dinga kallon wayar, tun sanda Ummanta tace mata tana ganin kamar lkci aka tsayar take wani jin tsanarsa a zuciyarta, gashi yaki gaya mata ko da gasken an tsaida lkcn ko ba a tsayar ba don Ummanta ba wai ta tabbatar bane ita ma a gari ta ji, dama tana Nigeria din ne ta san gun warce zata je taji ko hakan ne ko ba haka ba, ɗaga kiran tayi kafin ya katse ta kai kunne, muryarta kamar me bacci ta gaishesa, ya amsa, a hankali tace "Ya aiki?" Yace "Lafiya lau" Shiru tayi bata sake cewa komai ba, yayi ƙasa da murya yace "I don't know, kawai ina missing din ki ne yau, i want to be with you Baby" Ta kauda kai kamar irin yana kusa da ita din nan tace "Um" Yace "Yaushe za ku fara jarabawan?" Tace "Nan da wata daya" A hankali yace "Ohk, sai da safe, naga kamar kin fara bacci" Tace "Um, ina son tashi inyi karatu ne anjima shi sa na kwanta da wuri" Yace "To ci gaba da baccinki, sai mun yi magana" Daga haka ya katse wayar, ta jefar gefenta ta ci gaba da chatting da take da Ummanta. Washegari lahadi Khaleesat na zaune dakinta tana morning Supplications dinta taji ana kwankwasa kofar parlor, wayarta ta jawo tana duba agogo taga bakwai ya wuce, ta daure ta mike tana tafiya a hankali ta fito parlor, bayan ta karasa bakin kofar with calmness tace "Waye?" Taji muryar Housemate dinta yace "Good morning" bude kofar tayi ta koma gefe ya shigo, sau daya ya kalleta yace "How was ur night" Ta kulle kofar tace "Alhmdlh" Materials din hannunsa ya ajiye saman 1 seater sannan ya kwanta kan doguwar kujera, ita dai bin sa tayi da kallo taga har ya kulle idonsa yana gyara kwanciyarsa alamar bacci zae yi, tana tafiya a hankali ta koma dakinta, ta karasa azkar dinta sannan ta kwanta. Har wajen karfe daya na rana Khaleesat bata fito dakinta ba, ta ɗan juya daga kwancen da take tana kallon kofar dakinta jin ana knocking, kiranta taji Housemate dinta ke yi, mikewa zaune tayi still tana kallon kofar amma bata sauka daga kan gadon ba, Calmly tace "I can hear you" Yace "Are you alright? Naga kamar baki yi breakfast ba ko?" Shiru tayi bata ce komai ba, bude kofar taga yayi, ta gyara blanket din jikinta tana kallonsa, ya tsaya daga bakin kofar dakin yace "Hope nothing?" Ta langwabar da kai tace "Nothing" Yace "To me yasa baki fito kinyi breakfast ba or are you fasting? Beside today is sunday" Ta kauda idonta tace "Kawai dai..." Sai kuma tayi shiru, ya karasa cikin dakin yace "Kawai dai me?" Kamar baza tace komai ba sai kuma dai tace "Ina jin ciwo a kafana ne" Yace "Ciwo a kafa kuma? Yana maki haka ne?" A hankali tace "Once a while" Shiru yayi jin abinda tace, can yace "Then what is the cause?" Ta ɗan kallesa, sai kuma ta bude hannu alamar bata sani ba, yace "Kun taɓa zuwa hospital a kan hakan?" Ta dai yi shiru without looking at him, sai kuma tace "It's fine, i will get better before evening in sha Allah" Ya juya as if trying to diagnose without examination the cause of her leg pain at her age, sau daya ya kalli gaban dressing mirror dinta sai kuma ya juyo yana kallonta yace "Ok i get, Allah ya sauwake..." Ta ɗan kallesa, yace "Try getting a hot shower, you will feel better" Juyawa yayi ya fita daga dakin, a hankali Khaleesat ta koma ta jingina da pillow, ko tashi tsaye bata jin zata iya a yanzu dai, kilan zuwa can anjima ta ɗan ji relieve before she can stand up and do anything, kiran Abdul ne ya shigo wayarta ta kife wayar taki dagawa don ko magana bata so, after some minutes ta kalli kofarta jin knocking at the same time ya bude kofar dakin ya shigo ciki rike da cup din hot chocolate, sauke idonta tayi daga kallonsa ya karasa har side din da take ya duka yana mika mata Mug din hot chocolate din yace "Try drinking this, will get u pain reliever now" Ta amshi Mug din without looking at him a hankali tace "Thank you" Yace "You are welcome" Daga haka ya fita daga dakin ta bi sa da kallo babu ko kiftawa, yana fita kiran Abdul ya sake shigowa wayarta still taki dagawa daga karshe ma tayi silencing wayar, khaleesat na gama shan hot chocolate din ta ajiye cup din a bedside drawer sannan ta koma ta kwanta tayi lamo kan pillow, kamar zata kira Safiyyah daxu wajen karfe sha biyu sai kuma ta fasa hoping the ache will subside, har ta fara bacci Housemate dinta yayi knocking wajen karfe biyu almost 20 mins bayan fitarsa daxu, sai da ta amsa sannan ya bude kofar, ita dai bata juyo ba, ya zaga ta inda take calmly yace "Are you sleeping Halysaah?" Ta bude ido tana girgiza kai, ya ajiye ledan abincin hannunsa da pain reliever da ya siyo mata yace "Baki yi hot shower da nace kiyi ba?" Tace "Zan yi" Yace "Ohk ga maganin sai ki ci abinci ki sha" Ta mike zaune without looking at him, a hankali tace "Thank you" Yace "Zan fita but i will come back around 6pm in sha Allah" Tana kallonsa tace "Toh makullin gidan fa?" Ɗan murmushi yayi yace "Ai a jikin kofar kika bar sa daxu da kika bude min da safe" Tace "Amma baza ka tafi da shi ba ai" Yace "To taso ki kulle kofar" Ta wani kallesa, er dariya yayi yace "Shi fa Ajay nasan yanxu kuma ya mance abinda ya faru tsakanin ku, may be sai ranan da ya kara ganinki zai tuna, but for now i am assuring you ya mance wallahi he is even busy with his upcoming defense, beside you misperceived him, Ajay is more than nice and calm, ba shi da matsala, kawai dai shaidan ne ya saka rashin jituwa tsakaninku tun a ranan da ku ka hadu" Khaleesat dai ta kyabe baki don ko duk jikinta kunnuwa ne bazata taɓa yarda da abinda yake fadi ba, Jay yace "Baki yarda ba ko?" Ta buda ido sosai tace "To dama saboda me zan yarda?" Dariya kawai yayi yace "Take care of ur self Halysaah, in kin ci abincin ki sha magani, let me get you bottled water" Daga haka ya nufi kofa ita dai ta bi sa da kallo har ya fita, sai gashi ya dawo mata da ruwan gora mara sanyi ya ajiye a inda ya ajiye mata ledan abinci da magani wato bedside drawer, yace "See yah later" a hankali tace "Thank you, and pls do not mishandle the key" Murmushi kawai yayi ya gyada mata kai ya fita daga dakin ya kullo mata kofar, ta sauke idonta kasa, after some minutes ta dau ledan abincin da ya ajiye mata a hankali tana budewa don ganin abinda ya siyo mata. Karfe shidda saura Khaleesat na zaune kasan dakinta ta kwantar da kanta jikin gado tana voice note da Ummanta, zuwa sannan she is feeling very much better don har ta gyara dakinta ta wanke bandaki tayi wanka, parlor ne dai taji bazata iya gyarawa ba, wajen karfe hudu suka yi chatting da Safiyyah tace mata zata zo karfe bakwai, Khaleesat ta dan yi jim bayan taji kamar an bude kofar gidan, gabanta ne ya fadi bayan Ajay ya fado mata, ta ajiye wayar hannunta a hankali tana kallon kofar dakinta, after few minutes taji an yi knocking kofar dakin, she felt a bit relieved, with calmness tace "I can hear you" Taji muryar Housemate dinta yace "Can i open the door?" Tace "Okay" bude kofar dakin yayi yana daga bakin kofar a tsaye yace "Good evening Housemate, how are you feeling?" Tace "Da sauki" Yace "Are you sure?" Sai a sannan ta daga kai ta kallesa, ta dan kwantar da kanta gefen gado tace "It's better than before" Yace "To Allah ya sauwake, where you able to go to the kitchen?" Ta gyada masa kai, yace "Ohk" Har zai kulle mata kofar sai kuma ya tsaya yace "Ko mu dan yi strolling as exercise, around the neighborhood, it will help you feel much better too" Khaleesat ta daga ido ta kallesa, yace "I will be waiting for you at the parlor, make sure to put on ur jacket cause it's freaking cold outside" Yana fadin haka ya fita daga dakin, Khaleesat dai na ta zaune kamar me nazari, it took her almost 5 mins of deciding kafin ta mike a hankali, veil dinta kawai ta dauka ta yafa ta dau wayarta tana tafiya a hankali ta fito daga cikin dakin, tsaye ta gansa ya jingina jikin pillar dake kusa da study area yana danna wayarsa daya hannunsa rike da jacket dinsa, yana ganinta yace "Are you ready? Where is ur jacket?" Karasawa yayi inda take tsaye yace "It's cold outside" Yana fadin haka ya ajiye mata Jacket dinsa kan kujeran dake kusa da ita yace "Use this, bari in dauko wani" Dakinsa ya koma ita dai ta bi sa da kallo, ba a dau lokaci ba sai gashi ya dawo parlon with another Jacket, ya saka a kan rigar jikinsa yace "Mu je" Ta sauke idonta ta dau Jacket din nasa, Kofar parlon ya nufa ta bi bayansa har suka fita daga parlon, ya kulle kofar ya kalleta yace "Na lura kina son so much perfume ke dai" Ta girgiza kai tace "A'a ni ban sa ba yanzu" Yace "Ohk" A tare suke tafiya with nobody saying anything, tun ba su kai ko ina ba taji tana jin sanyi sosai, hakan yasa ta ɗan saci kallonsa sannan ta saka jacket din hannunta yace "Ai na zata baza ki sa ba kina forming big gal" Kawai dai tayi murmushi bata ce komai ba, tana jin kamshin turarensa da ya cikata na jikin Jacket din, dai dai yake tafiya da ita to keep same pace with her, slowly suke tafiyar with absolute silence har suka yi nisa away from home, Jay yayi breaking silence din yace "Soon za a fara snow" Tace "In sha Allah kafin nan mun gama Exams dinmu" Zai yi magana wayarsa ya fara vibrate ya ciro a aljihunsa yana duba me kiransa, ta gefen ido ta kalli wayar tasa taga Ajay, yayi silencing wayar ya mayar aljihunsa, ta tabe baki tace "Shi dole sai ya dinga damunka da kira ne as if you are with his kidney?" Jay yayi dariya yace "Kidney ai me sauki ne, cewa za ki yi kamar life dinsa na wajena dai, a rana sai ya kirani sau ashirin in banyi hankali ba" Khaleesat ta kyabe baki sai ga shi ya sake kiran wayar, Jay ya kara ciro wayar yayi picking ya sa Hands- free yana tafiya yace "What again?" Daga daya bangaren Ajay yace"I need ur laptop, zan duba references dinka, na mance zan shiga schl gobe, i am outside with my frnd now" Jay yace "Da laptop din na fita ai, kuma i am not coming back home anytime soon" Ajay yace "Gidan wannan mara kunyan ka koma kenan? Wai are you even okay Bruh? Me kake yi da wannan yarinyar da ya sa kake zama gidanta? Ko iskanci ka fara ne? In ma iskancin zaka yi why with that little local brat pls?" Jay that was trying not to laugh yace "Kai kar ka bata min rai fa" Ajay yace "On a serious note idan baka daina zuwa gidan nan ba i promise you am gonna report you back home kasan karamin aikina ne hakan ko?" Jay yace "In ka fasa, kai duk takurani da kake da yan iskan abokanka a can gida ban kai report ba sai ni da na bar maka gidan for peace to reign shi ne zaka kai karata? To references din ma baza a nuna ba, go and sort ur self out" Yana kai wa nan ya katse wayar ya mayar cikin aljihu, ita dai Khaleesat bata kallesa ba kuma bata ce komai ba amma har cikin ranta take jin Ajay bai mata ba, she doesn't like him or anything concerning him, ta tsani mutum that is too pompous and proud of himself, Jay yace "Baya karatu fa, in ma wani aiki ne sai dai kai kayi ya gani sannan yayi nasa, har ma nasan yafi naka at the end" Khaleesat tace "To me yasa har yanzu ba a koresa ba daga makarantar?" Dariya sosai Jay yayi yana kallonta yace "Baya karatu doesn't mean he is dull Halysaah, kinsan Genius? That is who Ajay is, he is naturally gifted, he graduated as one of the best medical student during our degree program in this state and masters, kuma kar kice wani karatu yake, mu ne dai sai mun yi karatun za mu wuce" Yana murmushi ya kare maganar, Khaleesat ta wani kyabe baki kamar bazata ce komai ba, sai kuma tace "To ai gwara kai karatun kayi ka wuce, shi kuma banza kawai yake ci" Jay na dariya yace "Ai shi sa na bar masa gidan cause idan na ci gaba da biyesa da abokansa wucewa zai yi ya bar ni, su kansa abokan nasa ina tausaya masu biyesa da suke" Khaleesat tace "Shi ne yasa kake Co-living?" Yace "Yeah, shekaranmu na karshe kenan idan Allah ya yarda so i need much privacy to study very hard to earn my PhD, in kana tare da Ajay ba wani abun arziki da zaka yi in dai bangaren karatu ne, sannan baya barina inyi bacci sosai, nuisance ne shi fa, Ya Subhanallah" Khaleesat tayi shiru tana kallonsa, sai kuma ta sauke idonta, yace "Year nawa kike yanzu?" A hankali tace "Year 3" yace "Kince Pharmacy ko?" Ta gyada masa kai, yace "Kin kusa gamawa kema ai in sha Allah" ita dai tayi shiru bata ce komai ba suna ci gaba da tafiya slowly, ita ce tayi breaking silence din after almost 10 mins da ya biyo baya tace "You know him back home?" Jay ya kalleta yace "Wai Ajay? Yeah he is my favorite, yanzu ma dai kin ga budurwa nake nema masa bashi da mashinshiniya ko daya wallahi" Khaleesat tace "Ashe bazai taba samu ba, ai he is way too rude and full of himself, wacece zata yarda ta auresa in dai ba auren dole aka mata da shi ba, ko makala mata shi aka yi?" Jay dai dariya kawai yake yana kallonta yace "Ya kai Saurayin ki?" Nan da nan mood dinta ya canza, taki ce masa komai tana ci gaba da tafiyarta, yana kallonta yace "Naga kin yi shiru ko compare and contrasting kike yi a zuciyarki? Tell me pls ya kai saurayinki?" Without looking at him tace "Kamar lokacin sallah yayi, and it's getting dark already" Yace "Ke ina ruwanki da sallah tunda ba yi kike ba?" Khaleesat was dumbfounded jin abinda yace, ta kasa kallonsa kuma taki basa amsa still walking slowly, Roadside chair ta hango ta tafi ta zauna, ya karasa wajen yace "Ko har kin gaji ne?" Tace "To da bazan gaji ba, muna ta tafiya for almost an hour now" Yace "Akwai wani Eatry a area din nan, mu je sai mu yi dinner before going back home, the eatry isn't far away from here" Khaleesat tayi shiru, ta san Eatry din da yake magana don sun taɓa zuwa da Abdul kuma abincin wajen shegen tsada ne da shi, yace "Let go" Yana fadin haka ya juya ya fara tafiya, hakan ya sa ta mike ta bi bayansa, ya jira har ta iso inda yake sannan suka ci gaba da tafiya a tare har suka isa Eatry din, suna shiga ta kalli Jay that was grinning kamar yaga wanda ya sani a cikin Eatry din, lkci daya ta hango Ajay that was sitted da wata baturiya a cikin eatry din yana mata magana, ga abinci kala kala a gabanta, shi kuma ruwan gora ne kawai a gabansa, Khaleesat ta dauke idonta speaking calmly tace "I think zan tafi gida kawai, dama ba wani yunwa nake ji ba, i will order a Lyft in koma gida" Jay ya riko gyalenta don har ta juya zata fita yace "C'mon Halysaah, so kike ya kara raina ki, kina fita zai yi zaton tsoronsa ne yasa kika kasa shigowa kika fita and he will be very happy, kawai kiyi fuska ki tafi ki zauna" Khaleesat ta tsaya bayan ta ɗan yi nazarin abinda Jay yace, kuma fa haka ne zai yi zaton tsoronsa take, hakan yasa ta karasa Jay na biye da ita a baya ya jawo mata kujeran dake facing inda su Ajay ke zaune ta zauna, Jay ma ya zauna sannan ya kalli direction din Ajay dake kallonsu babu yabo babu fallasa, Jay ya daga masa hannu with smile all over his face alamar Hi, Ajay ya dauke kai kamar bai taɓa saninsa ba a rayuwa, Jay ya daga kafadarsa yana murmushi sannan ya dau menu dake saman table ya mika ma Khaleesat yace "Duba abinda zaki ci" Ta amshi Menu din tana kallo, cikin few minutes Jay ya saka masu order aka kawo masu abincin, duk da Khaleesat tana facing din Ajay ko da wasa bata yarda ta kallesa ba, tayi kamar bata san da shi a Eatry din ba, Jay kuwa cin abincinsa kawai yake with full concentration not minding her in his front, lkci lkci Khaleesat ke kallonsa, ta lura he doesn't joke with food and sleep for anything, dariya ma ita yake bata, ita kam a hankali take cin abincin gabanta, ya daga kai ganin bata wani ci Crab patatoe Chips din gabanta ba yace "Should i fetch some of urs?" Ta wani kallesa tace "Do you have an extra stomach?" Bai san sanda yayi dariya ba yace "I don't understand an extra stomach?" Tana kallonsa calmly tace "Naga duk kai ka kusa cinye abincin kan table din nan" Jay ya bude ido sosai yace "Har da sharri? Me da me na ci a table din?" Ta tallabi chin dinta tana murmushi tana kallonsa wanda har sai da dimples dinta ya lotsa, Mistakenly ta daga ido suka hada ido da Ajay dake kallonsu babu yabo babu fallasa, nan da nan murmushin dake fuskarta ya bace ta sha kunu, Jay bai ma san tana yi ba don tuni ya ci gaba da cin abincinsa har ma ya diba na gabanta, Khaleesat ta kalli wayarta dake vibrate kan table, sosai gabanta ya fadi ganin Abdul ne ke kiranta, Jay ya daga kai ya kalleta yace "Ba kiran ki ake ba?" A hankali tace "Na sani" Yace "Why are you not picking?" Tayi shiru, sai a sannan ta tuna fa ashe ya kirata severally bata daga kiransa ba, Jay yace "Ko de saurayinki ne?" Ta daga manyan idanuwanta ta kallesa, yace "Ki daga mana kar kiyi laifi" Sauke idonta tayi ta daga kiran a hankali ta kai kunne tare da sallama cikin sanyin murya..... ✍🏻 07087865788 [5/14, 5:45 PM] khaleesat Haiydar ✍️: Read My Book "HALYSAAH" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=681294ff01c6bd900451c8e6 ✨✨ HALYSAAH✨✨ ✍🏻 By _Khaleesat Haiydar_ 17.... Daga daya bangaren Abdul yace "What is wrong with you these days Khaleesat? Me yake damun ki?" Tunanin abinda zata ce masa ta fara yi, tayi shiru gabanta na faduwa, ita ta ma rasa me yasa take ƙin daga kiransa kwanan nan, kawai a zuciyarta take jin bata son waya da shi, Jay ya daga kai ya kalleta jin tayi shiru ga waya ƙare a kunnenta, amsar wayar yayi ta zaro ido tana kallonsa da mamaki with fear, ya sa wayar handsfree ya rage volume sannan ya ajiye saman table ya ci gaba da cin abincinsa, a fusace Abdul yace "Wai baki ji na ne, or is something wrong with you?" A hankali Khaleesat tace "Ina jin ka mana, na mance wayar ne a gidansu Safiyyah, i just got it now" Sounding so provoked yace "Ni zaki raina ma hankali? Ke ce zaki bar wayarki tun jiya gidansu Safiyyah?" Khaleesat ta wani kyabe baki ta kauda kai tace "Haka dai kawai bazan ki daga kiranka ba, me yasa baza ka min uxuri ba?" Abdul yace "Wait Khaleesat, where are you getting ur liver from these days? Who is ur vendor? Yaushe kika fara samun courage din mayar min da magana?" Khaleesat tace "Toh ni yanzu me nayi? Nace maka wayar baya wajena and u are trying to create an issue out of nothing, Nan da few weeks fa za mu fara jarabawa, you are only adding more pressure to the one i am already in, ka dinga considering dina mana pls" Jay ya ɗan daga kai ya kalleta, sai kuma yayi murmushi ya dau ruwan gora ya bude yana sha, Abdul yace "A kanki aka fara jarabawa? What is the big deal ah jarabawan da zaki yi? Ko dai Safiyyah ce ke dora ki akan abinda bazai fisshe ki ba? Safiyyah ce take zuga ki har kika fara samun courage din mayar min da magana ko? Switch to video call now" Khaleesat taji gabanta ya fadi sosai, Jay dai murmushi kawai yake, a hankali Khaleesat tace "Ohk i will, amma kayi hakuri let me dress up first..." A mugun fusace yace "Ki bar shi" Yana fadin haka ya katse wayar, Khaleesat dai tayi shiru tana kallon wayar nata, Jay yace "Ki gama cin abinda zaki ci mu tafi Halysaah, it's pass magrib now zan je inyi sallah" Khaleesat ta daga idanuwanta tana kallonsa, yace "Ko ayi maki takeaway din abincin?" Ta sauke idonta bayan sun hada ido da Ajay da ya mike daga inda yake zaune, Jay ya juya ya ɗan kalli Ajay yace "Hey man, ka hada har nawa bills din" Ajay yaki kallon direction dinsa kai kace bai san sa ba ma, Jay ya kira daya daga ma'aikatan wajen ta karaso, ya sa tayi masu packaging abincin da Khaleesat bata ci ba, ita dai Khaleesat har sannan taki cewa komai kana ganinta kasan she is a bit disturb, Jay ya bi Ajay da kallo har ya fita daga Eatry din da baturiyar da suke tare, shi bai ma taɓa ganinta ba sai ranan duk kwashe kwashen Ajay ne, bayan ma'aikaciyar wajen ta gama packaging abincin, yana kallonta ya tambayeta bill dinsa, nan ta sanar masa Ajay ya hada har nasu ya biya, Khaleesat ta daga kai ta kalli waitress din jin abinda tace, Jay yace "Ok then" Mikewa yayi ya dau ledan abincin Halysaah yana kallonta, ta tashi ta dau wayarta, yana gaba tana biye da shi suka fita daga wajen cin abincin, Lyft din da Jay yayi masu order har ya iso, ya bude mata back seat yana jiran ta shiga, Khaleesat felt somehow hakan da yayi, don duk fitar da suke yi da Abdul bai taɓa mata haka ba, yawanci ma shi yake fara shiga sannan ta shiga, bayan ta shiga motar Housemate dinta ma ya shiga, sai da suka kusa gida wayarta ya fara vibrate, ta kasa duba me kiranta sanin kila bazai wuce Abdul ba, Jay dake danna wayarsa ya kalleta yace "Kiran ki ake ai" Bata ce masa komai ba ta kalli screen din wayar sai taga Safiyyah ce ke kiranta, ta daga da sauri ta kai kunne tace "Hello Sophie" Safiyyah tace "Am at the door, nayi knocking shiru" Khaleesat ta ɗan saci kallon Jay, sai kuma a hankali tace "Ohk na ɗan fita ne amma ina hanya yanzu" Da mamaki Safiyyah tace "Kin fita? Ban gane kin fita ba, Ina kika je?" Khaleesat tayi shiru, Safiyyah tace "Ko da Housemate din ki?" Khaleesat tace "Um" Safiyyah tace "Hmmm i see, to in dai baku kusa dawowa ba bari inyi tafiyata kawai" Da sauri Khaleesat tace "Aa ki jirani am on my way" Tana fadin haka ta katse wayar, ajiyar zuciya ta sauke don tayi tunanin Abdul ne ya kira Safiyyah shine ta kirata, after some minutes suka isa gida, ta bude side dinta ta sauka daga Uber din, Jay ma ya sauka, Apartment dinsu ta nufa, ta ɗan rage pace dinta ganin kamar motar Mustapha a vicinity din, shi dai Housemate dinta na biye da ita a baya, sai ga Safiyyah ta fito daga motar Mustapha, da murmushi fuskarta ta nufesu ta gaida Jay, ya tsaya ya amsa mata sannan ya wuce cikin gida, Safiyyah ta kalli Khaleesat tace "Toh ki gaida ya Mustapha, dama girki na tsaya maki na zata har yanzu bakya iya tashi" Khaleesat ta kirkiro murmushi tace "Ohk bari in gaishesa" Zagawa tayi zuwa side din Mustapha taga yanda ya bi Jay da kallo har Jay ya shiga cikin gida, gaishesa tayi kanta a kasa, ya kalleta yace "Who is he Khaleesat?" A hankali Khaleesat tace "Housemate dina ne" Mustapha ya kalli Safiyyah yace "There was a time da kika ce min mace ce Housemate dinta?" Safiyyah tace "Eh wallahi the lady packed out shine shi ya shigo, ai bai wani dade sosai da dawowa apartment din ba" Mustapha ya kalli Khaleesat yace "Me yasa zaki dinga zama gida daya da namiji da sunan Co-living Khaleesat, why not come stay together with ur frnd Safiyyah in my house?" Safiyyah ta wani kallesa, sai kuma ta kyabe baki, sai kace ya gama kwatar mata 'yan ci gun shegiyar matarsa balle ya kwatar ma ita da kawarta, ita dai Khaleesat tayi shiru bata ce komai ba tana wasa da veil dinta, Mustapha yace "Wani yare ne Housemate din naki?" Caraf Safiyyah tayi tace "He is from Tanzania, yaren can kasar yake yi, beside shi baya ma wani zama a gidan once a while yake zuwa yayi karatu kawai" Mustapha ya wani kalleta yace "Ke na tambaya?" Gefe ta koma bata sake cewa komai ba, Mustapha yace "Daga ina ku ke da daddaren nan Khaleesat?" Khaleesat tace "I was sick tun da safe shine muka je ya siya min abinci yanzu" Mustapha dai sai kallonta yake, after some seconds yace "I will talk to my wife, sai ki dawo nan gidana kiyi zamanki tare da Safiyyah har ku gama Exams, i think the exam is by the corner...." Khaleesat tayi murmushi kawai bata basa amsa ba, Safiyyah tace "Mu je in kai maki abincin da na kawo maki ciki" Bude bayan motar tayi ta ciro abincin, Khaleesat tayi ma Mustapha sai da safe sannan suka wuce apartment dinta tare da Safiyyah, nan parlor Safiyyah ta ajiye abincin tayi kasa da murya tana washe baki tace "Ban gane wannan fitar da ku ke yi da Housemate dinki ba Khaleesat? Ina ku ka je?" Khaleesat tace "Abinci fa muka je ya siya min, kuma ba wai lapiyata lau muka je ya siya min abincin ba" Khaleesat ta ajiye ledan abincin hannunta ta zauna gefen kujera tare da sauke boyayyen ajiyar zuciya, Safiyyah dake washe baki tana ma Khaleesat wani kallo tace "To ya aka yi yasan baki da lafiya, kuma how did he know what was wrong with you?" Khaleesat tace "Kinga Sophie wnn ba shine damuwata ba yanzu, muna gidan cin abinci Abdul ya kirani" Safiyyah ta wani yatsine fuska tace "So? Da ya kiraki sai aka yi yaya?" Cike da damuwa Khaleesat ta bata labarin yanda aka yi da kuma call dinsa da ta ki picking tun jiya, Safiyyah tace "Haba, to ko ke fa da kika fara kokarin kwatar ma kanki 'yan ci, ni sai nake ga kamar Housemate din nan naki ne ke baki Liver kike wasu abubuwa yanzu, banda haka yaushe har kika yi bakin gaya ma Abdul magana haka" Tana dariya ta kare maganar, Khaleesat ta dinga hararanta ganin ta ma maida abun joke, Safiyyah tace "In ni ce ke ma bazan kirasa ba wallahi, gwara kawai komai ya ruguje kowa ya huta" Khaleesat tace "Kin manta abinda yayi kwanaki kawai muka gansa kamar an jefosa Sophie? Kinsan yanzun ma ba karamin aikinsa bane sai ya iya kamo hanya ya zo" Khaleesat ta dafe kanta tsabar she is confuse, Safiyyah tayi shiru, can kuma ta kyabe baki tace "Kuma haka ne ba kai ne da shi ba sai ya iya kamo hanya tunda ba su dau kudi bakin komai ba, kawai anjima ki kirasa sai ki kisa abinda zaki ce masa da zai gamsar da shi, kuma kina iya cewa baki da lafiya gantalallen ya kamo hanya, ni dama ya tafka wani tsiya America su kwace visan sa kowa ya huta" Duk da damuwar da Khaleesat ke ciki sai da tayi dariya, Safiyyah tace "Allah kuwa, ban ki ba ya zo ya maki hauka da kaina zan kira masa 911 wallahi" Khaleesat dai tayi murmushin karfin hali kawai, wayar Safiyyah ne ya fara ring ta duba taga Mustapha ke kiranta, turo baki tayi tace wannan mutumi yana takura rayuwata a kasar nan, wai daga cewa zan kawo maki abinci ya zata yawo zani shine fa ya biyoni, kema baki ji ba wai ki dawo gidansa da zama, salon wataran matar ta saka mana guba a abinci mu ci mu mutu gaba daya, yanzu haka fa ko ga maciji bama yi da ita, ɗan fitar nan da yayi da ni muna nan dake sai ya zamar masa matsala, tana can ta cika tayi fam tana jiransa, ko a jikina kuwa, sai na ma lallabasa ya kai ni ya siya min ice-cream ta yanda zata ga na dawo rike da leda" Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya bata ce komai ba, Safiyyah ta mike tace "Bari in je, sai mun hadu Monday in sha Allah" Khaleesat ta rakata bakin kofa a hankali tace "Thank you Safiyyah" Safiyyah tace "No thanks kawata, ki ce ma Housemate dinki na tafi" Khaleesat ta gyada mata kai, a haka Safiyyah ta fita daga gidan, Khaleesat ta kullo kofar a hankali, abincin da Safiyyah ta kawo mata ta dauka ta kai fridge da wanda Housemate dinta ya sa ayi mata takeaway. Khaleesat ta fito wanka kenan taji Housemate dinta na knocking kofarta, ta dau Hijab dinta ta saka sannan ta nufi kofar ta bude tana kallonsa, yana rike da laptop dinsa yace "Good night Halysaah, i am sleepy" Khaleesat tace "To sai da safe, thank you for the dinner" Yace "No thanks.... kin kira BF din naki?" Khaleesat taki basa amsa, yace "Amma bari in tambayeki, a ina kika hadu da gayen nan ne? Don't know ko na taɓa tambayarki kwanaki...." Khaleesat ta jingina da kofa without looking at him tace "Back home" Yana gyada kai yace "I see, ni at first na zata you are not Nigerian, was thinking you are from Niger or Chad, probably Shuwa Arab" Khaleesat ta dinga kallonsa, bata san sanda tace "Why?" Yace "Na ganki kamar Buzuwa" Khaleesat ta sauke idonta bata basa amsa ba, yace "Ok, i will be on my way, good night" Daga haka ya juya ya bar wajen, a hankali ta sauke idonta sannan ta kulle dakinta ta jingina jikin kofar, she stood there for almost 5 mins kafin ta karasa cikin dakin ta cire hijab din jikinta ta ciro sleeping dress dinta ta saka, sanitary pad dinta dake gaban dressing mirror ta dinga kallo, sai kuma ta dauke daga wajen, sai da ta kwanta sannan tayi dialing number Abdul gabanta na faduwa, har ya katse bai daga ba dama tasan ba lallai ya daga ba, ta sake kiransa nan ma bai daga ba, ta bude WhatsApp tayi masa magana ta nan, reply yayi mata yace "I don't have ur time so do not border me" tabe baki tayi ta ajiye wayar ta kashe wutan dakin sannan tayi kwanciyar ta lumshe ido, nan da nan bacci ya dauketa. Washegari bayan Khaleesat ta gama azkar din da take yi, ta jawo wayarta a hankali, tunda ta tashi jikinta yake a sanyaye don mafarki tayi Abdul ya zo kamar yanda ya zo wancan lkcn still kuma ya sake haduwa da Housemate dinta a gidan, ba karamin daga mata hankali mafarkin nan yayi ba, WhatsApp dinta ta bude bayan tayi deciding zata masa message din ban hakuri duk da bata saka ran reply dinsa ba, cause it won't be funny if her dream comes true, tana shiga WhatsApp din ta ga ya turo mata hotuna kusan biyar tun 3 hours ago, bude message din tayi zuciyarta na bugawa don bata san hotunan menene ba, nan taga har da message yayi mata kafin yayi sending hotunan, ta fara downloading hotunan at the same tana duba message din da ya rubuto mata kamar haka "So now, kina kokarin nuna min cewa i made the mistake of letting you go to America to study right? Kin mance wacece ke ko? kin mance daga inda kika fito, then that is so foolish and stupid of you Khaleesat, amma ina me tabbatar maki idan har kika ci gaba da daukata for granted kamar yanda kike yi kwanan nan sai na sa kinyi da kin sani wallahi" Lkci daya Hawaye ya cika idon Khaleesat, ta sauke idanuwanta kan hotunan da ya turo mata, daya hoto ne da shi yayi mata a bakin kofar dakin Ummanta, yana zaune kan tabarma ta duka gabansa zata ajiye masa ruwa a Cup shine ya dauketa hoton, shekaru hudu da suka wuce kenan, she look so so young and meek a hoton, hoto na biyu kuma tana wajen debo ruwa a nan unguwansu ya zo ranan ya ganta a wajen, ita bata ma san yayi mata hoton ba ga zaninta duk a jike, hoto na uku kuma tana baƙin murhu a tsakar gidansu tana juye alalan siyarwan Ummanta a Cooler shi kuma ya zo gidan ranan, duk bata san ya mata hotunan nan ba sai yau da ya turo mata ta gani, hoto na hudu kuma ranan da ya kai ta zata zana Jamb ne, jamb din da bata ma yi amfani da shi ba daga karshe, sai kuma hoton karshe na ranan da zai kawota USA for the first time, looking at all the pictures da kuma looking at her now zaka ga banbanci me tazara sosai, infact the difference is very obvious don a yanzu she looks more beautiful, matured, nourished and well taken care of, yanzu skin dinta har wani glowing yake, in ma ba ka santa ba bazaka taba cewa ita ce a hotunan ba, bata san sanda ta fashe da kuka ba ta hade kanta da pillow tana kuka sosai, but like seriously Abdul bai yi deserving haka daga gareta ba, but did she also deserve irin abubuwan da yake mata? Kuma tun asali haka yake mata, Kuka sosai tayi babu me rarrashinta, bata ma san me take ji a zuciyarta ba a lkcn, she cried profusely for almost 30 mins, daga karshe tayi karfin halin mikewa zaune ta dau wayarta, she don't even know where to start from, Voice note ta fara masa muryarta na rawa trying to tell him she is sorry, amma bata kai ko ina a basa hakurin ba ta fashe da kuka sosai, cikin kuka ta ci gaba da basa hakurin, sai da tayi masa Voice note uku sannan ta ajiye wayar still crying.... ✍🏻 07087865788 [5/15, 3:23 PM] khaleesat Haiydar ✍️: Read My Book "HALYSAAH" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=681294ff01c6bd900451c8e6 ✨✨ HALYSAAH✨✨ ✍🏻 By _Khaleesat Haiydar_ 18..... Wajen karfe goma na safe Khaleesat na kwance dakinta idonta rufe duk da ba bacci take ba, ji tayi ana kwankwasa kofa, kamar bazata iya tashi ba daga karshe dai ta mike ta sauka daga kan gadon ta dau hijab dinta ta saka, tana tafiya a hankali ta fito parlor, ta tagar parlon ta duba ta ga Housemate dinta ne, ta karasa ta bude kofar, Yace "Sorry na tashe ki kina bacci, i forgot the key at home" Ita dai bata yarda sun hada ido ba a hankali tace "Ina kwana?" Yace "Lafiya lau, how are you feeling now?" Ta juya going back to the parlor tace "Alhamdulillah" Ya bi ta da kallo sannan ya shiga parlorn, dakinta ya ga zata koma yace "Halysaah" Ta tsaya, after few seconds ta juyo but couldn't let her eyes contact his, shi dai kallonta kawai yake, ya karasa inda take tsaye yace "What happened?" Girgiza masa kai kawai tayi, lkci daya hawaye ya fara sauka idonta, ya dauke kai na 'yan dakiku kafin ya sake juyowa ya nuna mata kujera yace "Sit" Komawa tayi ta zauna, ya zauna shima yana kallonta yace "Tell me what's wrong" Ta sunkuyar da kanta, yace "Are you sick?" Ta girgiza masa kai, yace "Wannan saurayin naki ko?" Ta kasa basa amsa wasu hawayen na sauka idonta, sai kuma ta fashe masa da kuka, mikewa yayi yace "Waye ya hadaki da wannan mutumi ne? Why did u allow him know ur weak point? Why are you always crying because of him? Is he happy making u sad now and then?" Khaleesat dai kuka take a hankali, yayi shiru for almost 2 mins yana jin ransa na baci, can ya kalleta yace "Kee in zaki yi facing study dinki is better you do so, give that ur so called boyfriend space, ur exam is around the corner" Sai a sannan Khaleesat ta daga idanuwanta da suka yi ja ta kallesa, sae kuma ya kwantar da murya yace "Kiyi hakuri Housemate, zan dinga sa ki a addu'ata Allah ya maki mafita, i can't just intrude cause ban san sanda ku ka san juna da shi ba, ban kuma san me ya hada ku ba, i will only include you to my prayers i promise Halysaah" Khaleesat ta gyada masa kai da kyar, sannan ta mike cikin sanyin murya tace "Nagode" Daga haka ta juya ta nufi dakinta, Jay ya koma ya zauna yana mamakin irin son da take ma gayen da har ta kasa rabuwa da shi duk da musguna mata da yake yi a soyayya, bata da aiki sae yi masa kuka, da kanwarsa ce daga ita har saurayin zai hada ya ci ubansu, kuma ya rabata da shi na har abada, tausayinta yaji har cikin ransa don bai san wani irin so bane wannan take masa da har take iya tolerating abubuwan da yake mata, and ya lura the guy is taking advantage of this to hurt her always, mikewa yayi ya tafi kitchen kamar yanda ya zarga yaga alamar bata yi breakfast ba har sannan don kitchen din ma bata shigo ba, fridge ya bude ganin abincin da Safiyyah ta kawo mata jiya yayi mata microwaving dinsa ya hada mata shayi sannan ya kai mata daki, sai da yayi knocking ta amsa sannan ya shiga dakin, tun da ya shigo Khaleesat ke kallonsa har ya ajiye mata abincin, ta sauke idonta a hankali tace "Nagode" kai kawai ya gyada mata, sai kuma ta bi sa da kallo har ya fita daga dakin, karfe sha biyu saura Khaleesat ta jawo wayarta jin yana vibrate, tana duba screen din taga Abdul ke kiranta, ta sauke idonta kasa tayi picking call din ta kai kunne amma bata ce komai ba, yace "Khaleesah...." ta kasa amsawa hawaye ya fara sauka idonta, yace "Can you hear me?" Da kyar tace "Um" Yace "How was you night" tana share hawayen dake sauka idonta tace "Alhamdulillah" Tun daga wannan rana Khaleesat ta fara avoiding duk wani abu da zai hadasu fada da Abdul, she want just nothing but peace with him for her sanity, bin sa kawai take a yanda yake so for peace to keep reigning, in ma bala'i yake mata a waya zata yi shiru ta gama saurarensa sannan daga karshe ta basa hakuri kamar yanda take yi masa da, ranan da bai kirata ba kuwa ita zata kirasa, hakan kuma da tayi ya sa ta samu kwanciyar hankali har take concentrating a karatun ta, amma fa in ta tuna irin kulawar da Housemate dinta ke bata always wanting to make sure she is fine sai taji she isn't lucky having Abdul, ana haka har exams dinsu ya rage some days, ranan Wednesday tana kitchen da safe taji ana kwankwasa kofa, ta fito daga kitchen din don dama she is expecting Safiyyah, ta bude mata kofa, Safiyyah ta shigo tace "Ai na zata zan zo in tarar baki tashi ba?" Khaleesat tayi kasa da murya tace "Aa i am in the kitchen" Safiyyah tace "Ohk, why are you lowering ur voice?" Still Whispering Khaleesat tace "My Housemate is sleeping" Safiyyah ta sake baki tana kallonta, sai kuma ta rike haɓa tace "Ikon Allah gadinsa kike kenan?" Khaleesat ta hade rai tace "Ban gane gadinsa ba, daxu fa ya zo, and dama bacci yake zuwa yayi da safe don yace min baya bacci da daddare" Safiyyah couldn't stop smiling tana kallon Khaleesat, Khaleesat ta wani harareta ta juya ta koma kitchen, Safiyyah ta karasa ta zauna kan kujera har sannan bata daina murmushi ba, sai ga Khaleesat ta fito daga kitchen, still tana magana kasa kasa tace "Ko dai kawai mu je waje ki min gyaran gashin, kinga Hand dryer yana ƙara in ana using dinsa, it's noisy" Safiyyah ta buda baki tace "Ikon Allah, to akwai socket ne a wajen?" Khaleesat tace "Zan sa Extension a kitchen sai mu fito da shi ta window ai zai yi, kuma akwai tap a garden din sai mu wanke gashin ma a nan" Safiyyah dai murmushi kawai take bata ce mata komai ba, yanda Khaleesat tace haka din tayi duk don kar karan Hand dryer ya tada Housemate dinta or any of their noise kamar yanda tace, abinda bata sani ba ashe ba bacci yake ba aiki yake yi a Laptop dinsa a daki, bayan sun isa karamin Garden din dake bayan kitchen Khaleesat ta ajiye duk shampoo da Conditioner din hannunta sannan ta bude gashinta, Safiyyah na kallon gashin tace "Tab, Allah sa Shampoo din da Conditioner su isa dai" Khaleesat ta wani hade rai tace "Ban gane ba, saboda bargo za ki wanke?" Safiyyah tayi dariya tace "To meye banbancin wannan da bargon Khaleesat? Babancinsa kawai wannan akan ki yake, ni naga ma kamar karuwa gashin yake Tabarakallah Maa sha Allah" Khaleesat tace "Ba abinda ya karu yana nan yanda yake" A haka Safiyyah ta fara wanke mata gashin, suka dau time sosai bayan ta gama wankewa ta fara busar mata shi da Dryer, Jay ya shigo kitchen zai yi making Coffee drink ya dinga kallonsu ta window din kitchen, he was confuse seeing her hair, is all that Hair or what? long, full and black, kawai yaji bai yarda gashinta bane, ya juya ya fara yin abinda ya kawo sa kitchen din, Khaleesat ta kasa kunne sosai jin kamar sound a kitchen, ai ko ta jawo mayafinta da sauri ta rufe kanta bayan ta hangosa a kitchen din ya juya masu baya, Safiyyah dai sai kallonta take, Khaleesat ta mike ta isa kusa da window din kitchen din tana kallonsa tace "You woke up early today" Ya juya ya kalleta yace "This is to 12" Khaleesat ta zaro ido don bata san lkci ya wuce haka ba, ashe sun bata lkci sosai wajen wanke gashinta, yace "Me kike yi a nan?" Tace "I am together with my frnd Safiyyah" Ya ci gaba da abinda yake yi yace "Ohk my regards" Juyawa tayi ta koma gun Safiyyah, bayan Drying har Stretching gashin sai da Safiyyah tayi mata, Safiyyah tace "You know what Khaleesat, anjima ki zo can gida sai in maki Kalaba din, i think i can feel my period, i need to go home" Khaleesat ta juya ta kalleta tace "Da gaske?" Safiyyah tace "Wallahi, gwara in tafi gida kar ya zo" Khaleesat tace "Ohk, amma ki bari in dafa mana indomie ki ci tukun ki tafi" Safiyyah tace "Ke bazan ci ba, bari in tafi kawai i am uncomfortable" A hankali Khaleesat tace "To shikenan" Safiyyah tace "Sannan pls Khaleesat nace ma Ya Musty ran sunday zaki zo gidan tunda kinga Monday za mu fara exams, ko 2 days ne sai kiyi kafin matarsa ta fito da baƙin halinta gaba daya, kin dai ga bazai ce bamu ji maganarsa ba yace ki dawo gidansa baki dawo ba, even if it's just 2 days come and spend in his house pls" Khaleesat tace "Wallahi ba wai bana son zuwa bane ko kuma ban ji maganarsa ba Safiyyah, bana son issue ne da matarsa, i don't want any problem" Safiyyah tace "I know, shi yasa nace ko kwana biyu ne kawai ki zo kiyi ai bazai ce baki zo ba, ranan Sunday sai ki debi kayanki kala uku ki taho kawai, probably ma daga karshe nima nan gidan zan dawo mu yi karatu tare, ni nasan ba lallai ma kiyi kwana biyun ba matarsa bata kirkiro wata matsala ba, so just chill ba zama zaki yi a gidan ba Likewise myself" Khaleesat tayi shiru kamar me nazari, sau biyu Mustaphan ke mata magana da kansa ta WhatsApp akan dawowar da yace tayi gidansa, iyaka sai tace masa in sha Allah tana nan zuwa before exam, Safiyyah ma tayi mata magana yafi a kirga, ko don Safiyyah zata daure kawai taje tayi kwana biyun a gidan, let it not be as if bata jin magana, a haka ta raka Safiyyah bayan tayi order din Uber da zai maida ta gida, Khaleesat na dawowa parlor taga Housemate dinta ya shirya zai fita, yana kallonta yace "Wai duk gashinki ne wannan ko dai ƙarin gashi kike yi Halysaah?" Ta daga idanuwanta ta kallesa bayan tayi realizing ashe ya ganta kenan daxu, sauke idonta tayi tace "Ƙarin gashi kuma?" Yace "Naki ne? Ai na gansa kamar ba naki bane, sorry" Ɗan murmushi kawai tayi without giving him an answer, can yace "Wait, amma ba ki jin zafi na damun ki? I mean baya takura ki gashin? isn't it too much?" Tace "How?" Sounding so serious yace "Ki rage mana, just cut half of it off kema ki huta, sai kiyi azumi uku, wannan ai burden ne Halysaah, it's too much, ji fa sai da kawarki ta zo taya ki wankewa don kema baza ki iya wankesa da kanki ba, all this while ni na zata irin wannan acuci mazan da ku ke yi ne kike daurawa a kanki, i never knew gashin ki ne" Khaleesat tayi murmushi ba tare da tasan tayi hakan ba, can ta kallesa calmly tace "But i am not complaining, kuma ai ba nauyi gashin yake min a kai ba" Ya wara ido yace "Ohh! my bad, haka ne kuma fa, hope you are reading so well for ur exam, kinga in few days time zaku fara, i think monday ko?" Ta gyada masa kai, yace "Wishing you the very best of luck Halysaah" a hankali tace "Thank you" Yace "See ya later" Ta gyada masa kai, daga haka ya juya ya nufi kofa ya fita daga parlon.... Da yamma Khaleesat ta gama shiryawa bayan Safiyyah ta isheta da kira wai taje ta mata kitson, Khaleesat ta dau handbag dinta da mukullin gida bayan Uber din da tayi order ya iso sannan ta fita daga gidan ta kulle, tana hanya kiran Safiyyah ya shigo wayarta, ta daga tace "Ina hanya fa" Safiyyah tace "Allah in baki zo ba sai dai gashinki yayi ta zama haka bani da lokacin maki wani kalaba kuma idan aka fara jarabawa" Khaleesat dai tayi murmushi, tasan kawai Safiyyah so take ta je gidan, karfe hudu da yan mintuna ta isa gidan ta sauka Uber sannan tana tafiya a hankali ta nufi apartment din, tsayawa tayi bakin kofa ta danna bell, lkci daya aka bude kofar, sai da gaban Khaleesat ya fadi ganin Surayya ce ta bude mata kofa, ta sauke idonta tace "Ina yini?" A takaice Surayya tace "Wa kike nema?" Khaleesat ta daga kai ta kalleta tace "Wajen Safiyyah na zo" Bluntly Surayya tace "To bata nan, sai ki juya ki koma inda kika fito" Khaleesat was just looking at her babu ko kiftawa, sai ga Safiyyah ta fito daga daki fuuu, tana huci tace "Wajenta kika zo da zaki tsaya sauraronta baki bangajeta ba kinyi shigowarki?" Khaleesat ta bude baki tana kallon Safiyyah, wato ta bangaje matar gida ta shigo tsabar neman jifa'i, Surayya ta juya a fusace tana kallon Safiyyah tace "Tunda gidan na ubanta ne ko naki uban sai ta shigo mu ga" Safiyyah tayi cilli da wayar hannunta ta fige dankwalin kanta tace "Wallahi kar ki ga na raga maki daxu saboda yaya, to yanzu baya nan cin kaza kazanki zanyi la'ada waje" Khaleesat was shock, ta kasa rufe baki tana kallonsu, Surayya ta nufi Safiyyah tana kunduma mata zagi kamar dai yanda tayi mata few hours ago a gaban cousin brother dinta, instead sai cousin din ya dinga ba Safiyyah hakuri without taking any action, dama Safiyyah a wuya take, sbda bakin ciki ne ma yasa ta dinga kiran Khaleesat ta zo gidan, Khaleesat ta zaro ido ganin yanda Safiyyah ta finciko Surayya cikin zafin nama, ba ayi wata wata ba suka fara tikar dambe a wajen, Khaleesat ta karasa ciki da sauri tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, meye haka kuke yi Safiyyah? Don Allah ku bari" Yaron Surayya dake kan kujera sai tsala ihu yake, Khaleesat tayi kokarin rabasu taga an cillar da ita gefe har sai da ta kusa faduwa, bata sake gigin zuwa kusa da su ba, ta bude wayarta da sauri ta fara neman number Mustapha, tana kokarin kiransa taga Surayya na harin fixgo wani flower vase zata buga ma Safiyyah a kai, hakan yasa Khaleesat ta tafi da sauri ta dauke Vase din daga inda yake, Safiyyah tayi using opportunity din ta fixge vase din a hannun Khaleesat ta maka ma Surayya a goshi, sai ga jini kuma hakan bai sa sun fasa damben da suke ba, ko da Khaleesat ta kira Mustapha ashe yana hanyar dawowa, cikin few minutes sai gashi ya shigo gidan, sai shi ne ya rabasu bayan sun yi ma juna laga laga, Surayya bata daddara ba tayi kukan kura tayo kan Khaleesat zata cafkota tana cewa "Kika bata Vase ta buga min, wallahi kema sai na ci kaza kazan ki" A nan ne Mustapha ya sauke mata mari ya fincikota yace "Ko kin fara hauka ne Surayya? Me kike son mayar da ni a kasar nan ne?" Ita dai Khaleesat ta tsorata sosai, Safiyyah na huci tace "Shegiya bayerabiyar banza kawai jaka jahila..." Bata rufe baki ba ita ma Mustapha ya kai hannu zai gaura mata mari ta kauce da sauri tana harare harare tana huci, Surayya dake kuka wiwi ta figi ɗan ta zuwa sama tana cewa "Wallahi sai dai ka zaba ko ni ko Safiyyah a gidan nan yau, in ko ba haka ba ni zan bar maku gidan kayi zaman auren da ita" Safiyyah ta sauke ajiyar zuciya ko ba komai dai ta fasa mata kai hankalinta ya kwanta ta kuma ji dadi, Mustapha ya zauna saman kujera ya dafe kai, juyawa Khaleesat tayi sum sum ta fita daga parlon wishing dama bata zo gidan ba kilan da haka bai faru ba, da tasan bala'in da za ayi kenan babu abinda zai fara fitowa da ita daga gida, Safiyyah ta figi dankwalinta zata bi ta, Mustapha ya mata tsawa yace "Kar ki kuskura ki fita daga gidan nan" Safiyyah ta fashe da kuka tana bubbuga kafa tace "Ni wallahi yaya na gaji, na gaji kuma haka, na gajiiii, dubi cin mutuncin da matarka ta min daxu kace in kyaleta, yanzu kuma daga kawata ta zo wajena in mata kitso shikenan sai ta fara kunduma mana zagi ta kamani da dambe??" Yace "Wuce dakin ki nace" Ita dai Khaleesat tuni ta kara gaba ta bar gidan. That same day wajen karfe biyar da rabi sai ga Safiyyah ta zo gidan Khaleesat, Khaleesat ta zauna gefenta bayan sun shigo parlor tana kallonta tace "Ban ji dadin abinda ya faru ba yau Sophie, da na sani da ban je gidan ba ma wallahi" Safiyyah tace "Ai abun duniya ne ya dameni kamar in hadiye zuciya shi sa nayi ta kiranki ki zo daxu, wai fa bayan na gama yi maki gyaran gashi na koma gida matar nan kamar jirana take ta kama zagina ta uwa ta uba a gaban mijinta wai don me zan zubar mata da sauran miyarta dake kitchen, kuma fa kar kice da miya a tukunyar Khaleesat, wallahi ba komai ciki sai wani guntun miya da yayi tsami sai bugawa yake, ni kuma na wanke na dafa indomie na ci kafin in taho nan daxu in maki gyaran gashi, Ya Mustapha ya hanani cewa komai ya bani hakuri na wuce daki, a banza tunda dai shi ma har uwayensa ta zaga, shine bata daddara ba da kika zo zata sake hadamu ta zage ga yan iska sai muyi shiru muna kallonta, ni wallahi so nayi ace ma na cire mata hakora biyu ta dawo wawulo, amma dai a juri zuwa rafi wallahi sai na mata illar gaske kafin in gama karatu a kasar nan, dama tun 3 weeks ago da muka zo muka kawo maki abinci da ni da Y Mustapha ta kara kullatata ta kara tsanata tunda har yau tayi tunanin da akwai wani abu tsakaninki da Mustapha, ko ga maciji fa bama yi da ita a gidan" Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya ta kamo hannunta tace "Ki dai dinga hakuri plss Sophie wataran sai labari, da ni ce ke ma wallahi bazan dinga biyeta ba a gidan nan" Safiyyah tace "To ai ba kowa ke da matattciyar zuciyar da kare ya lashe irin taki ba, amma wallahi tayi kadan in ki biye mata, tana ce min kule zan ce mata casss don ubanta, an gaya mata ita ta isa ta shiga tsakanina da Mustapha? Cousin dina ne fa, Uwarsa ce ta sha nono ta bar ma uwata, Babansa kuwa Cousin din babana ne halaq malaq, ina ga bai taɓa zaunar da ita ya mata bayanin nan dalla dalla bane, kuma ya ci sa'ar bana kai karar abinda matsiyaciyar matarsa ke yi min gida, don wallahi da tuni an dau mataki, amma dai bari mu yi hutu in koma Nigeria" Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya tace "Zancen gaskiya ke ma fa kina da naki Safiyyah, babu ta yanda za ayi kina zaune da mata ko ɗan wanke wanken nan da shara baza ki ke taya ta ba a gidan, Abinda fa idan an mana mun san baza mu ji dadi ba to kar mu yi ma wani, she is also human, kuma at times bacin rai ne ke triggering wani mugun halin mutum, kece kika yi triggering din halinta a gidan, babu ta yanda zaki ji dadi wataran kanwar mijinki ta zo gidanki ta zauna bata taya ki aikin komai sai dai in kinyi girki ta deba ta ci ta ajiye maki plate, ki duba wannan lamarin fa, mu mata muna da son kanmu wani lkcn..." Safiyyah ta dakatar da ita tace "Ohh wato goyon bayanta ma kike kenan Khaleesah? you are trying to say duk abinda take min yayi dai dai ko?? To nagode, dama ke baki taɓa goyon bayan mutum a duk halin da yake ciki, in dai mutum zai kawo maki damuwarsa to ya kara dulmiya kansa cikin damuwa ne, ni kuma ban taɓa kin supporting dinki ba no matter the situation, ko Abdul da nake zagi kullum kamar ɗa na nake goyon bayanki an gaya maki kema baki da naki baƙin halin ne wani lkci? Dama mistake nayi ma na zo gidan nan asirina a rufe da gidan Sandra na wuce da ba a kara bata min rai ba" Tana fadin haka ta mike ta figi jakarta ta nufi kofa kamar zata tashi sama, Khaleesat ta mike tace "Safiyyah" Banza da ita Safiyyah tayi har ta fice daga parlon ta kullo mata kofa, Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya ta koma ta zauna, a hankali tace "Ae shikenan" ✍🏻 07087865788 [5/15, 7:17 PM] khaleesat Haiydar ✍️: Read My Book "HALYSAAH" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=681294ff01c6bd900451c8e6 ✨✨ HALYSAAH✨✨ ✍🏻 By _Khaleesat Haiydar_ 19.... Ranan friday wajen karfe sha daya na safe Khaleesat ta gama Laundry da take a kitchen ta fito, a reading nook din parlon ta tarar da Housemate dinta yana duba textbooks dinsa, cikin few seconds ya dau wanda zai dauka ya dawo cikin parlon yana kallonta yace "Har kin gama kenan" Kai kawai ta gyada masa ta fara tidying din parlon, rana na farko kenan da ta fara ganinsa yayi shiga irin ta Hausa cikin fararen kaya, Taji yace "Hope you are studying well Halysaah" kai kawai ta gyada masa, yace "Alright, till later" Ta ɗan kallesa tace "Are you Nigerian?" Ya buda ido yace "Why do u ask?" Tace "Kawai nayi zatan ko daga Chad kake, or Niger" Dariya yayi yace "Hope it's fine now tunda kin rama?" Hanyar dakinta ta nufa ba tare da ta basa amsa ba, ya dau makullin motarsa ya nufi kofar parlon, sai bayan da ya fita sannan ta dawo cikin parlon ta tafi gun window ta ɗan bude drapery din jiki tana leka garage, ganin har ya tafi ta ci gaba da aikin da take yi a parlor. Wajen karfe biyar na yamma Khaleesat na kitchen tana girki at the same time suna waya da Abdul, tun 40 mins ago ya kirata suke magana har sannan, duk kwanan nan dai lafiya suke waya da shi, ya kuma ɗan rage mata wasu abubuwan da yake mata, he is being a little caring these days, a rana sai su yi waya sau biyu wani lkcn har sau uku har hakan na bata mamaki kamar dai ba shi ba, yanzun ma shi ne yayi encouraging dinta ta tashi ta fara girkin da take yi don bata yi niyyar girki ba, for weeks now kullum Housemate dinta ke masu takeaway na dinner wani lkcn har lunch, this made her soo lazy to go to the kitchen, breakfast dama tea and cookies take ci yawanci ko kuma ta ci da bread idan Housemate dinta ya siyo, wani lkcn ta ci french fries da kwai ko ketchup, kwankwasa kofar parlor taji ana yi, ta ɗan zaro ido sanin bazai wuce Housemate dinta ba, kilan ya mance makullinsa ko kuma yayi misplacing dinsa as usual, ta kalli wayarta dake ajiye a kan kitchen cabinet har sannan Abdul was on the line kuma a handsfree ta sa wayar, tana ɗan kame kame tace masa "Can u excuse me pls, i will call u back in the next 2 minutes pls" Abdul yace "Why? Me zaki yi? Is the call hindering you from doing anything?" Da sauri tace "Noo" don bata son tayi laifi, sai kuma a hankali tace "Just want to round up the cooking ne, na kusa gamawa ai" Yace "But my call isn't preventing you from doing so, wayan ba a ajiye yake ba? Continue with ur work kawai" Knocking ta sake ji, ta ma san Housemate dinta ne cause haka yake knocking dinsa, ta kalli wayarta tace "Ohk then" Abdul ya ci gaba da maganar da yake mata, a hankali ta dau wayar ta fita daga kitchen din almost tiptoeing kamar tana tsoron yaji sound din tafiyarta, ta nufi kofar parlon ta bude at the same time tana kokarin yi ma Housemate dinta alamar da yayi shiru ta hanyar dora finger dinta daya a lips dinta, lkci daya taji komai nata ya tsaya cak, a hankali ta zame finger dinta daga lebbenta tana kallonsa bata ko kiftawa zuciyarta na bugawa, ta cire wayar dake kunnenta looking speechless and Surprise at the same time, Calmly yace "Ko in koma ne?" Ta zaro ido cikin in ina tace "No, no, not at all, i... i was just being surprise, sannu da zuwa" Da sauri ta koma gefe zuciyarta na bugawa da karfi, Ya katse wayar dake kare kunnensa sannan ya shiga parlon, ta bi sa da kallo still shocked, gani take kamar she is daydreaming, ta kikkifta idanuwanta ta bude to be sure but still she is still seeing him, har sai da ya karasa cikin parlon ya zauna sannan ta bi bayansa, a hankali ta duka kusa da shi tana yaƙen karfin hali tace "Wai dama all this while kana garin nan ne? I am so confuse" Yace "Gashi kin gan ni, in baki yarda ba sai ki taɓa ki ji don ki tabbatar" Still feigning smile tace "I am seriously surprise, this is the least thing i expected today wallahi..." Sai kuma ta tashi da sauri tace "Let me get u water" Kitchen ta tafi zuciyarta na bugawa, sai da ta jingina jikin cabinet ta dafe kirjinta a hankali tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, na shiga uku" Tasan at anytime Housemate dinta zai iya shigowa gidan don yamma yayi sosai, cikin hanzari ta bude fridge ta dauko masa ruwan gora da drink with glass cup sannan ta fita da sauri, tana kirkiran murmushi ta durkusa gabansa ta ajiye masa tace "Tun yaushe kake garin nan amma?" Ya dau ruwan goran yana kallo yace "You are buying expensive water now? Sannu er gayu" Tayi dariyar karfin hali tace "Not at all, miyar ma ya kusa yi sai in zuba maka abincin, ko dama shi sa kace sai nayi girki?" Kawai murmushi yayi bai bata amsa ba, ta mike ta koma kitchen, gaba daya she is confuse on what to do, ta fara dube duben wayarta ta tuna ta ajiyesa kan kujera a parlor, fitowa ta sake yi ta tarar Abdul yayi picking din kiran da ake masa ta waya, cikin dubara ta dau wayarta ta nufi dakinta da sauri tana kallonsa ta gefen ido taga attention dinsa na kan wayar da ya fara, bandakinta ta shige ta kulle tace "Na shiga uku" Da ta tuna bata ma da lambar Housemate din nata ta sake jin mugun tashin hankali, yanzu ya zata yi? Da sauri ta fara dialing number Salem, ai ko yana fara ring ya daga, murya can kasa ta gaishesa without waiting for his full reply tace "Plsss how can i get in contact with my Housemate? ina son zan masa magana ne urgently" Salem yace "Ohk, muna ma tare, gashi nan" Bata san sanda ta sauke wani irin ajiyar zuciyar relieve ba, taji muryar Housemate dinta yace "Hello Halysaah, is everything alright?" Ta girgiza masa kai da sauri kamar yana ganinta tace "Plss i am sorry amma kar kace zaka dawo yau, my fiance is around, he just came without notice" Yace "Tohhhh, haka kuma aka yi ashe?" Ta wani turo baki kamar yana ganinta, yayi murmushi yace "Alright Halysaah, keep ur cool, duk sanda ya tafi sai ki sanar min" A hankali tace "Thank you" Yace "Not a problem" Shi ya fara katse wayar, ta kalli screen din sannan ta sauke ajiyar zuciya ta fito da sauri bayan ta bar wayar a dakinta, har sannan ta tarar Abdul bai gama wayar da yake ba, da alama business call ne, Khaleesat na tafiya a hankali ta tafi kitchen don saka masa abincin da ta girka, har sannan she is shock, babban damuwarta yanzu kasantuwarsu su biyu kadai a gidan, a da bata jin tsoron kasancewa da shi guri daya and that was almost 4 years back, but not anymore, he is complete changed all of a sudden in just a year, da tunanin nan ta fito daga kitchen, ta karasa har gabansa ta ajiye masa abincin, yana kallonta yace "How about ur Housemate, bata nan ne?" Ta ɗan yi murmushin karfin hali tace "Yeah bata nan" Ta mike ta koma edge din kujera ta zauna kamar bakuwa a gidan, a hankali tace "Ya su Momy da Aunty Hafsah?" Yace "Lafiya lau" Bata sake cewa komai ba, Ya kalli abincin da ta ajiye masa yace "I am full, ki rufe sai dai anjima" A hankali tace "Ok tafiya zaka yi da shi?" Yana dubanta yace "In tafi da shi ina?" Ta kirkiri murmushi tace "A'a ai tambaya kawai nayi" Yace "Na riga nayi lodging out of the hotel, i was in Maryland since morning" Khaleesat was speechless, bata gane yayi lodging out of the hotel ba, to ina zai kwana ko kuma wani hotel din zai kama? kai bata ma yarda ba don in yayi lodge out to ina trolley din kayansa yake, Tana murmushi da kyar tace "To ina akwatin ka?" Yace "Tana cikin mota" Ta hadiye abu da kyar tace "Motar wa?" A takaice yace "Ban sani ba" sunkuyar da kai tayi bata sake cewa komai ba, yace "Ko kina da plans ne yau? Naga kinyi mamakin zuwana da gaske" Ta zaro ido tace "Not at all wallahi, ai kai ma kasan daga schl babu inda nake zuwa, kawai dai nayi mamakin muna ta waya tun daxu ashe kana garin nan" Ya mike yace "To ki dena mamaki tunda ba ke kika siya min ticket din ba" Ta sunkuyar da kanta tayi shiru, dakinta ya nufa yace "Let me take a shower" Khaleesat ta gyada masa kai kawai ta bi sa da kallo, a very tall and masculine guy he is, just like her Housemate, and they are all handsome in their own different ways kamar su suka yi kan su, sai dai ita tafi ganin kyan Housemate dinta ko me yasa, a zahiri duk macen da ta samu Abdul in dai mayyar kudi ce kuma tana son namiji me tsantsan kyau ga kuma qualities na cikakken namiji pertaining to body structure not behavior... to duk walakancin da Abdul zai dinga mata zata jure tayi ta shanyewa don mijin nuna ma sa'a ne shi din, that is if behavior isn't included, amma Khaleesat dai dai da rana daya qualities din nan biyu na Abdul bai taɓa dada ta da kasa ba, a haka stepsisters dinta ko ga maciji basa yi da ita all because of Abdul, kiri kiri suke nuna mata jealousy dinsu daga su har iyayensu a fili, ba su kadai ba hatta wasu daga sa'aninta a anguwa sun dena kulata saboda shi, basu san baƙin cikin da take kunsa day by day ba, she wish zai koma ma daya daga stepsisters din nata da ita kam ta huta, kwantar da kanta tayi jikin kujera tana jin hankalinta na kara tashi, yana nufin kenan bazai tafi anytime soon ba? kilan ma yace nan zai kwana fa? Sosai hankalinta yayi mugun tashi da tunanin hakan, after a while ta mike a sanyaye ta dau abincin da ta zubo masa ta tafi da shi kitchen ta rufe, ana haka har lkcn sallan magarib yayi bai fito daga dakinta ba, Khaleesat dake ta zaune a parlor kamar bakuwa a gidan ta kalli kofar dakin nata a sanyaye, sai kuma ta tashi walking slowly ta nufi dakin, a hankali tayi sallama sai da ya amsa sannan ta bude, ta samesa zaune saman darduma alamar sallah ya idar yana danna wayarsa, gaba daya dakin ya cika da kamshin turarensa, murmushin karfin hali ta kirkiro ta dau hijab dinta tace "Sallah zan yi" Sai kuma ta juya zata fita yace "Ina zaki yi sallan?" Ta sake juyowa cikin sanyin murya tace "Parlor" Mikewa yayi ya bar kan darduman yace "Pray here, dama kin saba sallah a parlon ne?" Ya koma gefen gado ya zauna still pressing his phone, da kyar ta karasa kan darduman ta fara sallan, bayan ta idar ta dinga addu'ar Allah ya taɓa zuciyarsa ya tashi ya tafi ya bar mata gidan ita dai, muryarsa taji yace "Make me a cup of hot chocolate" Ta gyada masa kai tace "To" Mikewa tayi ta nufi kofa ta fita zuwa kitchen, abinda yace tayi ta masa sannan ta koma dakin rike da mug din, bedside drawer ta ajiye masa tace "In kawo maka abincin?" Yace "Aa bazan ci abinci ba, me yasa kike yawo da Hijab kamar matar liman" Tana murmushin karfin hali da kyar tace "Aa ina jiran lkcn isha ne" Yace "Cire Hijab din nan" Ba musu ta cire a hankali ta linke ta ajiye, yace "Ke kin ci abincin ne?" Duk da bata ci ba ta gyada masa kai don gaba daya ta nemi appetite dinta ta rasa, gun reading material dinta ta tafi ta zauna ta kunna laptop dinta tayi kamar karatu take, ya gama danne dannensa a waya ya dau chocolate dinsa ya fara sha, gaba daya Khaleesat bata fahimtar me take dubawa a laptop din gabanta, sun kusa awa daya a yanda suke, ita dai har sannan tana gaban laptop taki tashi, ta gefen ido ta kallesa ganin ya mike daga inda yake zaune, taga sallan isha zai yi, sai da ya idar sannan ita ma ta tashi ta tafi tayi sallan, nan ma babu kalan addu'ar dabata yi ba kan Allah ya taɓa zuciyarsa ya koma hotel dinsa, after a while ta mike ta dauke darduman ta linke ta ajiye, ya mike ya kamo hannunta yana kallonta yace "Why are you uncomfortable kamar kina tare da stranger a gidan nan ne Khaleesat?" Tayi dariyar yake tace "Stranger kuma Ya Abdul? Ai kai ba stranger bane, kai yayana ne, kuma da ai ka sha kwana gidan nan farkon da na zo kasar, kana kwanciya a parlor ni kuma in kwanta a daki" Yace "Kinsan da haka kike dari dari?" Ta sunkuyar da kanta ganin kallon da yake mata, zuciyarta ya dinga bugawa, har ji take kafafuwanta suna neman kasa daukarta, ya matso da ita dab da shi har tana iya jiyo breathing dinsa, calmly yace "Kinsan menene yasa nake kwanciya a parlor a sannan?" Ta girgiza masa kai without looking at him don she is soo uncomfortable with him drawing her closer to himself, yayi kasa da murya yace "Saboda u were still a baby sannan" Ta daga idanuwanta da kyar ta kallesa amma ta kasa cewa komai, yace "Yanzu kuwa ke ba baby bace, how old are you?" Ta kasa basa amsa, ya ɗan mata tsawa yace "Tambayarki nake?" Ta hadiye wani abu da kyar tace "I am 20" yace "To a sannan ina keeping distance between us because i was still grooming you" Ta kauda kai seeing how closer he was coming to her, juyo da kanta yayi yace "Meye haka?" Muryarta na rawa tace "This is against the teaching of islam Ya Abdul, ni ba muharramarka bace" Yace "Oh really? Dama wani ne zai aure ki ba ni ba ashe?" Ta kasa ce masa komai lkci daya hawaye ya cika idonta, duk tsiyar da yake mata da yaga hawaye idonta yake calming down, ya jawota jikinsa yayi kasa da murya yace "Kin zata ke irin matan da zan yi using inyi dumping ne Khaleesat? You are diff from them, ke matar da zan aura ce" Ta kasa basa amsa hawaye na zuba idonta, ita kanta tasan Abdul so na aure yake mata, a shekarun da suka yi tare iyaka yakama mata hannu babu dadi babu kari, amma daga 2 years back labarin ya sauya har bata son ya zo inda take don sai ya mata wasu abubuwa dake damunta, in ya tafi ta sha kukanta kuma ta kan yi kwana da kwanaki bata dawo dai dai ba, amma bai taɓa attempting saninta ba, muryarsa ne ya dawo da ita daga tunanin da ta tafi, as if whispering yace "I have tried Khaleesat, i abstained from doing anything that will distabilize you all this years because i want you to have the best education ta yanda zan iya nuna ki a ko ina as my wife, amma kullum ina jin urge dinki a raina I've tried so many times to ignore the urge, but menene ya rage yanzu? You have just a year and few months to round up, aurenmu kuma ko yau aka ce a daura babu abinda zai hana daurasa, i came all the way from Nigeria because all this days my feeling for you is distabilizing me and making me go nut Khaleesat, so now trust me, relax and keep calm pls baby gal" Khaleesat ta dade bata shiga tashin hankalin da ta shiga a sannan ba, don sarai ta fahimci inda maganarsa ya dosa, kuma lkci daya yake magana yana cire mata hijab din jikinta, common ya taɓa ta idan taki ta karfi yake yi mata balle wnn, gashi gaba daya yanayinsa ya canza alamar ya fara fita hankalinsa ma, ta kamo hannunsa jikinta na rawa tace "But kwanakin da suka rage ai basu da yawa ko Ya Abdul, why not be patient pls..." Ya kalleta da idanuwansa da suka kada strictly yace "I can't wait any longer" Muryarsa kadai sai da ya tsoratata hakan yasa tayi gum da bakinta, tana jin zuciyarta kamar zai fito daga kirjinta tsabar tashin hankali, kafin ya rabata da kayanta tayi kasa da murya still holding his right hand tace "Ohk pls ka bari inyi wanka tukun, kai ma ai ka yi" Ya dinga kallonta da idonsa da suka yi ja, ta sunkuyar da kanta trying to control herself kar ta fashe da kuka tace "I won't take long" Saketa yayi ya koma gefen gado ya zauna, tana tafiya da kyar ta nufi bandaki tana kallon wayarta dake gaban dressing mirror, ta ɗan kallesa, taga bin ta yayi da kallo, ta dake da kyar tace "Zan dau shower gel dina" Gaban mirror dinta ta nufa, dai dai sanda ya fara cire rigar jikinsa da sauri ta dau wayarta da wani Container din lotion da tayi pretending shower gel ne sannan ta shige bandaki ta kulle kofa, tap ta bude jikinta na rawa hawaye na sauka idonta ta fara dialing number Salem, yana fara ring ya daga, da kyar tace "Plss i want to speak to my Housemate plss" Salem yace "Oops wllhi bama tare yanxu" Ko rufe baki bai yi ba tace "Don girman Allah ka turo min lambarsa yanzu" Yace "Ohk let me send you" Yana katse wayar ta dinga kallon screen dinta tana jiran shigowar lambar Housemate dinta, her body was just shaking, ga wani bugawa da zuciyarta yake, cikin few seconds sai gashi ya turo mata lambar, da sauri tayi dialing ya fara ringing amma har ya katse bai daga ba, ta sake kira nan ma bai daga ba, sau uku tana kiransa bai daga ba, ta saki kuka ta durkusa kasan bandakin tace "Na shiga uku" Sake dialing number Salem tayi, yana picking tace "Pls bai daga ba ko zaka..." Salem bai jira jin sauran bayaninta ba yace "Bari in tura maki number Ajay, nasan dama ba lallai Jay ya daga ba don ba ko wani kira yake dauka ba, sai kice ma Ajay ya basa suna tare yanzu" Tana gyada kai da sauri tace "Ohk to Nagode" yana katse wayar sai gashi ya turo mata number Ajay, tayi dialing number da sauri hannunta na rawa, ai kuwa yana fara ringing da few seconds aka daga, da kyar tace "Plsss ina son zan yi magana da Housemate dina ne" Shiru taji yayi as if processing the voice, sai kuma a takaice yace "Waye wannan?" Ta fara shesshekar kuka muryarta na rawa tace "Don Allah kayi hakuri ka rufa min asiri ka basa ina son zan masa magana" Yace "Me ya faru?" Cikin kuka tace "I need his help plss" katse wayar taji yayi, hankalinta in yayi dubu ya tashi a moment din nan, ta shiga uku ta lalace, yanzu ya zata yi, ko dai ta kira Safiyyah, number Safiyyah ta duba da sauri tayi dialing amma har ya katse bata daga ba, ji tayi kamar za a bude kofar bandakin tayi saurin tsoma wayar hannunta cikin ruwan da ta fara tarawa a bath tub a gigice, ashe kunnenta ne ma yaji kamar an taɓa kofa amma ba kowa gun kofar, ta ciro wayarta taga screen din yayi baƙi, ta dinga yarfe ruwan da ya shiga tana kokarin kunnawa amma yaki kunnuwa, hade kanta tayi da bath tub hawaye masu zafi na sauka idonta.... *End of free pages, za mu ci gaba da update a payment group* *For continuation of the book Halysaah, pay 500 into 3276052019 Fcmb Hauwa Bello Jiddah* ✍🏻 _And ur evidence of payment via 07087865788_ *My special thanks to those that have already patronized since the beginning of this book, Thank you so much and i appreciate you*🥺 [5/18, 3:12 PM] khaleesat Haiydar ✍️: Khaleesat ta kusa minti sha biyar a bandakin cikin tashin hankali da confusion, banda kuka babu abinda take yi, she can't even think straight tsabar yanda ta shiga tashin hankali, to ko dai kawai ta fita ta gudu ta bar gidan ne, ko kuma taje ta basa hakuri ya rufa mata asiri, ta ma san bazai taɓa sauraronta ba, da kyar ta mike daga durkushen da take hawaye sosai na zuba idonta har sannan jikinta rawa yake, gani take kamar the world have come to an end for her, hannunta na rawa ta wanke fuskarta tayi karfin halin bude kofar bandakin a hankali tana leka Bedroom dinta, zaune ta gansa edge din gado yana danna wayarsa, suna hada ido ta bude kofar ta fito, ya dinga kallonta daga sama har kasa, hakan yasa ta sunkuyar da kanta zuciyarta na bugawa, Mikewa tsaye yayi yana mata wani kallo yace "So you just wasted my time all this while ba wankan kike ba dama?" tears was just rolling down her cheek tana girgiza masa kai muryarta na rawa tace "Don girman Allah kayi hakuri, kar kace zaka...." Dakatar da ita yayi ta hanyar daga mata hannu, tuni ta ja bakinta tayi shiru tana kallonsa a tsorace ganin yanda lkci daya yanayinsa ya canza, tana ganin ya nufota ta juya zata koma bandakin da gudu yayi saurin fixgota, ta rushe da kuka sosai tana cewa "Don girman Allah kar ka min haka ka rufa min asiri Ya Abdul" Yana mata wani kallo yace "You think i will just waste my time and money coming here at the end in kyaleki da childishness dinki in koma Nigeria? You must be joking, In kika ga na kyaleki yau sai in faduwa nayi na mutu" Zuwa sannan Khaleesat bata ma san kalmomin dake fitowa bakinta ba ta dinga basa hakuri a rikice, ta dai san ko da wasa bazata ce zata yi kokuwa da shi ba, ta ina ma zata fara, da hannu daya in ya riketa ko kwakkwaran motsi bazata iya ba balle ta kwace kanta, Knocking kofar da ta jiyo a kunnenta ne yasa ta zaro ido bakinta na rawa tace "Wallahi Housemate dita ce ta dawo kuma bata da makulli nata ya ɓata..." Yace "And so what? Ita zata hanani abinda nayi niyya ne?" Hawaye na sauka idonta tace "Don Allah ka bar ni in bude mata kilan mantuwa tayi, she is not spending the night here" Saketa yayi fuskarsa babu yabo babu fallasa yace "Remain here, i will open the door for her" Gyada masa kai kawai take zuciyarta na bugawa da karfi, ya dau rigarsa ya saka sannan ya nufi kofa ya fita, a hankali Khaleesat ta sulale kasa tana jin kamar numfashinta zai dauke tsabar tashin hankali, gashi sai knocking kofar parlon ake babu kakkautawa, da sauri ta mike jikinta na rawa ta bi bayansa tana shesshekar kuka at the same time tana tunanin to wa ke kwankwasa kofar Allah Ubangiji ya sa Housemate dinta ne, nan corridor ta makale don tuni har Abdul ya isa kofar parlon zai bude, ya murda makullin ya bude kofar, Khaleesat couldn't believe who she saw standing at the doorstep, ai bata san sanda ta karaso parlon da sauri ba hawaye na sauka idonta, Abdul dake kallonsa daga sama har kasa Calmy yace "How may we help you? Who are you looking for?" Maimakon wanda ke bakin kofar ya basa amsa kawai ya bi gefensa ya shigo parlon yana kallonta yace "Why did you call my line?" Da mamaki Abdul ya juya ya kalli Khaleesat da ta sunkuyar da kanta hawaye na sauka idonta ta lumshe ido, bata san sanda wani relieve ya zo mata ba lokaci daya, ta sake jin muryarsa yace "Me yasa kika kirani?" Ta daga kai ta kalli Abdul ganin irin kallon da yake mata at the same time ya nufo inda take cikin zafin nama, ganin haka ta fara komawa baya cikin rawar murya tana kallon AJ tace "I need you to help me pls" Ko rufe baki bata yi ba taji Abdul ya sauke mata wani wawan mari a kuncinta, AJ could not believe what he just saw cause bude baki yayi at first, ganin ya kara sauke mata wani marin cikin few seconds AJ ya isa gaban Abdul sending him double fist a fuska, he took Abdul unaware don bai gama recover daga fist din ba ya kara masa wasu ukun a jere, kan kace me ya fara punching dinsa kamar an aikosa, Rikicewa Khaleesat tayi da karfi tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, na shiga uku plss stop it" Tana matsowa kusa da su zata rike AJ da ya wani hankadata sai da ta fada kan kujera, Dai dai sanda aka bude kofar parlon Jay ya shigo, buda baki yayi ya jefar da wayar hannunsa saman kujera ganin Abdul a hannun AJ kamar ya samu punching bag, AJ gave Abdul no single space to retaliate, dukansa kawai yake kamar suna gidan dambe, Jay ya nufesu da sauri yana kiran AJ, da kyar ya samu nasaran rabasu yana ma AJ tsawa yace "Are you out of your mind Junaid? Are you mad, Meye haka?" Jay bai rufe baki ba Abdul ya koma kansa da fist din da bai samu yi ma AJ ba, ai ko ya kara ja ma kansa wani dukan wajen AJ, Jay that was shock at the attack Abdul just attacked him ya bude baki yana kallonsu, kar AJ yaje ya ma Abdul illa su shiga uku ya sa Jay ya kara rike AJ, Abdul that was beaten blue black ya nufi kitchen kamar mahaukaci vowing to unalive AJ, Khaleesat tsabar shock ko motsin kirki bata yi a inda AJ ya wurgar da ita, Jay na ganin Abdul ya shiga kitchen yasan makami kawai yaje daukowa, ya kalli Khaleesat da sauri yace "Tashi ki tafi daki" Ai kamar jira take ko rufe baki Jay bai yi ba ta mike a guje tayi Corridor ta tsaya tana zare ido, Jay ya fara jan AJ su tafi daki amma AJ yaki yana cewa "Don babansa me yake takama da shi a Nigeria? Who the F is he? Kakkaryasa zanyi in karya banza wallahi, in ya cika shege mu hadu a Nigeria" Jay yaki biye AJ haka dai ya ja sa har corridor zai shigar da shi daki, sai ga Abdul da wuka ya nufo su kamar Ɗan daba, ai ko karasa shigewa dakin basu yi ba Khaleesat ta riga su, tuni Jay ya sa ma dakin Key ya zare makullin ya saka a aljihu don tsaf yasan AJ sai yace zai bude kofar ga makami hannun Abdul, Abdul ya dinga bubbuga kofar saying all sort of abusive words at the same time