GORAN DUMA Na Maimuna Idris Beli. Ebook Publish by http://hausaebooks.cf Izan kuna bukatan wasu litttafan sai ku ziyarci shafinmuu na yanar gizo akan adireshi http://hausaebooks.cf Farkon littafi. . . Rumaisa'u wankan tarwadar mace matsakaiciyar tsawo da kiba, fuskar ta nada alamun hakuri da sanyin hali a wajen wanda ya karanci mata, amma mai rashin matsaya ga mutumin da ya cikawa kansa zargi a cikin mutane saboda rashin son maganar ta da karancin fara'ar ta. Ta na xaune a matsakaicin palon gidan su ita kadai, a tsakiyar palon bisa kapet tayi kaca-kaca da takardu. Ga wayoyin ta da na'urar kwanfuta(laptop) dake kapet, ga kuma robar ruwa da kwalin lemo a gepe. Wannan yasa ba sai an padi ayyuka ke caja gabban ta wanda fuskar ta da gabban suka kasa nuna gajia, watakila dan juria da son aikin har zuci. Can daya daga cikin wayan ta dake zube ta saki wata siririyar kara amma abun mamaki duk da haka sai ta firgita, ta dubi wayar da sauri kuma a tsorace xuciar ta na bugawa, duk da haka ta latsa sakon ya pito. A pili cikin ta Ya bayar da wani kuuu... Har sai da ta dan rankwapa na alamar ba a karar ya tsaya ba har da haipar mata ciwo. Ga abun da ke rubuce a cikin wayar '' yaushe ne kika shirya barin nunpashi na ya huta? Duk yadda kike jin aiki da dawainiya a rayuwa bana jin kin kama kapa ta, amma kin san wani abu? Mamakin yadda kike share al'amra na ma wani tapkeken babi ne a kundin da na ware miki, wanda ko wannan babin aka barni dashi ya isa abin wahalar da xucia. Rumaisa'u bayyana min siririn ki wanda ya rike ni na kasa ampani da Karpi wajen maganin ku ke da zucia ta! Ware min ko sakan goma ne daga lokutan ayyukan ki kiyi min wannan aikin Rumaisa. Daga MAHAUKACIN MASOYI. Tayi wurgi da wayar kamar wadda ta galla mata cixo a bayan ta, bayan ta kammala karanta sakon, tana satar kallon wayar, san nan ta koma satar bin palon da kallo, musamman jikin labulaye, harshen ta pal ambaton Hasbun Allahu wa ni'imal wakil, ta dora da padin '' A uzu bi kalimatuLlahi tammat min sharri makhalak '' Duk illahirin gabobin ta sunyi sakayau, babu nauyi tamkar idan an yanketa jini baxai bullo ba saboda tsoro da wasi wasi Tsawon piye sati hudu kenan tana pama da sakonnin wanda ke Kiran kansa da MAHAUKACIN MASOYI mutun da a yanxu ta para shakkar mutun ne ko aljan, mutun da aljan din na xahiri ko kuma ifiritai ne (hackers) suka hauro layukan wayoyi kamar yadda akan same su a yanar gizo? Cikin zarginta uku kowanne ta canka babu dama a cikim sa, in mutum ne ta wanne bututun yake hango halin da take ciki a lokacin da yake turo mata sako? Kamar yanzu da yayi maganar cakudewar ayyuka. Idan aljani ne ma wani bakin tashin hankalin ne dan babu ta inda aka gwamutsa mu'amalar mutane da ta aljamu bare har a gayyato musu batun soyayewa a irin haka. Zargin 'hackers' din ne ma mai dam sauki wai idan ta kawar da kai ga rashin yawan bayyanarsu a layukan waya ta wannan sigar, ko kuma lissapin nemo manuparsu a kanta da suka dame ta ita kadai... Wata dattijuwar mace para mai tsawo da kiba , tayi sallama ta shigo palon, da sauri rumaisau ta gyara sahu ta hadiye maitarta ta amsa sallamar matar, purkarta da gabobinta suka nuna ladabi, tana murmushi ta amsa sallamar matar mai alamin zapin nama ta dubeta tace, '' Rumaisau ki saki aikin nan ki huta haka,ga pura mai kyau can Alhaji ya shigo da ita, kije ki dama kisha... Rumaisamu tayi kokarin tattare tashin hankalim da take ciki tabawa cikin ta ajiyarsa, ta tare matar da rawar murya dake kokarin komai ya zama ba komai ba, ''Oh Abba ya shigo Hajia? Hajia tayi murmushi ta amsa mata tun da hamida ta bar mu gidan ya zame mana kamar hurumi, kirikiri alhaji ke nuna pipiko tsakanin mu, ni kaina sai na zage nake sanin shiga da pitar sa. Rumaisau tabi wayar ta da kallo tana murmishin hadawa zuciyar ta ayyuk biyu, tunanin gudan jinin ta Hamida, da kuma tausayin ta a matsayinta na mace mai rauni, wanda kuma zata tsaso kila cikin ratuwar da tapi tata wadda take tapia a cikin ta yanzu muni. Sai kawai taji hawaye na son cika mata ido, amma ta dage ta dadiye, ta cewa hajia '' to hajia wannan dai tsakanin ku ne'' hajia ta bar amsawa Rumaisau maganarta tabi ruwa, saboda damum kanta da nazarin rumaisau'un da take sonyi wanda puskar ta ke son karyata abun da zuciyarta ke kokarin bayewa, amma data hada nazarin nata da wasu daban sai ta yi saurin sharewa gudun batawa kai lokaci, ta jima da sanin rumaisa duk inda ake neman mutun mai kawaici ta cika mizami, mawuyacin abu ne kaji korapi a bakin ta duk yadda ka kai ga kwarewa hilarsa wani ya amayar da abun da zuciyarsa ta boye. '' baki da bukata ko ta neman addu'a ce daga gare ni!'' hajia ta sami kanta da furta wa rumaisau cikin tsura mata ido, sai rumaisaun ta dan diririce saboda pargabar ko tayi wani abu da ya dago halin matsin da take ciki. Ta hau hada takardu tana cewa '' hajia kiyi min izinin gobe na kai rubutun nan abuja nayi submiting. Hajia taci gaba da kallon ta, kallo mai cike da tuhuma. '' rumaisau kwanan ki nawa da zuwa Abuja kuma tunda kike rubutun nan kin taba kai shi takanas? Ji nake ta Email kike tura musu?'' a ladabce Rumaisau ta shiga kokarin kare kanta. ''akwai matsala ne hajia, kinga ban gama bugawa ba kuma ka'ida gobe laraba mujallar ke pitowa. Ba wai lallai ya zama sai nakai din ba,amma dai ina neman alparmar zuwan hajia saboda muhimmanacin rubutun'' hajia tayi siririyar daria tana ci gaba da yi mata wani irin kallo, wanda rumaisau ta kasa daurewa har sai da hajia ta ci gaba. Ko dai alkunyarki ke son gazawa ba zaki iya rashin Hamida ba ko? Ni dai abun da zuciata ta karantar dani ke nan, da sauri rumaisau ta tareta cikin zaro idaon bijirewa batun hajiyar tace ''ah! Hajia to na pasa zuwa tunda kin zargi hakan.. Wallahi ko kadan ba dan hamida zanje ba hajia. Nan da nan hajia ta tareta da na yarda daje rumaisau zan kuma sanarwa Alhj amma da sharadin zaki tashi yanzu ki nemi wani abu kisa a cikin ki. Cike dq jin dadin kulawar da hajia take mata ta yalwata para'arta da murmushi tace "ai na bari tuni tun bayan pitar hajia ta janyo wayarta a gajiye tankar wadda tayi gudun shekara ta kasheta, ta jepa akan kujera samnan ta pice debo purar da hajia ke mata tayi. Ta kori hataniya da rudin wannan duniyar da tilastawa kanta shan purar sosai har ta gamsar da ita, tayi wamda ta sallaci Isha'i, sannan ta zauna azkar din yammaci da bata samu damar yun sa a kan lokaci ba, sai tayi shi a yanzu tana mai nutsuwa da kaskantar da kai ga Mahalicci. Abin da ya karpapa mata gwuiwar isa gadon baccinta da wuri tare da tsammanin zatayi barci a nutse shine a zacin da tayi na kashe waya tare da yunkurin barin kano a gobe dan ganin gudun ruwan MAHAUKACIN MASOYI , wayar da yake kiran ta ta kashe, garin kano idan ma kyamarar sirri (CCTB) ya makala a garin to ta bar shi, cikin kwana biyu kuma sai ta gani ta ina zai leko ya rikitata? ABUJA karpe biyu da rabi na rana ta pito ofishin da jaridar Aminiya dake jabi da komawa masaukinta wajen Innarta a anguwar wuse. Duk a rikice take tun saukarta Abuja taji wata bala'in rashin nutsuwa ya mamaye ranta har yake bayyana a gabban ta, wayi ayyuka. Misali. Tana sauka bus din da ta kawota garin a matsayinta na wadda ta taho Abuja a gaggauce, dan zuwa opis maimakon ta dauki shatar motar da zata kaita Jabi kawai sai ta buge da daukar wadda zata kaita gidansu Wuse cikin wasiwasi, a cikin tadi din ne ta budo naurarta mai kwakwalwa ta lalubo rubutunta tana nazari da shawarar ta tura shi kawai ta Email din ta wuce gidan ta kwanta, anan kuma ta lalubo Moderm dinta cikin jakar sai ta tarar ta baro shi a kano, nan take ta yanke shawarar tsayawa wani kataparen kantin harkokin sadarwa da ke nan titin da zai sada ta da wuse daga Utaho kawai, ta tsaya anan ta tura rubutun, ana isowa Annur ta yiwa direba umarnin ya tsaya anan ta shiga ta pito. Ta kwashi i laptop tayi ciki , kataparen waje mai kamar komai da ruwan ka a bangaren sadarwa, wayoyin hannu , layukan waya, katin wayam kwanputa da sauran tarkacen da suka dangance ta, modem din da ta baro a gida ma wancan zuwan nata ta saye shi anan, haka dai gurin yake bangare bangare ko ina da abubuwan da ya kunsa. Yau tana shiga bangaren cafe ta tunkara, amma kamar wadda tazo daga kauye duk kaparta rawa take sai sassarpa take har ta isa inda ta nupa. Ba wani abu ne ya janyo hakan ba sai gain yadda kamar kowa a wajen ya zuba mata ido ne, da yake yawancin katangar dake tsakanin bangarorin ta gilas ce, kamar duk ma'aikatan wajen sun doro hankalinsu akanta. A gajiye ta karasa wajen ta zube a kujera tana numparpashi tamkar wadda tayi gudun pampalaki, ta yar da jakar naurar gepe ta zube wayoyinta akan tebur, mai kula da bangaren ya dago kansa daga printer da yake zaro wasu takardu yayi mata wani kallo shi ya tsinke tunanin ta, ta shiga zargin ko wani mummunan abu ne a jikin ta da mutane ke binta da kallo haka? A dabarance ta para nazarin shigarta , tana sanye ne da bakar after dress mai sheki da abon shudayen kananan dumatsu kalar riga da siket din material dinta na ciki, kanta nade shi da mayapin rigar kuma da yake ba zata iya putowa a haka ba sai ta kara da nade kapadar ta da lallausan mayapi mai matsakaicin girma shi ma shudi, jakarta da takalmin ta duk shudaye , idon ta sanye da siririn parin gilas, a zatonta ko ba ganin idon ta ba, ganin idon kowa ma babu kauyanci ko digo a cikin shigarta, duk da haka bata gamsu ba sai ta saci ido ta bude jaka da sunan lalube ta kalle puskarta tsab ta cikin jalar komai pes hatta hodar puskarta da man lebe (wetlips) babu abin da ya gigita su. Ta zuge jaka tana sauke ajiyar zucia cikin tsananin tashin hankali wanda ya karu lokaicn da ta lura mai wajen ya kapa mata ido ya pada da karpi laa kamar barauniyar da tazo tayi sata jiya... Lol. . GORAN DUMA 2 . . Ta zuge jaka tana sauke ajiyar xucia cikin tsananin tashin hankali wanda ya karu lokacin da ta lura mai wajen ya kapa mata ido kamar barauniyar da tazo tayi masa sata jiya yau ma ta dawo. Sai bakin su ya hau rawa shi da ita. '' madam... Madam.. Me kike bukata? Ita kuma tana rawar bakin cewa don Allah... Zan tura wani aiki... Ta na'urar kwanputa, ta me zan tura... Bai iya amsa mata ba sai gyada kai kawai yake kamar kadangare yana kallon ta kai tsaye , hannunta sai karkarwa yake ta parke jakar system dinta shi kuma da sauri ya karaso ya tura mata foot stool waiko zata dora kapa. Da wasa ba zata dorar da abun da tayi a naurar kwanputa ba, musamman da shi mai wajen ya dauki waya yana magana da wani harshe da bata samshi ba alamunsa kuma na nuna hankalinsa na kanta. Ba a dauki ko cikakken minti daya ba sai ga wani matsashi ya shigo mai matsakaicin tsayi da kaurin jiki puskarsa na da alamun para'a amma a halin yanzu kai tsaye ba za a yi masa passara ba , ya nemi guri ya zauna bayan sun gaisa da mai kula da wajen sai ya nemi kujerar da ke puskantarta ya zauna yana satar kallon ta, tana latselatsen keyboard, can tayi namijin kokarin dagowa suka dubi juna ido cikin ido shi ya kawar kamar a razane ita kuma ta hade puska. Ta nuna masa TV plasma dake makale a sama tace. '' bawan Allah kaga abun kallon can.' yayi pirgit ya dubi talabijin din sannan ya dube ta muryarsa na rawa yace ina... Patan dai ba tsarguwa kikayi ba? Ya mayar da kanta rai a bace tana matsawa siririn hancinta hura iska. Alamar dai haushin ta ji, amma bata tanka ba. Shi ma ya kawar da kai yana cewa batawa kai lokaci ne kayi abun kallo kace baza a kalle ka ba. Ta dago da sauri ta dube shi amma ba ita yake lallo ba balle ko a puskarsa ta karanci abun da yake nupi. Ta kokarta tace ko? Ya juyo cikin kada kai haka nace. Saboda haka kallon naki yapi kallon wannan akwatin da kike nuna min kaye... Yanayin yadda yake magana duk kwakwalwarta ta kasa gane inda ya dosa , puskarsa babu walwala bare ayi zargin irin mazan nan ne masu latselatsen yanmata. Tsam! Sai ta tattara kwanputarta ta mayar a haka ta zuge jaka tana cewa bari na bar muku wurin ko? Kila kuyi abin da zai ampane ku, dan kallona babu ma'anar da zai baku.. Malam nawane kudina? Ta mike rataye da jaka tana duban mai wajen ya girgiza kai kamar a darare me kika yi na kudi? Kije kawai . Ba ta ko tanka ba ta juya ta pice kaparta na hardewa kowa na damuwa da kallon ta har ta pice cikin sassarpa. Bata sami direban da ta bari cikin mota ba, sai kawai ta rungume hannu ta jingina da motar cikin rudani tana zuba idon ta inda zai billo. Cam sai gashi da mujalla a hanu cikin zapin nama ya bude motar yana neman apuwar ta , ta hango wannan gajeran mutumin da yake kallonta yapi talabijin yana doso inda suke. A hanzarce ta cewa direna sauri mubar wajen nan, cikin direba ya dauki wani kugi da yasa shi kasa bin umarninta yanayin yadda tayi maganar ya sa yayi zargin babu gaskia a tare da ita, tsoro ya ke ko wani abun ta sato tasa shi taka sawun barawa. Yakai ta ya sauke lambar motarsa kuma ta shiga kundin masu laipuka. Saboda haka kawai sai yaki tapia har gajeren mutumin ya karaso ya mika mata wayoyinta ta windon motar. Madan sanyin AC wajenmu ya sabbaba miki mantuwa.? Ta karba tana mayar masa da raddi haka ne musamman da yake daga kauyen mahudar rana na pito ba. Ya juya ya koma da karamin murmushi a puskar sa. ''Allah ya baki hakuri idan gaskiar tawa zapi tayi miki. Direba yayi ajiyar zucia ya tashi motar yana cewa kinga gara ma da muka tsaya. Ko kala bata ce masaba har suka hau titi, sanan tayi masa umarnin ya kaita opishin jaridar Aminiya kai tsaye ta gyara shirmen da tayi. Acam kuma ta watsar da dimuwarta tayi abin da ya kamata, karpe biyu da rabin nan ta pito da dokin zuwa gida don samun nustuwar zucia amma dai ta san wahalar da kai ne dan gaba daya tsarge take, sai kissipawa kanta take wani na biye da ita, bata jima bakin titi ba ta samu mota kuma da yake tsakiyar rana ne titin babu cunkoson ababen hawa, sai nan da nan tapiyar tayi musu sauri suna kan Berger flyover kiran innarta ya shigo wayarta da ke kunne ta dag cikin muryar ladabi tace Momi ina hanya kusa da isowa tana sauke wayar sai tabi ta da sabon sako hankalin ta kwance ta bude shi, dan a amintacciyar wayarta sakon yake, wayar da bata taba hadata da gigitaccen sakon Mahaukacin masoyi ba, saboda haka karsashinta ta para karantawa.'' Rumaisau garin Abuja ni'imtaccen gari ne ma'abocin dauke kewa da gadar da nutsuwa tankar yadda salihar puskarki take, amma yau na shiga rudani da nake ganin puskarki da ayyukanki a gigice. Kila kin halarci Abuja ne bisa radin kanki ban kuma cire tsammanin dan ki samarwa kanki nustuwa bane, amma yaya kika hana zuciyarki da gangar jikinki hakan Rumaisa? Laipin me wayarki tayi kika kashe ta? Inajiran amsa. naki MAHAUKACIN MASOYI. A Uzu bi kalimatuLlahi Tammat min sharri ma khalak. Wannan adduar ta karabto tana juya wayar duk da kuwa tayi mata nauyi a hannun, a yau kam taji a ranta ba bil'adama bane mahaukacin masoyi ba, kuma ba hackers bane duk yadda ake yi yana daga shaidanun aljanu da zata tashi tsaye neman tsarin Allah da shi har ta shiga gida cikin wannan ruwanin biyu take na mahaukacin masoyi da kuma na son canko dalilin da yasa ta zama madubin mutane a yau. Bakinta da Ayatul Kursiyu har da wattaba'u ta shiga gidan, innarta ce kadai a palon tana mata marhabin amma sai ta wayance da matsuwar shiga toilet, inda ta ajiye jaka a palo cikin sauri ta shige bandaki. Tayi tsaye gaban katon madubi tana kallon kata daga sama har kasa iyakar ganin da kwakwar juya bayanta ta kallo bataga abun kushewa ko abun kayen da za a damu halittarta da kallo haka ba, wannan yasa taji tausayin kanta ya mamayeta, duniyar nan kamar ba ta karbeta ba, duk inda ta shiga sai rayuwa ta zame mata kwado, ta rasa abun da take so ko kubucewarsa in ta samu, ko kuma puskartar kiyayya daga wanda rayuwa ta yarda su rayu tare. Da kyar ta rarrashi kanta yayin da zuciyarta ta samu dan wani sarari sakamakon jiyo kawar diyarda Hamida. Tayi alwalar sallar la'asar ta pito palon innarta da mai aikin dauke da kyakkyawa hamida yar kimanin shakara biyu da rabi, sa'a mai aiki ta dire Hamida da sauri tana cewa Yauwa tapi da gudu ki yiwa momi oyoyo. Kamar Hamida ta gane manuparta ta tahi a guje ta tari Rumaisau wadda kunyar idon tata uwar ya hanata tarar hamidan, sai ta bige da rike mata hannu kawai, idon ta akan sa'a tace. Sa'a ta amsa. Muna ciki uwar dakina daga wasa jiyo Hamida tayi bacci kawai sai kwantar da ita wajena. Suka karasa kujera Rumaisau ta zauna tana yar daria, yanxu wannan katuwar yarinyar kike goyawa Sa'a? Sa'a tayi daria tace ai shi yasa nace miki wasan goyo. Duk sukayi daria har innar Rumaisau wadda hankalin ta ke kanta, tana yi mata wani irin kallon tausayi. Sa'a ta mike tana cewa dan Allah dora yar nan a cinyarki taji sanyi kin