yana alkawarin sai ya ma AJ illa, AJ ya tafi jikin window ya tsaya yayi crossing kafa yana kallon kofar dakin, Jay dai ya zauna gefen gado looking speechless and confuse, sai kuma ya dafe kirjinsa da ya fara masa ciwo saboda fist din Abdul, ita dai Khaleesat na rakube jikin gado hawaye na sauka idonta tana kuka a hankali, banda bugawa da karfi babu abinda zuciyarta ke yi, taji muryar Abdul na cewa "Ke kuma sai na maki abinda har ki koma ga mahaliccinki baza ki mance ba, i will make sure you become useless and miserable, i promise you this, kasar nan kuma kamar kin bar sa don karatun ki ya zo karshe" Khaleesat ta kara sautin kukanta, Ajay ya daka mata tsawa yace "I will fling you out of this room in baki rufe ma mutane baki a nan ba" Jay ya wani kallesa, ita dai Khaleesat ko kallonsa bata yi ba kukanta kawai take, after a while ko ina yayi tsit a gidan ko tafiya Abdul din yayi oho, da kyar Khaleesat ta mike bayan kusan minti goma zata dau hijab dinta, Jay ya bi ta da kallo, bayan ta saka Hijab din ta juya suka hada ido, sauke idonta da ya kumbura don kuka tayi, sai kuma ta tafi ta dau karamin towel da ta gani gefen gado seeing traces of blood in Jay's lips, bandaki ta tafi ta jika towel din da ruwan dumi sannan ta dawo dakin without looking at him ta duka gabansa ta dafa gadon ta fara goge masa lip dinsa a hankali, AJ ya wani kallesu sai kuma ya tabe baki ya kauda kai yana kallon outside of the window, Jay dake kallonta yace "Thank you Halysaah" Ita dai bata ce komai ba kuma bata yarda ta hada ido da shi ba ta mike ta tafi bandaki da towel din, AJ ya juyo yace "Kai Malam bani makulli in bude kofar nan in fita" Mikewa Jay yayi ya nufi kofar ya fara budewa a hankali, AJ ya bi bayansa incase of necessity, yana bude kofar AJ ya rigasa fita at the same time being very conscious of everywhere in the house, both angle and corner, a haka ya fito parlon Jay ma that was at alert na biye da shi a baya amma fa sai da ya kulle kofar dakin da makulli sbda Khaleesat, and they realized Abdul ya fice daga gidan, AJ ya juya ya kalli Jay yace "Dau wayarka mu tafi gida" Jay yace "You think i can just go and leave her in here?" AJ ya masa wani kallo yace "How sure are you u are safe being in this apartment tonight? Mahaukaci ne fa gayen kuma zai iya dawowa at anytime, it's already dark now" Jay yace "Nasani, but bazan iya barin ta ita kadai gidan nan ba" AJ yace "Are you her family member or something?" Jay yace "Kai da ka taho nan family member dinka ce?" AJ yace "Look Jay, Billah bazan bari ka zauna a gidan nan ba, koma wani taimako zaka mata kayi mata ni babu ruwana amma baza ka zauna a gidan nan ba, i can't risk leaving you here even for 1 second" Jay that was quiet for a while yace "Toh ka tafi, zan biyoka a baya" AJ yace "Kafata kafar ka Malam, kaji nayi rantsuwa bazan bar ka gidan nan ba, dubi kullin da ya dinga maka babu abinda ka tabuka sai sake baki kayi kana kallonsa" A hankali Jay yace "So kake mu hade masa at the end mu zo mu yi abinda za ayi da an sani, ai gwara da na kyalesa kawai kai ba gashi ka basa kashi yanda ya kamata ba, beside in muka ce zamu dokesa tare hakan zai sa mu gigita yarinyar ne" AJ yace "Aa haukatar da ita za mu yi ba gigita ta ba, pls do what ever you want to do ka fito mu tafi gida, ni yunwa ma nake ji" Jay ya sauke boyayyen ajiyar zuciya yace "Wait for me outside then" Yana fadin haka ya juya ya koma dakinsa da Khaleesat take, AJ kuma ya fice daga parlon ya tsaya nan bakin kofa yana jiransa, bayan Jay ya bude dakin da makulli sai da yayi knocking sannan ya shiga ciki, tsaye ya ganta jikin bangon dakin hawaye na sauka idonta tana shessheka, ya tafi can jikin window ya tsaya yana kallonta, ita dai ta sunkuyar da kanta tana kuka a hankali, Calmly yace "Halysaah" Ta kasa daga kai ta kallesa, yace "Tell me how did you get to know this guy? A ina ku ka hadu? For how long ku ke tare da shi, kuma who is he? Iyayenki sun san da alakar ku?" Sai a sannan ta daga kai wasu hawayen na sauka idonta tana kallonsa, ya sauke ajiyar zuciya yana shafa kansa yace "Where are ur reading material? Suna dakin ki ne?" Kai ta gyada masa kawai, yace "Mu je ki dauka" A tare suka tafi dakinta, bayan yaga inda reading materials din nata suke ya karasa ya dauka har da laptop dinta, ya kalleta yace "Ina wayarki fa?" A hankali tace "Ya fada ruwa" Shiru yayi sai kuma yace "To mu je" Ta ɗan yi jim tana kallonsa, yace "Mu je mana" ba musu ta nufi kofa ya bi bayanta bayan sun fita ya kullo kofar, ita dai duk a tsorace take sai zare ido take tana ganin kamar Abdul zai sake dawowa gidan at anytime, ganin a tsorace take Jay ya shiga gaba yace "Follow me" Bin bayansa ta dinga yi hawaye na sauka idonta har suka fita daga parlon, har sannan Ajay na tsaye waje, ya juya ya kallesu, Jay ya nufi motarsa ganin Khaleesat ta tsaya yace "Mu je mana Halysaah" tana tafiya a hankali ta ci gaba da bin sa, back seat ya bude ya ajiye laptop dinta da sauran reading material dinta ya kulle sannan ya bude mata front seat, ta sauke idonta ta shiga motar ya kulle, yana kallon direction din AJ yaga har ya nufi gun motarsa ya shiga, zagawa yayi ya shiga driver seat ya tada motar, tuni AJ yayi zoom off, Jay ya bi bayansa. A hankali Khaleesat ta sauko daga motar tana kallon Jay da shi ma ya sauka ya bude back seat ya dauko laptop dinta da takardu ya kulle motar yace "Mu je" Sauke idonta tayi ta fara bin sa a baya walking slowly har suka shiga parlon gidan, ya nuna mata kujera yana kallonta, ta sunkuyar da kai sannan ta zauna, ya ajiye laptop da takardunta dake hannunsa sannan ya wuce sama, ta bi sa da kallo hawaye na taruwa idonta, sai kuma ta fara kuka a hankali tana jin kanta na sara mata, Jay ya tafi dakin AJ yana bude kofar dakin yaji yana wanka a bandaki, hakan yasa ya tsaya bakin kofar dakin don baya son issue, yana ta tsaye da tunani iri iri a ransa har AJ ya fito bandakin, AJ na ganinsa ya dakata da goge gashin kansa da karamin towel yace "Me kake nema a nan kuma?" Jay yace "Ban sani ba" Sai kuma ya karasa cikin dakin that was extra clean, kan kujera ya zauna without looking at AJ yace "We need to talk AJ" Ajay yace "Shi ne sai ka shigo min daki?" Jay yace "Zauna mu yi magana" Ɗan tsaki AJ ya ja yana ci gaba da goge gashinsa yace "Ina jin ka ba sai na zauna ba" Jay yace "I think my Housemate will stay here for a day or 2, before she sort her self out" AJ yace "As per you are her family member or who? Bata da iyaye ne? Ko nan din hotel ne?" Jay yace "Ban sani ba" AJ yace "No i am just asking a harmless question, like naga dai ba daga sama ta fado ba, kuma ba kai ka kawota America ba balle kace zaka samar mata solution, who are you to her? Yayanta ko Ubanta? Wanda muka mata ma Allah ya bamu lada, come off it Jawwad" Jay yace "Ai ba permission din ka na shigo nema ba Junaid, kawai sanar maka nake yarinyar nan zata yi kwana daya zuwa biyu a gidan nan kafin komai yayi settle" AJ yace "Toh ni na haifeka da zaka shigo ka gaya min zaka kawo yarinya tayi kwana biyu gidan nan? Ai sai dai ka kira su Abba ka gaya masu, beside the house is very big with multiple rooms to accommodate her, so ni ina ruwana, i just pray u don't have to explain ur self one day" Jay ya mike ya fice daga dakin banging the door behind him, AJ ya tabe baki yana feshe jikinsa da turaren jiki. Bangaren masu aikin gidan Jay ya nufa bayan ya sauko downstairs, ya basu umarnin da zai basu sannan ya dawo babban parlon gidan, Khaleesat dai na zaune ta jinginar da kanta jikin kujera tayi nisa tunanin da ta fada, ganin komai take kamar a mafarki, sai in taji tana da ta sanin abinda ya faru amma da ta tuna raping dinta Abdul yayi niyyar yi da Ajay bai zo ba sai taji ta nemi da ta sanin ta rasa, amma fa bata da nutsuwa bata da kwanciyar hankali, she was just restless and sick, bata san kuma me zai faru next ba a rayuwarta, muryar Jay ne ya dawo da ita daga tunanin da take ta gyara zama tana kallonsa a sanyaye, ya zauna kujeran dake kallon wanda take zaune yace "Bana son ki sa ma kanki damuwa Halysaah, ki kwantar da hankalinki pls kin ga kina da jarabawa a gabanki" Khaleesat ta sunkuyar da kanta hawaye ya fara sauka idonta, Yace "Kin yi sallah?" Ta gyada masa kai, yace "Ohk za a kawo maki abinci sai ki ci kafin mu yi magana" Ta girgiza masa kai tace "Bana jin yunwa" Yace "No, sai kin ci abinci ko ba yawa" Dai dai nan kukun gidan wanda bature ne ya taho da abinci zai kai dinning Area, Jay ya masa umarnin ya kawo parlon sanin abincin AJ na kan dinning din, dawowa kukun yayi Jay ya nuna masa inda zai ajiye abincin, nan ya jerasu a kasan lallausan Centre carpet, ya koma ya dauko sauran, bayan ya ajiye komai ya tafi Jay ya mike yana kallonta yace "Ki sauko ki ci abinci, let me pray" Ta gyada masa kai kawai, ya wuce sama sannan ta sauko kasa a hankali tana duba abincin da aka kawo mata taga duk abincin jajaye ne gashi abincinsu da yawa ita ba iya ci tayi ba duk shekarun da tayi a kasar su. Almost 30 mins after Khaleesat dake ta zaune tana tunane tunane ko abincin ta kasa ci ta daga kai taga Ajay ne ya shigo parlon, sunkuyar da kanta tayi, bai kalli inda take ba yayi wucewarsa dinning Area ya fara cin abincinsa, after a while Khaleesat ta daga kai a hankali jin footstep, taga Housemate dinta ne ke saukowa downstairs, ya karaso har inda take ya zauna kan kujera yace "Kin ci abincin?" Ta gyada masa kai, cook din gidan ya kira ya dauke sauran abincin ya tafi da su, Jay yace "To ki koma kan kujera" Ita dai Khaleesat kanta na kasa bata ce komai ba, har sai da Jay ya sake mata magana sannan ta mike ta koma kan kujeran ta zauna, AJ ya dawo cikin parlon ya tafi reading nook dake parlon, Jay ya bi sa da wani kallo har ya gama kakkabe kakkabensa ya zauna, ko uban me zai yi a can don yasan dai baya ma zuwa nan balle yayi karatun a nan, muryar Jay ya dawo da hankalin Khaleesat jikinta, taji yace "So Halysaah i want to even know what happen first of all at ur apartment today, don ni ban san me ya faru ba, Salem called me yace kin kirani ban daga ba and you sound disturb, and he gave you AJ's number, i rang you back quickly sai kiran bai shiga ba, shine nayi deciding in je can gidan kawai, menene ya faru?" Khaleesat ta sunkuyar da kai don bata ma san me zata ce masa ba, ta yaya ma zata fara cewa raping dinta Abdul ya so yi, muryar AJ suka ji a parlon yace "Allah ma yasa ba rashin kunyan da ta saba yi ma mutane taje tayi masa ba, kawai ta sa na doki bawan Allah a banza" Khaleesat dai bata dago kanta ba, shi dai Jay yayi murmushin da bai yi niyya ba yana kallon direction din da AJ yake, A hankali Jay yace "You are not saying anything Khaleesat" Hawaye ne ya cika idonta, ganin haka Jay yace "Or you don't want to talk about it?" Ta girgiza masa kai hawaye na sauka idonta da kyar tace "Ba haka bane, he tried molesting me" AJ that heard what she said duk da ba kallon direction dinta yake ba yace "He tried molesting you, amma da hannunki ai kika bude masa kofar ba ta window ya shigo ba" Jay ya wani kallesa yace "Stop this please AJ, why are you so wicked and heartless" AJ yayi wata dariyar bosawa, Jay ya dinga hararansa, ita dai Khaleesat hawaye ne kawai ke zuba idonta, tsabar ciwon da kanta ke mata har wani dishi dishi take gani, Cikin kwantar da murya Jay dake kallonta yace "Tell me who he is, and where did you know him from" Ta gyada masa kai tana share hawayen da yaki tsaya mata a hankali tace "Shekara hudu kenan na san shi....." *Don't even know where to start from, the patronage was massive🥺, thank you soo much for encouraging me fans, Allah ya biya maku bukatunku na alkhairi, Allah ya raya zuri'a, i soo much appreciate ur patronage, marasu auren cikin ku Allah ya baku mazaje na gari, masu aure kuma Allah ya ci gaba da baku zaman lafiya a gidajenku, Allah ya karo maku budi ninkin ba ninki, ya raba ku da iyayenku lafiya* 🥺 _Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta i owe you 500_ [5/19, 5:53 PM] khaleesat Haiydar ✍️: Khaleesat ta sunkuyar da kanta har sannan bata daina goge hawayen da ya ki tsaya mata ba, she look pained and traumatized, Shi dai Jay kallonta kawai yake waiting for her to continue with what she is saying, jin tayi shiru yace "Halysaah" Ta daga idanuwanta ta kallesa, Calmly yace "I am listening" muryarta na rawa tace "Kawai dai shi ne ke sponsoring dina" Ba Jay da ya kafeta da ido ba yana mata kallon mamaki, har AJ sai da ya juya ya kalleta daga inda yake zaune jin abinda tace, Jay was just speechlessly staring at her, can dai ya gyara zama yace "You mean shi yake sponsoring dinki a kasar nan? Are you related in anyway with him?" Ta girgiza masa kai kawai, da mamaki kawai yake kallonta, after few seconds yace "And ur parent allowed him to sponsor you har zuwa nan America?" Ta gyada masa kai without looking at him, mikewa AJ yayi, yayi wucewarsa sama, Jay ya bi sa da kallo don shi ma ya rasa abun cewa don mamaki, Jay ya maida dubansa kan Khaleesat a hankali yace "Ya kai kudin aurenki ne an sa maku rana?" Ta daga idanuwanta ta kallesa cikin sanyin murya tace "Nima ban sani ba, amma kamar ya kai" Jay yayi shiru for almost 3 minutes with different thoughts running his mind, everything just took him unaware, bai taɓa tunanin saurayin nata ne sponsor dinta all this while ba, can ya daga kai ya kalleta yaga ta jinginar da kanta jikin kujera looking so tired and pale, yana son sanin me ya hadata da Abdul, meye ma dalilin haduwarsu, sannan a ina ma suka hadu da shi din, what is this great thing that motivated her parent har suka amince ma stranger da basu hada komai da shi ba ya turo er su har wata kasa karatu, he just don't want to believe it's because of money they did this.... amma ganin yanayinta yasa yayi keeping all the questions to himself for now don baya son ya kara stressing dinta, she is already stressed, mikewa yayi calmly yace "I will be back now" Ita dai ta bi sa da kallo har ya haura sama, wasu hawaye taji na taruwa idonta, kawai so take tayi kuka me sauti ko zata ji saukin abinda take ji a ranta, ta hade kanta da kujera tana shessheka a hankali, Jay na haurawa sama ya tafi dakin da ya sa daya daga worker din gidan ya kara gyarawa, the room was big sai dai bai kai nasa da na AJ ba, kuma babu abinda babu a dakin sai Duvet na saman bed spread, ya bude press din dakin yaga babu a nan ma, juyawa yayi ya fita ya dau hanyar dakin AJ, yana isa ya danna code din bude kofar dakin ya murda yaga bai buduwa, yasan canzawa yayi kenan saboda ya shigo masa dakin daxu, knocking din kofar yayi, after a while AJ ya bude kofar yana kallonsa alamar what happen, Jay ya turasa gefe ya shiga cikin dakin, AJ ya bi sa da kallo yace "Ka dai san bana son haka Jawwad, what are you looking for?" Jay ya kunna wutan dakin that is more brighter yace "Duvet zaka bani, i don't understand dalilin da yasa zaka kwashe kaf duvet din sauran rooms din all to ur self, this is greed" AJ dai kallonsa kawai yake cause he is already angry shigo masa da Jay yayi daki, ganin Jay ya nufi inda duvet dinsa suke yace "Jay me zaka yi da duvet bayan kana da naka a daki?" A takaice Jay yace "I am giving my visitor" AJ ya bude baki yana kallonsa yace "What??? I don't understand, Duvet dina zaka dauka ka kai ma visitor dinka? are you even okay? Can you hear ur self pls?" Jay bai tanka sa ba ya dau na saman gadonsa kawai ya nufi kofa, AJ ya tare kofar on a serious note yace "In ka fita da duvet din nan ka canza min suna yau" Jay ya wani turasa daga bakin kofar har sai da ya kusa faduwa sannan ya fice daga dakin, sai bayan da ya fita ya juya ya kalli AJ da ya bude baki yana kallonsa with shock, Jay yace "Emmanuel" daga haka yayi wucewarsa ya bar AJ da bin sa da kallo, Jay na komawa ya ajiye duvet din kan gadon dakin da aka gyara ma Khaleesat sannan ya sauka downstairs, tana nan zaune yanda ya bar ta idonta a lumshe amma ba bacci take ba, yace "Halysaah" Bude ido tayi da sauri bayan ta dawo duniyar tunanin da ta tafi, yace "Tashi mu je sama, u need rest" Ita dai tayi shiru bata ce komai ba, ya dau laptop dinta da takardunta yace "Mu je" Sai bayan da ya fara tafiya sannan ta mike a hankali ta bi bayansa, har wani jiri take ji amma a haka ta daure ta bi sa har zuwa sama, ya bude kofar dakin ya shiga tana biye da shi, bayan ya ajiye laptop din hannunsa ya kunna mata na'uran da zai dumama dakin, ya nuna mata hanyar bandaki ita dai kai kawai ta gyada masa, ya ciro wayarsa a aljihu yayi dialing number sannan ya mika mata yace "In case u need anything sai ki kira number da nayi dialing it's my other line" Nan ma dai kai kawai ta iya gyada masa, yace "Good night Halysaah, pls kiyi bacci sosai, do not bother ur self kin ji?" a hankali tace "Toh" kofa ya nufa ta bi sa da kallo sai da ya bude kofar a hankali tace "Nagode" Ya juya ya sakar mata murmushi yace "I gat ur back" Daga haka ya fita ya kullo mata kofar dakin, Khaleesat ta ajiye wayar tasa da ya bata sannan ta zauna gefen gadon dakin a hankali staring at the window absently. Har karfe dayan dare Khaleesat bata ji ko digon bacci ya zo mata ba, tana dai kwance tayi lamo cikin duvet, her heart is soo heavy, har wani zafi take jin yake mata, ga wani zazzabin da taji ya lullubeta, tun da Jay ya bar ta take kuka, gani take kamar duniyar ya tsaya mata ne cak, ta ma rasa wani kalan tunani zata yi, abubuwan da suka faru daxu suka dinga dawo mata abun sai yake mata kamar mafarki, she wish mafarkin ne ma kawai, yanzu babban tashin hankalinta bata san me zai faru a Nigeria ba, bata san next step din Abdul ba, bata san me zai ma iyayenta ba, duk wannan tunanin ya hadu yayi distabilizing dinta, zazzabin da take ji ya karu sosai, tana son tashi taje tayi alwala tayi sallah ko zata samu sukuni amma ta kasa, duk jikinta ciwo yake mata ga ciwon kai kamar kanta zai fashe, da taji azaban yayi mata yawa kamar zata kira Housemate dinta ta tambayesa maganin ciwon kai amma ta fasa don bata san ko bacci yake ba, haka tayi ta juye juye jikinta yayi zafi sosai, yanda taga rana haka taga daren nan that was soo long to her, bacci ko na barawo bai dauketa ba, jin vibration din da wayarsa yayi yasa tayi karfin halin jawowa tana kallon screen taga alarm ne na karfe biyar, ta kashe alarm din tana son tashi don tayi sallah amma ta kasa, daga karshe dai haka tayi karfin hali ta daure ta tafi bandaki ta dauro alwalan, tana idar da sallan taji zazzabin da yafi na baya ya lullubeta gaba daya, kwanciya tayi saman gado ta rufe har kanta da duvet din. Wajen karfe takwas na safe Jay yayi knocking kofar dakinta, tana ji amma ta kasa amsawa, sau uku yana knocking jin bata amsa ba sai ya kira wayarsa dake wajenta nan ma tana kallon kiran amma ta kasa daga hannu ma ta dau wayar, sai da ya katse sannan ya bude kofar dakin da sallama ya shiga, yana kallonta da mamaki ya nufeta yace "Are you Okay Halysaah?" Kai kawai ta girgiza masa, ya duka kusa da ita yace "Baki da lafiya ne? Why didn't you call my line?" Hawaye ya gani idonta, yace "Haba Halysaah, ba nace kar ki sa ma kanki damuwa ba? Did you want to hurt ur self?" Ita dai bata ce komai ba, ya juya ya fita daga dakin, after some minutes ya dawo da Hot chocolate ya ajiye mata yace "Ki daure ki sha pls, let me get you medicine" Yana fadin haka ya juya ya fita daga dakin, ko da ya dawo ya ga bata tashi ba still, duk yanda yayi da ita ta tashi ta sha shayin ya bata magani taki tashi, gaba daya ya ma rasa yanda zai yi da ita, can ya kara dukawa kusa da ita yace "Did you have ur frnd safiyyah's number offhand?" Da kyar ta girgiza masa kai, yace "U have her IG handle? Is she active on IG?" Bata ce masa komai ba don ta ma kasa maganan, he look confuse at this point, can dai yace "To zaki iya daurewa ki tashi mu tafi asibiti?" Ta girgiza masa kai, mikewa yayi kawai ya fita daga dakin, downstairs ya sauka don AJ na dinning yana breakfast ga Legend dinsa zaune ɗan nesa da shi a dinning area din, Jay ya nufesa looking confuse yace "AJ, the girl is seriously sick fa" AJ dake sipping tea dinsa yace "Which girl?" Jay ya masa wani kallo yace "Please be serious AJ, wallahi bata da lafiya sosai" AJ yace "To yanzu daukar ta zaka yi ka kai ta Hospital kenan..." Jay yace "How?? ko tashi fa bata iya yi, plss ko zaka mata allura ta ɗan samu relieve tukun?" A hankali AJ ya ajiye Mug din hannunsa yana kallon Jay baya ko kiftawa, can ya matsar da shayin gabansa yace "Amma dai don Allah me yasa ka raina ni haka ne Jay? Me nayi maka? Kai me hannunka yake da bazaka mata allura ba sai ni?" On a serious note Ajay ke masa tambayoyin nan looking at him and waiting for his answer, Jay yace "Da gaske fa you are Heartless Junaid, ince maka yarinya ko tashi bata iya yi? Why are you like this pls?" AJ yace "But like seriously kai uban me hannunka yake da bazaka mata allura ba sai ni? Baka fi ni zama likita ba? Wato ni ne ɗan iska ko?" Juyawa Jay yayi ya bar wajen ya koma sama, yana bude kofar dakin ya ganta duke kusa da kofar bandaki, ya karasa kusa da ita da sauri ganin yanda ta galabaita yace "Did you throw up?" Kai kawai ta gyada masa tana maida numfashi, gun da ya ajiye hot chocolate din ya tafi ya dauko mata yace "Pls ki sha ko kadan ne sai in baki magani" Ta girgiza masa kai, yace "C'mon Halysaah, kadan fa za ki sha" Yana rike da cup din don kar ya sakar mata ta zubar, a haka ta kurbi shayin kadan, sai da yasa ta kara sha sannan ya ajiye shayin ya dauko magani, tana ganin maganin ta fara girgiza masa kai da sauri don har taji wani aman zai taho mata, bude kofar dakin aka yi Jay ya juya, AJ ya gani tsaye bakin kofar yana kallonsu, Jay bai sake kallon inda yake ba ya maida dubansa kan Khaleesat yace "Pls ki daure ki sha Halysaah, ko baki son ki samu relieve?" Kara girgiza masa kai tayi hawaye ya fara sauka idonta, lallabata Jay ya fara yi akan ta sha maganin, AJ ya wani hade rai yace "Kee baza ki amshi maganin da ake baki ba? Wa zaki ba wahala?" Jay yace "Ba ruwanka pls AJ, get out" Ita dai Khaleesat ko kallonsa bata yi ba tana fama da kanta, Jay bai sake takurata kan ta sha maganin ba ya mike yace "Toh ki daure ki hau kan gado ki kwanta, i am coming now" Ta gyada masa kai, ya juya ya nufi kofa, ko kallon Ajay bai yi ba ya fita daga dakin, AJ ya tabe baki ya juya ya koma downstairs. Haka nan Jay ya hado alluran da za mata don saukar mata da zazzabin, sai da ta ga ya dawo dakin sannan ta daure ta koma saman gadon tana ganin jiri ta kwanta, ya tsaya gefen gadon yana rike da alluran yana kallonta, ta marairaice ta girgiza masa kai kawai alamar bata so, ya kwantar da murya yace "To ya kike son in maki Halysaah? Kin ki shan magani" wayarsa dake aljihunsa ya ciro jin yana ringing ganin Salem ke kiransa ya ajiye alluran hannunsa yace "I am coming Halysaah" Fita yayi daga dakin, ya sauka downstairs ya tarar da Salem zaune parlor, bayan sun gaisa Salem yace "Slide dina nake son zaka duba min Jay" Shi dai AJ na zaune yana kallon kwallo ga Legend a gefensa, Jay yace "Ohk, but tunda ka zo pls zaka yi injecting Housemate dita she is sick" Salem yace "Ayya, shi sa ta kira jiya, Allah ya bata lafiya, tana can gidan nata ne?" Jay yace "No, she is upstairs, mu je in nuna maka dakin da take" A tare suka wuce sama, AJ dai kallonsa kawai yake a TV kamar bai san suna parlon ba, Jay bai shiga dakin ba bayan ya nuna ma Salem ya dawo downstairs ya zauna, Khaleesat bata yi ma Salem wani musu ba don ba ma ta da wannan strength din duk da yanda bata son allura haka nan ta bari ya mata, tsabar zazzabin dake jikinta ko zafin shigar alluran bata wani ji ba, Salem yayi mata Allah ya sauwake sannan ya fita daga dakin ya koma downstairs, Jay yace "Thank you, bari in duba maka" Sai bayan kusan minti talatin Jay ya tafi dakin Khaleesat ya sameta tayi bacci, ya sauke ajiyar zuciya ya karasa kusa da gadon ya kai hannu kusa da goshinta sai dai bai taɓa ta ba, nan yaji temperature dinta ya fara sauka, juyawa yayi ya dau sauran shayin da ta bari ya fita daga dakin..... Wajen karfe sha daya da rabi Khaleesat na kwance hannunta rike da wayar Housemate dinta, tun 20 min ago ta tashi daga baccin da ya dauketa daxu, she felt a bit relieved now da alluran da Salem yayi mata, sai dai har sannan kanta bai daina mata ciwo ba kamar ta cire ta huta, tayi kokarin ta tashi ma ta tafi bandaki amma ta kasa, she is so weak kamar warce ta dade tana ciwo, hakan yasa kawai ta jawo wayar Jay, da har zata shiga gallery dinsa to while away time amma sai taga it's not proper ta shiga hotunansa, hakan yasa ta shiga wani game da ta gani kawai tana yi daga kwancen da take, bude kofar dakin aka yi ta daga idonta, Jay ne ya shigo dakin AJ dake bayansa yaki karasowa ciki ya tsaya daga bakin kofar, Jay ya nufota yace "Ashe kin tashi, how are you feeling now Halysaah?" Ta gyada masa kai a hankali tace "Good morning" Yace "Morning Housemate, are you feeling much better now?" Kai kawai ta gyada masa, yace "Ohk bari a kawo maki breakfast, idan kinyi sai ki daure ki sha magani kin ji" Ita dai bata ce masa komai ba ya juya ya nufi kofa ya fita ya mika ma AJ wayarsa sannan ya sauka downstairs zai kawo mata breakfast, shi dai AJ daga sama har kasa yake kallonta, ta ɗan saci kallonsa to see if he is still standing by the door ko ya tafi, hada ido suka yi ta dauke idonta tana ci gaba da game dinta da take, after a while ta kara satan kallon bakin kofar taga ya bar wajen, sai ga Jay ya shigo ya ajiye mata tray din breakfast ta dinga kallon plate din baked beans irin na turawa a gefe da soyayyen kwai a gefe, with veggies, sai sausages, ga cup din hot chocolate with few slices of bread a gefe su ma, ita dai tasan ba iya cin wannan abincin zata yi ba, yana kallonta yace "Can you give me ur frnd Safiyyah's Home address?" Ta sauke idonta ta gaya masa address din, yace "Ohk, na ma san area din, i have a frnd there" Ita dai tayi shiru, ya dauko mata maganin da taki sha daxu ya ajiye kusa da ita yace "Pls ki daure kiyi breakfast din, sai ki sha drug din kafin in dawo" A hankali tace "Toh nagode" ya mata murmushi ya juya ya fita daga dakin ta bi sa da kallo. Jay ya tarar da AJ zaune a waje gurin shan iska dake compound din yanna danna wayarsa, hakan yasa ya nufesa ya zauna kujeran dake facing dinsa yace "AJ, i think i am confuse at this point, what do u suggest about this young girl's issue?" AJ ya daga ido ya kalli Jay yace "My suggestion is that... ka barta ta tafi duk inda ma zata ka cire hannunka da bakinka cikin wannan case din babu abinda ya shafe ka, a cikin kunnenka kaji tace shi gayen ne ke sponsoring dinta, babu kuma ta yanda zai yi sponsoring dinta without the consent of her parent, kaga they are comfortable with that, so who are you to intrude Jawwad? Baka san komai akan ta ko kan saurayin ba don me zaka zakalkale haka? Tare fa ka gansu, da can baya zuwa America din ya sameta ne a gidan? sai yanzu tasan yana molesting dinta? Girl's can be very cunning fiye da tunaninka, don't start what u can't finish Jawwad" Jay dake ta kallonsa yace "So now what are you insinuating?" AJ yace "Since you are daft kar Allah ya sa ka gane abinda nake insinuating" Jay dai kallonsa kawai yake, after a while a hankali yace "But duba da abinda ya faru tsakaninka da guy din kasan zai iya hurting dinta idan nace ta koma gidan nan AJ, she is no longer safe in that apartment, ka dai ga ba ma cikakken hankali ke gare gayen ba, ka duba fa wuka yaje ya dauko a kitchen" AJ ya gyara zama yace "Sai kayi mata hanyar komawa gun iyayenta as the good Samaritan that you are from Samaria, kaga in ta koma sai ta gaya ma iyayen nata abinda ke faruwa da abinda selfishness dinsu ya ja mata a kasar mutane, sai su yi sorting kansu a can kawai" Jay yace "Kar kace haka, we know nothing about why they allowed him to sponsor their daughter, we shouldn't judge them har sai mun san dalilinsu AJ" AJ yace "Dalilin banza, babu responsible parent din da za su damka ma kato irin wannan mutumin er su ya kai ta wata kasa da sunan karatu, it doesn't even make sense, sai kace ba musulmai ba, ko da cousin brother dinta ne ma abun bai yi tsari ba balle babu ko wani relationship na jini tsakaninsu, who does that" Jay ya sauke ajiyar zuciya yace "Duk da haka dai ni bazan yi judging dinsu ba tare da nasan komai ba, let give them benefit of doubt" AJ yace "Sai kayi ta basu ai, ni kam bazan bayar ba" Jay yace "But komawarta Nigeria yanzu bazai yiwu ba AJ, ba shine solution ba, Monday za su fara exams, John Hopkins university take ita ma fa" AJ yayi dariya har da kyakyatawa yace "Tabb, lallai gayen ya kashe kudi ba na wasa ba" Jay dai kallonsa kawai yake, AJ yace "Toh za a fara exams me kake nufi kenan? Naji ka ce apartment din nata is not safe for her anymore..." Jay yace "She will remain here har su gama exam kafin ta koma Nigeria wajen iyayenta" AJ ya wani kallesa da sauri yace "What do you mean? Kana nufin mu zauna gida daya da balagaggiyar yarinya da ba muharramar mu ba kamar wasu jahilai marasu tsoron Allah? Kai da wa za ku yi wannan nonsense din??" Jay yace "Duk yan iskan turawan da kake kawowa gidan nan ka basu daki su zauna dama muharramanka ne ban sani ba?" AJ yace "Turawa kace ai, kuma babu komai tsakanina da su kai ma ka sani, i am only helping most of them tunda ba a garin nan suke ba" Jay ya mike yace "Ita ma haka za mu yi helping dinta tunda ba a garin take ba, take it or leave it" yana kai wa nan yayi wucewarsa inda yayi parking motarsa, Ajay ya bi sa da wani kallo, can yace "Sai dai ku je can ku biya wani apartment din ku zauna tare, babu wanda zai takurani a gidan nan wallahi, dama ai kun saba zama gida daya tare, it's not a new thing, dole ne sae ta zauna gidan nan cikinmu mu ba maguzawa ba" Shi dai Jay ya shiga motarsa ya fita daga compound din ya kama hanyar gidansu Safiyyah.... *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* [5/20, 5:24 PM] khaleesat Haiydar ✍️: Jay na isa unguwan da gidansu Safiyyah yake sai ya mance apartment din da Khaleesat ta gaya masa, hakan yasa ya kira wayarsa dake wajenta, Khaleesat na zaune saman gado har sannan tana playing game da wayar, sosai gabanta ya fadi ta dinga kallon screen din wayar ganin image din hotonsa da number da yayi appearing, sai taga kamar shi din ne a gabanta take gani, sai da kiran ya katse ta zaro ido bayan tayi realizing bata yi picking ba har ya katse, bayan few seconds ya sake kira, dagawa tayi ta sa handsfree tayi shiru, yace "Halysaah" Tace "Na'am" Yace "I think i forgot the apartment u told me" Gaya masa ta sake yi yace "Thank you" Daga haka ya katse wayar ya ci gaba da driving dinsa, dai dai gaban apartment din yayi parking don motar Mustapha baya nan, yana tsaye bakin kofa yayi knocking gently, after a minute aka bude kofar parlon, komawa baya Safiyyah tayi tana kallonsa da mamaki daga sama har kasa, ya ɗan mata murmushi yace "Hi Safiyyah" Ta bude ido sosai tana leka motarsa da taga yayi parking thinking may be he is together with Khaleesat, ganin motar ba kowa ciki tace "Hi, good afternoon" Yace "How are you doing Safiyyah?" Lokaci daya tace "Ko dai Khaleesat bata da lafiya ne?" Da damuwa sosai tayi tambayar, Yace "Yeah bata da lafiya" Tace "Wallahi yanzu na gama shiryawa nake son in ci abinci inje gidan naga miss call dinta jiya ina ta kira har yau wayar baya shiga, and i am disturb" Yace "Shi yasa na zo in dauke ki idan ba damuwa so you can be together with her she is sick, probably idan kin mata magana zata ci abinci ta sha magani" Da sauri Safiyyah tace "Sure, bari in dauko gyalena" Juyawa tayi da sauri ta koma cikin gidan, shi kuma ya koma parking space, Surayya dake zaune a parlon ta kasa kunne duk tana jin conversation dinsu kafin Safiyyah ta shigo, Safiyyah ko kallon direction dinta bata yi ba ta tafi dakinta da sauri ta dauko jakarta da gyale sai wayarta sannan ta fice daga gidan, ganin Jay cikin motarsa yana jiranta ta bude gaban motar ta shiga tana cewa "Tun jiya ne bata da lafiyan? Kuma me yasa ta kashe wayarta?" Jay yace "Tace wayar ya fada ruwa ne" Safiyyah tace "Ohk" Sai da suka dau hanya sannan Jay yace "Amma tana can gidanmu fa, can za mu je yanzu" Safiyyah ta juya da sauri tana kallonsa da mamaki tace "Gidanku? Why? What happened?" Calmly yace "Before then za mu fara zuwa apartment dinmu sai ki dau mata kayanta da zata yi amfani da shi, we left yesterday with nothing" Safiyyah bata sake cewa komai ba tunani iri iri na yawo a ranta, to me ya faru? ta yaya Khaleesat da ta sani me shegen taurin kai ta yarda har ta bi sa can gidan nasu? Ko dai rashin lafiyar nata is critical ne haka? Da tunane tunanen nan suka isa apartment din, suka shiga ciki tare da Jay ta nufi dakin Khaleesat shi kuma ya zauna a parlor, bayan few minutes ta fito tace "Kala daya zan dau mata kayan ai ko?" Jay ya mike yace "No, 3 to 4 will be okay" Duk da confusion din da Safiyyah ta shiga bata dai ce masa komai ba ta juya ta koma cikin dakin, ta dau akwati ta saka ma Khaleesat kayanta da duk abinda zata bukata a ciki, tana fitowa daga dakin Jay ya mike yace "Kin dau mata duk abinda zata bukata?" Safiyyah ta gyada masa kai, suka fita daga parlon, duk ta kagu taje wajen Khaleesat ita dae, silently suka yi tafiyar har suka iso gidan, bayan Jay yayi parking ya sauka Safiyyah ma ta sauka, ya fiddo akwatin sannan suka nufi entrance din apartment din Safiyyah na biye da shi, bai ga motar AJ a gidan ba alamar ya fita, suna haurawa sama Jay ya tafi dakin da Khaleesat take yayi knocking, ya mika ma Safiyyah akwatin yace "Zaki iya shiga, zan je inyi sallah" Safiyyah ta amshi box din tace "Ohk" Bude kofar dakin tayi Khaleesat ta dinga kallonta har ta shigo, Safiyyah ta ajiye box din hannunta ta nufeta da sauri tace "Me ya sameki Khaleesat?" A hankali Khaleesat ta sauke idonta ta kasa cewa komai don bata ma san ta inda zata fara ba, sai ga hawaye. Safiyyah na tsaye dakin kusa da window bayan Khaleesat ta bata labarin duk abinda ya faru, tsabar yanda labarin ya kidima Safiyyah kasa ci gaba da zama tayi gefen gadon, Safiyyah tayi shiru for almost 2 minute tana tsaye jikin window tana girgiza kafa, ita dai Khaleesat goge hawayen dake sauka idonta kawai take, can Safiyyah ta sauke wani ajiyar zuciya me cike da takaici tace "A baya da nake gaya maki Abdul ɗan daba ne ba kin maida maganata abun wasa ba? Tunda uwata ta haifeni ban taɓa ganin ɗan iska kamar Abdul ba, yanzu da baki samu lambar kowa ba haka zai lalata maki rayuwa babu digon tsoron Allah a ransa? Ya kashe uban kudin zuwa USA kawai don ya zo yayi lalata? Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, amma naji haushi da ɗan uwan Housemate dinki bai sumar da shi ba an maida sa Airport a haka, tirr da Abdul, tirr da halinsa, i am so happy that things turn out this way, in sha Allahu karshensa ne ya zo a rayuwarki" Khaleesat ta fashe da kuka tace "Sophie ban san next action dinsa ba idan ya koma Nigeria, i am so restless" Safiyyah tace "Next action dinsa? Sai ya koma ya gaya masu uban da ya kawosa USA da Intention dinsa, ke in zaki dena wannan crocodile tears din naki ki dena don ba tausayinki zan ji ba, tunda dai bai samu nasaran lalata maki rayuwa ba ni duk abinda zai faru ma ya dade bai faru ba, kukan uban me kuma kike ma mutane? Ko nasaran da bai samu a kanki bane ya dame ki? Kuma wallahi ya ci sa'ar baki sameni a waya ba don kafin in karaso gidan sai 911 sun riga ni, tuni zan kirasu ince gashi can za ayi fyade, banda iskanci duk karuwansa basu ishesa ba sai ya zo ya kara dake? Gaskiya ki rike Housemate dinki da ɗan uwan nan nasa da kyau don mutane ne su wallahi, da ba don su ba da yanzu wani zancen ake ba wannan ba, don da na kai maki ruwan zafi yafi a kirga zuwa bandaki yanzu" Khaleesat dai bata sake ce mata komai ba tana share hawayen da yaki tsaya mata, Safiyyah ta rike haɓa har sannan tana mamakin Abdul, can tace "Kamar irin ya zo wajen matar nan tasa, ni wallahi da yaji suka barbada masa mu ga ta iskanci, shege kawai prostitute" Duk tashin hankalin da Khaleesat ke ciki sai da tayi dariya don ita bata taɓa jin inda aka ce ma namiji prostitute ba sai yau a bakin Sophie, Safiyyah tace "Ga dai katon daki an baki, kiyi karatun exams dinki cikin kwanciyar hankali, nima in abun duniya ya isheni in taho nan in sameki kafin dare yayi in koma den dina, don ko da wasa bazan ce ki dawo gidanmu ba ni kaina ban tsira gun tsinanniyar matar Yaya Musty ba kuma yaki kwatar min en ci, da zai bar ni ba nima sai in dawo nan kusa dake ba tunda ba rasa abincin da za su bamu mu ci za su yi ba, wannan dakin ai ya ishemu rayuwar America, bari kiji Khaleesat dama Allah ya riga ya rubuta Abdul ne silan zuwan ki Amurka ki hadu da mutanen arzikin ki, babu me canza haka ko yaki ko ya so dole sai ya kawoki ya hadaki da mutanen arzikin ki tunda Allah ya rubuta haka, iya role dinsa kenan a rayuwarki, kuma Allah ne zai basa ladan hakan bamu ba, ba shikenan ba?" Khaleesat dake ta kallonta ta girgiza mata kai tace "Ni bazan zauna gidan nan ba Sophie" Safiyyah na mata wani kallo tace "Ohk, Apartment din naki zaki koma ki kai ma Abdul din kanki kenan?" Khaleesat ta sauke idonta kasa muryarta na rawa tace "Bazan iya jarabawan ba Sophie, gwara kawai in koma gida, i want to go home, i want to go to my mother" Safiyyah zata yi magana aka yi knocking kofar dakin, Safiyyah ta amsa aka bude kofar Jay ya shigo, kallon Khaleesat yake yace "Kin sha maganin Housemate?" Ta gyada masa kai without looking at him, Safiyyah ta kallesa cike da damuwa tace "Ashe kuma iftila'in da ya faru kenan jiya Yaya Housemate? To Allah Ubangiji ya tsare na gaba, ku kuma Allah ya saka maku da alkhairi ya baku ladan hidimar da ku ke yi da kawata don bata da kowa a garin nan sai Allah sai ni da ku, kuma she is not longer safe in this state don Abdul can be cunning, azzalumi ne mugu, nasan har yanzu yana labe garin nan bai tafi ba, kuma ba imani ne da shi ba ina jin tsoron next move dinsa, Allah kadai yasan sau nawa ya koma apartment din nan yaga babu kowa ciki" Jay dai ya ɗan yi murmushi yace "She will remain here har ta gama exams dinta in sha Allah" Khaleesat ta kallesa ta girgiza kai cikin sanyin murya tace "Bazan iya exam din ba, Nigeria nake son tafiya" Safiyyah ta mata wani kallo kamar zata ce in tana da kudin jirgi ta tafi sai dai kuma kawai tayi shiru tana hararanta, Jay ya kwantar da murya yace "Saboda me baza ki iya exam ba Khaleesat, stop saying that pls, in sha Allah zaki yi jarabawan ki lafiya, in kun gama sai ki koma Nigeria" Safiyyah tace "Atoh shi dai na gani, kan wani tantirin ɗan iska take son lalata future dinta, duka duka fa shekarar karshe za mu shiga yanzu a makarantar" Khaleesat ta sauke idonta hawaye na sauka idonta don tasan baza su gane abinda take nufi ba, Jay ya sauke ajiyar zuciya yace "Try calming her down Safiyyah, and naga tun jiya bata wani ci abinci ba ban san ko tafi son abincin Nigeria ne ba, nasa cook din gidan yayi ordering ingredient din har an kawo, i don't know ko zaki girka mata a kitchen tunda kina nan" Safiyyah tace "To ba damuwa, let me cook for her" Yace "Alright" a tare suka bar dakin Khaleesat ta bi su da kallo hawaye na bin fuskarta. Tunda suka shigo kitchen din Safiyyah ke bin ko ina da kallo don the kitchen is so big and well equipped, irin modernize kitchen din nan, bayan Jay ya fita cook din gidan ya nuna mata ingredients din shinkafa da miya sannan shi ma ya fita, tuni ta hau girkin a kitchen din. Wajen karfe biyar Safiyyah na daki tare da Khaleesat hira kawai take mata kamar ba abinda ya faru, ita dai Khaleesat tayi shiru tana kallonta amma gaba daya hankalinta baya kan hiran, wayar Safiyyah ya fara ring ta jawo jakarta ta ciro wayar ganin Mustapha ke kiranta ta wani turo baki sannan tayi pick ta sa handsfree tace "Ina wuni yaya" Ko amsa gaisuwar bai yi ba yace "Waye ya zo ya daukeki a mota Safiyyah?" Safiyyah ta bude baki tace "Ohh haka matar taka tace maka? to ta manta a jirgi aka zo aka daukeni ba a mota ba, kuma munafurcinta zai kare mata wallahi" Tsawa ya daka mata yace "Ina maki magana kina min maganar banza? Are you okay?" Ta wani murguda baki tace "Toh ba ina hanya bane wai, haka kawai dai babu dalili bazan kama hanya in fito cikin sanyin nan ba yaya, ko ka manta jibi za mu fara exams ne?" Kashe wayarsa yayi, Safiyyah tace "Allah dai ya tsine ma Surayya albarka, kuma wallahi kafin mu gama exam mu bar kasar nan sai na mata abinda bazata taɓa mantawa ba a rayuwarta, ko da wasa kuma bazan ma gaya masa abinda ya faru dake ba kar yayi burgan cewa ki dawo gidansa ya kara ma matarsa extra nama" Ita dai Khaleesat tayi shiru bata ce komai ba, Safiyyah ta mike ta dau jakarta da gyale tace "Sai na zo gobe in sha Allahu, saura kar ki karasa cinye abincin ki zauna kina asaran hawayenki akan ɗan daba, ga lambata na sa maki a waya in da wani abu ko kuma kina bukatar komai kawai ki kirani" Daga haka ta fice daga dakin, Khaleesat ta sauke idonta kasa, Downstairs Safiyyah ta hadu da AJ wanda shigowarsa gidan kenan tana ɗan murmushi ta gaishesa ya tsaya ya amsa yana danna wayarsa yace "How are you doing" Tace "Alhmdlh ya karatu" Yace "Fine, ya naki" Tace "Muna ta fafatawa dai, to fa mun gode da hidima yaya, Allah ya saka da alkhairi da abinda ku ka ma kawata, Allah ya biya ku" Sai a sannan ya daga kai ya kalleta jin wai tana masa godiya, ita dai ta ci gaba da godiyar ta ba kakkautawa, Yace "Ameen" Tace "Yaya Housemate din ya fita ne, ni zan koma gida ne yanxu" Sai ga Jay ya shigo parlon from outside, ganinta yace "Ohk zaki koma Safiyyah?" Tace "Eh wallahi yamma tayi amma in sha Allahu zan shigo gobe da safe" Yace "To Allah ya kai mu, mu je inyi dropping dinki" Tuni AJ yayi wucewarsa sama, Safiyyah ta bi bayan Jay suka fita daga parlon tana mamakin inda karen gidan yake bata gansa ba tun daxu, sai bayan da suka dau hanya tace "Yaya Housemate...." Dariya ta ba Jay bai jira me zata ce ba yace "I am Jawwad Safiyyah" Tace "To ni dai don Allah kayi dubara ka amshe wayar da ka ba Khaleesat kar taje ta kira yan gidansu su gigita ta, kaga bamu san ko Abdul din na kasar nan ba ko ya koma Nigeria, in ta kira suka gaya mata wani maganar da kyar ta iya abun arziki a jarabawan nan" Jay yayi shiru cause he reason with what Safiyyah is saying, can yace "Haka ne kuma, i will tell her not to speak to anyone for now, amma bazan iya amsan wayar ba naga kamar it's whiling away her time" Safiyyah tace "To in da kati a wayar don Allah ka kone sa, in da WhatsApp kayi uninstalling dinsa kaga ta haka babu wanda zata ma magana, the exams is just for a few weeks, kamar gobe ne za mu gama" Yace "Sure i will do so Safiyyah" A haka suka isa gidansu ta sauka daga motar ta masa godiya yace "Ki gaida mutanen gidan" Tace "To za su ji" Yayi reverse ya dau hanyar gida hoping Khaleesat bata riga ta ma kowa magana back in Nigeria ba. Washegari da safe Jay yayi booking appointment na ganin likita saboda daren ranan ma Khaleesat dai bata yi bacci ba, yasan dai ba lallai su samu ganin likitan a ranan ba, so he was just helping her to manage her self with the drugs available, da Safiyyah kuma ta zo sai taji ta nemi zazzabin ta rasa dama kadaici ne da damuwa suka mata yawa. Ranan monday da safe Jay yayi dropping din Khaleesat school for her first exam, and he stayed behind har zuwa sanda za su gama don su koma gida tare, kawai shi dai baya son barin ta ita kadai, Jay is trying his very best na ganin Khaleesat ta sake ranta domin tayi karatun jarabawanta da kyau kar ta samu matsala, ga kuma Safiyyah dake encouraging dinta a gefe ita ma, kuma hakan yayi tasiri sosai don ta ɗan sake ranta tana karatun, AJ dai tun ranan da ya shigo ya ganta zaune a daki har bayan da suka yi Exams uku bata sake saka shi a ido ba, bata san ko yana gidan ba ma ko baya gidan, ita dai 24/7 tana daki, hatta abinci cook din gidan ne ke kai mata sama yayi knocking ta fito ta amsa, in ta gama still shi yake zuwa ya amshi tray din, bayan sati biyu da fara exam dinsu ranan suna da interval Safiyyah ta zo gidan da yamma, abinci ta kawo ma Khaleesat, Khaleesat taji dadi sosai ganin tuwo ne don dama tun jiya take sha'awan tuwon, Safiyyah tace "Kinga ba dadewa zan yi ba yanzu zan tafi kafin mutumin can ya fara kirana kamar Surayya ce ta bar gida" A hankali Khaleesat tace "Baza ki bari anjima kadan ba pls" Safiyyah tace "Wallahi yanzu Ya Mustapha zai fara kirana, bai ma san na fito ba, kuma nayi order din Lyft ma da zai maidani gashi nan ya kusa karasowa nan, tashi ki rakani kofar gida" Khaleesat ta girgiza kai tace "Kawai ki tafi za mu hadu schl tomorrow in sha Allah" Safiyyah tace "Wai ke baki gajiya da zama ke kadai a daki, don Allah ni dai tashi ki rakani kema ki ɗan yi strolling kafafuwanki" a hankali Khaleesat tace "Baza ki gane ba Sophie, wallahi i am not comfortable staying in this house, na kagu mu gama jarabawan nan in koma Nigeria" Safiyyah tace "Ae ranan Housemate dinki ya gaya min wai kince masa zaki koma apartment dinki nace lallai baki da hankali, Allah ma yasa Abdul bai sake gidan ba" Tana dariya ta kare maganar, sai kuma ta kwantar da murya tace "Kiyi hakuri kawata, nan da sati kadan zaki ga mun gama exams din in sha Allah, ki kwantar da hankalinki pls, yanzu dai tashi ki rakani" a hankali Khaleesat ta sauko daga kan gadon ta dau gyalenta suka fita dakin tare da Safiyyah, suna saukowa downstairs suka tarar da AJ a parlor da Jay, Khaleesat dai ta sunkuyar da kanta don sai yau taga AJ for almost 2 weeks, ita ta zata ma baya gidan ne, Jay na kallon Safiyyah yace "Are you going soon Safiyyah?" Safiyyah tace "Eh wallahi Yaya Jawwad Lyft dina yana hanya ya kusa" Yace "Alright, ki gaida mutanen gidan" Tace "In sha Allah za su ji" Sallama tayi ma AJ ya amsa mata, sannan ta kama hannun Khaleesat suka fita daga parlon, suna tsaye waje suna jiran karasowar Lyft wata mota ta shiga gidan bayan matukin motar ya fito daga cikin motar ya bude gate, Safiyyah tayi kasa da murya bayan sun shiga ciki tace "Ke kinga wani Ride me suna ride Khaleesat? Su dai da masu kudi kawai suke harkar su a kasar nan, in kin bibiya abokansu ne 'ya yan masu kudi irinsu" Khaleesat dai bata ce komai ba, bayan kusan minti uku sai ga Lyft din Safiyyah ya iso, Safiyyah ta bude bayan motar ta shiga, Khaleesat ta daga mata hannu, Safiyyah na mata murmushi tace "Sai mun hadu a schl kawata, kiyi karatu da kyau fa" Kai kawai Khaleesat ta gyada mata sannan ta koma cikin gidan, duk a dar dar take tafiya a babban compound din gidan, har yau ita dai ta kasa sakin jiki a gidan nan gani take kamar a kaya ma take she is so very uncomfortable, a haka ta isa parlon gidan ganin baki biyu dake parlon tare da su Jay wanda da alama abokansu ne Khaleesat ta sauke kai ta gaishesu, suka amsa da fara'a, ita dai ta nufi stairs, daya daga frnds din nasu taji yace "Bakuwa ku ka yi a gidan" AJ dake shan fruit salad yace "Eh, yarinyar wani abokinmu ne a Nigeria ta zo jarabawa" Jay ya saki baki yana kallon AJ da ke ta shan fruit salad dinsa ko ajikinsa, Ita kanta Khaleesat sai da ta ɗan juya ta kallesa sannan ta wuce sama, abokin na gyara zama yace "Waow, amma da gani da wuri abokin nan naku yayi aure, ya huta abunsa gashi mu duk mun kasa har yanzu" AJ dai ya ci gaba da shan fruit salad dinsa yace "Ai kam ya huta, mu ma da munyi auren da wuri duk da mun haifi kamarta ai" *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* [5/21, 6:02 PM] khaleesat Haiydar ✍️: Khaleesat na zaune da daddare tana duba course din da za su yi washegari a laptop dinta, sosai take kewan Ummanta tasan kilan tana ta mata magana ta WhatsApp taji shiru, she just pray everything is alright back home in Nigeria, duk in wannan tunanin ya fado mata sai taji ta kasa karatu, haka nan dai ta tsura ma laptop dinta ido, knocking din kofar dakin aka yi ta mike a hankali ta karasa gun kofar ta bude don tasan Jay ne, sau da yawa sai dai yayi mata knocking bai fiye shigowa dakin ba, daga nan bakin kofa yake tsayawa yayi mata duk maganar da zai mata, yana kallonta bayan ta bude kofar yace "Are you sure u are studying for ur next course Halysaah?" Ta gyada masa kai tana kallonsa, ya ɗan jingina da bangon wajen yace "Erm, sorry about what you overheard AJ saying few hours ago Halysaah, kinga dalilin da yasa nake barin masa gidan shi kadai ya karata kenan, he is a serious nuisance... Kiyi hakuri da abinda yace kin ji Housemate?" Khaleesat ta ɗan yi murmushi tana wasa da gefen gyalenta kamar bazata ce komai ba, sai kuma tace "Ai ni ban ma san tsoho bane sai yau" Jay couldn't help it but laugh out loud, Khaleesat ta daga idanuwanta tace "Allah kuwa ban san shi tsoho bane, don wanda ya isa haifata ai tsoho ne" akan kunne AJ da ya fito daga parlon dake sama, tsaye yayi yana kallonta, tana hada ido da shi ta kulle kofar dakin gbamm, AJ ya kalli Jay dake ta dariya, can ya juya fuuu ya bar wajen, Jay dai ya bi sa da kallo still laughing, har ransa yaji dadin abinda Khaleesat tace akan kunne Ajayn. Jay na dakinsa wajen karfe goma da rabi yana duba laptop dinsa AJ ya shigo dakin, sau daya ya kallesa ya ci gaba da abinda yake, AJ yace "That brat will not continue staying in this house anymore, ka samar mata wani alternative kawai in ba haka ba in kira gida in fada masu ka kawo mana yarinya tana rayuwa cikin gidan nan" Jay ya daga kai ya kallesa yace "Ni ai na zata har ka kira ka gaya masu, kuma tunda ba gidanka bane baka isa kace bazata zauna ta gama exams dinta ba" AJ yace "Ohk zaka sha mamaki" Daga haka ya fice daga dakin, Jay ya ja tsaki ya ci gaba da abinda yake. Washegari tare Jay ya dauko Khaleesat da Safiyyah ya kawo su nan gida bayan sun gama exams din ranan, bai shiga compound din ba ya tsaya a waje yace "I will be going out now, sai na dawo later" Khaleesat ta sauka daga motar tana kallonsa, a duk sanda baya gidan sai taji gidan duk babu dadi, duk da ko yana nan yawanci yana dakinsa sai in da wani abu ne yake zuwa kofar dakinta ya mata magana, but she prefer him to be at home always ko da baza su ga juna ba, duk sanda ya fita sai ta shiga kadaici wani lkcn har da damuwa, kuma in dai zai fita din sai ya gaya mata zai fita, yau kam she felt relieved tunda tare suka dawo gidan da Safiyyah, yana kallonta yace "Zan kiyi girkin yau tunda ga kawarki sai ta taya ki?" Khaleesat ta sauke idonta tace "Ohk" Yace "Alright take care" ta gyada masa kai ya ja motarsa ya wuce, ita da Safiyyah suka shiga gidan, Safiyyah tace "Kai na dade banga mutumin me kirki irin bawan Allahn nan ba, he is just extra nice, ni dai Allah ya sa it's what i am thinking" Khaleesat ta kalleta, Safiyyah ta washe maki tana wani murmushi, Khaleesat taki tanka ta, Safiyyah tace "Kinga kamar jiya muka fara exams gashi saura mana course biyu mu gama, baki ga farin cikin da nake ba za mu koma gida" Suna shiga parlon gidan suka ga AJ a zaune da kare a gefensa, sosai gaban Khaleesat ya fadi don tun da ta zo gidan ita dai bata ga karen da idonta ba sai da taji haushinsa wani lkcn, karen ya mike tsaye yana kallonsu AJ ya masa umarnin ya koma ya zauna, tuni Khaleesat tayi wucewarta sama, Safiyyah ta tsaya ta gaida AJ da fara'arta, ya amsa yace "How was ur exam?" Tace "Alhamdulillah, sauran mu kwara biyu, kawai intervals din ne ke da tsayi" AJ yace "Allah ya bada sa'a" Tace "Ameen" Daga haka ta wuce sama, dakin da Khaleesat take ta shiga, ta rike haɓa tana kallonta tace "Ni fa karfin halinki mamaki yake ban Khaleesat, ya kina gidan mutane zaki zo ki wani wucesa babu gaisuwa? Me yasa kike yin haka ne?" Khaleesat ta cire mayafinta without looking at her tace "Don baki ji abinda yayi min bane jiya, frnds dinsa suka zo gidan yace masu ai ni yarinyar abokinsa ce na zo exam" Safiyyah ta kyalkyale da dariya har da kyakyatawa tace "To meye a ciki, in bai fadi haka ba so kike su yi zaton zaman kanki kike cikin maza? Ai nan kare maki mutunci yayi, kinga dai ai abokan za su yi tunanin baban naki ne da kansa ya kawo ki gidan abokansa ki zauna kiyi exams" Khaleesat ta wani kalleta tayi shigewarta bandaki, Safiyyah ta zauna gefen gado tana kyakyala dariya tace "To duka duka shekararki nawa da bazai ce ke 'yar su bace, ni dai ban ga laifinsa ba" Bayan duk sun yi sallah Safiyyah tace "Kin ga ki tashi mu je in taya ki girkin kafin mutumin can ya fara doka min kira yanzu kamar makaho" a hankali Khaleesat tace "Ni kamar ma kar inyi girkin, i don't want to go downstairs" Safiyyah tace "Amma ai ko don saboda Housemate dinki sai kiyi, tunda kika ga haka kilan shi ma yana son cin tuwon da vegetable soup ne" Khaleesat ta marairaice tace "To ai ni i am not comfortable ne, ban ma taba shiga kitchen din ba fa" Safiyya ta mike tace "Mu je, ai ni na taɓa shiga har nayi girki" A haka ta ja Khaleesat suka sauka downstairs, da ba don Safiyyah tace kilan Housemate dinta na son cin abincin ba da babu abinda zai sa ma ta yarda tayi girkin, har sannan AJ na parlon amma babu karen a kusa da shi, shi dai wayarsa kawai yake dannawa bai kalli direction dinsu ba, a haka Safiyyah ta ja ta har zuwa kitchen din gidan, after a while suka gama girkin, Safiyyah tayi take away din wanda zata tafi da shi gida tana kallon Khaleesat tace "Ke ba yanzu zaki ci abincin bane naga baki zuba ba?" Khaleesat ta girgiza kai tace "Sai anjima" Safiyyah ta tabe baki tace "To mu je, Allah dai ya sa Yaya Musty bai kirani ba" Suna fitowa main parlor suka tarar babu kowa a parlon, suka haura sama, kafin su karasa hanyar dakin da Khaleesat take aka bude kofar wani Bedroom din wata mace da bazata wuce 23 years ba ta fito, English dressing ne jikinta amma kana ganinta kaga Hausa Fulani, she is so beautiful, yarinyar ta bi su da kallo da mamaki, Safiyyah na murmushi tace "Hi dear" Yarinyar ta mayar mata murmushin tace "Hlo" Ita dai Khaleesat ta dauke kai tana biye da Safiyyah suka tafi dakin da take, Safiyyah ta kulle kofar ta dora hannu a ka tace "Na shiga uku, ke yanzu Khaleesat me yasa baza ki daina abu kamar warce bata waye ba? Mun ga yarinya ta fito daga daki kika san ko gidansu ne maimakon kice mata Hi kamar yanda kika ga nayi amma kika wani yi shiru kamar kurma kina bin ta da ido?" Innocently Khaleesat tace "To ai naga bamu santa bane" A fusace Safiyyah tace "Gaskiya na gaji da halin ki, ke ko ina sai kin sa an mana kallon en kauye? Ki ga yarinya er gayu wayayyiya abinda kema wayancewa zaki yi yanda nayi ki ce mata Hi, to meye amfanin ilimin in baka iya zaman duniya da kowa ba? Ko ɗan uwan nan nasa da kike complain a kai kece baki iya siyasar zama da shi ba, ba gashi ni yana kulani ba har da tambayata ya exams, gaskiya ki canza hali Khaleesat, ya ci ace kin yi koyi da ni akan abubuwa da yawa" Khaleesat dai bata tanka ta ba, Safiyyah tace "Duk sai kika sa kunya ya kama ni tsamo tsamo, yanzu zata su kuma wa ennan en kauyen daga ina" Safiyyah ta dau jakarta tana ciro wayarta taga miss calls din Mustapha tace "Ahaf ai na sani" Tsaki ta ja ta fara kokarin order din ride din da zai maida ta gida. AJ ya bude kofar dakinsa jin ana knocking, tana kallonsa daga inda take tsaye ba tare da taje kusa kusa da kofar ba tana ɗan kame kame tace "Ya Ajay, naga wasu mata ne a gidan, kun yi baki ne?" AJ ya gyara tsayuwarsa yace "Ohk, su nawa?" Ta ɗan bude manyan idanuwanta tace "Su biyu" Ya gyada kai yace "Good, you saw the fair Slim one that is like yellow pawpaw?" Yarinyar tace "Sure" Yace "To sabuwar budurwar saurayinki ce, all of a sudden ya tattaro ta ya dawo da ita gidan nan suke zama tare, when i said i am reporting him back home he threatened me" The lady look totally speechless and confuse, a hankali tace "Budurwarsa kuma Ya Ajay?" Ya wani hade rai yace "Ina wasa da ke ne balle in maki karya?" Shiru tayi bata ce komai ba ta sauke idonta kasa, yace "She's been in this house for 3 weeks now, ya kai ta school ya dawo da ita" Yarinyar ta sake daga ido ta kallesa, AJ ya daga kafada ya kulle kofarsa, juyawa tayi tana tafiya a hankali ta bar wajen. Har waje Khaleesat ta raka Safiyyah bayan ta takurata ta rakata, sai ma da suka jira Lyft din ya karaso sannan Safiyyah ta shiga ta mata sallama, Khaleesat ta daga mata hannu sannan ta juya ta koma cikin gidan, zaune ta ga yarinyar daxu a parlor, suna hada ido Khaleesat ta sauke kanta sai ta kasa wuce sai da tace mata "Hi, i am Khaleesat" Ido kawai yarinyar ta zuba mata tana kallonta babu yabo babu fallasa kuma babu alamar zata amsa mata, hakan yasa Khaleesat ta fara tafiya ta wuce sama, lkci daya jikinta yayi sanyi ta shiga dakin da take ciki ta kulle. AJ ya fito dakinsa zai sauka downstairs kenan sai ga Jay ya hauro sama fixgosa yayi a fusace yace "Are you out of ur senses Junaid, what did u just do?" AJ yace "Ban gane what did i just do ba, Hadeeyah came, she requested to know the lady she saw in this house, kai kuma baka isa inyi karya saboda kare ka ba tunda ba tsoronka nake ji ba, when i told u to look for another alternative for the brat ai mayar dani mahaukaci kayi" Bude kofar wani daki aka yi sai ga Hadeeyar ta fito da Handbag dinta, Jay ya sake AJ, ya bi ta da kallo yace "Hadeeyah" ko juyawa bata yi ba ta ci gaba da sauka downstairs, ita dai tasan AJ ba wasa yake yi da ita ba balle yayi mata karya, yaushe ma ya sake maka fuska balle ya maka karya, Jay yace "Look Hadeeyah, ko da wasa kika ce zaki ma people back home wannan magana i won't take it likely with you, and that will be the end between me and you, cause u never gave me a listening ear" Sai a sannan ta juyo tace "And so effing what? Wannan ne dalilin da yasa all this days baka da lokacina dama ko Ya Jawwad? I am not surprise" Tana kai wa nan ta sauka ta nufi hanyar fita gidan, Jay ya kalli AJ da ya daga kafada shima yana kallonsa. Jay wasn't even that bordered kamar babu abinda ya faru, amma gaba daya ya fita harkan AJ a gidan, ko kallon inda yake baya yi, ya canza code din kofar dakinsa ta yanda ma bazai shigo masa daki ba, yasan ba lallai ma Hadeeyah ta gaya ma yan gida komai ba, she won't even dare try that, amma still yaki ko da kiranta a waya, dama ita ce me kiran nasa, daga Oxford University take kuma bata ma ce masa zata shigo Maryland ba she just came without notice, ita ko Khaleesat bata ma san abinda ke faruwa a gidan ba amma abinda Hadeeyah ta mata ya tsaya mata a rai. Ranan friday Khaleesat suka yi second to the last exam dinsu, na karshen kuma za su yi ranan talata, gaba daya ta kagu su gama ta bar kasar zuwa sannan hankalinta yayi gida, she just want to go home, duk da tasan Housemate dinta zai ce zai siya mata flight ticket amma gani take she is just a burden to him, for weeks now hidima kawai yake da ita, ya kai ta schl, at times ya jira ta gama jarabawa ya maidota gida, wani lkcn dab da sanda yasan zata fito exam zai koma schl din don daukota, he really tried for her during this period and he is always making sure that she is fine, bata ma san ta inda zata fara appreciating din shi da Safiyyah ba, they where by her side all through, ba don su ba da bazata iya jarabawan ba ma, yau kam tunda ta tashi take jin ta wani iri tana dai kwance da tunani iri iri a ranta, ji take kamar ta jawo monday. AJ na zaune reading nook din dake parlor yana kokarin hada references dinsa a laptop dinsa, ga textbooks kaca kaca a gabansa, gaba daya Jay ya bi ya goge duk wanda ya tura masa ta WhatsApp, infact duk wani abu da Jay yasan AJ zai karu da shi na bangaren PhD da suke sai da yabi ya goge tas, shi da AJ bai nuna masa ma yasan abinda yayi ba, shi yasa ya dukufa tun asuba yake reading nook, ɗaga kai yayi bayan yayi perceiving din wani turare da ya gauraye ko ina na parlon, he was a bit shock ganin wanda ya shigo parlon tare da wasu mutane biyu suna biye da shi, ya sauke idonsa, he was surprise and shock, sai kuma ya mike ya dawo cikin parlon, ya ɗan dukar da kansa yace "Sannu da zuwa Abba" Wanda ya kira da Abba yace "Ya karatun? Ina Ahmad?" AJ yace "He is upstairs, Abba surprise visit ka mana" Zaunawa Abban yayi saman kujera yana amsa gaisuwan da ma'aikatan gidan ke masa cike da ladabi sannan ya kalli AJ yace "I just branched to check on u both, daga England mu ke munje wani taro" AJ dai ya sunkuyar da kansa, sai kuma ga wata mata da bazata wuce 50 ba cikin shiga ta alfarma ta shigo parlon da wata yarinya that is 16 years old, AJ dai ya shafa kansa don shi abun ma dariya ya fara basa, ya dai gaisheta ta amsa, yarinyar ta tafi ta rungumesa tace "Ya AJ naga ka zama kato, are you going to the Gym?" Matar da suka shigo tare ta nemi waje ta zauna tace "Allah sa karatun yake" Wani kallo ya mata ta gefen ido ya wuce sama su kuma masu aikin gidan suka tafi dauko bottle water da lemo, direct dakin Jay ya nufa a dai lkcn da Jay ya bude kofar dakinsa ya fito, AJ yayi wata dariyar bosawa yace "Wallahi ga Abba da Aunty a parlor" Jay ya dinga kallonsa babu ko kiftawa, can yace "Abba da Aunty kuma?" AJ couldn't stop laughing, Jay ya ɗan leka downstairs yaga da gaske ne, buda baki yayi yana kallon AJ da ya kasa daina dariya, Jay ya sauke ajiyar zuciya ya jawosa yace "Look, let's talk pls Ajay...." Ajay yace "Talk about what? Ba dai baka jin maganata ba, zaka san yanda zaka yi da yarinyar nan yau, kaga ban ma kai report ba sun zo da kansu za su gane ma idonsu rayuwar da ka jefa kanka a Maryland" Jay dai kallonsa kawai yake, AJ ya daga kafada irin ko a jikinsa din nan ya sauka downstairs yana murmushi, Jay ya fi minti biyu tsaye thinking of what yo do, daga karshe dai ya nufi bangaren AJ, yana tura kofar dakinsa yaji dakin a bude, juyawa yayi ya tafi dakin da Khaleesat take yayi knocking, duk da ba bacci take ba amma idonta a kulle, ta bude idonta ta mike zaune sai gashi ya shigo dakin, Calmly yace "Bacci kike ne Halysaah?" Ta girgiza masa kai tace "A'a" yana kallonta yace "Ya na ganki haka ko baki da lafiya ne?" Nan ma ta girgiza masa kai tayi shiru, ya kwantar da murya yace "Gaya min gaskiya, ko dai tunani kike Housemate?" Calmly yake mata maganar kamar ba komai, ta ɗan yi murmushi cikin sanyin murya tace "A'a" Yace "Good, i think we have visitors a gidan nan yau, i will change you to another room wanda babu wanda yake shiga zuwa har sanda za su tafi, nasan baza su wuce kwana biyu ba bakin za su tafi in sha Allah" Ita dai tayi shiru tana kallonsa, ya sakar mata murmushi, ta sunkuyar da kanta, yace "Alright, ta so mu je ko?" Sauka tayi daga kan gadon ta dau gyalenta, yace "I will bring you all u need to the room afterward" daga haka ya nufi kofa tana biye da shi, direct ya nufi bangaren AJ da ita, ya bude kofar dakin yana kallonta yace "Here" ta sauke idonta tana kallon cikin dakin dake wani kamshi na musamman sannan ta shiga, ko da wasa bata san dakin AJ bane, Jay yace "I will be back soon Halysaah" Ta gyada masa kai, ya jawo kofar sai dai bai kulle ba tunda bai san code dinsa ba yanzu, sai bayan da ya bar wajen yaji dariya ya taho masa, to yanzu ta ina ma zai fara lallaba AJ, kawai yasan ya ma gama kashe AJ, to in ba haka ba bai san way out ba don bangaren AJ ne kadai Halysaah zata tsaya da babu wanda zai san tana gidan tunda babu me zuwa ko kusa da bangaren nasa sanin halinsa, amma kaf din gidan yasan Aunty sai ta bude ta shiga banda part din AJ, downstairs ya sauka da sauri don zuwa gaida su Abba, Khaleesat dai ta kasa daina bin dakin da kallo, komai na cikin dakin fari ne kal har wani kyalli yake tsabar neatness, ita abun yana mata kamar dakin wani important person ne a gidan Jay ya kawota, ta karasa ta zauna gefen gadon a hankali, she just don't know why she is not comfortable with the room. Jay dai na zaune parlor ne amma gaba daya hankalinsa na kan AJ dake ta shan fruit din da aka kawo ma Abba hankali kwance kamar shi aka kawo ma, Aunty kuwa tana dakin Abba dake nan downstairs tana gyara masa, AJ ya mike zai tafi sama, Jay na ganin haka ya mike ya bi bayansa da sauri, bayan sun haura sama Jay yace "Hey let's talk AJ" AJ ya wani kallesa, sai kuma yayi wani dariyar shakiyanci yace "Talk about what? Pls sort ur self out, ka daina ma involving dina a crime din nan da ka aikata, kar a zata tare muka aikata" Jay dai ya fara kokarin danne dariyar da ya taho masa don bai ma san ta inda zai fara masa bayani ba. *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* [5/22, 6:50 PM] khaleesat Haiydar ✍️: Parlon dake sama Jay ya ja AJ zuwa can yace "Ohk now, let me explain Bruh" AJ na girgiza kai yace "I am not interested pls Jay, ni fa bana son ma kana min magana a gidan nan kar ayi zaton tare mu ka kawota" Jay yace "Naji.... bayan yanzu bazan sake maka magana ba, kawai dai na duba naga duk gidan nan dakin ka ne kadai yake da wahalan shiga..." Nan da nan AJ ya hade girar sama da ta kasa yana kallonsa yace "I don't understand, me yasa kake using dakina kake misali? What are you insinuating? What is ur point??" Jay ya shafa sumar kansa a hankali yace "My point is, na kai Housemate dita dakin ka for the meantime before i find a way out, nasan can ne kadai su Aunty baza su ganta ba, tunda dakin ka out of bound ne" Haka AJ yayi dropping jaw yana kallon Jay baya ko kiftawa with shock written all over his face, Jay ya sosa kansa zai yi magana suka ji muryar Hajiya Rukayya warce suke kira da Aunty, ta karaso parlon tace "Jay ka je Abbanku na magana a parlor" Jay yace "To gani nan zuwa Aunty" Ta ɗan kalli AJ sannan ta juya ta bar parlon, Jay ya sauke ajiyar zuciya yana kallon AJ that was still looking at him ko kwakkwaran motsi baya yi, da alama ya ma kasa cewa komai, Jay yayi patting ɗin shoulder dinsa yace "I know u gat my back Bruh, you won't love seeing Abba Mad at me" Yana fadin haka ya juya ya bi bayan Aunty yana sauke wani ajiyar zuciya, after almost 15 mins Jay ya dawo sama, zaune ya tarda AJ a parlon dake sama ya tallabi chin dinsa da duk hannunsa biyu yana girgiza kafa, he looks restless, Jay dai ya danne dariyar da ya taho masa da kamar zai juya ya koma downstairs, AJ na ganinsa ya mike ya nufesa a fusace ya fixgosa yace "What offense have i done to you Jawwad? Why my room? Why will u take her to my privacy, my own comfort zone, what sort of nonsense is this plss? Dakina fa? Meye hadina da ita zaka kai ta har Bedroom dina?" AJ was so mad at him, nan da nan idonsa suka sauya launi, Jay yace "To Abba dai na kiran ka, je ka dawo sai ka ci gaba" AJ dai sai kallonsa yake yana huci, can ya turasa ya bar parlon kamar zai tashi sama, Jay ya wara ido yana shafa kansa yana ɗan murmushi, karkari dai iya abinda zai yi kenan bazai wuce haka ba, kuma ba wani kiransa da Abba yake yi kawai wahala ne bai so yasa yace masa ana kiransa downstairs, dakin Khaleesat ya koma ya dauko mata box dinta da abubuwan da yasan zata yi needing ya kai dakin AJ, Khaleesat ta mike da sauri ganinsa, a hankali tace "But Housemate i am not comfortable in this room" ya ɗan bude ido yace "Why? Meye da dakin Halysaah?" Tayi shiru bata ce komai ba, Calmly yace "C'mon Halysaah wannan ma ai yafi wancan da kike ciki" Yana murmushi ya kare maganar, ita dai tayi shiru bata ce komai ba, ya ajiye mata kayanta da wayarsa yace "If you need anything just call my line" Ta gyada masa kai, ya nuna mata hanyar bandakin dake babban dakin yace "In zaki yi sallah ga bandaki can" Nan ma dai ta gyada masa kai kawai, ya juya ya fita daga dakin ta koma ta zauna, gajiya tayi da zama tana son kwanciya amma ta kasa kwantawa saman gadon, ita kanta ta rasa dalili, can dai ta zamo kasa a hankali ta kwanta saman lallausan carpet dake dakin ai ko nan da nan bacci ya dauketa, throughout ranan haka Khaleesat ta yini a dakin ita kadai, tun da Housemate dinta ya kawo mata lunch har lokacin magrib yayi bai dawo dakin ba, sai Cook din gidan ne ya kawo mata dinner, tana zaune saman darduma bayan ta idar da sallahn isha taji an bude kofar dakin ta daga kai, sosai gabanta ya fadi ganin AJ, ta sauke idonta daga kallonsa, shi kam ko kallon inda take bai yi ba fuskarsa a murtuke ya tafi ya dau second phone dinsa da laptop, ya bude press dinsa ya dau pajamas dinsa sannan ya fice daga dakin, sai a sannan ta daga kai ta bi sa da kallo tana mamakin abinda ya shigo yi, don bata san me ma ya dauka a dakin ba, har sannan bata kawo cewar dakinsa bane, har ta fara bacci Jay ya shigo dakin da sallama, ta mike zaune daga kwancen da take a kasa, da mamaki yake kallonta yace "Me yasa kika kwanta a kasa Halysaah?" Ta girgiza masa kai kawai, yace "C'mon don't do that pls, ga gado zaki wani kwanta a kasa" Ta kalli gadon tace "Zan kwanta" Yace "Good, hope u need nothing?" Tace "Bana bukatar komai" Yace "Alright then, good night" A hankali tace "Thank you" ya mata murmushi yace "In kashe maki wutan dakin ko a maida maki dim light?" Tace "Dim light" Ya mayar mata wutan mara haske sosai sannan ya juya ya fita daga dakin, bayan fitarsa ta koma tayi kwanciyarta a kasa, ita gani take kamar master bedroom din gidan ne, may be that's why she is not comfortable, wajen karfe dayan dare dakin yayi sanyi sosai amma taki daukan duvet din saman gadon ta rufa, kawai ta lullube da Hijab dinta, she was so cold gashi Safiyyah bata hado mata kayanta da Sweater ba, tana ta kwance ta kasa bacci saboda sanyin da ya dameta sai juye juye take taji an bude kofar dakin, a hankali ta sauke Hijab dinta kasa kadan tana son ganin wanda ya shigo don har kanta ta rufe, taga AJ ne ya shigo, kallo daya yayi mata ya tafi daukar abinda zai dauka, zaro ido tayi bayan ta zargi anya ba dakinsa bane nan kuwa, sai bayan da ya fita taji ya kullo kofar ta mike zaune tana sake bin dakin da kallo with shock, dumin da taji dakin ya fara dauka gradually ne yasa ta gane ya kunna mata heatern dakin, ta koma a hankali ta kwanta sai da dakin yayi dumi sannan bacci ya dauketa..... Washegari da safe Jay na zaune main parlor tare da Abba da Aunty, cikin nutsuwa Abba ke masa magana amma shi gaba daya hankalinsa na sama kan Halysaah don tun da gari ya waye bai je wajenta ba, kawai dai Cook din gidan ne ya kai mata breakfast, AJ ya shigo parlon daga reading nook da yake zaune ya nufi dinning area zai yi breakfast, Abba ya bi sa da kallo, after a while yace "Baka yi breakfast din bane" Jay ya ɗan kalli AJ, Aunty kanta kallonsa take ita ma, without turning back AJ yace "Ban yi ba" Aunty tace "To ai naga cook din gidan ya kai maka Breakfast din sama daxu" Ko tankata AJ bai yi ba ya tafi dinning ya zauna, Abba na kallon Jay calmly yace "Is he Okay?" Jay ya ɗan shafa kai yayi kasa da murya yace "I think supervisor dinsa ne bai yi approving Article din da yayi publishing ba tukunna" Aunty tace "To banda abun sa ai ba wani abu bane he should add in more effort to his work kawai" Shi dai Jay bai ce komai ba, haka shi kansa Abba, after a while Jay ya mike ya tafi sama, direct part din AJ ya nufa bayan yayi sallama ya tura kofar dakin ya shiga. Wajen la'asar AJ na zaune parlorn dake sama, gaba daya he look moody, dama jiya da daddare a nan parlorn ya kwana tsabar takaici, har zuwa yanzu yaki ce ma Jay komai a gidan, Jay kuwa ko a jikinsa don ko kallonsa ma baya yi, su biyu ne kadai a gidan don Abba ya fita tare da Aunty da autarta zuwa gidan wani prominent friend dinsa a garin, da yake gobe da safe za su bar kasar zuwa Nigeria, AJ ya gyara zama yana bin Jay da kallo trying to be sure of what he is holding in his hand, he was very shock ya dai bi sa da kallo har yaga ya nufi bangarensa, ya tallabi chin dinsa yana girgiza kafa, sai bayan da Jay ya fito for the first time since yesterday AJ yace "Wallahi i will never forgive you for these Jawwad, i promise you am not forgiving you" Jay dai ya dake bai yi dariyar da ya basa ba, kuma yaki tankasa yayi wucewarsa ya bar sa zaune a gun, da daddare Khaleesat na duba laptop dinta Jay ya shigo dakin da sallama ta daga kai tana kallonsa ya zauna kan kujeran dakin yace "Hope you are better now?" Ta gyada masa kai, yace "Toh Allah ya sauwake, amma ki tabbatar kin sha maganin so that u get enough night rest" Tace "Zan sha" Yace "Alright Good night Housemate, bacci nake ji" Ta ɗan yi murmushi tana kallon agogo dake nuna karfe goma tace "Ai baka ma yi da wuri ba" Yayi murmushi kawai yace "Saura kar ki kwanta saman gadon yau" A hankali tace "Zan kwanta" Yace "Good" Daga haka ya fita daga dakin, shi kansa yasan tunda ta dawo gidan yake tauye ma kansa bacci, kuma ba wai baccin baya damunsa bane kawai daurewa yake yi, har ciwon kai yake yawan yi yanzu saboda baya bacci sosai, Khaleesat ta kashe laptop dinta ta ajiye sannan ta mike a hankali ta dauko maganin da ya kawo mata daxu ta sha sannan ta kwanta saman gadon, amma fa a dar dar take saman gadon, Jay na isa parlorn dake sama ganin AJ kwance kan kujera yana danna wayarsa yace "Do you care sharing my room with me today?" AJ yaki tankasa yana danna wayarsa, Jay ya daga kafada yayi wucewarsa dakinsa, after like an hour AJ ya mike zaune jin muryar Abbansa, Abba dake kallonsa yace "Is everything Alright Ahmad? Why are you lying down on the Couch?" AJ ya fara sosa kai yace "Eh yanzu zan tafi daki Dad, ban san sanda bacci ya daukeni ba" Yana fadin haka ya mike tsaye ya dau wayarsa ya nufi dakinsa, Khaleesat ta juya jin an bude kofa don ba bacci take ba, yana shigowa dakin kuma ya kulle kofar ya tsaya nan bakin kofar, rufe har kanta tayi da duvet, ya tafi gaban madubi ya tsaya yana tunanin Jay bai taɓa cutarsa ba irin na wannan lokacin, sosai abun nan ya tsaya masa a rai, ita dai Khaleesat tana ta sauraren taji ya bude kofar ya fita daga dakin amma taji shiru, hakan yasa ta sauke duvet din kanta a hankali suna hada ido ya watsa mata kallo yace "Meye kike kallona?" Ta wani kallesa, sai kuma ta juya masa baya bata ce komai ba, after almost 5 minutes ya bude kofar dakin ya fice, tsabar yanda bai yarda da neatness din duk dakunan dake gidan ba ya sa ya gwammace ya kwanta a parlor instead of going into any of the room. Da Asuba Jay ya fito dakinsa kenan zai sauka downstairs su yi sallah da Abba, tunda Abba ya zo tare suke sallah amma banda AJ da baya saukowa ayi sallan da shi sai dai yayi shi kadai a sama, Jay ya hadu da Abba yana haurowa sama, Abba yace "This shows baku sallah tare a gidan nan Jawwad, ma'aikatan gidan nan guda biyu duk Musulmai ne, ga ka ga Junaid, amma ace baza ku hadu ku yi sallah ba?" Da sauri Jay yace "Muna yi Abba..." Abba bai ce masa komai ba ya nufi bangaren AJ, Jay ya buda ido sosai, sai kuma ya bi sa da sauri yace "Zan kira maka shi Abba..." Abba yace "Jiya da nace ka kirasa ya sauko?" Jay ya kasa cewa komai, duk tunanin Jay za su ga AJ a Parlor a kwance amma sai yaga baya parlon, nan hankalin Jay ya tashi ya tsaya a inda yake tsaye ya kasa ci gaba da bin bayan Abba, he wish Junaid bai cire code din nambobin kofar dakinsa ba, Abba na tura kofan sai ga AJ da ya shiga bandakin dake parlorn da suka baro yayi alwala ya taho zai dau pray mat, shi ma zaro ido yayi yana kallon Abba kamar yanda Jay ma ya tsaya kallonsa, AJ ya juya suka kalli juna da Jay, tunda Abba ya kunna wutan dakin ya tsaya for like a minute bakin kofar dakin yana kallon Khaleesat dake bacci, sai kuma ya juyo ya fito closing the door gently, Daga AJ har Jay suka sunkuyar da kai a tare kamar munafukai, Abba dai sai kallon AJ yake, after 30 seconds of silence, speaking Calmly Abba dake kallon Jay yace "Abinda ke faruwa gidan nan kenan Jawwad, and you told me nothing about it?" Jay ya kasa cewa komai kuma ya kasa barin su hada ido da Abba, cikin nutsuwa babu fada Abba yace "Magana nake maka Jawwad" Da kyar Jay ya girgiza kai yace "I know nothing about it Abba" AJ ya bude baki yana kallon Jay da yaki kallonsa, Abba ya gyada kai yace "Ohk then, ku mu je mu yi sallah lokaci na wucewa" Daga haka ya juya ya bar su tsaye a wajen, Jay ya bi bayan Abba da sauri, AJ ya bi sa da kallo baya ko kiftawa, tuni har Abba ya sauka downstairs hakan yasa Jay ya tsaya Parlor sai ya tuna tuggun da AJ ya hada masa gun Hadeeyah just 3 days back, bai san sanda dariya ya taho masa ba, sai ga AJ da jikinsa yayi sanyi ya shigo parlon yana kallonsa, hakan yasa Jay ya danne dariyarsa ya hade rai ya sauka downstairs da sauri, AJ ya bi sa da kallo, sai kuma a hankali ya zauna saman kujera ya kai hannunsa baki, ganin abinda Jay yayi masa yake kamar a mafarki, bai taɓa shiga shock irin na wannan lokacin ba. Da safe kamar babu abinda Abba ya gani a gidan don bai sake masu maganar baz kuma da alama ko Aunty bai gaya ma ba, Jay ma yasan bazai taɓa gaya mata ba, karfe sha daya jirginsu zai tashi zuwa Nigeria don haka har sun gama shirin tafiya Airport, Abba ya kalli Jay yace "Junaid bai sauko yayi Breakfast ba ko an kai masa sama ne?" Jay yace "I don't really know" Abba ya dau wayarsa ya kira AJ, ba a dau lkci ba sai ga AJ ya sauko parlor shi dai ya kasa hada ido da Abbansa, Abba na kallonsa yace "Kayi breakfast ne, naga baka sauko ba" Without looking at his Dad yace "Na yi" Abba yace "Ohk, za mu tafi airport ne yanzu, get ready" a hankali AJ yace "Ohk" Daga haka ya juya ya koma sama, sai da AJ ya fara zaunawa a parlon sama for almost 5 mins, gaba daya jikinsa a sanyaye yake, gashi ya tsani shirun Abbansa don ba alkhairi bane shirun, gwara ace ma fada yayi ta masa ba kakkautawa da wannan basarwan da yayi kamar bai ga komai ba, his next move might not be funny, Jay ya cucesa, bai taɓa zaton haka daga Jay ba, to ko yace ma Abba bai santa ba ta yaya zai yarda da shi tunda a dakinsa ya ganta ba dakin Jay ba, ganin bata lkci kawai yake ya mike yana tafiya a hankali ya tafi dakinsa don dauko kayan da zai sa, yana shiga dakin Khaleesat na fitowa daga bandaki da hijab dinta har kasa ta fito wanka, ya wani kalleta daga sama har kasa fuskarsa a daure, ita dai tunda suka hada ido ta dauke kanta bata sake yarda ta kallesa ba tana dai tsaye hanyar shiga bandakin, ya dau kayan da zai dauka ya karasa gaban madubi ya dau tsadadden turarensa ya fice daga dakin, ta wani kyabe baki ta karasa shigowa cikin dakin. Har Abba suka isa Airport bai ce ma AJ komai ba akan daxu da asuba, kuma da alamar babu abinda zai ce masa, he was just speaking about something different in the car, a haka suka rabu normal normal a airport kamar babu komai, AJ yaki jiran Jay ya ja mota ya bar airport din ya kama hanyar gida, dole sai Uber Jay ya samu da zai maida shi gida, ko da ya isa gida ya ga AJ zaune a compound da non alcoholic wine a gabansa trying to use it to calm himself down at the same time trying to figure out wani hukuncin Abbansa zai ce zai dauka a kansa..... *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* [5/26, 9:45 AM] khaleesat Haiydar ✍️: Khaleesat felt so much relieve after leaving AJ's room, tana biye da Jay ta koma dakin da take, ba tare da Jay ya kalleta ba bayan ya ajiye laptop dinta dake hannunsa yace "Kin ji sanda aka bude kofa da asuba ne?" Khaleesat na kallonsa ta girgiza kai tace "I am not sure, may be ina bacci sannan, banyi bacci da wuri ba" Yace "Ohk" Tace "Why are you asking?" Ya juyo yana kallonta, ya ɗan mata murmushi yace "Nothing" Tace "But ai frnd din ka yana shigowa ya dau stuffs dinsa wani lkcn" Jay yace "Ohk" Har ya juya sai kuma ya sake dawowa yace "Kince baki yi bacci da wuri, ciwon kan ke damunki har yanzu?" Ta girgiza kai tace "A'a, kawai baccin ne dai bai zo ba" Yace "Ohk" Khaleesat ta bi sa da ido har ya fita daga dakin sannan ta zauna gefen gado a hankali, har cikin ranta take jin kamar ta jawo ranan talata, she is so tired tana bukatar kawai ta ganta kusa da Ummanta, she need her Mom's hug, Jay na fita ya kira ma'aikatan gidan su gyara ma AJ dakinsa, Jay made sure the workers left nothing untouched a dakin duk da babu abinda dakin yayi, amma irin gyaran da aka ma dakin da bandakin ba na wasa bane, sai da ko ina ya dawo yana sparkling tsabar gyara sannan Jay ya koma downstairs, amma still a ranan ma AJ bai kwana dakin ba, yayi kwanciyarsa a parlor kan kujera. Washegari which was monday AJ na zaune usual spot dinsa a compound da Coke din gwangwani a gabansa, har a sannan yaki ce ma Jay komai a gidan, not even Jay hatta ma'aikatan gidan duk ba wanda yake yi ma magana he is just keeping straight face, Jay ya fito daga cikin gida ya karasa har inda yake zaune, ko kallon direction dinsa AJ bai yi ba yana juya counter din hannunsa, Jay na kallonsa yace "Abba wants to speak to you" Yana fadin haka yace "Abba gashi nan" Ya ajiye wayar gaban AJ, Calmly Abba yace "How are you doing Junaid" AJ ya sauke idonsa ya gaida Abba, Abba ya amsa yace "You didn't call to know if we arrived safely" AJ yace "Ayi hakuri" Abba yace "It's fine, yaushe za ku dawo hutu" AJ yace "Ran Thursday zan dawo in sha Allah" Abba yace "What about Jawwad" A takaice AJ yace "I don't know" Abba yace "Hand the phone over to him" Jay ya dau wayarsa sitting in one of the chairs beside AJ yace "Na'am ina ji Abba" Abba yace "Kai yaushe zaka dawo" Jay ya ɗan yi shiru, sai kuma yace "Probably next week in sha Allah" Abba yace "Ohk Allah ya kai mu, earlier today you said you have something to tell me unfortunately ina tare da baƙi a lkcn, so what is it Jawwad" Jay ya ɗan shafa kansa thinking of where to start, can dai yace "Abba dama it's about the girl u saw yesterday" Abba yayi shiru at first, sai kuma "Ohk, what about her?" Jay yace "Abba ni ne na kawota gidan ba AJ ba, she is a student of John Hopkins also, she is having issue with House rent and she's writing exam, so shine kawai na kawota gidan nan zuwa sanda zata gama jarabawan...." Abba ya dakatar da shi yace "Did you and Junaid birth me or i birth you both?" Jay ya girgiza kai da sauri yace "Billah Abba i am not cooking up stories, believe me, all what i am saying is the truth ai kasan bana maka karya Abba, kawai dai ni na kai ta dakin AJ ne without even his knowledge cause Aunty will definitely see her in the house, part din AJ ne kawai nasan bazata shiga ba, kuma because of this... AJ parlor ya dawo yake kwana, wallahi babu komai tsakaninmu da ita kawai taimako ne, you can even speak to her to confirm ranka ya dade" Abba yace "If she is having rent issue don menene baza ku bata kudin hayan ta biya ba ko kuma ni ku min magana, na menene sai kun kawota nan gida cikin ku ta zauna? Is that ur home training? Dama addininku ya yarje maku da haka?" Jay ya sauke ajiyar zuciya a hankali yace "Kayi hakuri ka gafarce mu Abba, she will be rounding up her exam on Tuesday, and she will leave in sha Allah" Abba yace "Kaga da ba don nasan baza ka min karya ba Ahmad i won't listen to you, da Junaid ne ya tsaya mun wannan bayani bazan yarda da shi ba, and my plan was to start making arrangement na samar masa mace da zan aura masa a kai masa ita can ƙasar, tunda ka min wannan bayanin naji na kuma yarda amma daga kai har shi sati biyar na baku kacal ku gabatar min da macen da za ku aura, ita kuma i will send you some money to sort out her House rent" AJ ya daga kai yana kallon Jay bayan yaji abinda Abbansa yace, sai kuma ya mike kamar zai tashi sama ya bar wajen, shi dai Jay was speechless this was the least thing he was expecting to hear from Abba, jin Abba ya katse wayar ya zuba ma screen din ido, ya basu 5 weeks?? jay ya fi minti goma zaune a wajen kafin daga karshe ya sauke ajiyar zuciya ya mike ya dau wayarsa ya shiga cikin gida. The next day Khaleesat suka gama jarabawansu na karshe and she was so happy amma kuma da ta tuna wasu abubuwa kawai sai mood dinta ya canza, suna zaune tare da Safiyyah a cikin makarantar ganin yanayinta da yanda ta sauya lokaci daya tayi shiru, Safiyyah ta kalleta tace "Why are you like this Khaleesat?" Khaleesat ta daga kai ta kalleta, a hankali tace "I don't have the means of going back to Nigeria Sophie, the burden i am placing on my Housemate is too much ba shi ya kawo ni kasar nan karatu ba, he knows nothing about me, don me zan yi ta dora masa nauyina har haka?" Safiyyah tace "To ya za kiyi Khaleesat, tunda ba ke kika rokesa ya maki ba ai kawai addu'a zaki masa Allah ya saka masa da alkhairi, he is ur God sent Angel, ba gashi with or without Abdul kin gama jarabawanki lafiya ba" Khaleesat ta sauke idonta jin hawaye ya ciko mata, Safiyyah ta hade rai tace "To meye na kuka kuma?" Muryarta na rawa tace "Ni dai bana son yace zai sake kashe min kudi masu yawa in koma Nigeria, i am feeling guilty" Safiyyah ta wani kalleta, can tace "Kya rube a kasar nan kuwa, ke kina da hanyar komawa ne? Ko kuma aikatau zaki nema a kasar ki tara kudin komawa Nigeria? In ba dai kudaden Abdul dake account dinki zaki yi using ki biya kudin jirgi ba" Safiyyah na kai wa nan ta kyalkyale da dariya tace "Ko ya kwashe en kudaden nasa ne?" Ita dai Khaleesat tayi shiru taki ce mata komai, Safiyyah tayi dariyarta me isarta sannan tace "Allah ba batun wasa ba, ya kwashe kudaden nasa ne?" Khaleesat ta girgiza kai a hankali tace "Suna nan" Safiyyah tace "Miliyan nawa ne ma?" Khaleesat ta sauke idonta tace "Almost 9.5 Million" Safiyyah tace "To kawai ki siya Ticket abunki tunda dai yasan ba uban wani gareki a kasar ba da zai baki kudin komawa Nigeria ba, bayan shi kawo ki, in nice ke ma har shopping sai nayi na komawa Nigeria a cikin kudin wallahi, ai bazai san kin taɓa ba tunda ba shi ke ganin alert ba" Safiyyah na dariya ta kare maganar, ita dai Khaleesat bata tanka ta ba, Safiyya tace "Naji kinyi shiru ko baza ki taɓa ba? Wallahi yanzun nan in raka ki shopping mu fatattake kudin" Khaleesat tace "Ai ba nawa bane da zan fatattake su" Safiyyah ta kwashe da dariya tace "To ai sai kiyi ta zama a kasar, dama gulma ce yasa kika kawo maganar ba wani abu ba don nasan Jay kike saka ran ya biya maki ticket" Khaleesat dai kallon Safiyyah kawai take ta kasa ce mata komai, amma ita kadai tasan abinda take ji a zuciyarta, Safiyyah tace "In kuma in ma Ya Musty magana to, don dai Economy class ticket da zai siya mana bazai ce ya gagaresa ba" Da sauri Khaleesat tace "A'a, zan yi amfani da kudin account dina" Safiyyah tace "Atoh dai" Khaleesat ta gaya mata haka ne kawai don bata son taje ta ma Ya Musty magana.... Jay ne ya zo daukansu a schl din as usual, sai da ya fara dropping din Safiyyah sannan ya kama hanyar gida da Khaleesat, daxun nan yaga Abba ya sako masa dala dubu goma wai na House rent dinta, da ya gaya ma AJ sai cewa yayi ya masa transfer din Dala dubu biyar shi ma ya rike dubu biyar din tunda ba su suka kawota kasar ba, shi da Jay bai tankasa ba, Jay dake driving ya ɗan kalli Khaleesat jin shirun yayi yawa, yaga alamar tayi nisa tunanin da take, sai a sannan ya kula da idonta da yayi ja, a hankali yace "Halysaah" Juyawa tayi ta kallesa trying to look alright ta ɗan yi murmushi tace "Na'am" Yace "Are you okay?" Tayi yake tace "Na gaji ne kawai" Jay yayi shiru, bai sake ce mata komai ba amma yasan ba gaskiya ta fada masa ba, a ɗan few months din da yayi da ita har ya gama studying dinta gaba daya, he knows when she is happy, sad, bored, disturbed, and even tired, wannan karan yaga damuwa ne karara a fuskarta, ya dai ci gaba da driving dinsa har suka isa gida, bayan yayi parking ya juya yana kallonta, a hankali yace "Me ke damunki Halysaah?" Duk kokarinta na ganin ta nuna masa ba komai hakan yaci tura, don kawai ita ma gani tayi kuka ya taho mata, Jay ya jinginar da kansa da kujeran motar bai ce mata komai ba, kwana biyu ya huta da kukanta don a sanda ya dawo da ita gidan rana daddaya ne bata kuka don ma Safiyyah na taka mata burki kuma ya ga tana ɗan jin maganar Safiyyar wani lokaci, sai da tayi kukanta me isanta sannan yace "Sauka mu shiga ciki to" Ba musu ta bude motar ta sauka tana goge idonta, shi ma ya sauka, yana gaba tana biye da shi suka shiga cikin gidan. Khaleesat na kwance da yamma ta shiga Hisnul Muslim dake wayar Jay sai ga kira ya shigo wayar, a hankali ta mike zaune tayi picking call din ta kai kunne tayi shiru, daga daya bangaren taji yace "Kin tashi?" Tace "Uhm" Yace "Kin yi sallah?" Tace "Nayi" yace "Ohk will you mind going out to the park with me?" Khaleesat tayi shiru, sai kuma a hankali tace "Ohk, thank you" Yace "You are welcome, i will be waiting for you at the parlor downstairs" Tace "Ohk" After almost 15 mins Khaleesat ta sauko downstairs cikin shiri, sosai kayan jikinta yayi mata kyau sai dai ta rame sosai, shi kadai ne zaune parlon yana jiranta, tun da suka hada ido ta sunkuyar da kanta, ya mike ya jira har ta iso parlon yana kallonta, a tare suka fita zuwa parking space din gidan ya bude mata motar, ta ɗan kallesa tayi murmushi tace "Thank you" Ya bude ido yace "No thanks" bayan ta shiga ya kulle motar sannan ya zaga ya shiga driver seat, one of the best park na state din ya kai ta and she love everything about the park, the view was so fascinating and breathe taking, she felt so refresh and relieve taji kamar bata da wani damuwa a lkcn, Jay ya siya masu Wraps da fresh lemonade, wannan karan bata ji kunyar cin abinci gabansa ba, lkci lkci yake daga kai ya kalleta, ita dai ta dinga kallon feral horses dake park din from a far distance, can ta kallesa tace "Su ba a hawansu ne?" Yayi murmushi ya girgiza mata kai yace "Ba a hawa" Tace "And nobody is controlling them?" Yace "Sort of, they are just on their own with no supervision, ko kina son in kai ki inda zaki hau doki ne?" Er dariya tayi ta girgiza masa kai kawai, ya ɗan kalleta, kana ganinta kasan tana cikin farin ciki a lokacin, ta kalli wraps dinsa da bai karasa ci ba tace "You are not eating?" Yace "Za ki ci ne?" Tayi murmushi tace "A'a, na koshi, kawai naga baka ci da yawa bane" Yace "Na ci abinci daxu ne, i am full" Ta kalli lemonade din gabansa tace "To in dauka?" Yace "A karo maki wani kenan?" Ta girgiza kai da sauri tace "Aa fa, i just don't want it to waste ne" Ya dauki sauran lemonade din nasa ya ajiye mata a gabanta yana kallonta, ta dau straw din ta fara shan lemonade din a hankali, dauke ido yayi daga kallonta, wayarsa ya fara ring yana dubawa yaga AJ ne ke kiransa, yayi picking ya kai kunne, ita dai Khaleesat kallonsa kawai take, after few seconds Jay yace "Ni sai next week probably, ban gama abinda nake ba, do not book with me" Ajiye wayar yayi bayan AJ ya katse, ya kalli Khaleesat yace "Zaki jira har next week mu tafi Nigeria, or you will leave before then?" Khaleesat tayi shiru at first, a hankali ta sauke idonta tace "Yanda kace" Yana murmushi yace "Ko zaki bi AJ, he is leaving soon, yanzu ma ticket zai yi booking" Ta daga manyan idanuwanta ta kallesa, sai kuma tace "He that dislikes me shi ne zan bi sa?" Jay yayi dariya yace "How will you say he dislikes you Halysaah? He dislikes you shi ne yaje har apartment dinki yayi rescuing dinki? Ke ce dai baki ganesa ba har yanzu, AJ is nice just that yana da son girma ne kuma baya son raini, which i understand him because that's our heritage, kinga ke ko gaishesa baki yi" Tana wasa da straw din lemonade din gabanta tace "To ai nasan ko na gaishesa bazai amsa ba, saboda na taɓa gaishesa bai amsa min ba" Jay dai yayi murmushi yace "In kin ci gaba da gaishesa ae zae amsa" Tace "Ur frnd doesn't like me at all, he prefer my frnd" Jay yace "Who told you he is my frnd? AJ is my cousin bro Halysaah" Khaleesat ta daga kai ta kallesa tace "Da gaske?" Yayi murmushi yace "Ba ma kama ne?" Khaleesat ta buda hannu tace "Ni ban wani san yanda fuskarsa yake ba ai, ban taɓa kallonsa sosai ba" Jay yayi dariya, a hankali yace "To cousin brother dina ne, His dad is my father's junior bro" Khaleesat tace "To amma dai ka girmesa ko?" Jay na murmushi yace "Not at all, just 3 months ne tsakaninmu, we will clock 34 next year" Khaleesat tace "Shi ne yace ya haifeni?" Jay bai san sanda yayi dariya ba sosai, sai kuma yace "Zolayarki fa yake, but how old are you?" Ta sauke idonta kasa kamar bazata ce komai ba, sai kuma a hankali tace "I am 20" Jay ya wara ido yace "Waw, you are still a Baby Halysaah" ta wani kallesa, yana murmushi yace "To ai in AJ mace ne kuma an masa auren wuri ya isa ya haifeki" Yana dariya ya kare maganar, Khaleesat dai taki cewa komai still playing with the straw in front of her, a hankali Jay yace "Are you angry?" Ta daga kai ta kallesa, sai kuma tayi murmushi ta girgiza masa kai still looking at him, Jay ya kwantar da murya yace "U misunderstood AJ, yana da kirki sosai, kuma yana da tausayi, just that he is a no nonsense kuma baya son raini, sannan truly yana da girman kai na sani, but that doesn't make him bad, kuma da kinsan wanene shi zaki san yana ma da saukin kai" Khaleesat ta karasa shan lemonade din gabanta taki ce ma Jay komai, Jay ya kalli agogon wrist dinsa yace "Let go for horseback riding before it gets late" Khaleesat ta zaro ido tace "A'a ni dai bazan hau doki ba" Yana murmushi yace "To mu je dai" Shi ya fara tashi sannan ita ma ta mike suna tafiya a tare, satan kallonsa tayi suka hada ido ya ciro wayarsa yace "Let's take some pictures with this beautiful view" A hankali tace "Ok" Tana tsaye kusa da shi yayi masu hoton da wayarsa, yana kallon hoton da yayi masu ya taɓa hancinsa yace "Ya naga hancinki yafi nawa tsayi, ya naga kamar kin fi ni kyau" duk lokaci daya ya jero tambayar yana sake kallon hoton da kyau, ita dai Khaleesat tayi murmushi tace "Uhm is that an irony?" Jay yayi dariya yace "I am serious Halysaah" Wata er Africa ce ta zo wucewa ya mika mata wayarsa politely yace ta masu hoto pls, yarinyar ta amshi wayar zata masu hoton, yanda Khaleesat taji ta uncomfortable kusa da shi, shi ma dai kamar hakan ne cause he left a little gap between them, yarinyar ta masu hotuna masu kyau kuwa, ita kanta yarinyar sai kallon hoton take kafin ta mika ma jay wayarsa tana kallon Khaleesat admiringly tana murmushi tace "You are so Beautiful" Khaleesat ta sauke idonta tace "Thank you" Yarinyar ta daga masu hannu ta bar wajen, bayan Jay yayi mata godiya, kallo daya yayi ma hotunan ya mayar da wayar cikin aljihunsa yace "Let go for horseback riding Housemate" Wani park din ya kai su daban da ake hawa doki, duk yanda yayi da Khaleesat ta hau doki bayan ya biya masu kudi taki wai ita bata iya ba tsoro take ji, daga karshe ta marairaice tace "Ni dai kawai ka bani wayarka in dinga maka video sai kai ka je ka hau" Yayi murmushi kawai ya mika mata wayarsa yace "To ai shikenan" Khaleesat was so impressed with his horse riding skills kamar irin dama ya saba din nan, sai murmushi take masa, mutanen wajen ma suna ta kallonsa, Khaleesat's eyes were glued to him all through, tana yi tana masa video, sai after 7 suka bar wajen, tana kallonsa kafin su shiga mota tace "Where did you learn to ride horse confidently?" Yayi dariya yace "Back home" Tana murmushi tace "To ka taɓa zuwa nan ne?" Jay yace "Tab ai nan wajen zuwan AJ ne, kawai dai of recent ne muka dena zuwa" Khaleesat tayi shiru bata ce komai ba, sai da ya fara biyawa African Restaurant ya siya mata abinci, ganin leda daya ya mika mata yace "This is for you" Tace "Kai fa?" Yace "No, i am taking tea and bread this night" A hankali tace "Ohk, thank you" Bayan sun isa gida yayi parking, ta juya tana kallonsa a hankali tace "Thank you so much, Allah ya saka maka da alkhairi, i appreciate you" Without looking at her yace "Amma nace ki dena min godiya ko Housemate?" Tayi shiru, ya bude motar ya sauka sannan ita ma ta sauka, yana gaba tana biye da shi har suka shiga gidan, AJay na zaune parlor yana shan fruit salad yana kallon kwallo, ya juya ya kalleta don shi bai ma san bata gidan ba, suna hada ido abinda Jay yace mata daxu ya fado mata, ta sunkuyar da kai, kamar munafuka tace masa "Good evening" AJ ya gyara zama yana kallonta yace "Kin saba gaisheni ne zaki ce min Good evening??" Khaleesat ta ɗan kalli Jay da ya karasa cikin parlon, Jay yace "Good night Halysaah, if you need anything you call my line" A hankali tace "Thank you" Daga haka ta wuce sama, Jay na kallon AJ yace "Ba don na mata magana ba kana tunanin zata gaisheka ne dama? Ni ne nan na saka ta, sai me kuma in baka amsa ba?" AJ yace "Zamana take a gidan da zata gaisheni" Jay dai yaki tanka masa. *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* [5/26, 9:45 AM] khaleesat Haiydar ✍️: Washegari Wednesday da yamma Jay na zaune parlon dake sama tare da AJ da ya maida parlon wajen kwanansa, don tun da Khaleesat ta kwana dakinsa tsakaninsa da dakin kawai ya shiga ya dau kaya, ko bandakin dake dakin baya shiga, Jay dake kallonsa yace "Yanzu dai zan iya dawowa dakinka kenan tunda ka tashi a dakin?" AJ yayi banza da shi yana ci gaba da hada few kayansa da yake yi a tsadadden box dinsa da zai yi tafiya gobe, Jay yace "To wai kayi booking flight din ne da naga kana hada akwati?" AJ yace "Bana son Airline din da na gani jiya, anjima zan siya Ticket din Turkish Airlines" Jay yace "How many hours connection time for the layover?" AJ yace "Baya wuce 2 to 3 hours, ko ma bazai kai haka ba" Jay yace "Will you mind travelling same plane with my Housemate? I just remembered I will be meeting my Mami at the UK, tare za mu koma Nigeria da ita daga can" AJ yace "Of course I will mind Jawwad, because my OCD will never allow me board the same plane with her, ga Airline kala-kala ka nemi wani ka siya mata ticket mana, what is my business with her da zaka hadani da ita sai kace ni na kawota America, there is this Airline na mance sunansa Economy class ticket dinsu naga is just 600 dollars, you can get her the ticket as the Good Samaritan that you are" Mikewa Jay yayi bai ce masa komai ba ya bar parlon. Wajen karfe biyar da rabi Jay ya kwankwasa ma Khaleesat kofa, bayan ta bude yace "Ba abinda zaki dauka a can apartment din da zaki koma da shi Nigeria Housemate?" Khaleesat tace "Ohk, zan dau wasu kayan" Yace "To ki shirya sai in kai ki can ki dauka" Khaleesat na kallonsa a hankali tace "Pls kar kace zaka siya min ticket ina da kudi a account dina, i will get the ticket" Yayi murmushi yana kallonta yace "To Hajiya me kudi, kudin zai isa ki mana booking har ni da AJ?" Tana murmushi ta fara wasa da gefen gyalenta tace "Sae dai kai kadai, ni ai ban san wani AJ ba" Akan kunnen AJ da ya taho daga parlor zai sauka downstairs, ya tsaya yana kallonta babu fara'a, Jay ya juya ya kallesa yana murmushi yace "Je ki shirya ina jiranki downstairs Halysaah" Juyawa tayi ta tura kofar dakin a hankali, ko da Khaleesat ta sauko downstairs ta tarar da Jay yana jiranta, and it's almost 6pm, ya mike suka fita daga parlon, bayan sun bar compound din a motarsa ya ɗan kalleta yace "Kinga kin kara tsokanar AJ ko?" Ta marairaice tace "To ni ai ban san yana wajen ba, why is he always eavesdropping?" Jay yayi dariya yace "Ni dai ba ruwana" Ita dai tayi shiru bata ce komai ba, she can't even wait ta dena ganin AJ she is already exhausted with him and his problem, she can't wait to stop seeing him, suna isa apartment dinta abinda ya faru ya dawo mata fresh, kawai sai take ganin kamar trauma din ya dawo mata sabo a kwakwalwarta, lkci daya duk jikinta ya mutu, haka dai jikinta ba kwari ta tafi dakinta ta fara hada kayan da zata hada shi kuma Jay ta bar sa parlor yana jiranta, sau uku Safiyya na zuwa gidan debo mata kayanta kwanaki kuma duk Housemate dinta ne ke kawota, after a while Khaleesat ta gama daukan abubuwan da zata dauka a akwatinta, sauran kayan dakin duk ta haɗa su waje daya, ko zata dawo kasar ko bazata dawo ba ita dai bata sani ba, ta kuma bar ma Allah komai, ta gama tidying ko ina a dakin sannan ta fito wajen karfe shidda tana jan akwatinta a hankali zuwa parlor, kwance taga Housemate dinta kan doguwar kujera ya fara bacci, ta tsaya tana kallonsa, sai kuma ta tafi kusa da kujeran still looking at him ta ɗan tapping din jikin kujeran gently, a hankali ya bude ido sai kuma ya mike zaune yace "Kin gama ne?" Tace "Are you sleeping?" Yace "A'a, kawai na kwanta ne ina wani tunani, it's even time for magrib bari inyi sallah, kema kije kiyi" Bandakin dake parlor ya shiga ita kuma ta koma dakinta, sai bayan wani minti sha biyar din suka bar gidan, tunda suka fito gidan Khaleesat tayi shiru, shi ma kuma bai ce komai ba, amma ya lura mood dinta ya canza, kawai ya sa a rai bazai tafi da ita gida a haka ba, after a while ya ɗan kalleta yace "Would you mind watching a movie in Cinema tonight?" Khaleesat ta juya ta kallesa, sai kuma ta sauke idonta bata ce komai ba, yace "Ko baki kallo?" Tace "Ina yi, amma ba sosai ba" Yace "To yau za ki yi" Waje ya samu yayi parking, ya dau wayarsa ya shiga website din Cinema din dake Maryland to check their schedules for that day, yayi selecting movie din da za su kalla, da lokacin da za su kalla sannan ya siya masu ticket aka turo masa ta online, ita dai Khaleesat kallonsa kawai take, yana daga kai tayi saurin dauke idonta daga kallonsa, ya ci gaba da driving dinsa, without looking at her yace "I hope you will enjoy the movie" Ita dai bata ce komai ba har suka isa Cinema din, ya siya masu popcorn and lemonade, sannan suka nufi cikin Auditorium din da za a haska film din da ya siya masu ticket, in some minutes kuma za a fara haska film din, wannan ne zuwan Khaleesat Cinema na farko a rayuwarta duk da a baya babu irin takuratan da Safiyyah bata yi akan su je tare da frnds din Safiyyar amma ita dai bata yarda taje, suna shiga Jay ya fara cin popcorn dinsa kamar abinda ya kawosa kenan, ita dai Khaleesat dama bata wani damu da popcorn ba hakan yasa take ɗan ci jifa jifa tana kallon film da ake, she is beginning to like the film hakan ya sa ta tattara gaba daya hankalinta kan film din, after almost 35 mins da fara film din ta juya ta kalli Jay taga bacci yake, ta dade abu bai bata dariya haka ba, she couldn't believe he is seriously sleeping abun sa, ta rufe fuskarta da hannunta tana dariya a hankali, she don't know why she feel relieve a duk sanda take tare da shi, there is never a boring moment with him, gently ta kai hannu kusa da shi ta dauki popcorn dinsa daya, he was still sleeping ta dinga kallonsa maimakon film din da ya kawota ta kalla, idan yana bacci komawa yake so gentle and calm, a nan ne kuma ainahin handsomeness dinsa ke fitowa, if there is the sleeping princess then he will be the sleeping prince, har awa daya da fara film din Jay baccinsa yake kuma ta kyalesa bata tashesa ba, she watched the movie har sai da ya kusa karewa and she really enjoyed every bit of it, ta juya ta kallesa sai kuma ta dau popcorn daya ta matsa dai dai kusa da shi a hankali ta saka masa a baki, da sauri ta gyara zamanta ta maida hankalinta kan movie, ya bude ido, taji yace "What a nice movie" Sai a sannan dariya ya taho mata ta juya ta kallesa tace "Ain't you ashame of saying this?" Yana gyara zama yace "You don't like the movie? But it's nice, i like it" Tana murmushi tace "To in ka gama baccin ka tashi mu tafi, ni na gama kallona" Ya ɗan shafa kai trying not to smile yace "Wa yace maki bacci nake, i was only meditating duk nasan abinda ake yi ai, ba gashi an kusa gamawa ba" Ita dai murmushi kawai take tace "Naji, tashi mu tafi, a hanya sai ka bani labarin film din don akwai inda ban gane ba" Yayi shiru yaki cewa komai, tana danne dariyarta ta tashi ta dau sauran popcorn dinta da nasa, tashi yayi ya bi bayanta suka fita daga Auditorium din, lokaci lokaci take juyawa ta kallesa don ta tabbatar he is not walking and sleeping at the same time, da sauri ya jawota ta fado jikinsa bayan tayi missing step saboda waige waigen sa da take sai kuma yayi saurin saketa, within few seconds aka yi hakan, ta rufe bakinta da hannu don ba karamin tsorata tayi ba, yace "Yanzu da kin fadi kika fara min kuka kilan har mu kai gida" Ta marairaice tana kallonsa, Softly yace "Alright Sorry Halysaah" Ta juya ta fara tafiya a hankali, a haka suka fita daga cinema din bata sake waigen bayanta ba, yana biye da ita yana kallonta har suka isa gun da yayi parking. Wajen karfe goma suka isa gida bayan yayi parking ta juya ta kallesa a hankali tace "Thank you so much" Ya mata murmushi yace "You are welcome House mate" A haka suka sauka daga motar tana biye da shi suka shiga gidan, kafin ta shiga daki yace "Get me ur travelling documents" Ta kallesa zata yi magana ya daura fingers dinsa biyu a lips dinsa, ta sauke idonta sannan ta juya a hankali ta shiga cikin dakin, after some minutes ta fito ta mika masa, ya amsa yace "Good job, zan tura maki ticket din ta Email dina, sai da safe" A hankali tace "Allah ya tashe mu lafiya" Juyawa tayi ta koma cikin dakin ta kulle kofar, Jay ya tafi parlon sama yaga AJ kwance kan Couch yayi bacci, shi dariya ma yake basa, kawai mutum ya dora ma kansa wahala, juyawa yayi ya wuce dakinsa, wajen karfe sha biyun dare Khaleesat na ta juye juye ta kasa bacci ita kanta ta rasa dalili, message taji ya shigowa wayar Jay dake wajenta ta mike zaune ta jawo wayar tana duba message din taga Email ne ya shigo, tana bude Email din taga ticket din ya turo mata na Turkish Airline, kuma Business class seat, bata san me yasa taji hawaye ya cika idonta ba, ta ajiye wayar a hankali ta koma ta kwanta. *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* [5/26, 9:47 AM] khaleesat Haiydar ✍️: Khaleesat na zaune gefen gado tana kallon Jay dake kulle mata akwatunan ta, yana dagowa ta juya a hankali tana kallon window dake dakin, ya dau boxes din biyu yace "Let me get them in the car" Daga haka ya fita daga dakin, ta jinginar da kanta jikin gadon dakin har ya dawo, yana kallonta yace "Hope you didn't forget anything Halysaah" Ta gyada masa kai, yace "Ok, you know what? in dai muka fita kika hadu da AJ thank him and tell him you are leaving" With a smile on his face ya kare maganar yana kallonta, ta sauke idonta tana wasa da fingers dinta a hankali tace "Ohk" Yace "Good gal, mu tafi" Mikewa tayi ta bi bayansa tana rike da karamin handbag dinta walking slowly, suna fitowa walk way din babban corridor din sama sai ga AJ ya taho daga parlorn dake nan sama, Jay ya kalli kayan jikinsa ganin iri daya suka sa kuma tun safe ba wai sun hadu bane kawai coincidence, tunda AJ ya kallesu sau daya ya ci gaba da tafiyarsa, Khaleesat ta ɗan kalli Jay, ya gyada mata kai sannan ya nufi stairs, ita dai tana tsaye ta jira har AJ ya iso kusa da inda take sannan ta sauke idonta a hankali tace "Good morning, i want to thank and appreciate you for everything, i will be leaving today in sha Allah" Without looking at her yace "Jay dai zaki ma godiya ni me na maki" Ta bi sa da kallo har ya fara sauka downstairs, sai bayan da ya sauka sannan ta tabe baki ta bi bayansa tana tafiya a hankali, parlor ta tarar da Jay zaune yana jiranta, Jay ya bi AJ da kallo yace "Flight din naka na gobe ne amma?" AJ yace "I am leaving for the airport now" Jay yace "Ohk, zaka jira inyi dropping Housemate dina sai in dawo in kai ka airport din?" AJ yace "No, don't bother" Daga haka ya fita daga parlon tare da daya daga workers din gidan wanda da alama shi zai yi dropping dinsa airport din, Jay ya daga kai ya kalli Khaleesat, ya lura tunda gari ya waye jikinta yake a sanyaye, yana kallonta yace "Are you Okay Halysaah?" Ɗan murmushi tayi tace "Sure" yace "Kin gaya ma kawarki yau zaki tafi?" Khaleesat ta gyada masa kai tace "Na gaya mata" Yace "Ok, ita yaushe zata tafi?" Khaleesat tace "Yayanta yace ta bari ranan lahadi" Jay yace "Kin tabbatar baki mance komai ba kuwa a sama?" Ta gyada masa kai, yace "Je dai ki sake dubawa Housemate" Bata masa musu ba ta juya zata koma sama yace "Toh ki ajiye jakar taki mana" Ta dawo ta ajiye jakarta a kan kujera sannan ta wuce sama, Mikewa Jay yayi ya tafi gun jakar ya dauka ya bude sannan ya ciro Dala dubu daya a aljihunsa ya sa mata a jakar ya kulle ya mayar ya ajiye mata ya koma ya zauna, ba a dau lokaci ba Khaleesat ta dawo downstairs tace "Ban manta komai ba" Yace "Good" Mikewa yayi bayan yaji fitar motar AJ don dama jira yake yaji sun fita daga gidan, yana kallonta yace "Mu je, ur Flight is in an hour time in sha Allah" Khaleesat ta gyada masa kai ta dau handbag dinta, tana biye da shi suka fita daga parlon gidan, har gari ya fara duhu, suna shiga motarsa ta mika masa wayarsa dake hannunta kar ta manta, a hankali tace "Thank you so much" Ya amshi wayar sannan ya dauko pin a motar ya cire sim card din cikin wayar snn ya mayar mata yace "Your ticket is on the phone, in kin koma Nigeria sai kiyi SIM card replacement, in kuma baki son wayar sai in sa a kai maki sabo a Nigeria" Tayi murmushin karfin hali tace "Saboda me zance bana so, nagode sosai, Allah ya saka da alkhairi" Yace "To ai nasan ku mata da son sabon abu" Ta girgiza masa kai kawai tana murmushi bata ce komai ba, a haka suka bar gidan suka dau hanyar airport da tunani iri iri a ran Khaleesat, ko baccin kirki bata yi ba daren jiya ga wani daren, ko me zata je ta tarar a Nigeria sai Allah, it's now that reality is dawning on her, bayan sun isa airport Jay ya juya ya kalleta yace "You can sort ur self out ba sai na shiga ciki ba ai ko?" Ta gyada masa kai, da kyar tayi karfin halin cewa "Thank you so much Housemate, Allah ya saka da alkhairi da abubuwan da ka min" Kasa ci gaba tayi saboda hawayen da ya fara sauka a idonta she just can't thank him enough, gani take words aren't enough to thank him, shi dai Jay kallonta kawai yake with surprise, can yace "C'mon Halysaah, to menene abun kuka?" Ta kasa basa amsa ta rufe fuskarta da gyalenta tana kuka a hankali, Jay ya kwantar da murya yace "Pls ki dena wannan kukan, in nasan abinda zaki yi kenan i will have just order either Lfyt or an Uber that will be taking you to the airport" Dena kukan tayi tana goge hawayen da yaki tsaya mata tana kallonsa, ya bude motar ya sauka ta bi sa da ido taga Luggages dinta dake booth zai dauko, a hankali ta bude side dinta ta sauka daga motar tana bin sa da kallo, daya daga porters dake wajen ya ba luggages din nata ya shigar mata da shi ciki ya hada masa da tip dinsa, ita dai Khaleesat kallonsa take, ya juya ya dawo kusa da ita yace "Alright safe trip Halysaah, idan kinyi replacing Sim card dinki sai ki min magana ta WhatsApp, my regards to everyone back home" Ta sauke idonta a hankali tace "I will miss you" sai bayan da ta fada haka ita kanta tayi realizing abinda ta fada, sai kuma ta kasa dago kanta, ya ɗan yi murmushi yace "I will miss you too Housemate, in sha Allah next week i will be in Nigeria too" Bata iya ta kallesa ba ta gyada masa kai kawai ta juya a hankali ta bi bayan porter din da ya shigar mata da luggages dinta zuwa check in counter for her Boarding pass, kasancewar Business class ticket gareta all the processes were smooth and straight for her, daga karshe ta nufi waiting lounge don in 15 mins time za su fara boarding jirgi, tunda ta shiga lounge din take kallon wanda ta gani zaune da mamaki, ta kalli boarding pass dinta sannan ta kalli na hannunsa taga iri daya, wayarsa kawai yake dannawa, ganin bai ganta ba ta juya a hankali ta koma wani wajen daban ta zauna ta inda ma bazai ganta ba, bata sake waigen inda yake ba, iya drink kawai ta amsa a lounge din unlike wasu da ke ta cin abinci duk a cikin kudinsu, gaba daya ta nemi appetite dinta ta rasa saboda damuwa, da ta tuna inda zata sae taji har wani juya mata kanta yake kamar bata da lafiya, ta saƙa wancen a ranta ta kwance har daga karshe aka fara boarding din jirgi, sai da Khaleesat ta jira AJ ya fara tafiya sannan ta mike ta bi bayansa walking slowly, Har seat dinta wata Flight Attendance da ke welcoming dinta da fara'a ta kai ta, hada ido Khaleesat tayi da AJ that was sitting few seats away from hers, ta sunkuyar da kanta ta zauna Seat dinta tana mayar da Amenity kit din da aka ajiye mata a gefe, AJ ya kasa daina kallonta fuskarsa babu yabo babu fallasa, he can't even explain what he is feeling at that moment don bai taɓa ganin wanda ya gama rena masa wayo a duniyar nan kamar Jay ba, jiya wajen karfe sha biyun dare ya farka ya gansa yana duba masa waya ashe ticket din da ya siya yake dubawa, he felt like just leaving the plane at that moment, after a while kawai ya dauke kai yana kara gyara barrier din da zai sa ko hangota bazai dinga yi ba, Ita ma Khaleesat ko by mistake bata sake kallon direction din sa ba, a haka jirgin ya tashi, Khaleesat bata taɓa jin motion sickness ba tun da ta fara tafiya a jirgi amma yau ko don saboda pressure din da ta saka ma ranta ne kawai sai ji tayi as if she wants to throw up tun da jirgin ya daga, ta cire seat belt dinta da sauri ta mike ta nufi Lavatory din jirgin almost running, shi dai ya bi ta da kallo, Flight Attendance din da ta kawo mata Hot towel kafin tashin jirgin ne ta bi bayanta tana tambayar if she's okay, Khaleesat ta gyada mata kai kawai bayan ta fito daga Lavatory din, AJ ya bi ta da kallo har ta koma seat dinta ta zauna sannan ya tabe baki, Flight Attendance din ta duka kusa da ita tana tambayarta ko tana bukatar wani abu ne, Khaleesat ta girgiza kai tana murmushin karfin hali tace "Thank you, i am okay" Matar ta sake tafiya sai ga ta ta dawo da ruwa da orange drink, sai kuma wani drink daban duk a glass daban daban akan tray daya, ta duka tana mika ma Khaleesat ta dauki wanda take so, glass din ruwa kawai Khaleesat ta dauka ta mata godiya sannan ta sanar mata bazata ci abinci ba all throughout the flight don ma kar matar ta sake dawo mata, gani take tana cin abu zata yi aman da bata yi ba daxu, gyara kujeranta tayi ta kwanta ta lulluba da blanket din da jirgin yayi providing for business class passengers, nan da nan bacci ya dauketa, da za su sauka Turkey wajen karfe hudun asuba sai da wata Flight Attendance daban ta zo ta tasheta ta sanar mata jirgi zai sauka, Khaleesat ta mike zaune da kyar don ciwo kanta ke mata, tayi fastening seat belt dinta, bayan sun sauka Istanbul ta bi AJ da kallo har sai da ta daina hangosa sannan ta mike ta dau handbag dinta da waya ta bi bayansa tana tafiya da kyar leaving her Amenity kit behind, jiran awa biyu za su yi a Business Class waiting lounge na airport din kafin a canza masu jirgin da zai kai su Nigeria, ta riga AJ shigowa lounge din kilan masallaci ya tafi, ita ma tana ganin lokacin sallahn asuba yayi ta tafi tayi sannan ta dawo ta zauna a business lounge din, after like 15 mins sai gashi ya shigo, not far away from her ya zauna da ruwan gora a hannunsa, Ita dai ta jinginar da kanta jikin kujeran da take zaune ta daura handbag dinta a kafarta, she is having a terrible headache a lokacin, after almost 30 mins of sitting wani ɗan Nigeria ya dawo kusa da ita ya zauna, wanda shi ma daga nan Turkey zai je Nigeria a Business class, kuma jirginsu daya kamar yanda ta ga ticket irin wanda ta amsa bayan sun sauka Istanbul din a hannunsa shima, yana kallonta yayi mata sallama cikin nutsuwa, ta ɗan kallesa sannan ta amsa, yace "Guess you are coming from America right?" Tace "Uhm" Yana kallon Flight ticket dinta yace "Oops you are having the same name as my Mum, can i call you Jiddah instead of the real name?" Khaleesat dake sauraronsa without looking at him tace "Ohk" Yana murmushi yace "Alright, are you traveling alone Jiddah?" Ta girgiza kai tace "No" Ya buda ido yace "Ohk with who?" Ta kalli direction din AJ, shi ma mutumin ya kallesa suka hada ido don kallonsu kawai Ajayn yake yana jin conversation dinsu, mutumin na murmushi ya tashi yaje ya gaisa da AJ sannan ya koma ya zauna, shikenan Khaleesat ta samu lafiya, don bai sake ce mata komai ba kawai danna wayarsa yake tayi tunda shi dai bai san ko waye Ajayn a gunta ba, daga karshe ma ya tashi ya bar wajen, at last aka fara boarding din jirgin da zai kai su Lagos Nigeria daga Istanbul, Usman ya juya ya kalli Khaleesat da ta mike tana rike da handbag dinta, har AJ ya wucesu sai kuma ya tsaya amma bai juyo ba, ita dai tana tafiya a hankali har ta isa inda yake tsaye sannan ya ci gaba da tafiya tana biye da shi, har jirgi ya tashi Usman dake zaune not far from Khaleesat but close to AJ bai ce mata komai ba, this time around ma dai bacci kawai tayi har zuwa Nigeria. Karfe hudu saura suka sauka Nigeria washegari Friday, ita dai Khaleesat tun da ta ganta Lagos bayan ta gama da Custom da Immigration ta fara tunanin kuma yanda zata yi, to ko dai kawai ta tafi gidan Aunty Farida tunda a nan Lagos take, to ko tace zata je bata da sim din da zata kirata don ba gane anguwan zata yi ba kuma bata da lambarta a kai balle ko waya ne ta ara ta kirata a airport din, sai kuma tayi tunanin kiran Ummanta tunda tana da numberta a kai sai tace ta turo mata number Aunty Farida, gun wata mata warce taga kamar Bahaushiya ce ta nufa, ta gaisheta sannan tace "Don Allah Aunty wayarki zaki ara min in ɗan yi kira nawa ba caji" Matar ta fara kallonta daga sama har kasa, sai kuma ta bude handbag dinta ta ciro wayarta ta mika mata, Khaleesat ta amsa tace "Nagode" Dialing number Umma tayi ta kira taji a kashe, sosai jikinta yayi sanyi, ta kira har sau uku duk ana ce mata a kashe, a hankali ta zame wayar a kunnenta ta mika ma matar tace "Nagode, wayar ma a kashe yake" sai da matar tayi dialing wayar ta tabbatar eh a kashe din yake, kana ganin matar kasan she is not comfortable giving off her phone, Khaleesat na jan trolley dinta a hankali ta fito daga cikin airport din tana tunanin yanda zata yi, ko dai kawai ta tafi tashan da zata samu mota zuwa kano, since she have some money in her bank account, wani mutumi ne taga ya nufota, ya gaisheta da ladabi yana mata barka da zuwa, sannan ya nuna mata mota yace "Ke mu ke jira ki fito dama" She was looking at him with confusion, can ta kalli motar, shi ko har ya amshi Akwatunanta yayi booth din mota da su, sannan ya dawo ya bude mata back seat, zata yi magana sai ta hango AJ zaune front seat din motar, ta ɗan yi jim, sai kuma ta fasa cewa komai, ta tafi ta shiga motar, hotel drivern ya kai su kasancewar next available flight to lagos na karfe bakwai na magrib ne, dakin da aka biya mata na downstairs, shi kuma AJ sama taga ya tafi, All this while kuma bai ce mata komai ba, ita dai tana son ce masa ta gode amma bai bar space din hakan ba, ko tsayawa bai yi ba balle tayi godiyan, sai da driver din ya amshi passport din ta da zai mata booking din jirgi tare da AJ zuwa kano sannan ya bar hotel din, bayan Khaleesat ta shiga dakin babu dadewa aka kawo mata lafiyayyen lunch, duk da tana jin yunwa bata iya ta ci da yawa ba she is just restless, taje bandaki ta wanke baki tayi wanka ta dauro alwala ta fito, bayan ta saka wasu kayan tayi sallah sannan ta dau handbag ta bude zata ciro lip gloss dinta, a nan taga kudin da Jay ya saka mata, ta dinga kallon kudin ko kiftawa bata yi a sanyaye. Karfe shidda da yan mintuna drivern ya sake zuwa ya daukesu ya maida su airport, daga nan kuma suka hau jirgi zuwa garin kano, inda suka sauka airport din Aminu kano karfe tara saura na dare, this time around ma sai da drivern da ya zo daukan AJ ya sauka yayi mata magana tare da kai akwatunanta booth, ita dai tana ta tsaye don taxi kawai ta so dauka da zai kai ta gida, ganin drivern ya bude mata back seat ta karasa jiki a sanyaye ta shiga motar, sai da suka fita daga Airport din drivern ya kalleta ta madubi yace "Ranki shi dade wani anguwan za a ajiye ki?" Khaleesat ta ɗan kalli AJ dake zaune gaban motar yana danna wayarsa, sai kuma ta kalli drivern tace "Inda zan je da nisa, kar in bata maku lokaci gashi dare yayi, duk inda ka samu kawai ka ajiye ni zan samu abun hawa" Sai a sannan AJ yace "Ce maki yayi sauri yake?" Khaleesat tayi shiru, sai kuma tace "Ni Mariri zan je" Driver yace "Toh Allah ya kai mu lafiya Hajiya" Bayan tafiyar kusan minti arba'in suka iso Maririn, A hankali Khaleesat dake kallon drivern tace "Zan iya sauka a nan sai in karasa cikin layin saboda kar ku shiga baku samu wajen juyawa ba...." Drivern yace "Layin baya bulla ne? In dai yana bulla babu damuwa za mu samu hanya in sha Allah" Tace "Toh shikenan, nagode" Nan ta nuna masa inda zai bi ya shiga unguwan, shi dai AJ kallon ikon Allah kawai yake without uttering a word, haka jama'an anguwan suka dinga bin motar da ya dalle ko ina da haske da kallo, ba ko wani mai mota bane zai yarda ya shiga hanyar nan da motarsa cause driving is uncomfortable there in baka yi hankali ba sai ka goge motarka, gashi gidan nasu can ciki ciki ne, at last dai tace "Kawai in ka samu waje a nan zan sauka, ga gidan can" Drivern yace "Toh shikenan Hajiya" Haka ya samu yayi parking motar, sannan ya sauka zai dauko mata akwatunanta a bayan booth, ta bude motar ta sauka tana kallon kofar gidansu hankalinta ya ɗan kwanta ganin bata ga Babanta a kofar gidan ba, kan kace me yara yaran anguwan da suka ga ita ce a motar suka taho da gudu ana mata oyoyo, haka dai ta samu ta hadasu da akwatunanta sannan ta zaga zuwa side din da Ajay yake, tana wasa da gefen gyalenta ta kasa kallonsa tace "Thank you so much Allah ya saka da alkhairi" yace "Wanda ya hada ki jirgi daya da ni zaki ma godiya, Jay kenan" Sai a sannan ta ɗan kallesa, bata dai ce komai ba ta juya tana tafiya a hankali ta bar wajen, godiya tayi ma drivern ta masa kwatancen unguwan da zai shiga wanda a nan zai samu hanyar billa zuwa titi, yayi mata godiya shima ya shiga mota sannan ta nufi cikin gidansu gabanta na faduwa, a hankali tayi raising sack din cement that was use as barrier between the door and inside of the house zata shiga cikin gidan ta ci karo da kanninta da suka fito yi mata oyoyo da gudu bayan yara sun shiga da akwatunan ta, a haka suka shiga cikin gidan tare tana Rungume da su, zazzaune taga kishiyoyin ummanta biyu da 'ya yansu rakacaa a tsakar gidan har a lkcn ba a sauke tuwon dare ba gashi ana neman karfe goma, kananun yaransu ne kawai suka taso yi mata oyoyo da gudu, muryar wata makociyarsu dake zaune cikin gidan taji tana cewa "Ikon Allah sannu da zuwa Amarya ashe dai kina hanya dama" Khaleesat dai kallonta kawai take jin abinda tace, taji kishiyoyin ummanta na cewa "Ai ko dai, kinga mu da muke gidan ma ko gaya mana ba ayi ba balle mu shiga mu fita tahowar nata ya fasu, kinsan haka aka maida mu a gidan, to ga dai ta mun ganta kamar an jefota, mun kuma yi murna" Khaleesat ta gaishesu without waiting for response ta shige dakin Ummanta, zaune ta ganta a bakin kofa Umma dake kallonta cike da damuwa tace "Khaleesat me ya samu wayarki kusan wata daya? Dama kina hanya shine Abdul din bai gaya mana ba?" Khaleesat ta rungumeta a hankali tace "Umma lalacewa wayar yayi" Umma ta dago kanta tana kallonta tace "To shi ya dauko ki a tashar jirgin?" Khaleesat ta sauke idonta tace "A'a" Muryar kawar Ummanta da taji a dakin yasa ta daga kai don bata ma san tana ciki ba, Khaleesat ta gaisheta da murmushi, Mama Salame ta amsa da fara'a tace "Ashe dai kina hanya amarya" Khaleesat tace "Amarya kuma Mama?" Mama Salame tace "Au shi Awdul din bai gaya maki ba dama, ai yau ana saukowa sallan juma'a aka daura auran ku" *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* [5/26, 9:48 AM] khaleesat Haiydar ✍️: Khaleesat ta kwala wani karan da ya gigita Ummanta da Mama Salame, Umma ta mike da sauri tana kallonta a kidime, haka ma Mama Salame da tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, menene haka Khaleesah?" kishiyoyin Umma duk suka yo dakin a guje su ma don Khaleesat bata fasa ihun da take kwalawa ba cikin tashin hankali take cewa "Wallahi bana son shi bazan iya zaman aure da shi ba, na shiga uku na lalace, don Allah Umma ku min rai ku rufa min asiri, wallahi bana son sa" Umma dai sake baki tayi tana kallon Khaleesat tashin hankali karara a fuskarta gashi ta kasa cewa komai, daya daga kishiyoyin Umma da ake kira Mama Shatu tana gyara zaninta da ya kusa kwancewa saboda gudun da suka yi tace "Ji wani gulma da kinibibi? Shi Abdul din ne da ya daukeki ya kai ki kasan turai karatu yayi ta kashe kudadensa ne baki so yau? A ajiye batun ubanki a gefe, ke abinda ya kashe maki yau ko kaf kasar da uwarki ta baro za a siyar za a iya biyansa aka ce maki?" Ita ma daya Co-wive din da suke kira Mama Zubaida tace "A'a rainin wayo mana Shatu, gwara ai a rena mana hankali, don uwarta kasuwa ne nan da zata cika mana gida da ƙuwa, wannan ai iskanci ne da walakanci" Khaleesat bata fasa kuka da ihun da take a dakin Ummanta ba tana surutai ita kanta bata san takamaiman abinda take cewa ba tsabar tashin hankali, Kanninta Noor da Islam kuwa har sun fara kuka su ma a dakin, kan kace me har makota sun fara tururuwan shigowa gidan, aka tsaya cirko cirko bakin kofar dakin Ummanta ana salallami, Mahaifinta ne Malam Ali ya shigo gidan yana zazzare ido, shi ma ya karaso da sauri yana tambayar abinda ke faruwa a gidan, Mama Shatu ta tabe baki tace "Wai er da ta fi kowa ce ta sauka yau daga Amurka shine uwar ke sanar mata ai an daura aurensu da shi wanda ya kai ta waje karatu har ta dena ganin kowa da gashi, shine fa ta cika anguwa da ihu da koke koke wai ita bata son auren bazata zauna da shi ba, ga jama'a na ta shigowa an zata gobara muke, wannan ai tsabar sangarci da iya shege ne" Juyawa Malam Ali yayi ya nufi gun da ake ajiye itacen girki da sauri ya suri daya ya dawo ya nufo dakin Umma yana cewa "Ina take..." Matan makota dake tsakar gidan suka hau basa hakuri suna don Allah ya kyaleta, yaki sauraron kowa yana zazzare ido, Khaleesat na hangosa ta tafi bayan Ummanta da gudu tana kuka ta rungumeta, kanninta ma suka yi bayan Umma gaba daya suna kuka, Mama Salame ta tsaya tayi bake bake gabansa tace "Haba haba, haba Malam Ali, meye haka kake kokarin yi?" Yace "Salame ki bar ni dai inci malfar ubanta a wajen, mu zata tona ma asiri? Ni zata ja ma sabon bala'i da fitinan da ya girmeni?" Mama Salame tace "A'a wallahi baza ka doketa da wannan rafkeken icen ba ita ba jaka ba, mu je waje Malam Ali" Ita dai Umma kanta na kasa bata ce komai ba, haka Mama Salame ta samu ta tasa keyarsa ya fita daga dakin tana biye da shi, Mama Zubaida ta rike haɓa tace "Ikon Allah, mu muke ganin kinibibi iri iri a gidan nan, to in aka bibiya wani ta kyallara ido ta gani a Amurkan shine zata tona ma uban asirinsa da ke rufe, da can menene yasa ta hakura zata aurensa? Sai ranan da aka daura aure ta nemi tara mana mutan anguwa tace bata san zance ba? Yau ni nake ganin iskanci, to ta tsotsi nonon buzuwa ba dole ta iya makirci da kissa ba" Ita dai Khaleesat kuka kawai take a jikin Ummanta siblings dinta na kusa da ita suna taya ta, Mama Salame ta sake labulen dakin Umma duk don matan dake tsaye bakin kofar su kama gabansu, Umma ta juya tana kallon Khaleesat gaba daya ta kasa cewa komai, zamewa kasa Khaleesat tayi ta hade kanta da gwiwa tana kuka kamar ranta zai fita tana cewa "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, na shiga uku na lalace" a sanyaye Umma ta tafi gefen katifar dakin ta zauna ta kasa cewa komai. Karfe biyun dare Umma na zaune kan darduma da carbi a hannunta, Khaleesat ta tsallake kanninta ta fito daga cikin net din da take kwance bayan ta tuna ko isha'i bata yi ba, tunda Mama Salame ta daura mata net tace ta shiga ta kwanta wajen karfe sha daya take kwance duk da ba bacci take ba, don ko bacci barawo bata gani ba, amma tayi shiru cikin net din tunani iri iri na yawo a kanta, gaba daya ta ji kamar hawayenta ma ya kafe, har a lkcn babu maganar da ya hadata da Ummanta, tana jin jiri da zazzabi ta nufi kofa zata fita ta dauro alwala, Umma dai ta bi ta da kallo, bayan ta dauro alwalan ta dawo ta saka hijab dinta ta tada sallah, bayan ta idar tayi nafila raka'a biyu, tana zaune kan darduman ta jingina da bango tayi nisa tunanin da take, gani take kamar a mafarki ake sanar mata an daura mata aure da Abdul amma ta ki farkawa daga mummunan baccin nan har yanzu, muryar Ummanta yaji ta kirata a hankali, Khaleesat ta juya ta kalleta amma ta kasa amsawa, Umma ta mike ta koma kusa da ita ta zauna tana kallonta, cikin sanyin murya tace "Me ya faru kuma tsakaninki da Abdul din Khaleesat? Wani abun ya kara maki? Me yasa kika ce baki son auren?" Khaleesat ta fashe da kuka a hankali tace "Umma wallahi bana son sa, bazan iya zama da shi ba, in aka ce za a kai ni gidansa zan iya mutuwa wallahi, don Allah Umma ku taimakeni ku yi min rai" Umma ta kasa ce mata komai hawaye ya cika idonta ta fara gogewa da hijab dinta, Khaleesat ta daura kanta kan kafadar Ummanta tana kuka me tsuma zuciya tace "Don Allah ku taimakeni Umma, bazan iya ba wallahi" Umma ta rungumeta tana patting bayanta ita ma hawayen na sauka idonta amma bata iya ta ce mata komai ba, they sat there for almost 40 mins, jin tana sauke numfashi a hankali Umma ta gane bacci tayi, a haka Umma ta zauna wajen Khaleesat na jikinta don bata son tashinta har kusan lokacin sallahn asuba. Da safe wajen karfe tara Umma ta shigo dakinta rike da cup din kunu da kosai a roba, ta karasa kusa da Khaleesat dake kwance gefen katifarta ta ajiye mata sannan ta zauna cikin kwantar da murya tace "Ta so ki ci ko kadan ne Khaleesat" Khaleesat dai kallon cup din kunun kawai take, lkci daya hawaye ya cika idonta, Umma dai ta sunkuyar da kai, Islam ce ta shigo dakin rike da paracetamol da Umma ta aiketa ta siyo ma yayar tata, ta zauna kusa da Umma tace "Umma ga maganin na siyo ma Aunty" Umma ta amsa ta ajiye a gefenta tace "Tashi ki je ki karasa min aikin da na sa ki" Islam dake kallon Khaleesat ta mike a hankali ta fita daga dakin, Umma ta maida dubanta kan Khaleesat tace "So kike ki sa ma kanki wani ciwon ne Khaleesat nima ki sa min damuwa? Ki tashi ko kunun ne ki sha" Khaleesat ta girgiza mata kai cikin rawan murya tace "Ni bazan iya sha ba Umma" a sanyaye Umma tace "Toh ya kike son in maki Khaleesat?" Umma ta kasa ci gaba hawaye ya fara sauka idonta ta dafe kanta, kuka kawai Khaleesat take tana kallon Ummanta, Umma ta dake tana share idonta tace "Ko wajen Nenne zaki sai ki gaya mata ki ji abinda zata ce, ni kin san babu abinda zan iya yi akan lamarin nan Khaleesat" Ita dai Khaleesat bata ce komai ba, Umma ta mike a sanyaye ta fita daga dakin don juye mata ruwan wankan da ta dora mata a kan wuta yana ta tafasa, a haka ta ta dawo ta samu ta lallabata ta ɗan sha kunun sannan ta tafi waje yin wanka, kafin ta fito har Umma ta fiddo mata kayan da zata sa tayi tagumi tana jiranta, karfin hali kawai Khaleesat take amma ji take kamar zata iya collapse at anytime, bayan ta shirya Umma tace "Amma bana son yan gidan nan su san inda zaki, kar su gaya ma Malam" Khaleesat ta jinginar da kanta da bango, a hankali tace "Umma bazan iya zuwa ni kadai ba don Allah ki rakani" Umma tayi shiru, can tace "To zan fita in shiga gidansu Er Lami in jira ki a can, bana son su ga mun fita tare, bayan na fita da minti goma kema sai ki fito" Kai kawai Khaleesat ta gyada mata, Umma ta mike ta dau hijab dinta ta saka sannan ta dora nikab ta fita daga dakin, Su Mama Shatu da Mama Zubaida suna ta girka abincin siyarwansu da yaransu za su fita talla da shi, tace masu zata shiga makota sannan ta fita, duk suka bi ta da kallo sun tabe baki, Mama Shatu tace "Ma ji ma gani dai, a sanda ake mana fafa an tura 'ya kasar waje ga namu yaran a zube ai babu bakin cikin da ba a kuntsa mana ba" Mama Zubaida tace "Sun gana tattatse ɗan mutane rana daya su fito su ce basu san zance ba, ke ina kika taɓa ganin anyi haka? Ai na so Malam ya rarrade shegiya jiya da daddare, to dai ba kanta kadai zata ja ma babban magana ba, har shi Malam din" Duk Khaleesat na jin su, ita dai tana zaune ta jinginar da kanta da bango tana sauke numfashi a hankali, bayan minti goma da fitar Ummanta ta tashi da kyar ta fiddo gogaggen Hijab dinta ta saka sannan ta dora Nikab ta fita daga dakin, tunda ta fito suke kallonta, a haka ta nufi hanyar fita daga tsakar gidan tana ji kamar iska zai kadata ta fadi. Gidan da Ummanta tace zata jirata ta nufa, ta samu Ummanta a tsakar gida tana jiranta yan gidan ma duk basa nan, Umma ta taso suka fita daga gidan, tafiyar kusan minti sha biyar ne zuwa gidan Nenne daga gidansu, Nenne ta ajiye tsintsiyar hannunta tace "Dawowa yayi da ita daga inda take karatun don an daura aure?" Umma ta zauna kan tabarman tsakar gidan ta cire Nikab din fuskarta ta gaida Nenne, Khaleesat ta zauna gefen Ummanta, Nenne ta amsa tace "Ai dama nace ko da ta dawo sai ta huta an kintsa ta kafin ayi maganar wata tarewa tunda yace baya bukatar taron komai, amma baza mu dau yarinya haka kawai ace an je kai ta ba" Umma dai tayi shiru bata ce komai ba, a hankali Khaleesat ta cire Nikab din fuskarta ta ajiye, Nenne ta ɗan duka tana kallonta tace "Lapiya naga idanuwanta sun kumbura haka, me ke faruwa?" Umma ta sauke ajiyar zuciya ta kasa cewa komai, A fusace Nenne tace "Magana nake ku ka min shiru fa? Meye haka aka shigo min da ita da kumburarrun ido" Cikin rawan murya Khaleesat tace "Nenne ni bana son sa, bana son auren..." Nenne ta saki baki tace "Baki son auren kuma?" Khaleesat ta gyada mata kai hawaye wasu na bin wasu a kuncinta, Nenne ta nemi waje ta zauna tace "Atoh dai, ni dama shegen bai taɓa kwanta min ba, amma abun dubawa a nan shine na isa da Alin? Ashe ma ba er banza bace ni a gunsa kenan" Nenne ta mike ta shiga dakinta ba a dau lokaci ba ta fito ta dire wani babban ledan hannunta sannan ta bude tace "Kun dai ga duk wata shegiyar kyautarsa da yake kawo min ban taɓa amfani da ko daya ba duk na tara masa kayansa waje daya, ga atamfofinsa nan da turarurruka da tarkace, ba ruwana ban yi amfani da su ba, ke ma Zahra'u inda abunsa da kika san ya taɓa baki ki tattaro su waje daya, shi Ali ina ma yayi amfani da nasa shi ya sani, sai ya shiga kasuwa da wuri wuri" Ita dai Umma tayi shiru bata ce komai ba, Khaleesat kuwa kuka take a hankali, Cikin sanyin murya Umma tace "Kin mance abinda ke kasa ne Nenne, ai yanzu ba maganar wai abinda ya bamu bane damuwar" Nenne tace "Yo ina ruwana da abinda ke ƙasa, ko ina ruwan yarinya da abinda ke kasa? Sai a ma jikata auren dole kike nufi kenan? Ni fa tun asali katon mutumin nan bai min ba sam, ayi mutum ba fara'a ya shigo maka sandan sandan ya fita gansan gansan? A duba fa wannan lamari, da kyar kaga murmushinsa kamar rikakken ɗan ta'adda da aka kusa yi ma preedom, yo wannan uban kudi na ubansa wa ma yasan ko ta'addancin suke da garkuwa da jama'a, hatta ruwan gidana gansamemen mutumin nan bai taɓa sha ba, yanda na ajiye masa haka yake barin min tsiyata bai san yarana mata ruwan gora suke siya min ba ya zata durawa nake, haka zai zauna maka kamar sarki yayi ta danna waya ga gidan er banza ya shigo, to ban isa da Ali ba kannensa mata ma basu isa da shi ba, shi kawai ta kansa yake a rayuwar nan baya duba makomar er da ya haifa a cikinsa, ko dan yaga yaran rakacaa an haifa masa ne ba kwantrol oho, gashi ba jin maganar yayyin uban nasa zai yi ba balle ince ku je ku samesu, in kuma muka ce mu tafi mu kai rahotu gidan yan sanda daga karshe mu za a kulle, to ni Ramatu ya zan yi? Amma dai ba komai zan aika a kira min Alin anjima, hatta batun daurin auren sai jiya da za a daura muke samun labari" A hankali Umma tace "Shi ma Malam din shekaranjiya da yamma suka kirasa suka sanar masa ga abinda suke so za ayi" Nenne tace "Tirrr, duk sun rainamu sun mayar da mu yan iska kawai, na tabbata shi kansa Alin bai taɓa rokon Awdul din naira biyar ba balle uban Awdul" Umma ta girgiza kai tace "Bai taɓa ba kam, jarabawa ce kawai Allah ya dora mana babu yanda mu ka iya" Nenne tace "A'a har da dai iskanci, ku baku da baki? ke da er taki baza ku iya kwatar en cin ku ba, ita kadai ce mace a gidan? Tun asali dama kin maida kanki gantalalliya a gidan" Umma dai tayi shiru, Nenne tace "Ko kuma kawai ku tafi gida zan daidaici lkcn da zai koma gida da magariba in taho gidan" Umma tace "Toh shikenan Nenne" a haka Khaleesat da Ummanta suka bar gidan bayan Nenne ta dama mata fura da nono ta tilastata ta sha. Khaleesat na kwance dakin Ummanta wajen karfe shidda na yamma, har zuwa sannan ta kasa cin komai tun bayan furan da ta sha gidan Nenne, tun da suka dawo gida take karatun qur'ani don ta rasa me ke mata dadi a duniyar kawai bata son tayi ta daga ma Ummanta hankali yasa ta hakura da kuka sai na zuci kawai da take yi, gaba daya taji duniyar yayi mata zafi, da ta tuna wai fa ita matar aure ce yanzu kuma matar Abdul, sai taji dama kawai Allah ya dau ranta ta huta, bayan taji she is exhausted da karatun qur'anin da take tayi shine ta kwanta gefen katifar Ummanta, tayi nisa tunanin da take jin hawaye na taruwa idonta ta mike zaune tana kallon Ummanta dake gyara kayan su Islam a dakin tace "Umma ina wayarki?" Umma ta kalleta tace "Ko sati ba ayi ba na nemeta na rasa an dauke a gidan nan" Khaleesat tayi shiru tana kallon Ummanta, sai kuma ta jawo handbag dinta a hankali ta bude ta ciro wayar da Jay ya bata duk da babu SIM card a ciki, she just want to do something that will keep distracting her from her worries, har zata shiga game sai kuma ta fasa ta shiga gallery din wayar, ta ɗan yi jim na few seconds kafin ta bude hotunan, a hankali take flipping tana kallon each and every image of him and AJ, sai a sannan ta lura da kaman da suke yi even though it's not obvious, wani hotansu tare ta tsura ma ido ganinsu cikin shiga ta alfarma irin ta sarauta, ita dai tana ta kallon hoton babu ko kiftawa, sai kuma tayi flipping zuwa next image, haka ta dinga ganin ire iren hotunan, wani taga Jay shi kadai wani taga Ajay shi kadai, ko kuma ta gansu tare, with horses and so many things related to gidan sarauta, kashe wayar tayi a hankali ta mayar cikin jakarta ta ajiye jin muryan Babanta ya shigo gidan, ya ɗaga labulen dakin Ummanta yana kallonta yace "Ki fita ga Abdul can ya zo yanxu" Sosai gaban Khaleesat ya fadi ta dinga kallon Babanta bata ko kiftawa, Umma ta juya ta kallesa tace "Ta fita kuma Malam? Dama ana haka? Ai ina ga ba sai ya zo ba sai ya jira har zuwa sanda zata tare ko" Malam Ali da ya bude baki yana kallonta yace "Wato dai duk wani salon dauko min magana kun iya shi Zahra'u, in ya zo ta fita sai aka yi yaya? Addini ne ya haramta hakan ko kuwa shirmen ku? Kuma da kike batun tariya ko gobe yace yana bukatar ta tare mu muna da ja ne dama?" Umma tace "Ai ko muna da ja Malam, tunda baza mu dau yarinya haka kawai mu kai ta dakin miji ba, duka duka ma yaushe ta dawo kasar" Khaleesat ta fashe da matsanancin kuka tana jin kamar zuciyarta zai fashe ta huta, Babanta da ya bude baki yana kallonta yace "Ni kike neman tona ma asiri ko ko ya kike so inyi? Sabon magana za ku ja min ke da uwarki kenan? In ma ba yanzu za a tare ba tunda ya zo ai sai ki fita ku gaisa tunda ba haramun bane, in kun gaisa sai ki dawo cikin gida" Khaleesat taki cewa komai sai kuka take, Ya daka mata tsawa yace "Kar ki ga ina lallabaki don uwarki, zaki tashi ki fita ko sai na rarrade ki da icce" Khaleesat na kuka ta sauka daga kan gadon, Umma da hawaye ya cika idonta ta kauda kanta, Khaleesat ta dau Hijab dinta ta saka ta fita daga dakin tana kuka sosai, Kishiyoyin ummanta dake zaune tsakar gida duk suna sauraron abinda ke faruwa sai tabe baki suke, ganin Malam Ali ya bi bayan Khaleesat, Mama Shatu tace "To rakata wajen nasa zaka yi ne Malam?" Sai kuma ya juyo da sauri yace "Au to" Ya nufi ɗan karamin dakinsa dake tsakar gidan, Mama Zubaida ta tabe baki tace "Ma ji ma gani dai" Khaleesat na fita kofar gida hawaye na sauka idonta taga motarsa wanda ke dauke da tinted glass yayi parking dai dai inda su AJ suka tsaya jiya, ko saukowa bai yi daga cikin motar ba, hawaye na bin fuskarta ta tafi ta tsaya kusa da motar taki budewa kuma tasan yana kallonta, after almost 5 mins taga ya sauke glass din motar yace "Ni zan sauko in same ki?" Ita dai taki kallonsa, kuma taki cewa komai, after few seconds ta bude gaban motar a hankali ta shiga amma ta ki kulle motar, yace "Sauron unguwan ku zaki cika min a motata, are you in ur right senses?" A hankali ta ja motar har sannan taki yarda ta kallesa ta kulle, gabanta sai faduwa yake don jin muryarsa take kamar ana tsira mata allura a kunne, Lokaci daya ta juya da sauri tana zaro ido ganin ya zuge glass din ya tada motar ya kara volume din sautin da yake ji sannan ya ja motar, a rikice ta fara kokarin budewa motar taji a kulle gam, ta kwala wani azababben kara tace "Na shiga uku na lalace, don girman Allah kayi hakuri ka rufa min asiri ina zaka kai ni? Ka bude min in sauka...." Ko kallonta bai yi ba fuskarsa babu yabo babu fallasa yake driving dinsa idonsa na kan hanyar dake gabansa, ta rikosa da hannu biyu cikin gigicewa tana masa magiyan ya bude mata motar, bai yi wata wata ba ya sauke mata wani lafiyayyen back hand slap a fuska, sai da taji dumm na few seconds, lkci daya jin ta da ganinta ya dauke na ɗan lokaci, duk da haka bata sake sa daga rikon da tayi masa ba tana kururuwan ya bude mata motar, ya fincikota ya jefar kan kujeran motar cikin kaushin murya yace "Kika sake taɓa ni sai na wanka maki wani marin" Lokaci daya duk jikin Khaleesat ya mutu saboda shock, ta dinga sauke numfashi da kyar idonta na ganin dishi dishi daga marin da yayi mata tana kallonsa, shi dai driving dinsa kawai yake fuskarsa babu yabo babu fallasa...... [5/26, 9:48 AM] khaleesat Haiydar ✍️: Sai da Khaleesat taga sun bar unguwansu gaba daya sannan reality yayi hitting dinta ta kara fahimtar me Abdul ke da niyyar yi, she felt so helpless at this point, ta jinginar da kanta jikin kujeran motar hawaye masu zafi na sauka idonta ta kasa cewa komai, shi dai driving dinsa kawai yake bai ko kalleta ba, ganin tafiya kawai yake ta juya tana son ko hakuri ne ta bude baki ta basa amma tsoron kar ya sake marinta yasa ta kasa don babu alamar rahama a fuskarsa, ta rufe fuskarta da hijab din jikinta hawaye wasu na bin wani a idonta, tsabar tashin hankali da firgicin da ta shiga a wannan moment din kilan da za a duba jininta za a ga ya hau, bayan tafiyar kusan minti talatin taji ya tsaya cak, da sauri ta sauke Hijab dinta zuciyarta na bugawa tana kalle kallen inda suke, taga dai dai wani eatry ya tsaya, ita dai kallonsa take har sannan hawaye bai daina sauka idonta ba, ya sauka daga motar without looking at her ya kulle, ta bi sa da kallo har taga ya shiga gidan cin abincin, ta fashe da matsanancin kuka tana waige waigen wajen cikin tashin hankali, babban wajen cin abinci ne sosai, ga mutane suna ta kai kawo a gurin, glass din motar ta fara bubbugawa da hannunta amma taga nobody is noticing her, ta fara kalle kallen cikin motar taga bunch of keys da ya ajiye ta dauka da sauri ta fara bubbuga glass din motar da shi da karfi, hakan ya ja attention din wani mutumi da ya fito daga cikin eatry din zai shiga motarsa dake kusa da inda Abdul yayi parking, ita dai bata fasa bubbuga glass din ba tana kuka sosai tana cewa don girman Allah ya taimaketa, da alama baya ganin cikin motar saboda tinted glass din, ya zaga ta gaban motar yana duba ciki, ta dinga kuka tana cewa don Allah ya taimaketa, ba ta damu ko yana jin abinda take cewa ba ko baya ji ita dai kawai ya taimaketa, mutumin ya tafi ya taho da wani security dake wajen, dai dai nan wani soja da ya fito eatry din zai shiga motarsa shi ma ya karasa gun motar kan kace me attention din jama'an dake gurin gaba daya ya dawo kan motar Abdul, Khaleesat bata fasa kukan da take ba duk da ta samu relieve ganin mutanen da suka zagaye motar wasu na kokarin mata magana suna haska cikin motar da fitila, mutane duk suka tsaya aka yi cirko cirko a kusa da motar, ita dai kuka me sauti kawai take kamar ranta zai fita, babu wanda bazai ce sato ta aka yi a lkcn ba, bayan wasu mintuna Abdul ya fito daga Eatry din rike da abinda ya siyo, yana zuwa inda yayi parking yaga jama'a jikin motar ya tsaya yana kallon ikon Allah, Security din dake tsaye wajen don yaga sanda Abdul yayi parking ya shiga eatry din, ya kalli sojan dake tsaye yace "Ga me motar nan ya fito" Da wani expression Abdul yace "What happened?" Sojan yace "Bude motar ta sauko Malam" Abdul yace "Ban gane in bude mota ta sauko ba, matata ce a ciki" Sojan yace "Ai bamu mu sa ka ba, mota kawai zaka bude ta sauko, ba wani abun tashin hankali bane ai" Nan jama'an wajen suka dinga cewa ya bude motar suna hayaniya, Abdul ya bude motarsa da Key din hannunsa daga inda yake tsaye, Khaleesat na jin alamar yayi unlocking din motar ta bude ta sauko da sauri tana kuka, Sojan ne ya fara mata magana yana nuna mata Abdul yace "Waye wannan?" Ta fashe da matsanancin kuka muryarta na rawa tace "Ni ban san shi ba" Kallonta Abdul ya dinga yi da mamaki babu ko kiftawa, hayaniya sosai mutanen wajen suka hau yi sojan na kokarin calming dinsu, Sai kuma ya sake kallon Khaleesat yace "Baki san shi ba? To garin yaya kika shiga motarsa?" Tana shessheka tace "Kawai dauko ni yayi a unguwanmu wallahi, ni ban san shi ba" Tuni matasa yan zaman kashe wandon dake wajen suka fusata suka zagaye Abdul suna dure duren ashar suna kokarin fara mazgarsa, gaban Eatry din ya cika da jama'a an zo kallo wasu har sun fara video, with the intervention of the soldier and the security men da wasu responsible mutanen dake wajen aka saka Abdul cikin motar Sojan don tsaf sun kula matasan za su yi aika aika ne a wajen, wannan opportunity din Khaleesat tayi using cikin dubara ta sulale cikin jama'ar wajen without letting anyone to notice her don gaba daya hankalin mutane ya koma kan Abdul a wajen, a haka ta samu ta tsallaka titi ko waigawa bata yi ta afka wani layi, nan ma tayi ta tafiya da sauri da sauri gabanta na faduwa, duk inda taga alamar hanya ce haka ta dinga bi ba tare da tasan inda zata ba, tafiyar kusan minti arba'in tayi a kafa hawaye na zuba idonta, ko sanin unguwan da take bata yi ba, daga karshe tsabar yanda ciwon kai ya matsa mata ga jiri dake ta kwasarta ya sa ta samu gaban wani gida ta zauna ta hade kanta da gwiwa tana shesshekan kuka, tana ta zaune for almost 10 mins