kama kin wani rike mata hannu kamar yar awo, wannen abinci zan kawo miki? Ba ni ruwan zapi kawai, wato ta share korapin sa'a a parkon maganarta. Momi ina wuni, mun same ku lapia? Momi tayi murmishi irin na manya masu son karantawa kai korapi tace lapia kalau rumaisau yaya ayyuka? Taki duban momi kai tsaye saboda tsarguwa da tayi da kallon da momin take mata ta amsa AlhamduliLlahi momi, yaya Abba yana lapia? momi ta amsa lapiyarsa kalau ya halarci taron karawa juna sani a lagos sai jibi zai dawo ranar da zaki tapi kenan, kila ki dan jira shi ko? Tunda na san da sapiya zai dawo. Da sauri Rumaisau tace ai na pasa kwana biyun gobe da sape zan koma... Nan ma sai momi ta bita da kallon nazari amma sai ta kasa cigaba da yi mata kawaici. '' rumaisau kina tare da wata matsala ne? A dan gigice Rumaisau ta para girgiza kai A.a momi, me kika gani? Kai tsaye momi ta amsa puskarki na nuna babu nutsuwa a cikin ta, yakenki na nuna karpin halinki kawai, hajia ta sanar min kwana buyi kika ce mata zakiyi, yanxu kina dira kince da sanyin sapia gobe zaki tapi me ya kawo wannan sauye sauyen ko kina puskantar wata barazana ne? Rumaisau ta daddage ta bayyanar da karpin halin ta a puskarta da muryarta tace babu komai momi, wani aiki ne zai mayar dani kano a geben wanda ban san da shi ba sai da nazo yau, momi ta rausaya kai gepe cikin saduda ba tare da rai ya so ba tace ai shike nan idan hakane wannan aikin ba karami bane kamar yadda kika pada mana kapin para shi, in dai kuwa ojan-ojan din tapiye- tapiye za su dinga padowa cikin sa ai yapi karpin karami rumaisa u... Rumaisau ta tare innarta da daria mai sauti. Momi bai canja ba daga yadda na pada muku ni dai kuci gaba da yi min adduar patah alkhairi a dukkan al'amurana sanyaye momi tace shikenan Allah Ya yi miki albarka, Ya yi miki katanga da kuncin dunia dana alkiyama. Cikin murna da parin ciki ta amsa da Aamiin na gode. Momin tace da ita to dauketa taji duminki mana wata kila ma kewar ganinta ya kawo ki.. Raimaisau ta sa hannu ta dauki Hamida tana daria tace zolayata kawai kike momi yarinyar da ta pi sonku dani zan batawa kaina lokacin zuwa ganinta takanas? Suna daria su duka Sa'a ta shigo da parantin kayan ruwan zapi. 25/12/2012 ratar kwanaki goma sha hudu aka samu da zuwanta Abuja cikin kwanakin nan duk yadda mahaukacin masoyi ke son muna mata hatsabinbancinsa ta hanyar sakonninsa ya muna mata kwarewarsa a wayoyinta biyu, ta kala-kalar tsoro da hasashe babu wanda bata gayyatowa zuciyarta ba har idan abun yayi tsamari sai ta kashe wayoyi duk lokacin data kunna kuma shayar da ita tsoro da mamaki a tsarin kalamansa. Wannan pargaba da tashin hankalin suka dinga motsa mata larurarta ta hawan jini da ta gamu da ita wasu shekaru da suka wuce, abin boyewar ya zamar mata biyu, wato boye barazanar mahaukacin masoyi da take puskanta da kuma boye cutar da barazanar ke haipar mata gudun kada ta tashi hankalin iyayen ta da marikanta. Cikin dabara take zuwa asibiyi ganin likita haka zalika cikin dabara take shan magungunan ta, akwai wani ciwon nata mai hadari da ta taba haduwa da shi na rudewar kwakwalwa da gazawar wasu sassanta a cam lokacin baya. Paruwar wannan rudani da motsawar hawan jininta ya sa likitanta ya bata shawarar ta rika kwantar da hankali da bawa kwakwalwarta hutu saboda gudun motsawa wancan ciwon. . GORAN DUMA 3 . . Likitanta ya bata shawarar ta rika kwantar da hankali da bawa kwakwalwarta hutu saboda gudum motsawan wancan ciwon. Sanin girman hatsarin ciwon a tare da ita yasa take son watsar da captar mahaukacin masoyi ta dauke ta miyar da babu gishiri, amma sai hakan ya paskara wani lokacin sai ta zabi kashe waya in ta kashe kuma sai ta rasa abun dauke kewa ko sadarwa tsakanin ta da mutane, 30/01/2013 yau laraba da dare wajen karpe tara, ta gundura da kallon talabijin sai ta dauko na'ura mai kwakwalwarta ta lika modem ta hau yanar gizo kai tsaye ta nupi kapar sada zumunci ta facebook cike da dokin shiga dandalin duniyar marubuta da wata kawarta marubucia mai suna kamshi ( Hawwa Abubakar Lawam maiturare) ta gayyace ta. Dandalin duniar marubuta na fb cike yake da daruruwan marubuta da makaranta ana ta harkokin arziki tare da kuma abubuwan karuwa da na nishadantarda, tana shiga taci karo da wani rubutu da marubuci Muhammad Lawan Barista yayi mai take '' zaman 'ya 'yana nake'' duk lokacin da wani sabani ya shiga tsakanin Mamuda da matarsa Aliya sai ta bude baki ta ce masa Mudi nipa zaman yayana nakeyi in bandan su ba Wallahi da tuni ka manta da ka taba sanina, abun na damunsa kwarai tun yana ji yana hadiyewa abun a ransa yau dai ya yunkura ya sanar dani yana kuma jira yaji daga gareni shin matar tasa tana sonsa kenan? Kuma wane mataki ya kamata ya dauka akanta? Ni dai ya rantse min yace babu wani abu da yake mata na cutarwa sai dai ma tsabar kyautatawa ,wacce shawara ya kamata na bashi? Da dokinta ta shiga rubutun tana juya abun a ranta '' zaman yaya kamar wata kalmar ado ce ko ta panshe takaici a bakin mace lokacin da sabani ya shiga tsakanin su da mazajensu, duk da akwai masu pada da gasken kuma suyi a aikace amma daga matar har mijin basu kula da hatsarin da suke ciki na gaza sauke hakkokin juna lokacin da suka ki daukar mataki akan kalmar ba da yake tapi ganin laipin matar , ta tashi nata sharhin sai tace. ' mata pa akwai kwakwazon korapi, tare da gaza hakuri in an kwatanta musu irin sa na tabbatar duk matar da mijinta yace mata don 'yayana nake zaune dake. Mawuyacin abu ne wannan auren nasu ya dore saboda yadda zata tattara kauna ta yanke masa. Ta pito ta cigaba da bun ragowar labarun da marubuta suka aiko, tayi tsokaci (comment) a wanda take muradi tayi jinjina (like) a wadanda suka burgeta. Ranta ya para haske kirjinta ya dan samu sarari dama zan kapin mahaukacin masori ba karamin kaye da sanda nishadi duniar marubuta ke bata ba. Ta bar nan ta tapi dandalin masorya jaridar Aminiya, zababbiyar jaridarta kenan tun kapin ta zama marubuyarsu saboda haka ita ma wata ginshikice a padada mata zucia, jakar sakonninta (inbox) ya rika kuka ta duba akwai wulgawar sakonni kusan goma a ciki. Kamar zata share su ba tare data duba ko daya ba kasanwewarta marubucia bugu da kari kuma mace wada bata tsallake neman maganar maza marasa mapadi a fb, amma da ta tuna kila akwai wadanda zasu iya dangantarta a masu sakon yan uwa ko abokan aiki da kawaye sai ta tapi inboz din kamar yadda tayi tsammani ta tarar sakon yayarta Balaraba, wadda ke paman yi mata mitar taje Abuja taki zuwa gidan ta kuma ta tsiri wata muguwar dabi'a ta kashe wayoyi , ta amsa mata da ban hakuri da alkwararin share mata hawaye, tana barin Balaraba taci karo da sabon sakon Mahaukacin masoyi Username dinsa kenan Mahaukacin masoyi. Zuciyarta ta para bugawa pat-pat amma da karpin hali ko karanta sakon batayi ba ta tapi bincike bangonsa (wall) abun da ta tarar bazai mata ampanin komai ba sabon acct ne haihuwar shekaran jiya, babu komai a cikinsa na dorarwa, adireshin ma banda suna babu komai bude, bata tsawaita wani tunani ba ta toshe shi yadda bazai sake sa ido a kanta a fb ba cikin jin karpin gwuiwar abun da tayi taci gaba da harkokinta tsawan awa daya. Tana shirin sauka saboda lokacin baccinta yayi ta koma inbox saboda tunanin kar ta bar sakon da suka kamata sai kuwa taci karo da sabon mahaukacin masoyi mai karin I a karshe, wato mahaukacin masoyii shaidar ya harbo jirginta ya kuma dana mata wani tarkon, na para mamakin yadda kike son bude kwanji ki guje min duk da ban bude nawa na para sonki da yanke kaunar rabuwa dake ta dalilin wani abu ne mai sauki na. Idona a kanki yake Rumaisau ki daina wahalar da kanki da tsammanin zaki iya kubce min, wannan wani irin zalunci ne don Allah? Kin kashe wayoyi saboda ni, na share wannan takaicin kin shigo dandalin sada zumunta na cika da doki na biyo ki amma kawai dan rashin adalci sai ki kulle tsakanina dake? Ki daina tsammanin zan yarda da wannan.. Bata ko karasa karanta sakon ba tayi baya a guje ta pice daga fb din sannan ta kashe na'urar gaba daya ta bige da rapka tagumi. Ta tabbatar da kanta in ta kai karshen sakon kila mahaukacin masoyi ya pada mata kalar kayan da ke jikinta da irin yanayin zaman ta nan rudanin a yanzu ne ta para ji a ranta ya kamata ta san waye mahaukacin masoyi. 