wani mutumi dake ɗan nesa da ita yana zaune kofar gidansu ya mike ya nufota, don tun da ta shigo layin ta zauna ya ganta, sallama yayi mata ta dago kanta a tsorace, yace "Baiwar Allah lafiya dai ko?" Ta girgiza masa kai da kyar tana goge idonta tace "Bana jin dadi ne, kuma gida zan je" Yace "Ikon Allah, to ina ne gidan naku?" Without second thought tace "Hotoro" Yace "Hotoro? To bari in samo maki adaidaita sahu sai ya kai ki" Ta gyada masa kai cikin rawan murya tace "Nagode" Ya juya ya bar wajen, bayan wani minti goman sai gashi ya dawo cikin adaidaita sahu bayan yaje har bakin titi ya samo mata adaidaita sahun, ya sauko daga ciki yana kallonta yace "Toh ga adaidaita sahun na samo maki Hajiya" Tace "Nagode" Ta mike da kyar ta dafa adaidata sahun sannan ta shiga ciki, mutumin ya ciro wayarsa ya mika mata yana kallonta yace "Ki saka min lambarki sai inji ko kin isa gida lafiya" Ta girgiza masa kai a hankali tace "Matar aure ce" Mutumin yace "Ohh, na gane to, Allah ya tsare Hajiya, Allah ya baki lafiya, na biya sa kudinsa ba sai kin basa ba" Ta gyada masa kai tace "Nagode, Allah ya saka da alkhairi" yace "Ameen ya Allah" a haka mai adaidaita sahun ya bar layin. Har suka isa hotoro Khaleesat bata san sun iso ba, sai da me adaidaita sahu ya ankarar da ita, dai dai kofar gidan Gaje ta sa ya tsaya, ta sauka tayi masa godiya ta shige cikin gidan, nan gaban Gaje dake zaune tsakar gida ta zuba tana kuka kamar zata shide, Gaje tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'una, Khaleesah? Me ya faru? daga ina kike haka?" Da kyar Gaje ta lallashi Khaleesat tayi shiru bayan lokaci me tsayi, sannan ta fara gaya mata abinda ya faru, Gaje ta saki salati a rikice tace "Mun shiga uku mun lalace, yanzu gidan yan sanda suka tafi da Awdul din kenan?" Cikin kuka Khaleesat tace "Ban sani ba nima" Gaje tace "To kuwa zaman gidan nan bai kama ki ba Khaleesah, yasan bayan gidanku baki da inda zaki taho a kano da ya wuce gidana ko gidan Nenne, wannan fa ba karamin kess bane, Awdul na zuwa nan ya ganki sai ya zata da hadin bakina kika yi abinda kika yi, ya sa yan sanda su kulleni in shiga uku" Cikin kuka Khaleesat tace "Toh ya zanyi yanzu Baaba Gaje?" Gaje ta mike ta figi gyalenta a igiya tace "Ta shi mu je" Jikin Khaleesat na rawa ta mike ta bi Gaje suka fita daga gidan, da kafa suka tafi gidan kawar Aunty Farida da ake ce ma Maman Fu'ad, bayan sun shiga gidan Gaje tayi mata bayanin duk abinda ke faruwa, Maman Fu'ad tunda ta rike haɓa har gaje ta gama bada labari bata iya tace komai ba, Gaje tace "Don haka ki rufa mana asiri Sadiyah ta kwana gidanki zuwa gobe a ga abinda hali zai yi" Maman Fu'ad ta sauke ajiyar zuciya ta kalli Khaleesat, gwalo ido tayi ganin jinin da ya kwanta idonta tace "Me ya samu idonki?" A hankali Khaleesat tace "Marina yayi" Maman Fu'ad ta saki salati tace "Mari?? Har sai da jini ya kwanta maki a ido? ga lebenki ma a fashe? A'a gaskiya tsinanne ne wannan mutumi" Gaje ta rike haɓa tana kallon idon Khaleesat sai kuma ta fashe da kuka tace "Yanzu wannan har mijin aure ne in ba don Ali ya cuceki ba, dubi fa tafin hannunsa a fuskarta?" Maman Fu'ad tace "Da kyar ma in baya shaye shaye wannan, gaskiya duk yanda za ayi a raba auren nan domin ceto yarinyar nan daga halaka, yanxun nan zan kira farida kuwa" Gaje ta rufe bakinta da sauri tace "Ki kirata kice mata me? Rufa mana asiri ba wanda yasan tana nan, ina me tabbatar maki kilan yanzu an tafi da Awdul din police station, kinga ai dole ya kai yan sandan gidansu Khaleesat don wanke kansa su tabbatar matarsa ce, in kuma yayi haka ai za a bazama nemanta ne a gari" Maman Fu'ad tace "Ba komai Gaje, ki tafi kawai ki kyaleta a nan kar su je can gidan naki baki nan" Gaje ta mike da sauri tace "Don Allah ki bata ruwan zafi in kina da shi tayi wanka" Maman Fu'ad tace "Kar ki ji komai Gaje" A haka Gaje ta bar gidan, yanda Khaleesat taga daren jiya wannan daren ma haka ta gansa, ga ciwon kai, ga ciwon ido, ga zazzabi duk ta rasa inda zata sa kanta taji dadi, she don't even know who to speak to at this point. Washegari karfe tara Gaje ta shigo gidan, tun daga bakin kofa ta fara ba Maman Fu'ad labarin abinda ke faruwa tace "Sadiyah wajen karfe goma suka zo nemanta a gidana wallahi jiya har da shi Awdul din, ni dai jikina sai rawa yake don tare yake da yan sanda, yanxu haka daga can Mariri nake, uwarta na can hankalinta a tashe ko bacci bata yi ba sai koke koke, uban kuma yace da hadin bakin uwar Khaleesat ta gudu, babu kalan tijaran da Awdul bai yi ba jiya, keee abun dai babu kyau, ni dai hankalina ya tashi sosai, ina tsoron kar a gano ni na ajiyeta Awdul ya hadani da hukuma, shine na zo kawai ta shirya tayi hakuri ta koma gida duk abinda Allah yayi dai dai ne" Khaleesat dake jin duk abinda Gaje ke cewa ta fashe da matsanancin kuka tace "Don girman Allah kar ki ce masu ina nan Baaba Gaje, wallahi har duka zai iya min" Maman Fu'ad dai na tsaye da atamfar mutane da zata yanka ta hau kan keke ta kasa cewa komai sai zazzare ido take, ita ma tsoro take kar daga karshe ace ai a gidanta aka boye Khaleesat, ta ina zata fara ma Baban Fu'ad bayani in aka zo tafiya da ita gashi bai gari, Gaje tace "Toh ya kike so inyi Khaleesah, Awdul fa ya maida maganar nan babban magana wallahi, wai kin tozartasa a cikin mutane jiya kin sa an tafi caji opis da shi, ba ki da kowa da zai tsaya maki a lamarin nan sai Allah, Malam Ali na can kamar zai haukace shi ma ya saka uwarki a gaba sai ta fito dake" Khaleesat ta hade kanta da gwiwa tana shesshekan kukan, Gaje ta make hannun Fu'ad dake ta jan yakunannen gyalenta sannan ta ja kujeran tsugunno ta zauna ta rafka uban tagumi tace "Ni dai ban san kuma yanda zan maki ba Khaleesah, ina talaka da ni Awdul yasa a daureni wa zai cece ni, sai ma Kinga kallon da yake min jiya kamar bai yarda da ni ba" Khaleesat ta dago da kyar tana kallon Baaba Gaje hawaye na sauka idonta, Baaba Gaje dai zai zazzare ido take tace "Ni ban ma yarda bai sa CID unguwar nan su kula da shige da fice na ba, yanxu hka sai da na zaga kamar zan je Yan kaba sannan na taho gidan nan" Cikin sanyin murya Khaleesat tace "Don Allah Baaba Gaje ki min alfarman dauko min jakana a can gidanmu" Baaba Gaje ta gwalo ido tace "Wani jakar?" Khaleesat tace "Karamin jakata, akwai wayata a ciki zanyi amfani da shi" Baaba Gaje tace "Um um Khaleesat, ta yaya zan dauko jaka ana gani na da rana tsaka?" Khaleesat ta girgiza mata kai tace "Karamin jaka ne bai da girma, ko a gyalenki zaki iya boyewa don girman Allah ki rufa min asiri ki taimakeni Baba Gaje ki dauko min, har da kudi cikin jakan, zaki ga jakar kusa da akwatina a gefen katifar Umman mu" Maman Fu'ad dai sai baza ido take taji Khaleesat zata bar gidanta amma shiru bata ji ba, can dai tace "To ke ina kika nufa daga gidan nan yanzu?" Khaleesat na share hawayenta a hankali tace "Idan ta dauko min jakar zan san inda zan je in sha Allah" Maman Fu'ad ta sauke boyayyen ajiyar zuciya, faridan ma bazata kira ba kar daga karshe a gane ita ta ajiye Khaleesat a gidanta ta shiga uku, Da kyar Baba Gaje ta yarda zuwa Mariri dauko jakan don duk a tsorace take, shi ma sai da Maman Fu'ad ta saka baki tunda taji ance in dai aka dauko jaka to za a bar gidanta, shi sa tayi ta lallaba Gaje taje Mariri dauko jakar, bayan kusan awa daya sai ga Gaje da jakar ta kudundunosa a gyalenta, Khaleesat ta amsa jakar ta bude ta ciro wayar Jay dake ciki, ta ga dollars din da ya bata suna ciki har sannan, Call log ta shiga sai kuma ta kalli Maman Fu'ad tace "Don Allah ki ara min wayarki bani da Sim card a nawa" Maman Fu'ad tace "Ai ko babu kati, tunda ga wayar Gaje bari in bada dari biyu a siyo sai ki saka a nata wayar ki kira" Nan duk dubara Maman Fu'ad tayi kar a ga Khaleesat tayi kira da wayarta idan bincike yayi bincike, Gaje ta mika ma Khaleesat wayarta ta fita ta amso mata katin dari biyun da Maman Fu'ad ta dauko ta bada, Khaleesat na saka katin ta fara dialing number Jay, ta kira yafi sau biyar sai dai kiran ya dawo mata alamar bai je ba, bata hakura ba still tayi ta kira baya shiga bata san ko katin ne yayi kadan ba kuma Number sa na Nigeria yake using a can din ma, wasu sabbin hawayen suka fara sauka idonta ta sake shiga call log din wayar tana scrolling slowly, number AJ ta gani shi ma Nigeria Line dinsa, ta ɗan yi jim tana kallon number, sai kuma tayi dialing tana share hawayen dake zuba idonta, ringing ya fara yi har ya katse bai daga ba, ta sake kiransa, sai da ya kusa katsewa sannan yayi picking, muryarta na rawa tace "Good Afternoon" Shiru yayi, kafin yace "Wacece?" Ta sauke idonta tace "Ni ce" Yace "Ke wa?" Da kyar tace "Plss i want to speak to you" Kawai ta fashe da kuka uncontrollably, shiru yayi for almost 15 seconds, can yace "What happened?" Tana kuka tace "I need to speak to you pls" Ya kara yin wani shirun, can yace "Where are you?" Tace "Hotoro" He still kept quiet for some seconds kafin yace "Address" Katse wayar Khaleesat tayi ta tambayi Maman Fu'ad address din unguwan, Maman Fu'ad ta gaya mata sannan ta tura masa ta message, Gaje dake zaune kan kujera tace "Wanene wannan din da kika kira?" Ita dai Khaleesat tayi shiru wasu hawayen na taruwa idonta, Baba Gaje tace "Gashi idon naki sai kara ja yake yi, wallahi makantar da ke kawai yayi niyyar yi matsiyacin nan" Bayan kusan 35 mins wayar Gaje ya fara ring, Gaje ta mika ma Khaleesat da sauri tace "Ko wanda kika kira ne?" Khaleesat ta amsa tana kallon wayar taga AJ ne ke kira, dagawa tayi yace "I am outside" Khaleesat ta ajiye wayar sannan ta kalli Maman Fu'ad tace "Aunty don Allah kina da Nikab?" Maman Fu'ad tace "Yaushe rabona da Nikab, bani da shi yanzu kam" Khaleesat ta mike tana rike da handbag dinta da wayar Jay ta fita daga gidan, not far away from the house yayi parking, yana jingine jikin motar ya rungume hannunsa looking at a different direction, tana tafiya a hankali ta nufesa tana kallonsa, tana isowa kusa da shi ya juya jin Footstep, ya gyara tsayuwarsa ya dinga kallon idonta babu ko kiftawa, she tried her best na ganin bata fashe da kukan da ya taho mata ba amma ta kasa daurewa ta hade kanta da jikin motar ta fara kuka har da shessheka. [5/26, 9:21 PM] khaleesat Haiydar ✍️: Ajay bai ce mata komai ba sai da tayi kukan me isarta don kanta tayi shiru, tana share idonta ta daga kai ta kallesa taga kallonta yake har sannan, Calmly yace "He did all this to you?" Kai ta gyada masa wasu hawayen na taruwa idonta, yayi shiru for a while kamar me nazari, sai kuma yace "Ɗan kano ne?" Nan ma ta gyada masa kai, yace "A ina yake a kano?" Muryarta na rawa tace "I don't really know" Zai yi magana Baba Gaje ta leko kofar gidan kamar munafuka tana zazzare ido, Ajay ya ɗan sauke kansa ya gaisheta bayan sun hada ido da ita, fitowa tayi da sauri tana kalle kallen Unguwan tace "Lafiya lau ɗan nan, wallahi yarinyar nan tana cikin mummunan masifa, bata da kowa sai Allah, ta dawo daga turai ta tarar an daura mata aure da lafcecen yaron nan ɗan iska, dama kuma duk mun san ɗan iska ne muke kauda kai tunda bamu da yanda za mu yi, ashe bai ma yi shawara da ita ba kansa tsaye ya taho ya samu iyayen da ya raina suka daura aure shekaranjiya, to tunda tace bata son auren in dai ba tsinannen mutumi ba ai sai ya kyaleta ga mata kaca kaca a duniya, wani mugun kuduri ne a ransa haka da yasa aka daura auren a gaggauce ko shiri babu? dubi fa abinda ya mata a fuska daga ya dannata a mota taki bin sa, yanxu haka duk ya baza CID a unguwan nan ana nemanta, sai kaga tijaran da yaje ya ma iyayen nata jiya da daddare, shi sa ka gan mu duk a tsorace" Tun da ta fara magana Ajay ke kallonta ko kiftawa baya yi, mamaki ne sosai kwance a fuskarsa, can ya kalli Khaleesat dake kuka kamar Baaba Gaje na dada tunzurata, ya sake kallon Gaje yace "Aure kuma Mama?" Gaje tace "Wallahi da gantalallun igiyoyinsa har uku a kanta yanxu haka, tun jiya ta gudo nan bayan ta samu ta tsere da kyar daga hannunsa" Gaje ta fashe da kuka tana matsar kwalla da gyalenta tace "Wallahi bata da kowa sai Allah, iyayen basu da bakin magana, basu da ta cewa, ni kuma ba kowa bace makociyarsu ce mun yi zaman Mariri tare kuma ni talaka ce, ni ko taimaka mata ne kayi ka kai ta wajen masu kare hakkin ɗan Adam ta kai masu kukanta su kwato mata hakkinta da ake neman tauyewa" Har sannan Ajay ya kasa cewa komai, can ya bude gaban motarsa yana kallon Khaleesat, Baaba Gaje ta fara tura ta ciki tace "Maza shiga ku je ya kai ki ofishinsu, in ma rike ki za su yi su rikeki ki zauna har sai sun bi maki hakkin ki, amma kar ki ce nasan komai, kar ma ki saka ni a maganar" Khaleesat dai kuka kawai take ta shiga motar, Baba Gaje ta amshi wayarta dake hannunta ta kulle motar gbamm tace "Maza ku je" Ajay dai ya zaga ya bude driver seat ya shiga, Da sauri Baaba Gaje ta koma gate din Maman Fu'ad kamar ba daga kusa da motar ta taho ba, ta makale tana kallonsu har suka fita daga layin, driving kawai AJ yake idonsa a kan titi, gaba daya he look speechlesss, tunda ya kalleta sau daya bai sake kallonta ba, ita dai Khaleesat ta rufe fuskarta da Hijab dinta saboda hasken rana dake damun idonta kuma tana tsoron kar ace su hadu da Abdul dan motar babu Tint, har sannan bata daina kukan tashin hankalin da take ba, after driving for 20 mins AJ ya kalli wayarsa dake vibrate, Number Jay ne ke kiransa, hakan ya sa ya rage tafiyar da yake ya gangara gefen titi yayi parking sannan ya dau wayar yayi picking ya kai kunne a hankali yace "Jay" Khaleesat ta zame hijab dinta daga fuska jin sunan da ya kira ta juya ta kallesa, Calmly taji yace "I am cool" tambayarsa Jay yayi ko ya bar Kano, AJ yace "Am still around, when are you leaving Maryland?" After few seconds AJ yace "Alright, we will talk later" Daga haka ya katse wayar ya ajiye ya jinginar da kansa jikin kujerar motar ya kafe titi da ido for almost 2 mins, can ya sake daukar wayarsa don duba available flight to Abuja ranan, yaga jirgin karfe uku kuma saura just few seats, National ID card dinta da passport dake motarsa tun ranan da suka dawo US da drivern su na Lagos ya amsa a wajenta don mata booking ticket to kano, ticket ya siya mata immediately na zuwa Abuja sannan ya ajiye wayar, Aunty na nan gidansu na kano sun zo biki shi sa ma bazai fara kai ta can gidan ba, juyawa Khaleesat tayi da kyar ta kallesa tana dafe kanta pleadingly tace "Kanwar Ummata tana Lagos, don girman Allah ka taimakeni i want to go to her plss" Shi dai kallonta kawai yake, Calmly yace "Where in Lagos?" Tace "Zan kira in tambayeta, amma bani da numberta ne" Ya ga alamar gaba daya she is confuse and in fear, yace "Ta yaya zaki kirata baki da numberta?" Wayarsa ta dauka da sauri ta shiga call logs dinsa tana duba number Baaba Gaje, dialing tayi yana fara ring Baaba Gaje ta daga, da sauri Khaleesat tace "Baaba Gaje don Allah number Aunty Farida za a duba a wayarki sai a turo ta wannan layin" Baba Gaje tace "Har kun je wajen kare hakkin ɗan Adam din?" Khaleesat tace "Ki dai turo min don Allah yanxu Baaba" Baaba Gaje tace "Toh bari in je makota kin san ban san kan wayar ba ai" Khaleesat ta gyada kai da sauri tace "To ina jira" Katse wayar tayi ta jinginar da kanta jikin kujera tana sauke numfashi, wani dishi dishi take gani tsabar kuka, Shi dai Ajay idonsa na kan titi alamar dai kansa ya gama kullewa, ya kalli agogon wrist dinsa yaga karfe biyu ya gota, driving motar ya ci gaba da yi da tunani iri iri a ransa ya nufi wani eatry ya sauka ya shiga ciki, Khaleesat ta dinga bin haraban wajen da kallo sai kuma ta rufe fuskarta da Hijab dinta da sauri zuciyarta na bugawa, incident din jiya ne kawai ke dawo mata a kai as if she is hallucinating, sai taga kamar yanzu incident din ke faruwa yanda Abdul yayi parking ya fita daga mota ya shiga eatry, kan kace me ko ina na jikinta ya fara rawa taji kamar numfashinta zai dauke, ba a dau lokaci ba Ajay ya fito daga gidan cin abincin da leda a hannunsa, yana shiga motar ya ajiye ledan da sauri yana kallonta yace "Me ya faru??" Ta dago kanta hawaye caba caba a fuskarta, sai kuma ta kamo hannunsa gam tace "I just want to leave here plss, don Allah mu bar nan" Gaba daya ta dawo kamar warce ta zauce, ya fara bin area din da kallo tunaninsa ko Abdul din ta gani, can ya sake kallonta bayan ya zauna cikin motar, cikin nutsuwa yace "Look, stay calm.... You are safe" Ya gyara mata kujeran motar a hankali ta yanda zata ɗan kwanta yana kallonta, sai da ya jira for almost 10 mins yaga ta ɗan nutsu tana sauke numfashi a hankali, lkci lkci yake kallon agogonsa saboda flight din da yayi booking, after a while ya ɗan duba fuskarta yaga kamar ta fara bacci, tada motar yayi ya bar wajen, still sai da ya kara tsayawa a pharmacy ya siya mata magunguna, ko kashe motar bai yi ba don kar ta ma san yayi parking, har yaje ya dawo kuma bacci take, ya ja motar ya dau hanyar airport hoping jirgin bazai tashi kafin su isa ba, suna isa airport din bayan yayi parking yaga saura minti sha biyar kawai jirgin ya tashi kamar yanda suka sa a ticket, tapping din kujeran motar yayi gently don har lkcn bacci Khaleesat take, a tsorace ta farka kamar yanda tayi daxu a eatry tana ganinsa kuma tayi shiru tana sauke ajiyar zuciya, ya bude ledan abincin da ya siya ya ciro mata takeaway din ya bata yace "Take a little before ur flight..." Ba musu ta amshi abincin tana kallonsa a hankali tace "Lagos din zan je?" Yace "In kin je zaki gani" Sai da ya hade mata rai sannan ta ci abincin cokali uku da kyar tana hadiyewa kamar magani, ya bude drugs dinta ya bata ta amsa ta sha da ruwan goran hannunta, without looking at her ya mika mata wayarsa yace "Saka min number mutumin nan" Zaro ido tayi tana kallonsa, yace "Ko bakya ji na ne?" Kamar zata yi kuka tace "Kiransa zaka yi?" Yace "Amsa ki sa min number sa nace" Hannunta na rawa ta amshi wayar ta saka masa lambar Abdul don tana da shi a kanta, ya amshi wayar yana kallon number sannan ya ajiye wayar yace "Dama an mashi alkawarin aurenki ne?" Ta sunkuyar da kanta cikin sanyin murya tace "Um, tun shekara hudu da suka wuce" Shiru Ajay yayi yana kallonta, but because of how cautious he is with time kar tayi missing flight dinta kawai ya ciro Eye drop din da ya siya mata ya mika mata ta diga a idonta, tsoro ya sa ta kasa digawa don bata san wani kalan azaba zata ji ba, daga karshe ya fixge eye drop din babu yabo babu fallasa ya diga mata a cikin idon, tuni ya sauka daga motar yana jiran in ta gama kururuwan da take ta sauko, daga karshe ta sauko daga cikin motar tana rufe idon da Hijab dinta, dayan wayarsa ya mika mata wanda ticket dinta ke ciki, daga ita sai handbag din ta da wayarsa ta nufi cikin airport din tana waige waige kamar iska zai kadeta ta fadi, kana ganinta kasan ba dai dai ta ke ba, she is traumatized and stressed, tsoron Abdul kuma ya gama shigarta sosai, shi dai yana tsaye jikin motarsa yana kallonta har ya ga shigarta cikin airport din, komawa cikin motarsa yayi yana duba full name din Abdul ta true caller, wani number yayi dialing yana fara ring aka daga yace "Zan turo maka wata number yanxu, ina son kasa a bincika min location dinsa a cikin garin kano, i will be waiting for feedback" Bayan ya katse wayar ya ajiye ya jinginar da kansa da kujeran motar, yana nan zaune har bayan 20 mins just to be sure bata yi missing flight dinta ba kafin ya bar airport din, Khaleesat ta dinga bin cikin jirgin da kallo kamar idanuwanta za su fito jin anyi announcing za su tashi zuwa garin Abuja, Abuja kuma? Ita wa ta sani a Abuja? Hawaye ne ya cika idonta ta dinga waige waigen cikin jirgin, me yasa ya mata booking ticket din Abuja. [5/28, 8:42 PM] khaleesat Haiydar ✍️: Khaleesat na zaune hall din da jama'a ke jiran Luggages dinsu a Arrival, duk da bata da kayan da zata jira amma rashin sanin inda ta nufa yasa ta zauna wajen tana bin kowa da kallo, tun 15 mins ago jirginsu ya sauka Abuja, daurewa kawai take don wani bacci take ji tare da gajiya, vibration taji a jakarta dake cinyarta alamar ana kiran waya, a hankali ta bude jakar ta ciro wayar da AJ ya bata tana kallon screen din, har ya katse bata daga ba don number kawai ta gani ba ayi saving ba bata san ko ta daga ba ko kar ta daga, kiran wayar da ake ta yi continuously ne yasa tayi picking tayi shiru tana sauraron me magana taji namiji ne, ta amsa sallaman da yayi mata, sannan yayi introducing kansa ya sanar mata shi ne ya zo daukanta Airport, a hankali Khaleesat tace "Ohk" Mikewa tayi ta fita daga Arrival din tana kalle kallen inda yace mata yake a Airport din, sai ga shi ya nufota bayan ya gane ita ya zo dauka, gaisheta yayi da ladabi yace "Babu kaya ko Hajiya?" Khaleesat ta gyada masa kai kawai, yace "Bismillah, Motar na can nayi parking" Tana biye da shi suka isa inda motar yake, ya bude mata back seat ta shiga ya kulle sannan ya zaga ya shiga driver seat, Ita dai Khaleesat ji tayi kawai yana sanar mata sun iso, bata san for how long suka yi tafiyar ba don bacci ne ya dauketa throughout the journey, gyara zama tayi tana kalle kallen compound din gidan da suke ciki, ta kalli Drivern da ya bude mata back seat, ta sauko a hankali tace "Nagode" Gida ne babba irin na zamani, tana biye da shi ya kai ta har zuwa Entrance din shiga babban parlon gidan ya danna bell, ba a dau lokaci ba aka bude kofar wata budurwa ce warce bazata wuce ta ba ta gani tsaye, da ladabi Drivern yace "Bakuwar da na dauko Airport ce Hajiya" Yarinyar ta ɗan yi murmushi ta koma gefe tana kallon Khaleesat tace "Sannu da zuwa sister, come in" Khaleesat ta shiga parlon yarinyar ta kullo kofar tana nuna mata kujera ta zauna, bayan Khaleesat ta zauna yarinyar na kallonta tace "I am Inteesar" Khaleesat ta daga idanuwanta ta kalleta tace "Sunana Khaleesat" Yarinyar tace "Welcome Khaleesat, bari in ma Ammin mu magana" Daga haka ta juya ta bar parlon, after a while sai ga ta sun shigo parlon da wata dattijuwa that is in her middle 50, zamowa kasa Khaleesat tayi a hankali tana gaisheta, da fara'a matar da ake kira da Ammi ta dagota tace "A'a, koma kiyi zamanki kan kujera diyata" Khaleesat ta koma ta zauna kan kujeran, Matar ta zauna kusa da ita tace "Sannu da zuwa, ya hanya?" Khaleesat tace "Alhmdlh, ina yini" Ammi tace "Lafiya lau, ya kika baro mutan gidan?" Khaleesat tace "Suna lafiya lau" Ammi tace "Ai na zata tare da Yariman ku ke, ashe ke kadai ce" Ita dai Khaleesat ta sunkuyar da kanta tayi shiru tana wasa da gefen hijab dinta, Ammi ta kalli Inteesar tace "Inteesar ki kai ta daki ta huta" Inteesar tace "Ohk" Tare suka tafi dakin Khaleesat na biye da ita, Ammi ta bi su da kallo. Wajen karfe takwas na dare Khaleesat na zaune daki tare da Inteesar da ta mayar da ita Television, ita dai a hankali take cin fruit salad din gabanta, tun zuwanta gidan in dai ta kalli Inteesar by mistake zata ga kallonta kawai take, da sun hada ido kuma sai Inteesar ta mata murmushi, Khaleesat wasn't bothered da kallon don farkon haduwarsu da Sophie haka ita ma take mata, tayi ta kallonta a makaranta ko gajiya bata yi kuma da sun hada ido sai ta mata murmushi, bayan sun zama best of friends ne Sophie ke gaya mata she is soo beautiful shi yasa bata gajiya da kallonta, sai bayan sun zama kawaye Sophie ta dena mata maganar kyanta, kuma dama da wuya taje waje bata ga mutane na kallonta ba, ba maza ba hatta yan uwanta mata haka suke kallonta, muryar Inteesar taji a hankali tace "You are Beautiful Khaleesat" Khaleesat ta ɗan kalleta sai kuma ta mayar mata da murmushin da take mata kawai, Inteesar tace "Sosai fa" Cikin sanyin murya Khaleesat tace "And you too Inteesar" Inteesar tayi dariya tace "A'a gaskiya ba kamarki ba, ni dai ina son mu zama frnds in baza ki damu ba, Ya Prince yace gobe zaki tafi Lagos da safe, don Allah ki bani numberki mu dinga zumunci ta waya, probably baza ki sake dawowa gidanmu ba" Sosai Khaleesat taji wani relieve ya zo mata bayan taji Inteesar tace zata tafi Lagos da safe, dama gaba daya hankalinta yayi gun kanwar Ummanta, Allah ya gani daurewa kawai take amma ita kadai tasan me take ji both mentally and physically, tana cikin tashin hankali sosai but she is trying her best to act normal, Khaleesat tace "Ohk amma nayi misplacing wayana ban yi welcome back, idan nayi zan amshi lambarki gun sa" Inteesar tace "Ohk to ba damuwa, amma zaki dade a lagos ne in kin je?" Khaleesat tace "Zan ɗan yi kwana biyu a can in sha Allah" Inteesar tace "Akwai sisterna dake aure can, idan baza su dawo gida for New year ba in sha Allah zan je Lagos din so that i will meet with you there" Murmushi Khaleesat tayi tace "Toh shikenan Allah ya kai mu lafiya" Inteesar ta tashi ta bude press ta dauko mata kayan baccinta don dakinta ta kawo Khaleesat, bayan ta ajiye kayan gefen gado tace "You can change to this idan kinyi wanka, i will be back later" Khaleesat tace "Alright, thank you so much" Bayan few minutes da fitan Inteesar Khaleesat ta tashi a hankali ta tafi bandaki, da ta tuna auren Abdul dake kanta tashin hankalinta ninkuwa yake, sai da ta ci kukanta me isarta sannan tayi wanka ta fito daga bandakin, ta gama saka kayan da Inteesar ta bata kenan tana kokarin daure gashinta sai ga ta ta shigo dakin, Inteesar ta wara ido tace "Waow is all that ur hair Khaleesat?" Khaleesat dai ta mata murmushin karfin hali tana ci gaba da daure gashinta, Inteesar that was looking at the hair with fascination tace "Bari in baki Hair net" Hair net dinta ta dauko ta ba Khaleesat, Khaleesat ta amsa tace "Nagode sosai" Washegari karfe tara da rabi na safe Khaleesat ta gama shiryawa tana jiran Drivern gidan, kayan Inteesar ne jikinta da yake yanayin jikinsu daya babu me cewa ba kayanta bane, tana zaune gefen gadon Inteesar duk da Hijab ne har kasa jikinta amma sanyi take ji sosai, ga AC dake dakin a kashe amma she is shivering, tun da ta tashi da asuba tasan she is not feeling okay, breakfast din ma da kyar ta sha shayi kawai, ko irish din bata ci ba balle bread, she is trying all possible best to look alright don kar ayi cancelling tafiyarta zuwa lagos yau, Mai aikin gidan ce ta Kwankwasa kofa ta sanar mata driver yana jiran ta, Khaleesat ta tashi da kyar ta dau handbag dinta ta fita daga dakin zuwa parlor, nan ta tarar da Ammi zaune, Khaleesat ta karasa ta duka kusa da ita tana mata godiya don sosai suka sake mata kamar da can sun taba saninta, daga karshe dai Inteesar ta bi su har Airport don rakiya, haka kawai jininta ya hadu da Khaleesat, ita kanta Khaleesat don bata cikin nutsuwarta ne amma she so much appreciate Inteesar's care toward her, a haka dai suka rabu kamar sun jima da sanin juna, Khaleesat ta shiga cikin airport din ta amshi boarding pass dinta don Ajay ya tura mata ticket ta Email din wayar da ya bata hade da hoton National ID dinta da yayi snapping tun karfe bakwai na safe, bayan ta amshi boarding pass dinta ta nufi Departure Lounge. Karfe sha biyu saura suka sauka garin Lagos, Khaleesat ta sauka a jirgi da taimakon wata mata don zazzabi ne sosai ya rufeta but she is still pretending to be fine, a haka suka fito Airport din daga Arrival matar na tambayarta za a zo daukanta ne ko Taxi xata hau, Kafin Khaleesat tace komai ta hango wani kamar AJ tsaye jikin wata mota yana danna wayarsa, sai da ta kifta ido ta bude to be sure he is the one she is seeing, ta kalli matar kusa da ita da kyar ta sanar mata yayanta ya zo daukanta, a haka suka rabu da matar, Khaleesat ta nufi inda ta hango Ajay, sae da ta iso kusa da motar ya daga kai ya kalleta, ta sunkuyar da kai a hankali tace "Ina yini" Calmly yace "Ina wayar da na baki?" Jakar hannunta ta nuna masa tace "Yana ciki, na sa silent ne" Driver seat ya bude ya shiga sannan ya bude mata daya side din motar, zagawa tayi ta shiga ta jinginar da kanta ta lumshe ido, ya tada motar suka bar Airport din, Google map yayi ta using after almost 45 mins ride Khaleesat ta fara gane inda za su, amma kuma sae ko ina yayi mata sabo a area din ko don she is not stabilize ne bata dai sani ba, ta juya ta kallesa shi dai driving dinsa kawai yake with the assistant of his google map, at last suka shigo wani unguwa yayi parking ya dau wayarsa yayi dialing number, muryar Aunty Farida taji bayan anyi picking, Khaleesat taji kamar an yaye mata ƙaso tamanin cikin damuwarta jin muryar kanwar Ummanta, bayan few minutes sae ga ta ta fito daga cikin wani gate, tun da AJ ya hangota daga nesa ya fahimci da ita yake waya don kana ganinta ka ga Khaleesat, yayi driving din motar har zuwa dai dai kofar gidan da ta fito, yana parking Khaleesat ta bude motar da sauri ta sauka da sauran last strength dinta ta nufi Aunty Farida ta fada jikita, Aunty Farida ta rikota da sauri kafin ta kai kasa, wata makociyarta ce ta taimaka mata suka rike Khaleesat suka shiga da ita cikin gidan, shi dai AJ na tsaye kusa da motarsa yana kallonsu har suka shiga ciki, sai kuma ya jingina da motarsa yana kallon yara dake wasa few houses away, wayarsa ya ciro jin yana ringing ganin me kiransa ya daga yace "Ya ake ciki?" Daga daya bangaren mutumin yace "Ranka shi dade sai daxu ya kunna wayar tasa, an kuma duba location din nasa yana cikin garin Abuja yanxu haka" AJ yayi shiru kafin yace "Ohk, i will get back to you nagode" Daga haka ya katse wayar ya mayar aljihunsa, sai ga Aunty Farida ta fito daga cikin gidan, yayi ƙasa da kansa ya gaisheta, ta amsa cikin sanyin murya tace "Sannu da kokari fa, Allah ya saka da alkhairi, mu shiga ciki sai mu yi magana ko" Bai ce mata komai ba ya bi bayanta zuwa cikin compound din, Compound ne me dauke da apartment uku self contain each, AJ ya tsaya daga balcony din apartment din bai shiga ba har sai da Aunty Farida ta kara lekowo ta masa magana sannan ya cire takalmansa ya shiga parlon ya zauna saman kujera yana kallon Khaleesat da ta juya baya kan 3 seater din da take kwance, Aunty Farida ta tafi kitchen dauko masa ruwa, ya ciro wayarsa yana dannawa absentmindedly, Sai ga Aunty Farida ta fito kitchen ta ajiye masa ruwan a kusa da shi sannan ta zauna, da damuwa tace "Sannu da kokari Junaid, Allah ya saka da alkhairi, mun gode sosai" AJ ya daga kansa ya kalleta yace "Amma dai kince bai san inda kike a lagos ba ko Aunty?" Aunty Farida tace "Gaskiya bai san nan gidan ba, tsohon gidan da na baro ne dai ya sani, shi ma wani lokaci ne da ta zo Lagos dubani bani da lafiya, ta zo da kwana uku sai ga shi shima ya zo, to yau wata hudu kenan da barina wancan Unguwan na dawo nan" Ajay dai yayi shiru idonsa a kasa, Aunty Farida tace "Kuma ba unguwa daya bane, shi wancan Unguwan da na baro a Ojota ne, daga can zuwa nan ma tafiya ce me zaman kansa, ba kuma wanda yasan nan na dawo" Ajay yace "Toh shikenan, jikinta da zafi ne?" Aunty Farida tace "Ehh na ji da zafi sosai gaskiya, makociyata da ta rike min ita muka shigo yanzu nurse ce, tace zata rubuta min magunguna in siyo mata" Ajay yace "Ohk, bari zan fita yanzu sai in siyo magunguna da allurai da drip ayi mata karin ruwa" Aunty Farida tace "To Allah ya saka da alkhairi, amma baka sha ko ruwa ba Junaid" Ajay ya ɗan yi murmushi yace "Bari in je in dawo dai" A haka ya fita daga parlon ya tafi pharmacy ya harhado mata magunguna da drip da allurai. Wata mace ce warce bazata wuce shekaru hamsin da bakwai ba zaune wani kantamemen parlor cikin isa, mai aikinta na duke gabanta tana yanke mata kumbar kafafuwanta, cikin fada take cewa "Banda ma naci irin naka dama ina kai ina er matsiyata? Er talakawa? Wanda cin yau da kyar na gobe da kyar, ai kai ba class dinta bane ta ko ina, you just stoop ur self so low Abdul, babu wanda ya isa da kai babu wanda zai baka shawara ka dauka, na rasa irin wannan taurin kai naka, tun asali i am against you marrying that poor wretched girl, kuma har gobe ba wai nayi na'am bane kawai bani da yanda zanyi da kai ne Babana, baka jin maganata ko na ubanka balle na yayarka, yanxu ina amfanin kaskantar da kai da matsiyaciyar tayi cikin talakawa yan uwanta a gaban gidan cin abinci, abu har police station, da mutuncinka da iliminka a maka haka? In zaka dau shawarata yanzu gwara kawai ka saketa case ya dawo sabo fil, uban me zaka ci da ita kuma bayan wannan abun da ta maka a idon duniya? Idan yarinya kake so ni duk inda zan shiga zan je in samar maka yarinya karama da ta fi ta komai kuma er gidan arziki ba tsiya ba, kai ko Nijar din ne ma ni sai in shirya inje da kaina in samo maka wata buzuwar er gidan arziki ba talakawa ba, kai ga ma er wata kawata shuwa Arab yanda kaga ita wannan da makale ma ita ma haka take tass da ita, ga gashi, sannan su ba talakawa bane" Wata matashiya ce er shekara 39 dake zaune parlon ita ma ta juya da sauri ta kalli warce ke magana tace "Momy ban gane abinda kike nufi ba? Wai nufinki ya saketa kenan?" A fusace Momyn tace "Toh uban me zai ci da ita idan bai saketa ba Meema? Er talakawa ce fa, a kanta aka fara kyau a duniya ne da bazai rabu da ita ba?" Warce ta kira da Meema ta girgiza kai tace "A'a wallahi Momy, ai idan ya rabu da ita yanzu ma ita da iyayenta ne suka ci riba, duk uban hidimar da yayi mata sai kice ya saketa daga karshe ko tausayinsa ba ki ji ba Momy? Ae wallahi bata isa ya saketa ba, ko don mu kuntata mata yanda ta kuntata ma Abdul baza mu yi fatan ya saketa ba, dole sai ta shigo gidan nan, balle shi ba mahaukaci bane da zae saketan, yarinyar da ya tura har America karatu duk don dai ta zama presentable cikin mutane kar a mana dariya daga karshe ta saka masa da wannan walakanci da tijara haka?" Abdul dake zaune parlon shi ma duk yana sauraronsu ya mike yace "In har aka ga na saketa to bana numfashi ne a duniya, kuma duk inda ma take zata dawo hannuna nan ba da jimawa ba kuwa, a nan ne zata gwammaci bata taɓa sanina a rayuwarta ba, i will make life a living hell for her" Momy ta tabe baki tace "Shi dama talaka ai bai gaji abun arziki ba, shi yasa babu ruwana da su ko da wasa, hanyar jirgi daban ta mota daban, kai ne da jajibe jajibenka kasa ubanka ya tafka asaran kusan miliyan dari akan matsiyaciyar yarinyar nan" Tuni Abdul ya fice daga parlon, Meema na kallon uwarsu tace "Ai ki ma dena maganar asaran miliyan dari Momy, don yanxu babu wannan zancen asaran nake ji" Momy dai ta tabe baki tana kallon me aikinta tace "Ke kar fa ki yanka ni inyi mugun bata maki rai yanzu, ya zaki dinga gaftare min naman yatsu" Hakuri mai aikin ta hau bata. Wajen karfe biyar na yamma Khaleesat ta ɗan kishingida a 3 seater, hannunta rike da bowl din pepper soup din da Aunty Farida tayi mata, gaba daya ta kasa shan pepper soup din Offals din, don jinsa take kamar magani a bakinta gashi har sannan jikinta babu kwari ga ciwon kai, ta kalli drip din dake hannunta taga ko quarter bai yi ba amma har ta gaji ta rasa inda zata sa kanta taji dadi, tun da AJ ya kawo magungunan da drip ya ajiye ya bar gidan har sannan bai dawo ba, ga abincinsa Aunty Farida ta zuba a cooler ta ajiye a tray tun daxu tana jiransa, tambayoyi ne da yawa ke yawo a zuciyar Aunty Farida tana son tambayar Khaleesat ko shine ya taɓa biya mata jirgi kwanaki da Umma bata da lafiya amma ganin yanayin da Khaleesat ke ciki ta bar duk tambayoyin nan a zuciyarta, Aunty Farida ta kalli Khaleesat tace "Ki daure ko kadan ne ki sha, ko in dama maki custard?" Khaleesat ta girgiza mata kai, dai dai nan aka kwankwasa kofar parlon, Aunty Farida ta mike ta yafa gyalenta sannan ta tafi ta bude kofar ta koma gefe, da sallama Ajay ya shigo parlon yana kallon Aunty Farida yace "Tare da brother dina muke" Aunty Farida tace "To ku shigo mana" a hankali Khaleesat ta gyara zamanta tana kallon Jay babu ko kiftawa, ganinsa ta dinga yi kamar a mafarki, Jay ya sauke kansa ya gaida Aunty Farida ta amsa da fara'a, sannan ya juya yana kallon Khaleesat shi ma babu ko kiftawa, lkci daya hawaye ya cika idonta tana kallonsa, walking slowly ya karasa har cikin parlon ya duka gabanta yana kallonta, a hankali yace "Are you feeling better now Housemate?" Da sauri ta gyada masa kai hawaye na sauka idonta, and truly she felt better immediately, shi dai AJ na tsaye yana kallonsu, haka Aunty farida da ta koma one sitter a sanyaye ta zauna, Jay yayi kasa da murya still looking at her yace "Kiyi hakuri, everything will be okay soon in sha Allah, i promise you" Ta gyada masa kai da sauri with so much hope from his assurance, yana kallon bowl din hannunta Softly yace "Take ur soup" Ba musu ta dau spoon din ta fara shan pepper soup din a hankali, Aunty Farida ta kalli Ajay tace "Baka zauna ba Junaid" Ajay ya sauke kansa ya karasa 2 seater ya zauna, Aunty Farida ta share hawayen da ya cika idonta, da kyar tace "Mu ma duk ba da son ran mu bane abubuwan nan ke faruwa haka ba, ba mu da yanda za mu yi ne kawai, amma babu nagartattun iyayen da za su dau er su su ba Abdul aure" [5/29, 8:10 PM] khaleesat Haiydar ✍️: Sai da Jay yaga Khaleesat ta ci pepper soup din me ɗan yawa sannan ya mike ya koma kusa da Ajay ya zauna, After a while Ajay yayi breaking din silence din da ya ziyarci parlon yace "Iya daukar nauyin karatun ta kawai yayi Aunty?" Aunty Farida zata yi magana wayarta ya fara ring, dauka tayi ganin Umma ce ke kiranta ta wayar makociyarsu Sha'awa, ta mike ta tafi dakinta don daga wayar, Ajay dai kallon Khaleesat yake kamar yanda Jay ke kallonta don har ta shanye pepper soup din, ta ajiye bowl din kasa tana kokarin disconnecting drip din hannunta ta yanda zata bar cannula din kawai, Jay ya mike yana kallonta yace "What happened? Do u want to ease ur self" Da kyar tana girgiza masa kai tace "I think i want throw up" Ya karasa cikin hanzari yayi disconnecting din mata, ta tashi ta wuce bandakin Aunty Farida da sauri tana toshe bakinta, sai ga Aunty Farida ta fito daga daki, ta kalli inda Khaleesat ke zaune ganin bata nan ta kalli kofar bandaki, zaunawa kan kujera tayi a sanyaye tana kallonsu tayi kasa da murya tace "Yanzu yayata ta kirani wai an zo an tafi da mahaifin Khaleesat" Da mamaki Jay da Ajay ke kallonta, Ajay yace "Kamar yaya kenan?" A sanyaye Aunty Farida tace "Baban Abdul din ne yasa aka je aka tafi da shi" Daga Ajay har Jay kallonta suke with confusion da kuma mamaki, fitowar Khaleesat daga bandaki ya sa Aunty Farida tayi shiru bata sake cewa komai ba, bayan Khaleesat ta kwanta kan 3 sitter din Aunty Farida ta juya tana kallonta tace "Ko zaki shiga daki a maida maki drip din?" Khaleesat ta gyada mata kai don ita ma ta gaji da kwanciyar kujeran, Aunty Farida ta mike tace "Bari in ma makociyata magana sai ta sa maki a daki" Daga haka ta fita daga parlon, after some minutes sai ga ta ta dawo da Neighbor dinta Bayerabiya, Khaleesat ta tashi ta koma dakin Aunty Farida, Bayerabiyar ta bi ta ciki ta sa mata drip din, ita dai Aunty Farida na zaune parlor tayi nisa tunanin da take har makociyarta ta fito ta tafi, Aunty Farida ta kalli su Ajay a hankali tace "To abinda yayata ta kirani ta gaya min kenan" Ajay yace "So suke a biya su kudin makarantar da ya dinga biya mata?" Aunty Farida ta girgiza kai tace "Ai ba iya kudin makaranta bane Junaid" Ajay yayi shiru yana kallonta, Jay yace "Bayan makaranta akwai wani abu na kudi da ya hadasu ne?" Aunty Farida tace "Kwarai kuwa.... Shekarun baya Malam Ali wanda shi ne mahaifin Khaleesat dreban babban mota ne, babu garin da baya zuwa da kaya a babban mota a fadin Nigeria, kuma motar tasa ce iyaka idan kana da lodi ya kai maka kayan ka har inda kake so sannan ka biyasa, har Nijar ya sha shiga da kaya daga nan Nigeria ta haka ma ya hadu da yayata Aunty Zahra'u warce ita ce mahaifiyar Khaleesat, don mu yan Nijar ne mahaifinmu har yanzu yana nan da ransa mahaifiyarmu ce dai Allah yayi ma rasuwa shekarun baya, to bayan ya auri yayata ya kawota Kano Nigeria ya ajiyeta cikin matansa biyu, bayan en watanni da auren shine na dawo wajen yayata tunda bata da kowa a Nigeria bata san kowa ba, nan rikona ya dawo hannunta a lkcn ina da shekara goma, tsangwama da kyara babu irin wanda ban sha ba a wajen kishiyoyin yayata, gashi bata iya ce masu komai tunda ita ma ba barin ta suka yi ba, mace ce me hakuri da kauda kai, in zanyi magana ma sai ta hanani, a haka ta samu makaranta ta saka ni tunda a can kasarmu ina karatu aka daukoni aka kawo mata, sai da tayi shekara biyar a gidan sannan Allah ya bata Khaleesat, Mahaifin Khaleesat na da rufin asirinsa sosai don haka bamu rasa komai a gidan ba sai zaman lafiya da kwanciyar hankali daga kishiyoyinta wani lokacin har da uwar mijin, jifa jifa mu kan kai ziyara Nijar gun iyayenmu da yan uwa da abokan arziki, bayan shekaru 12 da auro yayata a lkcn Khaleesat na da shekara bakwai sai abokan Mijin yayata da yan uwa suka dinga zugasa akan ya shiga siyasa ya nemi wani babban mukami zai samu tunda yana da jama'a sosai, kuma ba laifi yayi karatunsa, matansa ma suka dinga zugasa akan ya fito takara, yayata tayi kokarin ganin ta hanasa tunda bai rasa komai ba a sana'arsa ta dreban mota amma ya ki, haka nan ya daga babban motarsa ya siyar har da sabon gidan da ya fara ginawa a nan Ɗan Ladi na sidi, ya daga duk en kadarorinsa ya siyar ya shiga siyasa gadan gadan, duk matansa sai da ya biya masu Hajji suka tafi da mahaifiyarsa, ya kuma canza ma ko wacce kayan daki, ya ba kowa kudi a hannu, kusan mutane goma sha biyu ya biya ma Hajji a lkcn, banda matasan anguwa da ya dinga biya ma kudin makaranta, yayi ta facaka da kudi a karshe dai ya zo ya fadi zabe, duk wa enda suka dinga zugasa suka juya masa baya, Allah ya rufa masa asiri bai amshi bashin banki da wani abokinsa ke ta zugasa ya amsa ba kasancewar da zaben ya gabato bashi da kudi kuma a hannu, bayan faduwarsa zabe aka shiga yanayi na babu a gidan, cin yau da kyar na gobe da kyar ga yayata na da cikin yan biyu, dama gidan da yake haya me tsada tuni ya saki bayan kudin hayan sun kare muka dawo mariri gidan gadonsa da ya bari a walakance don saura kadan ya kyautar lokacin da yake campaign sai gashi gidan ya mana amfani ya rufa mana asiri, makaranta me tsada da yaran gidan ke zuwa duk ya ciresu suka dawo gida suka zauna babu karatu, iyayen basu yi dubaran mayar da su na gwamnati ba, duk muka shiga mawuyacin hali a gidan, sai sanda ya samu mota yake lodin kaya ya kai a biyasa, sanda babu mota kuma sai dai kowa ta ciyar da kanta a gidan, yana kuma fin wata da watanni bai samu ko da karamar mota ba, duk ka zo kofar gida zaka gansa a zaune babu abun yi shi ma duk ya fita hayyacinsa, tuni yayata ta siyar da kayan dakinta ta fara sana'a ina taimaka mata, ta kuma saka Khaleesat a makarantar da zata iya biya don Khaleesat ta taso da kwazo da hazaka ga ta yarinya ce me shiga rai ko don kalan fatarta, don a unguwan ma gidan buzaye ake kiran gidanmu, hatta Mahaifinta kiri kiri yake nuna yafi sonta a cikin sauran yaransa wanda hakan ya ja mata tsana da kyara a gun matansa da yan uwanta, ko sanda yake da mota a hannu tsaraba na musamman yake ma Khaleesat ko da bazai yi ma uwarta ba, ana haka yayata ashe duk cinikin da nake sai ta kwasa ta ba mijinta a boye ban sani ba, ga dai matansa duk da hali na babu da aka shiga a gidan basu bar yayata ba, kullum cikin hada mata tuggu da makirci ake wajen miji da uwarsa, cikin wannan yanayi yayata ta haifi yan biyunta wanda haihuwan da tayi na karshe kenan a gidan, a lkcn matsaloli har sun fi na da, jarin yayata ya karye kuma babu wani abu da zata siyar ta tada jarin, ga jegon yan biyu tana yi ga yunwa wani lkcn sai makota ke zubo abinci a kawo mata, iyayenmu a can Nijar ba masu karfi ba balle su taimaka mana, a haka na bi wata kawata zuwa nan garin Lagos tana siyar da abinci, kafin nan fa nayi aure har na fito, duka auren bai cika shekara daya ba, na auri wani abokin mahaifin Khaleesat, karayar arziki na samun Malam Ali na dinga fuskantar matsaloli gun mutumin da matansa uku wanda daga karshe ya sakeni dama ba saboda Allah yayi auren ba saboda kalan fata ta yayi, ina nan Lagos nake tallafa ma yayata da 'ya yanta uku, don bana son karatun Khaleesat ya tsaya duk da ta samu Foundation sosai sbda makarantar da ubanta ya sa ta ma a sanda yake da rufin asirinsa yafi na sauran yan uwanta tsada, na zo Lagos da yan shekaru yayata ta kirani wataran wai gashi an ba Baban Khaleesat babban mota har zai kai kaya kudu, matsaloli sun fara warwarewa tunda har an biyasa kudin kai kayan kuma kudade masu tsoka gashi har ya siya kayan abinci masu yawa ya ajiye a gida, tace in Maza in dawo gida kawai dama ita hankalinta ba a kwance yake da zamana a lagos ina sana'a ba, a haka ta takurani har sai da na dawo Kano, a sannan Khaleesat na da shekaru sha shidda tana kuma gab da gama secondary don da wuri aka sakata a makaranta, na dawo da wasu kwanaki ranan muna zaune tsakar gida da yamma sai ga mahaifin Khaleesat an shigo mana da shi ranga ranga ko motsin kirki bai yi, wanda duk gaba daya mun zata yana hanyar kudu har ya kusa Lagos, ga dai shi babu ko kwarzanen ciwo a jikinsa kuma wa enda suka kawosa suka ce ai daga asibiti ma aka taho da shi a can wajajen garin yarbawa, sannan kwanansa uku a asibiti aka sallamosa wasu mutane da suka shaidasa tunda dreba ne suka biya kudi aka sako sa a mota aka dawo da shi Kano, sosai hankalinmu yayi mugun tashi a wannan lokacin, sae da Malam Ali yayi kwana biyu a gida ana ta addu'a da neman taimako kafin ya farfado gaba daya har yana iya magana, nan fa yake sanar mana barayi ne suka kwace Trailer da kayan mutane a ciki bayan sun shaka masa wani farin abu, tashin hankalin da duk muka shiga bazai misaltu ba a lokacin, daga Trailern har kayan cikin trailern ya doshi miliyan dari da tamanin" Shiru Aunty Farida tayi tana goge hawayen dake zuba idonta, Jay that was shock ya kalli Ajay dake kallon Aunty Farida babu ko kiftawa jin zunzurutun amount din da ta kira, Aunty Farida na share idonta ta ci gaba tace "A ranan yan sanda sun kusa goma suka zo a motoci, a haka aka sa ma mahaifin Khaleesat ankwa ana jan sa kamar barawo aka fita da shi yaransa da matansa na kururuwa suna ihu, Khaleesat kadai ce bata motsa daga inda take zaune da littafi a hannunta ba sai hawaye kawai, duk aka cika kofar gidanmu babu masaka tsinke kai kace barawon gaske aka zo dauka, mun shiga tashin hankalin da baya faduwa a wannan rana, kuma duk mutanen da yayi ta biya ma Hajji a sanda yake da hali, da kuma mutanen da ya taimaka ma aka rasa wanda zai bi yaga inda ma aka kai sa, ashe daga kano Abuja aka nufa da shi, bayan dogon binkice aka gano trailern an yasar a wani gari an kuma juye duk kayan cikin trailern, dama me trailer daban, me kaya daban, adadin kayan cikin trailern kuma zai yi na miliyan dari, to ba kowa bane me kayan cikin trailern nan illa mahaifin Abdul, sam ba a yarda babu sa hannun Mahaifin Khaleesat a juye kayan cikin trailern ba, dama kuma yan unguwa na jin haushin ya samu lodi me yawa haka ya tafi kai kayan shi kadai ko yaron mota bai dauka ba, kuma ko wani dreba an san sa da yaron mota daya ko biyu, nan aka yi ta zuga baban Abdul akan kar ya yarda wai dama planning Baban Khaleesat yayi don ya taɓa yi ma wani mutum haka da dadewa yace barayi sun kwace kaya a hanya sai yafewa mutumin yayi, kuma wai don yaga Alhaji Musa wato mahaifin Abdul me kudi ne sosai shi yasa zai cucesa yace an sace kaya tunda yanxu ta kare masa bai da komai, kuma wallahi sharri ne ba haka Baban Khaleesat yake ba, bai cin kayan wani baya taɓa abu in ba nasa bane, beside bai taɓa sanin Baban Abdul ke da kayan ba sai da iftila'in ya faru sannan yaga me kayan, shi dai kawai ance masa ga Lodi zai kai lagos ya kuma amince tunda sana'ar sa kenan kuma kullum fatan samun Lodi yake, ko da babu zugin yan anguwa baban Abdul bai yi kama da mutumin da zai iya yafe kudinsa ba don kana ganinsa kasan bashi da mutunci bashi da kirki, sai da Mahaifin Khaleesat yayi wata uku bamu sa shi a idonmu ba kafin aka dawo da shi kano duk ya rame yayi baki ya dawo kamar ba shi ba, da kyar aka bari muka gansa a fursin da aka ajiyesa na nan kano, ranan duk bamu yi bacci ba bayan mun dawo gida, yayata ta shiga tashin hankali mara misaltuwa don tun dauke mahaifin Khaleesat dama ta fara alalan siyarwa don mu rufa ma kanmu asiri saboda ɗan jarin da nake da shi nima duk ya karye bani da komai, kafin ma a dawo da mahaifin Khaleesat kano sau uku muna zuwa gidan Alhaji Musa a Nassarawa GRA domin mu basa hakuri ko zai dubi halin da muke ciki ya taimaka a sake mana Baban Khaleesat amma duk aka mana koran kare, na farko masu gadi ne suka kore mu, na biyu Matarsa ranan ta rako baƙinta ta gan mu tayi mana cin mutunci ni da yayata da Baaba Gaje ta sa aka kore mu, na uku kuma ɗan cikinsa Abdul wanda dama shi kadai ne namiji a 'ya yansa, ana haka aka shiga kotu ko lauya baban Khaleesat bashi da tunda bamu da halin daukan Lauya, rana na farko da aka kawo Malam Ali kotu daga prison ni da Khaleesat da kishiyar yayata Mama Shatu ce muka je kotun don sauraron karan, to a ranan Abdul yaje kotun shi ma a matsayin daya daga lauyoyin mahaifinsa ashe shi ma Lauya ne, sarai na ganesa da na gansa a kotun don ranan karshe da muka je gidansu har ce ma masu gadi yayi in muka sake dawowa su rike mu yan sanda ne za su zo su tafi da mu, zaman kotu da akayi a wannan rana babu wani positive outcome da ke nuni da cewar da nasara a case din, kwata kwata babu alamun nasara tunda Malam Ali ba kowa bane, kuma ba shi da kowa bai da komi, bashi da wanda zai tsaya masa, haka aka dage shari'ar zuwa wani watan shi kuma za a maidasa prison cikin motar da ta kawosa ko belinsa anki badawa, Khaleesat ta dinga kuka sosai a haraban kotun tana kallon yanda aka shigar da babanta motar prison, nima ina rungume da ita ina hawaye, wanda wannan ne ya ja hankalin Abdul da fitowarsa daga kotun kenan zuwa kanta, ba shi ba hatta sauran jama'an wajen kallonta suke, Alhaji Musa babban mutum ne kuma me kudi wannan yasa har da yan jaridu a haraban kotun, wani ɗan jarida ya nufo mu yana tambayar me za mu iya cewa game da zaman da aka yi yau a kotu, budan bakin Khaleesat cikin kuka sai cewa tayi Allah ya saka ma babanta sharrin da aka masa, ina tunanin a nan ne Abdul ya fahimci er gidan wanda suke ƙara ce Khaleesat, duka duka shekarunta sha shidda a sannan amma duk wanda ya kalleta sai ya sake kallonta, ranan ma tsautsayi yasa ta fito babu Nikab duk da ba a shiga da Nikab amma duk inda zata bata fita babu Nikab, in ma bata sa ba uwarta zata tilastata ta saka, hatta nima bana fita babu shi haka Mahaifiyarta saboda bakin jama'a, kun ji inda Abdul ya fara ganin Khaleesat, a sannan kuma kawai motarsa ya shiga, sai wani Lauya me zaman kansa ya nufo mu, ya ja mu gefe yana kokarin calming din Khaleesat, nan ya tambayeni me ya faru, me ya kawo mu kotu, nayi briefing din masa komai nima ina kuka, ya tambayeni zuwa yaushe aka daga karan, na sanar masa, yace to in basa lambata in sha Allah anjima zai kirani yaga abinda za ayi akan case din kuma mu kwantar da hankalinmu, ko wayar bani da shi a sannan, instead sai na basa Address din unguwanmu Mariri, ita dai kishiyar yayata na zaune karkashin bishiya tayi tagumi, a haka muka bar kotu ranan rai babu dadi muka koma gida, bayan kwana biyu ranan da yamma wajen karfe shidda muna zaune tsakar gida ko wacce na fafutukar abinda zata dora ta ciyar da kanta da yaranta, don yanzu kowa takai takai a gidan, kishiyoyin yayata har sun sake 'ya yan su maza kanana suna fita almajiranci suna ciyar da kansu, matan kuma a dora masu talla su tafi can bakin kasuwa, yayata dama ina taimaka mata muna sana'a a gida, kudin waec din Khaleesat ne dai muka kasa hadawa gashi saura kwanaki kadan a fara, kamar daga sama sai ga Mahaifin Khaleesat ya shigo gidan kamar an jefosa, Khaleesat ce ta fara ganinsa ta tafi da gudu ta rungumesa, duk muka mike tsaye a tsorace muna kallon ikon Allah baki bude, yayata tayi karfin halin tunkararsa tana tambayarsa daga ina yake haka, kar dai gudowa yayi daga gidan yari, Baban Khaleesat yace kawai shi dai ce masa aka yi an bada belinsa daxu da rana, sai gashi kuma aka daukosa aka kawo har gida aka ajiyesa, tsabar mamaki duk muka kasa cewa komai a tsakar gidan, yayata ta kama hannunsa hawaye cike idonta ta kai sa dakinsa don shi ma duk a firgice yake kana ganinsa kasan ba karamin wahala ya sha ba, sai a sannan yaran gidan suka fara ihu suna murnan dawowan mahaifinsu suna ta tsalle tsalle, sauran matan duk suka bi bayan yayata zuwa dakin Baban Khaleesat" [5/30, 7:48 PM] khaleesat Haiydar ✍️: Khaleesat na zaune hall din da jama'a ke jiran Luggages dinsu a Arrival, duk da bata da kayan da zata jira amma rashin sanin inda ta nufa yasa ta zauna wajen tana bin kowa da kallo, tun 15 mins ago jirginsu ya sauka Abuja, daurewa kawai take don wani bacci take ji tare da gajiya, vibration taji a jakarta dake cinyarta alamar ana kiran waya, a hankali ta bude jakar ta ciro wayar da AJ ya bata tana kallon screen din, har ya katse bata daga ba don number kawai ta gani ba ayi saving ba bata san ko ta daga ba ko kar ta daga, kiran wayar da ake ta yi continuously ne yasa tayi picking tayi shiru tana sauraron me magana taji namiji ne, ta amsa sallaman da yayi mata, sannan yayi introducing kansa ya sanar mata shi ne ya zo daukanta Airport, a hankali Khaleesat tace "Ohk" Mikewa tayi ta fita daga Arrival din tana kalle kallen inda yace mata yake a Airport din, sai ga shi ya nufota bayan ya gane ita ya zo dauka, gaisheta yayi da ladabi yace "Babu kaya ko Hajiya?" Khaleesat ta gyada masa kai kawai, yace "Bismillah, Motar na can nayi parking" Tana biye da shi suka isa inda motar yake, ya bude mata back seat ta shiga ya kulle sannan ya zaga ya shiga driver seat, Ita dai Khaleesat ji tayi kawai yana sanar mata sun iso, bata san for how long suka yi tafiyar ba don bacci ne ya dauketa throughout the journey, gyara zama tayi tana kalle kallen compound din gidan da suke ciki, ta kalli Drivern da ya bude mata back seat, ta sauko a hankali tace "Nagode" Gida ne babba irin na zamani, tana biye da shi ya kai ta har zuwa Entrance din shiga babban parlon gidan ya danna bell, ba a dau lokaci ba aka bude kofar wata budurwa ce warce bazata wuce ta ba ta gani tsaye, da ladabi Drivern yace "Bakuwar da na dauko Airport ce Hajiya" Yarinyar ta ɗan yi murmushi ta koma gefe tana kallon Khaleesat tace "Sannu da zuwa sister, come in" Khaleesat ta shiga parlon yarinyar ta kullo kofar tana nuna mata kujera ta zauna, bayan Khaleesat ta zauna yarinyar na kallonta tace "I am Inteesar" Khaleesat ta daga idanuwanta ta kalleta tace "Sunana Khaleesat" Yarinyar tace "Welcome Khaleesat, bari in ma Ammin mu magana" Daga haka ta juya ta bar parlon, after a while sai ga ta sun shigo parlon da wata dattijuwa that is in her middle 50, zamowa kasa Khaleesat tayi a hankali tana gaisheta, da fara'a matar da ake kira da Ammi ta dagota tace "A'a, koma kiyi zamanki kan kujera diyata" Khaleesat ta koma ta zauna kan kujeran, Matar ta zauna kusa da ita tace "Sannu da zuwa, ya hanya?" Khaleesat tace "Alhmdlh, ina yini" Ammi tace "Lafiya lau, ya kika baro mutan gidan?" Khaleesat tace "Suna lafiya lau" Ammi tace "Ai na zata tare da Yariman ku ke, ashe ke kadai ce" Ita dai Khaleesat ta sunkuyar da kanta tayi shiru tana wasa da gefen hijab dinta, Ammi ta kalli Inteesar tace "Inteesar ki kai ta daki ta huta" Inteesar tace "Ohk" Tare suka tafi dakin Khaleesat na biye da ita, Ammi ta bi su da kallo. Wajen karfe takwas na dare Khaleesat na zaune daki tare da Inteesar da ta mayar da ita Television, ita dai a hankali take cin fruit salad din gabanta, tun zuwanta gidan in dai ta kalli Inteesar by mistake zata ga kallonta kawai take, da sun hada ido kuma sai Inteesar ta mata murmushi, Khaleesat wasn't bothered da kallon don farkon haduwarsu da Sophie haka ita ma take mata, tayi ta kallonta a makaranta ko gajiya bata yi kuma da sun hada ido sai ta mata murmushi, bayan sun zama best of friends ne Sophie ke gaya mata she is soo beautiful shi yasa bata gajiya da kallonta, sai bayan sun zama kawaye Sophie ta dena mata maganar kyanta, kuma dama da wuya taje waje bata ga mutane na kallonta ba, ba maza ba hatta yan uwanta mata haka suke kallonta, muryar Inteesar taji a hankali tace "You are Beautiful Khaleesat" Khaleesat ta ɗan kalleta sai kuma ta mayar mata da murmushin da take mata kawai, Inteesar tace "Sosai fa" Cikin sanyin murya Khaleesat tace "And you too Inteesar" Inteesar tayi dariya tace "A'a gaskiya ba kamarki ba, ni dai ina son mu zama frnds in baza ki damu ba, Ya Prince yace gobe zaki tafi Lagos da safe, don Allah ki bani numberki mu dinga zumunci ta waya, probably baza ki sake dawowa gidanmu ba" Sosai Khaleesat taji wani relieve ya zo mata bayan taji Inteesar tace zata tafi Lagos da safe, dama gaba daya hankalinta yayi gun kanwar Ummanta, Allah ya gani daurewa kawai take amma ita kadai tasan me take ji both mentally and physically, tana cikin tashin hankali sosai but she is trying her best to act normal, Khaleesat tace "Ohk amma nayi misplacing wayana ban yi welcome back, idan nayi zan amshi lambarki gun sa" Inteesar tace "Ohk to ba damuwa, amma zaki dade a lagos ne in kin je?" Khaleesat tace "Zan ɗan yi kwana biyu a can in sha Allah" Inteesar tace "Akwai sisterna dake aure can, idan baza su dawo gida for New year ba in sha Allah zan je Lagos din so that i will meet with you there" Murmushi Khaleesat tayi tace "Toh shikenan Allah ya kai mu lafiya" Inteesar ta tashi ta bude press ta dauko mata kayan baccinta don dakinta ta kawo Khaleesat, bayan ta ajiye kayan gefen gado tace "You can change to this idan kinyi wanka, i will be back later" Khaleesat tace "Alright, thank you so much" Bayan few minutes da fitan Inteesar Khaleesat ta tashi a hankali ta tafi bandaki, da ta tuna auren Abdul dake kanta tashin hankalinta ninkuwa yake, sai da ta ci kukanta me isarta sannan tayi wanka ta fito daga bandakin, ta gama saka kayan da Inteesar ta bata kenan tana kokarin daure gashinta sai ga ta ta shigo dakin, Inteesar ta wara ido tace "Waow is all that ur hair Khaleesat?" Khaleesat dai ta mata murmushin karfin hali tana ci gaba da daure gashinta, Inteesar that was looking at the hair with fascination tace "Bari in baki Hair net" Hair net dinta ta dauko ta ba Khaleesat, Khaleesat ta amsa tace "Nagode sosai" Washegari karfe tara da rabi na safe Khaleesat ta gama shiryawa tana jiran Drivern gidan, kayan Inteesar ne jikinta da yake yanayin jikinsu daya babu me cewa ba kayanta bane, tana zaune gefen gadon Inteesar duk da Hijab ne har kasa jikinta amma sanyi take ji sosai, ga AC dake dakin a kashe amma she is shivering, tun da ta tashi da asuba tasan she is not feeling okay, breakfast din ma da kyar ta sha shayi kawai, ko irish din bata ci ba balle bread, she is trying all possible best to look alright don kar ayi cancelling tafiyarta zuwa lagos yau, Mai aikin gidan ce ta Kwankwasa kofa ta sanar mata driver yana jiran ta, Khaleesat ta tashi da kyar ta dau handbag dinta ta fita daga dakin zuwa parlor, nan ta tarar da Ammi zaune, Khaleesat ta karasa ta duka kusa da ita tana mata godiya don sosai suka sake mata kamar da can sun taba saninta, daga karshe dai Inteesar ta bi su har Airport don rakiya, haka kawai jininta ya hadu da Khaleesat, ita kanta Khaleesat don bata cikin nutsuwarta ne amma she so much appreciate Inteesar's care toward her, a haka dai suka rabu kamar sun jima da sanin juna, Khaleesat ta shiga cikin airport din ta amshi boarding pass dinta don Ajay ya tura mata ticket ta Email din wayar da ya bata hade da hoton National ID dinta da yayi snapping tun karfe bakwai na safe, bayan ta amshi boarding pass dinta ta nufi Departure Lounge. Karfe sha biyu saura suka sauka garin Lagos, Khaleesat ta sauka a jirgi da taimakon wata mata don zazzabi ne sosai ya rufeta but she is still pretending to be fine, a haka suka fito Airport din daga Arrival matar na tambayarta za a zo daukanta ne ko Taxi xata hau, Kafin Khaleesat tace komai ta hango wani kamar AJ tsaye jikin wata mota yana danna wayarsa, sai da ta kifta ido ta bude to be sure he is the one she is seeing, ta kalli matar kusa da ita da kyar ta sanar mata yayanta ya zo daukanta, a haka suka rabu da matar, Khaleesat ta nufi inda ta hango Ajay, sae da ta iso kusa da motar ya daga kai ya kalleta, ta sunkuyar da kai a hankali tace "Ina yini" Calmly yace "Ina wayar da na baki?" Jakar hannunta ta nuna masa tace "Yana ciki, na sa silent ne" Driver seat ya bude ya shiga sannan ya bude mata daya side din motar, zagawa tayi ta shiga ta jinginar da kanta ta lumshe ido, ya tada motar suka bar Airport din, Google map yayi ta using after almost 45 mins ride Khaleesat ta fara gane inda za su, amma kuma sae ko ina yayi mata sabo a area din ko don she is not stabilize ne bata dai sani ba, ta juya ta kallesa shi dai driving dinsa kawai yake with the assistant of his google map, at last suka shigo wani unguwa yayi parking ya dau wayarsa yayi dialing number, muryar Aunty Farida taji bayan anyi picking, Khaleesat taji kamar an yaye mata ƙaso tamanin cikin damuwarta jin muryar kanwar Ummanta, bayan few minutes sae ga ta ta fito daga cikin wani gate, tun da AJ ya hangota daga nesa ya fahimci da ita yake waya don kana ganinta ka ga Khaleesat, yayi driving din motar har zuwa dai dai kofar gidan da ta fito, yana parking Khaleesat ta bude motar da sauri ta sauka da sauran last strength dinta ta nufi Aunty Farida ta fada jikita, Aunty Farida ta rikota da sauri kafin ta kai kasa, wata makociyarta ce ta taimaka mata suka rike Khaleesat suka shiga da ita cikin gidan, shi dai AJ na tsaye kusa da motarsa yana kallonsu har suka shiga ciki, sai kuma ya jingina da motarsa yana kallon yara dake wasa few houses away, wayarsa ya ciro jin yana ringing ganin me kiransa ya daga yace "Ya ake ciki?" Daga daya bangaren mutumin yace "Ranka shi dade sai daxu ya kunna wayar tasa, an kuma duba location din nasa yana cikin garin Abuja yanxu haka" AJ yayi shiru kafin yace "Ohk, i will get back to you nagode" Daga haka ya katse wayar ya mayar aljihunsa, sai ga Aunty Farida ta fito daga cikin gidan, yayi ƙasa da kansa ya gaisheta, ta amsa cikin sanyin murya tace "Sannu da kokari fa, Allah ya saka da alkhairi, mu shiga ciki sai mu yi magana ko" Bai ce mata komai ba ya bi bayanta zuwa cikin compound din, Compound ne me dauke da apartment uku self contain each, AJ ya tsaya daga balcony din apartment din bai shiga ba har sai da Aunty Farida ta kara lekowo ta masa magana sannan ya cire takalmansa ya shiga parlon ya zauna saman kujera yana kallon Khaleesat da ta juya baya kan 3 seater din da take kwance, Aunty Farida ta tafi kitchen dauko masa ruwa, ya ciro wayarsa yana dannawa absentmindedly, Sai ga Aunty Farida ta fito kitchen ta ajiye masa ruwan a kusa da shi sannan ta zauna, da damuwa tace "Sannu da kokari Junaid, Allah ya saka da alkhairi, mun gode sosai" AJ ya daga kansa ya kalleta yace "Amma dai kince bai san inda kike a lagos ba ko Aunty?" Aunty Farida tace "Gaskiya bai san nan gidan ba, tsohon gidan da na baro ne dai ya sani, shi ma wani lokaci ne da ta zo Lagos dubani bani da lafiya, ta zo da kwana uku sai ga shi shima ya zo, to yau wata hudu kenan da barina wancan Unguwan na dawo nan" Ajay dai yayi shiru idonsa a kasa, Aunty Farida tace "Kuma ba unguwa daya bane, shi wancan Unguwan da na baro a Ojota ne, daga can zuwa nan ma tafiya ce me zaman kansa, ba kuma wanda yasan nan na dawo" Ajay yace "Toh shikenan, jikinta da zafi ne?" Aunty Farida tace "Ehh na ji da zafi sosai gaskiya, makociyata da ta rike min ita muka shigo yanzu nurse ce, tace zata rubuta min magunguna in siyo mata" Ajay yace "Ohk, bari zan fita yanzu sai in siyo magunguna da allurai da drip ayi mata karin ruwa" Aunty Farida tace "To Allah ya saka da alkhairi, amma baka sha ko ruwa ba Junaid" Ajay ya ɗan yi murmushi yace "Bari in je in dawo dai" A haka ya fita daga parlon ya tafi pharmacy ya harhado mata magunguna da drip da allurai. Wata mace ce warce bazata wuce shekaru hamsin da bakwai ba zaune wani kantamemen parlor cikin isa, mai aikinta na duke gabanta tana yanke mata kumbar kafafuwanta, cikin fada take cewa "Banda ma naci irin naka dama ina kai ina er matsiyata? Er talakawa? Wanda cin yau da kyar na gobe da kyar, ai kai ba class dinta bane ta ko ina, you just stoop ur self so low Abdul, babu wanda ya isa da kai babu wanda zai baka shawara ka dauka, na rasa irin wannan taurin kai naka, tun asali i am against you marrying that poor wretched girl, kuma har gobe ba wai nayi na'am bane kawai bani da yanda zanyi da kai ne Babana, baka jin maganata ko na ubanka balle na yayarka, yanxu ina amfanin kaskantar da kai da matsiyaciyar tayi cikin talakawa yan uwanta a gaban gidan cin abinci, abu har police station, da mutuncinka da iliminka a maka haka? In zaka dau shawarata yanzu gwara kawai ka saketa case ya dawo sabo fil, uban me zaka ci da ita kuma bayan wannan abun da ta maka a idon duniya? Idan yarinya kake so ni duk inda zan shiga zan je in samar maka yarinya karama da ta fi ta komai kuma er gidan arziki ba tsiya ba, kai ko Nijar din ne ma ni sai in shirya inje da kaina in samo maka wata buzuwar er gidan arziki ba talakawa ba, kai ga ma er wata kawata shuwa Arab yanda kaga ita wannan da makale ma ita ma haka take tass da ita, ga gashi, sannan su ba talakawa bane" Wata matashiya ce er shekara 39 dake zaune parlon ita ma ta juya da sauri ta kalli warce ke magana tace "Momy ban gane abinda kike nufi ba? Wai nufinki ya saketa kenan?" A fusace Momyn tace "Toh uban me zai ci da ita idan bai saketa ba Meema? Er talakawa ce fa, a kanta aka fara kyau a duniya ne da bazai rabu da ita ba?" Warce ta kira da Meema ta girgiza kai tace "A'a wallahi Momy, ai idan ya rabu da ita yanzu ma ita da iyayenta ne suka ci riba, duk uban hidimar da yayi mata sai kice ya saketa daga karshe ko tausayinsa ba ki ji ba Momy? Ae wallahi bata isa ya saketa ba, ko don mu kuntata mata yanda ta kuntata ma Abdul baza mu yi fatan ya saketa ba, dole sai ta shigo gidan nan, balle shi ba mahaukaci bane da zae saketan, yarinyar da ya tura har America karatu duk don dai ta zama presentable cikin mutane kar a mana dariya daga karshe ta saka masa da wannan walakanci da tijara haka?" Abdul dake zaune parlon shi ma duk yana sauraronsu ya mike yace "In har aka ga na saketa to bana numfashi ne a duniya, kuma duk inda ma take zata dawo hannuna nan ba da jimawa ba kuwa, a nan ne zata gwammaci bata taɓa sanina a rayuwarta ba, i will make life a living hell for her" Momy ta tabe baki tace "Shi dama talaka ai bai gaji abun arziki ba, shi yasa babu ruwana da su ko da wasa, hanyar jirgi daban ta mota daban, kai ne da jajibe jajibenka kasa ubanka ya tafka asaran kusan miliyan dari akan matsiyaciyar yarinyar nan" Tuni Abdul ya fice daga parlon, Meema na kallon uwarsu tace "Ai ki ma dena maganar asaran miliyan dari Momy, don yanxu babu wannan zancen asaran nake ji" Momy dai ta tabe baki tana kallon me aikinta tace "Ke kar fa ki yanka ni inyi mugun bata maki rai yanzu, ya zaki dinga gaftare min naman yatsu" Hakuri mai aikin ta hau bata. Wajen karfe biyar na yamma Khaleesat ta ɗan kishingida a 3 seater, hannunta rike da bowl din pepper soup din da Aunty Farida tayi mata, gaba daya ta kasa shan pepper soup din Offals din, don jinsa take kamar magani a bakinta gashi har sannan jikinta babu kwari ga ciwon kai, ta kalli drip din dake hannunta taga ko quarter bai yi ba amma har ta gaji ta rasa inda zata sa kanta taji dadi, tun da AJ ya kawo magungunan da drip ya ajiye ya bar gidan har sannan bai dawo ba, ga abincinsa Aunty Farida ta zuba a cooler ta ajiye a tray tun daxu tana jiransa, tambayoyi ne da yawa ke yawo a zuciyar Aunty Farida tana son tambayar Khaleesat ko shine ya taɓa biya mata jirgi kwanaki da Umma bata da lafiya amma ganin yanayin da Khaleesat ke ciki ta bar duk tambayoyin nan a zuciyarta, Aunty Farida ta kalli Khaleesat tace "Ki daure ko kadan ne ki sha, ko in dama maki custard?" Khaleesat ta girgiza mata kai, dai dai nan aka kwankwasa kofar parlon, Aunty Farida ta mike ta yafa gyalenta sannan ta tafi ta bude kofar ta koma gefe, da sallama Ajay ya shigo parlon yana kallon Aunty Farida yace "Tare da brother dina muke" Aunty Farida tace "To ku shigo mana" a hankali Khaleesat ta gyara zamanta tana kallon Jay babu ko kiftawa, ganinsa ta dinga yi kamar a mafarki, Jay ya sauke kansa ya gaida Aunty Farida ta amsa da fara'a, sannan ya juya yana kallon Khaleesat shi ma babu ko kiftawa, lkci daya hawaye ya cika idonta tana kallonsa, walking slowly ya karasa har cikin parlon ya duka gabanta yana kallonta, a hankali yace "Are you feeling better now Housemate?" Da sauri ta gyada masa kai hawaye na sauka idonta, and truly she felt better immediately, shi dai AJ na tsaye yana kallonsu, haka Aunty farida da ta koma one sitter a sanyaye ta zauna, Jay yayi kasa da murya still looking at her yace "Kiyi hakuri, everything will be okay soon in sha Allah, i promise you" Ta gyada masa kai da sauri with so much hope from his assurance, yana kallon bowl din hannunta Softly yace "Take ur soup" Ba musu ta dau spoon din ta fara shan pepper soup din a hankali, Aunty Farida ta kalli Ajay tace "Baka zauna ba Junaid" Ajay ya sauke kansa ya karasa 2 seater ya zauna, Aunty Farida ta share hawayen da ya cika idonta, da kyar tace "Mu ma duk ba da son ran mu bane abubuwan nan ke faruwa haka ba, ba mu da yanda za mu yi ne kawai, amma babu nagartattun iyayen da za su dau er su su ba Abdul aure" *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* Alhamdulillah! Shin kunada labarin MG’s Beauty Lounge zai buɗe a ranar Litinin, 2nd June 2025 – daidai lokacin Sallah!😍 ‘Yan mata da mata masu son kyau a Kaduna, lokaci yayi da za ku haskaka a wannan Sallah! MG’s Beauty Lounge ya buɗe da kwalliya, tsafta da ƙamshi irin na sarauniyar zamani! Ga abin da zaki samu idan kika ziyarce mu: Gyaran gashi da kitson zamani Kwalliyar Sallah mai ɗaukar ido Wanke ƙafafu da pedicure mai sanyaya rai Kayan gyaran fata na gaske Lalle mai kyau da salo na zamani Tura-turai, humra, incense da ƙamshi masu daɗi Shirin amare da na musamman Ba kawai gyara muke ba – kulawa ce ta musamman ga kowace sarauniya. Zo ki ji daɗin wanke ƙafa, lalle, kwalliya, ki saya kayan kyau da ƙamshi – komai a wuri guda mai kyau. Adireshi: Block 21, Nnamdi Azikiwe by Makarfi Road, bayan gidan Indomie, kusa da Sorera Restaurant, Kinkinau, Kaduna. Tambaya/Booking: WhatsApp: 08062991549 Kira: 09016108092 / 08064532391 Ki zo ki gani da idonki – ki ji daɗin sauyin MG’s Beauty Lounge. Bi mu a IG & TikTok: @MGsBeautyLounge [5/30, 8:55 PM] khaleesat Haiydar ✍️: *Gaisuwa da fatan alkhairi zuwa ga me kasuwar garin Dutse Hajiya Aunty Zahrah da Hajjaju Sadiya Chamo Ex in-law, Hajiya Nafeesah Mom twins da Ummu Zainab Maman Ramla, Aunty Maryam Dan Ladi nasidi kema na gaisheki da katon murya, Hajiya Jumare da Hajiya Asmy me kayan amare, Oum Nabeelah, Mardiyyah, Uwar Janan, Halysah Garba 😂 i hail you all with respect yan Palace* ‍❤‍🩹 ❤‍🩹 Manyan Membobin _❤‍🩹Khaleesat's Citadel_❤‍🩹 *Su Meenah parrot🐔, Oum Noor, Nafeesah Jawwad, Rukayya, Fidomashi, Siyam, M manal, Mrs Barrister, Shanono Esq, Ummilos, Na'imatu, Zulaiha, Ummu Abdrhm, Khaleesat Haiydar is saying a big thank you to you all for ur support always, Allah ya bar min ku*🥰 Aunty Farida ta numfasa a hankali tace "Da yake Abdul shi kadai ne namiji gun mahaifinsa, mahaifin ya dauki son duniya ya dora masa kuma bai jin maganar kowa sai nasa, duk abinda Abdul yake so shi mahaifinsa ke so, bayan yaga Khaleesat a kotu babu tantama zuwa yayi ya samu uban ya nuna yana sonta zai kuma aureta, wannan dalili yasa babu bata lokaci suka janye kara a kotu suka bar maganar miliyan dari da sharadin Malam Ali zai ba Abdul auren er sa Khaleesat, mu dai har yau bamu san ko da wata yarjejeniya da aka yi a kotun ba ko babu, mun dai san an janye kara kawai kuma duk muka yi farin ciki sosai da hakan, burin mu kawai Malam Ali ya dawo gare mu ko da bazai tsinana mu da komai ba amma mu dinga ganinsa a tare da mu a matsayin kantangar gida, balle duk mun san yayi ma iyalansa hidima dai dai gwargwado ya kuma kyautata masu yanda ya kamata, jarabawa ce kawai ta fada masa, bana mantawa Khaleesat ta shiga damuwa sosai a lkcn tana ta koke koke wai ita bata son Abdul tun ma bata san kalansa ba bata gansa ba tace bata sonsa bazata iya aurensa ba, mu kam idonmu duk ya rufe da son ganin an wanke Malam Ali daga laifin da ake zarginsa da shi, ni da uwarta muka yi ta bata baki muna kwantar mata da hankali muka ce ko tafi son a maida mahaifinta prison ne, ko don mahaifinta bazata hakura ba ta amince da bukatar Abdul na son aurenta don case din ya mutu gaba daya, gashi tun bayan dawowar Malam Ali yayi ta rashin lafiya ko kudin kai sa asibiti babu, duba da hakan ne ma yasa muka yi ta karfafa ma Khaleesat gwiwa muna bata baki, a haka dai muka samu muka lallabata ta fara hakura, nan kishiyoyin Ummanta suka fito da baƙin cikinsu da hassada a fili tunda su ma ai suna da 'ya ya mata sa'annin Khaleesat da ma wa enda suka girmeta amma shine Abdul zai ce sai Khaleesat, nan fa duk suka hau gaba sosai da yayata saboda ɗan mai kudi ya ga Khaleesat yace yana so, ranan farko da Abdul ya fara zuwa unguwan cewa yayi shi bazai shigo da motarsa layin ba ta fito bakin titi ta samesa, gashi daga gidan zuwa bakin titi akwai tafiya sosai, haka nan uwar ta lallabata ta shirya ta saka nikab dinta kannenta biyu suka rakata har bakin titin ta samesa, a ranan kuma ya bata babban waya ya kuma hadata da dubu hamsin, ba ma ita ta amsa ba don nuna masa tayi bata so shine ya ba kannenta yayi tafiyarsa, da kudin aka samu aka biya mata waec dinta tunda ba mu da yanda za mu yi, a kaf tarihi ban taɓa jin wanda yake neman yarinya da isa da gadara da walakanci kamar Abdul ba, for almost 2 months in Abdul zai zo unguwan mu sai dai dole ta fito titi ta samesa shi bazai shiga layin da motarsa ba, watarana ne ya kira bata da lafiya shine da ya tashi zuwa dubata da yamma ya shigo layin a karo na farko tunda ya fara zuwa gurin ta, daga nan kuma ya dena cewa ta fito bakin titi in ya zo sai dai ya karasa ciki da motarsa, ya kai ya kawo har cikin gida yana shigowa, tun a wannan lokacin Abdul baya raga ma Khaleesat, fadan yau daban na gobe daban, bashi da fahimta bashi da uxuri, ga nuna isa da gadara abinda yace yake so dole shi zata yi, haka nan yarinyar nan ke hakuri da halinsa duk don saboda mahaifinta, rana daddaya ne baya sa ta kuka, sai dai ni da uwarta mu yi ta bata hakuri muna ganin duk me sauki ne tunda har yana sonta kuma yaji zai aureta ya zauna da ita wataran zata canza sa da kanta, ni dai a sanda na fara sarewa da lamarin Abdul jikina yayi sanyi shine watarana da ya daga hannu ya mareta har sai da shatin yatsunsa ya kwanta fuskarta, mu dai har yau bata gaya mana me tayi masa da yayi mata haka ba don a cikin motarsa hakan ya faru, nan jikin uwarta ma ya fara sanyi kan lamarin har ta samu Mai gidanta ta gaya masa amma Malam Ali yayi ta kakkarewa har da cewa duk wanda ma ya kara tada maganar Allah ya isa, ana haka har ya biya mata jamb ya kai ta da kansa ta zana don fara jami'a tunda waec dinta ya fito kuma sakamakonta yayi kyau sosai, kawai rana daya kwatsam ubansa ya kira mahaifinta wai ga abinda Abdul yace yake so, wato zai tura Khaleesat Amurka tayi karatu a can, duk kawaicin da yayata take wannan karan sai da ta nuna bata amince da hakan ba, don ana ta bin su a yanda suke so ba hakan ke nufin bamu da ta cewa akan lamarin Khaleesat ba, ba Yayata ba har kakar Khaleesat Nenne ta nuna rashin amincewarta a wannan bukatar tasu, babu ta yanda za a dau yarinya karama haka da ko mallakan hankalinta bata gama yi ba ace za a tura ta har Amurka da sunan karatu, in haka ne kawai a daura auren mana sai ya kai ta duk inda ma zai kai ta tayi karatu, in ko ba haka ba babu inda er ta zata je da sunan karatu sai dai duk abinda zai faru ya faru, a nan dai laifin Mahaifin Khaleesat ne da ya dau tsoron duniya ya dora ma Abdul da mahaifinsa ba kuma tsoron komai ba sai tsoron kar su sake maidasa inda ya baro wato prison, dama tunda ya baro can ya dawo gashi nan gashin nan dai kamar ya ɗan samu matsala a kwakwalwarsa, yau lafiya gobe akasin haka, ya dawo kamar ba Malam Ali ba, a lokacin duk ya gigice yayi ta bala'i wai ina ne ba a tura yaro karatu a zamanin yanxu, yarinya me shekara sha bakwai ce za ace ma yarinya, inda yake shiga ba nan yake fita ba, hakan ya zame masu bacin rai sosai da mahaifiyar Khaleesat har sai da ta bar gidan ta koma gidan Mahaifiyarsa warce ita ma yaki sauraronta, haka nan Malam Ali ya dau Khaleesat ya damka ma Abdul ba tare da amincewar uwarta ba ya kai ta karatu Amurka, Shiru Aunty Farida tayi tana kallon su Ajay dake kallonta duk suna sauraronta, a hankali tace "Tun daga sannan shi yake sponsoring komai nata a Amurka, cin ta da shan ta, da suturanta komai dai shi ne, sai san da ya ga dama ne yake bari ta zo hutu Nigeria, mu tsakaninmu da ita dama sai sanda muka ganta ko kuma muyi magana ta WhatsApp, gashi yaki a daura auren nasu wai sai ta gama karatun wanda wnn ne ke kara daga mana hankali, a haka ake ta rayuwar bamu da kwanciyar hankali, a ko da yaushe fatanmu shine ayi ayi auren don duk wasu iyaye nagari baza a same su da kwanciyar hankali ba ace yau er su budurwa bata gabansu, kusan kullum sai uwarta ta zubda hawaye kan wannan lamari sanadiyar hakan har sai da hawan jini ya kamata, ace bata da iko da er ta sai dai abinda Abdul da ubansa suka tsara gashi mai gidanta ya dau tsoron duniya ya dora masu sai jan sa suke kamar rakumi da akala.... ko wata biyu ba ayi ba ranan yayata ta kirani take sanar min sun kawo kudin auren Khaleesat, duk muka yi farin ciki sosai da hakan, muka yi fatan Allah ya sa hakan alkhairi ne a rayuwar Khaleesat tunda mu ma mun fi son ayi auren kowa ma ya huta, kawai ranan juma'an nan da ta wuce sai ga kiran yayata wai an daura auren Khaleesat da Abdul, nace mata ban gane ba, Khaleesat din ta dawo ne? Sannan dama ana daura aure haka ba shiri? Nan take gaya min ai mahaifin Abdul din ne ya kira Baban Khaleesat da yamma likis yace ga bukatarsu gobe juma'a, babu bata lokaci kuma aka daura auren kamar yanda suka bukata washegarin, nace mata to shikenan Allah sa hakan shine mafi alkhairi, zuwa satin da za a shiga zan shigo kanon tunda tace Khaleesat din ma na Amurka bata dawo ba, ban kuma san komai dake faruwa ba sai ranan Lahadi da kirani, mun yi waya da kai babu dadewa sai ga yayata ma ta kirani tana kuka" Ajay ya sauke idonsa kasa, Calmly yace "Amma dai baki ce mata tana nan ba har yanxu ko?" Aunty Farida ta girgiza kai tace "Ai tunda muka yi waya kace kar in nuna ma kowa nasan inda take wallahi ban nuna ma yayata nasan komai ba, ita kanta har yanxu bata san inda Khaleesat take ba, Nasan Baaba Gaje bazata gaya mata ba ita ma" Ajay ya sauke ajiyar zuciya yace "Shikenan, yanxun ma kar ki nuna tana wajenki, in sha Allah za mu ga yanda za ayi, in ma kudin baban nasa da abinda ya kashe mata na makaranta za a mayar masu wannan ba matsala bane in sha Allah" Aunty Farida ta gwalo ido jin abinda yace, ko dai bai ji amount din da ta kira bane da kyau, a hankali tace "Kudaden ne da yawa ai Junaid, miliyan dari fa banda abinda zai ce ya kashe mata na makaranta da bamu sani ba" Ajay yace "Bazai dai ce ya kashe mata sama da miliyan dari a makarantar ba, mu ma duk makarantar muke ai, in ma yace haka miliyan dari biyu ba abu bane da muke fatan zai gagara a mayar masu, so kawai kar ki ce ma kowa tana wajenki, we will see how things will go in sha Allah" Ita dai Aunty Farida tsabar yanda jikinta yayi sanyi ta kasa cewa komai, dama tun da ya sakko daga mota jiya taga kalansa take ta kallonsa tana mamakin inda Khaleesat ta samo shi, hatta wanda ya kira ɗan uwansa bata ga yayi kalar tsiya ba shima, Shi dai Jay yayi shiru bai ce komai ba idonsa akan buhun shinkafa biyu da babban jarkan man gyada da carton din taliya dake parlon Aunty Farida, kana gani kasan food vendor ce, Ajay ya mike yana kallon Jay alamar ya tashi su tafi, Jay ya sauke boyayyen ajiyar zuciya yana kallon Aunty Farida a hankali yace "Bacci take ne?" Ajay ya wani kallesa sai kuma yayi ficewarsa daga parlon, Aunty Farida ta mike tace "Bari in duba ta" Dakinta ta nufa Jay ya bi ta da kallo, after few seconds sai ga ta ta fito tana kallonsa tace "Ehh bacci take" Yace "Ohk, amma Drip din na raguwa kuwa?" Aunty Farida tace "Eh yana sauka" Mikewa yayi yace "Toh shikenan, sai anjima Aunty, kilan zuwa gobe da safe in sha Allah za mu shigo" Aunty Farida ta ɗan yi murmushi tace "Toh Allah ya kai mu Jawwad, mun gode sosai" Murmushin ya mayar mata ya nufi kofa, har ya fita ya sake juyowa yace "Amma Aunty ki ɗan dinga duba drip din idan ya kare sai kiyi ma makociyar taki magana ta cire" Aunty Farida tace "Ina sha Allah, mun gode Jawwad" Daga haka ya fita daga parlon ya nufi kofar gida, cikin mota ya tadda Junaid har ya tada mota, ya karasa ya bude front seat ya shiga ya zauna ya jinginar da kansa da kujeran motar ya lumshe ido ya bude, saukansa kenan daga America ko hutawa bai yi ba balle ya ci abinci, yayi wanka kawai suka taho gidan Aunty Farida da Ajay, har suka isa gidan Cousin sister din parent dinsu dake Banana Island babu wanda yace komai a cikin motar, it's almost 7pm tsabar traffic din Lagos da ya rike su a hanya, bayan Ajay yayi parking Jay ya sauka daga motar ya nufi entrance din shiga gidan Ajay na biye da shi, a parlor suka tarar da Hajiya Fatima warce suke kira da Ummi, ta amsa gaisuwar da suka mata ta bi su da kallo, Ajay dai ya nufi sama, Tana kallon Jay tace "Baka ci abincin da aka ajiye maka ba Jawwad, ina ma ku ka je haka sai yanxu ku ke dawowa?" Jay ya shafa kansa a hankali yace "Wajen wani abokinmu" Daga haka shi ma ya wuce sama, ta bi sa da kallo. Wajen karfe tara na dare Ajay ya gama saka pajamas dinsa, Jay ya ajiye mug din tea dake hannunsa yana kallonsa Calmly yace "So now what is ur suggestion Ajay, gaba daya kai na ya kulle akan issue din nan, that guy have evil in mind shi yasa ya saka aka daura auren tun bata dawo ba, he have a different plan, abinda kayi masa a USA na ransa har yanzu.... He married her immediately just to deal with her, I don't think he still loves her, he married her to take revenge" Ajay yace "Dama ai ba saboda Allah ya sa aka daura auren ba, akwai abinda yake nufi da hakan, ashe ma karamin ɗan iska ne shi ban sani ba tun da bai yarda da kansa ba, da ya yarda da kansa bazai dinga kashe waya ba" Jay yace "Kamar ya?" Ajay yace "Na karbi numbersa na sa a duba min location dinsa, his location was showing Abuja on Sunday, tun sunday din har zuwa yau bai sake kunna wayarsa ba, kuma baya location din da aka gansa bayan na sa an je can" Jay ya bude baki yana kallonsa, can yace "Ban gane ka sa an je can ba, what are you trying to do? Plss ni bana son wannan dabancin naka Ajay, ni na zata fa ka shiryu, is that why u were busy shouting ku hadu a Nigeria on that very day? No pls ka girmi haka yanxu Prince, why spare ur precious time for a tout like him, don ni wallahi kallon tout nake ma gayen, sannan kar ka manta barrister ne shi kamar yanda kanwar mamarta ta gaya mana, definitely yasan plan dinka a kansa da yasa ka dage ku hadu a Naija, kaga bazai bar wayarsa a kunne ba kuwa" Ajay yace "Ai sai dai bai kunna wayarsa ba amma wallahi duk sai ya janye batancin da yayi min a parlon nan ranan, ya zata ana zagina a tafi scot free? I will so deal with him" Jay ya tabe baki yace "Yanxu dai that aside, meye abun yi" a takaice Ajay yace "Abun yi kawai a makasa a kotu ya fadi duk abinda ya kashe a biyasa ya saketa taje tayi rayuwarta, cause in har ta zauna zaman aure da mutumin nan zai iya kasheta har lahira, don prisoner zai mayar da ita kawai" Jay yayi shiru at first, can yace "But Ajay bamu san ko anyi a rubuce kan cewar an basa aurenta a madadin kudin da mahaifinta zai biya mahaifin Abdul din ba, sannan gayen nan Barrister ne, kana ganin zai bari ayi wannan yarjejeniyar babu sa hannu or anything of such ta bangaren shari'a?" Ajay yace "Su na ma iyayenta kallon talakawa marasu galihu da basu da wani say shine za su tsaya wani yarjejeniya? Ai masu arziki ke yarjejeniya, bayan sun san har a tashi duniya iyayen nata ba samun hanyar biyan miliyoyin kudin nan za su yi ba? Ai hankalinsu da tunani ma bazai je kan wata yarjejeniya ba cause they just assume sun samu yarinyar sun gama kuma ba wani abu da zai gifta ya hana hakan, so now we are taking this case to court, da bakinta zata ce ma alkali bata auren a kotu, iyaka ace ta biyasa abinda ya kashe mata na karatu sannan tayi masa wani auren ba shikenan ba" Jay yayi murmushi yace "Case din babanta da shi mahaifin Abdul din fa?" Ajay yace "We will reach der also" Jay yace "I just hope the agreement isn't in written form, but before mu je kotu nawa ne a account din ka Ajay?" Dariyar da Ajay bai yi niyya ba yayi yana shafa kansa, can ya kallesa yace "Why are you asking me that silly question Jay?" Jay yayi murmushi yace "Let me know first cause the money in my bank account isn't more than that amount" Ajay yace "200M?" Jay yace "Ban sani ba" Dariya sosai Ajay yayi yace "Na raina capacity dinka Bruh, meye kuma 200M a account dinka? Na zata account dinka ya doshi 1 Billion yanxu, Ohhh i remember baka wasa da investing fa, sannan kai Momy's boy ne har account din Momy ajiye kudi kake, Allah sa 200M din ma baya account dinta" Jay yaki tanka sa, Ajay yace "Kasan me, yanxu 600M or more ya kamata ace mun ajiye aside for this case cause I don't trust that stupid guy zai iya tripling kudin a kotu, i will get some more money from dad, Billah i am doing all this for the sake of humanity not because of that little brat, in don ta ita ne bazan yi ba, infact in don ta ita ne ba ruwana a case din ma" Jay dai danna wayarsa kawai yake bai ce komai ba don hankalinsa gaba daya yayi kan drip din da aka sa ma Khaleesat, yasan zuwa yanxu dai ya ci ya kare. Abdul na zaune gidan wani cin abinci tare da abokansa biyu da ke sauraronsa, Abdul yayi sipping energy drink din gabansa ya ajiye ya ci gaba da magana yace "I am still trying to gather more informations about the guy, kuma duk inda take yanxu da taimakon guy din taje can don bata da kowa a cikin garin kano or anywhere da zata je sai wajen sa, all of a sudden fa kawai naga yarinya ta canza attitude tana min wani sabon kalan raini, at first na zata naughty frnd din nan nata Safiyyah ce ke zugata duk da ita ma sai nayi maganinta don nasan da hadin bakinta a abubuwan nan da ke faruwa, i will fish her out too, ashe wai er ficiciyar yarinyar nan maza take kulawa a kasar suke bata liver take min raini, Billah sai na kauda gayen nan a doron kasa this is a promise i am making, sai dai uwarsa ta haifi wani, zai san gonata ya shiga sannan zai san bai daki banza ba, ba a dukana a ci gaba da rayuwa lafiya, he said we should meet in Nigeria ko? nasan yanxu shi ma yana bibiyan inda zai sameni, i don't want to be taken unaware shi yasa nake kashe wayata don nasan definitely zata basa lambata, idan na gama shirya masa tuggu zan bude wayar yayi tracking dina ya zo ya sameni inda nake, wallahil Azeem sai na kawar da shi kuma babu abinda zai faru, ita kuma duk inda take zata shigo hannuna nan ba da jimawa ba kuwa, sai dai in ban cika Abdallah Musa ba" Abokinsa Aminu yace "Toh kai baka ga fuskar guy din bane?" Abdul yayi wani murmushi yace "Ai ni yanxu ban damu da naga fuskarsa ko ban gani ba, burina in ga na aika sa barzahu, kun yankar mana ticket din da nace?" Aminu yace "But ta yaya zaka samu informations din wanda baka taba sani ba, baka da lambarsa ba, baka san komai kansa ba, baka san wanene shi ba, baka ma san inda yake a Nigeria ba ko kuma wanda ya san sa, How will that be possible Abdul?" Abdul yayi wani irin murmushi yana bubbuga kafarsa da kasa a hankali, sai kuma ya karyar da kai yace "Na zata you will be among people that will never underate my capacity and intelligence Aminu, ai ina da lambar wayarta ko? Kuma ni nayi mata registering sim card din, toh abokina dake aiki a kamfanin network din sim da take amfani na ba phone number dinta ya duba min duk calls dinta ya kuma turo min numbers din da take waya da su frequently a America, he just sent them to me few minutes ago" Yana kai wa nan ya mike yana wani murmushi yace "Let go" Dariya kawai abokan nasa ke yi, suka tashi duk suka fita daga eatry din. [6/2, 1:05 PM] khaleesat Haiydar ✍️: Wajen karfe goma na dare Khaleesat na zaune dakin Aunty Farida da fruits a gabanta ta kasa sha, ita dai Aunty Farida na zaune opposite dinta ta zuba mata ido don har ta gaji da ce mata ta sha fruit din, ga abinci ma taki ci, tun tuni makociyar Aunty Farida ta shigo ta cire mata drip din bayan ya kare, ta daga kai ta kalli Aunty Farida a hankali tace "Aunty su Housemate dina sun tafi ne?" Aunty Farida tace "Waye kuma Housemate din ki?" Khaleesat ta sauke idonta tayi shiru, Aunty Farida tace "Junaid din ne Housemate din ki?" Khaleesat ta girgiza mata kai tace "Wanda suka zo tare" Aunty Farida tace "Ohk, tun daxu ai suka tafi kina bacci, ta yaya ya zama Housemate din ki?" Khaleesat na juya fruits din gabanta a hankali da fork tace "Gida daya muke da shi a America" Aunty Farida ta ɗan buda ido da confusion tace "Gida daya kuma? Kamar yaya? Amma ba kin ce makociyarki mace bace?" Khaleesat tace "Eh daga baya ta tashi daga apartment din, shi ne shi ya dawo gidan" Aunty Farida tace "Ikon Allah, shi kuma Junaid din a ina kika san shi?" Khaleesat tace "Cousin brothers ne ai, dalilin Housemate dina na san shi" Aunty Farida ta kafe ta da ido, Khaleesat ta sauke kanta bata boye ma Aunty Farida duk abun da ya faru tun daga dawowar Housemate apartment dinta, yanda ya biya mata kudin jirgi to and fro ta dawo Nigeria ta duba Umma, irin zaman da suka yi da shi da kirkin da yayi ta mata, har zuwa lkcn da Abdul ya zo kasar a karo na biyu da kuma abinda ya faru tsakaninsa da Ajay, da yanda suka maidata gidansu har ta gama Exams, babu abinda ta boye ma Aunty Farida hawaye na zuba idonta, Aunty Farida ta kasa cewa komai sai kallonta kawai take jiki a sanyaye, after almost a minute Aunty Farida ta sauke ajiyar zuciya tayi tagumi don she is just speechless bata san ma me zata ce ba, amma ta fahimci wani abu a labarin da Khaleesat ta bata..... Washegari wajen karfe goma na safe Jay ya bude kofar dakin Ajay ya samesa tsaye yana buttoning din shirt dinsa ya gama shiryawa, Jay ya jingina da jikin kofar dakin ya rungume hannu yana kallonsa calmly yace "You know what Ajay?" Ajay ya dau face cap dinsa ya saka, yana kokarin daura agogonsa a hannu yace "All ears" Jay yace "I think we shouldn't say anything to Abba akan kudin da muka yi magana jiya" Sai a sannan Ajay ya juya ya kallesa yace "Why?" Jay yace "Kasan zai yi querying dinmu about what we are using that huge amount of money for, i think gwara in amshi kudi wajen Mamina kawai, cause you know i can't lie to Abba idan yayi insisting akan abinda za mu yi da kudi haka, zan iya gaya masa me za muyi da kudin if he insist" Ajay ya masa wani kallo daga sama har kasa yace "Sannu saint, ita Mamin ce bazata yi querying dinka akan me zaka yi da huge sum of money din ba?" Jay yace "Yeah, but i know how to convince her" Ajay yayi wani murmushi yace "Mamin ce zaka yi convincing, i see" Bai jira amsar da Jay zai basa ba ya dau makullin mota da wayar sa ya bi gefensa ya fice daga dakin ya sauka downstairs, Jay ya bi sa da kallo, after a while ya jawo kofar dakin ya kulle sannan ya bi bayansa, Ummi dake zaune parlor ta bi su da kallo ganin alamar fita za su yi tace "Ina kuma za ku da safen nan?" Without looking at her a takaice Ajay yace "Bar beach" Ummi tace "Dama ana zuwa Bar beach da safe?" Ajay yace "Eh" daga haka ya fice daga parlon, Ummi ta kalli Jay tace "Wai Beach za ku?" Jay ya ɗan sosa kansa yace "A'a sai da yamma, yanxu dai kawai yawo za mu yi a gari" Ummi ta tabe baki tace "Ai shikenan, traffic ma kadai ya isheku, Mami ma suna hanya yau in sha Allah, sun ma kusa sauka" Jay ya sauke kansa yace "Eh haka tace min" Ummi tace "To sai kun dawo" Jay yace "Allah ya sa" Daga haka ya fita daga parlon, ya tarar da Ajay a mota yana jiransa, yana shiga motar Ajay yace "Ko ina ruwanta da inda za mu, ni bana son sa ido a rayuwata, shi yasa bana sauka gidanta a garin nan, i hate what i don't like" Jay yace "Ikon Allah, what's wrong with her asking us where we are going?" Ajay yace "That's very wrong, we are not kids da zata dinga tambayar mu inda za mu idan za mu fita, ko Abba baya controlling din mu yanda matar nan take yi, i don't think i am going back to that house zan je in kama hotel kawai" Jay ya girgiza kai yace "Kai fa matsala ne da kai kamar gidan haya, ni ban ga wani abu ba don ta tambayemu inda za mu da safe, it's normal ai" Ajay ya kallesa yace "To ni ba kai bane da ake controlling yanda aka ga dama a family, kai da kaga za ka iya sai ayi ta controlling dinka Jawwad" Jay bai sake ce masa komai ba, Ajay ya ja motar suka fice daga gidan. Da sallama Safiyyah ta daga buhun dake makale kofar shiga compound din gidansu Khaleesat, Mama Shatu da Mama Zubaida ne tsakar gida ko wacce na zaune bakin murhunta ana girka abincin talla hayakin icce duk ya cika ko ina na gidan, Mama Zubaida sai mita take an siyo masu jikakken icce, gaishesu Safiyyah tayi suka amsa ana mata wani kallo kasa kasa, Safiyyah ta tsaya suka gaisa da Labiba dake wanke robobin da za a zuba abincin siyarwa, sannan ta nufi dakinsu Khaleesat ta daga labulen ta shiga da sallama, zaune ta tarar da Umma ta jingina da bango hannunta rike da carbi ga kawarta Mama salame da wata Zaliha makociyarsu sai Sha'awa ita ma makociyarsu zaune dakin ko wanne yayi jigum, zaunawa Safiyyah tayi tana kallon Umma ko gaisheta bata yi ba ganin yanayinta tace "Umma baki da lafiya ne?" Umma tayi karfin halin cewa "Sannu da zuwa Safiyyah" Safiyyah ta gaisheta sannan ta gaida sauran mutanen dake dakin, ta sake maida dubanta kan Umma kan tace komai Mama Salame da ta san kawar Khaleesat ce ita tayi kasa da murya tace "Tsakaninki da Allah Sapiya baki san inda kawarki Khaleesah take ba?" Safiyyah ta zaro ido tace "Kamar yaya Mama?" Sha'awa ta gyara zama tace "Ae tun ranan asabar rabon da a saka Khaleesat a ido, daga ta dawo kasar waje ta tarar an daura mata aure da audallah washegari Asabar aka nemeta aka rasa, babu inda ba a shiga neman Khaleesah ba amma babu ita babu labarinta, jiya jiya yan sanda suka zo suka tafi da Malam Ali" Safiyyah da ta shiga wani shock jin wai an daura ma Khaleesat aure da Abdul ta ajiye jakarta a gefe ta dafe kirji tace "Wani Abdul din aka daura mata aure da?" Sha'awa na gyara barkakken zaninta tace "Audullah saurayinta dai da kika sani, ranan juma'an nan da ta wuce aka daura masu aure, tana dirowa kasar aka sanar mata shine ta gudu har yau babu ita babu labarinta, gashi an tafi da Malam Ali an kullesa" Safiyyah tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Mikewa tayi tsaye ba tare da tasan tayi hakan ba tsabar shock din da ta shiga maganganun Sha'awa na yawo a kanta, hawaye ne ya cika idonta tana girgiza kai ta kasa cewa komai, ina jin bayan Khaleesat da tayi bakin cikin auren da aka daura mata da Abdul idan aka cire su Jay babu wanda yayi bakin ciki kuma irin Safiyyah, don ji tayi kamar an aza mata katon dutse a kirji tsabar bakin cikin wannan labarin, kawai ta fashe da kuka cike da tausayin kawarta, Abdul fa?? Housemate din Khaleesat ne ya fado mata a rai, nan Safiyyah ta dinga rera masu kuka kamar ita ce Khaleesat din, muryar Nenne suka ji a tsakar gida tana kunduma ma su Mama Shatu da Mama Zubaida zagi tana cewa "Wato har sararin kunna rubabbun murhun ku kuka samu a gidan nan baku dubi bala'in da ake ciki ba, ai in dai ɗa ne kowa ma ya haifa wallahi, yanda ku ke nuna halin ko in kula da abinda ya samu ɗa na ku ma dai kun haifi 'ya yan nan naga, shegu masu fararen kafafuwa tunda ɗa na ya auro ku yake shiga bala'i sinka sinka a duniya amma saboda baku da imani da tausayi ko wacce ta zauna bakin shegen murhun ta" Mama Zubaida ta kauda kai tana tabe baki tayi kasa da murya tace "Sai kuma yunwa ta kashe mu saboda yan sanda sun zo sun dauki Malam" Ita dai Mama Shatu sai juya miyarta take kar ya kone taki ko kallon inda Nenne take, Nenne na huci ta nufi dakin Umma ta dage labulen tana kallon cikin dakin tace "Saka dogon hijabi da rike carbi ba shine mafitarki ba Zahra'u, duk inda kika tura yarinyar nan waya kawai zaki buga masu ki ce ta dawo tun lamari bai lalace mana gaba daya ba, in ko ba haka ba wallahi sai a wanke daya daga kanninta a ba ma Awdul din tunda abinda yayi ta shi yayi su, in jar fata da gashi irin ta buzaye ne su ma duk suna da shi, babu abinda zata gwada masu sai shekaru tunda ta basu shekaru bakwai, don bazan zuba ido a karo na biyu ɗa na ya koma fursin ya tagayyara ba, Allah kadai yasan nawa na kashe wajen shige shige har Allah ya bamu mafita a wancan lokacin da aka kullesa, tun asali bata san bata son Awdul din ba sai bayan da ya kashe mata uban dukiya da bazai lissafu ba? Wace masifa ku ke son ja ma ɗa na ke da er ki a garin kano? Shi kadai fa ya rage min namiji sai mata, wallahi ki fito da ita Zahra'u in ya so su riketa a sake min ɗa na, nasan har da hadin bakin makirar tsohuwar can Gaje, yanxu kuma zan kama hanya in tafi Hotoron duk inda ku ka boye Khaleesah sai kun fito da ita baza ku kara ja min salalan tsiya ba, sha'awa taso ki rakani gidan tsohuwar banzan can Gaje" Da sauri Sha'awa ta mike ta figi baƙin gyalenta ta fita daga dakin ta bi bayan Nenne dake huci suka fita daga compound din gidan, Mama Zubaida da Mama Shatu suka saki guda a tare bayan Nenne ta fita, Mama Shatu ta kyalkyale da dariya tace "Ana yi muna hura murhu, ma ga dai karshen wannan dirama me dadin kallo a gidan nan, su buzuwa sai a koma dajin da aka shiga aka nemo maganin farin jini ayi ma Malam bayanin lamari ya kwabe, ba dai 'ya yanmu bane munana masu baƙin jini, maji ma gani dai" Umma dake jin duk abinda suke cewa ta jinginar da kanta da bango hawaye na sauka idonta Mama Salame na bata hakuri, Safiyyah dai jingina tayi daga bango a inda take tsaye hawaye na zuba idonta ita ma, ganin abun take kamar a mafarki wai an daura auren Khaleesat da Abdul, to amma ina Khaleesat zata tafi tun ranan Saturday ita da tasan Khaleesat ko kawaye bata da su a kano, Housemate ne ya fado mata, ta dau jakarta da sauri tana share hawayenta ta fita daga dakin Umma, Umma ta bi ta da kallo hawaye masu zafi na bin idonta daga ranan asabar zuwa yau har ta rame, ko abinci bata iya ci ta kira Aunty Farida yafi a kirga akan ta zo gareta ko zata ji saukin radadin da take ji a zuciyarta, Mama Zubaida da Mama Shatu suka bi Safiyyah da wani kallo suna tabe baki har ta fita daga compound din, Mama Zubaida ta matsa kusa da Mama Shatu da yake murhunsu kusa da kusa yake, tayi kasa da murya tace "Kin ga ki hakura da dafa waken nan da kika ce don gaskiya zai bata mana lokaci ga waje da nisa, gwara mu je a kara kada hankalinta taji ta tsanesa da auren kuma taki dawowa, in ya kama a kadata ta shiga duniya duk sai mu ce ayi, kudi ne dai zai yi kuka ba wani abu ba, kinga daga karshe in ma Labiba ko Lamisah duk wanda yace a basa duk daya ne a wajen mu babu banbanci, babu abinda zata gwada masu sai farin fata da uban gashi kamar na doki, in idanuwa ne su ma suna da shi, sannan suna da hancinsu dai dai gwargwado, tun asali kece kika yi ta makon fiddo kudi da ba a kai ga haka ba ma wallahi" Mama Zubaida ma tayi kasa da murya tace "Wallahi ban taba zaton aikin mutumin na ci haka ba Shatu, kinsan Malaman Jabu sun yi yawa yanzu sai dai ka kai masu kudinka su yi cefanen gidansu, shi sa kika ga ina ta ja da baya naki sakin kudi dama jarina ba jarin arziki ba, kinsan tun bayan rasuwar Malamin nan da yayi mana aiki kan Parida naki sakewa da Malamai don asaran kudi kawai mutum yake shi din dai ne malami gangariya amma mutuwa ta dauke mana shi kwatsam, gashi har yau duk uban kyan parida babu mashinshini tana can tana tuwo tuwo a Legas tana aiko ma yayar kudi kuma in sha Allahu a haka zata kare ga dai kyan da diri da komai amma babu mashinshini, to in anyi duniya don manzon Allah haka Khaleesar ma zata kare, amma yanxu tunda muka samu sabon Malamin nan naga aiki da cikawa kema kin san fiddo kudi bazai kara min wahala ba, ba gashi har na sa an amso min adashina ba daxu, in sha Allah sai mun karkato da hankalin Abdul kan 'ya yan mu, ko Labisah ko Labibah, ba dai kyau suke takama da shi ba wai su buzaye, to wallahi sai dai su ga ana aure....." Shiru Mama Zubaida tayi ganin Salame ta fito daga dakin Umma ta ci gaba da juya miyarta with serious face, Safiyyah na fita kofar gida ta ciro wayarta a jaka don tana da number Housemate, tayi dialing numbersa gabanta na faduwa tana hoping yasan whereabout din Khaleesat, jin Khaleesat take a ranta kamar er uwarta ta jini, she can't imagine halin da take ciki yanxu, yana fara ring Jay dake mota tare da Ajay ya daga wayar ganin Safiyyah ke kiransa yayi picking ya kai kunne calmly yace "How are you Safiyyah?" Da kyar Safiyyah tace "I am fine, ina kwana?" Yace "Lafiya lau, kin dawo Nigeria kenan?" Ta gyada kai da kyar tace "Pls tambaya nake son in maka Ya Jawwad" Jay yace "Ina jin ki Safiyyah" Safiyyah tace "Don Allah kasan whereabout din Khaleesat, wai tun Saturday ta bar gida har yanxu ba a san inda take ba, yanxun nan na zo gidansu nake samun labarin" Hawaye na zuba idonta ta kare maganar, a hankali Jay yace "Halysaah?" Lkci daya Ajay ya juya ya kallesa, sai kuma ya fixge wayar ya katse ya ajiye, Jay dai kallonsa kawai yake, can yace "Kawarta ce fa" Ajay yace "And so? Assignment din announcing whereabout dinta aka baka ne? Me yasa baka da sirri ne kai?" Jay yace "But it's nothing, kawarta ce kuma tana sonta sosai, nasan bazata gaya ma kowa komai ba" Ajay ya dau wayar jin ya fara ringing, yayi rejecting call din Safiyyah sannan ya saka wayar a silent ya zura a aljihunsa yace "Dama ka saba tona ma mutane asiri kayi ruining plan dinsu ai" Jay yace "Bani wayata malam" Calmly Ajay yace "Bazan bayar ba" Dai dai sanda Ajay yayi parking a kofar gidan Aunty Farida ya kashe motar ya sauka ya bar Jay a ciki. Nenne na isa kofar gidan Gaje tare da Sha'awa er rakiyarta suka ga yan sanda biyu kofar gidan Gaje da motarsu, ga yan unguwa sun tsaya cirko cirko ana salallami, Nenne ta ja burki inda take tsaye tana gwaggwale ido sai ga wata er sanda ta kado keyar Gaje sun fito daga cikin gidan, Gaje na rusa kuka cikin rudewa take cewa "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, wallahi ban san inda take ba tsakanina da Allahn da ya halicce ni, in nasan inda take Allah ya tsine min albarka, Al-qur'anin Allah babu abinda na hada da ita ba dangin iya ba na Baba haduwar gidan duniya ne kawai, don manzon rahama ku min rai ban hada komai da ita ba" Er sandar tace "Amma ai an ganta ta shigo gidan ki ranan asabar da daddare, iya gaskiyar ki kadai ne zai cece ki a wannan case din aki kai ki furson, in kuma kika ce zaki ci gaba da karya zaki ga illar karya kuwa" Cikin tashin hankali zufa na keto ma Gaje ta ko ina tace "Wallahi zan fada gaskiya ku tsaya ku saurareni, tsakanina da Allah ta zo gidana da daddare wajen karfe goma tace in rufa mata asiri amma bata gaya min abinda ke faruwa ba, ni kuma da na tashi sai na kai ta gidan wata er dakina Sadiyah Chamo, Sadiyah ce ta bata mafaka a gidanta ta kwana, kashegari kuwa ta kira wani gingimemen mutumi a wayarta ya zo da katuwar motarsa ya dauketa suka tafi inda ban sani ba, idan na maku karya a wannan zance kada Allah yayi min rahama" Er sandar tace "Ina gidan Sadiyar yake?" Jiki na rawa Baba Gaje ta nuna hanyar gidan Maman Fu'ad, er sandar tace "Shiga mota mu je ki nuna mana gidan" Gaje ta rushe da kuka tana cewa "Na shiga uku na lalace ni Al-haqqatu na ja ma kaina masifa a garin kano" Bayan mota aka bude ma Gaje tana kuka ta shiga er sandar ta dago mata yakunannen gyalenta dake jan kasa ta dora kan cinyarta sannan ta shiga bayan motar ita ma, tuni Nenne ta juya sum sum tun ba a lura da ita ba ta shige wani layi, sai juyawa sha'awa tayi taga gefenta wayam babu Nenne..... Next update at night in sha Allah. [6/2, 8:30 PM] khaleesat Haiydar ✍️: A hankali Khaleesat ta ɗan bude curtain din dakin Aunty Farida tana leko cikin parlon ta hada ido da su gaba daya, sauke idonta tayi ta shigo parlon walking slowly ta tafi ta zauna kan kujera kanta a kasa, tun da taji sallama ta tashi ta tafi dakin Aunty Farida don saka Hijab dinta, gaishesu tayi still not looking at them, Jay ne kawai ya amsa yana kalllonta calmly yace "How are you feeling now Housemate?" Sai a sannan ta daga kai ta kallesa a hankali tace "I am much better now" Kallon Ajay tayi suna hada ido ta sunkuyar da kanta tace "Ina yini?" Yana danna wayarsa yace "Fine" Aunty Farida ta shigo parlon daga kitchen ta ajiye masu tray din Can drink da ruwa da taje dauko masu, sannan ta zauna kan kujera tana kara gaishesu, Jay yace "Ya me jiki" Aunty Farida tace "Da sauki, abinci ne dai bata ci har yanxu" Jay ya daga kai ya kalli Khaleesat, sauke idonta tayi ta dau plate din abincin da Aunty Farida ta zuba mata not long ago, ta bude murfin ta ajiye sannan ta dau spoon ta fara cin abincin a hankali, Aunty Farida na kallonsu tace "Bari in kawo maku abinci" Ajay ya kalli Jay, Jay yace "A'a mun yi breakfast Aunty, mun gode" Aunty Farida tace "To ai rana tayi yanzu" Bata jira taji me zai ce ba ta tafi kitchen zata zubo masu abincin, ita dai Khaleesat a hankali take cin abincin hannunta, mikewa Ajay yayi, Jay ya sa hannu a aljihunsa ya ciro wayarsa, Ajay yace "Zan yi waya a waje" Daga haka ya fita daga parlon kafin Aunty Farida ta fito daga kitchen, Jay yayi murmushi bai dai ce komai ba, bude wayarsa yayi yaga miss calls din Safiyyah har shidda, yayi dialing number dinta ya saka handsfree, yana fara ring Safiyyah ta daga kamar jira take, yayi kasa da murya yace "Can you hear me Safiyyah?" Tace "Ina jin ka, plss ba a san inda Khaleesat take bane tun ranan asabar, kuma ni nasan bata da inda zata je a garin kano" Yace "Where are you at now?" Da sauri tace "Nima a kano nake ai, jiya da yamma na dawo daga Maryland shi ne na zo gidansu yau nake samun labari she is away from home tun ranan Saturday after receiving the news of her marriage with Abdul, wai Abdul fa aka daura mata aure da" Safiyya na kai wa nan ta fashe da kuka, Jay yace "I mean are you at home or where?" Cikin kuka tace "A'a yanxu na baro gidansu, ina bakin titi ma haka, i am just confuse, Khaleesat bata da kawaye bata zuwa ko ina, i don't know where she will be now, i am disturb don Allah in kasan inda take kar ka boye min plss Ya Jawwad trust me" Calmly yace "Look, this should be confidential Safiyyah, i trust you are saying nothing to anybody about this...." Da sauri Safiyyah tace "Na rantse babu wanda zan ce ma komai Ya Jawwad, trust me, i am also not in support of the fruitless marriage" Jay yace "Ohk, here is ur frnd speak to her....." Mikewa yayi ya mika ma Khaleesat wayar, ta amshi wayar tana kallon screen din dama tun jiya take wishing ace Sophie na kusa da ita ko ba komai zata dinga Consoling dinta tana karfafa mata gwiwa da bata assurance, lkci daya hawaye ya cika idonta cikin rawan murya tace "Sophie" Safiyyah ta sauke ajiyar zuciya tace "Khaleesat, i am so happy you are safe and sound, dama fatana kenan, plss kina ina haka yanxu in taho don Allah" Khaleesat ta girgiza mata kai cikin sanyin murya tace "Bana kano Sophie" Da mamaki Safiyya tace "To kina ina?" Khaleesat ta daga kai ta kalli Housemate dinta dake kallonta, sauke idonta tayi da kyar tace "Ina Lagos" Safiyyah tace "Lagos wajen wa? Ko wajen Aunty Farida?" Khaleesat tace "Um" Safiyyah tace "Amma Umma bata san kina nan ba" a hankali Khaleesat tace "Bata sani ba" Safiyya ta sauke wani ajiyar zuciyar tace "Pls kar ki tada hankalinki kinji kawata, i know ur Housemate won't allow u do that, kuma in sha Allah babu zaman aure tsakaninki da Abdul don bai yi deserving din ki ba, i can't imagine what he will turn you into, in Allah ya yarda bazai ci nasara akan ki ba, Allah zai raba auren cikin gaggawa, shi kadai yasan mugun Intention din dake ransa akan ki shi yasa yayi haka, amma Allah ya fi sa" Khaleesat dai gyada mata kai kawai take hawaye na sauka idonta ta kasa cewa komai, Housemate dinta ya mike ya nufeta ya amshi wayar a hannunta ya koma ya zauna yace "Safiyyah" A sanyaye Safiyyah tace "Na'am Ya Jawwad, Please kawata bata da wanda zai tsaya mata akan issue din nan, ba da intention me kyau ya saka aka daura auren ba wallahi, mugu ne azzalumi, har abusing dinta yana yi" Jay dake sauraronta yace "In sha Allah we will try our very best ki taya mu da addu'a" Safiyyah tace "In sha Allah, but how can i be reaching her?" Yace "Don't you have her aunt's number" Safiyyah tace "Sure ina da shi, i will be calling her ta wayar Aunty Farida" Jay yace "Keep this confidential pls Safiyyah" Safiyyah tace "Trust me Ya Jawwad, i now have rest of mind knowing my frnd is safe" Da haka suka yi sallama ya ajiye wayar, Khaleesat ta ajiye plate din abincin hannunta don ta kasa ci, iya spoon uku kawai ta iya yi, tuni Aunty Farida har ta ajiye ma Jay abincin da ta zubo ta nemi waje ta zauna, sai da ta jira suka gama waya da Safiyyah sannan ta kallesa tace "Ina Junaid din ga abincin na zuba maku" Jay yace "Aunty bamu dade da cin abinci ba da gaske" Aunty Farida tace "Ai ko in baku ci ba bazan ji dadi ba, haka jiya ku ka bar min abincin ku ka ki ci, yanxu fa karfe biyu da rabi ake nema kuma breakfast kace kawai ku ka yi" Jay dai murmushi kawai yake, can yace "Toh zan ci Aunty" Tace "To ko kai fa, ina Junaid din kayi masa magana ya shigo ku ci" Jay na shafa kansa yace "Ai shi ya ci snacks a mota bazai ci abincin ba na sani, bai fiye cin abinci da rana ba" Aunty Farida tace "Ikon Allah to saboda me?" Jay yace "Haka yake, iya breakfast da Dinner kawai yake yi" Aunty Farida tace "Iko sai Allah" Jay na kallon abincin da Khaleesat ta rage ya mike ya dauko yace "Zan ci wannan kar mu bata abincin Aunty" Aunty Farida tace "Don Allah ka ajiye ka debi abinci ga plate nan Jawwad" Yace "Aunty wannan fa ya isheni ba iya cinyewa zan yi ba ma" Spoon din ya dauka ya fara cin abincin, Khaleesat dai kallonsa kawai take, Aunty Farida tace "Ai shikenan" Karfe uku da yan mintuna Ajay da Jay suka bar gidan, Jay ne ke driving din idonsa akan titi yace "To ya ku ka yi da Lauyan?" Ajay yace "He said we should meet in kano" Jay ya ɗan kallesa yace "Zuwa gobe kenan?" Ajay yace "Sure, tomorrow in the morning za mu tafi kano" Jay bai sake cewa komai ba har suka isa gida, yau dai traffic din da ɗan sauki, bayan Jay yayi parking ya juya yana kallon Ajay yace "Please since gobe za mu tafi kano ka bar maganar hotel da kace zaka koma" Ajay yace "Ai matar ne ta fiye takura da sa ido" Jay yayi dariya bai dai ce masa komai ba suka sauka zuwa cikin gidan, Ummi na zaune parlon Hadeeyah na kwance kusa da ita da daura kanta a saman cinyar Ummin, ba tare da Ajay ya kalleta ba ya gaisheta a takaice zai wuce sama Hadeeyah ta gaishesa ya amsa yana haura stairs, Jay ya zauna parlon ya gaida Ummi ta amsa tace "Sai yanxu? Ko dai ba Bar beach din ku ka je ba?" Jay ya ɗan buda ido yace "Mun fasa" Yana magana ne yana kallon Hadeeyah da ta hade rai tana danna wayarta kamar bata gansa ba, Ummi ta kalleta tace "Ke baki ga yayanki bane" Hadeeyah na ci gaba da danna wayarta tace "Oh, ok, Good evening" Jay yace "Ya hanya?" Tace "Lafiya lau" Ummi na kallonsa tace "Mami tana sama" Jay ya mike yace "Ohk" Sama ya wuce, Hadeeyah ta bi sa da kallon gefen ido har ya fara hawa stairs, bayan ya tafi Ummi na kallon Hadeeyah tace "Fadan ku ka sake yi kenan?" Hadeeyah ta ɗan yatsine fuska taki cewa komai tana danna wayarta, Ummi ta kyabe baki tace "Kun fi kusa dai" Jay na bude kofar dakin da yasan Maminsa na ciki ya sameta zaune tana waya, ya karasa ya zauna kusa da ita yana kallonta yayi mata side hug ya jinginar da kansa a shoulder dinta a hankali yace "Mami" Mami tayi ma warce suke wayar sallama ta ajiye wayar hannunta tana kallonsa tace "Ina ka je tun safe Son? I was thinking zaka zo airport kayi picking din mu" Jay ya ɗan kalleta yace "Karfe nawa ku ka iso Mami?" Tace "Karfe sha daya da rabi na safe" Jay yace "Mun fita ne da Ajay, Ummi bata gaya maki ba" Mami tace "Kaga da ubansa ne zai sauka Lagos duk abinda yake yi barin sa zai yi ya tafi ya taro sa, amma kai uwarka ta sauka Lagos ya ja ka kun tafi gantali" Jay bai ce mata komai ba, Mami na kallonsa tace "Duk karatun ne yasa ka fada haka? Are you okay?" Jay yace "Stress din tafiyar da nayi zuwa Nigeria ne" Mami tace "Nasan shi zai zugaka ku dawo Nigeria kar ka biyo min ta UK" Jay ya ɗan hade rai yace "Ya fa riga ni dawowa Nigeria Mami, ni ba jiya na dawo ba, shi kuma ai tun last week yake Nigeria" Mami ta tabe baki bata ce komai ba, Jay ya mike ya nufi kofa yace "Zan je inyi wanka" Mami tace "Dama gobe ka shirya mu tafi Bauchi ban san gantalin da yake jan ka ku ke yi a Lagos ba, kai da ko ance ka sauka Lagos baka taba yarda sai gashi saboda Junaid na lagos kai ma ka zauna a lagos, to gobe za mu tafi Bauchi kuma Hadeeyah ma a can zata yi hutu" Jay ya juya ya kalleta yace "Mami ni ban gama abinda nake yi ba, kawai ku yi tafiyar ku" Bai jira me zata ce ba ya fice daga dakin. Wajen karfe biyar da rabi Jay da Ajay suka sauko downstairs, dakin dake kasa suka nufa don Mami na ciki tare da wata bakuwarta warce suka hadu da dadewa a Saudia suna zumunci sun zama kaman en uwa, jin Mami ta shigo Lagos sai matar ta taho gidan gaida Mami tunda ita ma a Lagos din take, Ajay ya zauna kan 1 sitter dake dakin ya gaida Mami sannan ya gaida frnd dinta, Jay ma ya zauna ya gaida kawar Maminsa, matar me suna Hajiya Batula ta amsa da fara'a tana kallonsu sai kuma ta kalli Mami tace "Wanne ne son din naki a ciki Hajiya?" Mami tayi pointing Jay tace "That is my son" Matar na kallon Jay tace "Maa sha Allah, ai kuwa ga kama na gani" Shi dai Ajay danna wayarsa kawai yake bai dago kansa ba, Jay ya mike yace "Mami za mu je Gym ne" Mami ta kallesa tace "Da yamman nan ga uban traffic din Lagos ne zaka je Gym?" Jay yace "Ai ba nisa Gym din" Hajiya Batula tace "Nan Area din ma ai da Gym ba sai sun je da nisa ba" Jay ya kalli Ajay yace "Mu je" Mikewa Ajay yayi ya nufi kofa Jay ya bi bayansa suka fice daga dakin, Hajiya Batula tace "Amma ɗan uwansa ne wannan din ai ko, naga suna yanayi sosai" Mami tace "Eh Cousin dinsa ne" Hajiya Batula tayi kasa da murya tace "Ko dai shi ne ɗan sarkin dai?" Mami ta tabe baki tace "Shi ne" Hajiya Batula tace "Ya sunansa?" Mami tace "Sunansu daya Ahmad amma Junaid ake kiransa" Hajiya Batula tace "Ikon Allah, shi kam Jawwad babu ruwansa..." Cike da takaici Mami tace "Ni babban bakin cikina yanda har yanxu Jawwad bai san ciwon kansa ba, hakan na ci min tuwo a kwarya wallahi, controlling dinsa kawai yake yana bin sa, ko a America din ma Junaid din ne ke juyasa" Hajiya Batula tace "A'a gaskiya bai san ciwon kansa ba naga alama, shi ko kishi baya yi, kuma gaskiya Mai martaba ya nuna son kansa a fili karara nada ɗan sa da yayi Yarima me jiran gado a maimakon Jawwad, ina ce Jawwad din ya girmi ɗan sa?" Mami tace "Ya basa watanni har uku" Hajiya Batula ta rike haɓa tace "Amma in tambayeki mana Fulani, bayan rasuwan mahaifin Jawwad wato me martaba Sarki Ahmadu Yusuf shi brother din nasa wanda shi ne sarkin yanxu bai nemi rikon Jawwad a gabansa ba?" Mami tayi shiru, can tace "Cikin Jawwad na da wata bakwai mahaifinsa me martaba ya rasu aka nada kaninsa wato mahaifin Junaid, dama su uku ne gun babansu Sarki Yusuf Ibrahim, daga Mahaifin Jawwad wanda shi ne babba sai Mahaifin Junaid sannan Maimuna warce nake gidanta yanxu suna kiranta da Ummi...." Hajiya Batula tace "Ikon Allah, to amma...." Shigowar Ummi dakin ne yasa Hajiya Batula tayi saurin canza topic din tace "Yanxu goben za ki koma Bauchi kenan Hajiya?" Mami tace "In sha Allah" Ummi ta ajiye plate din hannunta tace "Sannun ku, gashi nan kaza na tsaya gasa maku" Hajiya Batula na murmushi tace "Allah sarki, sannu da aiki" Ummi tace "Bari in kawo maku drinks din, a can parlor mai aikin ta ajiye" Daga haka ta fita daga dakin, Mami tace "Da ma kin ci gaba da maganar ki, ita ma ai bata so Junaid din da aka nada Yarima me jiran gado ba" Hajiya Batula tace "To ke sai kika zuba ido aka yi hakan Fulani? In uban Jawwad din bai mutu ba a ina kanin nasa zai samu har yayi sarauta? Kuma shine bazai yi kara ya nada ɗan yayansa da ya mutu ya bar masa sarautan Yarima me jiran gado ba sai ya nada ɗan cikin sa?" Mami tayi wani murmushi tace "Ni fa ko a jikina hakan da aka yi, Jawwad is doing fine beside shi mulki ma baya gabansa, as far as my son is okay, i think da a nada sa Yarima da kar a nadasa duk daya..." Hajiya Batula tace "To halan Junaid din kadai sarkin ya haifa?" Mami tace "Wani Junaid? Amaryarsa da suke kira da Aunty na da ɗa me shekara 29, ita in son samu ne ma a nada ɗan ta Yariman ai" Hajiya Batula ta rike haɓa tana kallon Mami. Ajay yayi parking kenan bayan sun dawo gida wajen karfe bakwai na dare ya kalli Jay zai yi magana wayarsa ya fara ring, ya dauka yana duba me kiransa ganin number wani abokinsu ne da kamar bazai yi picking ba kawai sai kuma ya daga ya kai kunne, after few seconds of listening to what the frnd was saying ya zaro ido yace "What???" Kallonsa Jay yayi da sauri don intonation din da yayi using ya nuna ba lafiya ba, Da kyar Ajay ya cire wayar a kunnensa yana kallon Jay dake kallonsa shi ma babu ko kiftawa, Nan da nan Jay yaji hankalinsa ya tashi don babu inda mind dinsa yaje immediately sai gun Khaleesat, Ya fixge wayar hannun Ajay yace "What's happening plss?" Ajay ya kasa cewa komai tsabar yanda ya girgiza, Jay ya shiga call logs din wayar da sauri yaga Adams abokinsu ne ya kira nan yaji hankalinsa ya ɗan kwanta don yasan ba abu bane da ya shafi Khaleesat, dialing number yayi amma har ya gama ring ba a daga ba, a hankali Ajay yace "Salim aka harba" Jay bai san sanda ya ajiye wayar hannunsa ba yace "What? Harbi kuma? Is he dead?" Ajay ya dau wayarsa shi ma ya kara dialing number Adams amma har ya katse bai daga ba, available flight to kano ya fara dubawa immediately..... [6/3, 9:01 PM] khaleesat Haiydar ✍️: Washegari sai da rana Ajay da Jay suka samu ganin Salem a hospital din da aka yi admitting dinsa, iya kafadarsa ne kadai aka nannada ma bandage alamar a nan aka harbesa amma duk kamanninsa ya canza alamar ya ci duka ba na wasa ba, Jay ya zauna kujeran dake kusa da gadon yana kallon Salem that was in pain yace "Hasbunallah, How did this happen Salem?" Shi dai Ajay na tsaye ya rungume hannu shi ma yana kallon Salem ganin yanda aka canza masa kama, ya ma kasa cewa komai, Salem dake kishingide jikin pillow da kyar don ko iya motsa kafadarsa daya baya yi ga duk jikinsa yayi tsami yayi karfin halin cewa "Ban san su ba suka yi attacking dina" Jay yace "Har gida suka same ka?" Salem ya girgiza kai yace "I stayed out late yesterday in wudil naje gurin wani abokina, he insisted i stay till the next day amma saboda ina da abun da zanyi washegari da safe a kano sai naki kwana a garin muka yi sallama da shi, bayan na kusa unguwan da nake da zama sai na lura da wata mota na biye dani a baya amma ban yi tunanin komai ba na zata ya shigo layin ne bai san hanya ba shine yake bi na ko nima fita zanyi daga unguwan mun fita tare, bayan na shigo layin mu babu kowa saboda dare yayi tun kan ma in sauko daga motata in shiga gida in bude gate sai nake ma motar alama da hannu ya tafi gaba zai samu hanya, sai kawai matukin motar ya fito ya nufo ni, duk da haka ban wani damu ba na zata direction zai tambayeni, na tsaya har ya iso dai dai gabana ban ankara ba kawai sai jin saukan naushi nayi ta ko ina a fuskata ina kokarin defending kai na sai sauran mutane ukun dake cikin motar suka fito su ma suka hau dukana ta ko ina at the same time they were asking me about a girl i know nothing about, wai inyi providing dinta ko su kashe ni" Da wani expression Jay ke kallonsa, sai kuma ya mike da sauri ya dafa gadon da Salem yake kai yace "A girl?" Salem ya gyada kai da kyar yace "Wai Khaleesat, ni ban ma taba jin sunan ba wallahi, suka yi ta dukana wai sai na fadi inda take ko su harbeni" A tare Ajay da Jay suka kalli juna, Salem yace "Kashe ni suka yi niyyar yi banda Allah ya rufa min asiri kururuwan da nake yi wani soja dake kusa da gidanmu ya fito da bindiga, da wani makocina da ya fito da adda, kafin makota na su fito ne suka min harbi har biyu daya ya sameni a kafada daya kuma bai sameni ba ya sami gate, sojan da makoci na suna fitowa suka shige motarsu suka tsere, ni wallahi ban taba jin sunan yarinyar da suka ambata ba ma" Aunties din Salem biyu ne suka shigo ward din da sallama, Ajay ya gaida su sannan ya fita daga ward din ya tafi haraban asibitin ya zauna, after almost 10 mins Jay ma ya fito, inda Ajay ke zaune ya nufa ya zauna bai dai ce masa komai ba, Ajay yayi breaking silence din yace "He is tracking me, ni yake nema ba Salem ba, but tana da number Salem a wayarta ne?" Jay ya sauke wani ajiyar zuciya yace "Yawanci shi take kira ya bani waya if there is anything she wants to tell me, ko number ka ma ai Salem ne ya tura mata, instead cewa zaka yi he is tracking the both of us tunda nima ta kira layina ai ranan, but how did he get Salem's line?" Ajay yayi murmushi yace "Definitely layinta ya sa a duba masa numbers din wa enda take waya da, and he is using that to track us" Jay ya mike yace "We need to take down our sim card AJ, decidedly zai samu information mun shigo kano since we are in his list, sannan i think before anything ya kamata mu fara fighting for her innocent father's release tunda ita Halysaah yanxu bai san inda take ba and she is safe where she is, but the Man needs help" Ajay yace "No, i don't think she is safe with her aunt, although aunt din tace bai san inda ta koma ba amma as far as yana da number wayarta zai iya sakawa ayi tracing din inda take ita ma" Jay ya juya yana kallonsa yayi shiru, he just realize of course hakan zai iya faruwa cause ya daina underrating Abdul yanxu, Jay ya sauke wani ajiyar zuciya yace "That guy is something else Ajay, duk wata salon mugunta ya sani adding it to his career skills, ina jin kawai a duba mana if there is flight zuwa Niger republic a biya masu kawai su tafi can da aunt dinta har zuwa sanda za mu gama da Case din dad dinta, in the other hand shi kuma mun yi sue dinsa requesting for divorce for her" Ajay yayi shiru, can yace "But what if she is needed in court?" Jay yace "For now her lawyer will represent her, in ma an bukace ta a court we will sort that out" Jay yace "I think that's cool, amma ya kamata mu je gidan su gun mahaifiyarta" Ajay dai kallonsa kawai yake, can yace "Is that necessary?" Jay yace "Of course, kasan aunt dinta tace mana the mother is not medically fit, kada wannan damuwar yayi weighing dinta down" Ajay yace "Sai mu je a matsayin su wa?" jay ya mike yace "Human right" Abdul na tsaye rike da takardan da mahaifiyar sa ta mika masa daga shigowar sa parlor idonsa na kan takardar yana karanta content din jiki, Meema yayarsa ma na zaune parlon tana kallonsa fuskarta dauke da bacin rai karara, wani murmushi Abdul yayi ya cukuikuye takardar ya jefar kan kujera, Mahaifiyar sa dake ta kallonsa ta tabe baki tace "To yanxu menene amfanin wannan tozarcin da kaskantar da kai da ake yi? Sam kace kai baza ka ji maganata ka dau shawara ta ba Abdallah?" Meema ta katse ta tana kallonta a fusace tace "Haba Momy ta yaya kike son ya ji maganarki bayan uban kudin da ya kashe ma tsinanniyar shegiyar yarinyar? Ai jin maganar ki ba nasa bane wallahi, kuma don an kawo masa sammaci ba shi ke nufin ya hakura zai saketa ba, kotu ce kawai za a shiga ayi ta gwabzawa, kuma in sha Allahu duk inda kafafuwana za su shiga sai na shigar da su don Abdallah yayi nasara a wannan case din, bazan taɓa bari a tozarta min kanina ba ga mari ga tsinka jaka bazai taɓa yiwuwa ba wallahi, alamar koma waye ya zugata ta yarda aka yi karansa zai iya biyan ko nawa aka ce ya biya a kotu, kai jama'a amma yarinyar nan anyi babbar er iska butulu, dama ni tun asali ban goyi bayan da yace zai kai yarinyar nan Amurka ba ina jiye masa tsoron kar idonta ya bude, to gashi nan bayan karatun har da karuwanci ta dinga yi da manyan kasar nan tunda gashi har ta samu wanda zai tsaya mata da lauya ya biya makudan kudin da aka kashe mata kilan yace har da miliyan 100 da ubanta ya salwantar, abun arziki dai bai amshe mu ba a family din nan, ban ga laifin ki da baki son talakawa ba Momy, shi yasa nima bana son su na tsane su" Momy dai girgiza kafa kawai take tsabar takaici da bakin ciki ta kasa cewa komai, Meema ta kalli Abdul daka safa da marwa a parlon yana ɗan murmushi tace "Ka kwantar da hankalin ka Abdul, as far as ina numfashi kuma uwar mu na numfashi ko don ka rama duk abinda yarinyar nan tayi maka za mu shiga mu fita har sai kotu ta baka ita, in sun san wata ai basu san wata ba, koma waye ke taka mata baya daga karshe kashe kudadensa kawai zai yi a banza don sai ta shigo gidan nan mun ci ubanta da izinin Allah, banda kaddara me ma zaka yi da er gagurumin barawo kuma makaryaci, daga basa dukiya ya kai Lagos yace an kwace mota" Sama Abdul ya wuce kamar zai tashi sama, Momy ta bi sa da kallo cikin bacin rai tace "Kai Allah Ubangiji ya tsine ma mutanen nan albarka, yanda suka sa ɗa na a damuwa Allah ya saka duk zuri'arsu a damuwa, ita kuma yarinya Allah ya kasheta ma duk mu huta, tun da lamarin nan ya faru ko abincin kirki Abdallah yaki ya zauna ya ci a gidan nan, in ya fita tun safe sai dare muke ganinsa gaba daya ba shi da sukuni akan er talakawa, wannan wani irin iftila'i ne ya same mu" Meema tace "Tashi tsaye kawai za mu yi ayi abinda ya kamata Momy, gidan nan ai kamar ta shigo sa ne in sha Allahu, da bakinta zata ce ita ta hakura a kai ta gidan mijinta kawai, kuma ta shigo nan ta same mu muna jiranta" Daga haka Meema ta mike ta bi bayan Abdallah. Jay na zaune tare da Ajay a office din lauyansu suna sauraron sa, lauyan yace "He is trying to re-litigate a case already resolved in court, don an riga an rufe case din a kotu tunda yace ya yafe, har lauyoyinsa sun yi filing notice of discontinuance kuma kotu tayi approving sannan ta kulle case din ta yi releasing debtor dinsu from any further liability, but like seriously ban san wani irin lauya bane ɗan sa, don har da written confirmation of debt forgiveness da suka yi a kotu duk yana nan, why let them arrest the man again? Ko dai ɗan nasa bai gaya masa consequences din hakan da yayi bane cause this is pure abuse of process and malicious prosecution" Jay yace "To yanxu meye abun yi Barrister?" Lawyern ya ajiye pen din hannunsa yace "Za mu yi Filing motion to dismiss the already forgiven case, and we will plead abuse of process, sannan muyi Raising estopped from pursuing the debt again in near future, just that za mu yi presenting documentation of the original debt forgiveness and court records to the court, wannan ma ai sun yi breaching court order ne kuma hakan laifi ne me zaman kansa" Ajay yace "That is because suna ganin ba shi da wanda zai tsaya masa ko shekara nawa zai yi a kulle, his family have no voice to do so, that was why the breached the court order for their selfish interest" Lauyan yace "Babu matsala in sha Allah za mu shigar da kara kotu, and the man will be bailed out while the case is going on, they will even have to pay him damages...." Bayan la'asar Ajay yayi parking a kofar gidansu Khaleesat, dai dai inda yayi parking ranan da suka yi dropping dinta da daddare, a bayansu kuma wata mota ce ita ma tayi parking, Guard uku ne suka fito daga cikin motar dukkansu suka yi tsaye jikin motar da suka sauka, shi dai Jay kallon unguwan kawai yake, Ajay ya bude mota ya sauka, ya jingina da motar ya rungume hannunsa, Jay ma ya sauko sannan ya zagayo inda Ajay yake tsaye yace "Where is the house?" Ba tare da Ajay ya kallesa ba yace "Gashi nan kana kallo" Jay ya kalli gidan dake opposite dinsu, wani almajiri ne ya zo wucewa Ajay ya kirasa, yaron ya taho da sauri Ajay yace "Shiga cikin gidan can kace ana sallama da Maman...." Sai kuma ya kalli Jay alamar ya fadi sunan, Jay na kallon almajirin yace "Kace ana sallama da Maman Halysaah" Almajirin yace "Toh" Da sauri ya nufi gidan, Ajay yace "Meye kuma Halysaah? How is that even a name? In zaka kira sunanta na asali kawai ka kira" Jay na kallonsa yace "Meye sunan nata na asali?" Ajay bai kallesa ba har sannan yace "Ka fi ni sani ai, tunda ka fi kusa da ita" Jay ya ɗan yi murmushi bai sake ce masa komai ba, Nenne ce ta leko kofar gidan tana zazzare ido kuma bata yarda ta fito waje ba, tana yin ido hudu da su Jay sannan ga wasu samudawa da ta gani har uku tsaye jikin wata motar ta juya ta koma cikin gidan da sauri har tana tuntube, sai ga Mama Zubaida tana gyara gyalenta da ta yafa akan daurin kirjin da tayi, Mama Shatu na bayanta tana kokarin saka hijabinta ta bai bai, tsaye duk suka yi daga cikin gidan suna leko su Ajay da samudawan dake jikin mota a tsaye, Mama Shatu tayi karfin halin cewa "Ina wuninku?" Jay ne ya karasa har inda suke tsaye, shi dai Ajay na rungume da hannunsa yana kallon ikon Allah, Jay ya gaishesu duk suka amsa kamar munafukai suna gwale ido, Jay yayi kasa da kai yace "Mahaifiyar Halysaah mu ke son gani" Da sauri Mama Zubaida tace "A'a to ku shigo mana, Bismillan ku ai tana ciki, fakewa kawai suka yi da cewar bazata iya fitowa ba bata da lafiya, lafiyarta lauz ku shiga har dakin ku sameta" Duk tunaninsu an zo tafiya da Umma ne kamar yanda aka zo aka tafi da Malam Ali, Jay ya juya ya kalli Ajay dake jin duk conversation din su daga inda yake tsaye, ko ba a gaya masa ba yasan stepmom din Khaleesat ne matan, ya kulle motarsa yana kallon wa enda ke tsaye jikin mota yayi masu alamar da cewar za su fito in 5 mins sannan ya karasa har inda Jay ke tsaye yana jiransa su shiga gidan, su Mama Zubaida kuwa har sun koma tsakar gidan sun tsaya cirko cirko suna jiran su ga yanda za a shigo a fitar da Umma, da hannu suka nuna ma Jay da Ajay hanyar dakin Umma, Jay ne yayi sallama bakin kofar dakin, shi dai Ajay na tsaye a gefe yana kallon white t-shirt dinsa to be sure ruwan taɓon da yayi gaja gaja a compound din bai fallatsar masa a jiki ba, Mama Shatu da Mama Zubaida a tsakar compound din suke zubar da duk wani ruwan da suka yi aiki haka ma yaransu, sun maida compound din kamar na mahaukata, gashi simintin da aka masa duk ya dagargaje ya kusa komawa kasa, shi yasa in suka zubar da ruwa sai ya cabe, kudaje sai safa da marwa suke ta ko ina, ga kwanuka gaja gaja, igiyoyin gidan kuwa duk an rataye kaya, Ajay na ganin Jay ya shiga dakin Umma shi ma ya shiga ciki da sallama, dukawa Jay yayi daga bakin kofar ya gaida Umma da Maman Salame dake dakin, Ajay ma yayi hakan ya gaishe su, ganin haka Maman Salame ta tashi da sauri ta shimfida masu darduma a kan ledan dakin tana masu sannu da zuwa, duk tunaninta ita ma zuwa aka yi za a tafi da Umma amma sai bata ga alamar hakan a tattare da su ba duba da yanda suka yi gaisuwa cikin girmamawa, Jay ne kawai ya zauna kan darduman Ajay kuwa ya kasa zama ga wani zafi da yake ji a duk jikinsa, ya ciro handkerchief dinsa yana goge zufan goshinsa, Mama Salame ta dau mafici ta mika masa, ya ɗan yi murmushi ya amsa yace "Nagode" Mama Salame ta dage labulen dakin tana cewa "Yau mun fi sati biyu basu kawo wutan ba, ance tiranspoma tayi bindiga" Nenne dake makale kofar bandaki rike da buta ta dinga leka dakin Umma bayan Maman Salame ta daga labulen, haka su Mama Zubaida da suka ji shiru ba a taso keyar Umma an fito da ita ba, Jay na kallon Umma dake zaune don ko ba a gaya masa ba yasan ita ce mahaifiyar Khaleesat duba da kalan fatarta sannan babu ta inda Khaleesat ta bar ta, ba karamin kama Khaleesat ke yi da mahaifiyarta ba a nan ta samo asalin kyanta, Yayi kasa da murya yace "Ya jikin Umma?" Cikin sanyin murya Umma tace "Alhamdulillah da sauki" Ajay ma yayi mata ya jiki ta amsa tana kallonsu gaba daya don jira kawai take taji me ke tafe da su, in ma cewa za su yi tafiya suka zo yi da ita dama a shirye take tunda hijab dinta na jikinta, shiru ne ya biyo baya a dakin, don Jay bai san ta inda zai fara introducing kansa ba ma, haka ma Ajay da yayi shiru zafi na neman hallaka sa, after few seconds Ajay yayi karfin halin breaking silence din a hankali yace "Makaranta daya mu ke tare da Jidderh a can America, so kawarta ta sanar mana abinda ke faruwa shi ne muka nemi ta bamu address mu zo nan duba ki" Sosai hankalin Mama Salame ya kwanta jin abinda Ajay yace, Mama Salame tace "Allah yayi maku albarka, kuma mun ji dadi mun kuma gode da zuwan da ku ka yi" Jay ya kwantar da murya yace "Kiyi hakuri Umma kuma ki kwantar da hankalinki, muna tabbatar maki in sha Allah komai zai wuce nan ba da dadewa ba, don za ayi duk abinda ya kamata, mahaifinta ma in sha Allahu za mu yi abinda ya dace a sakesa a yan kwanakin nan, ita kanta Halysaah zata dawo gida in sha Allah" Maman Salame ta daga hannu sama cike da farin ciki tace "Alhamdulillah ya Allah, gaskiya mun ji dadin jin hakan daga gare ku, don bamu da wanda zai tsaya mana sai Allah, Alhamdulillah" Ita dai Umma kanta na kasa hawaye na zuba idonta, Ajay yace "Zuwa gobe da safe in sha Allah za mu shigo" Mama Salame tace "To Allah Ubangiji ya kai mu goben lafiya, mun gode, mun gode" Mikewa Ajay yayi ya kara yi ma Umma sallama sannan ya fita daga dakin kar yayi suffocate, heat wan finish prince, don in akwai abinda baya shiri da shine zafi, baya son zafi ko yaya yake, Nenne na ganin Ajay ya fito daga dakin Umma ta sake komawa cikin bandaki da sauri, su Mama Zubaida da Mama Shatu suka bi sa da kallo har ya fita daga compound din, to su waye wannan kuma su da suka baza ido da kunne su ga an fito da Umma tana kuka, bayan fitar Ajay da few minutes sai ga almajirai suna shigowa gidan da buhun shinkafa biyu, carton din taliya biyu, carton din indomie biyu, manyan gallon na manja da mangyada, da carton din maggi duk kuma aka dinga dire su a kofar dakin Umma, daga Nenne har su Mama Zubaida haka suka saki baki suna kallon ikon Allah, Maman Salame ta taso zuwa bakin kofa tana kallon kayan abincin da mamaki tace "Ikon Allah, har da uban hidima haka??" Jay ya ajiye ma Umma 100k yace "Gashi Umma ayi cefane da wannan, in sha Allah gobe za mu shigo da izinin Allah" Bai jira cewar Umma that was speechless and shock ba ga hawayen dake sauka idonta kawai ya fita daga dakin..... [6/6, 5:08 PM] khaleesat Haiydar ✍️: Jay na fitowa dakin Umma, Nenne dake tsaye tsakar gida bayan ta fahimci ba yan sanda bane ta rushe da matsanancin kuka ta nemi er kujera ta zauna tana kallonsa tace "Da wannan uban kudaden da ku ka kashe na siyo kayayyakin abincin nan ai da belin ɗa na ku ka yi, wallahi maraya ne ba shi da kowa, in ba wani ikon Allah ba sai dai ya rube a can, wancan karan ni kadai nasan wahalan da na sha na ganin an sako sa, babu inda kafata bata shiga ba wallahi, na dinga bi gida gida ina neman taimakon kudi" Jay ya kwantar da murya yace "In sha Allah za mu yi bakin kokarin mu na ganin an sako sa kaka, ki kwantar da hankalin ki" Nenne na matsar kwalla da gefen haɓar zaninta tace "Ɗan nan ina hankalina zai kwanta ɗa na na can furson? In dai daga gidan radio da talabijin ku ke ni dai na amince ku zo ku dau muryata da fuskata in nemi taimakon al'ummar musulmai ku watsa ni duniya ta gan ni ina jawabi, kilan gwamna ma in ya gani yaji tausayina ya saka baki a sakar min ɗa na" Jay yace "Ba sai anyi haka ba Kaka, ina tabbatar maki nan ba da dadewa ba zai dawo gida in sha Allah" Nenne tace "To daga ina ku ke? Ko dai kungiyar kare haƙƙin en Adam ne" Jay ya ɗan yi shiru, Mama Zubaida da Mama Shatu dai sun yi cirko cirko a tsakar gida suna gwale ido suna kallon Jay, Jay yace "Makarantar mu daya da Halysaah a can Amurka, shi ne muka samu labarin abinda ya faru mu ka zo" Nenne ta mike da sauri tace "To ai yau kusan sati daya kenan ana neman ta ko sama ko kasa, wallahi bamu san inda take ba, ita uwar ta na daki tana jimamin ta, ni kuma ina nan ina jimamin ɗa na, haka muka raba abun, amma tun da yarinyar nan ta samu labarin daurin aurenta da annoban nan Awdul ta shiga duniya, wallahi bakina da nata tace min bata son sa bazata iya auren sa ba, tun da uwata ta haifeni ban taɓa ganin inda ake auren dole ba" Nenne na kai wa nan ta fasa sabon kuka, Jay dai ya ma rasa abinda zai ce mata, beside baya ma son yayi magana gaban su Mama Zubaida da suka wangale kunnuwa suna saurare, kawai ya saka hannu a aljihunsa ya ciro dubu ashirin din da yayi saura, yaje har gaban Nenne ya mika mata da ladabi yace "Ga wannan Kaka, in sha Allah za mu shigo gobe" Nenne ta daga hannu da sauri tace "A'a, gwara ku hada kawai ku kai furson a sako min ɗa na, don yafi min ko wani kudi a duniya" Jay yayi murmushi yace "Ki amsa kaka, na maki alkawarin za a sako sa nan ba da dadewa ba in sha Allah" Nenne ta amshi kudin da hannu bibbiyu tana sa masa albarka cikin rawan murya tace "In ma Allah ya sa kun zo gobe ba ku sameni a nan ba ku sa a raka ku gidana babu nisa daga nan" Yana murmushi yace "In sha Allah Kaka" Daga haka yayi mata sallama sannan ya fita daga gidan su Mama Zubaida suka bi sa da kallo babu fara'a ko wacce da abinda ke yawo a ranta, Nenne ta kulle kudin a habar zaninta ta soke tace "Dama gobe da asuban fari zan je gun Malam Na ta'ala, Allah ya sa in samu kwale kwalen da zai tsallakar da ni da sassafe" Dakin Umma ta nufa tace "To ke Salame kike ko wa? Ki fito mana ki shigar mata da dukiyar nan dake bakin kofa kar a faki ido a sungume mata wani abun, kayan abinci ai dukiya ce me zaman kanta a yanxu, Allah kadai yasan dubu dari nawa suka kashe wajen siyo kayan abincin nan...." Maman Salame ta fito daga dakin Umma ta fara shigar da kayan abincin ciki, Mama Shatu ta shige dakinta fuska a murtuke, Mama Zubaida ma ta tabe baki ta shige nata dakin ta sako tsumman labulenta dake rataye da kyauren dakin. Jay na fita waje ya tarar da Ajay cikin mota yana zaune a kujera me zaman banza ya kwantar da seat din kujeran idonsa a lumshe, Jay ya bude driver seat ya shiga yana kallon Ajay jin yanda ya kure AC din motar gaba daya, Ajay ya gyara zamansa yana kallonsa, Jay dai yayi murmushi ya fara driving motar Ajay ya nuna masa hanyar da suka bi suka fita ranan da yayi dropping Khaleesat, motar dake bayan su ma ya bi su, Ajay sai sake kare ma unguwan kallo yake with distress har suka isa main road, bayan sun hau saman titi ya kalli Jay yace "In za a samu gida ko na 30M zuwa 50M ne a siya pls su bar wannan vicinity din" Jay yace "I think that will be okay idan anyi releasing mai gidan but not now" Ajay yace "Duk daya ne Bruh, plss kayi ma Salisu magana a fara duba gidan daga yau zuwa gobe, that house isn't healthy for a living thing, ta yaya me rai zai dinga rayuwa a gida irin wannan? This is so pathetic, or am i exaggerating pls?" Jay yace "But haka kawai baza mu yanke decision without the release of the head of the House ba, so kake mu kara triggering saurayin nata bayan har yanxu ba mu yi achieving ko abu daya ba, we are following everything step by step Ajay, we will reach der in sha Allah" Ajay bai sake cewa komai ba, amma da gaske hankalin sa ya tashi kwarai ganin condition din cikin gidan most especially the compound, in ba dole ba shi kam babu abinda zai sake kai sa gidan nan, it's not about the house structure or where it's located but the hygiene of the house, sai kace cikin prison, ji yake kamar har ya kamu da cholera don har wani zazzabi zazzabi ya fara ji, ya kai hannu ya rage Ac din motar, shi dai Jay driving dinsa kawai yake. Washegari da yamma haka nan suka sake komawa gidan bayan Lauyan su yayi requesting su tambayi matan Malam Ali ko da akwai wani written debt forgiveness document kuma original one din da kotu ta bashi bayan masu karansa sun janye karar, cause in dai babu takardun to sai dai ayi case din biyan bashin da yake bin Alhaji Musa amma ba dai su yi karan sa ba, Bayan Ajay yayi parking ya juya yana kallon Jay yace "Zan jira ka" Er dariya Jay yayi yace "Toh ai da baka biyo ni ba kayi zaman ka a gida kawai" Bai jira cewar Ajay ba ya sauka daga cikin motar ya nufi cikin gidan, yau ma dai kamar jiya ba su kadai suka zo unguwan ba don securities da suka biyo su har sun fi na jiya tunda basu san ko Abdul na da Spy a unguwan ba, infact bazai ma rasa ba, definitely za a basa labarin wasu sun zo gidan su Khaleesat jiya, so they are not loosing guard by any means, and they are never going to let him take them unaware, A takaice Jay ya gaida Kishiyoyin Umma dake zaune tsakar gidan sun yi rashe rashe da su, yau ko murhu basu kunna ba don dawowar su kenan daga wajen Malamai, tun asuban fari suka bar gida sai yanxu suke dawowa, duk suka bi Jay da kallo, Jay dai yana tafe yana kallon Islam da Noor dake ma Umma wanke wanke a tsakar gidan don ko ba a gaya masa ba yasan siblings din Khaleesat ne duba da pheomelanin din su, a tare suka gaishesa ya sakar masu murmushi yace "How are you?" Murmushin kawai suka yi basu ce masa komai ba Islam na wanke wanke Noor na mata dauraya, Jay ya isa har kofar dakin Umma yayi sallama, Umma da ta gama gyara dakinta kenan ta saka turaren wuta na tsinke ta amsa sallaman sa, a kullum in zaka shigo dakin Umma a haka zaka tarar da shi fes fes, duk da ba komai bane a dakinta don ta siyar da komai nata amma kullum a gyara zaka same dakin da turaren tsinke, Jay ya shiga dakin Umma na kallonsa tace "Sannu da zuwa" Tabarma ta dauko ta shimfida masa don bata yi tunanin zai dawo yau kamar yanda yace mata jiya ba, Jay ya zauna yana murmushi ya gaisheta, Umma ta zauna kan dardumanta ta amsa gaisuwar sa, har a sannan zaka ga damuwar dake tare da ita alamar karfin hali kawai take, sai kuma ta mike tace "Bari in kawo maka ruwa" Ruwa ta debo masa a cup din stainless ta karaso ta ajiye masa a gabansa sannan ta koma ta zauna, yace "Nagode Umma" Ɗan murmushi kawai tayi, Mama Zubaida da Mama Shatu suka yi tsit a tsakar gida ko wacce ta kasa kunne ko zata ji abinda ake cewa a dakin Umma, Ajay ne ya shigo gidan duk suka zuba masa na mujiya, sau daya ya kallesu ya dauke kai ya nufi dakin Umma, yau dai tsakar gidan a bushe yake bai yi gaja gaja da ruwa ba da yake basu yi girkin siyarwa ba, Islam na tsaye bakin kofar dakin Umma bayan ta shiga da kayan wanke wanken da suka yi da twin sis dinta, Ita kuma Noor na share inda suka yi wanke wanke, Idan Ajay ya kalli Noor sai ya kalli Islam, ya amsa gaisuwar da Noor ke masa tana rike da tsintsiya, yana isa bakin kofar dakin Umma ya ja dogon hancin Islam don ita ce ke mugun kama da Khaleesat har bakinsu iri daya ne, murmushi tayi tana kallonsa yace "How are you?" Ta sauke idonta bata ce komai ba yanda dai Khaleesat ke yi, da sallama ya shiga dakin Umma, Jay ya daga kai yana kallonsu don bai yi tunanin zai shigo ba, Umma ta amsa sallamansa, ya zauna daga gefen Jay sannan ya gaisheta, Umma ta amsa da murmushin karfin hali tana masa sannu da zuwa, after some seconds Jay ya fara magana a hankali yace "Umma akwai wasu takardu na yarjejeniyar kotu na yafiyan bashin da aka yi ma Mai gidan nan, Allah yasa kun san in da takardun suke ana bukatarsu ne" Umma tayi shiru, can tace "To, amma wallahi ban sani ba sai dai ko a duba dakinsa ko suna nan" Jay yace "Eh a duba Umma, Allah ya sa a gani" Umma tace "Ameen" Mikewa Umma tayi ta fita daga dakin, Mama Zubaida da Mama Shatu suka bi ta da kallo har ta shiga dakin Malam Ali, after almost 8 mins sai ga Umma ta fito da wasu takardu wanda bata san ko na menene ba dai zata kai masu su duba ko akwai wanda ake nema a ciki, a haka ta wuce Kishiyoyinta da idanuwansa duk ke kanta, ta koma dakinta ta mika ma Jay takardun sannan ta koma kan dardumanta ta zauna, Jay ya dinga duba takardun daya bayan daya, yaga har da takardun makarantar Malam Ali, ashe har Degree garesa a Agriculture, kafin nan kuma sai da yayi diploma, yana ta dai duba tulin takardun har daga karshe yaga wasu takardun da yake saka rai na yarjejeniyar yafiyar da aka yi ma Malam Ali a kotu na biyan bashin Mahaifin Abdul ne, ya mika ma Ajay shi ma ya amsa yana duba takardun, Jay ya kalli Umma yace "Ina jin wannan ne takardun da muke nema" Umma tace "To Alhamdulillah" Jay yace "To za mu koma, duk yanda ake ciki za mu dawo in sha Allah" A hankali Umma tace "To Allah ya saka da alkhairi, amma sai dai akwai wata uwar dakina da bata ji ba bata gani ba yan sanda suka tafi da ita shekaranjiya har yanxu ba a ma san wani caji ofis din aka kai ta ba" Ajay dake kallonta yace "Ko Baabar nan ta Hotoro?" Cike da karfin hali Umma tace "Ita, wallahi bata ji ba bata gani ba aka je aka tafi da ita" Ajay yayi shiru yana kara mamakin stupidity din Abdul, he don't think that guy is okay in anyway, after some seconds ya kalli Umma a hankali yace "Za mu bincika inda aka kai ta mu yi bailing dinta in sha Allah" Umma ta share hawayen da ya kawo idonta ta kasa cewa komai, Jay yace "Ki kwantar da hankalin ki Umma, in sha Allah komai zai wuce da izinin Allah" Cikin rawan murya Umma tace "Allah ya sa" Jay ya kalli Ajay, tsabar tausayin Umma kawai yaga gwara su gaya mata gaskiyar inda Khaleesat take ko zata ɗan samu sukuni a ranta, Jay ya sauke idonsa a hankali yace "Sannan Umma akwai