31/1/2013 tana zaune a gida dab da azahar mubarak autan hajia ya kirata a waya '' anti kin pita binciken da kika ce zaki? A tausashe tace A,a mubarak, wani abu ya paru ne? Ya amsa a ladabce yana daria . Babu abun da ya paru dama neman alparma zanyi ki karaso nan B.U.K ki dauke ni na bada aron mashin dina kin san kuma hana goyon nan ya janyo karancin abin hawa. Tayi yar daria tace ban pita ba amma bari nazo na dauke ka yace godia nake anti amma dai a dan gyara laipin aron babur din da na bayar. Tace masa karka damu. Cikin sauri ta debi wayoyinta da tun hantsi ta kunna take jiran sakon mahaukacin masoyi wanda tayiwa tanade tanade marasa lissapi bai kira din ba, har ta sallaci azahar ta dawo da tsakkamin zata tarar da sakon sa nan ma shiru, har zuwa lokacin da mubarak ya nemi agajinta. Hajia taimaka ki ara min mota in dauko mubarak. Ta samu hajia a palonta ta pada mata haka tana yar daria hajia tayi mata kallon tsab ta ce a.a kiyi daria da kyau. Kina pama da kanki zaki je wani dauko mubarak? Ina babur din sa? Kai tsaye ta amsa yayi paci yace min ya rasa mai liki saboda matsalar masu gyaran sannan ga kwarancin abun hawa a gari, shine sai ke zaki dauko shi? Ta wuce kan talabijin ta dauko makullun motar tana cewa to yaya za ayi hajia? Nima ina son ganin wulgawarsa a gidan tun sape bakina ke tsami ba abokin hira. Hajia tayi daria tace Allah ya bada sa'a Allah ya kiyaye hanya. Tana picewa ta amsa Aamiin hajia ta sauke kai tana girgizawa xuciyarta cike da tausayin Rumaisau tattausar mace mai kirkin gaske amma Allah Ya kaddaro rayuwarta cikin jarrabawarSa. Bata taba jin wanda ya zauna da Rumaisau ya padi rashin kirkinta ba duk kuwa wanda yace batada kirki da zarar ka dube shi zaka ga rashin kirki a puskar sa. Tun kapin ta shiga makarantar tayi kiransa a waya Mubarak karpa na shigo ka cika min mota da abokanka inba haka na karka kuma taso ni zuwa daukar ka. Yana daria ya amsa na san da haka shi yasa ma na ware gepe. Tace dashi cikin daria aha! Ka shirya na shigo. Yace amma akwai yan uwan ki mata nasan... Yaki karasawa yana daria ita ma tayi dariyar tace babu matsala. Tana shiga ta ciko mota da Mubarak da abokan karatunsa mata, sai wani nataccen abokinsa shau'aibu da ya matsa sai an dauke shi har yana cewa Rumaisau, anti in ma ba zaki dauke ni ba sai na daura dankwali kona yapa gyale, sai in ara cikin yan matan nan bazaki rasa mai spare a jaka ba. Dole Rumaisau ta yi daria tace mai yayi zapi? Shigo mu tapi. Ta hada su a gaba shi da Mubarak ta tashi motar yayinda wasu tunanuwa masu nauyi suka wulga a zuciyarta, tunanin da ke pawar sa ta kukan jini inda anayi duk da ta san akan su tana kukan da yapi jini ciwo. Haka ta tashi motar ta pice a guje tana satar kallon wurare a makarantar, wadda ta kasa hadiye wa sai da ta para zubar da hawaye, sannan ne mubarak ya tuno katon kuren da ya tapka, yayi saurin dora hannu aka ya kame baki yana satar kallon titi cike da nadama. Ba yau ya para gayyato rumaisau tazo daukarsa ba amma yana sane da yadda matsayar dalibai jiran shigowa bus a nan makarantar ke zama wani katon abun pami a raunin Rumaisau, dan haka sai ya kan yi gaba su hadu a hanya ta dauke shi su pice ko zatayi hawaye kadan ne. Saboda haka ne ita da Mubarak suka yi dip a motar, matan baya keta hiranrsu , shu'aibu da ya rasa abokin hira yake saka musu baki, Mubarakk ya rasa bakin bawa Rumaisau hakuri ita kuma ta kasa daina zubar da hawaye har suka pito makarantar suka hau babban titi. Mubarak dubo min gilas dina a jaka. Rumaisau ta pada dan tsananin kaunar ta manta abin dake sata hawaye da kunan zucia. Cikin doki mubarak ya dauko jakarta yana cewa inaga dai anti gayyatar karshe na miki ta zuwa ki dauke ni indai ranmu zai dinga baci haka ta karbi gilas din tana dariar yake tace ko baka gayyato ni ba mubarak inna surantawa kaina makarantar nan inayin abun daya pi haka, gara ma ka dinga gayyato min ina zuwa kila na saba da kallonta gwauruwar ta... Ta kasa ci gaba da magana saboda kukan da ya toshe mata makogwaro ta bige da bude gilas kawai ta saka sannan ta hadiye kukan. Motar tayi tsit har suka kawo mahadar tituna na kabugam yanzu ta hakura da kukan duk da karpin hatsi tasa masa amma dai yabi umarninta ne da taimakon hango wasu mata biyu datayi suna bara a tsakanin motoci. Matan ba wai tsoppin almajirai da ido ya saba gani ba, a'a matasan mata yan shekaru ashirin da biyar zuwa talatin kuma abun da yapi shayar da takaici shine da yanayi irin na mazan da sukayi kaurin suna wajen hawa gajimare ( shaye-shaye) bata magana cika jakar mamaki da alhininta ba sai ga su gabanta dayar zuro hannu ta rike sitiyari tana layi, Hajia ki taimake ni kamar yadda Ubangiji Ya miki sutura ki bani na siye abinci da dan hayaki... Dayar kuma ta cape da cewa bata wulga ta kantaba... Kina hada mutum da Allah baya nupin an rasa yadda za ayi in motar nan cancakar naso sacewa na rantse yanzu zan muku rupa ido in dauke shi.. Ko ba haka ba? Suka dubi juna ita sa su Mubarak zai yi magana ta hana shi dayi masa inkiyar ya bude mata jaka amma sai ya kankame jakar ya juya keya ta pahimci manuparsa saboda jaka tayi yar daria ta dube su da kyau tace aini ma da na ganku murna nayi da Allah ko yar naira shirin ce ku bani goro zanci. Nan da nan kamar walkiya suka bace daga gare ta, duk motar kowa ya rude da daria lokacin da suka sami hannu suka wuce. Shu'aibu yace anti yaya akayi kika san mashayan nan ba sa son a roke su kudi? Tana daria tace ko daya, na san wanzami baya son jarpa, amma dai nayi mamaki in labari aka bani shayeshayen mata ya kai matakin pito da su kwararo da dabi'u irin na yan daba, Wallahi karyatawa zanyi.. Amma sai idona yaga zahiri.. Shu'aibu ya tareta da padin anti ai gara wadannan da ganinsu kin san dama sun gagari iyayen su ne akwai wata budurwa a anguwar mu bazan iya kirga sau nawa na ganta a make ba, na sha kamata na kai ta gidan yayata a tsare ta yapi a kirga, ina mata gudun batagari su cimma wata mummunar manuparsu akanta. '' Innalillahi wa innan ilaihi raji'un. Rumaisau ta pada cikin kololuwan bayyana takaici da alhininta sannan ta dubu mubarak tace mubarak ko akan shaye shayen mata zanyi batuna a wannan watan ne.? Good! Wannan zai kayatar kuma zai padakar. Zaka taimakeni da bincike kenan? Ya amsa mata da karpapawa, babu matsala yau zuwa gobe ina cikin yanci. Ko baka cikin yanci ma naga ai kana dagawa kayi aikina. Ta pada ba tare da ta dube shiba da yayi dan nazarinta sai yayi daria yace Allah ya sa ban kauce hanya nayi kuskure a magana ta ba. Tayi daria kawai, shuaibu yace ka kawota gidanmu taga yarinyar danayi maka maganarta idan tana da bukata. Cikin sauri Rumaisau tace mai zai hana? Idan babu damuwa muje gida kuci abinci sai mu pito tare. Ok babu matsala inji shuaibu, mubarak ya dora da cewa sai kuma ina? Tace da sape ka raka ni freedom nayi cigiyar hajia Maryam (Maryam Babban suna, ina gaida duk mai suwa Maryam , (Dan Aunty) ) 1/2/2013 ta wayi garin ranar yau da kumajin datajima bata tabadarwa kanta shi ba har ga Allah tanaji a ranta sunyi hannun riga da Mahaukacin masoryi tunda dai gashi kwana 2 kenan babu sakonsa a waya saboda shi ma ta kara lokutan hawa fb amma ya bacewa ganinta wannan ba karamin dadi ya yiwa ranta ba ta shirya karasa watsar da shi da tunanin yadda zata gungura rogowar tsumman rayuwarta data ke wa take gawa taki rami . Ba kamar yadda ta so ba wato zuwa freedom tare da mubarak sai Alhj ya bashi wani aiki na wakiltarsa daurin aure garin katsina, a ranar juma'ar da jiran bikin nadin sarauta a washegari asabar, wannan yasa ita kadai taje freedom bayan an sauko masallaci. Bata sami ganin hajia Maryam ba kan abin da yakai ta, sai dai ta samu garantin ranar samunta, bata dawo haka ba sai da ta shiga sashin labarai neman ji daga wanda ya kawo wani rahoto game da yadda wata yar maye ta dabawa wani matsashi wuka. A ranar yau Rumaisau ta kara godewa Ubangiji da Ya jukuntota a mai son bincike dayin rubutu game da abubuwan da zasu ampani al'umma, saboda yadda take haduwa da ayoyinsa iri iri masu kara mata tsoron Allah da goge maSa, da kuma masu sanyata gudun yi maSa butulci da daukar sabonSa ba a bakin komai ba. Tana freedom radio akayi sallar la'asar dan haka kapin ta pita sai da tayi alwala ta shiga masallacin mata tayi sallah. Bayan ta idar ta bude jaka ta hau goge gogen puska da gyara daurin kallabi ta gama tana mayar da kayan jaka taken shigowar