maganar da zan gaya maki yanxu, amma don Allah kar ki gaya ma kowa har zuwa sanda za mu gama abinda muke" Ajay ya juya ya wani kallesa don har ya gano maganar da Jay zai gaya ma Umma, Umma na share idonta tace "To in sha Allah" a hankali Jay yace "Halysaah na Lagos, amma don Allah ba ma son kowa yasan hakan Umma, ko makusantan ki kar ki gaya ma tukun....." Umma da zuciyarta ke bugawa tace "Lagos kuma? Wajen wa a Lagos?" Jay yace "Tana wajen sister din ki ne, amma mun ce mata kar ta nuna maki tana wajenta har sai sanda komai ya dai daita, shi yasa ma har yanxu bata gaya maki ba" Umma tayi shiru, amma fa ji tayi wani nutsuwa ya zo mata, lkci daya kuma taji hankalinta ya kwanta kamar an yaye mata kashi saba'in na damuwar da take ciki, Umma tace "In sha Allahu babu wanda zai ji hakan daga gare ni, yanda ku ka tsaya mana ku ma Allah Ubangiji ya tsaya maku haka, Allah ya saka maku da alkhairi..." Umma ta kasa ci gaba hawaye masu zafi na sauka idonta, A haka Ajay da Jay suka fita daga dakin Umma za su koma Office din lauya din su da takardun hoping shi ne kotu zata bukata, yau ma dai Ajay ji yayi kamar zafi zai kashesa a dakin Umma amma haka ya dinga daurewa har suka fita daga dakin sannan ya ciro handkerchief dinsa yana goge zufan da yayi, ya kalli Islam dake zaune bakin kofar dakin Umma da takardan makaranta a hannunta alamar karatu take, Noor kuma na hura gawayi a can gefe, ya saka hannu a aljihu ya ciro kudaden da bai san ko nawa bane ya mika ma Islam yana kallonta yace "Ku raba ke da er uwarki" Islam taki amsan kudin, ya hade rai yace "C'mon collect it" Jay dake kallonta shi ma ya sakar mata murmushi yace "Karba mana cutie" Islam ta kalli Noor amma still taki amsan kudin, Ajay ya zare mata ido yace "Kee, amsa nace" A hankali ta kai hannu ta amshi kudin, Ajay da Jay suka fita daga compound din, Kishiyoyin Umma suka dinga kallon uban kudin da aka ba Islam kamar idanuwansu za su fito ko kiftawan kirki basa yi, Islam ta tashi ta shiga dakin Umma da kudin a hannunta, Mama Zubaida ta mike ta ma Mama Shatu alamar su shiga daki, duk suka shiga dakin Mama Shatu sannan suka sake labule, Mama Zubaida ta rike haba tace "Anya kuwa Shatu baza mu san yanda za mu yi Abdul ya samu labarin abinda ke faruwa a gidan nan ba? Ni wallahi ban yarda wa ennan samarin basu san inda Khaleesat take ba, kina fa ganinsu kin ga 'ya yan masu kudi, dubi suturan da suka sa wa, ji motocinsu, sannan kalli fatarsu kalan ta yan hutu, in fa muka yi sake Shatu bakin ciki ne zai kashe mu a gidan nan muna ji muna gani" Mama Shatu tace "Ke ma dai wallahi kin fiye gaggawa, sai kace kin manta me Malamin yace mana, duka duka ba yau muka kai masa kudin ba, to mu zuba ido ya fara aiki mana tukun" Mama Zubaida tace "Duk da haka dai gwara mu ma mu dinga yin namu ta bayan fage Shatu, kada mu sakankance mu bar malami da aiki shi kadai, ya kamata tun wuri mu san yanda za mu yi mu ankarar da Abdul abinda ke faruwa a gidan nan, don gaskiya na sha jinin jikina da wa ennan zaratan samarin, ke ki ga tulin kudin da suka ba Islam, sannan kalli uban kayan abincin da suka jibge jiya daga karshe don walakanci aka biyo mu da kwano uku uku da taliya bibbiyu da man gyada da manja, sai maggi leda bibbiyu ga mayunwata, ke kiji wai yau Zahra'u ce da tsam mana kayan abincin da aka jibge mata, bayan haka Allah kadai yasan nawa suka bata a daki tunda ba gaya mana zata yi ba, ga Nenne ma a gaban mu aka bata rafar kudi yan dubu dubu, anya bamu shiga uku ba Shatu? Ni fa jikina yayi sanyi hankalina ya tashi, meye hadin su da Khaleesat din da har suke wannan hidima haka a kanta, mu ga 'ya yanmu a zube har yau babu mataya sai talla suke, ni fa wallahi ko tsirara zan yi yawo gwara inyi da dai Zahra'u da zuri'arta su ji dadi a duniya" Mama Shatu tace "Yanxu dai Gwaska za mu samu ya raka mu gidan su Abdul din tunda yace yasan gidan uban sa, nasan Abdul din zai taka ma yan iskan burki har ma ya bamu makudan kudi fallasa asirin abinda ke faruwa da mu ka yi" Mama Zubaida tace "Atoh dai tun wuri my gaya masa abinda ke faruwa, zuba ido ba namu bane wallahi, amma sai dai jibi kenan za mu je gidansu Abdul din don Gwaska ya tafi dambatta daxu uwarsa ke gaya min yaje kai kaya can" Mama Shatu tace "Ai jibin kamar gobe ne, kin ga gobe dama mu gama girkin mu da wuri mu tafi inda wannan matar ta mana kwatance daxu a gidan Malam" The next day wajen karfe biyar da rabi na yamma Sha'awa tayi sallama bakin kofar dakin Umma dake yi ma yan biyun ta gyaran gashi, babu kowa gidan don duk yan matan gidan basu dawo talla ba, kananun yaran kuma sun tafi gantali, tun Sha'awa bata shigo dakin Umma ba take cewa "Umma yanxu Ladingo ke sanar min an sako Gaje, wai daxu taje unguwan taga ana ta shiga gidan yi mata jaje" Umma ta sake gashin Noor ta mike da sauri tace "Da gaske Sha'awa?" Sha'awa tace "Wallahi kuwa Ladingo bazata min karya ba Umma, tace Gaje dai ta dawo gida ga yan unguwa na ta tururuwan shiga yi mata jaje tun daxu" Umma ta jawo Hijab dinta tace "To bari in je gidan Allah ya sa da gaske ne dai" Sha'awa tace "Da ina da kudin mota ai da mun je tare Umma, kusan kwanan ta biyar fa a kulle, don ma akwai kanwarta da zata kula da jikokinta tunda uwarsu na can Libiya ta tafi aikatau, ubansu kuma yayi watsi da su, banda haka da yaya makomar jikokin nan nata fisabilillahi?" Umma bata tanka ta ba ta gama saka hijab dinta ta daura nikab ta dau purse zata fita, Noor da Islam suka marairaice wai za su bi ta, ganin in ta tafi su kadai zata bari a gida yasa tace su saka hijab gaba daya, haka nan duk suka saka Hijab suka fita daga dakin Umma na biye da su, kusan kullum sai Umma taje gidan Gaje sau biyu ta duba ko ta dawo amma sai taga akasin haka sai dai ta samu kanwarta Iya a gidan, jiki a sanyaye take juyawa ta koma gida don Iya na ganinta take fara masifar ita ta saka er uwarta a uku, Umma zata fita gidan tare da yan biyunta sai ga su Mama Shatu da Mama Zubaida sun shigo wujiga wujiga da su, kana ganin fuskokinsu kasan a gajiye suke likis, ga wuyan hijabinsu duk yayi jagab da zufa, kafafuwarsu kuwa kamar wa enda suka dawo daga gona, Umma dai tayi masu sannu da zuwa kawai ta fita daga gidan su Islam na biye da ita, ai ko tana isa gidan Gaje taga da gaske an sako Gaje, Gaje na ganin Umma tayi kamar bata taɓa saninta ba a duniya, yanda take amsa gaisuwa da jajen masu shigo mata haka ta amsa ma Umma kamar ranan ta fara ganinta, ita dai Umma na zaune tayi shiru ta ma rasa me zata ce, su Islam na zaune gefenta, Gaje bata sake kallon direction dinta da yaranta ba, duk wanda ya shigo haka take sanar masa yanda Maman Fu'ad ta ci amanarta tace ma yan sanda ita bata taɓa ganinta ba ma balle wata Khaleesat, In tayi bayanin sai ta rushe da kuka tace "Ban taɓa tunanin Sadiyah zata min butulci haka ba duk alakar da ke tsakanin mu wai bata taɓa gani ba, kaji tsoron Allah kaji tsoron mutumin yau kawai, duk kyautata ma yarinyar nan da nake amma ta barni ni kadai raina a cikin matsalar da na tsoma kaina" Ita dai Umma tayi tagumi tana sauraron duk abinda Gaje ke cewa. [6/9, 7:26 PM] khaleesat Haiydar ✍️: Sai bayan da aka yi sallan Magrib Umma ta bar gidan Baaba Gaje da yan biyun ta, kuma har ta bar gidan Gaje bata nuna ta taɓa saninta ba don casually ma take amsa mata kamar yanda take ma kowa da ya shigo mata jaje, Umma dai a sanyaye ta baro gidan, tana isa gida taga mutane tsattsaye a kofar gida kowa da abinda ke fitowa bakinsa, sosai taji gabanta ya fadi gashi ta kasa fahimtar akan me ake ta surutu haka, can dai ta dubi wata makociyarsu dake tsaye wajen tace "Munnira me ke faruwa?" Munnira tace "Wallahi Umman su Khaleesah nima fitowa ta kenan da naji hayaniyar tayi yawa, amma wai kamar wasu mutane ne da ba a san ko su waye ba suka shiga gidan naku suka yi aika aika, ance a katuwar mota suka zo...." Umma ta kasa cewa komai tana kallonta, da kyar take jan kafa tana rike da su Islam ta shiga gidan har sannan gabanta bai daina faduwa ba, Su Mama Shatu da Mama Zubaida ta gani tsaye da 'ya yan su duk sun yi cirko cirko a tsakar gidan da makota ana ta maida magana, tsakar gidan dai cike yake da jama'a kowa na fadin albarkacin bakinsa, Umma ta dake tace "Wai me ke faruwa ne a gidan?" Mama Zubaida ta wani kalleta a walakance tace "Ina kuwa za mu san me ke faruwa tunda mu dai muna zazzaune sai ga wasu kattin gardawa sun kusa goma babu annuri a tare da su sun shigo mana gida da makamai suna tambayar dakin Malam, basu tsaya iya dakin Malam ba hatta sauran dakunan gidan nan sai da suka shiga..." Sai a sannan Umma ta lura da bakin kofar shiga dakin Malam Ali, gaba daya yayi kaca kaca da takardun da ta mayar daxu bayan su Jay sun dau wanda za su dauka, har kayan cikin dakin sai da aka watso su waje har da er katifarsa da akwatin kayan sakawan sa da butar alwalansa, Umma ta juya tana bin tsakar gidan da kallo taga har dakinta an fito da kaya an yi watsi da su waje, da kyar Umma ta karasa kofar dakin Malam Ali ta leka ciki taga basu bar komai ba, dama ba wasu abun kirki ke cikin dakin ba, can ta juya tana kallon Kishiyoyinta amma ta ma rasa me zata ce, Mama Shatu ta kyabe baki tace "Ni takaicina dakunan mu da suka shiga wai ina takardun da Malam ya ba mu ajiya, ni ko nace mu muka san wasu takardu mu da bamu yi karatu ba ta yaya Malam zai bamu takardu mu ajiye ai sai dai ko ya ba er sa da aka kai turai karatu daga karshe tayi ma wanda ya kai ta karatun butulci wai bata son sa kuma, amma ina mu ina ajiyar takardu mu da muke jahilai" Umma bata tanka ta ba ta duka tana tattara takardun dake watse bakin kofar su Islam suka je suna tayata, a haka duk ta maida kayan Malam Ali cikin dakinsa, su Mama Zubaida sai hararanta suke, can Mama Shatu ta kyabe baki tace "Mu dai mun san ko ma wani takarda suke nema bazai wuce yana da alaka da er ki ba kilan kotu za a shiga, tun da kika haifi yarinyar nan muke shiga jarabawa munana a gidan nan, ko kuma muce tunda aka auro ki, mu da bamu san wani talauci ba balle wahalar rayuwa, daga auro ki karayar arzikin da ba a taɓa yin irinsa a tarihi ba ya samu Malam, sannan gashi sanadin er da kika haifo ga abinda ya samu Malam a karo na biyu, daga ke har 'ya yanki babu wani abun alkhairi a tare da ku sai masifa, ina ma Malam zai yada kwallon mangwaro ya huta mu ma mu huta ki tattara ki koma can kasar ku ki auri buzu ɗan uwanki" Sha'awa dake tsakar gidan wanda tana daga cikin mutanen farko da suka shigo bayan Mama Zubaida da Mama Shatu sun kurma ihu, amma fa sai da gardawan suka fita sannan suka samu bakin ihun neman agaji su da yaransu, Sha'awa tace "Haba Mama Shatu, wannan wani irin magana ce kike yi haka don kin ga Ummansu Khaleesah bata tanka ku a gidan nan, wannan ai cin fuska ne, kar fa wataran ku kureta ayi dauki ba dadi a gidan nan, don mai hakuri bai iya fushi ba wallahi" Wani zagi Mama Shatu ta kundumo mata a fusace, Sha'awa ta rama tace "Wallahi ba dai ubana ba, sai ko in naki uban me gyaran keke dake kabari" Ganin fada na kokarin kaurewa a tsakar gidan Umma da wasu mata suka fitar da sha'awa dake kunduma ma Mama Shatu zagi ta uwa ta uba, ga su Labeebah na kokarin dambe da Sha'awa dake zagar masu uwa su ma duk aka rirrike su, a haka dai aka fitar da Sha'awa dake gyara daurin zaninta da ya kusa faduwa gashi babu komai kasan zanin, tana huci take cewa "Shegu en kutumar uba masu bin bokaye, ko jiya sai da aka bani labarin kun je wajen wani boka na kuma san warce ta raka ku, kun ga kuwa Umman Khaleesah ta fi ku ko a wajen Allah tunda bata san hanyar zuwa gun Malamai ba" A haka dai aka fitar da Sha'awa daga gidan, Umma dai jiki a sanyaye ta tafi kofar dakinta ta tarar su Islam suna ta maida kayan cikin dakin da aka watso waje bayan sun kunna er fitilar dake ba dakin hasken, Noor na kallon Umma tace "Umma kinga babu kayan abincin a inda suke" Umma ta kalli inda Maman Salame ta ajiye mata kayayyakin abincin da su Jay suka kawo taga wayam, tsayawa tayi tana kallon wajen babu ko kiftawa tsabar mamaki yasa ta kasa cewa komai, muryar Nenne taji a tsakar gidan cikin fushi tana cewa "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, meye haka aka cika gidan nan kamar ana taron farin ciki? Ku yan unguwan nan tsabar munafurci da gulma bakwa tashi shigowa sai iftila'i ya faru sannan ku bi ku cika ma mutane gida ko wacce da warin jikinta, farin cikin iftila'in ku ke ko menene haka? Doo Allah duk ku fita ku ba mutane waje mu ji da daya, ai ba kanmu farau ba, en iska kawai magulmata" Rai bace ta nufi dakin Umma hannunta rike da jarkar manja daya hannun kuma rike da tocilan ta, ta tsaya daga bakin kofa tace "Zahra'u me suka dauka a dakin Alin da suka zo?" Umma da ta zauna gefen katifar ta tace "Shigowa ta kenan nima Nenne, na je gidan Baaba Gaje an sakota daxu da yamma" Nenne ta kalli kayan da su Islam ke shigarwa daki tace "Har dakin naki suka shiga ne? To ni Usama ce min yayi iya dakin Ali suka shiga suka watso kayan ciki, ke kuma wa ya watso naki tsummokaran waje?" Mama Shatu tace "To shi da ya sulale ya gudu ya bar gidan ta yaya zai ce iya dakin Malam suka shiga? Ai babu dakin da basu shiga ba a gidan nan yau, mu ma duk mayar da namu kayan mu ka yi, hatta babban jarkan mangyada da na siya jiya sun dauke, iya shi suka dauka a dakina, Ita kuwa Zubaida kwashin adashin da aka kawo mata suka dauke" Nenne ta fara matsar kwalla cikin rawan murya tace "Lallai na ga abinda ya isheni bai ishi Ubangijina ba, to yan fashi Awdul din ya aiko mana wannan karan? Don dai duk mun san yafi karfin wani kudin adashin da bai taka kara ya karya ba balle wata jarkan mangyada, Allah mun gode maka da wannan rantsattsiyar jarabawan da mu ke ciki mun gode maka Allah, Alhamdulillahi ya Allah, Ina ga in ba tattarawa muka yi muka hakura da zaman birni mu koma kauye gaba daya ba muna cikin mummunan hatsari a Mariri gashi ba mu da gata, kar wataran cikin dare mun saki baki muna bacci su babbake mu, su babbake banza tunda babu me tsaya mana" Ita dai Umma tayi shiru bata ce komai ba, Nenne na kallonta tace "Su kuma samarin da suka sha uban fararen kaya suka zo mana nan suna kwambo dama yaudarar mu suka zo yi bamu sani ba, sun zo nan sun gama cika mana baki sai gashi tunda suka karkade wandonsu suka fita bamu sake ganin keyar su ba, to ina amfanin karya? har da ce min za a saki Ali kwanan nan ashe duk yan iskan gari ne makaryata bamu sani ba" Umma dai kallon Nenne kawai take, Nenne ta mika ma Islam jarkan manjan hannunta tace "Ba ruwana, wahalan da nake ta sha kan Ali ko shi ya halittoni duniya ai sai haka, kai kenan kullum ayi ta garkame ka kamar kasungumin barawo, sai kace wanda yayi ma Allah wani saɓon da bamu sani ba, saura kadan kwale kwalen da na hau jiya zan je nema masa taimako ya kife da mu banda Allah ya tsare, to ina dalili bayan ba shi kadai na haifa ba, in ya kasheni sauran su yi yaya? ke ungo amsa ki mika ma uwarki ta tsiyaya min manja, nawa ya kare" Islam tace "To ai an kwashe kayan abincin gaba daya Nenne" Nenne ta gwalo ido tana kallon direction din da aka ajiye kayan abincin taga wayam, bude baki tayi tana kallon Umma tace "Zahra'u ina kayan abincin? Ko kasuwa ki ka kai kika siyar? Fatarar taki ta kai haka Zahra'u?" Umma tace "Saboda me zan kai kayan abinci kasuwa in siyar Nenne, daga zuwa gidan Baaba Gaje in dawo nima na tarar an kwashe kayan abincin" Nenne ta ajiye jarkan hannunta a kidime ta saki salati tana tafe hannu tace "Baki kulle dakin bane Zahra'u?" Umma tace "In zan fita ai ina sa ma dakina kwado, to fasa kwadon aka yi, ga makullin ma a jakata" Nenne ta juya ta fita daga dakin dai dai shigowar Usama wani almajirin Malam Ali dake tare da shi tun yana da arzikinsa, kuma har yanxu dai yana tare da shi, Nenne na haska sa da tocila tace "Yauwa Usama kace iya wani daki mutanen suka shiga a gidan nan?" Usama yace "Iya dakin Alhaji kawai suka shiga" Nenne bata sake cewa komai ba ta nufi dakin Mama Zubaida don yafi kusa da ita, tana dage labulen dakin ta fara haske hasken tocila, sai kuma ta duka karkashin gadon karfen dake dakin ta hango carton din indomie biyu an tura su can ciki, ta kwalo ma Usama kira ya karaso da sauri tana haska masa karkashin gadon tace "shiga ka jawo min kwalayen taliyar yaran can" Ai ko ya shiga ya kwaso su ya fito da su, Nenne ta shiga cikin dakin tana duba bayan kyaure nan ma taga Babban jarkan man gyada ta sa Usama ya fiddo waje, ta gama duba dubenta a dakin bata ga wani kayan abincin ba sannan ta nufi dakin Mama Shatu, a bayan kyaure taga buhun shinkafa daya da quarter an lullube da zani, ta kwalo ma Usama kira shi ma ta saka ya kinkimo su ya fitar waje, a dakin Mama Shatu still taga kwalayen taliya da na maggi da jarkan manja duk ta sa Usama ya fiddo su waje, Nenne na kallonsa tace "Kwashe su ka mayar dakin Zahra'u Usama" Yace "To Nenne" Sai a sannan Nenne ta juya tana kallon su Mama Shatu da suka yi wuki wuki da ido ko wacce na kokarin diban ruwan alwala a buta, Nenne tace "An dai yi asara duniya da lahira, barayin banza barayin wofi, tirrr da halin ku, wato ga sabon jarin kayan abinci kun samu ko, tunda Zahra'un ta maida kanta er wahala warce bata san ciwon kanta ba, da ban ce a tsam min manja ba shiru zata yi maganar ta bi rariya ta bar ku da haram, ko zama da ku kadai ya isa ya dinga jefa Ali a masifa iri iri, ai ba kyau zama da jahilai shine kawai bai gane ba" Daga haka ta juya ta koma dakin Umma. Khaleesat na bakin pampon dake compound din Aunty Farida tana wanke wanke, ita kadai ce a gidan gaba daya don duk sauran tenant dake gidan sun fita aiki, Aunty Farida kuma ta tafi kasuwa, juyawa Khaleesat tayi jin an bude gate, ta mike tsaye tana kallonsa, murmushi ya sakar mata ya rufe gate din ya karaso cikin compound din shi ma yana kallonta, ta sauke idonta a hankali tace "Sannu da zuwa" Yace "Good morning Halysaah" Ɗan murmushi tayi ta sunkuyar da kai ta gaishesa sannan ta juya ta tafi ta bude masa kofar shiga parlon Aunty Farida tana kallonsa, yace "Aunty fa? ina ta kiran wayarta no response" Khaleesat tace "Eh ta bar wayar a gida ne ta tafi kasuwa" Ya kalli plastic chair dake veranda din Aunty Farida yace "Let me seat here ba sai na shiga ba, i just came to check on you" Khaleesat ta sauke idonta a hankali tace "I really appreciate Housemate" Yace "To ki zauna mana" Ta kalli second chair din dake wajen sannan ta zauna, sake gaishesa tayi da ladabi tana kallonsa, yace "Lafiya lau Halysaah, how is ur body?" Tana wasa da gefen karamin veil din jikinta tace "Naji sauki" Yace "To amma naga kin rame, baki cin abinci ne?" Tayi shiru, yace "Baki ci ko?" Ta ɗan yi murmushi tace "Ina ɗan ci kadan" shiru ne ya biyo baya for almost 30 seconds, ta ɗan daga kai ta kallesa taga kansa a kasa, ajiyar zuciya ya sauke calmly yace "Everything will be alright soon in sha Allah Housemate" Nan da nan hawaye ya cika idonta, da kyar tace "But i don't know my mom's condition, i am really worried" Jay yace "Don't worry, Umma tasan kina nan, mun je can gidanku da Ajay, i assure you everything is fine back home do not worry ur self pls, yanxu dai we are working on clearing ur dad first before anything, soon in sha Allah he will be free from the debt" Hawaye na sauka idonta tace "To amma ni bazan iya zama da Abdul ba tsoron sa nake wallahi, kawai torturing dina zai yi yayi revenging abinda nayi masa, i am afraid" Jay yace "Do not be Housemate, we won't allow that happen in sha Allah, we will go to any extent na ganin hakan bai faru ba" Khaleesat dai tayi shiru tana share hawayen idonta, after some seconds yace "Baki tambayi Ajay ba?" Ta daga kai tace "Na zata tare ku ke yana waje" Jay yace "Not at all yana kano, bai ma san nayi tafiya ba, i took an early morning flight, zuwa 12 noon kuma zan koma kano in sha Allah, i just came to check on you" Khaleesat na kallonsa cikin sanyin murya tace "Nagode sosai, kuma naji dadi" Ya kalli agogon wrist dinsa dake nuna karfe sha daya saura yace "I will be leaving for the airport now kar inyi missing flight dina, kafin Ajay yayi noticing i am not home ya fara damuna da kira" Khaleesat tace "Ko ruwa baka sha ba, ko in kawo maka shayi? Kilan ma baka yi breakfast ba ko?" Da damuwa tayi tambayar tana kallonsa, Yace "No i am okay Housemate" Wayarsa ne ya fara ring ya ciro yana kallon screen din yayi murmushi sannan ya nuna mata screen din taga Ajayn ne ke kiransa, mayar da wayar yayi aljihunsa sannan ya fiddo 100k ya mika mata yace "In case you need anything Halysaah" ta girgiza masa kai tace "A'a Nagode, bana bukatar komai wallahi" Mikewa yayi ya ajiye mata kudin a kafarta ya fita daga balcony din yace "Take care of ur self Housemate, idan na sake samun lkci ko zuwa nan da few days ne zan dawo in sha Allah, my regards to Aunty Farida" Khaleesat ta mike tana kallonsa ta kasa ce masa komai wasu sabbin hawayen suka cika idonta, ya daga mata hannu kawai ya nufi gate don bai ma son ganin hawayen nata, tana kallonsa har ya fita sannan ya rufo gate din, parlon Aunty Farida ta shiga ta zauna kan kujera ta rufe fuskarta tana rera kuka tana shessheka..... Bayan few weeks na zirga zirga a cikin garin kano, da kuma zuwa court lauyan su Jay yayi Succeeding na amsan Bail din Malam Ali, afterward suna sa ran kotu tayi dismissing claim din Alhaji Musa saboda previous debt forgiveness dake kasa, a kuma yi masa imposing monetary sactions for abuse of process, all this weeks Jay da Ajay where so cautious of der movement in kano and they were at alert In case of necessity ko kadan basu ba Abdul chance din yi masu ba zata ba cause sun san bazai rasa informant a unguwan ba, ranan da suka yi dropping din Malam Ali a gida bayan kotu ta bada bail dinsa farin ciki gun iyalinsa da wasu yan unguwan ba a cewa komai barin ma Umma, sai shigowa gidan ake ana taya sa farin ciki, shi ko Malam Ali har kasa ya duka cikin ladabi yana gode ma Jay da Ajay, shi dai Ajay ya juya ya koma jikin motarsa ya tsaya ya rungume hannu, ga motar escort dinsu a bayan motar tasa, Jay har ya gaji da ce ma Malam Ali ya dena masu godiya, Calmly yace "Don Allah Baba ka dena mana godiya, mu saboda Allah muka yi..." Malam Ali na gyada kai yace "To... to...to wannan gaskiya ne, Allah Ubangiji ya maku albarka, Allah ya saka da alkhairi, Allah ya kara daukaka, Nagode Nagode" Duk a birkice yake godiyan, Mama Shatu ta dauko tabarma ta shimfida tace "Taho ka zauna ka huta ko zaka dawo seti Malam, naga duk a firgice kake" Nenne ce ta shigo unguwan bayan wani almajiri yaje har gidanta ya sanar mata Malam Ali ya dawo, mayafin nata ma a baibai ta yafa ga dankwali da ta kima a kan mayafin tana hade hanya ta taho gidan ɗan nata, bata kula da Ajay a kofar gidan ba ta shige ciki da sauri, Ajay ya ciro wayarsa dake vibrate a aljihunsa yana duba me kiran sa, gyara tsayuwarsa yayi yana kallon screen din wayar babu ko kiftawa ganin Aunty Farida ke kiransa, haka kawai yaji zuciyarsa ta harba don Aunty Farida bata kiransa all this while, in ma da wani abu shi ne ke kiranta, ya kalli Jay da ya fito daga cikin gidansu Khaleesat, har sannan ya kasa daga kiran Aunty Farida. [6/10, 6:29 PM] khaleesat Haiydar ✍️: Jay ya karasa har inda Ajay ke tsaye yace "I think we can take our leave now, nan da friday sai a basa makullin sabon gidan, we just hope he will accept it" Shi dai Ajay bai ce masa komai ba don bai ma san me yake cewa ba, ganin yanayinsa Jay yace "Are you alright Bruh?" Jin Ajay bai basa amsa ba ya kalli wayar hannunsa that was still vibrating yace "Who is calling you?" Ajay ya sake kallon screen din sannan yayi picking dab da kira na biyu zai katse, kunne ya kai wayar yayi shiru yana sauraron yaji abinda Aunty Farida zata ce, muryar Khaleesat yaji a hankali tace "Good evening, Plss can i speak to my Housemate?" At first shiru Ajay yayi, can babu yabo babu fallasa yace "About?" Khaleesat ta girgiza kai murya can kasa tace "Ba komai, kawai dai ina son zan masa magana ne" Jay dai kallon Ajay kawai yake don bai san da wanda yake wayan ba, a takaice Ajay yace "Don't you have his digit?" Bai jira cewarta ba ya katse wayar ya mayar aljihu, Jay yace "Who is that?" Banza Ajay yayi masa ya bude driver seat ya shiga ya tada motar fuskarsa a daure, Jay ya daga shoulder sannan ya zaga ya shiga gaban motar shi ma bai sake kulasa ba, Ajay ya ja motar suka bar anguwan motar bayansu na biye da su. Bayan sallahn magariba Malam Ali na zaune tsakar gida tare da Nenne da duk matansa sai yaran gidan gaba daya, Nenne ce kadai zaune kan kujera er tsugunno, sauran duk kan tabarma suke a zaune kowa na jiran jin dalilin zaunar da su da Nenne tayi, Umma dai na kusa da bakin kofar dakinta da su Islam da Noor a jikinta, Nenne tayi gyaran murya tace "Da farko dai nayi farin ciki ainun da dawowan ɗa na daga furson a karo na biyu, ina rokon Allah ya sa iya bakin wahalarsa kenan sannan muna fatan yayi zuwan karshe kenan, wa ennan samari da suka zo suka tsaya mana kuma har suka kubuto da Ali Allah Ubangiji ya masu albarka don da farko na zata makaryata ne kawai en neman suna, duk da dama inda naje ance min za a roki Allah ya kubutar da ɗa na, nafi tunanin ma rokon Allahn da aka yi ne kawai hakan ta faru ba wai don samarin nan ba, mun dai gode koma ya ya ne, sannan shawaran da zan bada shi ne muyi bulaguro mu koma kauye gaba dayanmu na en shekaru kafin komai ya lafa, mu ma hankalinmu zai fi kwanciya da hakan don Alhaji Musa da tsinannen ɗan sa ba barin mu za su yi mu zauna lafiya ba, duk da kotu ta wanke Ali amma Allah kadai yasan wani sharrin za su billo da shi don mutane ne wa enda babu Allah a ransu, wallahi sai su iya sa wa duk a kona mu cikin dare muna bacci, kunga ance zaman lafiya yafi zama ɗan sarki shi sa cikin rufin asiri mu tattara komatsanmu ko zuwa gobe da magariba ne Ali ya mana shatan katuwar tirela mu koma kauyen mu" Mama Zubaida da Mama Shatu da suka saki baki suna kallon Nenne kusan a tare suka ce "Kauye kuma Nenne?" Nenne na kallonsu da kyau tace "Kwarai kuwa kauye, don dama can ne asalinmu, na gaji da tsallaka kogi cikin kwale kwale zuwa neman ma Ali taimako wataran inje in kife, gwara tun da sauran mutuncinmu mu bar garin nan" Mama Zubaida na girgiza kai tace "Inaaa, ai bazata saɓu ba gaskiya, sai dai ni a bar ni a nan in ci gaba da kasuwancina ina rufa ma kaina da 'ya ya na asiri, akan matsalar da buzuwar matarsa da er ta suka jawo baza a cucemu a mayar da mu riga ba, bazai ma taɓa yiwuwa bane gaskiya" Mama Shatu ta cafke tace "Sai dai ya tattara matarsa da 'ya yanta su kuma kauye Nenne, amma mu kam muna nan tunda ba mu ko 'ya yanmu muka jawo magana ba, dama mu ke ciyar da kan mu balle mu ji tsoron zamu rasa abinci" A fusace Nenne tace "A yaushe ku ka fara ciyar da kan naku munafukan Allah? ba sai bayan da ku ka tsiyace sa da fararen kafafuwan ku ba tukun? Ai ko Alhamdulillah kowa zai ma Ali shaidan kula da iyalinsa banda jarabawan shegun mata da Allah ya hadasa da, ku ne nan ku ka ja masa karayar arziki, dama ance min dukkanin ku babu alkhairi a tare da shi gwara ma Zahra'u, wallahi ce min aka yi in dai zai rabu da ke da Zubaida to arzikinsa zai dawo kaca kaca har fin na ɗa, Zahra'u ce kadai matarsa ta arziki aka ce min, da zai ji ta nawa ma duk ya sallameku in ga inda za ku koma idan ba kauyen ba, ke Zubaida kin manta kauyen da uwarki da ubanki suke sai sati sati ake kawo ruwan pampo? Kin manta ko wutar lantarki ba a ja maku har yau a kauyen ba? Kauyen da muka je na dawo ina ta amai da gudawa watana daya a asibiti amma har kina da bakin kushe namu kauyen da babu abinda babu? To wani ɗan iskan ne ma yace Rano kauye ce tukunna? Sannan ke shatu baza ma a kira garin iyayenki da kauye ba sai dai ace daji, haka nan muka dawo kano maguzawan mayu suka kamani da kyar aka samo kaina ba don Allah yayi da sauran shan ruwana a duniya ba da tuni na rasu wallahi" Shi dai Malam Ali yayi tagumi yayi shiru bai ce komai ba don tun kan Nenne ta kawo wnn shawara dama yake jin gwara ya koma garinsu don bai san da me Alhaji Musa da ɗan sa za su billo ba kuma, shi dai bai yarda kotu zata wankesa akan kudaden nan masu yawa ba gani kawai yake dadin baki su Ajay suke masa, Nenne tace "Yau ga samun waje kai, ita Zahra'u me yasa bata kushe shawarata ba sai ku masu fararen kafa, ko da yake ita ta guduwan er ta da ta shiga duniya ma take, mu bar ta taji da wannan ma" Mama Shatu tace "Wace er ta? Ai wallahi ko rantsuwa nayi bazan yi kaffara ba Zahra'u tasan inda er ta take, mu dai ne kawai aka rena ma wayo aka raina mana hankali" Mama Zubaida tace "To ai ba ma sai kin rantse ba Shatu, kwarai kuwa Zahra'u tasan inda Khaleesat take" Nenne dai sai kallon Umma da ko kallon kishiyoyin nata bata yi ba take, a hankali Nenne tace "Lallai biri yayi kama da mutum, na kuma yarda da maganarku don Zahra'u da na sani da har yanzu tana nan kan darduma sanye da dogon hijabi tana rike da carbi tana kuka ba dare ba rana duk ta fita hayyacin ta, kawarta Uwar Salame da makociyarku sha'awa me daddawa su yi ta shigowa suna dannarta su zazzauna kusa da ita kamar me takaba, amma ina lura da ita yau kusan sati uku kenan tana ta harkar gabanta kamar babu abinda ya faru, nima dai ko rantsuwa nayi bazan yi kaffara ba tasan inda Khaleesah take" Malam Ali ya gyara zama yana kallon Umma cikin lallami yace "Kiyi ma girman Allah Zahra'u ke da er ki ku rufa min asiri yanda Allah ya rufa maku, duk inda er nan ta tafi kiyi masu waya ta dawo ta amshi auren mijinta hannu bibbiyu, dama Allah ya riga ya kaddara Abdul ne mijinta mu din banza ne za mu canza hakan? don girman Allah ta rufa min asiri, ina cikin tashin hankali har yanxu wallahi don ban san kuma da me Alhaji Musa da ɗan sa za su dawo min ba, rufin asirina shi ne na damka masu Khaleesah kawai, in har suka kasheni wallahi banza kawai za su kashe tunda ba galihu ne da ni ba, tunda aka maida ni furson din nan nake rashin lafiya me tsanani, yanzu haka maganar da nake yi kirjina kamar an aza min katuwar dutse, ku yi min rai ke da er ki" Kamar zai yi kuka ya kare maganar, Nenne na matsar kwallan da babu tace "In wani abu ya same ka dama da Zahra'u da er ta zan yi kuka wallahi, don su ke kokarin salwantar min da kai ta karfi da yaji" Umma da hawaye ya cika idonta tace "To wai ta yaya zan san inda Khaleesah take ni ba waya ba balle ku yi tunanin tana kirana? Ko kun ga ina zuwa wani waje daga cikin dakina ne?" Mama Zubaida tace "Na rantse da wanda raina ke hannunsa Zahra'u kinsan inda makirar er ki take, don haka sai dai ki rena ma wani hankali amma ba mu ba, duk abinda ya samu mijinmu dama har karshen duniya mun yi ta ja ma ke da 'ya yanki Allah ya isa kenan, banda samun waje ita Khaleesah har tana da ta cewa da har zata bude baki tace bazata zauna da Abdul ba? Da me tafi Abdul din banda rufa mata asiri da yayi zai aureta? Mutumin da ya maida ta fess ya maida ta mutum ya kashe mata dukiya babu adadi don butulci da samun waje tace ita bata son sa kuma a ina aka taɓa tafka wannan iskancin? Wallahi ba a samu wanda zai ci ubanta bane shi yasa ta samu waje da yawa" Umma tace "Tun da har kuke tunanin nasan inda take kuma baza ku rasa sanin inda take ba ai, kilan ma za ku fi ni sani, don haka sai ku je ku fito da ita ku kai ta gidan Abdul din" Umma na kai wa nan ta mike ta shige dakinta, Mama Shatu tayi kasa da murya tace "Al-qur'an tasan inda take, da bata san inda take ba wallahi da har yau bata dena koke koke ba kilan har sai tayi rashin lafiya, kuma ni na ma fi zargin tana wajen kanwarta ne a garin Legas wallahi, in da ba haka ba ai da tuni mun ga Farida a gidan nan kamar an jefota amma gashi kusan sati uku har yau shiru Farida bata zo ba" Mama Zubaida tace "Ahaf ai mu ba yara bane" shi dai Malam Ali sai zazzare ido yake, Nenne tayi kasa da murya tace "Gaskiya na yarda da maganarku, don nima ina ta mamakin me yasa har yau farida bata zo ba, ita da ko tari yayarta tayi zata hawo mota ta kamo hanyar kano, amma ace an rasa Khaleesah yau sati uku shiru bata kamo hanya ba, ai da alamar tambaya" Malam Ali ya share zufar goshinsa duk da sanyin da ake shi ma yayi kasa da murya yace "To yanxu meye shawara? Ko ni zan shirya in tafi Lagos din ne?" Sosai hankalin Umma dake tsaye bakin kofarta daga cikin daki ya tashi don duk tana jin abinda suke cewa, Mama Zubaida tayi kasa da murya tace "Ai ban ma yarda da shiga dakin da tayi ba kilan er uwar zata kira, ko da yake bata da waya, kawai ina ga a gaya ma...." Mama Shatu ta ɗan tsunguli Mama Zubaida alamar tayi shiru, lkci daya Mama Zubaida tayi tsit, Nenne ta mike tana kallon Malam Ali tace "Mu je daga gefe mu yi shawara Ali" Mikewa Malam Ali yayi ya nufi can hanyar fita daga compound din Nenne na biye da shi, Mama Shatu ta mike tayi ma Mama Zubaida alamar su shiga ciki, suna shiga daki Mama Shatu tace "Ke ya muna neman maganar auren nan ya rushe gaba daya ko zai hakura yace a basa Labeebah ko Lamisah amma kike basu shawaran su je Lagos?" Mama Zubaida tace "Wallahi gaba daya na sha'afa kinsan kwakwalwar tawa, kuma kece kika kawo maganar Khaleesah, tun asali ma bai kamata mu ce komai ba gashi yanxu mun karkato da hankalinsu zuwa Lagos, sai fa Malam ya iya shiryawa ya kama hanyar Lagos wallahi" Mama Shatu tayi shiru, can tace "Ai ko in yaje lagos din nan shikenan tsarinmu ya lalace don taso keyarta zai yi su dawo kano ya mika ma Abdul ita, kinga shikenan mun tashi a tutar babu mun kai ba malamai kudadenmu a banza, tunda duk mun san Abdul din na sonta kuma hannu bibbiyu zai amsheta su fara rayuwar aure" Mama Zubaida tace "Toh kuwa ina ga da kaina zan kira Farida ince mata in har tasan Khaleesah na wajenta to tayi maza maza su bar gidan don Malam zai kama hanyar lagos tare da Abdul" Mama Shatu tace "A'a bari in shiga dakin Zahra'u in gaya mata hakan, tunda ga Nenne da Malam can sun kebe bamu san maganar da suke ba" Bata jira cewar Mama Zubaida ba ta fita zuwa dakin Umma, Zaune ta tarar da Umma bakin katifarta abun duniya ya isheta gashi babu waya hannunta, kuma in tace ta fita daga gidan ta amshi waya a makota tasan dole za a zargeta, kuma daxu da safe suka yi waya da farida ta wayar Mama Salame take sanar mata jibi za su Nijar da Khaleesat, Mama Shatu na kallon Umma tayi kasa da murya tace "Zahra'u, ga can Nenne da Malam suna shirya yanda za a tafi legas wajen Farida gobe da asubar fari, in dai kinsan Khaleesah na wajenta wallahi kiyi maza ki buga mata waya su bar gidan su tafi wani wajen, a ajiye batun kishi a gefe abinda baza ka so ma danka ba kar ka so ma ɗan wani, don duk mun san Abdul ba mutumin kwarai bane, kuma a zamanin nan an dena auren dole, mu ma ba a mana dole ba don haka baza mu yi ma 'ya yan mu ba" Mama Shatu na kai wa nan ta juya ta fice daga dakin, Umma ta mike gabanta na faduwa ta ɗan leka tsakar gidan taga Nenne da Malam Ali tsaye a can lokon tsakar gidan suna magana kasa kasa.... Jay ya fito daga kitchen hannunsa rike da mug din shayi yana juyawa a hankali, Step Mom din Ajay ce zaune parlon cikin shiga ta alfarma, a ranan ta sauka gidan tare da jakadiyarta sun dawo daga kaduna, Jakadiyarta na dinning area tana yanka mata fruit, Jay ya tsaya dai dai inda yake don bata san ya fito daga kitchen din ba, da wani kallon tsana kawai yaga take bin Ajay dake haurawa sama hannunsa rike da laptop dinsa, after few seconds Jay ya ci gaba da juya shayin hannunsa yana kallonta, tana jin sound din cokali ta juya da sauri tana ɗan murmushi ta hau canza channel din TV, shi dai Jay ya karasa cikin parlon bai sake kallonta ba, Jakadiyarta ta taho ta ajiye mata fruit din da ta gama yankawa cikin ladabi take sanar mata ga kayan marmarin, Cike da isa Aunty ta dau Apple ta fara ci, ta ɗan kalli Jay ganin sama zai wuce shi ma tace "Gobe Abbanku zai shigo wani taro" Jay yace "Mun yi waya da shi" Daga haka shi ma ya wuce sama, ta wani taɓe baki ta bi sa da kallo, Jakadiyar da ta zube gefenta cikin girmamawa tayi kasa da murya tace "Ranki shi dade, Allah ya ja zamaninki, daxu na jiyo mana wani labari Allah ya sa zaki yi maraba da wannan labarin" A takaice Aunty tace "Labari akan me?" Jakadiyar ta gyara zama tace "Akan Yarima" Aunty ta ajiye Apple din hannunta ta ba jakadiyar gaba daya attention dinta tace "Me kika jiyo?" [6/11, 8:28 PM] khaleesat Haiydar ✍️: Har mahaifin Abdul ya gama bambamin da yake yi a parlon Momy kamar zai ari baki bata ce masa komai ba illa rungume hannu da ta yi tana zaune kan kujera tana girgiza kafa fuskarta babu fara'a, Meemah dake zaune parlon ita ma dai bata ce komai ba fuska a murtuke, Alhaji Musa yayi bala'in sa me isarsa sannan ya juya zai bar parlon a fusace, sai kuma ya sake dawowa yana huci yace "Ina wawan Abdallan yake? Ina yake yaga abinda rashin tunaninsa da rashin daukan shawarar sa ya ja min" Momy ta tabe baki ita ma cike da takaici tace "Ai Alhaji yau kwana uku curr rabonsa ma da gidan gaba daya, kuma ba a samun sa a waya, ya kashe wayar" Rai bace Alhaji Musa yace "Duk shi ya ja min wannan bala'i ina zamana, wa yace masa dama ana harkar arziki da talaka? Sam ai ba a shige ma talaka duk yanda yake kuwa, tun asali zuri'ar da yake son in hada da wancan barawon mutumi ba wai nayi na'am da hakan bane, kawai bani da yanda zan yi da Abdallah ne" Momy ta gyara zama zuciyarta na tafarfasa tace "Atoh dai, har na gaji da nanata wannan sentence din da kayi Alhaji, ai ba a abun arziki da talaka don tun asali dama a tsiyace ya zo duniya kuma a tsiyace zai koma, kana zaman zaman ka gashi Abdullah ya ja maka asaran makudan kudi har da su taran kotu, wai kai da aka zalunta kai ne kuma da biyan tara saboda rashin adalci, ai Abdul bai kyauta mana bai duba mana ba, ace shi bazai dau maganata a matsayina na uwarsa ba? Babu yanda banyi discouraging dinsa kan tsinanniyar yarinyar nan ba na nuna masa ba ajinsa bace yaki saurarata wallahi, kyanta ne kawai ya rudesa wato kyan ɗan maciji, har tayin er aminiyata nayi masa amma firr yaron nan yaki, to ga dai abinda ya ja mana" Meemah tace "Ni duk ba wannan ba Momy, kawai so nake in san wasu 'ya yan shegun ne suka tsaya mata haka har suka maida case din kotu? Sannan ga auren ma suna kokarin kotu ta rabasa ta karfi da yaji, kun ga kenan mun tashi a tutar babu, kuma babu tantama duk yanda aka yi ma su suka boye yarinyar, su waye en iskan nan ne?" Alhaji Musa na safa da marwa a parlon yace "Don kotu ta kori karar nan ba shi ke nufin na bar wannan mutumi da ya salwantar min da dukiya ba, mu zuba mu gani da shi, sai na lahira ya fi sa jin dadi wallahi" Daga haka ya bar parlon kamar zai tashi sama, Momy ta sauke wani ajiyar zuciyar takaici tana girgiza kai tace "Abdallah bai duba mana ba wallahi, ya kaskantar da mu a idon duniya kawai, wai yau talaka ne ya ci nasara a kan mu a kotu, this is a big slap to us, kuma ko uban menene dalilinsa na dinga kashe waya ba a samun sa oho? Ni taran da aka ci Alhaji ne ma yafi ƙona min rai wallahi, ga mari ga tsinka jaka, ki sake kiran wayarsa kiji ko zai shiga" Meemah tace "Baza fa a samesa a waya ba Momy, mu da ganin Abdallah sai ya cika burin dake ransa kema ai kin san halinsa, gwara ma ki saka ma ranki salama mu bi sa da addu'a kawai" Momy ta kalleta tace "Wato kin san inda yake kenan?" Meemah tace "Ke dai kawai ki bi sa da addu'a Allah ya basa nasaran abinda ya saka a gaba Momy, amma shegiyar yarinyar nan ai kamar ta shigo gidan nan ne babu me hana hakan, don baza mu yi biyu babu ba" Momy ta tabe baki tace "Har ga Allah ni so nayi kawai ya hakura da er matsiyatan nan Meemah, kada tsautsayi ma yasa a hada iri da ita mu shiga uku, hada iri da talaka ai ci baya ne Meemah, don ni har cikin raina naki jinin talaka wallahi balle in hada zuri'a da su" Meemah tace "To ai dama bama fatan a hada iri da ita Momy, personally bazan ma bar hakan ya faru ba trust me, kawai ta shigo gidan ta gane Allah daya ne, ke kuma ki fara masa fafutukar wani auren da wuri wuri" Momy dai tayi shiru, can ta tabe baki tace "Allah ya sa ya saurareni to" Meemah tace "Haba dai zai saurareki, da kaina zan masa magana, a samar masa yarinya dai dai class dinsa" Momy tace "To ai shikenan, yanxu tracing din matsiyaciyar yarinyar ya sa a masa kenan?" Meemah tace "Ko ma dai menene mu dai mu zuba ido mu bi sa da addu'a kawai Momy" Mikewa Momy tayi tace "Bari in je in lallaba babanku, na dade ban ga ransa ya baci irin haka ba, haba ai abun da bacin rai, wai ace talaka yayi nasara akan ka a kotu bayan kai ne me gaskiya ai abun da ciwo" Daga haka ta wuce sama, Meemah ta dau wayarta tayi dailing number da take samun Abdul da shi ta tashi ta shiga dakin dake parlon. Da asuba ko sallah ba ayi Malam Ali ya fito da er jakar da yake tafiya da shi bayan ya mulke jikinsa da basilin saboda sanyin da ake, bin dakunan matan nasa yayi duk ya kwankwasa masu kofa, Mama Zubaida da Mama Shatu suka fito suna kallonsa da mamaki suka ce "Lafiya Malam?" Mama Zubaida tace "Ko tafiya kauyen ne ya taso?" Shi dai bai tanka su ba ya dinga goge takalminsa da yayi ƙura, Umma ce karshen fitowa ita ma ta tsaya tana kallonsa ta kasa cewa komai don tasan manufarsa, ko baccin kirki bata yi ba daren jiya tsabar yanda hankalinta ya tashi, Nenne ce ta shigo gidan yafe da zaninta tana ganin Malam Ali tace "Yauwa ko sallah kar ka jira kayi idan kaje tashar kayi a can Ali, ga er soyayyiyar nama da gurasa na kullo maka ka ci a hanya" Mama Shatu tace "Tafiya zai yi ne Nenne?" Nenne tace "Babu ruwan ku, ku dai ku yi masa fatan Allah ya kiyaye hanya" Malam Ali ya amshi kullin nama da gurasan da Nenne ke mika masa, yana kallon matan nasa yace "Toh sai Allah yayi min dawowa" Mama Shatu tace "To ai shikenan, Allah Ubangiji ya tsare Malam" Mama Zubaida ma tace "Allah ya tsare duk da muna da hakkin ka sanar mana inda zaka je da asuban fari Malam" Nenne tace "Bazai sanar ba Zubaida, uban me sanin inda za shi zai kara maki?" Mama Zubaida ta juya ta koma daki, Mama Shatu ma ta tabe baki ta koma dakinta, Nenne ta kalli Umma tace "Wato ke ce isasshiyar da bazata yi masa Allah ya kiyaye ba ko Zahra'u" Shi dai Malam Ali tuni har ya fice daga gidan, Nenne na nuna Umma tace "Mugun abun ku zai kare maku da ke da er ki wallahi, babu wanda ya isa ya salwantar min da ɗa na lokacinsa bai yi ba" Daga haka ta bi bayan Malam Ali da sauri zata rakasa bakin titi ya samu adaidaita sahun da zai kai sa tasha. That same day bayan an idar da sallahn asuba Jay ya shigo parlorn Mai martaba da sleepy face ta dalilin kiran da yayi masa, ganin irin zaman da Abba yayi kamar yana fadarsa ya gane serious issue Abban zai yi discussing da su kenan, ya kalli Ajay dake parlon zaune shi ma alamar kiran sa Abban yayi, Aunty ma na zaune parlon, Jay ya sauke kansa ya karasa kusa da Ajay ya zauna kasan lallausan carpet din parlon, dabi'ar Abba ne sai ya iya minti biyar zuwa goma kamar me nazari kafin ya fara magana in ya tara ku, Jay ya sunkuyar da kansa ya lumshe ido, Ajay ya ɗan kallesa sanin sai ya iya bacci a haka, ai ko yaga baccin yake, Ajay ya ɗan tunkudesa da elbow dinsa, Jay ya bude ido da sauri yana gyara zama, shi dai Abba kallonsu kawai yake, At last Abba yayi gyaran murya cikin nutsuwa yace "First of.... Ina son sanin zaman me ku ke har yanxu a garin nan baku karasa gida ba?" Duk suka yi shiru babu wanda yace komai kansu a kasa, Calmy Abba yace "Ohk take ur time, amma kuyi kokari ku je gida kafin hutun ku ya kare, Secondly.... maganar da nayi da ku a Maryland naji babu wanda yace min komai a kai har yanxu, ga lokacin da na baku ya cika, nayi maku uxurin mantuwa shi yasa nake tunatar da ku yanxu..." Nan ma duk suka yi shiru babu wanda yace komai, shi ma Abban yayi shiru yana kallonsu yana jiran amsa a duk sanda suka shirya, sun san shirun da Mai martaba yayi amsarsu yake kira ko da zai dau 10min ko fin haka ma kafin su basa amsan he won't mind zai jira su patiently, sanin halin Abban nasa yasa Ajay ya daga kai, Softly yace "Ayi hakuri ranka shi dade ba mantawa muka yi ba, in sha Allah we are working on that very soon" Mai martaba yace "Is that so?" Ajay ya sauke kansa don kalman Abba na nufin bai gamsu da abinda yace ba kenan, Shi dai Jay yaki dago kai, a hankali Ajay yace "A gafarce mu a ɗan kara mana lokaci Abba..." Aunty da har ta fahimci maganar da ake ta ɗan yi gyaran murya ta nemi permission din magana gun Mai martaba, ya gyada mata kai alamar ta fadi abinda zata fada, cikin nutsuwa tace "In na fahimci maganar da ake ranka shi dade, magana ce akan su fito da matan aure duba da yanda shekarunsu ke gaba ba baya ba, wannan magana kuma ba sabuwar magana bace don an fi shekara 3 ana yin ta amma babu wani progress, a takaice basa daukar maganar da muhimmanci, to amma dai ina ga ka ɗan sha'afa ne ur Highness, don shi Jawwad ai akwai maganar sa da Hadeeyah a kasa duk da ba wai maganar tayi karfi bane kuma wannan hadi, hadi ne me kyau da zai kara karfafa zumunci don mahaifiyar Hadeeyah jininka ce kuma ita ta kawo wannan shawara duk da Fulani wato mahaifiyar Jawwad uwar dakinta ce tun asali, shi kuma Junaid a yanda na lura da shi zai fi maraba da zabin ka garesa duba da nature dinsa da rashin choice dinsa, don haka shi Jawwad a tsaida maganar sa da Hadeeyah kawai ina ga hakan zai fi, shi kuma Yarima i think we should get him a princess from neighbouring states, ko ni zan iya jagorantar hakan don arranged marriage zai fi suiting dinsa duba da nature dinsa, kuma ina son a bar komai a hannuna ranka shi dade..." Ajay ya daga kai ya kalleta zai yi magana mai martaba ya dakatar da shi, Ajay ya sauke kansa, Speaking Calmly Mai martaba dake kallon Ajay da Jay yace "Za ku iya tafiya, Allah yayi maku albarka" Sai a sannan Jawwad ya dago kai ya kalli Aunty dake ɗan murmushi ganin Mai martaba yayi na'am da shawaranta, tuni Ajay har yayi disappearing daga parlorn fuska a murtuke, Jay ya mike shi ma ya bi bayan Ajay yana tafiya a hankali, bai taɓa sanin baya son Hadeeyah da aure ba sai yau da Aunty ke bada shawaran a tsaida ranan aurensu da ita, yasan kuma duk abinda Aunty tace kamar Abba ya aikata hakan ya gama ne, kawai yaji hankalinsa yayi mugun tashi yaji wani zufa na keto masa, dakinsa ya shige ya kulle da makulli ya jingina da kofar ya lumshe ido zuciyarsa na bugawa, Ajay na shiga dakinsa shi ma ya kulle da makulli ya zauna gefen gado ya dafe kansa da hannu biyu, this is not the first time da Aunty ke kasalanda akan duk abinda ya shafesa gashi Abbansa baya basa listening ears ko me Aunty tace masa kawai haka za ayi abun nan komin munin abun, at this point he felt he is of no importance to his father, he felt dejected, and it's been like this for so many years, he have no one to stand for him, a hankali ya juya yana kallon wayarsa dake vibrate, Number Aunty Farida ya gani a gaban screen din wayar, ya kalli agogo yaga karfe shidda da minti biyar na safe, request din Khaleesat na jiya da ta kirasa ya tuna, hakan yasa har kiran ya katse bai daga ba knowing she might be the one calling, kiran ya sake shigowa ya kalli screen din nan ma bai daga ba har ya katse, sau hudu kiran na shigowa continuously, hakan yasa ya maida attention dinsa kan wayar ya ɗan yi jim with different thought running his mind, ganin kiran ya katse an sake kira making it the 5th time of calling yasa ya dau wayar ya daga ya kai kunne yayi shiru waiting to hear who is on the line, a hankali ya mike jin abinda Aunty Farida ke ce masa ta wayar, bai san sanda ya zame wayar daga kunnensa ba rate din heartbeat dinsa na karuwa, da sauri ya nufi kofarsa ya bude ya fice daga dakin ya murda kofar dakin Jay yaji a kulle, knocking ya dinga yi non stop kafin Jay ya bude kofar da mamaki yana kallonsa yace "What is it?" Ajay ya shiga dakin yana shafa gashin kansa da wani expression yace "He tracked her to Lagos" Still Jay yayi a inda yake tsaye ko kwakkwaran motsi baya yi yana kallon Ajay, Ajay ya ja numfashi sannan ya zauna kan kujeran dakin ya lumshe idanuwansa ya jinginar da kansa jikin kujeran trying to calm himself, Jay was speechless and shock at the same time, da kyar ya ja kafa ya zauna gefen gadonsa ya dafe kansa da yaji yayi masa nauyi, kamar an tsikare Ajay ya mike yace "Book us ticket to Lagos" Daga haka ya fice daga dakin. [6/12, 8:02 PM] khaleesat Haiydar ✍️: Aunty Farida ta share hawayen da yaki tsaya mata tana kallonsu Ajay da kyar tace "Wallahi ban san ko har su nawa bane a motar, ban ma san ya motar take ba tunda ina cikin gida sanda abun ya faru, yaran makota dake diban ruwa a bakin rijiyar tare da ita ne suke cewa kawai suna diban ruwa sai ga motar ta shigo street din, wasu mutane suka sauka a motar suka ja ta zuwa cikin motar suka tafi da ita, a sannan an idar da sallahn subahi kenan kun ga gari bai waye ba ai" Ajay was speechless, bai taɓa zama confuse haka a rayuwar sa ba don ya ma rasa abun cewa, likewise Jay dake jingine jikin mota tun da suka iso unguwan dama shi bai ce komai ba, Ajay ya daga kai after some seconds ya kalli Aunty Farida a hankali yace "Amma yana da number ki ne Aunty?" Aunty Farida tace "Ba shi da wannan number tawa gaskiya sai tsohon layi na, kwanaki Maman Khaleesat tayi rashin lafiya sai na tafi kano dubata to a hanya na yar da wayata, da na zo kano sai na siya sabon layi kafin inyi welcome back din tsohon layin, to har yanxu ban yi welcome back din ba" Ajay yayi shiru yana nazari, Aunty Farida na hawaye tace "Tsautsayi yasa ta fita deban ruwan yau, amma tunda ta xo wallahi ni ke diban ruwana bana barin ta dibar min tunda har yanxu gata nan ne dai bata dawo dai dai ba, wani lkcn ma da daddare idan na dawo kasuwa nake yi tunda ana wahalar ruwa a season din nan don yawanci rijiyoyi kafewa suke yi sai ana bari ruwan na taruwa sannan a diba, gashi ba a samun wuta balle a samu ruwan pampo, a jiyan nayi girki me yawa ne na wani biki duk sai na gaji ban deba ruwan da daddare ba, da na tashi kuma sai nake jin zazzabi, kun ji dalilin fitarta ta debo mana ruwa kenan" Ajay ya jingina da motarsa ya lumshe ido ya bude, gaba daya ƙansa ya gama kullewa, bai yi zaton Abdul ya wuce yanda yayi zatonsa ba, the guy is really something else ko wani salon tactics na mugunta ya san sa gashi har yau yaki kunna wayarsa balle a san inda yake, ko by mistake baya kunna layin, shi dai Jay dama bai taɓa underrating Abdul ba dai dai da rana daya duba da irin actions din da ya dinga portraying, kawai dai tracing din Halysaah har zuwa Lagos is the least thing da yayi zaton Abdul zai yi, tunda bashi da access da Aunt dinta, but like seriously how did he even find his way, bayan bashi da active line din Aunty Farida sannan bai san unguwan da take ba, ya sauke wani boyayyen ajiyar zuciya yana tunanin ta inda za su fara billo ma wannan lamari, tunda dai babu ta yanda za su ce yayi kidnapping Halysaah da ke a matsayin matarsa ta sunna. Khaleesat na zaune at the far end of the large room ta hade kanta da gwiwa, zuwa sannan ta hakura da kukan da take don ba ma ta da strength din kukan amma tana jin zuciyarta na mata zafi ga wani azababben ciwon kan da take ji da kishin ruwa da ya dameta, tafi awa sha biyu zaune a dakin ba ci ba sha, don tunda aka shigo da ita har zuwa sannan babu wanda ya sake zuwa dakin, infact bata ji motsin kowa a gidan ba alamar ita kadai ce a ciki, bandakin dake cikin dakin take shiga tayi alwala ta fito tayi sallah duk da ba sanin lokaci tayi ba kawai tana amfani da instinct dinta ne, at this point in time tasan bata da wani sauran gata sai wajen Allah, domin kuwa tasan Abdallah ne kawai zai sa a zo ayi mata irin wannan daukan, wasu hawaye masu zafi suka zubo idonta tana tausayin rayuwarta, all she could remember vividly was that tana bakin rijiyan dake kusa da gidansu Aunty Farida tana diban ruwa wasu mutane biyu suka zo a mota, lokaci daya kuma suka yi leading dinta zuwa motar tasu, at first turje masu tayi ta fara kokarin raising alarm tana ihu, yaran dake bakin rijiyan duk suka gudu suka shige gidajensu, tana kururuwa daya mutumin ya rufe fuskarta da wani Handkerchief da sauri, taji ta shaƙi wani abu kamar dust, lkci daya kuma ya cire handkerchief din a fuskarta, daga nan kuma ko kokarin ihun bata sake yi ba cause she became weak, ita dai tasan all through the ride she was conscious but not fully, gashi ta kasa tabuka komai don duk jikinta ya mutu, kanta yayi mata nauyi idonta suka dinga juya mata.... Da sauri Khaleesat ta dago kanta ta mike tsaye jin ana ƙoƙarin bude kofar dakin ta waje da makulli, gabanta ya dinga bugawa da karfi idonta na kan kofar har ya bude ya shigo, she wasn't expecting anyone but him dama, ta sauke kanta bayan sun hada ido, wasu sabbin hawayen suka fara zuba idonta, muryarsa taji ya daki kunnenta cike da isa da gadara yace "Har yanxu Body guards din naki basu biyo bayanki bane? Ai yaci ace sun iso zuwa yanxu don naga It's almost 12 hours now, how comes basu zo cecen ki ba duk capacity din su" Sai a sannan Khaleesat ta daga kai ta kallesa cikin rawar murya tace "Ka ji tsoron Allah...." Kasa ci gaba tayi ta fashe da matsanancin kukan takaici, shi dai yana tsaye yana kallonta da wani murmushin mugunta kwance fuskarsa, ta dago kai da sauri jin yana takowa har zuwa inda take tsaye, mannewa tayi da bango tana jin kamar bangon ya tsage kawai ta shige gabanta na bugawa da karfi, sai da ya zo dab da ita cikin kwantar da murya yace "Me kika ce?" Ta girgiza masa kai da kyar gabanta na ci gaba da faduwa muryarta na rawa tace "Kaji tsoron Allah Ya Abdul, kaji tsoron...." Bata rufe baki ba taji saukan lafiyayyen mari a fuskarta wanda sai da taga taurari, ta dafe kuncinta tana kallonsa babu ko kiftawa, cikin husky voice dinsa yace "You still have the guts to repeat what u just said saboda baki da kunya ko? Ni zaki gaya ma in ji tsoron Allah? To tsoronki zan ji ko tsoron uban ki dake Mariri idan ban ji tsoron Allah ba?" Da kyar Khaleesat ta dake tace "Ka zageni amma kar ka sake zagar min uba" Still bata rufe baki ba ya sake sauke mata wani wawan marin a other side of her face, this time around sai da dakin ya juya mata don ba marin wasa yayi mata ba, ya fixgota yana mata wani irin kallon da ya gigitata don tuni idonsa yayi jajur yana huci yace "Ina magana kina mayar min how dare you poor wretched girl?" Ta fashe da matsanancin kuka tana jin dama Allah ya dau ranta kawai ta huta a wannan lokacin, zata durkusa kasa ya hadeta da bango yace "Yau ina body Guards din naki dake goya maki baya kina min iskanci? Tell me where they are today? Da aurena a kanki kike hulda da wasu banzayen gardawa saboda ke jahila ce warce bata san me take ba" Tana kuka sosai bata san sanda tace "To wai ana aure dole ne dama Abdul? Nace bana son auren, bana son ka, gwara kawai ka kasheni duk mu huta" Da karfi ya bugata da bango har sai da taji numfashinta ya dauke na few seconds, yana mata wani mugun kallo yana huci yace "Dama ke baki san aurena wajibi ne a gare ki ba ko kina so ko ba kya so? Dama shi ubanki bai gaya maki hakan ba ko mantawa kika yi saboda kin fara bin maza? Wallahil Azeem kin ji rantsuwar musulmi ko? Duk ranan da kika sake yunkurin guduwa ko kuma yin wani silly act to rayukan twin siblings din ki za su zama fansar aurena idan kika kuskura kika min jakanci, ko kina so ko baki so lallai dole ki zauna da ni ko kuma in salwantar da ran kanninki i am promising you this Billahil Azeem, kuma babu abinda zai faru don tamkar na kashe banza ne daga ke har iyayenki babu abinda za ku yi, su kansu Body guards din naki ba kyalesu nayi ba don sai na dau revenge din intruding da suka yi a sabgata, i will teach them a lesson kina ji kuma kina gani" Khaleesat ta kasa cewa komai don sama sama kawai take jin numfashinta kalmansa na cewa zai salwantar mata da siblings dinta ya sa jikinta ya fara rawa, ya juya cike da isa ya tafi ya bude closet din dakin wanda duk kananun shegun kaya ne yace "All this are your wears, in kin yi sallah kin shirya ki zo ki sameni a dakina which is 3 rooms away from this, ina jiranki at exactly 7pm and this is just 6:30pm" Yana kai wa nan ya fice daga dakin yana rike da key din dakin, a hankali Khaleesat ta sulale kasa tana sauke numfashi tana jin wani abu ya tsaya mata cak a zuciya, gashi ba ta ma da strength din da zata yi kuka sosai ko zata ji relieve don tun jiya rabonta da abinci, she was just weak and helpless, ga idonta da taji ya fara ciwo saboda marin da yayi mata don dama ba warkewa idon yayi gaba daya ba lkci lkci tana jin yana damunta, tsoro da fargaban kada ya sake dawowa dakin yayi mata fiye da abinda yayi mata yasa Khaleesat tayi karfin halin mikewa da ɗan sauran strength din ta da ya rage tana tafiya da kyar ta shiga bandakin dake cikin dakin ta tara ruwan pampo tana sha ko zata ji saukin abinda take ji a zuciyarta, bayan ta sha ruwan ta dinga kallon fuskarta da yayi ja ta madubi, a hankali ta zame kasan bandakin ta jingina da tile din bangon hawaye masu zafi na zarya a fuskarta, tafi minti goma a haka lokaci daya ta yunkura ta mike bayan ta tuna time din da ya bata kar ya sake dawowa, she wish akwai makulli a jikin kofar bandakin don da kulle bathroom din kawai zata yi in ma mutuwa ne tayi a haka don yafi mata kasancewa da Abdul, cikin rashin kuzari ta cire hijab dinta da kayan baccin dake jikinta ta fara wanka da shower gel din dake bandakin, komai na bukatar mace akwai a banɗakin everything is just set, after a while ta gama wankan ta wanke bakinta ta fito sanye da dogon hijab dinta with different thoughts running her mind, tunda ya bar kofar dakin a bude ko dai ta samu ta lallaba ta fita and find a way for her self, duk da tasan Abdul will never be that stupid da zai bar kofa a bude har ta samu ta fita, infact in ma ta fita daga building din gidan tasan definitely akwai mai gadi a bakin gate kuma babu ta yanda zai bar ta ta fita, kilan ma Abdul din ya sanar masa in zata fita kar ya bude mata gate, but still ita dai burinta ta samu ko daki me makulli ne ta shige ciki ta kulle kofar sannan ta bar key din a jiki yanda ko spare key idan aka saka za a bude kofar bazai budu ba sbda key din da ta bari a jiki, da wannan tunanin ta nufi kofa gabanta na faduwa ta bude kofar dakin a hankali zata fita suka kusa cin karo da shi, rikicewa tayi ta juya da sauri zata bar bakin kofar ya fixgota, bakinta na rawa tace "I am very thirsty" fuskarsa babu wani rahama yace "Follow me" Bata iya ta masa musu ba tunda taga kiris yake jira ya mareta a ko da yaushe, at every slight opportunity marin ta kawai yake, tana biye da shi zuciyarta na bugawa suka shigo Main parlor din gidan, karshen haduwa gidan ya hadu amma ita ko lura da hakan bata yi ba don ta kanta kawai take, tana biye da shi ya kai ta har kitchen din gidan, ya juya ya kalleta a takaice yace "Gashi nan ki dafa abinda zaki ci don bani da time din fita in siya maki komai tunda kina da hannun girki, after that ki dafa min lipton ki kai min dakin da nace" Ita dai Khaleesat na rakube jikin kofar kitchen din gaba daya hankalinta baya jikinta, taga yayi ficewarsa ya bar mata kitchen din, ta bi sa da kallo har ta dena ganinsa, ta zame kasa ta hade kanta da gwiwa cikin rawan murya tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, na shiga uku na lalace" ta kusa minti biyar a haka kafin ta yunkura ta mike tana goge hawayen da yaki tsaya mata, tana tafiya a hankali ta nufi kofar parlon ta murda taji a kulle kuma babu makullin a jiki she wasn't surprise don tasan dole zai kulle gidan, haka duk sai da ta bi dakunan dake gidan ta murda su taji a kulle kuma babu makullansu a jiki, a sanyaye hawaye na bin fuskarta ta koma kitchen din, duk da rabonta da abinci tun jiya amma ko yunwan bata ji tsabar tashin hankali, kawai jikinta ne yayi weak taji strength dinta duk ya kare, wnn yasa ta ɗan hada shayi kadan a cup zata sha, shi ma dai ta kasa sha don bata da appetite, haka nan ta zubar ta dau black tea din da yace ta dafa masa ta fito daga kitchen din, dai dai san da ya shigo parlon, sunkuyar da kai tayi rate din heartbeat dinta na karuwa cause he is just wearing short and singlet, cike da karfin hali tace "Ga tea din" Babu yabo babu fallasa taji yace "A nan nace ki bani tea?" Ita dai bata ce komai ba amma kana ganinta kasan a mugun tsorace take, tana hade hanya ta nufi inda yace ta kai masa shayin yana biye da ita a baya, da ace tashin hankali da fargaba na kashe mutum ya ci ace ya kashe Khaleesat a wnn moment din, a bakin kofar dakin ta tsaya cikin rawan murya tace "Ga tea din" Wani tsawan da ya kidimata yayi mata don bata ma san sanda ta shige dakin ba ta je ta ajiye masa Mug din tea din a kasa tana waige waige, ya shigo dakin ya tura kofar fuska a daure yace "Cire Hijab din nan, kuma yau ya zama first and the very last day da zaki min yawo da Hijab a gida" Ta durkusa kasa ta fashe masa da kukan tashin hankali tana kallonsa, ya mata tsawa yace "Are you daft?" Cikin kuka tace "Wallahi sallah nake son inyi ne kayi hakuri" Darduma ya nuna mata a takaice yace "Je kiyi" Jiki na rawa ta mike ta tafi kan darduman ta fara sallah jikinta na rawa, tayi raka'a ya fi sha biyar ita kanta bata sani ba, kawai daga bayanta taji ya fixge hijab din, tun bai karasa cirewa ba ta fara kokuwa da shi ta rike hijab din gam tana kiran Ummanta cikin rikicewa, amma da yayi mata wani riko da hannu daya sai da ta gane Allah daya ne, don ko kwakkwaran motsi kasawa tayi, tana ji tana gani ya fixge hijab din ya jefar da ita kan gado rokonsa ta dinga yi da duk kalman da ya fito bakinta tana cewa "Ina rokon ka da girman Allah kayi hakuri Yaya Abdul, don Allah ka min rai kayi hakuri, in kana yi ma darajan iyayenka kayi hakuri, wallahi ban gama sallan da nake ba...." Ya gama kare mata kallo at the same time yana surveying every bit of her beautiful and breathe taking body, komai yayi masa yanda ya kamata, ashe asalin kyanta na boye all this while bai sani ba, yayi tarayya da mata iri iri amma bai taɓa ganin mace that is so beautiful while naked kamar ta ba, iya haskenta kadai ya isa ya rikita mutum, tuni idanuwansa suka sauya launi ya cire singlet dinsa yana kallonta kasa kasa yace "In ma kika yi taurin kai kece a wahale don that isn't stopping me in anyway Baby gal, just relax and i won't be rough" Kara gigicewa Khaleesat tayi tana rokonsa at the same time tana kokarin sauka daga kan gadon ya fixgota ya mayar da ita saman gadon yana kallonta cikin husky voice dinsa yace "Do not allow me give you a dirty slap...." Bata ma san me yake cewa ba still zata sake sauka taji ya danneta kan gadon, roughly ya fara exploring dinta kamar ya samu er hannu.... [6/13, 9:19 PM] khaleesat Haiydar ✍️: Ko minti uku Abdul bai yi da fara taɓa ta ba Khaleesat taga ya koma gefe lkci daya, da sauri ta mike tana komawa baya har sannan bata dena kukan da take tana basa hakuri ba cikin rikicewa, after some seconds ya juya ya kalleta da rinannun idonsa, suna hada ido ta kara rikicewa muryarta na rawa cikin kuka take cewa "Don girman Allah kayi hakuri, i am begging you please kayi hakuri" Ya jefa mata wani kallo ya mike kamar zai tashi sama ya nufi kofa ya fice daga dakin, ganin hakan tayi kamar a mafarki ta kasa ko kwakkwaran motsi, kamar ance ta sauke kanta taga jinin da ya ɓata farin zanin gadon da take kai, ta dinga komawa baya a hankali tana kallon jinin babu ko kiftawa zuciyarta na bugawa at the same time, and she realize daga jikinta yake fita, lokaci daya ta tuna rabonta da period tun a Maryland almost a month and some days, from nowhere taji relieve ya zo mata, ta jingina da jikin gadon hawaye masu zafi na sauka idonta, tafi minti biyar a hakan ganin zata ci gaba da soiling zanin gadon ta sauka ta dau hijab dinta ta rungume, har sannan jikinta bai daina rawa ba, tana ta tsaye a dakin tana tunanin yanda zata yi, ta kalli kafarta jin period din yana gangaro mata, ajiye hijab dinta tayi ta shiga bandakin da ke cikin dakin, after few minutes ta fito ta dau hijab dinta ta saka, tana kallon zanin gadon da ya baci ta fara ƙoƙarin cirewa a hankali har ta cire gaba daya, bude kofar dakin taji anyi ta mike tsaye da sauri zuciyarta na bugawa tana kallonsa, ya wani harareta yace "What are you using that for?" Bakinta na rawa tace "A'a wankesa zan yi ne" Yace "Ajiye bana so, zo ki fitar min a daki" Ta sunkuyar da kanta babu musu ta ajiye zanin gadon a gefen gado ta nufi kofa a tsorace kamar munafuka, amma ta kasa bin gefensa ta fita daga dakin saboda fargaba, gashi he is blocking the way, ta fi 30 seconds tsaye zuciyarta na bugawa ta kasa fita, shi dai kallonta kawai yake babu yabo babu fallasa, da kyar tace "Zan wuce" Ganin kallon da yake mata bata sake cewa komai ba haka nan ta raɓa ta gefensa ta fita daga dakin, kallon inda ta tsaya yake don nan din ma dai sai da tayi staining dinsa da jini, ita dai tuni har ta shige dakin da aka fara ajiyeta ta tafi bandaki da sauri tana jin maranta na kullewa, ita da ko ciwon mara bata yi sai dai wani lkcn tayi ciwon baya ko kafafuwanta su rike shi ma kawai na 'yan awanni ne, ta samu dai ta wanke jikinta ta fito tana dukawa sbda ciwon da take ji a mara, a haka ta bude closet din da ya nuna mata tana duba ko zata ga pad, amma taga babu alamarsa, ta fara tunanin yanda zata yi gashi tana jin alamar saukan period din nata a jikinta, ita ko da kyalle ne idan ta samu zata iya manage da shi, amma duk dube dubenta bata ga alamar akwai kyalle ko dankwali a closet din ba, duk kananun kaya ne, she was so confuse and in pain at the same time, ta rasa yanda zata yi, sai da tayi sahu ya fi a kirga zuwa bandaki ta wanke jikinta ta sake fitowa, kuma a haka ba heavy flow take ba a ranan farko, ko zama ta kasa yi ciwon mara ya addabeta, hawaye ya fara sauka idonta ta karasa kusa da gadon dakin ta durkusa ta daura kanta saman gadon ta lumshe ido trying to endure the pain she is feeling, tafi 20 mins a haka taji budewar kofar dakin, da sauri ta dago kanta daga gefen gadon har sannan tana duke, ta kallesa gabanta na faduwa, ya shigo dakin ya ajiye ledan hannunsa yana mata kallon sama har kasa a takaice yace "Me ye ma'anar hakan?" Muryarta na rawa tace "I am having cramps" Yace "Yaushe kika fara cramps? Is this also among ur lies?" Ta sunkuyar da kanta wasu sabbin hawayen na sauka idonta, yace "Bazan sake fita gidan nan da daddaren nan ba saboda ke, after all mate din ki ne ke enduring labor pain" Ita dai bata ce masa komai ba har ya fita daga dakin, sai a sannan ta dago kanta with tears rolling down her face, ta kalli ledan da ya ajiye, rarrafawa tayi zuwa gun ledan ta bude taga Sanitary pad ne, daya ledan kuma abinci ne da ya siyo mata a eatry da bottle water, ta daure ta mike tsaye da kyar bayan ta cire pad daya ta bude closet ta dau sabon underwear dake ciki ta tafi bandaki, bayan ta gyara jikinta ta wanke hijab dinta da yayi staining a bandakin sannan ta fito, rigan bacci wanda ya ɗan fi sauran mutunci ta dauka ta saka, ya saukar mata har kusa da gwiwa, kasa cin abincin da ya siyo mata tayi, haka nan ta bude ruwan goran ta sha sannan ta dau pillow ta ajiye a kasan dakin ta dau duvet din saman gado ta kwanta tana jin ciwon cikinta na tsananta, ita rabonta da ciwon mara tun ranan farko da ta fara period, haka nan hawaye yayi ta zuba idonta, har ta samu bacci ya dauketa taji budewar kofa, taki bude idonta tayi lamo a inda take bugun zuciyarta na tsananta, ya zagayo har inda take ya duka gabanta, hannu ya kai forehead dinta hakan yasa ta bude ido da sauri, magani ya mika mata da ruwa a hannunsa ta sauke idonta sannan ta daure ta mike zaune ta amshi maganin da ruwan hannunsa ta sha, ajiye sauran ruwan tayi a gefenta har sannan ta kasa kallon idonsa, taji yace "Meye da gadon da baki hau ba?" Kai kawai ta girgiza masa yace "Get on the bed now" Tashi tayi ta koma gefen gadon ta zauna, kana ganinta kasan a tsorace take, ya dau pillow da duvet din ya ajiye mata saman gadon, kwanciya tayi ta lulluba da duvet din ta kulle idonta, tana ji ya fita ya kullo mata dakin, ta bude idonta da sauri taga ya kashe mata wutan dakin, hawaye taji na gangarowa ta gefen idonta, gradually taji ciwon maran ya fara subsiding after almost an hour of taking the drug he gave her, daga nan kuma bata san sanda bacci me nauyi ya dauketa ba, wajen karfe ukun asuba yunwa ta farkar da ita, ta mike zaune tana bin dakin da kallo har wani rawa jikinta yake saboda yunwa don rabonta da abinci tun shekaranjiya ga kuma maganin da ta sha babu komai a cikinta, zamowa tayi daga kan gadon tana laluba ledan abincin da ya kawo mata taga ya dauke, rasa yanda zata yi tayi, tana ta zaune a haka kawai taji ya bude kofar dakin hannunsa rike da wayarsa da ya kunna fitila, shigowansa na uku kenan zuwa dakin amma duk bata sani ba tana bacci, haskata yayi da wayarsa ya karaso cikin dakin ya kunna switch din fitila, ita dai ta sunkuyar da kanta kamar munafuka tana jin zuciyarta na throbbing, yace "Me kike yi a nan?" Sai a sannan ta daga kai da kyar ta marairaice amma bata ce komai ba, ya daure fuska yace "Nace me kike yi a nan?" Da kyar tace "I am hungry" Yace "Me yasa baki ci abincin da na kawo maki jiya ba?" A hankali tace "Na kasa ci" Juyawa yayi ya fita daga dakin, ta lallaba ta koma saman gadon ta kwanta tayi lamo, after almost 10 mins sai gashi ya dawo dakin da abincin bayan yayi microwaving din mata, nan kan bedside drawer ya ajiye mata abincin da ruwan gora, bata jira yace mata komai ba ta mike zaune tana sunkuyar da kai kamar mara gaskiya ta kai hannu ta dau abincin, shi dai yana tsaye yana kallonta, a hankali ta fara cin abincin har sai da ta ci rabi sannan ta kallesa cike da karfin hali tace "Na koshi" Yace "Cinye sa" Bata masa musu ba ta ci gaba da cin abinci har sai da ta cinye, amma fa da kyar ta dinga turawa, ta ajiye plate din a saman beside drawer, juyawa yayi ya fice bayan ya kashe wutan dakin, Khaleesat ta koma ta kwanta tayi lamo kan pillow, ta ma rasa wani tunani zata yi at this point, ta goge hawayen da taji yana gangaro mata, ba ita ta koma bacci ba sai da aka yi sallan asuba. Wajen karfe bakwai na safe ta fito daga wanka daure da towel tana tafiya a hankali ta bude closet din dakin tana tunanin abinda zata saka, kana kallon fuskarta kasan tana cikin damuwa me tsanani, fargabanta yanxu idan ta gama period ya kenan? Ta ina zata fara nema ma kanta solution yanxu, what next? ta fashe da kuka a hankali tana jin kirjinta na mata zafi, ta jingina da closet din tayi kukanta me isanta tana tausayin rayuwarta, daga karshe ta goge hawayenta a sanyaye ta dau wata riga wanda har kasa ne amma it's transparent, ajiyewa tayi gefen gado ta cire hair net din dake kanta tun shekaranjiya, tana tafiya a hankali ta karasa gaban madubin dakin, turarurruka iri iri ne da mayuka, da man kai, ta dau turaren jiki kadan ta shafa sannan ta shafa ma kanta man gashi don tana barin sa ya kara kwana daya a haka bata shafa mai ba duk tangling zai yi barin dama cukuikuyesa kawai tayi cikin Hair net din Aunty Farida, ita ma Aunty Farida haka gashinta yake, infact dukkansu har Umma da su Islam duk texture din gashinsu daya, tana cikin shafa ma gashinta oil aka bude kofar dakin, still tayi a inda take gabanta ya fara faduwa, taki yarda ta kalli direction dinsa, da kyar ta ajiye oil din hannunta ta dau Hair net zata mayar da gashinta ciki, taga ya amshe net din a hannunta ya juyo da ita yana kallonta, ta sunkuyar da kanta kirjinta na heaving shi dai kallonta kawai yake, short ne kadai jikinsa shi ma da alamar he just took his bath, ya jawota jikinsa ya daura goshinsa saman gashinta at the same time yana shafa dogon baƙin gashinta a hankalin, Khaleesat ta runtse ido zuciyarta na bugawa, murya can kasa taji yace "Why did u change ur mind abou me? It's all my fault right?" Jin bata ce komai ba ya dago kanta yana kallonta, kawai jin bakinsa tayi a nata bayan ya lumshe idanuwansa, tsoron turje masa take yi don bata san me zai biyo baya ba idan tayi hakan, jikinta ya dinga rawa kamar me zazzabi hawaye na sauka idonta tana girgiza masa kai amma ta kasa cewa komai kar ya mareta kamar yanda ya saba, a haka ya ja ta zuwa saman gadon dakin yana sarrafata, he made sure he romanced her deeply to the extent that sai da ya birkice mata kamar ba shi ba, daga karshe kuma ya kyaleta kar ya kasa controlling kansa gashi tana period, amma fa sosai ya iya kai zuciyarsa nesa kafin ya kyaleta ya koma can edge din gadon yayi rub da ciki tare da lumshe idonsa, everything about Khaleesat is just perfect for a Man, laushin jikinta kadai ya isa ya kara gigita mutum, Khaleesat ta koma daya side din gadon a hankali take kukan takaici faduwar gabanta ya tsananta, juyawa yayi ya kalleta after some minutes yaga yanda dogon gashinta ya rufe duk fuskarta tana kuka, sai kuma ta zamo a hankali daga saman gadon ta kife kanta da jikin gadon tana shessheka, ji tayi ya dafata ta juyo a firgice tana komawa baya don bata san sanda ya zagayo ba, ya sa hannu biyu ya maida duk gashinta zuwa gefen fuskarta yana kallonta, tuni ta daina kukan da take saboda tsoro, ta sunkuyar da kanta kirjinta na heaving, jawota yayi jikinsa ya rungumeta ya lumshe ido, ita dai tayi tsit tsabar firgici, a haka ta dinga jin bugun zuciyarsa tana jikinsa, they were like that for 3 mins daga karshe taga ya mike a hankali ya fita daga dakin ta bi sa da kallo tana share sabbin hawayen dake sauko mata a fuska, throughout ranan haka Khaleesat tayi ta zama a daki sai dai ya kawo mata abinci, da ta tuno abubuwan da Abdul yayi mata daxu sai ta firgita, sai ya zama kamar tana hallucinating ne, hakan ya dinga sa mata ciwon kai taji kamar zazzabi zai rufeta, saura kadan panic attack ya kamata a dakin banda Allah ya takaita mata, gaba daya yanxu tunanin menene makomar rayuwarta take, shikenan haka zata hakura tayi zaman aure da Abdul ta ci gaba da shanye duk bakin cikin da zai kunsa mata a zaman aurensu bata da me tsaya mata tunda shi din mijinta ne? Did she even have a way out with the way things turn out to be all of a sudden? Is this going to be the beginning of a new era a rayuwarta? Shikenan irin rabuwar da zata yi da su Housemate dinta kenan? Kilan ma ba lallai ta sake ganinsu ba a rayuwarta? Shikenan haka Abdul zai ci gaba da caging dinta a gidansa ga threatening din kashe mata siblings da yayi idan taki zama da shi? Duk wa ennan tunanin suka sa ta dinga kuka tana tausayin sabuwar rayuwar da take kokarin fadawa, don tasan Abdul na gane ta gama period bazai daga mata kafa ba and that is the end of her, kuma shikenan dole ta zauna tayi zaman aure da shi ko da yankan naman jikinta zai dinga yi kuwa don azabtarwa, tunda Ummanta ta haifeta tana jin bata taɓa shiga irin wannan tashin hankalin da take ciki ba a wannan lokacin, tana jin alamar zai shigo dakin take goge fuskarta ta langwabe a zuwan ciwon ciki take.... Cikin wannan yanayin Khaleesat tayi kwana uku a gidan tare da Abdul, a wannan kwanaki ukun kuwa duk da halin da take ciki a haka yake sakawa taje tayi masu girki a kitchen wai shi baya son abincin restaurant, Khaleesat bata taɓa fatan kar period dinta ya dauke ba kamar irin wannan lokacin, she wish she will keep on flowing continuously like the woman with the issue of blood amma tasan dole ya dauke nan da kwana biyu don bata wuce 5 days in tana period, sosai hankalinta ke kara tashi idan ta tuna hakan, yau tunda gari ya waye tayi wanka ta saka pad take kwance kan gado saboda azababben ciwon kan da take, all these pass days bata wani samun baccin kirki da daddare tsabar damuwar da ta saka ma kanta da tunane tunane, daga karshe dai haka ta daure ta fita zuwa kitchen da kyar don dora breakfast kafin ya fito daga dakinsa kamar yanda yayi mata umarni 2 days back, tana fita parlor ta leka compound din gidan taga babu motarsa alamar ya fita, ta murda kofar parlon taji a kulle kamar yanda tayi tunani, Zaunawa tayi kan kujera ta dafe kanta hawaye masu zafi na zuba idonta, after a while ta mike tana shesshekan kuka ta wuce kitchen din, tana cikin hada breakfast taji alamar shigowar motarsa gidan, after a while aka bude kofar parlon, ƙasa kunne tayi jin kamar muryar mace take ji a parlor, can kuma taji tsit, ita dai ta ci gaba da abinda take yi jiki babu kuzari har ta gama ta tsaftace kitchen din sannan ta juya zata fito ta kusa cin karo da wata mace in her late 30's zata shigo kitchen din, daga sama har kasa matar dake tsaye kofar kitchen din take mata wani irin kallo da za a iya kira da kallon kaskanci, ita dai Khaleesat tunda ta kalleta sau daya ta sunkuyar da kanta ita kanta bata san sanda ta gaisheta ba don duk ta rude gashi kuma taga suna kama da Abdul duk da bai taɓa nuna mata wani nasa ko da a hoto ba, a walakance matar tace "Da ban kwana ba zaki gan ni munafukar Allah, Er gidan matsiyata ma ci amana.... A gidan ubanki kika san ni da zaki gaisheni?" Sai a sannan Khaleesat ta sake daga kai tana kallonta da mamaki cause kalmomin matar kawai a bazata suka zo mata, bata san sanda tace "Ki zageni amma banda iyayena...." Bude baki Meema tayi da mamaki tana kallonta ganin guts dinta, kafin tace komai Khaleesat ta bi gefenta zata fice daga kitchen din wanda saura kiris ta bangajeta wajen fitan, cikin zafin nama da bacin rai Meema ta fincikota ta dawo da ita gabanta sannan ta sauke mata wani wawan mari ta shakota tana kokarin kai ta kasa ta nakadi banza, Khaleesat ta kwala wani kara, dai dai isowan Abdul wajen, lkci daya yanayinsa ya canza don a kan idonsa yayar tasa ta sauke ma Khaleesat mari sannan ta shakota tana kokarin dukanta, cikin daga murya yace "Zo ki fita ki bar min gidana Amina, how dare you? Me tayi maki zaki mareta haka? Baki da hankali ne? Get out of my house pls, fita ki bani waje" Sake baki Meema tayi tana kallonsa babu ko kiftawa, cikin zafin nama ya tafi ya bude kofar parlon kirjinsa na sama da kasa yace "Ki fita nace Amina kar in rama mata" Cikin karfin hali Meema ta dafe kirjinta da hannu daya tace "Abdallah ni kake cewa in fita a gidanka?" Ya jefar da wayar hannunsa yana huci ya nufeta kamar zai kai mata duka cikin daga murya yace "Na ce ki fita din ko gidanki ne? Get out of this house before i loose my control Amina, gerrout" Ita dai Khaleesat makalewa tayi jikin kofa jikinta na rawa, sum sum sum Meemah ta karasa ta dau handbag da karamin travelling bag dinta don dama daga airport yaje ya daukota saukanta garin kenan, ta nufi kofar fita parlon sannan ta juya tana kallonsa da mamaki tace "Abdallah ni kake daga ma murya kake cewa in fita in bar gidanka akan wancan matsiyaciyar? Har kake ikirarin zaka kai min hannu? Ni din Abdallah?" Da karfi yace "Duk nayi, fitaa ki bar min gidana malama" Fita tayi daga parlon ya bi bayanta kamar zai tashi sama ya tafi ya bude mata gate din gidan, ta fita yayi banging gate dinsa ya kulle, har ya dawo parlon Khaleesat na makale jikin kofa ita tsabar yanda ta tsorata ma ko digon hawayen marin da Meemah tayi mata babu a idonta, ya karasa kitchen din yana kallonta, sunkuyar da kanta tayi, sai a sannan taji hawaye ya fara zuba idonta. [6/14, 9:16 PM] khaleesat Haiydar ✍️: Juyawa Abdul yayi ya fice daga kitchen din ba tare da yace mata komai ba ya dau wayarsa ya nufi dakinsa, Khaleesat ta bi sa da kallo tana goge hawayen dake zuba idonta har ta dena hango sa, jingina tayi da kofar kitchen din ta kai hannunta fuskarta dai dai inda Meemah ta mareta don sai a sannan ta fara jin zafin marin, fashewa tayi da kuka tayi me isarta kafin ta fito daga kitchen din tana tafiya a hankali ta tafi ta zauna kan 1 seater dake parlorn tana share hawayen da yaki tsaya mata, abubuwan da Abdul yayi ma Meemah ne suka dinga dawo mata a kai don hakan yayi mugun shock dinta, but she just don't want to believe senior sister dinsa yayi harrassing haka har da koranta, to ko dai ita ce Aunty Aminan da suke ce ma Meemah don taga sosai suke kama da ita, tana ta zaune parlon bayan wani lokaci sai gashi ya fito daga dakinsa, sunkuyar da kanta tayi tana wasa da fingers dinta, ya karaso cikin parlon yace "Kin yi breakfast din ne?" Da Authoritative voice yayi tambayar yana kallonta, hakan yasa ta ɗan rikice kamar mara gaskiya ta girgiza masa kai with fear all over her face, sai kuma ta mike da sauri ta nufi kitchen ya bi ta da kallo har ta shiga ciki, shayi rabin cup ta hada sannan debi Irish kadan a plate don tension yasa ta rasa appetite dinta gaba daya , sai kuma ta tuna shi ma bata basa breakfast din ba, tunanin ko ta kai masa parlor ta fara yi don a kwanaki ukun nan Bedroom dinsa take kai masa breakfast din kamar yanda ya umarce ta, kamar munafuka ta makale jikin kofar kitchen din tana kallonsa tana son tambayarsa ko ta kawo masa breakfast din nasa parlorn amma ta kasa don bata san me zai ce ba kar yayi mata masifa, wayarsa kawai yake dannawa bai ma san tana wajen ba, juyawa tayi a hankali ta koma kitchen din a sanyaye ta hada masa breakfast din ta fito da shi parlor, jikin kujera ta tsaya a hankali tace "Ga breakfast din nan" Daga kai yayi ya kalleta, gabanta ya dinga faduwa ta sauke idonta daga kallonsa, jin bai ce komai ba yasa ta karasa har gabansa ta duka ta ajiye masa breakfast din, yace "Ke ina naki?" Taki barin su hada ido tace "Yana kitchen" Yace "Dauko" Mikewa tayi ta tafi ta dauko nata ta dawo tana kallonsa, yace "Ajiye ki ci a nan" Bata masa musu ba kanta a kasa ta zauna gefensa da ya nuna mata ta fara tuttura irish din kamar dole tana satan kallonsa ta gefen idonta, a hankali taga ya jawota jikinsa taji gabanta yayi mugun faduwa, calmly yace "I am a monster to you right?" Da sauri ta girgiza masa kai zuciyarta na bugawa, yace "Gashi nan, kin maida ni dodonki" Ita kanta bata san sanda hawaye ya cika idonta ba, yayi kasa da murya yana zame hulan kanta yace "Now tell me what u want from me, tell me what's on ur mind.... amma before then ki sani bazan taɓa rabuwa da ke ba saboda ina son ki Khaleesat, rabuwa dake will be the last thing i will do on earth no matter what, You know i love you genuinely from onset, i loved you wholeheartedly and i gave u the best of everything I could, i loved you even before you become the woman you are today, i love you since when u were just a 15 year old teenager tun baki girma ba, yea i know about my flaws but loving you is all that matters, not in the sense that abubuwan da nake yi are right, i am obsessed with you Baby, may be you can change me in ur own way...." Khaleesat ta rufe idonta tana jin kamar ta fashe da kuka, jin kalamansa take kamar ana soka mata mashi a kirji, Ya dora forehead dinsa a nata murya can kasa yace "Why not give me a chance and forgive my flaws Khaleesat?" Bude idonta tayi hawaye suka hau zarya a idonta, har cikin ranta taji bata son jin maganganun da yake mata, a hankali yace "Forgive me, i know i wronged you in all ways, but don't forget ina sonki, ina kuma sonki ne saboda Allah, they are many beautiful ladies out der buh i chose you Khaleesat" Lokaci daya gaba daya tunaninta ya tafi kan Housemate dinta, kasa daurewa tayi ta fashe da matsanancin kuka, ya daura kanta a saman shoulder dinsa patting her softly, ta dinga kuka kamar an aikota, shi dai bai ce mata komai ba, sai da tayi kukan me isarta sannan ta hakura don kanta tayi shiru tana sauke ajiyar zuciya, ya daga kanta yana kallonta taki yarda su hada ido, breakfast dinta ya ajiye mata a kusa da ita, ba musu ta fara ci a hankali da tunani iri iri a ranta, muryarsa taji ya daki dodon kunnenta "Yaushe zaki gama period?" Gabanta yayi mugun faduwa, ta ajiye cup din shayin dake hannunta ba tare da ta kallesa ba, a hankali tace "Ai ban dade da farawa ba" Yace "Yau kwana hudu da farawan ki" Da kyar ta dake tace "A'a, uku ne.... first day din ai bana yi sosai..." Yace "Saura kwana nawa ki gama kenan?" Sosai gabanta ke bugawa, ta sunkuyar da kanta cike da karfin hali tace "Kilan nan da kwana uku ko hudu" Jin bai ce komai ba ta daga kai a ɗan tsorace ta kallesa, taga kallonta yake without blinking, sauke idonta tayi tana wasa da karamin cokalin dake cikin mug din shayinta, ya dauke shayin ya mayar gefe, taga ya kai hannu shoulder dinta zai sauke siririn hannun rigar dake jikinta, sosai hankalinta ya tashi amma bata ce masa komai ba gabanta na ci gaba da faduwa, ya sauke rigan gaba daya yana kallon bare chest dinta, hawaye ne ya cika idonta taki yarda su hada ido, can dai tayi karfin hali muryarta na rawa tace "Toh baka sha shayin ka ba zai huce" Yayi kasa da murya yace "Wa ennan zan sha... " Momy ce tsaye parlor tana kallon Meemah dake rusa kukan bakin ciki uwa er yarinya, ga trolley dinta a gefenta, bacin rai ne karara kwance fuskar Momy da idanuwanta suka ƙankance tana huci, mai aikin gidan ce ta shigo parlon rike da bowl din pepper soup din da tayi ma Momy, cikin ladabi ta risina tace "Hajiya ga farfesun nan ya kammala" a fusace Momy ta figi throw pillow ta jefa mata tace "Don ubanki wuce ki ban waje ke da farfesun, baki ga magana nake bane zaki shigo min parlor kai tsaye, yau ga jahilar mata kai" a tsorace mai aikin ta juya da sauri ta bar parlon ta koma kitchen ta kullo kofar, Momy tace "Na kusa daina daukan tsinannun masu aikin nan don sun isheni haka kuma, na kori wancan shegiyar da ta shigo min parlor da yan uwan Alhaji da suka zo daga kauye babu izinina yanxu kuma an kawo min wannan jakar da ko kwana biyu bata yi ba ta fara nuna halayyan dabbobi" Ita dai Meemah kuka kawai take tana fyace hancinta da handkerchief, tsabar kuka idonta har sun suntume, Momy ta kara kankance idanuwanta tana kallon Meemah tace "Shi Abdallahn ne yayi maki haka Meemah?" Meemah ta hadiye wani abu da ya tokare mata wuya don bakin ciki tace "Momy da kin ga tijaran da Abdallah yayi min akan yarinyar nan ko, hmmm, ki bari kawai Momy, Momy kare bazai ci abinda Abdul yayi min ba, bayan zagi da cin mutunci wai ni ya kora a gidansa, kora irin ta walakanci" Momy ta zauna kan kujera with disbelief, duk da AC dake aiki a parlorn sai zufa take yi dama ga ta narkekiya, tana gyara zama tace "Ko dai ya sha wani abu ne Meemah??" Cikin rawan murya Meemah tace "Babu abinda ya sha wallahi Momy don lafiyan Allah ya dauko ni a airport muna ta hira, tare fa da ni duk aka yi tracking yarinyar nan tunda akwai wani tsohon saurayina wanda aikinsa kenan, amma wai yau akanta Abdallah zai min irin wannan tijara haka tun ba aje ko ina ba, duka duka fa kwananta yau hudu da shiga hannunsa, amma ya rufe ido ya zazzageni ya ci min mutunci ya koreni" Momy tayi wani murmushin takaici tana girgiza kafa tace "Kin ga abinda nake ta gudu kika kasa ganewa kenan ai ko? Dama ance duk abinda babba ya hango yaro ko uban me zai hau bazai taɓa hangowa ba wallahi, ba ya kwana da ita ba dole ki ga abinda yafi haka ai, babu yanda banyi in lalata batun auren nan ya hakura ba amma sam Meemah kika ki bani hadin kai ki ka koma bayan Abdallah, har da bin wasu malamanki da basu taka kara sun karya ba duk don yarinyar ta shigo hannunsa, to ai ta shigo kuma kin ga abinda ya biyo baya daga shigowarta, to wallahi zai kai ya kawo wataran Abdallah yace bai san mu ba akan yarinyar nan, ni na haifesa ba wani ya haifar min shi ba sarai nasan abinda zai iya aikatawa" Meemah ta dinga kallon Momy babu ko kiftawa don ita sai yanxu ta kara fahimtar dalilin Abdul nayi mata irin wannan mugun tijara kan yarinyar da yake ta ikirarin zai koya ma lesson idan ta shigo hannunsa, sarai kuwa ya kwana da ita dole ya birkice haka ya haukace kanta, dama buzaye da aka sani da mugayen asiri, Meemah tayi wani murmushin takaici tace "To kuwa yanda nayi ruwa nayi tsaki har sai da yarinyar nan ta shiga hannunsa to haka zan yi har sai ya rabu da ita a kwanan kuwa ba da jimawa ba" Momy ta kwado ma sabuwar me aikinta kira, matar ta taho a guje har sai da tsantsin tiles ya kwasheta sbda ruwan dake kafarta sai ga ta a kasa timmm, A fusace Momy tace "Wallahi tallahi kika kuskura kika illata min tiles sai na cire cikin kudin albashinki, yau naga er iskar mata kawai, kullum na kiraki sai kin azabtar min da tiles saboda kauyanci? Wannan wace irin mata Adama ta kawo min haka da sunan me aiki?" Har kasa mai aikin ta zube tana ba Momy hakuri, cikin tsawa Momy tace "Miko min wayata dallah ki fita ki bamu waje, er kauyen banza" Mai aikin ta kalli wayar dake kan center table dab da inda Momy ke zaune, ta karasa da sauri ta dau wayar ta mika ma Momy, Momy ta warce, mai aikin ta bar parlon, Momy ta mika ma Meemah wayar tace "Dubo min lambar Godiya, glasses dina yana daki" Meemah ta amshi wayar ta dubo number aminiyar Momy sannan tayi dialing ta mika mata, a kashe suka ji wayar, Momy tace "Tayi tafiya me muhimmanci kenan, bari zuwa anjima in sake kiranta" Meemah da kanta ya gama kullewa tace "Tabddi jam, lallai nayi babban kuskuren da ban taɓa yin irinsa ba Momy, sai ma fa kinga kayan dake jikinta da naje gidan, tana kitchen tana soye soye" Momy dai tayi shiru tana girgiza kafa don bakin ciki da takaici, can tace "Dauko min gyale da jaka a daki, ina zaman zamana kin janyo min kashe kudin da banyi budgeting ba Meemah, duk ke kika ja min wannan masifa da kika ki jin maganata wallahi, in hada iri da matsiyata akan wani dalili? A farko dai na hakura na zuba masa ido da yaki jin maganata, amma yanxu kuwa wallahi sae ya rabu da yarinyar nan, babu dalilin da zai sa in hada zuri'a da ita, ga kuma rashin adalcin da aka yi ma Alhaji ga asara ga biyan tara" Tashi Meemah tayi ta tafi dauko ma Momy gyalenta da handbag, all this while dama ita ke ta shiga malamai don Khaleesat ta shiga hannun Abdul Momy ko bin ta kanta bata yi tunda dama ba son auren take ba, Momy na ficewa daga gidan da driver dinta Meemah ta tafi dakinta da wayarta tayi dialing number Malamin da tasa yayi mata aiki. Runtse ido Khaleesat tayi bayan taji duk maganganun da Abdul yayi, yana rungume da ita saman gadonsa kamar zai maidata jikinsa, it's past 8pm na dare, jin taki cewa komai s hankali yace "Khaleesat" Bude idonta tayi wasu hawaye masu zafi suka silalo fuskarta tace "Um" Yace "Say something" Still tayi shiru hawaye na zuba idonta don bata ma san me zata ce masa ba at this point, ya dago kanta yana kallonta yayi kasa da murya yace "Say something pls" Da kyar muryarta na rawa tace "Ban san me zan ce ba" Yace "Say anything" Shesshekan kuka ta fara yi masa tana jin zafi a zuciyarta, me kuma yake son ta ce masa, tunda yace bazai taɓa rabuwa da ita ba ko me zai faru, meaning dole ko tana so ko bata so haka zata ci gaba da rayuwa da shi a matsayin mijinta, so me yake son ta ce, ta dai dake da kyar har sannan muryarta na rawa tace "Kawai alfarma daya zan nema wajenka" Murya can kasa yace "Say it Khaleesat" Tayi karfin halin cewa "I don't want you to hurt anyone because of me...." Kasa ci gaba tayi tana kuka a hankali, ya dinga kallonta don sarai yasan su wa take nufi, Calmly yace "Ohk u mean ur Body Guards that sue me?" Ita dai kuka kawai take, Ya ɗan yi wani murmushi yace "I don't think i will leave dem cause they started everything first, they intruded in what wasn't der business, basu baki labarin harbin da aka yi ma wani dake da alaka da su ba, I mean Salem..." Khaleesat ta daga kai da sauri ta kallesa hawaye na sauka idonta gabanta na faduwa, lkci daya ta tuna sanda Aunty Farida ke sanar mata Ajay yace mata an harbi wani abokinsu a kano, yana wani murmushi yace "To su ma ana nan ana targeting din su, amma in kince in kyalesu i will do that under 2 condition..." Khaleesat dai kallonsa kawai take ta kasa cewa komai duk jikinta yayi sanyi, yace "The first condition is that.... zaki yi magana ta waya da su ki gaya masu ke za ki zauna da mijin ki they should back off, sannan ki gaya masu su janye karan da suka kai kotu..." Bata san sanda ta fashe da matsanancin kuka ba, ya dinga kallonta sai kuma yayi murmushi yace "Baza ki yi ba kenan?" Muryarta na rawa tace "Ban ce bazan yi ba" Wayarsa ya dauko ya mika mata yana kallonta, da kyar tace "Bani da number ai" Yace "Amma aunt dinki na da shi ai... Call her and ask her to send you the number" Ta girgiza masa kai tana jin kamar numfashinta zai dauke sbda rikicewan da tayi bayan ya fadi conditions dinsa, cikin kuka tace "Bani da numberta offhand" Yace "Ni ina da shi, i will call her now sai ki gaya mata ta turo maki number daya daga cikinsu, and mind you kada ki kuskura ki ce mata komai, number kawai zaki yi requesting ta turo maki" Ta fashe masa da kuka sosai tace "Why are you doing this plss Ya Abdul" Yace "Ohk, i will revenge and nothing is gonna stop me, i promise you this, shi abokinsu da aka harba ai yayi surviving, i hope they survive too....." Tana kuka sosai tace "No plsss..." Wayar ya dauka yayi dialing number din Aunty Farida yana fara ringing ya mika mata yana kallonta. [6/17, 7:43 PM] khaleesat Haiydar ✍️: Har Aunty Farida ta ɗaga kiran Khaleesat bata amshi wayar da Abdul ke mika mata ba hawaye na zuba idonta, lkci daya ya hade rai yana mata wani irin kallo, babu shiri ta amshi wayar hannunta na rawa, a sanyaye tace "Aunty" Cikin rikicewa Aunty Farida tace "Khaleesat?" Khaleesat ta sauke idonta tayi shiru, hankali tashe Aunty Farida tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Khaleesat kina ji na? Don Allah kiyi magana, Hello Khaleesat" Khaleesat ta kasa ce mata komai hawaye masu zafi na sauka idonta, kiris ya rage ta fashe mata da matsanancin kuka a wannan lokacin, Abdul ya fixge wayar yayi a hannunta ya katse yana mata wani mugun kallon da ya tsorata ta sosai yace "Are you daring me?" ta fashe masa da kukan da take dannewa tana girgiza masa kai, a fusace yace "Ohk then, since abinda kika zabar masu kenan to ina me tabbatar maki zan aikata hakan nan ba da jimawa ba kuwa, sannan bayan nayi zan sanar maki, don bani da imanin kyale duk wani mahalukin da yace zai shiga hurumina, i don't mind sending that person to his early grave, and mind you.... i will so deal with them yanda in their next life baza su kara shisshigi akan abinda bai shafesu ba, if you think i am bragging watch and see, bani da conscience...." Khaleesat ta girgiza masa kai cikin karfin hali tace "Duk ba sai ka masu komai ba, zan yi abinda kace" Wayar ta amsa a hannunsa ta cire a Flight mode din da ya saka sannan ta sake dialing number Aunty Farida, yana fara ringing Aunty Farida ta daga da sauri tace "Khaleesat, kina ji na Khaleesat?? Hello" Khaleesat ta dake ta hadiye sauran kukanta cike da karfin hali tace "Na'am Aunty" Cikin tashin hankali Aunty Farida tace "Kina ina Khaleesat?" A hankali Khaleesat ta daga kai ta kalli Abdul taga ya wani murtuke fuska yana kallonta kamar bai taɓa fara'a ba a rayuwarsa, ta sunkuyar da kanta wasu sabbin hawayen na zubo mata cikin sanyin murya tace "Aunty Number Ahmad za ki turo min yanxu plss" Aunty Farida da duk ta rude tace "Ahmad kuma Khaleesat? Wanene Ahmad? Kina ina ne yanxu?" Shi dai Abdul wani devilish look kawai yake mata, tayi kasa da murya tace "Aunty Number Junaid zaki turo min" Da sauri Aunty Farida tace "To bari in turo maki yanxun nan" Katse kiran Aunty Farida tayi cikin rawan jiki ta tura ma Khaleesat number Ajay, number na shigowa Abdul ya amshe wayar a hannunta yana kallon number for almost 5 seconds, can yayi wani murmushi ya mayar mata da wayar, cike da isa yace "Kirasa ki gaya masa abinda nayi instructing din ki" It took Khaleesat almost 30 seconds kafin ta iya dialing number Ajay, shi ma saboda irin kallon da Abdul ke mata ne, exactly irin kallon da yake mata in zai gaura mata mari, cikin muryarsa dake tsoratata taji yace "Kika kuskura kika yi magana da wata muryar da ba normal voice dinki ba zaki sha mamaki wallahi, and immediately he picks just go straight to ur point, do not give him a breathing space to say anything to you, go straight and tell him kin hakura zaki zauna da mijinki, kin ji me nace maki?" Ita dai bata ce masa komai ba hawayen takaici na zuba idonta, sai da kiran ya kusa katsewa Ajay ya daga, ta ɗan kalli Abdul da bai fasa mata wani irin kallo ba, da kyar ta daure tace "Hello, good evening....." Mikewa Ajay yayi jin muryarta, bata jira ya gama processing ba ta ci gaba a hankali tace "Dama ina son in ce maka ni na hakura zan zauna da mijina, and i appreciate all what you've done for me kai da Yaya Jawwad, thank you so much" Ajay ya juya ya kalli Jay da shigowar sa dakin kenan, as if counting his words yace "Come again!" Yana fadin haka ya saka wayar a handsfree sannan ya nufi Jawwad yana kallonsa, Khaleesat ta kalli Abdul, sai kuma ta sunkuyar da kanta tace "Cewa nayi ni na hakura yanxu, zan zauna da mijina, and thank you for all what you've done for me...." Wasu sabbin hawaye suka hau zarya a fuskarta tana ji kamar ta fashe da kukan dake cin ta, Abdul ya fixge wayar a hannunta ya katse sannan ya kashe wayar gaba daya, Ajay ya kalli Jay that looks speechless and shock at the same time, lkci daya ya jefar da wayarsa saman gado, cikin nutsuwa yace "Nayi da na sanin bata lokacina akan yarinyar nan, i regret wasting my very precious time...." Jay ya ma rasa me zai ce, walking slowly ya karasa gaban window din dakin yana kallon Ajay that was boiling from inside, a hankali yace "Look Ajay, i think those words are not coming from her heart, sakata yayi ta fadi hakan pls mu yi mata uzuri, she is forced to say all what she said, ba mu san situation din da take ciki ba let consider that plss" Ajay ya masa wani kallo yace "Billah na cire hannuna a lamarinta kaji na rantse Jay, i have nothing to do with her case again, after all i was just doing it just for the sake of humanity not because of her, ko kasheta yake ya kamata ta gaya mana haka? Mu zata dauka for granted? Beside she spoke confidently meaning she is okay with what he asked her to say, i am leaving this state first thing tomorrow morning, so unfortunate i waste my time on the brat, don taga mun yi stooping kan mu so low shi yasa ta dauke mu for granted" Yana kai wa nan ya fice daga dakin kamar zai tashi sama, Jay ya lumshe ido ya bude don bai san me zai sake ce masa ba da zai sa ya sauraresa, kuma tunda har ya rantse magana ta kare, ya zare hannunsa kenan babu abinda zai sa ya sake involving kansa, zaunawa yayi gefen gado ya dafe kansa da yaji ya masa nauyi, at the same time letting out a sigh, kalmomin Khaleesat ne suka dinga dawo masa kai, he felt really disappointed in her too, but can kasan zuciyarsa tausayinta ne ya mamayesa ya kuma yi mata uxuri, ya rasa menene yasa shi shiga yanayin da ya shiga a wnn lkcin, da kyar dai daga karshe ya mike ya fita daga dakin yana tafiya a hankali. Daren ranan nan Khaleesat bata yi baccin awa biyu ba cikakke, da bacci barawo ya saceta zata farka a firgice, bata taɓa jin abu ya tsaya mata a rai irin abinda Abdul ya sa tayi ma su Housemate dinta ya tsaya mata ba, gashi ko digon hawaye yaki fita idonta, her heart is just heavy, but did she have a choice? In bata yi hakan ba yayi ma su Housemate dinta wani mugun abu ai bazata taɓa yafe ma kanta ba, tunda har yake ikirarin ba shi da imani babu abinda bazai iya aikatawa ba, tasan kuma sarai zai iya aikatawa din, tunanin sabuwar rayuwar da take kokarin fadawa take, is she going to survive this at all? Is this not going to be her end? A ranta taji kilan lokacin mutuwarta ne ke tinkarota, sai a sannan taji hawaye masu zafi for the first time a idonta, ta kai hannu a hankali tana sharewa ta juya tana kallon Abdul dake baccinsa hankali kwance, dai dai nan alarm din wayarsa ya kada, ta juya da sauri tayi backing dinsa tana goge hawayen da ya fara zubo mata sosai, after some seconds taji alamar ya tashi yana karanto addu'an tashi bacci, ita dai hawaye kawai take, sai da taji yayi sallah ya fita daga dakin sannan ta mike zaune tana kuka a hankali. Nenne ta bude hannu tana kallon su Aunty Farida cikin nutsuwa tace "To kun ga ai baza mu shiga hurumin Allah ba, ko akwai me tsaurin idon da zai shiga a cikin ku? Allah Ubangiji ne kadai yasan daliliin da ya maidata hannun mijinta cikin ruwan sanyi babu tashin hankali, to don me za mu shiga hurumin da ba namu ba? A'a gaskiya banda ni tunda ni dai nasan wanene Allah, kuma shi kadai yasan hikimarsa ta yin hakan, da yasan Khaleesah zata cutu hannun Awdul da bazai fara basa sa'ar sungumeta ba don bamu fi sa sani ba, ko ba komai ɗa na zai samu kwanciyar hankali ya ci gaba da sabgogin rayuwarsa kamar ko wani ɗan adam, mu mun yarda da kaddara mummuna ko kyakkyawa tunda mu musulmai ne, kuma duk abinda Allah yayi mu din banza za mu ce don me, domin haka nake cewa Allah ya bata zaman lafiya da mijinta, ɗan halayyarsa da yake yi mara kyau Allah ya gyara sa ya dena, ai babu wanda bai da taɓon wani mugun abu a rayuwar nan, in sun dawo kano mu kuma sai mu je ganin daki mu sa albarka, duk sanda ya bar ta ta zo ta gaida mu a Mariri sai ta zo bakinta alekum, shi kuma Ali Allah ya sa karshen wahalarsa kenan a duniya" Wani irin kallo Aunty Farida ke ma Nenne zuciyarta na tafarfasa, Umma dai kanta na sunkuye bata ce komai ba amma ita kadai tasan abinda take ji a zuciyarta, Mama Zubaida tace "Amma dai Nenne ai ya kamata a bibiyi halin da take ciki, an taɓa tarewa haka kawai a zo a sungumi yarinya a mota da asuba ba a san ko shi din ne ba ko ba shi ba amma duk a rasa me bibiyar hakan, wannan ai abun dubawa ne, tun da mu dai har yanzu bai ce mana shi ya dauketa ba" Nenne tace "To er bakin ciki, shi din ne ya sungumeta ba kowa ba aniyarki ta bi ki, kuma ai halaliyarsa ya sunguma ba wata ba, duk wanda ya sake cewa zai bada shawara a wannan lamari idan ban sa Ali ya sallamesa ba shegiya uwata da ubana suka haifeni, kwata kwata bakwa neman ma ɗa na sauki a rayuwar nan, burin ku kawai tashin hankali ya kashe Ali ku huta ni kuma in shiga uku, ita uwar da ta tsugunna ta haifi yarinyar bata da bakin magana sai ke me baki kamar ta dorinar ruwa?" Mikewa Mama Zubaida tayi ta shige dakinta, Mama Shatu ta kyabe baki tace "To Allah ya kyauta, in ya dawo mana da gawar ta ai sai mu zauna mu yi zaman makoki ba shikenan ba" Nenne tace "Sai dai ki ga gawar er ki Labeebah amma ba Khaleesah ba, kuma bakin cikin da ku ka kasa boyewa ne zai kashe ku ke da Zubaida" Mikewa Umma tayi hawaye cike idonta ta shiga dakinta, Nenne ta kyabe baki ta mike tana kallon Aunty Farida tace "In Ali ya dawo ki ce masa nace ya zo ya amshi tuwo da miyar taushe zan ajiye masa, wallahi wata guda zan yi ina masa girki ya marmaro" Daga haka ta fice daga gidan, Aunty Farida tayi tagumi hawaye cike idonta. Meemah ta shigo parlon Momy ta zauna tana ɗan murmushi, ta jira har Momy ta gama wayar da take yi da aminiyarta godiya sannan tace "Momy na samesa a waya" Da sauri Momy tace "Ya daga kuma?" Meemah tace "Eh ya daga bayan yaga text din da na tura masa kenan" Momy na gyara zama tace "Toh Alhamdulillahi nagode ma Allah, sai yace maki me?" Meemah tace "Kema kinsan dole zai taho ai, amma tsorona daya kada ya kira Daddy kuma ya daga waya yace masa ba haka ba" Momy tayi wani murmushi tace "Bazai daga ba, tunda na riga na gaya masa abinda ke faruwa ai" Meemah ta sauke ajiyar zuciya tace "Alhamdulillah, in ya samu flight yau za mu iya ganinsu a gidan nan" Momy tace "Me zai hana ya samu jirgi, ai da sauran lokaci dole zai samu" Mai aikin Momy ce tayi sallama tana makale jikin kofar parlon duk da a bude yake amma bata shiga ba, hannunta rike da tray me dauke da plate din gasasshen kaza da lemon kwali biyu, Meemah ce ta amsa sallaman tana mata wani kallo tace "Tun da kika ga kofa a bude ba sai ki shigo ba, kin wani raɓe jikin kofa kamar munafuka, don Allah ki dena wannan kauyancin yana damun mu a gidan nan" Momy ta hade rai tana kallonta har ta karaso ta ajiye plate din, cikin ladabi tace "Ga kazar ta kammala Hajiya" Momy tace "Kalan Hijabin nan naki na daga min hankali a gidan nan, kar ki sake saka min shi, in yar wa zaki yi to ki yar bana son shi kwata kwata yayi kalar talauci" Mai aikin ta dukar da kai tace "Toh Hajiya in sha Allah bazan sake sa shi ba, kiyi hakuri" Fita tayi daga parlon da sauri, Momy ta dau plate din tulin kazar da aka ajiye mata ta fara ci tana cewa "Ai dama tunda aka ce min zai taho da ita hankali na ya kwanta, don dama taho da ita shi ne me wuyan...." Meemah tayi murmushi ita ma ta dau yankan kaza daya tana ci tace "I trust you Momy" Khaleesat ta saka Hijab dinta har kasa tana harhada wasu daga kananun kayan dake cikin closet din dakin kamar yanda Abdul ya umarceta tayi, absentmindedly take aikin don tayi nisa a tunanin da take, bude kofar dakin yayi ya shigo, ita dai bata juya ba tana ci gaba da abinda ya sakata, ya karasa har bayanta ya tsaya, taki juyowa gabanta na faduwa, juyo da ita yayi yana kallonta ta sunkuyar da kanta, yace "Me ya sa baki son ki saki ranki har yanxu? Always looking worried" A hankali ta daga kanta ta kallesa amma bata ce komai ba, yace "Kin gama hada kayan ne?" Girgiza masa kai tayi, yace "To gama" ta juya ta ci gaba da abinda take, shi dai yana tsaye yana kallonta, pad ta dauko a karshe zata saka cikin karamin trolley din yace "What are you using that for? Ba yau zaki gama ba?" Taki kallonsa zuciyarta na bugawa tace "Amma ban gama ba ai" Bata jira me zai ce ba ta saka a akwatin sannan ta kulle ta mike tsaye, kamo hannunta biyu yayi yana kallon cikin idonta, speaking slowly yace "Promise me you won't act silly har mu isa kano Khaleesat" Ta rasa dalilin da hawaye ya cika idonta, shi dai kallonta kawai yake, after some seconds yace "If you try anything silly, zaki yi matukar mamakin abinda zan yi, i promise you" Da kyar tace "Toh, amma plss ina son inyi waya da Safiyyah, i am missing her" Yace "Baza ki yi waya da Safiyyah ba, amma idan muka isa kano zan fara kai ki gidanku ki gaishesu sannan mu tafi gidanmu" Ita dai bata ce komai ba hawaye na zuba idonta, a haka suka bar gidan zuwa airport tunda yana da hoton National ID dinta a wayarsa. Da yamma suka sauka garin kano, driver din gidansu har ya iso airport din yana jiransa, Drivern ya bude ma Khaleesat back seat bayan ya gaisheta, kanta a kasa ta shiga motar, kana ganinta kasan tana cikin damuwa sosai gashi ta kara zagbewa gaba daya, Abdul ya shiga ta daya side din, sannan drivern ya shiga motar ya tada suka bar airport din, sai bayan da suka fita daga cikin airport Abdul ya gaya ma drivern inda zai fara kai su, sun yi nisa sosai da tafiyar Abdul ya juya ya kalli Khaleesat da tayi nisa cikin tunanin da take, hannunta ya saka cikin nasa wanda hakan ya dawo da ita reality, ta ɗan kallesa, yayi kasa da murya yace "Are you hungry?" Girgiza masa kai tayi, ya jawota zuwa jikinsa yana kallonta, ita dai bata ce masa komai ba zuciyarta na bugawa, a haka suka isa Mariri wajen karfe biyar da rabi na yamma, Drivern na parking daga opposite din gidansu Khaleesat Abdul ya bude motar ya sauka, jiki a sanyaye Khaleesat ta sauka daga motar, ta ma rasa ko farin ciki zata yi ko akasin haka ganinta a kofar gidansu, Abdul ya bi ta da kallo har ta shiga cikin gidan sai a sannan hawaye suka cicciko mata ido, Noor ce ta fara hangota tana hura gawayi ta taso da gudu ta rungumeta, sai a sannan sauran en gidan duk suka juya suna kallon Khaleesat, Umma dake zaune bakin kofar dakinta ita ma ta dinga kallonta, Mama Zubaida da Mama Shatu suka taɓe baki suna kallon juna, Aunty Farida dake gyara dakin Umma ta fito da sauri jin sunan wanda Noor ta kira, Khaleesat ta tafi ta rungumeta ta fashe da matsanancin kuka, Farin ciki wajen Aunty Farida ba a cewa komai don duk tunanin su Ajay ne suka dawo da ita gida, sallaman Abdul yasa duk suka juya suna kallon hanyar shigowa gidan da mamaki, nan da nan fara'ar Aunty Farida ya bace, su Mama Shatu ne kawai suka amsa masa sallaman, ya karaso cikin compound din, Aunty Farida ta saki Khaleesat ta tafi ta zauna kusa da Umma fuskarta babu yabo babu fallasa, Mama Zubaida ta mike da sauri ta shimfida masa tabarma ita da Mama Shatu na masa sannu da zuwa, ya zauna kan tabarman yana kallon Umma ya gaisheta, Umma ta amsa tace "Sannu da zuwa" Aunty Farida ta mike ta shige dakin Umma, Abdul ya gaida su Mama Zubaida dake ta washe baki, duk suka amsa da fara'a, Ita dai Khaleesat na durkushe kusa da Ummanta kanta a kasa, Abdul ya kalli Umma yace "Baba baya nan ne" Umma tayi karfin halin cewa "Eh bai dawo ba" Ko rufe baki bata yi ba sai ga Malam Ali ya shigo gidan da rabin buhun dankalin Hausa a hannunsa, ajiyewa yayi ganin Abdul da Khaleesat, yace "A'aa, ikon Allah, baki mu ka yi yau a gidan" Abdul ya tashi ya tafi har inda Malam Ali ke tsaye ya gaishesa, Malam Ali ya amsa yana kame kame, ya tafi da sauri ya dauko tabarma ya kara shimfida ma Abdul yace "Yi zaman ka a nan, bari in zubo mana ruwa a buta lokacin Magariba yayi" Da sauri ya tafi ya dauko butoci biyu ya tafi zai debo ruwan, Umma ta mike ta shige dakinta, Khaleesat ta bi bayanta, Nenne ce ta shigo gidan da sallama tace "Allah me hikima, sannunku da zuwa Awdul" Abdul ya gaisheta, ta jawo kujera ta zauna tana facing dinsa tace "Lafiya lau wallahi, ya iyayen naka, ina kokarin daura sanwa kenan sai ga wani almajiri da gudu ya zo ya sanar min ai kun zo, kasan ɗan albarka ne almajirin nan duk wani abu da ke faruwa a gidan Ali kamar kiftawan ido yake rugowa ya sanar min, ni kuma in ina da er dabino kwara uku in basa la'ada, nayi farin cikin ganin ka wallahi, ina matar taka, in ji tare ku ke?" Yace "Tare mu ke" Sai ga Malam Ali da ruwa a butoci yace "Ai ina jin tana dakin uwarta" Nenne tace "Kai kuma lafiya? ina zaka da butocin ruwa ko karfe shidda bai yi ba?" Malam Ali yace "Au? To to bari a ajiye, na zata magariba ta yi" Da sauri ya koma ya ajiye butocin ya dawo, Nenne tayi kasa da murya tana kallon Abdul tace "To Awdallah, ka dubi girman Allah ka rike amanar da muka baka, yanxu kai ne uwarta kai ne ubanta, duk ta kuskure maka ka kawota wajena ni zan san yanda zan yi da ita, kuma albarkacin auren da ya shiga tsakaninka da jikata ka kara ba Mahaifinka hakuri ya yafe ma Malam Ali komai ya wuce a wajensa don girman Allah, don yanxu kam duk mun zama daya tunda ga aure har ya shiga tsakani, Allah Ubangijin ya baku zaman lafiya ya kauda duk wata fitina ya kawo zuri'a dayyaba" Abdul yace "In sha Allah Kaka" Nenne na murmushi tace "To madallah, gashi ko tuwon dare ban yi ba balle in zubo maka" Yace "Ba komai, can gidanmu za mu wuce yanxu yamma tayi" Nenne tace "Gaskiya kam, bari in fito maka da ita ku tafi, go slown hanyar nan bata da kyau" Tashi Nenne tayi ta nufi dakin Umma, kuka kawai Khaleesat take Umma tayi tagumi tana kallonta ta ma rasa abun cewa amma daurewa kawai take ita ma hawayen bai zubo mata ba, don bakin ciki Aunty Farida na jingine jikin bangon dakin ita ma ta kasa cewa komai, a haka Nenne ta shigo dakin ta same su, taɓe baki tayi tace "Ta so ki fita mijinki na waje na jiranki" Ita dai Khaleesat bata ce komai ba tana kuka kamar ranta zai fita, Nenne tayi kasa da murya tace "Wato a yanda kanwar uwarki ke zube ba mashinshini shekara da shekaru haka kema kike son ki zauna mana tunda kyau kawai gare ku amma babu farin jini, banda samun waje ki samu miji zankadede kamar Awdul amma son zuci irin taki da na uwarki da kanwarta bazai sa ku yi farin ciki da hakan ba, in a baya Awdul ɗan iska ne dama Allah ya taɓa halittar da bai shiryar ba in yayi niyya? Daga yanda Awdul ke magana a kintse na gane ya shiryu wallahi, to ko kawota da yayi ta gaishemu kadai ya isa mu shaida shiriyarsa, wallahi ku dinga jin tsoron Allahn da ya halicce ku, duk wanda burinsa ya raba aure to tsinuwar Allah ne zai tabbata a garesa, kuma in sha Allahu Khaleesat tayi aure kenan mutuwa kadai ne zai rabata da mijinta tunda duk mun san yana sonta, tashi ki fita gun mijinki ku tafi munafuka kawai, duk da can baki san baki son shi ba sai da ya aika ki kasar turawa idonki ya bude a can" Cikin kuka Khaleesat tace "Ni wallahi bana son sa, bana son sa, bazan iya zama da shi ba" Nenne tace "Aikin banza, to uban me ya rage kuma bayan ya kwana da ke? Ai duk rashin son da kike masa dole ki zauna da shi tunda ya kwana dake yau kusan satin ki daya a gidansa ba kuma ajiye ki zai yi yana kallo kamar hoto ba tunda shi ba ɗan iska bane, kuma gidan Ali ba Obalande bane da za a tara masa fararen zawara har biyu a gida, Farida ma kadai ta ishemu, tashi ki fita ki bani waje ko in tafi in kira maki Ali yanxun nan ya fitar min da ke, tun da uwata ta haifeni ban taɓa ganin er da bata son kwanciyar hankalin ubanta ba sai ke" Umma ta share hawayen dake zuba idonta tana kallon Khaleesat tace "Ta shi ki je Khaleesah, Allah ya maki albarka, Allah kuma ya baku zaman lafiya" Mikewa Khaleesat tayi tana kuka sosai ta fita daga dakin Ummanta, Nenne tace "Atoh dai, iya addu'ar da za mu yi mata kenan a matsayin mu na rikakkun musulmai, tun da muka ga haka to Allah ne kadai ya san hikimarsa nayin hakan, kuma dama an gaya min aurenta da Awdul aure ne me kyan gaske in har zata kwantar da hankalinta, gashi mun shaida yana son ta, kuma ta dalilinta arzikin ubanta duk zai dawo har ma ya fi na da, wallahi haka aka ce min, kawai dai babba ba a son yayi ta surutu ne shi sa nake jan bakina nayi shiru" Har suka bar gidan da Abdul hawaye ne kawai ke zuba idon Khaleesat, dubu talatin ya ba kishiyoyin ummanta ko wacce 15k, ya ba Islam 50k, Nenne ya bata 20k, Malam Ali kuwa bai amsa kudinsa ba sai ajiye masa Abdul yayi kan tabarman dake bakin kofar dakinsa, babban tashin hankalin Khaleesat yanxu period dinta da ya dauke, don kafin su taho kano a dari dari tayi sallahn Azahar kar ya shigo ya ganta, tasan yau dai ƙaryar ta ya kare kawai, a haka suka iso gidansu Abdul bayan sallan magrib, Driver na shiga babban compound din da mota Khaleesat taji gabanta ya tsananta faduwa, bayan yayi parking a space din parking Abdul ya sauko daga motar yana kallonta, da kyar ta iya saukowa daga motar zuciyarta na bugawa sosai wanda ita kanta bata san dalilin hakan ba all of a sudden, ya fara tafiya tana bin sa har suka isa entrance din shiga parlorn gidan.... [6/18, 7:34 PM] khaleesat Haiydar ✍️: Khaleesat na tafiya a hankali ta shiga parlon tana karanto addu'o'i a ranta don irin faduwar da gabanta yake yi isn't normal, ga tsikar jikinta sai tashi yake, she was so uncomfortable and restless at the same time, Abdul ya kulle kofar parlon ya kalli mahaifiyarsa dake zaune cikin parlor ita da kanwarta Aunty karima da Meemah, ko wannensu da bowl cike da farfesun kayan ciki a hannu, Khaleesat ta sunkuyar da kanta ganin gaba dayansu zubo mata ido suka yi suna kallonta fuskarsu babu yabo babu fallasa, amma kana kallon kwayar idanuwansa babu abinda zaka gani sai tsantsan kiyayyarta, da kyar ta karasa tsakar parlon kamar zata harde ta fadi, ta duka kasa cikin sanyin murya ta gaishesu gaba daya, instead Momy sai ta dauke kai tana kallon Abdul tace "Flight din sai na dare ka samu kenan Babana, bayan tun sassafe Meemah tayi maka text" Aunty Karima ta hau kwalo ma mai aiki kira ta zo ta karo mata farfesu, Abdul bai ce ma Momy komai ba ganin babu wanda ya amsa gaisuwar Khaleesat cikinsu ya kalleta yace "Ta shi mu je" Khaleesat ta ɗaga kai ta kallesa amma bata tashi ba ga zuciyarta sai bugawa yake, Momy tace "Ta tashi ku je ina? Wacece ita din tukunna?" A takaice yace "Matata ce" Aunty Karima ta gyara zama da mamaki tace "Ikon Allah, ita ce er gidan barawon da yayi ma Alhaji sata har na miliyan dari kenan?" Meemah tace "Kwarai kuwa gashi kin gane ma idonki, ita ce dai er matsiyatan da Abdul ya makale ma saboda rashin sanin darajan mahaifinsa bai dubi rashin kirkin da aka yi ma Daddy a kotu akan hakkinsa ba ya koma ma yarinyar, dama yawon ta zube uwarta ta shigo yi Nigeria shi ne ta hadu da ubanta bayan sun yi watsewarsu ya aureta...." Katse ta Abdul yayi a fusace yace "Idan kika ci gaba da voicing gibberish zaki sha mamakin abinda zan maki a nan Amina, bridle ur tongue" Aunty Karima ta bude baki da mamaki tace "Amina kai tsaye? Ko ka fara shaye shaye ne Abdul? Akan shegiyar yarinyar nan kake nema kayi ma yayarka rashin kunya?" Abdul ya kalleta yace "Kar ki sake sako min baki tunda ba dake nake ba, stay out of anything that concerns me, Momy ce dolen ki ba ni ba" Momy tayi wani murmushi tace "Rabu da su Babana, take her inside ta huta, sannunku da zuwa" Tana fadin haka ta tashi ta taho kusa da Khaleesat ta dafa ta tace "Welcome my daughter, ku je sama kin ji" Da kyar Khaleesat ta mike tsaye duk jikinta a sanyaye ta bi bayan Abdul, Momy ta koma ta zauna ta bi ta da kallon gefen ido, har ta ga sun haura sama sannan ta kalli su Meemah tayi kasa da murya tace "Sam baku da hankali baku da tunani, haka muka yi da ku daxu?" Meemah da ke huci tace "Ni matsala ta kinsan ban iya pretending bane Momy, wallahi ban iya ba ko nace zan yi" A fusace Momy tace "To in kin san ruguza min plan za ki yi ki ja min asara to tun wuri ki tattara ki tafi gidan Suwaiba bana son hauka, duk ba ke kika ja mana wannan bala'i ba? da sa hannun ki fa abubuwan nan suka faru, ai wallahi sati daya yayi ma yarinyar nan yawa a gidan nan in dai ni na haifi Abdallah, don haka duk wanda bazai iya abinda nace yayi ba to ya bar gidan nan kawai kar ya ja min asara" Aunty Karima tace "Toh Momy kar kuma fa yace zai koma can gidansa da ita, kin san babu me sa shi babu me hanasa idan yayi niyyar yin abu" Momy tace "Ku dai ku zuba min ido kawai ku ga ikon Allah, ance maku ni mahaukaciya ce warce bata san abinda take yi ba irin ku? Ai ni ba yarinya bace nasan me nake yi" Mikewa Momy tayi tana tafiya gansan gansan ta nufi staircase, Meemah ta kyabe baki tace "Wallahi ji naki zuciyata bazata iya wani pretending ba akan shegiyar yarinyar nan me kamar sadaka yalla, ban taɓa jin tsanar mutum a duniya irin yanda na tsaneta ba, Abdul bai taɓa min kalan tijaran da yayi min akan ta ba, kuma fa a gabanta yayi min haka tana ji tana kallo" Aunty Karima ta sauke ajiyar zuciya tace "Nima ba gashi yayi min ba Meemah, fatan mu kawai komai ya zo karshe cikin gaggawa, mu yi yanda Momy tace kawai" Khaleesat ta dinga bin dakin da Abdul ya kawota da kallo wanda babu tantama dakinsa ne, a hankali ta zauna saman kujeran dakin tana kallonsa yana cire agogon wrist dinsa alamar zai shiga bandaki yayi alwala, abinda aka yi mata a parlor ne kawai ke yawo a kanta, tayi nisa tunanin da take yi sai gashi ya fito daga bandakin yana kallonta yace "Shiga kiyi alwala" Sosai gabanta ya fadi ta daga kai tana kallonsa, ta dake tace "Ai ban gama ba" Wani tsawan da ya gigitata ya daka mata, yana mata wani mugun kallo yace "Kar ki raina min hankali, is it going to take u forever to finish ur period? Karya kike yi kin gama" Tsabar yanda ta tsorata jikinta har bari yake ta ma rasa me zata ce masa, yace "Idan na dawo masallaci i will check for my self" Daga haka ya fice daga dakin kamar zai tashi sama, hawaye ya fara zarya a idonta, wannan moment din take ta tsoro gashi ya zo kuma babu yanda ta iya, shesshekan kuka ta fara yi cikin tashin hankali, bayan ya fita da kamar minti biyu taji an bude kofar dakin, ta juya da sauri gabanta na faduwa, Momy ce ta shigo dakin ta sakar mata murmushi ta nufota tace "Ya sunanki daughter? Mu sai yace mana Khaleesat, ni dai nace Khaleesat ai ba sunan yanka bane" Khaleesat ta sauke idonta zuciyarta na bugawa a hankali tace "Sunana Hauwa" Momy tace "Maa sha Allah, ashe uwata ce, welcome to the family my dear, taso mu je kiyi sallah" Khaleesat felt a bit relieve da gesture din Momy toward her, ta mike tsaye Momy ta kama hannunta suka fita daga dakin, can bangarenta ta tafi da ita har cikin Bedroom dinta sannan ta nuna mata bandakin dake dakinta tace "Ki shiga ciki kiyi alwala, amma kafin nan let's do a mother and daughter talk first my dear" Khaleesat ta daga kai tana kallon Momy, Momy ta nuna mata kan kujera tana mata murmushi tace "Get sitted Mamana" Khaleesat ta zauna kan 2 seater dake dakin Momy ta zauna gefenta tana facing dinta tace "Kar ki boye min komai mamata, ki daukeni tamkar mahaifiyarki, ki gaya min gaskiya wani abu ya shiga tsakaninku da Abdul ne tun bayan da ya dauke ki?" Sosai Khaleesat taji tambayar yayi mata nauyi a kai, hakan yasa ta kasa kallon Momy ta sunkuyar da kanta kawai, Momy ta kwantar da murya tace "Akwai dalilin da ya sa nake tambayarki haka ne Mamana, kar ki ji kunya ki boye min komai, open up to me" Girgiza mata kai kawai Khaleesat tayi ba tare da ta bari sun hada ido ba, Momy ta kamo hannunta tace "Kar fa ki ji kunyata ki boye min komai mamana, gaskiya zaki gaya min" a hankali Khaleesat tace "Gaskiya na gaya maki Momy" Momy ta dinga kallonta kamar dai bata yarda ba, can tace "To saboda me? Anya kuwa gaskiya kike gaya min Mamana?" Khaleesat bata dago kanta ba tace "Period nake yi ne" Momy tace "Toh kin gama yanxu?" A hankali Khaleesat tace "Daxu na gama" Momy ta sauke boyayyen ajiyar zuciya tace "To naji dadin jin hakan mamana, don nasan irin daukan da Abdul ya tafi ya maki bayan dawowar ki daga makaranta, hakan bai ba iyayenki daman yi maki duk abubuwan da ya kamata su maki ba a matsayinki na budurwa kafin ki tare gidan mijinki, basu samu daman yi maki shirin xuwa gidan miji ba, amma tunda ya kawo ki nan in sha Allah zan maki duk abinda ya kamata diyata...." Ita dai Khaleesat tayi shiru har sannan bata dago kanta ba, Momy ta mike tace "Ta shi mu je bandaki ki ga...." Khaleesat ta mike tsaye ta bi bayan Momy har zuwa bandakinta, Momy ta nuna mata wani babban flask tace "Kin ga wannan flask din? To zaki dinga tsiyayan ruwan ciki ki sirka da ruwan zafi a pampo ki dinga tsarki da shi" Momy ta dauko wasu ɓakakken sabulai dake nannade a leda ta mika mata tace "Sabulan nan su ma tsarki zaki dinga yi da ko wannensu, in kin yi sai ki ajiyesa inda kika ga na dauko yanzu don naki ne" Momy ta nuna mata wani roba dake rufe a bandakin shi ma tace "Wannan ma diba zaki yi kiyi tsarki da shi, kin ji?" A hankali Khaleesat tace "Toh Momy" Momy ta dauko wani kwalba dake boye a cikin bandakin, Khaleesat dai bin ta kawai take da kallo ta bude flask din ta tuttule abinda ke cikin kwalban, sannan ta mike tace "Yauwa mamana, duk ki tabbatar kinyi amfani da su yanda nace, sai kiyi alwala ki fito" A hankali Khaleesat tace "Toh Momy" Daga haka Momy ta fito daga bandakinta ta shimfida ma Khaleesat darduma, sannan ta zaune kan kujera ta jirata har ta fito daga bandakin, Momy ta mike ta nuna mata darduman tace "In kin idar da sallan kar ki fito, kiyi zamanki zan kawo maki abinci" Khaleesat tace "To Momy" Daga haka Momy ta fita daga dakin ta kulle da key ta tafi da makullin tana ɗan murmushi, a corridor ta hadu da Abdul ya taho daga dakinsa bayan ya shiga bai ga Khaleesat a ciki ba, Momy tace "Har ka dawo masallacin Babana?" Yace "Na dawo, tana ina ne Momy?" Momy ta ja kunnensa tace "Yanxu abinda kayi ma yayarka ya kamata Babana? Kasan ta fa wani lokacin ba hankali ya ishi yayar taka ba, da sai kayi hakuri ka kyaleta da halinta kawai" Ya hade rai yace "Dukanta fa take kokarin yi Momy? A ina ta san ta ko kuma me tayi mata da zata zageta kuma ta nemi ta doketa??" Momy ta kama hannunsa suka shiga dakin baƙin dake kusa da su tana kallonsa tace "Ai na mata fada sosai Babana, yanxu ma haushin abinda kayi mata ne yasa tayi abinda tayi a parlor amma kayi hakuri kaji Babana" Yace "Naji, ina Khaleesat din take?" Momy tace "Bazan fa baka matar ka ba sai zuwa jibi in ma zaka cire ido a kanta ka cire, tun da baka bari iyayenta sun gyarata yanda ya kamata ba to ni zan gyarata" With confusion Abdul yace "Gyarata kamar yaya Momy?" Momy tace "Ka taɓa ganin inda aka dau mace budurwa aka kai ta gidan miji haka nan? To fin karfin iyayenta da kayi kuma suna shakkar ka shi yasa suka baka ita haka babu yanda suka iya maka, amma a al'adar mu ta Hausa babu inda ake yin haka, ni kuma kaga bazan baka ita ba sai nayi mata duk abinda ya kamata na gyarata, in kuma rashin kunya zaka yi min to yi Babana, Khaleesah dai bazan baka ita ba sai zuwa nan da jibi in sha Allah, zan mata duk abinda ya kamata a matsayin ta na 'ya ta" Abdul ya kasa cewa komai yana kallon Momynsa, Momy tace "Mu je ka ci abinci" Bata jira cewarsa ba ta fita daga dakin, bin bayanta yayi ya fita amma duk tsaurin idonsa sai yaji nauyin ce ma uwar tasa komai, haka nan Momy ta dauko masa abincinsa da ta hada masa da kanta ta jera masa su a dinning sannan ta koma kitchen zata hada abincin Khaleesat, Abdul ya zauna kujeran dining amma ya kasa cin abincin, shi fa bai yi niyyar ma kwana gidan da Khaleesat ba don irin burin da ya ci a kanta yau ai sai Allah, nan da nan yaji ransa ya baci, ya mike ya shiga kitchen ya samu Momy ta sa mai aikinta ta jera ma Khaleesat abinci a tray, don irin abin da ta hada mata har ya fi na Abdul, Momy na kallon mai aikin tace "Tafi ki kai mata bangarena ki jirani ina zuwa" Mai aikin ta fita daga kitchen din da tray din, Abdul na kallon Momy a fusace yace "Toh wai menene yasa Meemah zata ce min Daddy ba shi da lafiya critically bayan ma ashe baya kasar?" Momy tace "To ai ganin likita yaje a Amurka, ko bai gaya maka bane? Karfe hudu na yamma jirginsu ya tashi, shi yasa kaji nake cewa baka taho da wuri ba don duk zatona zaka tarar da shi" Abdul yayi shiru yana kallon Momy, Momy tace "Ni dai bari in je wajen diyata, kar ka wani huce kan Meemah don ba ita ta hanaka matarka ba" Daga haka Momy ta bar sa tsaye a kitchen din, tsaye ta tarar da Mai aikinta a bangarenta tana jiranta don kofar a kulle yake, Momy ta bude mata suka shiga ciki, Mai aikin ta ajiye abincin gaban Khaleesat, Momy na kallon mai aikin wanda ranan ne ranan farkon da ta shigo mata daki tace "Toh fita ki ban waje...." Mai aikin ta fita da sauri ta kullo kofar, Momy tayi murmushi tana kallon Khaleesat tace "Ga abinci nan Mamata" Momy ta tafi ta dauko handbag dinta ciro wani kulli ta dawo kusa da Khaleesat ta bude kullin ta barbada mata abinda ke ciki a farfesun kayan cikin dake cike a bowl tace "Maza ki shanye har romon kin ji" Kai kawai Khaleesat ta gyada mata, Momy ta tafi ta zauna kan kujera tana murmushi ta dau remote ta kunna TV din dakin, a hankali Khaleesat ke shan farfesun tunani iri iri na yawo a kanta, to yanxu kenan hakuri kawai zata yi da auren Abdul, since gaba daya family dinta sun nuna sun yi accepting auren, sannan ga Mum dinsa ma ta ga tana sonta, kilan zaman aure da Abdul a kaddarar rayuwarta yake, she should just accept it with good faith, most important of all gashi mahaifiyarsa na sonta, his sister won't be an issue tunda mamansa na sonta, kawai ta saka ma ranta salama ta amshi auren tunda haka Allah ya kaddara mata, Housemate dinta ne ya fado mata, lkci daya taji hawaye ya cika idonta, da sauri ta sunkuyar da kai kar Momy ta gani cikin dubura ta dinga goge hawayen tana jin wasu masu zafi na sakkowa, sai da Momy ta tabbatar ta ci abincin sosai, sannan ta umarceta da taje tayi wanka ta tabbatar ta sake tsarki da duk abubuwan da ta nuna mata a bandaki, kafin Khaleesat ta fito Momy ta dauko mata kayan bacci da inner wears, Khaleesat ta shirya tayi sallan isha'i, Momy bata tashi barin dakin ba sai kusan karfe tara da rabi, bayan ta sa Khaleesat ta kwanta kan gadonta sannan ta kashe mata wutan dakin ta bata remote din Ac a kusa da ita, tayi mata sai da safe ta fita daga dakin, har ta kulle kofar ta sake budewa ta shiga tana kallon Khaleesat tace "Ko tashi kika yi zaki kama ruwa cikin dare kiyi tsarki da abubuwan nan fa Mamana kar ki manta" Khaleesat tace "Toh Momy" Momy ta kara mata sai da safe sannan ta fita ta kulle kofar da makulli ta sauka downstairs, Abdul kadai ne zaune parlor yana kallon kwallo amma kana ganinsa kasan ransa a bace yake, Momy tana kallonsa tace "Sai da safe Babana" Ciki ciki ya amsa mata, ta juya ta koma sama zuwa dakin da su Meemah suke, duk suka dinga kallon Momy bayan ta shigo, Aunty Karima tace "Ya dai Momy duk ta yi?" Momy tayi wani murmushi tace "Tun yaushe kuma" Meemah tace "Alhamdulillahi, shi Abdul din fa?" Momy tace "Shi ai dama a miyar shinkafa aka ce na zuba masa maganin, sai ruwan lipton, na kori mai aikin taje bakin pampo tayi wanke wanke shine na samu duk na zuba masa nasa" Meemah tayi murmushin mugunta tana gyara zama sanin Momy bata bin malaman banza, kai in malami yace zai amshi kasa da 1M a wajenta ma bata yarda da ingancin aikinsa ba, inda ake aikin da gaske take zuwa, ko da kuwa miliyan biyar zata kashe bata kyashi don tasan aiki na gaske ake mata. [6/19, 8:55 PM] khaleesat Haiydar ✍️: Washegari da safe bayan Khaleesat ta shirya cikin tsadadden Abayan da Momy ta bata, Momy ta gama hada mata shayin da take yi cikin cup tace "To zo kiyi breakfast din kar ya huce Mamana" Khaleesat bata ce komai ba ta karasa ta zauna kan darduman da aka jera mata breakfast din, Momy tayi murmushi tace "Idan farfesun bai isheki ba sai ki bude warmer ki ƙara, dankalin ma akwai saura a warmer in bai ishe ki ba" Ita dai Khaleesat kai kawai ta gyada mata, tana juya shayin gabanta a hankali da spoon din ciki, Momy ta koma kan kujera ta zauna tana kallonta tace "Duk da ma ina lura jiya baki wani ci abincin da aka kawo maki da yawa ba, ko maganin cin abinci zan sa a samo maki mamana" Khaleesat tayi murmushin karfin hali bata dai ce komai ba ta dau shayin tana kallon ciki, sai tayi tunanin lipton din ne kilan ya fashe a cikin ruwan shayin, sipping din shayin tayi kadan ta ajiye sannan ta fara cin irish din, Momy dai kallonta kawai take kasa kasa, Bude kofar dakin aka yi Momy ta juya, ganin Abdul tace "Sai yanxu ka tashi Babana" Bai ce mata komai ba ya karasa ya zauna saman kujera, Khaleesat ta ɗan kallesa taga kallonta yake, sauke idonta tayi a hankali tace "Ina kwana" Ya kauda kai yace "Lafiya" Momy tace "Ka tashi kaje kayi breakfast din ka" Yace "Momy za mu je shopping ne, bata zo da kaya ko daya ba" Momy na kallonsa tace "To wanda ka gani a jikinta yanxu kai ka siyo mata?" Shiru Abdul yayi yana kallon Momy, Momy tace "To har na tura ma Meemah kudi su je su yi mata siyayya ita da Karima tunda kai baka da ƙara" Mikewa Abdul yayi ya nufi kofa ya fice daga dakin, Momy ta bi sa da kallon gefen ido, sai da Momy taga Khaleesat ta gama cin abinda zata ci na breakfast din sannan ta mike ta fita ta kira mai aikinta ta fitar da sauran abubuwan da Khaleesat ta rage, bayan mai aikin ta fita Momy ta bude bayan labulenta ta dauko wani karamin jarka ta kawo ma Khaleesat tace "Wannan tsumi ne Mamana, daga yanxu har zuwa dare nake son ki shanyesa gaba daya" Ita dai Khaleesat kallon jarkan take, Momy tace "Kin ji ai ko?" Khaleesat ta gyada mata kai tace "Toh Momy" Momy ta dauka ta mayar bayan labule sannan tace "In zaki yi kallo sai ki kunna TV abun ki, bari in je zanyi bakuwa ban san ko ta iso ba" Khaleesat tace "Toh" Momy ta fita daga dakin ta kulle da makulli tana rike da makullin ta sauka downstairs don aminiyarta godiya ta kirata ta sanar mata tana hanya, tana shigowa parlor taga Abdul zaune dinning area da breakfast din da Khaleesat ta rage a gabansa, da karfi Momy ta kwala masa kira, ya juya yana kallonta, ta karasa wajen da mugun sauri tace "Banda abun ka ba ga naka a kitchen ba Abdul me zaka yi da wanda aka rage? Ko har kaci wannan din ne?" Abdul dake kallonta yace "Ban ci ba, amma menene idan na ci?" Momy ta kwalo ma mai aikinta kira, Mai aikin ta taho da sauri Momy ta kunduma mata wani ashar tace "Nan nace ki ajiye sauran abincin er iska kawai er neman jidali? Me yasa ke dakikiya ce? Wallahi zan kore ki fa a gidana na gaji da maganar da kike sa ni kamar kanwar uwarki, yau ga shegiyar mata kawai" Abdul ya kalli Momy yace "Ni fa nace ta kawo min nan, beside what is wrong with the food da bazan ci ba?" Momy ta mata tsawa tace "Dauka ki wuce ki ban waje guntuwar banza kawai" Mai aikin na ba Momy hakuri ta dauke jiki na rawa ta tafi kitchen da breakfast din, Momy ta kalli Abdul dake kallonta, yace "I want to understand meye da abincin da bazan ci ba Momy?" A takaice Momy tace "Kayan gyaran mata mana? Ko kai na mace ne?" Bata jira cewarsa ba ta bar wajen ta shige kitchen ya bi ta da kallo, Tuttular da shayin tayi a sink sannan ta juye sauran irish din da kwai da farfesun duk ta cakudesu waje daya tace "Gasu nan ki kai ma karnuka, in kuma kwadayin ki ya ja ki kika ci ke kika jiyo" Mai aikin ta risina ta amsa tace "Toh Hajiya" Sai da Momy ta jirata har ta dawo bayan ta kai ma karnukan can cage dinsu sannan Momy ta dau breakfast din Abdul ta kai masa kan dining din tace "Ga naka nan" Daga haka ta juya ta bar wajen, dai dai shigowar Godiya gidan, da fara'a Momy ke mata sannu da zuwa Abdul ya dauke kai kamar bai ganta ba don ya tsani matar with passion, tun asali dama baya gaida ta, Haka Momy ta ja ta zuwa sama tana cewa "Mu je ki ga surkar tawa ku gaisa" Da ido Abdul ya bi su har suka haura sama, Momy na isa kofar dakinta ta bude da makulli suka shiga, Khaleesat dake gyara gadon Momy ta mike tsaye tana kallonsu, Momy na murmushi ta kalli godiya tace "Kin ganta" Da fara'a sosai Godiya tace "Maa sha Allah, ai ko ga ta kamar balarabiya Maa sha Allah, sannu amarya, ya sunanki?" Momy na murmushi tace "Sunan Baabata gareta, Hauwa sunanta" Khaleesat ta zame kasa ta sauke idonta ta gaida Godiya, Godiya ta karasa kusa da ita ta dafata tare da ɗagota ta zaunar da ita gefen gadon Momy tace "Lafiya lau diyata, ya bakunta?" Khaleesat bata ce komai ba kuma bata dago kanta ba, Momy na kallon Khaleesat tace "Kin sha tsumin da nace ki sha kuwa?" Khaleesat ta gyada mata kai tace "Na sha" Momy tace "To maa sha Allah, Allah ya maki albarka Mamana, zuwa anjima sai ki kara sha kin ji" Khaleesat tace "To" Bayan few minutes Momy da Godiya suka fita dakin, Momy ta sake kulle kofar da makulli sannan ta cire makullin suka tafi wani daki dake sama, bayan sun shiga Momy ta kulle kofar tana kallon Godiya tayi murmushi tace "Duk tayi amfani da abubuwan babu gardama godiya, iya na jarkan nan ne kawai ya rage yanzu" Godiya ta zauna gefen gado tace "To madallah, shi ma Abdul din duk kinyi yanda aka ce kiyi da na sa?" Momy tace "Kwarai kuwa" Godiya tayi wani murmushi ta bude handbag dinta ta ciro wani babban laya bakikirin da shi ga er karamar kwado a jiki ta mika ma Momy tace "To aikin karshe kenan wannan Hajiya, Malam ya ce ki samu inda kika san baza a taɓa tono sa ba ki binne a cikin gidan nan" Momy ta zauna gefenta tana murmushi ta amshi layan tace "To laya nawa na binne gidan nan ba a tono ba godiya, ai wannan karamin aiki ne a wajena don ba sabon abu bane" Godiya tace "Yauwa, bayan kin binne Malam yace ki basa yarinyar kawai, wallahi yace min in har ta wuce sati biyu Abdul bai rabu da ita ba to bazata wuce sati biyar ba a gidansa" Fara'ar fuskar Momy ya bace tace "Har sati biyar Godiya? Ni da yace min sati daya kacal a waya" Godiya tace "Halan bai gaya maki irin abubuwan dake ƙan dan ki bane? Da yaya ma aka samo kansa har asirin nan yayi tasiri? Ai abubuwan ƙan Abdul sun fi karfin wani asirin wallahi kiji in gaya maki" Momy ta sauke ajiyar zuciya tace "An taɓa gaya min haka da dadewa wallahi, don ni akwai malamin da yace min ma yanda asiri ke cin ubansa shi sai an wahala asiri zai ci sa" Godiya tace "To wallahi Malam sai da ya tura masa aljanu don ma ki ji Hajiya, aikin nan sai da Malam ya hada da wasu malaman don aiki ne me wahalan gaske yace min wallahi" Momy tace "To ni fargabana kada fa in mika masa yarinya ace asirin nan bai ci ba abinda muke gudu ya afku mu shiga uku Godiya" Godiya tace "Sai kace yau Malam ya fara maki aiki? Ai da aikin bai yi ba kinsan bazai boye mana ba, sai dai ya kara mana lokaci yayi wani sabon aikin fa, dama yace in na yarinyar ya ci shine zai sa na Abdul din ma yayi tasiri sosai" Momy tace "Haka ya ce kam" Godiya tace "Don haka zuwa gobe ki basa ita kawai su tafi an gama aiki sai jiran result, kuma ina me tabbatar maki zaki sha mamaki" Momy na murmushi tace "Toh shikenan godiya, nagode sosai, zan tura masa cikon dubu dari biyar dinsa anjima" Da yammacin ranan bayan Momy taga Abdul ya fita gidan tayi maza ta aiki mai aikinta kasuwa saboda tayi amfani da daman ta haƙa rami a garden din gidan ta binne layan da Godiya ta kawo mata, bayan mai aikin ta tafi Momy ta zaga zuwa garden din gidan ta samu spot me kyau ta fara haƙa rami da wuka, bayan ta haka yayi zurfi yanda take so sannan ta jefa layan ta mayar da ƙasan wajen ta dau wani dutse ta dora dai dai wajen don kada a ga alamar an tono kasa, tap ta bude don wanke hannunta da wuƙan da tayi using, Khaleesat ta karasa bakin window din dakin Momy jin ƙaran bude ruwan pampo, in ta gaji da zaman dakin dama jikin window take zuwa ta tsaya tana kallon waje, ta tsaya jikin window din tana ta kallon Momy dake ta wanke hannunta bayan ta wanke wuƙan, bayan ta gama ta kara komawa kusa da dutsen tana seta sa da kyau ta yanda ko da wasa baza a ga tonannen ƙasa ba, sai kuma ta mike ta fara tsinko doddoya dake Garden din, sannan tayi using wuƙan hannunta ta yanki pumpkin leaves isasshe bayan ta gama ta bar garden din tana rike da ganyayyakin hannunta, babu abinda Khaleesat ta kawo a kai don tunaninta ganye Momy taje diba a garden din, Momy na kai ganyayyakin kitchen sai ga su Meemah sun dawo daga shopping din da ta aikesu su yi ma Khaleesat, dariya Momy ta dinga yi a parlor ganin wasu shegun abayoyi masu saukin kudi da suka kwaso ma Khaleesat irin wanda ake dinkawa a kano, ga wasu shegun dogayen riguna su ma masu arha, hatta inner wears da suka siyo duk very low quality ones ne, babu wani abu na arziki da suka siyo ma Khaleesat, Momy na ci gaba da dariya tace "Duk maida su cikin ledojin kawai na yafe ganin wannan tarkace haka karima, amma baku da kirki yaran nan" Aunty Karima na dariya ta maida kayan cikin leda ta kulle tace "Su ne dai dai er talakawa ai Momy, da so kika yi ki ga abayan dubu hamsin zuwa sama? Ai ita Meemah ma en gwanjo ta so mu je muyi selecting mata kawai" Dariya kawai Momy take, ita kuwa Meemah danna wayarta kawai take don duk wani abu da ya shafi Khaleesat ko kadan baya bata dariya, she just can't wait taga irin rabuwan da Abdul zai yi da Khaleesat don shine babban abinda ke gabanta yanxu. Wajen karfe takwas da rabi Momy na zaune parlor da Abdul tana ta yi masa hira, shi dai wayarsa kawai yake dannawa baya responding kamar ma bai san me take cewa ba, Momy ta kwalo ma mai aikinta kira, Mai aikin ta taho da gudu tace "Na'am Hajiya?" Momy tace "Zaki ga Kankana da na yanka a kitchen ki dauko ki kai ma Mamata a sama" Mai aikin tace "To Hajiya" Juyawa tayi ta koma kitchen sai ga ta ta dawo rike da bowl din kankanan tana kallon Momy cikin ladabi tace "Amma Hajiya dakin a kulle yake" Momy tace "A'a a bude yake tun daxu, ki je ki kai mata" Bayan mai aikin ta tafi ta kai water melon din ta dawo ta tafi kitchen ta ci gaba da aikin da take, Momy ta dau wayarta tace "Bari in inyi waya da Alhaji, daxu na ga kiransa ina kitchen wallahi" Shi dai Abdul bai ce mata komai ba har ta shiga dakin dake downstairs ya bi ta da kallo... Bayan minti biyu ya mike ya nufi stairs direct ya tafi bangaren Momy, yana bude kofar dakin Khaleesat dake zaune saman darduma bayan ta idar da sallah ta gama duk addu'o'in da zata yi ta juya ta kalli kofar, sosai gabanta ya fadi bayan sun hada ido da Abdul, ya karasa cikin dakin babu yabo babu fallasa yace "Ta shi mu je shopping...." Khaleesat da gabanta ke faduwa ta nuna masa ledan da Momy ta kawo mata daxu duk da bata duba kayan ciki ba cikin sanyin murya tace "Ai Momy ta sa an min shopping din, ka gan su can ma" Ya hade rai yace "Kee... Get up nace, i am not asking for ur opinion" Ta sauke idonta ta mike tsaye da kyar ta dauke darduman tana linkewa, sosai taji hankalinta ya tashi, a ranta ta dinga addu'an Allah ya kawo Momy dakin immediately, fixge darduman hannunta yayi ganin it's taking her a whole eternity to fold, ya ajiyesa saman kujera sannan ya kama hannunta suka nufi kofa fuskarsa a daure suka fita daga dakin, Khaleesat dai bin sa kawai take a tsorace, downstairs suka sauka har sannan yana rike da hannunta, babu kowa a parlorn sai mai aiki dake goge goge a dining area, ya dau makullin motarsa da ya bari kan center table, Khaleesat ta marairaice masa cikin rawan murya tace "Ya Abdul Momy fa bata sani ba, kar ta shiga dakinta taga bana nan, kaga babu dadi haka" Wani kallon da yayi mata yasa tayi shiru zuciyarta na bugawa, bata sake gigin ce masa komai ba har suka fita parlorn gidan zuwa parking space, Khaleesat taji hawaye ya cika idonta bayan ya sa ta shiga motarsa ya shiga driver seat, mai gadi ya bude masa gate ya fice gidan da motar. Momy ta fito parlor tana kallon Mai aikinta tace "Naji kamar fitar mota, waye ya fita?" mai aikin tace "Alhaji karami ne ya fita" Momy tace "Shi da wa?" Mai aikin tace "Shi da matarsa" Shiru Momy tayi don bata yi tunanin zai ce zai tafi da Khaleesat yau ba, don so tayi taga yanda za su kwashe, shi yasa ma ta basa hint din dakinta a bude yake, ta zata can din kawai zai bi ta ko kuma ya kai ta dakinsa, Momy ta sauke ajiyar zuciya, ganin mai aikinta sai kallonta take ta hade rai tace "Lafiya kike kallona haka munafuka?" Da sauri mai aikin ta juya ta bar wajen, Momy ta juya ta koma daki amma fa zuciyarta ya kasa nutsuwa sam sam, gani take kamar Abdul zai yi tarayya da Khaleesat, duk da malaminta bai taɓa mata aiki bata ga result me kyau ba amma a wnn case din sai take ɗari ɗari kada abinda suke gudu yaje ya afku dama ga Godiya tace aikin me wahala ne, ai kuwa da ta shiga uku ta lalace, number Godiya tayi dialing ta zauna gefen gado tana jiran tayi picking. Hawaye kawai Khaleesat take tana dafa shayin da Abdul ya sa ta dafo masa a kitchen, ita ta ma riga tayi give up yau don bata da wani dubaran da ya rage mata in ba so take ta fusata Abdul ya doketa ba, she will just accept her kadr with good faith, gwara tayi accepting dinsa kawai a mijinta tunda haka Allah ya kaddara mata, goge hawayenta tayi tana tafiya a hankali ta tafi kai masa lipton din dakinsa, tana bude kofar ya ajiye wayar hannunsa yana kallonta, kanta a kasa ta karasa har inda yake ta duka ta ajiye masa black tea din, ta mike zata bar wajen ya jawota ya zaunar da ita gefensa yana kallonta, ita dai bata bari sun hada ido ba zuciyarta na wani irin bugawa, ya dago kanta suka hada ido, sauke rigar baccin jikinta yayi slowly yana kallonta babu ko kiftawa, ta sunkuyar da kanta bugun zuciyarta ya tsananta sosai, tana ji tana gani ya cire duk abinda ke jikinta yana kare ma each and every part of her body kallo, bata sake yarda sun hada ido ba, a hankali ya kwantar da ita, ta runtse idonta da sauri jikinta na rawa ganin inda yake kokarin kai bakinsa, after some seconds Khaleesat ta bude idonta a hankali tana kallonsa jin bai yi abinda yayi niyya ba, taga wani wajen daban yake kallo babu ko kiftawa, after some seconds ta ga ya mike ya nufi kofa ya bude, fuska daure yake kallonta babu yabo babu fallasa yace "I need my privacy....." Khaleesat ta mike zaune da kyar tana kallonsa, lokaci daya jikinta yayi sanyi, ta jawo Hijab dinta da ya cire tun zuwansu gidan ta saka sannan ta dau kayan baccinta ta nufi kofa, bata bari ta hada ido da shi ba ta fita daga dakin taji ya kulle kofar da makulli, juyawa Khaleesat tayi tana kallon kofar..... [6/20, 7:35 PM] khaleesat Haiydar ✍️: Da Asuba Khaleesat na zaune kan gado ta dafe kanta da yayi mata nauyi sosai, tun karfe uku da rabi bacci ya kaurace mata, bayan tayi sallahn nafila ta kai ma Allah kukanta shine take ta zaune saman gado tana tunanin rayuwarta, in 3 weeks time za su yi resuming school wanda shekarar su na karshe kenan za su shiga a makarantar but unfortunately tasan baza a koma da ita ba, ko kadan bata saka ran zata koma John Hopkins ba dama, but it's really hurtful don duk shekarun da tayi a makaranta zai tashi a banza kenan, ta goge hawayen da ya gangaro mata jin ana kiran sallan asuba ta sauka daga saman gadon, sai da ta dafa bango sbda juya mata da kanta ke yi, tun da ta tashi daxu take jin jikinta kamar ba ita ba, she can't even understand how she is feeling, sai da ta koma ta zauna na yan mintuna sannan ta tashi tana tafiya slowly ta wuce bandaki, wanke bakinta tayi sannan ta dauro alwala ta fito daga bandakin, bayan ta idar da raka'atanil fajr tayi sallan asuba, har karfe bakwai na safe Khaleesat na zaune kan darduma duk da ta idar da azkar din ta, in tayi wannan tunanin tayi wancan a haka dai har ta mike daga karshe tana tafiya a hankali ta nufi kofa ta bude ta fita daga dakin, bata karasa parlon ba ta tsaya tana kallon Abdul dake kwance saman 3 seater idonsa a lumshe yana sauraron karatun qur'ani ta wayarsa dake gefensa, duk tunaninta bacci yake ganin yanda ya lumshe ido, har zata juya ta koma dakinta taga ya bude ido yana kallonta, ta sauke idonta ta karasa cikin parlon tana tafiya a hankali ta duka kusa da shi cikin sanyin murya tace "Ina kwana" Yace "Lafiya" Bata sake cewa komai ba kanta a kasa, after some seconds ta mike zata bar wajen, calmly yace "I need breakfast, ban ci abinci da daddare ba" Ta daga kai ta kallesa, sai kuma tace "Toh...." Juyawa tayi ta nufi kitchen don ganin me zata girka, doya da kwai tayi deciding tayi don shi tagani available a kitchen din, wajen karfe takwas ta gama komai ta kai har gabansa a parlon ta durkusa ta ajiye, ganin bread a kan dining table ta mike ta tafi ta dauko sannan ta dawo ta ajiye masa tana kallonsa a hankali tace "Gashi na gama, in hada maka shayin?" Without looking at her yana danna wayarsa daga kwancen da yake yace "Ohk" Hada shayin tayi bayan ta gama ta koma gefe tana kallonsa a hankali tace "Na gama" Ajiye wayarsa yayi ya sauko daga saman kujeran, shayin ya dauka yana sha, ba tare da ya kalleta ba yace "Ke ina naki shayin?" Shiru tayi bata ce komai ba, jin tayi shiru ya daga kai ya kalleta, sunkuyar da kanta tayi, sai kuma ta mike ta nufi kitchen, ba a dau lokaci ba sai ga ta ta dawo da cup da tea spoon, ta