sako ya kasa a wayarta,.da karpin hali irin na dan daudun daya kamo kadangare ta capko wayar ta para duba sakon. ''Rumaisau ban kasance ma'abocin sauraron wakoki ba amma abun mamaki wata waka ce yanzu take gilmawa kunnena wadda ta motsa min dubun taki kaunar a makoshi na, kin san wakar? Itace wakar YAR MAYE. Wakar ta shige ni! Ta sani tsausayin kaina piye da tausayin matan dake je pa kansu a haln shaye-shaye, saboda na san giyar kaunarki ta make ni piye da yadda ko wanne irin kayan maye ke make ma'abotansa. Idan kin taba nazari akan yan maye ki zace ni da kalar tsausayi piye da yadda kika san su, mahaukacin masoyi. Tayi iyakar kokarinta wajen hadiye rudaninta saboda wasu mata biyu dake salla gepenta kuma wannan dakewar tata xe ta bata samar yin wani tunani na zaton duk yadda akayi mahaukacin masoyi akwai kapar da yake samun labaran halin da take ciki ya turo sakonsa a kansa in dai shi ba junnu bane. Bata tsawaita tunani ba bare ta samo abun da zai kore mata wanda ya gaskata ta para latsa wayarta ta kira Mubarak. Mubarak wa ka sanarwa cewa zanyi rubutu akan masu shayeshaye kuma waka sanarwa zuwa na freedom? Mubatar ya jima yana jan numpashi kapin ya amsa mata anya nayi maganar da wani? Kusan mapa Wallahi na manta maganar tun jiya da muka je unguwar su Shuaibu. Tayi ajiyar zucia ita ma ta jima tana jan numpashi sannan tace Ina shuaibu? Yace munyi waya dashi yau da sape yake cemin yana kwance a gida saboda ya gamu da masassara (zazzabi), wani abu ne ya paru? Muryar Rumaisau na rawa tayi saurin girgiza kai kamar yana gabanta a'a babu komai kanajin babu wanda zai iya sanina wajen shuaibu har ya bashi batun ina bincike akan mashayan mata? Nan ma Mubarak ya ja pasali sannan ya amsa anya ina tantama wai me ya paru ne? Tayi dariyar karpin hali tace ok babu komai yaya katsinan? Ina patan kana shirin ganin gari? Mubarak ba dan ransa ya so ba ya yarda da wannan ninkuwa bai bai din da tayi masa ya amsa a sake sukayi sallama suka ajiye wayoyi. Tana daukar mota ta pigeta sai Dawaki road gidan Hafsat yayar Mubarak, wadda take tsararta kuma tare ma sukayi yammatancin su . Hafsat da tsohon cikinta ta karbeta cike da mamaki . Rumaisau bata irin wannan ziyarar ta bazata to yaushe ma ta ke son zuwa gidanta duk irin shakuwar da sukayi? Suka zauna apalo Hafsat ta sa aka cikata da kayan sanyi amma ko kallon inda suke Rumaisau taki yi. Tayi nazarin agogo sannan ta sauke ganinta akan Hafsat tana padin Hapsat wata almara ke paruwa dani, shine na daukota na kawo miki mu tattauna akanta, a gaggauce saboda kin san babu lokaci. Hapsar ta gyara zama idonta akan Rumaisau sai dai bata tanka ba. Ta budo sakonnin mahaukacin masoyi tun daga parko tana mata bayani tare da yanayin da sakonnin ke samun ta, har Rumaisau ta dire wa hapsar ta dauki abin, dan daria kawai ta ke tuntsira mata sai da ta ga ranta ya baci ne ma sannan ta dawo ta saurare ta . To wai ke me kike zato? Rumaisau ta dan harare ta. Idan na zata mai zai kawo ni gidan ki? Da ba sai nayi zamana nayi hukunci da zatona ba? Hapsat na kunshe baki tace Allah Ya baki hakuri amma ni nayi zargin ko a makaranta shapinki na jarida ne wani ya boye yake wasa da hankalinki haka? Rumaisa tayi saurin girgiza kai tace kuma a lambobin wayata wadda bana hulda da kowa sai dangina salonninsa na parko pa a layina dan alkawari yayi su layin dako layika na cin amana shi dai bai kamata yaci ba, hapsat ma bata son tsawaita wannan maganar akan layi dan ta san makoma abin. Saboda haka tayi saurin tare Rumaisau da cewa anya kuwa ba Yusha'u bane? sai kawai Rumaisau tayi zuru tana kallon haprsat kamar wadda hankalinta baya jikinta tace ko a tatsunia bai kamata kiyi zaton yaya Yushau ba, me ya ani da yaya Yushau zai bata lokacinsa a kaina? Ko kin manta ne ? Ai ko a layin mutane nake zaton mai turo min sako bai kamata ki kawo yaya yshau ba. Hapasar ta rausaya kai cikin sallamawa tace haka ne wai dama da ake zargin mai wayar a cikin dangi.. A dan kupule Rumaisau tace ko mun rage mu biyu daga ni sai shi ya kamata in pita waje neman mai turo min sako. Hapsat tayi shiru saboda rashin abun cewa, kamar amsa ga abin da sukayiwa tagumi suna tantama sai ga taken shigowar sakon mahaukacin masoyi.. Rumaisau na dubawa ta gashi ne, sai ta mikawa hapsat wayar ba tare data karanta ba. Ta mike da hannu dunkule tana dukan hannun hagu tare da pareti a palon. ''Rumaisau akace mutun mutun gida ne da rabin mutun da wanda ba komai ba, wanda yake mutun shine mai yin shawara da al'amuransa, kuma mai ra ayin madaidaici wanda yake rabin mutun shine mai shawara amma bashi da madaidaicin raayi ko kuma yana da madaidaicin raayi amma ba shawara, wanda yake ba komai ba shine mara shawara, kuma mara raayi. Wani babban sahabi yace mana ''kuyi shawara da mutanen kirki na gama yi miki sanin raayi madaidaici wato tuni na san cikar rabautarki ashe ke guda ce naji a raina kina son kiyi shawara akan harkar soyayyata haka ne? Ina sauraron abunda hukunci zai yanke min, mahaukacin masoyi. A pili Hapsat ta karanto sakon, zuciyarta na harbawa , hannunta sai karkarwa yake ... . GORAN DUMA 4. . . a pili Hafasar ta karanto sakon zuciyarta na harbawa, hannunta sai karkarwa yake idon ta cikin na Rumaisau bakin ta na rawa tace da wa kikayi zancen zaki zo neman shawara a gurina? Babu tsoro a puskar Rumaisau ta kebe baki tace da harshena dai ban pitar da sautin zan nemi shawarar wani ba dazun nan a freedom na zanta da zucia ta ina pitowa kuma kai tsaye na nupo gidan ki. Mun shiga uku, hapsat ta pada tare da wurgar da wayar a dan tsorace cikin jikinta yasa da sauri Rumaisau ta isa gareta ta ruko kapadarta tana daria matsalata dake tsoro Wallahi, baki san babu abin da zai iya samun dan Adam ba sai abin da Ubangiji Ya kaddaro maka ba? Bana tsammanin wani katon Al'amari cikin sakonnin mahaukacin masoyi, kawai dai na gajia da bacin lokataina da tunanina ne wajen wassapa shi yada sakonninsa. Hapsat tayi kasake sai nan take ta dawo hakalinta ta mika hannu ta dauki wayar ta sake duba lambar, nan take ta dannan maballin kira, ta gama bincike dab da zata shiga sai ta katse, kusan sau goma tana gwadawa hakan na paruwa a karshe ta kwape lambar a wayarta ta jira nan ma hakance ta paru suka dubi juna kowacce puskarta da jarumta tace ina horonmu da addua da mayar da lamari ga Allah Rumaisau karmu raya wani mugun abu a cikin sakonnin nan mu kwantar da hankali mu kuma dauke su ba komai ba ki bani kwanaki biyu nayi wani dan bincike idan kin amince zan sanar da sani. Rumaisau tayi saurin girgiza kai ban amince sani yaji ba kin san sanida surutu maganar tana iya zuwa kunnen su hajia ba tare da mun shirya mata ba, cikin saduda hapsat tace hakane amma dai surutun sani mai maana ce ki daina suppanta shi da wani aku... Ta kare da zolaya duk kuma suka yi daria suna pitowa harabar gidan suka ci karo da sani mai gai ya wangale masa kopa ya shigo. Suka tsaya jikin motar da Rumaisau tazo da ita suna jiran karasowar sani . rumaisau ta rungume hannu a kirji tayi puska ma'ana ta shiryawa shegantakar da sani mijin hapsat zai zo yayi mata, tunda ya saba, lallai kuwa idon masu hidima da ke karakaimar yi masa maraba da xuwa bai tsure shi ya kasa girgije su ya nupi su kai tsaye ba. Hapsat na dan boye puska tana satar daria tayi masa sannu da zuwa hankalinsa na kan rumaisau yana mata kallon sama da kasa a karshe yace a'a yau mutanen zuhdu ne suka tuno da mu? Ta tuno da ita dai Allah Ya sani ba dan kai nazo ba. Ta tare shi tana nuna masa hanyar wucewa ya tuntsire da daria yace matsalata dake kenan sai ki dinga dagewa sai kinyi pada kuma da yake ba dabiarki bane sai ba yayi miki kyau har tapia ke nan. Bazaki zauna mu gaisa ba gashi naga puskarki da abin karatu... Wannan kalaman nasa suka sata daria kawai ta bude kopar mota ta shige suna dan barkwanci har ta pice... Ta tattara duk wata sabga da zata iya dugunzuma mata hankali a ratuwarta ta watsar, in sako ya shigo wayarta ta daina budo shi inta hau fb ta share inboz sai komai nata ya dawo dadai. Sati daya a tsakani sai mahaukacin masoyi ya dawo kwado mata kira a waya da parko share kiran ta dingayi amma daga bisani sai ta yanke shawarar ta daga wayar suyi ta ta kare ita da mai kiran, amma idan ta daga sai iska shuuuu... Babu motsin murya sunyi haka ya zarce sau goma a karshe kawai sai tayi blockin din layin sa gaba daya a wayoyin ta ba tare da jin cewa zata yi nadama ko kaico ba. Sati na biyu akayi rasuwa a kauyen su Rogo hajia nada ganawa da liyitanta a Egypt daidai wannan lokacin bisa larurar ciwon sugar da take pama dashi, alh kuma tare dasu tapi saboda haka ta wakilta Rumaisau taje gaisuwar. 