duka kasa ta fara hada shayin nata, ya kalli madaran da ta zuba a shayinta ya dau wani spoon ya kara mata madaran, ita dai bata bari sun hada ido ba, a plate daya ya dibar masu doyan ya fara ci, ita dai juya shayinta kawai take a hankali, after some minutes ganin bata fara cin doyan ba ya daga kai ya kalleta yace "Ko a baki za a baki?" Ta ɗan yi murmushin karfin hali ta dau fork ta fara cin doyan a hankali, da ta kallesa sai su hada ido, kana ganinta kasan she is not comfortable a wajen don ya riga ya sa mata tsoronsa a zuciya, daga karshe ta ajiye fork din hannunta a kan tray, ya daga kai ya kalleta, a hankali tace "Na koshi" Bai ce mata komai ba, ta koma gefe tana shan shayinta slowly, after a while Abdul ya mike ya koma saman kujera, ta tashi ta dau sauran abincin ta kai kitchen, sai da ta wanke utensils da suka yi using sannan ta fito daga kitchen din, magana take son yi masa amma tana tsoro, ya kalleta tayi saurin sunkuyar da kai kamar munafuka tana wasa da yatsunta, yace "Me ya faru?" Ta karasa ta duka daga gefensa a hankali tace "Dama pls ina son zan yi magana da Safiyyah, ka taimaka ka kira min ita ta wayarka" A takaice yace "Bazan kirata ba, kanwar baabarki ce Safiyyar?" Sosai jikin Khaleesat yayi sanyi, ta sunkuyar da kanta tayi shiru bata ce komai ba, yace "Tafi ki bani waje" A hankali ta mike a sanyaye ta wuce dakinta, goge hawayen da ya taru idonta tayi ta zauna gefen gado, after a while ta share hawayen da ya ki tsaya mata ta mike ta cire hijab din jikinta ta linke ta ajiye sannan ta shiga bandaki, brush tayi sannan tayi wanka, ganin abubuwan wanke gashi a bathroom din ta wanke gashinta ta tsane da karamin towel sannan ta dau wani towel din ta daura ta fito, tana tsaye gaban madubi tana shafa man gashi taji an bude kofar dakin, da sauri ta juya gabanta ya fadi sosai ganinsa, kana ganinsa kasan daga wanka ya fito shi ma, cikin dubara ta gyara daurin towel dinta tana jin zuciyarta na bugawa ta ci gaba da oiling gashinta, ya karaso har inda take tsaye ya tsaya a bayanta yana kallonta ta madubi, ita dai ta kasa dago idonta tana jin saukan numfashinsa a bayanta, ta ajiye oil din hannunta a hankali don duk ta daburce, shi dai yana tsaye dab da ita yana kallonta ta madubi, ya kai hannu zai yi loosening din towel din kirjinta, juyowa take son yi da sauri kamar zata yi kuka cause bazata iya ganin kanta ta madubi a yanda yake ganinta ba, yaki barin ta juyo hakan yasa ta runtse idonta zuciyarta na bugawa, bai fasa kallonta ta madubin ba har ya cire towel din jikinta ya jefar saman gado, he kept his eyes glued to her cause he just can't stop admiring her bare body any time he set his eyes on her, gaba daya taki yarda ta bude idonta, bata ankara ba kawai sai jin su tayi a saman gado, bata san sanda ta bude ido ba ta fashe da kuka tana turasa a tsorace ganin yau kai tsaye kawai far mata yake kokarin yi babu bata lokaci, ita kanta bata san inda ta samu courage din turasa ba duk da tsoronsa da take, da mamaki yake kallonta yana sauke numfashi, ganin kiciniyar sauka take yi daga saman gadon tana kuka, cikin kakkausan murya yace "I will give u a dirty slap" Danneta yayi yanda ko motsin kirki bazata iya ba balle tace zata sauka daga saman gadon, ta dinga masa kururuwa tana kokarin kwatar kanta don bata taɓa tsorata ta gigice da lamarin nan ba irin yau, duk yanda Abdul ya so cimma burinsa a wnn moment din hakan ya faskara, kawai ya tuna ita ba irin matan da ya saba mu'amala dasu bane, he couldn't have his way no matter how hard he tried, he was so confuse as at how intact she is even though he knows she is a virgin, hakan yasa ya fara romancing dinta roughly to make his way more slickier, cause he was determined in fulfilling his mission today, wani wawan marin da yayi resetting dinta back to default ya sauketa mata don duk da yanda ya danneta she is still struggling so hard to free her self under him, Khaleesat taji kamar numfashinta na yi mata gardama, at this moment tasan babu me kwatar ta hannunsa sai Allah, she was so weak and in severe pain hakan bai hanata struggling ba cikin kuka take cewa "Don girman Allah ka rufa min asiri Abdul, wallahi mutuwa zan yi bazan iya ba, it's soo painful...." Ya kara sauke mata wani marin cause he is seriously trying to find his way by all means, Gaba daya Abdul komawa yayi kamar bai taɓa tarayya da mace ba a wnn lkcn, ya koma kamar Amateur da ta mance inda zai bi, duk wani dubaransa was fortile, he was really frustrated and vexed, Ganin how helpless she was ga numfashinta na neman daukewa ya rungumeta gam jikinsa yana kallon fuskarta da tafin hannunsa ya kwanta ta dalilin marin da yayi mata, lumshe ido yayi yana sauke numfashi kamar wanda yayi tsere, saukan hawayenta ya dinga ji a kirjinsa ya lumshe idonsa zuciyarsa na bugawa, after almost a minute yayi kasa da murya da kyar, yana shafa dogon gashinta yace "I am sorry Khaleesat, i am sorry" Ita dai hawaye kawai take tana sauke ajiyar zuciya, tana jin wani azaba in between her, they were like this for almost 5 mins, Abdul ya saketa ya koma can karshen gadon ya dafe kansa dake sara masa, ga wani azababben ciwon mara da yake ji, da kyar ya mike ya dafa bango na ɗan lokaci kafin ya nufi kofa ya fice daga dakin, Khaleesat ta takure cikin duvet tana sauke ajiyar zuciya hawaye wasu na bin wani a idonta, bata san lkcn da baccin wahala ya dauketa ba a haka. Karfe sha biyu saura taji hannu a forehead dinta, bude idonta da suka kumbura tayi a hankali don sosai kanta yayi mata nauyi, suna hada ido ta sauke idonta, Calmly yace "Ta shi ki shirya mu tafi shopping" Da kyar ta mike zaune tana kara rufe jikinta da duvet, sai kuma ta fara jawo towel din da ya cire mata daxu, shi dai bai ce mata komai ba yana kallonta, har cikin ransa he felt bad ganin yatsunsa kwance a fuskarta, cikin dubara ta daura towel din sannan ta mike tsaye lkci daya ta duka kasa da sauri tana runtse ido, yana kallonta yace "What?" Lokaci daya hawaye ya idonta, cikin rawan murya tace "Bazan iya ba, zafi nake ji sosai" Ya hade rai yace "Zafin me?" Ta kasa kallonsa hawaye na sauka idonta, yace "Me na maki da za ki ji zafi?" Ita dai bata dago kanta ba gabanta na faduwa, mikewa yayi ya fice daga dakin ta bi sa da kallo, after a while Khaleesat taji fitar motar sa a gidan, ba karamin daurewa Khaleesat tayi ba ta tafi bandaki, sai da tayi sit bath sosai sannan taji ta samu sukuni, tayi wanka ta dauro alwala ta fito. Karfe biyu saura tana tafiya a hankali tana dingishi ta fito parlor, ledan kayan da Momy ta bata ta gani a parlon, ta karasa ta bude ledan sai a sannan taga irin kayan da su Meemah suka siyo mata, a hankali ta daure ledan ta dau kayan walking slowly ta koma dakinta da su ta ajiye ta dawo parlon ta tafi kitchen don daura girki... Momy dake zaune parlor tana kallon Meemah da wani expression tace "Bacci fa kika ce Meemah??" Meemah ta ajiye gyalen jikinta tace "Wallahi kuwa Momy" Momy tace "To baccin me take wajen karfe sha dayan safe??" Meemah tace "In kin tambayeni in tambayi wa?" Momy ta gyara zama tace "Toh baki tafi dakin kin dubo ba?" Meemah tace "In lafiyarta qlau ai kinsan taso ta zai yi ta fito ta gaisheni barin ma da nace masa kin bani sako in bata, sai ce min yayi magani ta sha tana bacci" a hankali Momy tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Meemah tayi wani murmushi tace "Kinsan Allah Momy, kawai jikina ni tun asali ya bani ba lallai irin wannan asirin yayi tasiri lokaci daya ba, bance bazai yi tasiri ba amma sai ya gama moreta tukun, kin ga in rabo ya shiga kafin nan kuma ai mun shiga uku mun lalace, hada iri da talaka ya tabbata" a fusace Momy tace "Ke dai a rayuwarki baki taɓa furta alkhairi sai sharri Amina? Asirin kusan miliyan biyun kike ce min ba lallai yayi tasiri ba? Ko kina hauka ne?" Meemah tace "A'a ni bance bazai yi tasiri ba Momy, cewa nayi..." Momy ta dakatar da ita rai bace tace "Bana son ki sake saka min mugun bakin ki a lamarina, ki tashi ki ban waje kar in yi mummunan bata maki rai wallahii" Mikewa Meemah tayi ta kyabe baki tace "Shi Abdul din da duk mun san yanda idonsa ke kan mata ne kike tunanin zai bar yarinyar nan su kwana gida daya babu abinda ya shiga tsakaninsu?" Wani zagi Momy ta kunduma mata tace "Baza ki tafi ki ban waje ba, me mugun alkaba'i kawai, duk ba ke kika ja mana wannan bala'i ba?" Meemah na tabe baki tayi tafiyarta sama, Mikewa Momy tayi ta fara zaga parlor tana jin zufa na keto mata duk da Ac dake kunne, sai kuma ta dau wayarta ta wuce sama da sauri. Wajen karfe hudu da rabi Abdul ya dawo gida, Khaleesat ta idar da sallah tana zaune kan darduma ya shigo dakin ya ajiye shopping bags din hannunsa, ta mike a hankali tana kallonsa tace "Sannu da zuwa" Yace "Ki duba ko akwai abinda ba a siya ba" Tana kallon bags din ta karasa inda ya ajiyesu tana duba tsadaddun Abayan da ya siya mata kala kala, da takalma da handbags, irin dai quality din da yake siya mata a baya, duk wani abu da zata bukata sai da ya siyo mata, har da tsadaddun turaruka iri iri da man gashi, da na shafawa, kallon lube din da ta ciro a siyayyan ta dinga yi don at first tayi zaton na shafawa a fuska ne, sosai gabanta ya faɗi ta ɗan kallesa taga kallonta yake, da sauri ta dauke kai zata ci gaba da ciro sauran abubuwan da ya siyo ya mika mata hannu alamar ta basa lubricant din, ta mika masa ba tare da ta bari sun hada ido ba, juyawa yayi ya dau ledan kayan da Meemah ta kawo daxu ya fitar da shi daga dakin, a hankali Khaleesat ta zauna gefen gado nan da nan hawaye ya cika idonta, bata san sanda ta fashe da matsanancin kuka ba tana tuna azaban da ta sha daxu. Wajen karfe takwas da rabi na dare Khaleesat ta gama dafa ma Abdul tea din da ya sa ta ta dafa masa, gaba daya tun daga sanda ya dawo har zuwa yanxu bata da sukuni a gidan, tana sanye da hijab ta karasa har inda yake zaune a dakinsa yana karatun Alqur'ani, ta durkusa ta ajiye masa shayin, zata mike ya jawota jikinsa bayan ya rufe qur'anin, yayi kissing goshinta yana kokarin cire mata hijab din har dai ya cire, lkci daya jikinta ya fara rawa tana son kwace kanta, ƙin saketa yayi ya riketa gam, tun tana ganin abun kamar wasa tunda a zaune yake, har sai da ta gansu saman gado ya rabata da komai na jikinta sannan idonta yayi clear, ihun da ta dinga masa tana kuka tana kokuwa da shi bai sa ya fasa abinda yake yi ba, upon yayi using lube da ya siyo amma kamar daxu yanxun ma dai bai iya yayi mata komai ba, after a while ya sake ta, fuskarsa a daure yace "Fita" Ta sauka kan gadon da sauri ta dau hijab dinta ta saka ta fice daga dakin jikinta na rawa, zaunawa yayi gefen gado ya rike kansa da yayi masa nauyi yana sara masa. Throughout washegari Abdul bai bi ta kanta ba a gidan, ta dai gaishesa da safe ya amsa babu yabo babu fallasa, amma hatta breakfast da tayi bai ci ba balle lunch, sosai taji guilty conscience na damunta don tana tsoron kamun Allah, tunda tayi karatun addini tasan kuma meye aure, amma yanxu ita kanta tasan ba intentionally bane taki basa hadin kai, kasa daurewa tayi wajen karfe uku na rana jiki a sanyaye ta samesa a parlor ta durkusa daga gefensa a hankali tace "Don Allah Ya Abdul kayi hakuri idan nayi maka laifi" Shiru tayi don ita kanta tasan she sounds stupid, Babu yabo babu fallasa yace "Laifin me?" Ta sauke idonta ta kasa cewa komai, Yace "Ohk kinsan ma abinca kike yi kenan" Ta girgiza masa kai da sauri, kallonta kawai yake don duk yau ji yayi kamar an dauke masa sha'awarta, unlike before da ko me zata yi feeling din nan nata dai na nan a ransa, kawai ji yayi baya ma son ganinta kawai, Calmly yace "Tashi ki bani waje" A hankali ta mike ta bar parlon. Da daddare bayan magrib yana kwance parlor ya kunna karatun Alkur'ani ta wayarsa yana saurare, tun da Khaleesat ta fito zata je daukan abinci a kitchen ya bi ta da kallo, har ta fito daga kitchen din ta wuce dakinta da abincin, ya mike zaune, after a while sai ga ta ta sake fitowa ta kai plate din kitchen, hijab ne har kasa a jikinta, still da ta fito haka ya bi ta da kallo, ita dai ta gefen ido kawai take kallonsa har ta koma dakinta, Bayan isha'i ya bude kofar dakinta, sosai ta tsorata ganinsa, suna hada ido ta sunkuyar da kanta don dama zaune take kan darduma ta idar da sallah, Yace "Make me a cup of tea" A hankali tace "Toh" Jiki a sanyaye ta tashi taje ta dafo masa tea din ta kai masa dakinsa, haka kawai gabanta ya dinga faduwa ganin kallon da yake mata, ta dai ajiye cup din tea din sannan ta fita ta koma dakinta ta kashe wuta ta kwanta ta shige cikin duvet, banda faduwa babu abinda gabanta yake yi, har ta fara bacci ta ji ana cire duvet din jikinta ta mike zaune a tsorace tana kallonsa kamar zata yi kuka don ya kunna dim light a dakin, yace "Nan wai wayo kika yi kika zo kika kwanta da wuri?" Sunkuyar da kanta tayi zuciyarta na bugawa bata ce masa komai ba, ya xauna gefenta ya jawota jikinsa a hankali, yayi kasa da murya yace "Kar ki manta you are my wife legally Khaleesat, why are you making everything seems hard for us both?" Kuka ta fara yi a hankali, yana magana kamar me rada yace "You just have to stay calm and relax plss, i promise i won't hurt you Khaleesat, the lube will help, jiya kin ki sakin jiki shi yasa bai yi ba" Khaleesat dai kukan tashin hankali kawai take bata ce masa komai ba tana kallon lube din da ya ajiye saman gado, kwantar da ita yayi taking off her nighty ya fara bi da ita gently kamar yanda yace, duk yanda Khaleesat ta saka ma ranta yau dai zata daure kawai tayi hakuri yayi abinda zai yi amma yana fara taɓata ta fara masa kuka da karfi tana turjewa, tsabar feelings dinta da yake ji yau duk bai ma san tana yi ba, banda lallabata da bata hakuri babu abinda yake yi yana bi da ita a hankali, don burinsa kawai yayi accomplishing mission dinsa yau ya maida ta mace, amma me? even with the help of so much lube hakan yayi seeming impossible, magiya ya dinga yi mata kamar zai mata kuka yake rokonta she should let him pls don gani yake kawai don taki sakin jiki ne, sosai yake rokonta as if his life depend on what he is trying to do, ita banda kukan azaba babu abinda take tana kokarin kwace kanta tana turasa da duk sauran karfinta, mari ya sauke mata a fusace ya shakota yana huci yace "Is all this among ur plan??" Kasa magana tayi saboda shaƙeta da yayi da karfi, ya wani turata har sai da ta fadi kasan dakin, yana huci ya sauka daga saman gadon ya nufeta yace "Ni xaki raina ma hankali? Ni zaki dinga dauka for granted?" Cikin kuka tana komawa baya ta dinga cewa "Don girman Allah kayi hakuri, wallahi bani bace Ya Abdul, nima ban san me yasa haka ba" Ya dagota da karfi yana kallonta da idanuwansa da suka yi jajir yana wani irin numfashi yace "Saboda kin saka a ranki baki son aurena baki son zama da ni shi yasa baza ki bani hakkina ba?" Jikinta na rawa ta dinga girgiza masa kai tace "Wallahi a'a, don girman Allah kayi hakuri...." Wurgata yayi da karfi har sai da ta buga da bango, ya juya ya fice daga dakin kamar zai tashi sama, ƙasa motsi Khaleesat tayi tana ganin duk dakin na juya mata, yana fita dakin da minti goma taji fitar motarsa a gidan, kuka Khaleesat ta dinga yi sosai ko ina na jikinta na mata ciwo a dakin, ta fi awa daya kwance inda ya wurgata, ji take kamar bazata iya tashi ba ga azaban da take ji a ƙasanta, da kyar ta rarrafa zuwa bandaki daga karshe, bayan ta gyara jikinta ta fito ta kwanta nan kasan dakin tana kuka a hankali ga wani azababben ciwo da kanta yake mata, tashi zaune tayi ta jingina da gado tana tunanin what exactly will be the problem, don ita ta riga tayi give up din Abdul a matsayin mijinta, ko dai tana da wani ciwo ne da bata sani ba a wajen, if not ko yanda yayi using lube din nan should have been enough, to ko ce masa zata yi su je asibiti don ya dena zargin hanasa take yi, bazata so Allah ya kamata da laifin hana mijinta kanta ba, hawaye masu zafi suka dinga sauka idonta, she wish zai bata listening ears ya saurareta yasan she is not doing this purposely, sai wajen karfe daya da rabi na dare taji shigowar motar Abdul, gabanta ya dinga faduwa tana kwance kasan dakin har taji alamar ya shiga dakinsa, mikewa tayi da kyar ta saka hijab dinta tana dingishi ta fita daga dakinta, tsaye tayi tana kallon kofar dakinsa gabanta na faduwa don bata san me zai ce zai mata ba idan ta shiga dakin, daga karshe tayi shahada ta bude a hankali ta shiga gabanta na faduwa, wanka taji alamar yake yi a bandaki, ta dinga kallon wrist watch dinsa da wayoyinsa da sauran ledan Prophylactic dake ajiye gefen gadon, sosai jikinta yayi sanyi ta dinga kallon prophylactic din, taji hawaye masu zafi na sauka idonta, bayan few seconds ta juya a hankali ta fita daga dakin, wasu sabbin hawaye na sauka idonta ta koma dakinta ta kwanta saman gado tana shesshekan kuka. [6/23, 2:54 PM] khaleesat Haiydar ✍️: Wajen karfe bakwai Khaleesat ta fito daga dakinta tana tafiya a hankali, duk da zazzabin da ta tashi da shi yau haka nan ta daure ta fito, tana hangosa kwance kan kujera yana danna wayarsa sai da gabanta ya fadi sosai, ta sauke kanta ta karasa har inda yake kwance ta durkusa cikin sanyin murya ta gaishesa, wayarsa kawai yake dannawa yaki kallon direction dinta balle ya amsa gaisuwarta fuskarsa a daure, bayan kusan minti daya ta mike jiki a sanyaye ta juya ta wuce kitchen, hawaye taji ya cika idonta ta kai hannu tana gogewa sannan ta fara preparing breakfast, bayan kusan minti arba'in ta fito daga kitchen din zata tambayesa ko ta kawo masa breakfast din yanxu duk da yanda gabanta ke faduwa, amma sai bata gansa a parlon ba, hakan yasa ta juya ta koma kitchen din ta dauko breakfast din ta kai dinning table ta ajiye, zata tafi dakinta kenan sai gashi ya fito daga nasa dakin har ya shirya alamar wanka yayi, tana kallonsa a hankali tace "Na gama preparing breakfast din" Banza yayi mata ya wuce ta, ta bi sa da kallo har ya shiga parlor, a sanyaye ta bude kofar dakinta ta shiga hawaye na taruwa idonta, ta zauna gefen gado tana goge hawayen a hankali, lamo tayi kan pillow tana shesshekan kuka, tunani iri iri ne ke mata yawo a rai, me ke faruwa da ita ne? Ko tana da wani ciwo ne da bata sani ba, who is she going to talk to about this? Hawaye taji na zubo mata sosai, how is she going to explain to Abdul that this isn't her fault? Ta yaya zata fahimtar da shi ya gane? Tafi awa daya kwance tana saƙe saƙe a ranta, a hankali ta mike zaune jin alamar fitar motarsa daga gidan, da kyar ta mike daga karshe ta tafi parlor tana tafiya a hankali, dinning area ta nufa ta duba taga bai taɓa komai ba a breakfast din da ta ajiye masa, ta juya a sanyaye ta koma parlor ta zauna ta jinginar da kanta da kujera hawaye na sauka idonta, after a while ta tashi da kyar ta fara gyara gidan sannan ta hada shayi ta dawo parlorn ta zauna amma ta kasa sha saboda damuwa, daga karshe kawai ta koma dakinta. Wajen karfe uku taji ya dawo gidan, ita dai tana ta zaune dakinta bata fita ba, bayan kusan minti biyar ya bude kofar dakin nata, kallo daya yayi mata yace "You have Visitors" Daga haka ya juya ya bar wajen, tayi jim tana tunanin su waye visitors din, mikewa tayi ta dau veil din Abayan dake jikinta ta rufe kanta sannan ta fito parlor tana tafiya a hankali, buda ido tayi ganin Aunty Farida da Nenne da step mothers dinta zaune a parlor, da gudu ta tafi ta fada kan Aunty Farida ta rungumeta cike da farin cikin ganinta, Nenne ta hade rai tana kara hakikancewa kan kujera tana kallon TV da aka kunna a parlon, Aunty Farida ta dago kan Khaleesat tana kallonta ganin yanda ta rame, a hankali tace "Ya kike Khaleesat?" Khaleesat ta sauke idonta cikin sanyin murya tace "Lafiya lau Aunty, Ummana fa? Me yasa baku zo da su Islam ba?" Aunty Farida tayi kasa da murya tace "Ke baki gaida su Nenne ba" Sai a sannan Khaleesat ta tuna da sauran mutanen parlon, zamowa ƙasa tayi a hankali tana kallon Nenne tace "Ina yini Nenne?" Nenne tace "Akan me zaki ce min ina wuni ni da nake er banza mara mutunci a idonki? Ita Faridar da kika makalewa kina shigewa jikinta da an biye ta tata da bata kashe auren nan har lahira ba? Da an biye ta Farida da Zahra'u idan kin ganki a wannan gida haka Allah ya tsine min albarka, to sai me don kin gan ni kin kauda kai kinyi kamar baki ganni ba da sauran matan ubanki? Ai babu komai" Khaleesat ta hade rai ta gaida su Mama Shatu dake zaune fuska duk babu walwala suka amsa mata babu yabo babu fallasa suna kare mata kallo, Nenne ta gyara zama cikin bacin rai tace "Banda matan ubanki da suka takura aje a san inda kike a ga halin da kike ciki sannan ni da na amshi sabon lambar Awdul wajen Farida nayi ta doka masa kira har yaje ya dauko mu ya kawo mu kin zata akwai wanda zaki gani a gidan nan ne? Ita farida Allah Allah take ta koma Legas ta ci gaba da tuwo tuwonta a can, uwarki kuma ba sanin ciwonki tayi ba balle ta samar mana hanyar zuwa ganin halin da kike ciki, amma me? haka nan albarkacin Ali nace dole dole sai naje naga halin da kike ciki, haka nan na uzura ma Awdul da kira yaje ya dauko mu, kuma Alhamdulillahi ga ki nan har wani haske kika kara alamar kina cikin kwanciyar hankali da zaman lafiya da mijin ki, to meye zaki yi kamar baki taɓa sanin mu ba daga abun arziki dai" Mama Zubaida tace "To ai sai a zaga damu cikin gidan mu sa albarka tunda Allah bai yi mu za mu kawo amarya ba" Nenne tace "A'a, ba bin kwakkwafi da tsegumi ya kawo mu ba kaman en iska, tunda dai yarinya na cikin kwanciyar hankali da zaman lafiya dama mu hakan ne kadai fatan mu, don haka babu me shiga mata ko ina a gidanta, in ma ce maku aka yi ku yi hakan don wata mugun manufa taku to baza ayi ba, don ni ban yarda da yanda ku ka dage sai an zo gidan Khaleesah ba tunda ni ba yarinya bace, dama kuma Ali yace ko minti sha biyar kar mu yi, da mun samu ganinta mu kamo hanya mu dawo tunda mu ba iyayen banza bane" Mikewa Khaleesat tayi ta tafi kitchen ta bude fridge ta dauko ruwa da drinks ta daura kan tray ta kai masu parlorn ta ajiye, ita dai Aunty Farida sai bin ta da kallo take don kana kallon fuskarta tasan akwai damuwa, gashi tana son kebewa suyi magana da ita amma tana gudun fitinar Nenne, Nenne na kallon Farida tace "Karfe nawa yanxu?" Farida tace "Uku da minti goma" Nenne na gyara mayafinta tana kallon Khaleesat tace "Toh kitchen za ki kai ni mu gana ko kuwa? in mun gama magana sai kije ki ce masa za mu koma ba zama muka zo yi masa ba" Aunty Farida ta dake ta mike tace "Kafin nan bari in ɗan yi magana da ita Nenne" Nenne ta kalleta da sauri tace "Ai ba kashe aure ya kawo mu ba Farida, in baza kiyi mata magana a gabanmu gaba daya ba to ki rike maganar ki kawai don ba alkhairi bane, haka kawai baza ki ja yarinya ki keɓe da ita ki kitsa mata tsiya da salon kashe aurenta ba" Aunty Farida ta dinga kallon Nenne, Nenne ta mike tana rike da babban jakarta tana kallon Khaleesat tace "Kai ni kitchen din" Khaleesat taji kamar tayi kuka bayan Nenne ta hana Aunty Farida tayi mata magana, rai babu dadi ta nufi kitchen Nenne na biye da ita a baya bayan ta jaddada ma farida a kunne kar ta bari su Mama Zubaida su shiga ko ina na gidan, su Mama Shatu da Mama Zubaida sai tabe baki suke, Nenne ta tura kofar kitchen din bayan sun shiga, tana kare ma kitchen din kallo tace "Maa sha Allahu kai kaji waje sai kace daki uku a hade, kuma iya girki kawai ake yi a nan?" Ita dai Khaleesat bata ce komai ba, Nenne ta zauna kasan tiles din kitchen din ta zuge jakarta tana kallon Khaleesat tace "To kin tsaya min kerere a kai" Dukawa Khaleesat tayi a gabanta tana kallonta, Nenne ta fito da wasu kulle kulle har ƙashi biyar, ta dinga kwancesu daya bayan daya cikin nutsuwa, murya can kasa tace "Kin ga wannan?" Khaleesat dai kallon kullin da Nenne ke nuna mata kawai take, Nenne na magana a hankali kamar tana tsoron wani ya ji tace "Cikin ruwan wanka zaki dinga diba kadan kadan kina zubawa kiyi wanka, duk wani mugun abu da mutum zai maki ko kuma yayi maki to da izinin Allah zai koma kansa da zuri'arsa, sharrin zai lalace na har abada, Wnn kuma a kunu zaki dinga zubawa ki sha kayanki ke kadai, wannan girki zaki dinga yi maku da shi gaba daya ku ci, ba wani mugun abu bane kawai saboda zaman lafiyanku da kwanciyar hankalin ku babu kuma ɗan iskan da zai iya shiga tsakaninki da mijin ki, sai ki ga kanku ya hadu kuna ma juna nutsattsen soyayya bakwa son laifin juna, wnn na hayaki ne shima duk wani mugun abu idan an maki zai karye ya koma kan me shi da izinin Allah, da kyar aka tsam min wallahi, kin dai gansa ɗan mitsitsi ko Ali ban dibar ma ba tunda naga bashi da yawa na kawo maki ba don halin ki ba, wannan na karshen shi kuma na sha ne da wanka, in kinyi wankan sai ki kada shi ko cikin ruwan shayi ne ki dinga shan abun ki" Ita dai Khaleesat tayi shiru tana ta kallon abubuwan da Nenne ke mata bayaninsu sinka sinka cikin nutsuwa, Nenne ta gyara zama fuskarta a daure tace "Wallahi in kika sa nayi asaran lokacina da en kudadena kika ki amfani da wannan abubuwan da na shiga kauyuka takanas na samo maki to in na maki Allah ya isa sai ya bi ki tunda ni ba baiwar buzuwar uwarki bace, duk ita ya kamata ta maki wannan abun amma gantalalliyar bazata yi ba, dama kuma sari nasan ke da ita bakwa amfani da duk wani abun taimako da nake baku, wani lkcn matsalarku ce ma ke shafan ɗa na yayi ta wahala a duniya, to wannan in ma kinki yi wallahi kanki kika cuta don dangin Awdul ba mutanen arziki bane duk mun sani, kuma ba lallai su barki ki zauna lafiya a gidan mijin ki ba barin yanda suka dau ƙaran tsana suka dora ma ubanki saboda shi talaka ne, to ni dai gashi nan albarkacin ubanki na maki wannan wahala, haka nan na shiga wani kauye duk mayu na fito da kyar, to ya rage naki kiyi ko kar ki yi, in ma baki yi ba Allah ya isa" Khaleesat dake kallonta tace "Toh in ya gan su sai in gaya masa na menene su?" Nenne ta saki baki tana kallonta, a fusace tace "Ke dai sokuwa ce mahaukaciya, to uban wa yace maki a gabansa za ki yi? Yau naga bala'i, wannan wace irin shashashar yarinya ce? dama ba sai ya fita ba zaki yi maza kiyi duk abinda zaki yi kafin ya dawo? Ni da ban yi boko ba ma nafi ki hankali da wayo? wannan wace irin jaraba ce Zahra'u ta haifar ma Ali? To ki kwasa ki nuna masa tunda baki da seti" Khaleesat ta wani hade rai ta kauda kai, Nenne tayi kasa da murya tace "Ae sai ya fita duk zaki yi komai cikin sirri, yanxu boyewa zaki yi inda ko da wasa bazae gani ba" Khaleesat tace "Toh ae zae ji warin hayakin kuma, sannan ni bama ni da abun yin turaren wutan ai" Nenne tace "To dama ai shegen a gantale ya dauko ki bai bari duk mun shirya maki turaren wuta ba da sauran abubuwan da ake kai mata da su gidan miji, yanxu dai nasan shi zai maida mu gida ina da manyan robobin turaren wuta har biyu da na ajiye maki zan basa turaren da kasko ince ya tsaya gun masu siyar da gawayi a bakin hanya ya siya maki ko leda uku ne ya taho maki da shi, sai ki dinga hurawa a kaskon tunda ga AC a parlon nan da nan zai kama maki in kika hura" Khaleesat bata san sanda tayi dariya ba, Nenne tace "To shikenan ki maida ni mahaukaciya ina kokarin taimakon rayuwarki" Khaleesat tace "Na ji" Nenne tace "Yauwa to, yanxu gasu nan maza ki je ki boye inda bazai gan su ba kwata kwata" Khaleesat ta amsa ta nemi waje a nan kitchen din ta boye, Nenne tace "Yauwa to haka ake yi, yanxu maza tafi ki ce masa zamu tafi kar ya ga mun zaune masa a gida, dama ni wnn abubuwan yasa nayi ta doka masa kira yau kwana uku kenan, har Allah yayi ya zo ya dauke mu" Mikewa Khaleesat tayi ta fita daga kitchen din Nenne na biye da ita murya can kasa tace "Ko ruwan gidansa mu dai bamu sha ba balle yace" Khaleesat na tafiya a hankali ta nufi dakin Abdul, knocking tayi tana jiran ya amsa, after almost a minute ya bude kofar, ta sunkuyar da kanta tace "Za su tafi" juyawa yayi ya koma dakinsa, hakan yasa ta dawo parlor, Nenne na kallonta tace "Kin gaya masa?" Kai ta gyada mata ta tafi kusa da Aunty Farida ta zauna a kasa, Su Mama Shatu kana ganin fuskokinsu kaga bakin ciki da hasadda karara a kwance, bayan kusan minti biyar Abdul ya fito daga dakinsa yana murmushi yace "Har za ku koma Kaka?" Nenne tace "Wallahi kuwa Awdul, ai dama ba zama za mu yi ba, ni dai nayi farin cikin ganin jikata cikin kwanciyar hankali dama duk haka muke so" Shi dai bai ce komai ba, Nenne ta mike tace "Don haka yanxu sai ka maida mu gida kawai" Abdul yace "Toh naga ko abinci bata baku ba ai" Nenne tace "A'a mu muka hanata don duk a koshe mu ke, ruwan ma in ka lura ai bamu sha ba" Shi dai murmushi kawai yayi, a haka Nenne ta kada keyarsu Mama Zubaida da Mama Shatu suka fita daga parlon, Ita dai Khaleesat na biye da su duk jikinta a sanyaye, Aunty Farida ce last din fita a parlorn, tana kallon Khaleesat tayi kasa da murya tace "Za ki ga sako na ajiye maki bayan throw pillow din kujeran da na zauna, kar ki damu kafin in koma lagos zan samu lokaci in zo ni kadai kin ji?" Kai kawai Khaleesat ta gyada mata, Bayan Abdul ya bude motarsa ya kalli Khaleesat da duk jikinta yayi sanyi ganin su Aunty Farida za su tafi, yace "Mu je sai mu yi dropping din su mu dawo" Nenne dake kokarin shiga bayan mota ta dakata tace "Toh ai babu waje a motar, a ina zaka dora ta Awdul?" Aunty Farida tace "Sai ta shiga gaban motar Nenne ni in koma baya" Nenne tace "A'a babu ruwana wallahi, a irin narka narkan jiki na Shatu da Zubaida mu uku ma ya muka kare a baya balle kin shigo cikinmu Farida? Ko dai a cinyar su zasu dora ki?" Shi dai Abdul murmushi kawai yayi, Khaleesat tace "Toh ni sai in zauna a bayan" A fusace Nenne tace "To ke dole sai kin bi mu ne kamar en matan amare? Kawai don na zo gidanki sai in koma gida da ciwon jiki? ni wallahi in da matsi a mota ma bana shiga, da mun sani da bamu taho da Zubaida ba don duk ita ta cika waje..." Abdul ya kalli Khaleesat yace "Don't worry, ki koma ciki kawai" Hawaye ne ya cika idonta tana kallonsa, Aunty Farida ta yi ma Nenne wani kallo ta shige gaban motar, Nenne ta kyabe baki ta shiga bayan motar tana hararansu Zubaida da su ma duk suka shiga motar kuma babu warce tayi gigin gogan jikin Nenne a cikin motar, Nenne tace "To duk ku sauka Khaleesah ta fara shigowa ta dawo kusa da ni tunda ba wani auki gareta ba, ku ne abun tsoron dama" Babu musu duk suka sake sauka daga motar suka koma gefe, Nenne na kallon Khaleesat tace "Ba sai kin yi kuka ba, shigo ki matso kusa da ni mu ga adadin wajen da zai rage, in ya kama wata sai ta hau adaidaita sahu" Khaleesat ta goge idonta ta karasa ta shiga cikin motar ta matsa kusa da Nenne, space din da ya rage a motar tsaf zai dauke su Mama Zubaida, Nenne ta tabe baki tayi kasa da murya tace "Duk fa wari suke, in Farida ta shigo nan ai jikina za su rakube in ta shakan wari su cuce ni, in de ba kusa dani Faridan zata dawo ba, kuma Zubaida duk ta fi warin, banda akwai turare da AC a motarsa ai da mun ji kunya" Ita dai Khaleesat bata ce komai ba su Mama Zubaida suka shigo motar Nenne na yatsine yatsine, a haka suka bar gidan. Sai kusan karfe biyar suka isa Mariri, bayan Abdul yayi parking dai dai kofar gidansu Khaleesat Nenne ta bude motar ta sauka tare da Khaleesat, su Mama Zubaida ma duk suka sauka da Aunty Farida suna ma Abdul godiya sannan suka shiga cikin gida, Nenne na gyara gyalenta tace "To Allah yayi maka albarka Awdul mun gode, amma dai zan yi maza in karasa gida akwai sakon Khaleesat da zan dauko in bata tunda Allah ya kawo ku ta tafi da kayanta kawai" Yana zaune driver seat ba tare da ya juya ba yace "Toh Kaka" Tana kallon Khaleesat tace "Mu je ki taho da sakon" Khaleesat bata ce komai ba ta fara bin Nenne zuwa gidanta, bayan sun yi nisa Nenne tace "Ai kinga shegen bai ce bari ya karasa gidan nawa da mu a motar ba, gaba daya baya ganin mutuncin gidana dama" Ita dai Khaleesat tayi kamar bata ji me tace ba, har suka isa gidan Nenne Khaleesat na gaisawa da mutanen anguwan, Nenne tace "Munafukai, sun yi mamakin ganin ki haka ai, kinsan duk ca aka yi kin shiga duniya kin gudu, sai daga baya kuma aka ji kina gidan mijin ki" Murmushi kawai Khaleesat tayi, bayan sun shiga gidan Nenne ta dauko turaren wutan ta saka su a katon leda da kasko biyu sannan suka fito, suna isa kofar gidansu Khaleesat Nenne ta saka ledan a bayan motar Abdul tana cewa "Kaga har mun dawo Awdul, dama turaren wutan ne ba wani abu ba, don haka ku yi maza ku tafi kar Magariba ya tarar da ku a hanya" Yace "To Kaka" Khaleesat na kallonsa tace "Zan shiga in gaida Ummata" Bata jira cewarsa ba ta shiga cikin gidansu ya bi ta da kallo, ko minti uku bata yi da shiga dakin Ummanta ba sai ga Nenne, tana tsaye bakin kofar dakin bayan ta dage labule tace "Abun kuma ba hauka bane ai, taso ki fita yana jiran ki..." Khaleesat ta daga kai tana kallon Nenne, Nenne tace "Ae sai yayi mana kallon mutanen banza marasu hankali, taso nace ki fita kar ki ja mana reni" Umma na kallon Khaleesat tace "Ku je Khaleesat, kin ga yamma tayi" Fuska a daure Khaleesat ta mike ta fita daga dakin, Nenne ta rakata har bakin motar Abdul, tana shiga gaban motar yayi ma Nenne sallama ya ja motarsa ya bar wajen, har suka isa gida ana kiraye kirayen magrib bai ce mata ba, ita ma bata ce masa komai ba, bayan yayi parking ya sauka motar ita ma ta sauka, tana tafiya a hankali ta bi bayansa suka shiga gidan, Kitchen ya shiga direct, har zata wuce dakinta ta tuna sakon da Aunty Farida tace ta bar mata kan kujera, ta karasa inda Aunty Farida ta zauna ta dauke throw pillow din wajen ta dinga kallon Dollars din dake ajiye da wayoyi biyu, daukan 1000 dollars din tayi wanda Jay ne ya bata da zata dawo Nigeria, ta dau wayoyin biyu, daya na Ajay daya na Jay, lkci daya jikinta yayi sanyi hawaye suka cika idonta, muryar Abdul taji a kanta yace "What's that?" Da sauri ta boye hannunta a baya tana kallonsa tsabar yanda ta gigice. [6/24, 6:29 PM] khaleesat Haiydar ✍️: Abdul ya zagayowa ya tsaya gabanta yana kallonta ya mika mata hannu yace "Give me what you are hiding" Sosai gabanta ya fadi tana kallonsa ta kasa cewa komai, tsawan da ya gigitata ya daka mata yana mata wani kallo, lkci daya hawaye ya cika idonta ta mika masa wayoyin da kudin hannunta, amsan su yayi yana kallon su, ta sunkuyar da kanta zuciyarta na bugawa, Calmly yace "Who gave you this?" Kasa dago kanta tayi hawaye na zuba idonta tana jiran jin saukan mari at anytime, juyawa yayi ya bar wajen ya nufi dakinsa yana rike da wayar da dollars din, Khaleesat ta bi sa da kallo har ya shiga dakin, taji kafafuwanta sun kasa daukanta tsabar yanda ta tsorata, da kyar ta karasa ta zauna gefen kujera tana jin bugun zuciyarta na karuwa, tana goge hawayen dake sauka idonta.... Abdul na shiga dakinsa ya zauna gefen gado ya ajiye dollars din yana jujjuya wayoyin hannunsa ganin iri daya ne with different colors, kuma duk a mace suke babu caji, Exactly irin second phone din da yake using ne, ya mike ya tafi yayi plugging din wayar Jay da chargern sa, sannan ya koma ya dau kudaden ya kiraga yaga 1k dollar ne, ya ajiye su saman gadon yana kallonsu, jin za a tada sallah a masallaci ya shiga bathroom dinsa, bayan ya fito zai tafi masallaci ya kulle Bedroom din nasa da makulli, har sannan Khaleesat na zaune parlor ta kasa motsi a inda take zaune, tana ganinsa ta mike tsaye a tsorace tana kallonsa, ko kallonta bai yi ba ya nufi kofa ya fita daga parlon, a sanyaye ta tafi dakinta hawaye na sauka idonta zata je tayi alwala ita ma. Abdul na dawowa masallaci bayan ya bude dakinsa ya shiga ya dau wayar Jay ganin har yayi caji ya kunna kansa, ya cire wayar jikin chargern ya dauko wayar Ajay ya jona, sannan ya koma gefen gado yana duba wayar tunda babu lock jiki, gani yayi ba Sim card a wayar, ya dai ci gaba da dube dubensa, babu inda bai shiga ba a cikin wayar yana bincike but bai ga komai ba don babu any form of Media a wayar, messages ma ko daya bai gani ba, bayan ya shiga Email yaga Business class flight ticket da Jay ya siya mata da zata dawo Nigeria, ya dinga kallon Ticket din for almost 30 seconds, sosai fa yayi mamaki ba kadan ba, fita yayi daga Email din ya shiga Gallery din wayar hoping zai samu hoto a ciki, a nan ne ya ga Hotunan Jay, wanda duk yawanci tare zaka gansu da Ajay, Zooming pic din Jay yayi yana kallonsa with full concentration, sai kuma ya koma kan Ajay shi ma ya dinga kallonsa baya ko kiftawa, at once ya gane da shi ne suka samu Encounter a Amurka, but sai ya ga Ajay looks familiar, where did he know him from? mikewa yayi da sauri ya dauko wayarsa ya shiga Instagram dinsa yayi Searching sunan da yake tunanin ya san sa da shi a Instagram, amma sai yaga account dinsa is locked, komawa yayi ya zauna ya kasa dena kallon hoton Ajay babu ko kiftawa, can ya kara duba hoton Jay yayi Zooming dinsa yana kallo, kawai bai san me yasa yaji yafi jin tsanar Jay ma akan Ajay, mikewa yayi ya dauko wayar Ajay don har ya ɗan yi caji, babu lock a wayar hakan ya sa ya shiga, nan yaga Ticket da aka siya mata from Kano to Lagos, iya shi kadai ya gani a wayar babu hotuna, babu WhatsApp, babu komai, hatta sim card babu a wayar, fita yayi daga dakinsa ya tafi dakin Khaleesat ya sameta tana sallah, tun da taga yanda ya tsaya mata a bakin kofa taki idar da sallan da take yi da wuri kamar me Tuhajjud, muryarsa taji cikin tsawa yace "Idan baki sallame sallan nan da kike yi continuously ba zaki ga abinda zai faru yanxu" Sosai jikinta yayi sanyi, haka nan ta daure ta sallame sallan tana ji kamar bango ya tsage ta fice daga dakin tsabar tsoronsa, duk da yanda gabanta ke faduwa haka ta hade rai taki kallon direction dinsa barin da ta ga both wayar Jay da Ajay a hannunsa, ya karaso cikin dakin yana mata wani kallo cikin daga murya yace "Wayoyin su wanene wannan??" Still taki kallonsa, wani tsawa yayi mata yace "Are you stupid? Are you Mad? Ina maki magana kina kallon wani direction din daban?" Sai a sannan ta kallesa, har sannan fuskarta a daure yak, amma Allah ya gani daurewa kawai take, yace "I am asking you whose phones are this?" A takaice tace "My Housemate and his Brother....." Ya dinga kallonta babu ko kiftawa, she just realized she said her Housemate to him, ta kallesa a sanyaye, ganin kallonta yake yi baya ko kiftawa, ta sauke idonta a hankali tace "I mean...." Ya girgiza kai yace "No, you mean ur Housemate, dama Housemate dinki ne ranan da na je kika min karya? Dama gida daya ku ke tare da wannan katon banzan da na gani?" Gani tayi shiru fa ba nata bane, don shirun nata duka kawai zai ja mata, in ma maganar tayi ba hakan zai hana ya doketa ba in yayi niyya, ta wani hade rai duk da mugun faduwan da gabanta ke yi, a takaice tace "Eh, he is my Housemate, Nancy moved out of the apartment shi ne shi ya shigo, and i have no choice but to live with him, tunda bana son in dinga bothering dinka da Expenses, kuma naga in just few months za mu yi hutu, dama nufina idan mun yi hutu sai in ce maka ka canza min wani apartment din since a sannan ne zaka yi renewing house rent dina" Kallonta kawai Abdul yake yi babu ko kiftawa, ita dai ta kasa kallonsa gabanta na faduwa tana expecting ta ji saukan mari at anytime a cheek dinta, Calmly yace "So, shi ne kike zaune gida daya da shi ku ke rayuwa, ku yi sharing same kitchen, same parlor and same corridor, if coincidentally kin fito daki shi ma ya fito sai ku kusa karo da juna ko? Ki fito babu hijab ya gan ki haka, ki fesa turare ki zo ki wucesa yana jin kamshi, in ma ya kama ki zauna ku yi hira da shi, in kinyi girki ya diba ya ci" Sai a sannan Khaleesat ta kallesa tace "I don't mind if you believe me or not... But shi baya kwana gidan, karatu kawai yake zuwa yi ya tafi don suna da gidansu a Amurka" Abdul ya dinga kallonta, sai a sannan ya tuna abubuwa masu tsadan da ya dinga gani a kitchen sanda yaje, tun daga kan bottle water, cikin nutsuwa yace "Shi ne dalilin da ya sa kika fara min wasu stupid attitude kenan? Kin samu wanda yake siya maki duk abinda kike so a gidan har ma ya ɗebe maki kewa, To bari ki ji, ko duk jikina kunnuwa ne bazan taɓa yarda babu wani intimacy da ya hada ki da shi, ke kika san me kike basa da yasa yake siya maki abubuwa masu tsada yake ajiye maki a kitchen, sannan har ya cire kusan 5000 dollars ya siya maki Business class ticket kawai don ki dawo Nigeria...." Nan da nan hawaye ya cika idon Khaleesat, ta mike tsaye tana kallonsa tace "Ko me zaka fada bazan ce maka ba haka bane, amma put this at the back of ur mind, ba kowa ke da halin son taɓa warce ba muharramarsa ba kamar ka, kuma shi bai dau kudin Business class ticket wata tsiya ba shi yasa ya siya min, akwai difference sosai between you and him" Kallonta Abdul ya dinga yi da mugun mamaki, bata ankara ba sai jin saukan tagwayen mari tayi a fuskarta, ta fashe da kuka tace "Iya mari kawai?? ka kasheni mana ka huta kawai Abdul...." Ya fizgota da karfi yana huci yana kallonta da idanuwansa da suka yi jajir yace "Ni kike comparing da wani ɗan iska matsiyaci can??" Cikin kuka tace "May be if i do that you will change ur terrible ways, he made me realize i am dating a monster because of his kind attitude toward me, babu komai tsakanina da shi amma shi din mutum ne me kirki da sanin darajan ɗan Adam da sanin ya kamata, he always make sure i am fine, baya barina da damuwa komin kankantar sa, kuma ko da kuskure bai taɓa saɓa min ba a duk zaman mu da shi a America, kyawawan halayyarsa da irin yanda yake interacting yasa naji i am fed up with ur attitude, all this made me realize you are enslaving me ba sona kake ba, why not treat me the way he is treating me idan har sona kake da gaske? Bani da daraja da mutunci a idon ka, kullum cikin duka da cin mutunci nake a wajenka tun sanda baka aureni ba, iyayena ma basu da mutunci a wajen ka, to menene yasa baza kayi releasing dina zuwa inda za a ga mutuncina da na iyayena ba kuma a san darajata? Is it my father's fault da kaddarar sa ta zo a yanda take? Ku kan ku kun san bai ci kudin mahaifinka ba, bai salwantar masa da kayansa don son rai ba, ba ku tunanin ko ba ta sanadin mahaifina ba sai kun yi asaran kudaden nan tunda ku ma a kaddarar ku hakan take? Kuma meye zaka daga min hankali a kan su bayan kace baza ka sakeni ba kuma kowa yasan igiyar auren nan a hannun ka yake? Duk cikin rashin lissafin naka ne yasa kake kishi da su bayan ka ri ga ka aureni??" Turata yayi har sai da ta bugu sosai da bango sannan ya juya ya fice daga dakin kamar zai tashi sama. Wajen karfe dayan dare Khaleesat dake kwance taji an bude kofar dakinta, da kyar ta bude idonta da yayi mata nauyi tsabar kuka da ciwon kai, tana ta kwance a yanda take bata juya ba duk da bata ga ya kunna wutan dakin ba, duvet din jikinta ya sauke kasa ya jawota kusa da shi yayi kasa da murya yace "Kinsan da igiyata a kanki kike da effrontery din kawo min maganar wani katon banza can har kike comparing dinsa da ni? What wrong have i commit to you da kike ganin shi yana da halayya masu kyau wanda ni bani da shi" Khaleesat taji zuciyarta na mata wani zafi jin useless question din da yake tambayarta, tayi kamar bacci take taki motsawa, yayi kasa da murya yace "Khaleesat..." Still tayi kamar bata jin sa, duk da idonta a rufe yake she could feel the tears accumulating in her eyes, kiranta ya sake yi a hankali jin bata amsa masa ba ya juyota zuwa jikinsa yana kallonta cikin duhun, ya dora goshinsa kan nata yayi kasa da murya yace "But you know i love you so much Khaleesat, da bana son ki bazan yi wasting shekaru kusan biyar a kanki ba, i gave you the best of everything i can kema kin sani" Bata san sanda ta turasa ba tsabar wani tsanarsa da take ji a rai jin abinda yake cewa, ta mike zaune muryarta na rawa tace "Duk saboda kana sona kake dukana kake marina kamar jaka? Shi ma duk cikin so ne? Plss ka koma ka fahimci menene kalmar so...." Sauka ta fara kokarin yi daga kan gadon tana shesshekan kuka, ya rikota da sauri yaki barinta ta sauka, ta fashe da matsanancin kuka sosai tana jin zuciyarta na mata zafi saboda bakin ciki, ya rungumeta gam a jikinsa, a hankali yace "Kiyi hakuri, amma Allah ya sani ina son ki, in ma baki yarda ba i owe you no explanation tunda Allah shi ya sani, kuma today should be ur first and last warning Khaleesat.... I mean in ur life do not ever ever dare compare me with any stupid guy born of a woman, kar ki sake kawo min zancen wani ɗan iska ko shi wanene a kunne na, sannan bazan yi taking zaman da ku ka yi tare da shi and whosoever da kuma alakar ku personal ba because you are my wife now, duk wannan ya zama pass and shi ne looser, kuma har abada babu wata alaƙa da zai sake hada ki da shi don ubansa har duniya ta nade kuwa, ba wai ban ji zafin alakar da kika yi creating da su a America bane a raina, fadin zafin da naji ma is just an understatement wallahi, amma considering the fact that you are my wife yasa nayi letting bygone to be bygone, so let me keep using that to calm my self kar in masu abinda ke raina...." Wani mugun tsanarsa ne ke karuwa a ran Khaleesat jin kalmomin da ke fitowa bakinsa, wasu hawaye masu zafi suka dinga sauka idonta tana tausayin kanta da irin monster din da Allah ya bata as miji, kokarin kwace kanta take yi a jikinsa zata sauka daga kan gadon yaki saketa yace "Ohk bokare min za kiyi don ina baki hakuri? But i said i am sorry, and i promise i won't hurt you again, na dena dukan ki...." Ƙin ce masa komai tayi tana kuka a hankali, ya kwantar da ita kirjinsa yana shafa gashinta a hankali yace "Billah ina son ki Khaleesat, duk abinda kika ga ina maki saboda ina son ki ne, but kin ki bani hakkina saboda ke akwai wani plan din a xuciyarki, probably ma su suka koya maki haka" Daga kai Khaleesat tayi ta kallesa tsabar bakin ciki bata san sanda tace "Ai ba kowa ne bashi da aikin yi kamar ka ba" Shiru yayi yana kallonta babu ko kiftawa, ita kanta shirun tayi gabanta na faduwa don bata san sanda kalman ya fito bakinta ba, Instead sai ji tayi yayi kasa da murya kamar me rada yace "Where is the Lubricant?" Sosai gabanta ya fadi jin abinda yace, yana rungume da ita jikinsa ya bude bedside drawer kamar yasan nan din ta ajiye kuwa, ya laluba ya dauko, shesshekan kuka ta fara yi zuciyarta na bugawa, yayi kasa da murya yace "Kinsan tsinuwar Allah kike tara ma kanki kuwa?" Cikin kuka tace "To ai ba ni bace" Yace "To waye?" Muryarta na rawa tace "Wallahi ban sani ba" Cikin kwantar da murya yace "Promise me today will be different plss Baby" Ta kasa cewa komai hawaye masu zafi na sauka idonta ga faduwan da gabanta yake yi, gently ya fara cire kayan baccin jikinta yana kallon kwayar idonta cikin duhun dakin, a wannan dare Abdul bai yi bacci ba tsabar bacin rai, sai dai bai hantareta ba bai zageta ba, bai kuma doketa ba, haka ya mike ya fice kawai ya bar mata dakinta ya koma nasa, ya shiga bandaki ya sakar ma kansa ruwan sanyi duk da mugun sanyin da ake a garin, bayan ya fito ya saka Pajamas dinsa ya kunna karatun qur'ani a wayarsa ya kwanta amma ko rintsawa bai yi ba har asuba. Tunda Khaleesat ta idar da sallan asuba take zaune kan darduma bayan ta gama azkar dinta, gaba daya jikinta a sanyaye yake, zuwa yanxu kam sosai lamarin nan ya fara bata tsoro, ko baccin kirki bata yi ba daren jiya tsabar yanda abun ya tsaya mata a rai, kawai tayi deciding tayi amfani da abubuwan da Nenne ta kawo mata zuwa anjima, sai da gari ya waye sosai sannan ta mike tana tafiya a hankali ta fita daga dakin zuwa parlor, sosai gabanta ya fadi ganinsa zaune a parlon da cup din shayi a gabansa, ta sunkuyar da kanta zuciyarta na bugawa ta tafi ta durkusa ɗan nesa da shi a hankali tace "Ina kwana" Maimakon ya amsa sai ji tayi yace "Meye nake perceiving a cikin kitchen kamar maganin gargajiya?" Khaleesat ta daga kai ta kallesa, shi ma kallonta yake fuskarsa babu yabo babu fallasa, rasa me zata ce masa tayi tana wasa da fingers dinta, a fusace yace "Bakya ji na ne?" Bakinta na rawa da kyar tace "Nenne ce ta kawo min" A takaice yace "Na menene?" Ta sauke idonta tace "Magani ne kawai, dama ta saba bani in dinga amfani da shi a gida" Mikewa yayi yace "Mu je ki bani su" Ta shi tayi kamar munafuka ta nufi kitchen din ya bi bayanta, ita kanta taji kamshin itatuwan da ta shiga kitchen din, ta bude inda ta ajiyesu ta dauko, ya mika hannu, ta karasa ta basa, yace "Ba a min amfani da irin wa ennan abubuwan a gida" Kai kawai ta gyada masa, fuska daure yace "Kin ji me nace maki? Kar ki sake amsa idan ta baki" A hankali tace "Na ji" Juyawa yayi ya fice daga kitchen din ya koma parlor ya zauna, ya ajiyesu nan kasan tiles, tana fitowa daga kitchen yace "Get ready za mu fita, kuma kar ki bata min lokaci" Cikin sanyin murya tace "Toh" Dakinta ta tafi, bayan kusan minti talatin sai ga ta ta fito cikin shiri, dai dai nan shi ma ya fito daga dakinsa rike da wayarsa da car key, yana gaba tana biye da shi suka shigo parlor, ya dau ledan magungunan da Nenne ta kawo mata ya nufi kofar fita daga parlon ita dai tana biye da shi a baya, a booth dinsa ya saka ledan magungunan, sannan ya zaga zuwa driver seat, ita ma ta shiga front seat, bayan ya gama warming motar ya fita daga gidan. A sanyaye Khaleesat ta fito daga Office din Dr Mariya with different thoughts running her mind, ta ɗan juya ta kalli Abdul da ke bayanta shi ma ya fito office din likitan, ƙin kallonta yayi, hakan ya sa ta ci gaba da tafiyarta slowly, sai ga Dr Mariya ita ma ta fito daga Office din zata masu rakiya zuwa parking space, hira suke yi kawai da Abdul suna tafiya a tare, ita dai Khaleesat na can gabansu, har dai suka fita daga reception din hospital din suka karasa parking space, Dr Mariya na kallonta tana murmushi tace "To amarya plss inji labari opposite of this kin ji? There is nothing wrong with you, In kinyi amfani da duk shawararin da na baki komai zai tafi dai dai in sha Allahu, hakuri kawai za ki yi it's always like that dama, Allah Ubangiji ya bada zaman lafiya, in dai na samu lokaci zan zo har gida mu gaisa" a hankali Khaleesat tace "To Nagode Aunty, Allah ya kawo ki lafiya" Dr Mariya na murmushi tace "Ameen" Sai kuma ta kalli Abdul tace "To Barrister ku gaida gida, ina kuma tabbatar maka in sha Allah matsalar ta zo karshe tunda kaga mun dade ina magana da ita, kuma hopefully ta dau duk abinda nace mata" Yace "Thanks for your time Dr" Zagawa yayi ya shiga driver seat, Khaleesat kuma ta shiga front seat, ya tada motar suka bar hospital din, har suka yi nisa bai ce mata komai ba, ita ma dae shiru tayi tana ta tunane tunane, sae da taga unguwan da suka shigo tayi realizing gidansu ya kawosu, bayan yayi parking ya sauka motar, ita ma ta sauka, booth ya tafi ya bude ya ciro ledan da Nenne ta kawo mata, da mamaki tana kallonsa tace "Ina zaka kai wannan?" A takaice yace "Momy zan kai ma, naga tana dealing da irin abubuwan nan, she can use it if she want, ke dai baza kiyi amfani da su ba a gidana" Khaleesat ta marairaice masa tace "Noo pls, ni dai gwara kayi disposing dinsu don Allah" Fuska daure yace "Bazan yi disposing din su ba" Bata san dama haushinta ne fal zuciyarsa ba bayan Dr Mariya ta dubata ta tabbatar masa lafiyarta qlau babu wani abu da yake hindering passage dinsa, everything is normal, kawai hadin kai taki basa, Khaleesat ta sunkuyar da kai a sanyaye bata sake cewa komai ba, ya nufi entrance din gidan nasu, tana tafiya a hankali ta bi bayansa har suka shiga parlorn gidan, da mamaki Momy ke kallonsu tace "A'a, daga ina ku ke da safen nan, sannun ku da zuwa" Abdul ya zauna ya gaisheta, ta amsa tana kallon Khaleesat da ta zauna kasan carpet tana gaisheta, Momy ta amsa da fara'a sosai fuskarta tana welcoming dinta, Momy na kallon Abdul tace "Amma ba daga gida ku ke ba ko" Yace "Eh, daga asibiti mu ke" Da mamaki Momy tace "Asibiti kuma, waye ba lafiya?" A takaice yace "Bata ji dadi bane, amma da sauki" Momy na kallon Khaleesat tana murmushin karfin hali tace "Allah sarki, sannu Mamana, Allah ya kara lafiya" Sai kuma ta kalli Abdul tace "Ko wajen Dr Mariya ku ka je?" Yace "Eh" Mikewa yayi ya ajiye mata ledan magungunan kusa da ita yace "Kakarta ce ta kawo mata wnn jiya, ni kuma kin san bana son irin abubuwan nan na gargajiya shi ne na kawo ko zaki yi amfani da su ke" Momy tayi kuri da ido tana kallon ledan da mamaki, sai kuma ta dauka ta bude da sauri, lkci daya ta saita kanta tana murmushin karfin hali tace "Allah sarki, ai kam nasan halin ka baka san itatuwa, zan ko yi amfani da su dama nawa sun kare tas" Ita dai Khaleesat kasa dago kanta tayi, Momy was shock har cikin ranta amma tayi karfin hali take wayancewa, can ta kalli Khaleesat tace "Amma baki fara amfani da su ba ko" Khaleesat ta girgiza kai ba tare da ta kalli Momy ba tace "A'a jiya ta kawo min banyi amfani da komai ba" Momy tace "To to, hakan yayi" Ta kalli Abdul tace "In dai an samu wasu a dinga kawo min kawai" Mikewa yayi yace "Za mu koma Momy" Momy tace "Da wuri haka? To wai ka koma aiki ne?" Yace "Ban koma ba tukun" Momy tace "Toh shikenan, Allah ya tsare nima in sha Allahu ina nan shigowa in kawo mata turarrukan wuta da na jiki" Shi dai bai ce komai ba ya nufi kofa, Khaleesat ta mike tana yi ma Momy sallama, Momy duk fa a rude take ta gyada mata kai kamar kadangariya tace "To Mamata, sai na shigo, ku gaida gida, maza bi sa ku tafi" Daga haka Khaleesat ta bi bayan Abdul da har ya fita daga parlon, Momy ta dau wayarta har tana tuntube ta shiga dakin dake downstairs ta fara kiran Dr Mariya don family Dr dinsu ce for long, Dr Mariya na dagawa suka gaisa da Momy cikin fara'a, Momy tace "Yanxu Abdul ya zo min da matarsa yace daga asibiti suke, naga duk ba shi da walwala nasan yana da zurfin ciki bazai gaya min ko menene ba, shi ne na kira inji lafiya dai ko Dr? Ko juna biyu gareta? kinsan dama yace bai son haihuwa da wuri, in dai juna biyu ne da ita gwara in yi dubara in dawo da ita wajena don ni dai ina son ganin jikana, kar yaje ya bata wani abu da zai lalata cikin taje ta sha" Dr Mariya tayi dariya sosai, bata boye ma Momy komai ba tayi mata bayanin dalilin zuwansu Asibiti, Momy ta sauke wani irin ajiyar zuciya ba tare da tasan tayi hakan ba, sai kuma ta bige da cewa "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, kinsan yarinya ce fa, duka duka Allah yasa tayi shekara ashirin, har da yarinta abun nata dae" Dr Mariya tace "Wallahi nima haka nace masa don dae in kwantar masa da hankali kar ya dinga jin haushinta, amma shekara ashirin ai ba yarinya bace Hajiya, aka ma er shekara sha biyar aure ta zauna balle er shekara ashirin, ni dai na bata shawarwari Allah ya sa tayi amfani da shi, kar tun yana hakuri da ita hakurinsa ya kare a fara samun matsala gaskiya" Murmushi kawai Momy take tana Allah Allah su gama waya da Mariya ta kira Godiya, daga karshe Momy tace "To Allah ya sa ta dau shawaran naki Dr, kuma zan yi ma yayarsa magana ita ma taje gidan anjima ta kara nutsar da ita in sha Allahu" A haka Momy suka yi sallama da likitan, Momy tayi wani dariya tana girgiza kai sannan ta fara dialing number Godiya, aikin miliyan biyu ai ba wasa bane, sun dade suna waya da Godiya a waya, daga bisanni suka yi sallama, Momy na ta murmushi ita kadai bayan Godiya ta sake jadadda mata Malamin yace lokacin ma da ya dibar masu za ayi sakin baza a kai haka ba, don gab ake da yin sakin cikin kwanan nan kuwa, Meemah da ta shigo dakin ta tarar Momy na waya ta zauna duk tana sauraron conversation dinsu har suka yi sallama tace "To shikenan Momy yanxu haka zai saketa ba mu ci ubanta ba na huce haushin abinda yayi min a kanta?" Momy tace "Ke wa ke ta wani cin ubanta? Ance maki shi ne a gabana sai kace wata yarinya? Ni dai in na samu Abdul ya rabu da ita an gama min komai, kuma hakan kadai ne a gabana yanxu ba shashanci irin naki ba, ke kinsan menene hada iri da talaka kuwa? Ke kiji matsiyaciyar kakarta har ta fara shige shigen malamai tana kawo mata asiri banda Allah yasa Abdul din ya gani, to karyarsu ta sha karya wallahi, cikin kwanan nan zai kora masu ita bayan ya saketa" Mikewa Meemah tayi ta fita daga dakin don kwata kwata ba haka ta so ba ita, so kawai tayi a bar ta tayi ma Khaleesat dukan mutuwa ko zata jin sanyin abinda Abdul yayi mata a kanta. [6/25, 8:35 PM] khaleesat Haiydar ✍️: Bayan Khaleesat sun koma gida tayi wanka sannan ta canza kaya tayi sallan azahar ta fito ta dora lunch a kitchen, tana ta zaune parlor bayan ta gama hada komai na girkin tayi tagumi tayi nisa tunanin da take bata san sanda ya fito daga dakinsa ba, ya karaso parlon yana kallonta yace "Burden din mutane nawa ne a kanki da kike tagumi haka" Juyawa tayi ta kallesa tana gyara zamanta amma bata ce masa komai ba, tunda suka dawo gidan sai yanxu yake mata magana bayan ya gama cika da batsewan sa kenan, Yace "I am asking you" Shiru tayi still bata ce komai ba, ya zauna kan kujeran dake facing dinta yace "Mutane nawa kike ciyarwa da kike tunanin yanda za ki yi?" Bata san sanda tayi murmushi ba tana wasa da fingers dinta, kamar bazata ce komai ba, sai dai a hankali tace "Ba ina son zan yi magana da frnd dita Sophie ba kace bazan yi ba" Yana kallonta yace "Kiyi magana da ita ki ce mata me?" A hankali tace "Babu komai, i am just missing her kawai" Wayarsa dake hannunsa ya cire ma lock sannan ya mika mata yace "Speak to her in my front" Amsan wayar tayi ta shiga contact dinsa ta duba number Safiyyah sannan tayi dialing, yana kallonta yace "Sa a handsfree" Ba musu Khaleesat ta saka kiran a Handsfree, yana fara ring Safiyyah ta daga, a hankali Khaleesat tace "Sophie" Safiyyah tace "Omg Khaleesat? Wallahi I've been expecting your call for so long kawata amma shiruu, Ya Allah, number Abdul din ne wannan?" Khaleesat ta ɗan kalli Abdul da ya kafeta da ido tace "Um, nasa ne" Lkci daya har Safiyyah ta gane wayar a handsfree yake sanin wanene Abdul, a hankali tace "Ohk then, ki gaida min shi sosai pls, but can i come over in gan ki if he will permit that pls?" Cikin sanyin murya Khaleesat tace "I will speak to him about it" Safiyyah tace "Alright dear, take care of ur self, i will be waiting for ur feedback" Khaleesat tace "In sha Allah" a haka suka yi sallama, safiyyah ta kalli wata aunt dinta dake kusa da ita cike da bakin ciki tace "Wallahi nasan yana gefenta shi yasa ban tofa nawa ba, Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Her marriage and Abdul is the worst thing that have happened to me last year, yanxu shikenan ta zama matarsa duk guje mata hakan da na dinga yi, ba irin addu'an da ban sa ta akan Allah ya rabata da Abdul ba, nayi ta mata sha'awan Housemate dinta amma Allah ya riga ya kaddara Abdul ne mijinta, dubi yanda take min magana kina jin muryarta kinsan tana cikin damuwa da matsin rayuwa, gashi karshen watan nan za mu koma school ban kuma ga alamar zai bar ta taci gaba ba" Safiyyah ta fara matsar kwallan bakin ciki, ita dai tana jin babu wanda ya kai ta bakin ciki da auren Khaleesat da Abdul, Abdul ya amshi wayarsa da Khaleesat ke mika masa bayan tayi sallama da Sophie, a hankali tace "Thank you" ajiye wayar yayi yace "Sai hankalin ki ya kwanta yanxu tunda kin yi magana da kanwar Baabarki ko" Cikin sanyin murya tace "Plss ina neman favour din ka barta ta zo wajena don Allah, i am missing her so much" A takaice yace "Baza ta zo ba, in barta ta zo ta ji dadin zuga ki kamar yanda ta saba? you think i don't know saboda tasan wayar a Handsfree yake shi yasa tayi composing words dinta without saying anything silly yanxu, duk ba ita bace ta fara ruining tunanin ki, very stupid girl" Khaleesat dai kallonsa kawai take hawaye cike idon ta, kawai tayi deciding tayi masa maganar abinda ya tsaya mata a rai all this while, hoping Allah zai sa yayi considering din request din nata, cike da karfin hali tace "Amma don Allah Yaya Abdul kar kace bazan koma makaranta ba, we are resuming end of this month kuma kasan wannan shekaran kadai ya rage min plss kar ka bari inyi asaran shekarun da nayi a baya, kayi considering expenses din karatun plss, in kuma zai yiwu kawai a min transfer ba lallai sai can kasar ba..." Hawaye na sauka idonta ta kare maganar tana kallonsa, ya mike yace "You think i am stupid da zan bari ki kara komawa America ki ci gaba da karatu? to ai kai ki can ma da nayi tun farko i deeply regret doing so, nayi da na sanin kai ki karatu America da har ya bude maki ido, kuma tunda ba kudin ki ko kudin wani naki aka kashe ba all this past years ina ruwanki da asaran da za ayi? How is the lost going to affect you da kike nagging akan expenses din? Ina ce kudina ne sai ko kudin mahaifina? So babu ruwanki, na gwammace inyi asaran duk abinda na kashe maki da dai ki koma kasar nan, kuma kika kuskura kika sake kawo min maganar karatu sai nayi mummunan saɓa maki wallahi, kuma bari kiji, common University din kasar nan ma baza ki yi ba balle na wata kasar don babu inda aka ce lallai lallai sai kinyi karatu, at first nayi tunanin kina da kamun kai da nutsuwa ne shi yasa confidently na kai ki America, amma sai kika tafi kina rayuwa da wani ƙaton ɗan iska a gida daya without my knowledge, ya kai ya kawo ko kudi na tura maki sai kiyi kamar baki gani ba for days tunda kin samu ɗan iskan dake siya maki abubuwa, not even one guy, kattin maza har biyu kika je kina mu'amala da su a can, ko wanne kuma ke kika san abinda kike basa da yake kashe maki kudi, so ko da kuskure kika sake kawo min maganar karatu wallahi sai na maki abinda har ki koma ga Allah baza ki manta ba" Yana kai wa nan ya dau wayarsa ya fice daga parlon kamar zai tashi sama, Khaleesat ta bi sa da kallo hawaye masu zafi na sauka idonta. Har dare Khaleesat na dakinta abun duniya ya taru ya mata yawa, wajen karfe sha biyun dare har ta fara bacci taji an bude kofar dakinfa, a hankali ta bude idonta, wutan dakin taga ya kunna sai kuma ya kashe, ita dai tana kwance bata juyo ba, ya karaso inda take kwance ya cire duvet din jikinta ya cire hulan kanta yana shafa dogon gashinta ya kai fuskarsa kusa da nata murya can kasa yace "You gave me Neither lunch Nor dinner today, saboda kinfi karfin a gaya maki gaskiya ko?" Ita dai bata ce komai ba duk da tana jin sa, dagota yayi zaune ya rungumeta yace "Then let me have you since you are not giving me what u cook" Bai jira abinda zata ce ba ya fara kissing dinta, Sosai Abdul ya bata lokaci wajen romancing dinta irin yanda yasan zai gigita ta, in ba ita ba ma babu warce ya taɓa romancing har haka, ko lube din bai dauko ba yau don baya ganin zasu bukace sa ma, a wannan moment din Frustration dinsa yafi na kullum don sosai ya kai zuciyarsa nesa bai kai mata hannu ba, yana wani irin huci ya fixgota da karfi yace "Why are you doing this to me Khaleesat? Why are you frustrating me?" Kasa ce masa komai tayi jikinta na rawa hawaye na zuba idonta, ta gaji da ce masa ita bata san abinda ke faruwa ba, cikin daga murya jikinsa na rawa yace "Ki bani amsa? Me na maki kike wahal dani kike cutata haka?" Khaleesat dai ta kasa ce masa komai jikinta na rawa don tsoron magana ma take ya gaggaura mata mari, yana wani irin huci ya turata yace "Ki jika abun ki ki sha" Yana fadin haka ya sauka daga saman gadon ya saka Pajamas dinsa ya fice daga dakin kamar zai tashi sama, Khaleesat dai ta jawo duvet ta rufe jikinta har sannan zuciyarta na bugawa ta fashe da matsanancin kuka, bayan kusan minti goma taji fitar motarsa a gidan gaba daya. Da yammacin ranan Momy na parlonta da Godiya sai ga Abdul ya shigo kamar an hankado sa, Momy na kallonsa tace "A'a Babana, sannu da zuwa" Juyawa yayi ya fice daga parlon ganin Godiya, Momy ta ɗan zaro ido tana kallon Godiya sai kuma ta mike da sauri ta tafi kusa da kofar ta bude tana leka corridor taga bangaren Abbansa ya tafi, ita ta dade bata gansa cikin irin wannan yanayin ba ma, ta kulle kofar ta dawo tana kallon godiya tace "Anya Godiya Malamin nan ba maye bane kuwa, kin ga dama yace Abdul zai zo yau gashi kuma ya zo din kamar an jefosa" Godiya tayi wani dariya tace "Ke ma dai wallahi sai kace yau Danger ya taɓa maki aiki da zaki yi mamaki? Yanxu dai sai ki tashi kije ki dora masa girkin da ya fi so da maganin" Momy tace "Ikon Allah, in dai kana da kudin ka zaka ga aiki da cikawa kawai, yanxu ki dubi yanda ya shigo mana a firgice kamar mara lafiya" Godiya tace "Ina kuwa lafiya dama an hanasa angwancewa da amarya, sai kace baki san maza in suka kwallafa rai kan wannan lamari ba" Suka kwashe da dariya gaba daya har da kyakyatawa, Momy tace "Toh yanxu zan tura cikon aikin nan na karshe, yaushe zaki koma wajensa mu je tare in masa godiya" Godiya tace "Nan da kwana uku in sha Allah, kin ga bari in tashi in tafi mai gidana na hanyar dawowa yau" Momy tace "Haka fa kika ce, toh shikenan sai mun yi waya dai kawai" A haka Momy ta raka Godiya har gun motar ta sannan ta dawo cikin gidan ranta fari ƙal, bangaren Alhaji ta nufa ta tarar da Abdul kwance a parlor idonsa a lumshe, zaunawa tayi gefensa tana kallonsa cikin kwantar da murya tace "Babana baka da lafiya ne?" A takaice yace "Hutawa nake yi Momy, i need privacy pls" Momy tace "Toh shikenan, bari in sa a daura maka favorite din ka, ina Mamata fa?" Shiru yayi yaki ba Momy amsa, Momy ta mike ta nufi kofa ta fita daga dakin ta kullo kofar, sai a sannan tayi wani murmushi ta koma bangarenta zata dau maganin da Godiya ta kawo mata wanda zata zuba a cikin girkin abinda Abdul ya fi so, sai da ta kori mai aikinta can compound sannan ta fara girka masa Pounded yam da Vegetable soup, cikin miyan ta zazzage duk maganin da kyauta ta kawo har kala uku, wajen karfe bakwai ta gama ta dau abincin ta kai masa dining table ta ajiye, dama iya cin sa kawai ta girka wato malmala daya kuma ba babba ba, miyar ma ɗan tsut yanda zai cinye gaba daya, sai bayan isha Abdul ya ci abincin da Momy tayi masa, ya bar ma mai aiki ta kwashe sannan ya wuce sama zuwa dakinsa, Momy ta fito dakin Meemah kenan ta bi sa da kallo har ya shiga dakinsa sannan ta bi bayansa, tana shiga dakin tace "Wai lafiya Babana? Ko dai akwai wani matsalan da kake boye min ne" a takaice yace "Ba komai, zan shiga wanka" Yana fadin haka ya fara cire kayan jikinsa, Momy tace "To ka ci abincin?" Yace "Na ci" Momy na murmushi tace "You like it?" Yace "Miyan yayi dadi, but it's little" Tana murmushi tace "To maa sha Allah, amma ai ya isheka dai" Yace "Ya isa" Tace "Toh je kayi wankan ka nima bari inje in ci abinci" Fita tayi daga dakin ya shiga bandaki, Momy na zaune parlonta tana cin farfesu dake cike cikin bowl din hannunta Abdul ya shigo, kallonsa tayi ganin yanda ya shirya sai zuba azababben kamshi yake, tace "Har zaka tafi Babana" Yace "Eh, sai da safe" Tace "To ko in zuba maka farfesun ka kai ma Mamata" A takaice yace "A'a ni ba gida zan kwana ba" Momy tayi murmushi tace "To Allah ya tsare Babana" Yace "Ameen" Daga haka ya fita daga gidan. The next 10 days a gidan Abdul was a living hell for Khaleesat, gaba daya Abdul ya sauya mata a gidan ya dawo kamar wani monster, dukanta da yace ya dena sai dai bai samu slightest opportunity din yin hakan ba, kawai ya maida ta punching bag dinsa a gidan barin in ya zo gareta bai samu biyan bukata ba, kuma bai fasa zuwa mata da bukatar tasa ba amma as usual sai dai kawai ya doketa ya fita bai cimma burinsa ba, kwata kwata ya dena cin abincin gidan, ya dena kwana sai sanda ya ga dama, duk wani ingredients din girki ya dena siyowa sai dai tayi ta cin indomie, hatta bottle water ma da ya kare yaki siyowa, kuma ko Satchet water yaki siya ya ajiye, sai dai ta sha ruwan pampo, gaba daya Khaleesat ta fita hayyacinta a gidan ta dawo kamar ba Khaleesat ba, ga karyewa da gashinta ya dinga yi sosai saboda tsananin damuwa, kana ganinta kasan tana cikin jarabawan rayuwa, bata da aiki sai kuka sai kuma addu'a da sallan dare, gaba daya ta maida duk lamarinta ga Allah, kullum haka take kwana ta tashi da zazzabi amma ina taga fuskar ce masa bata da lafiya, sai dai tayi ta daurewa a haka, in ma ta gaya masa don ya zagi iyayenta ba komai bane a wajensa, in zazzaɓin ya rufeta sai dai ta kwanta har sai sanda zata ji dama dama sannan ta daure ta tashi. Ranan Friday tana dakinta a kwance ko breakfast bata yi ba har kusan karfe sha biyu da rabi, zuwa yanxu ta gaji da cin indomie da ma tana da dakakken yaji sai ta dinga yin ko shinkafa da mai da yaji ne amma babu, indomie duk ya fita a kanta bata iya ci ko ta dafa, gashi haka take dafasa babu yaji balle albasa, bude kofar dakin nata yayi ta mike zaune da sauri tana kallonsa gabanta na faduwa, kamar zai fasa mata dodon kunne taji yace "Ina Cufflinks din da na bari a parlor shekaranjiya?" Sauka tayi daga kan gado, ita dai ta gyara parlon ta goge ko ina jiya da yau amma bata ga wani Cufflinks dinsa ba, a hankali tace "Toh bari in duba a parlon" Wani mugun kallo yake mata hakan yasa ta raɓa tabi ta gefensa ta fita daga dakin zuciyarta na bugawa ta tafi parlor tana dudduba Cufflinks din, da alama masallaci zai je don yin sallan juma'a, babu ta yanda za ace iya Cufflinks din da yake tambayarta yake da shi a gidan, amma sbda neman hanyar da zai musguna mata yake shi yasa zai saka ta gaba ta fito da abinda bata gani ba, kuma rabonsa da gidan tun shekaranjiyan, tana cikin dube dube a parlon shi kuma yana tsaye fuskarsa a murtuke alamar he is loosing his patient aka bude kofar parlon, Momy ce ta shigo da Cousin sis din Alhaji Musa, warce suke kira da Ummu, Yau kwanan Ummu uku a Nigeria daga Dubai inda take aure da yaranta duk a can, kuma a yau zata koma Dubai shi ne ta sa a kawota ta ga matar Abdul kafin a kai ta airport, duk da Abdul yaje ya gaisheta san da ta zo, Khaleesat da duk a rude take ta kalli Abdul a hankali tace "Wallahi ban gansa ba da nake gyaran parlorn jiya da yau, kilan ka sha'afa ko a daki ka bar su ne ka manta" Bata rufe baki ba ya sauke mata wani gigitattcen mari yana huci ya fixgota yace "Ni zaki gaya ma a daki na bar su?" Ta dafe kuncinta hawaye cike idonta tana girgiza masa kai, nan da nan fuskarta yayi ja, ko minding uwar sa da Cousin sis din Babansa da suka shigo parlon bai yi ba, duk suka yi cirko cirko baki bude suna kallon ikon Allah, cikin tsawa yace "Baza ki fito min da shi ba sai na maki dukan tsiya a nan?" Tana shesshekan kuka tace "Nace maka ni ban ga wani links din ka ba wallahi...." Bata rufe baki ba ya sake sauke mata wani wawan marin, Momy da taji ranta yayi fari tass cikin kwantar da murya tace "Subhanallahi, Babana ka bi a hankali, hakuri ake Babana" Ummu ta jefar da handbag dinta kan kujera ta nufesa cikin bacin rai tace "Abdallah?? kana hauka ne kake marin mace haka don uban ka?" Momy ta wani hade rai tana kallon Ummu, Abdul yaki ko kallon Ummu dake masa magana, ya wani haure Khaleesat a mugun fusace har sai da ta fadi kasa, Wani Mari Ummu ta sauke masa a fuska, cikin fushi tace "Ashe kai jahili ne shashasha ban sani ba?" Juyowa yayi yana kallon Ummu da mamaki baya ko kiftawa, Momy ta dinga huci tana kallon Ummu ita ma, nan da nan idanuwanta suka kankance don bacin dai, tunda ta haifi Abdul bata taɓa marinsa ba haka ma ubansa sai gashi yau an maresa a gabanta, Abdul dake kallon Ummu kamar me counting din words dinsa yace "Ummu akan wannan jakar yarinyar kika mareni??" Ummu tace "Na mare ka din, zaka rama ne? Wawa kawai mahaukaci ka saka yarinya karama haka a gaba kana duka? Tarbiyar da aka maka kenan? In na san abinda zan zo in tarar a gidan ka kenan uban me zai kawo ni?" Abdul da idanuwansa suka sauya launi ya kalli Khaleesat yace "Ki je... na sake ki" Yana fadin haka ya dau makullin motarsa ya fice daga parlon kamar zai tashi sama, Khaleesat ta bi sa da kallo babu ko kiftawa kamar bata fahimci abinda yace ba, Momy ta sauke wani bayanannen ajiyar zuciya tace "To Alhamdulillah, Alhamdulillah, Alhamdulillah" Sai kuma ta kalli Ummu tace "Ke kuma Muhusina kin ci darajar Musa banda haka da babu uban da zai hanani rama ma ɗa na marin da kika masa don tunda na haifesa ban taɓa marinsa ba haka ma ubansa, kuma Abdul yayi min dai dai hukuncin da ya dauka, dama me ake da auren er gidan talakawa er gidan matsiyata? Ai ba class din mu bace ita, kuma duk bama goyon bayan wannan tsinannen auren, kawai irin wannan rana muke ta jira gashi Allah ya kawo mu cikin ruwan sanyi, Alhamdulillah Allah na gode maka, Allah na gode maka, yau zan yi bacci cikin farin ciki da kwanciyar hankali burina ya cika, effort dina kuma bai tashi a banza ba" Momy na kai wa nan ta nufi kofa tana tafiya gansan gansan farin ciki fal a ranta mara misaltuwa tana murmushi ta bude kofar parlon, Khaleesat ta bi Momy da kallo with shock ko kwakkwaran motsi ta kasa tsabar mamaki, maganganun Momy suka dinga yawo a kanta kamar a mafarki, Ummu ta zauna gefen kujera ta dafe kanta tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Sai a sannan Khaleesat taji hawaye masu zafi na silalowa fuskarta, ta mike tana tafiya a hankali ta tafi daki ta dauko hijab dinta har kasa ta fito.....