16/02/2013 tana zaune cikin yan uwa a gidan gaisuwar har bayan sallar azahar sannan ta tapi gidan Goggonta karpe uku take jira ta karasa ta dauko hanyar dawowa gida saboda haka ta kimtsa komai tana zaune kawai. Goggonta ta shigo tana mata wani irin kallo sannan tace Yushau bai san ke hajia ta turo ba sai yanzun nan nake pada masa. Rumaisau ta daidaita maganae goggo a memory dinta amma ta rasa gane ta inda maganar ko wani abu a cikin ta zai ampaneta, saboda haka ta hadiye a sanyaye tace ashe yazo? Goggon ta amsa mata eh tun sape yana nan ai ina tsammamin ma ya riga ki zuwa. A dai ci gana da hakuri Ubangiji Yana son bayinSa masu hakuri, rayuwar dai kina ganin yadda take hutsirewa kana tsaka da kara mata burika, wadanda kake kokaawar imma a sannu ko wadanda kake son sawa karpi rauwar Garbati nan ta isa mutun aya Ruma, shekaru goma sha shidda bai leko gidan ba yana can kudu da kyar akayi masa kiranye ya dawo gida anata parin ciki da murna har anyi masa matar aure kinga duka duka bai hada sati 2 da dawowarba Allah Ya karbi abinSa , ai wannan gudun dunia wajibi ga mai son cikawa da imani rumaisau jinta kawai take ta san waazi take mata abin da take waazi a kansa ma ta kasa tantancewa musamman da yake akwai batun yushau da aka yi shimpidar waazin a kasan ta kasa gane me goggo take son nusassheta akan hakuri da yushau, wanne tawaye take da bukatar ta yi hakri akan sa? Amma dai da yake baya da jayayya sai ta rausaya kai tace Allah Ya samu cika da imani. Goggo na amsawa hakan yayi dadai da shigowar Yushau cikin daikin puskar Rumaisau babu yabo ko pallasa ta taishe shi sannan ta mayar da hankali akan wayarta, tana dube dube goggo ta sa musu ido a pakaice yushau na satar kallon rumaisau yace nansan bada mota kika zo ba ko? Ta dago sarato tana kallon sa amma yanayin puskar hakurinta ta hana a gane yadda ta karbi batun muryarta na rawa tace hakane motar haya na hawo. Yadanyi dariar da yake tunanin zata sami matsuginni a zuciyarta yace aina sanki da tsoron tukin daguwar hanya. Ta share daria da batun nasa hanyar muyar da hankali a wayar ta tana nazarin sakonnin makaranta rubutun ta a jaridar Aminiya, karpe nawa zaki tapi? Ya pada kamar bai damu da yadda ta share shi ba ta dago agogon hannunta ta duba ba tare da ta bude shi ba tace ina jiran karpe uku ta karasa ne sai na komai shima ya duba agogon yana padin nima ita nake jira sai mu koma tare ta danyi kasake bukatar tasa na mata kururuwa a kwakwalwa sai pamar kwakwalwar cetayi aikin da zuciayar nata ta kasa, wato ta girgiza kai tace nayi alkawari da dan mashin zai zo ya kaini tasha, kai tsaye ya amsa mata sai na biki na dauke ki. Bai jira cwarta ba ya pice abinsa. Sararo ta hada binsa da kallo da sauraron wayarta mai take shigowar sakon murya, sai da ya pice ta sauke idon akan wayarta cike da rudani da mamaki shakarunta nawa da yankewar samun sakon murya a waya.? A lokacin da take samun sakon wayar ma daga wani muhimmin mutun ne a duniyarta. Wasa! Tana budewa sai ga lambar mahaukacin masoyi kawia sai ta mike ba tare data shawarci kanta ba , goggo ta dan bita da kallo ita kuma ta tsawaita muryarta tace goggo yau na manta banje hawa dutse ba, mintina ashirin bari naje na dawo. Goggo da yake ta san rumaisau da maganar son hawa dutse bata zargi komai a ranta bam ta santa duk sanda tazo ta kan ware lokaci ta shiga daji ta hau dutde shi yasa yanzu ta amsa mata da cewa ai da yake ba zuwan nustuwa yau kikayi ba kiyi sauri to ki dawo kije gidan gausuwar kizo ku tapi kar ya gaji da tsumayinki ya tapi. Ga yamma ga wahalar mota kinga babu dadi. Rumaisau na kokarin picewa tace idan ya gaji da tsumayi kawai yayi tapiyarsa dama ina da ajandar kwana idan hali yayi. Goggo bata samu amsa mata ba ta kule. Ba zata iya tantance yadda akayi ba ta isa wajen dutsen ba, ta sulale a sanyaye ta haye samansa sannan kamar yadda ta saba ta siga juyawa a hankali tana hango karshen gari (harizone ) wannan aladar muhimmiyar gaske ce a rayuwarta dan ta kan kara mata imani da tsoron Allah wanda Ya halincci wannan makekiyar duniyar da take zagayawa a cikin ta, duk kuma da girman nan nata sai ta zama bata isa abin iya kallo ba cikin abin da Ubangiji ya halitta amma sai ya kebance ita kankanuwar duniyar d niimomi masu tarin yawa, Ya karrama dan Adam a cikin ta sannan Ya bashi zabin makomarsa a hannun sa, a cikin ta aljanna ko wuta, wanda yabi Allah cikin ta yayi kunci a gare shi to muminancinsa ya bayya na, wanna ya ki yarda da AllantakarSa ko ya zama pandararren bawa to tayi masa yalwa rabonsa kenan. A yanzu hawaye ne ke diga a puskarta ba kuma wannan karatun kadai ya sanyata hawaye ba har da tuna yadda duniyar nan ta shude mata da mutun muhimmi a cikin ta, kamar yadda ta tabbatar ita ma wata raba zata shude. Rauninta kuma ke raya mata ba zata taba samun wanda zai maye mata gurbinsa ba, wannan tunanin ne ya pado mata da na sakon mahaukacin masoyi, a rikice ta zauna dandamalin dutse ta dauko wayarta a jaka cike da doki hannunta na karkarwa ta danna muryar... Rumaisau kin taba nazari akan zucia? Harumin gaske ne ke rike akalarta ya ja sabanin ta jashi, tawa zuciyar kamar ni take ja. Ma'ana ban cika jaurimi amma na kasa yarda ni rago ne dan na rike hujjar zuciyata na ja ne ga alkhairi ne wato ke. Zuciyar tawa na da karpin hali ko? Bana ganin bakinta ni kuma dan ta gamsu kin hada dukkan alkhairan da idan anyi paputuka a kanki ba a sarayar da lokutar a wopi ba, dan ma duniar nada abun tsoro ko? Gangancin shigar haske cikin duhu da shigar duhu cikin haske ya isa kada zuciyar mai imanin mutuwa wadda bata bukatar imani cikin sharudanta, ga wanda ya yarda da ita da wanda bai ma yarda da ita bam duk ba wanda take ragewa duk sanda na yi tsaye cikin lambu ina kallon sararin samania sai na cika da shakkar anya kuwa ozone layer da akce yana kekkecewa ne yake kara gudun dunia ba waccan mutuwar ke kusatoni ba? Duk sanda na tuna haka sai nayi kwalla ina ganin kamar zanyi mutuwar da babu gata, wato wadda na ke so bata yarda ina son ta ba. Mukwana lapia. Bata gama tantance matsayin da zuciyarta da azancin ta suka karbi sakon mahaukacin masoyi na yanzu ba ta hanga yushau ya nupo ta kai tsaye yana ta sauri kamar mai shirin tashi sama.. Ambaton MUTUWA wadda take da kishiyar rayuwa asakon mahaukacin masoyi ya sata kallon Yushau na tahowa garau! Saboda tunaninta da yake son tino rayuwar ta ta baya. Yau da gobe a rayuwarta. Mutuwa a cikin rayuwarta. Kaddarori marasa dadi na rayuwarta. ASALIN RUMAISA'U. Mahaipin ta... . in shaa Allahu gobe zamu ci gaba daga inda muka tsaya.. . Dan AuntyGORAN DUMA 5 . . ASALIN RUMAISAU Mahaipinta Aliyu Ahmad dan karamar hukumar Rogo ne a kano. Mahaipiyarta Khadija inyamura ce mutumiyar Enugu wadda ta musulunta a hannun mahaipinta sukayi aure da zama a garuruwa daban-daban kasancewarsa dan sanda. Mahaipinta dan dangi ne sosai a kauyen Rogo da cikin garin Kano duk da cewa su biyu ne kacal a gurin nasu mahaipan wato shi da kuma yayansa Usman mahaipi ga Yusha'u da kannensa mata hudu sai Mubarak auta, mahaipinta da mahaipiyar ta akwai zama na soyayya da pahimtar juna mai kwari a tsakanin su, Allah bai wadata su da iyali masu yawa ba daga yayarta Balaraba (Aisha) sai ita auta har a halin yanzu wajen uwa da uba. Bayan rauni na kasanxewarta a jinsin mata masu rauni sai wata jarrabar Ubangiji Yayi mata na kasancewarta daga masu pama da larurar nan ta sankarar jini (sickle cell ) cutar da gatan da iyayenta ke nuna mata bai hanata tasowa cikin wata irin mawuyaciyar rayuwa ba , alal alakka sun karbi kaddarar haihuwarta da Ubangiji Ya nupe su dayi suna godia a gare Shi tare da rashin gazawa ko kosawa cikin tarin dawainiya gare ta yadda ya kamata, duk wani sikila ya samu. Iyayenta naji da ita suna tausaya mata suna tattalinta ninkin yadda suke tattalin yayarta Balaraba sun jure duk wani alayi na ciwonta, kai karewa saboda ita innarta ta koma karatu bangaren lapia bayan tayi digirinta na parko akan Na'uwa mai kwakwalwa (computer engr.) kapin aure, bayan sun haipeta da shekara daya ta karkade zaninta ta koma makaranta inda ta karanto wanda ya kara taimaka mahaipiyar kwarai wajen yadda take kula da rayuwar ta. Tayi karatu a tape kuma cikin gata kamar yadda ya kamata har matsayin kammala babbar sakandire ta pito da sakamako mai kyau, saboda haka ta sa ran shiga Jami'ar Bayero ta kano dan karanta aikin jarida. A daidai wannan lokacin mahaipanta zaune a enugu saboda haka ta debo zaman karatunta ba dan son ran iyayen ba ta dawo wajen yayan mahaipin nata Alh Usman wanda ke zaune a kano kuma shahararren dan kasuwa a kasuwan kantin kwari. Daidai wannan lokacin Balaraba yayarta ta auri Mukhtar ma'aikaci a garin Abuja , shima Alh Usman Ya aurar da yayansa mata uku, Atika, asiya, maimuna sai Hapsat kadai wadda take tsararta sannan Mubarak sai ko babban yayan su Yusha'u da ya tasamma zama tuzuru babu aure. Yushau ba a gaban iyayensa ya girma ba tun daga yaye kakarsu ke rike dashi a Rogo har bayan rasuwarta ma sai yaci gaba da zama inda yapi wayo , can yayi firamare da sakandire yazo gidan su kano yayi NCE a FCE kano bayan kammalawan sa saboda sabo da rogo sai ya kuma komawa can ya kama aikin koyarwa amma idon kudi da ya gani lokacin zaman karatunsa a kano yake zuwa kasuwa gun mahaipin sai ya hana shi mayar da hankali ga koyarwar inda bai hada shakaru biyu cikinta ba ya ajiye ya dawo kano yaci gaba da harkokin kasuwanci. Duk sauran kannensa ma sunyi karatu daidai gwargwado na iyakar sakandire suka yi aure, Asiya da Atika da suka auri yan boko sun sami damar ci gaba har sun para aiki, amma Maimuna na zaune a gida da kasuwancinta, albarkacin Rumaisau yabawa hapsat damar dorawa daga sakandiri bayan nacin ta sami B.U.K ta gaza sai ta bige da sa'adatu Rimi collage. Hankali da nutsuwar Rumaisau tare da rashin kuzarinta wani abu ne da sam baya dada yushau da kasa, yana mata kallon wata muguwar shagwababbiya kuma mai shegen raki, wadda yake ganin ba a kanta aka para ciwo ba amma akwai alamar tapi kowa kururuta shi, kullun ita ke nan cikin ciwo da neman uzuri ayadda ta baro gidan su suke kirkirar mata shagwaba da mayar da kai baya haka anan gidan nasu babu wanda ta rage, alh da Hajia , hapsat da Mubarak kuma suka pi kowa taya bera bari a wajen su komai na Rumaisau na musamman ne kai saboda Rumaisau sun hakura da yawa daga jin dadin rayuwar su, saboda Rumaisau Alhi ya cire duk wani A.C a cikin gidan, panka idan Rumaisau na guri cikin su hudun nan babu mai shan iskarta, in kuwa shi ya guntse ido zai kunna duk zasu taso kansa da korapi. Duk wani aikin gida na mata babu ruwan Rumaisau da shi ko ta sa kanta zatai hajia kan hana, abincinta na musamman ruwan wankanta na musammam, duk inda zata pita kuma sai anyi dawainiyar da ba zata yi tapiar kasa ba, ba ta da aikin da ya wuce taci ta sha ta pita yawon makaranta, anjima kuma ta ishe su da rakin ciwo. Ba wannan ne kadai abin da ke damun Yushau akan rumaisau ba, har da matsayin karatunta wanda sam baya kaunar wata mace ta taka matsayinsa, in kuma har ta taka din to yana mata kallon wata gagara kundila a duk wani nau'in halin tsiya. Wadannan dalilan ne suka hana shi iya boye kin da yake wa rumaisau wanda ya hada da hapsat saboda tattalinta ga rumaisau da kuma kama turbar rumaisau na zurpapa ilimin boko. Hakurin Rumaisau da zaton alkhairinta yasa bata taba hasashen yushau ya tsaneta ba, pahimtar da tayi masa kawai shine shi daban ne a cikin gidan mai wani murdadden hali da kake kasa passarawa, yana da pushi yana kuma da halin sauye-sauye, saboda haka ta koyi zama dashi, bata cika nuna shigarta wani hali a gaban sa ba dan gudun yaki bata muhummanci taji haushi, bata daguwar hira dashi , bata neman taimakonsa ko wanne iri, kuma idan hajia ko Alh sunyi masa umurnin kaita makaranta ko asibiti yana paman kumburi ta kan bashi hakuri tare da karawa kanta nustuwa dan kai yaga giggiwarta, amma duk da haka bata tsira ba, akwai wani lokaci da Alh ya sanya shi kai ta taronsu na masu ciwon sikila ya jirata har aka tashi taron, a hanya sun taho yana paman cika da batsewa har ya pashe da cewa '' inda zaka san ciwon nan shipcin gizo ne har da wata kungiyam wai dan tsabar lalacewar zamani ciwon ake wa kungida ko ya san ba ciwon ne ya dame ku ba wata hanyar neman kudi kawai kuka mayar da ciwon. Rumaisau tayi murmushi tana kallon tagar motar kapin da kyar ta samo abin cewa '' yaya yushau kamar yin kungiyar zai pi rashin ta ampani, ni dai tana kara min imani da godia ga Allah wanda ya halicce mu yadda Ya so ba dan kiyayya ba, sai dan Ya zamo jarrabawa a gare mu kawai dai kayi mana patan ya zama mana kappara. Yushau yayi wani tsaki sannan ya tsule bakin sa. Shekararta ta karshe a BUK hapsat ta kammala NCE har ta para aiki, mahaipanta sun dawo Abuja da zama a wannan shekarar ne ta hadu da gwarzon masoyin da take jin har dunia ta nade baza tayi irin sa ba. Ba wai tana rasa masoya ba ne, sai soyayyar bata wani nisa saboda rashin goyon bayanta, ko kuma in sun san matsalarta su kauce. Sun hadu a wata laraba ne tana tsaye a bus stop cikin BUK new site tana jiran motar da zata kai ta old site ita kadai ce tsaye a wajen sai pama take da rikon tapkekiyar lema a hannu, saboda hadarin daya para daurewa, zai iya zubar da ruwa bagatatan, saukar ruwa a jikinta kuwa wani tushen tashin hankalli ne da zai iya motsa ciwonta. Daidai wanan lokacin Auwal Yazo giptawa ta gabanta da motarsa. Tabi motar da kallo cikin tunanin yadda suka kwashe da Mominta a hutun daya gabata. ''Rumaisau da zaki iya tuki a kano sai na sai miki mota, saboda yau da gobe duk sapiyar Allah da yammaci sai na tuno yadda zaki pita ko zakii dawo gidam sai na dinga jin kamar zanyi tsuntsuwa nazo na dauke ki m na san wahalar da dalibai suke sha'' ta dubi mahaipiyarta cike da so da kauna tace momi ai kina min addua in Allah Ya so ba zan tabe ba. Momi ma ta zura mata ido tana murmushi tace duk da haka zan iya siyen motar? Ta kada kai tace in hankalinki zaipi kwanicia ki siya mana... Momin ta tareta da padin to wacce iri kike so pada min idan kudina basu kai ba in nemi taimajon dadinki. Rumaisau tayi daria tace ta daidai kudinki nake so. Momi ma ta sake yin daria tace shikenan zan baki mamaki. Auwal ya kula da kallon da Rumaisau tabi motarsa dashi ta madubi. Kasancewar shi ma ya sa mata ido kawai sai ya taka birki , sannan yayo baya ya risketa, ganin haka yasa ta dauke puskarta zuwa kallon wani gurin daban, tama ajiye lema ta bude jaka ta ciro gilas ta kwama. Auwal data kara jan hankalinsa sai ya bude mota ya puto ya zagayo wajen tana share puska ya dubeta sama da kasa yace '' Mace! mace akwai waskiya, yadda kikayi puskar nan badan naga sanda kika zubo min ido ba in na kwana dubu ina rantsewa babu wanda zai yarda idan nace kin kyasa.'' da sauri ta dago ido ta dube shi sannan ta dubi motar a takaice tace ba kai nake kallo ba...'' ya tare ta da sauri wa kike kallo? Ta nuna masa motar tana cewa gata ai tapi ka kyau. Ya danja da baya baki bude na alamar shan mamaki ya kallo motar tasa sannan ya dubi kansa yana gyara kwalar riga tare da gilashin idon sa cikin daria sosai ya dapa motarsa yace yanzu wannan tapi ni kyau don Allah? Dube ni pa ki gani son kowa kin wadda ta rasa , ni ba dogo ba, ni ba gajere ba, ni ba pari ba ni ba baki can ba, ga idom ga dogon hanci, shape din ba irin na maza , komai yaji pa kar ki bari kiyi asara yarinya. Mota ki kayleta in kina raye sai ki ga kinyi wadda tapi ta... Nipa na ma tsaneta daga yau... Dan kishi ne dani... Yanzu ta daga kai suna duban juna ita dashi kai tsaye bada zummar komai cikin ranta game da shi ba sai game da maganganunsa kasancewarta mai sanyin hali tana son mutun mai barkwanci, ba ta sami abin cewa ba ya rigata da padin yaya naji zaki danyi manejin tapiyar dani? Karon parko tayi murmushi ta girgiza kai kayi hakuri a patar bakina kawai kalmar ta tsaya, bani motarka da kallo amma zahiri ba ita din nake nazari ba, wata duniyar tunanin na tapi daban kasan ana haka ko? Ya kada kai yana murmushi ma sani amma dai kinji nace bana son kisiya? Ta sunkuya tana murmushi ta dauki lemarta ta mike tana padin kodai kishiyi? Sukayi daria su duka ya karbi lemar hanun ta. Zo mu tapi kinga ruwa na shirin sauka kai ya daki puskarki yayi mata lilla. Ta girgizakai tana murmushi nagode kawai amma bana hawa lift. Da sauri ya tareta waya pada miki lift zaki hau? Ke da motarki.. Na rantse zaki iya shape komai a duniata saboda haka kece alparmar tawa ba ni zan zama alparmarki ba. Ta kara dubansa da kyar a sanyaye tace wannan dokin pa? Daga ganin sarkin pawa sai miya tayi...'' ya sake tareta da padin watalila na kalla naji wata kwakkwarar zumunta ta sarkape zucia ta, da na karaso na kalli puskarki sai kawai naji mun zama JINI DA TSOKA daya. Ta sake duban sa da kyau tana daria abin da take ji a ranta game dashi, shine ya iya dadin baki, da bata dandani shekaru da yawa a dunia ba , parat daya zai wapce imaninta. Ta lumshe ido kai tsaye tace bana son bata maka lokaci ko juyar da karramammun kalamanta, gashi ciki dole na zabi daya. Kai tsaye shima ya amsa kin zabi bata min lokacin indai ba kishia ne dani ba, karramammun kalamaina karki wani kalli karancin su, yadda ya kamata su pito a kunnen ki ne, wallahi ban tsara su dan in burge ki ba, zo mu tapi don Allah. Bai jira cewarta ba ya bude mata kopa. Ta danyi jim sai ta kasa tankwabewa ta shiga moyar. Ya rupe sannan yazagaya ya shiga yana mika mata lemarta ya tashi motar,.har suka zo bakin gate kalma daya ta hada su, menene sunan ki? Kai tsaye ta amsa masa Rumaisau Aliyu Ahmad. Yace sunan ki mai dadi, ni sunana Auwal Ibrahin Hadi. Bata tanka ba shima baii kuma tankawa ba har suka zo bakin gate wata iska mai karpin gaske ta taso da alamun yanzu ruwa zai sauke, kirjin Rumaisau ya para dukan uku-uku cikin matsananciyar pargaba ta dubi maza da matan dake tsaitsaye cikin tashin hankali , ta tabbatar duk yadda hankalin su zai tashi bai pice pargabar zasuyi mura ba, ita kuwa in ruwan ya daketa zai wahala batayi ciwon da ya kusantarta da ita da kabari ba. Rage gudun da Auwal yayi yasa pargabar ta karuwa, saboda zaton sauketa zaiyi amma sai taga ya nupi titi zai haura, ta sauke ajiyar zucia muryarta na sarkewa ta dube shi tace da ka taimaka ka dauki matan can nasan baza a rasa wadabda zasuyi hanyar da zakayi ba, za ka sami lada idan ka taimake su. Ya dan ja pasali yana duban titi ba tare da ya dubeta ba yace. allah ya kawo mai taimakon su ni bana daukar mata a motata. Ta dan juma tana duban sa duba na rashin pahimta sannan tace ni ba ka gane nawa jinsin bane? Yayi murmushi ba tare da ya dubeta ba. Kakkarpar alakar da zuciya ta ta kulla dake ya koro wancan kudurin nawa daga naki jinsin, kin zama yar gida a zuciata da duk wani abu da na mallaka. Ta gaji da kallon sa ta kawar dakai . Ruwa ya para sauka da karpuli cikin sauri ta balle jakarta ta puto da rigar sanyi ta saka tana kumbiya-kumbiya. Bai tanka mata ba amma dai hankalinsa na kanta duk da idonsa na titi, tana bayyana alamun jin sanyi amma kawaicinta ya hana ta zuge gilashin bangarenta, kuma da hakan yasa yayi mata aikin da ta kasa yana cewa na lura kunama ce ke, kawaicinki kuma na son hanaki abinda kike so... Tayi yar daria ta amsa nida na zo ci rani har ga Allah bai kamata in zake ba. Ya watsar da wannan batun nata yace ina zan kai ki? Tayi dira-dira alamar canki-canki sai ta kasa zabar gurin zuwa tayi shiru kawai sanyi na kadata. Hankalinta yayi gida amma ta inda zata bi taje? Ina zata pake ta sami motar? Ya juyo yayi dan nazarinta cike da mamaki yace ina zaki je? Muryarta na rawa tace ai na kasa zaba ne, bana son sanyi, ruwa in ya dake ni illa yake min, da makaranta zanje amma na pasa saboda sanyi, yanxu inka sauke ni kapin na samu motar ma ruwan yayi min abinda yaga dama. Yaci gaba da kallon ta cikin nazari bai pahimci abin da yake son pahimta ba ya kada kai yace nima ba zan iya ajiyeki ruwan ya dake ki ba, ina da ganawa karpe uku sai dai ayi min uzurinta, inane unguwar ku. Muryarta taci gaba da rawa saboda laipin da takejin zata yiwa kanta da gidansu, a ganta saurayi ya sauketa kamar zubar da mutunci ne, amma kamar wannan zabin zaipi dukan ruwan. Na gode Allah Ya saka maka da alkhairi, a Gandun Albasa nake. Yace hanyarmu daya kenan ni a Na'ibawa nake, ziyara na kawowa wani malamina shekaru na biyu da barin makarantar nayi digirina na para aiki a karkashin gwammanti, ya kamata na ajiye iyali Allah bai kawo ba sai yai Allah Yayi min katarin daura damba, Rumaisau tayi dip kamar ruwa ya cinyeta tausayin kanta ne ya hanata nazarin amsar da zata bashi taji kaunarsa a ranta, sai dai taki yarda irin kaunar da take dorewa da aure ce, kauna ce kawai irin wadda dan Adam ke wa wanda yake zaton mutumin kirki ne ko kuma wanda yayi ma alkhairi? Tayi sararo tana kallonsa kawai yana jin kallon da take masa a jikin sa, amma ya hadiye ya juya ya kalle ta. Ta juya a hankali tabi tagar da kallo tare da sauke ajiyar zucia ba tace komai ba. Bakida abin cewa akan abin da na pada? Ta girgiza kai a nuste tace kar ka batawa kanka lokaci nasan ban cancanta zama iyali ba. Yayi saurin yi mata duban rashin pahimta amma ya takaita azarbabi wajen ce mata Ai ina tsammanin ba ayin komai babu hujja ko? Ki pada min dalili dan duba na gani. Ta muskuta tace dashi don Allah kayi hakuri. Yayi kasake yana kallonta sannan yace indai ba laipi zanwa Allah ba to bazan iya hakura ba... Ta tare shi da padin ina patan nan gaba ba zaka zarge ni da rupa-rupa ko yaudara ba? Ya ki daukar maganarta da muhimmanci ba tare da nuna damuwa ba yace ina saka rai alkhairi ya biyo baya, idan kuma akasinsa ya samu zan dogara ga Allah, amma ki sani idan akwai laipinki ciki Allah ne baZai barki ba. Musamman da yake a rupe kike ba ni uzurinki. Tayi shiri kawai shi kuma ya share maganar ya shiga tambayarta karatu, da wani abubuwa da yake jin suna da muhimmanci a cikin alakar da yake son kullawa da ita, cikin ikon Allah suna wuce Gadon kaya babu ruwan babu iska ko hadarin ma babu saboda haka taji ranta ya apu da son ta sauka ta hau motar haya ta karasa, amma ta kasa yi masa magana har sai da aka kira shi a waya ana nemansa wajen taro ya bayar da uzurin sa yana sauke wayar tace kawai ka sauke ni anan na shiga mota na karasa, sai ka wuce sabgoginka, da yake tun parko ke ika kirkiramin sabogogin ba, karki yi mamaki inna ki bin umarninki. Dole tayi daria ta share zancen , ya tsayar da motar a harabar gidan su yana dan zuba mata ido saboda yadda yaga kamar ta kadu da ganin wani da ya tsaya da motarsa kusan lokaci daya dasu. Da sauri ya kallo motar dan ganin tana rawar jikin picewa, ta juya ta dube shi da duban rashin pahimta ya nuna Yushau yana padin wanene wancan? Ta dubi Yushayu sanan ta dube shi atakaice tace Yayana ne. Yayi zuru yana kallon yushau haka kawai yaji hannkalinsa baikwanta da shi ba sam ya kada kai bisa dole ya bude kopar suka puta lokaci gidam da sauri ya nupi yushau dake kokarin rupe mota yayi masa sallama tare da mika masa hannu. A wulakance yushau ya amsa idon sa na kan rumaisau sannan yace Yaya kuke da wannan? Auwal yayi zuru yana kallon Yushau da rumaisau yadda yushau yayi magana puskarsa babu walwala ne yabawa Auwal damar nustuwa ya karance shi. Akwai alanar nutsuwa a rumaisau sai dai a rikice ta debo masa amsa dan Ajin mune.. Ya taimake ni ne saboda ruwan da ya tare ni..hanyarsa kenan shi yasa ban nemi sauka ba da muka wuce inda ake ruwan. A gadarance yushau yace kina pada min hanyarsa ce dan kun shirya kullun ya dinga dauko ki yana kawo ki ko? Ban san iyakar tsawon lokacin da zan dinga pada miki nan arewa ba kamar can kudu bane, babbar kazantace aga mace ta dauki namiji aboki.. Ganin yana neman tsinkata ta tare shi da cewa larura ce yaya yushau nayi gudun dukan ruwa ne . Yushau yayi tsaki tare da yin gaba yana cewa duk illar da dukan ruwa yake dashi ai bai kai na sayar da mutumci ba, koda yake wayewarku ta halatta muku haramci. Rumaisau tayi suguri ranta yayi mugun baci, ta san yushau bai iya magana ba sam, haka yake yinta kamar kashi, amma a yau ta para shakkar dan tazo cin arziki gidan sune, a sanyaye ta dubi Auwal da yayi shiru rungume da hannu yana kallon kasa tace na pa gode zan shiga ciki, ya dago da alamun tunani ya dubeta me yasa kika ki pada masa gaskiyar matsayin da na zaba mana? Sai kika alakanta mu da jabun dangantaka? Ta dan ja nunpashi sannan ta amsa har yanzu kai kake kidi da rawarka, da zaka bi ta tawa zamuyi sallama ne mu rabu har abada, karatu ya kawo ni garin nan yakamata naji dashi shi kadai. Mts! Ni bana son hargitse-hargitse wallahi. Ya pahimci cikin bacin rai take saboda haka sai da ya shirya kalaman da zai mata sannan yace kina da wanda kika tsayar? Ta girgiza kai , puskarta a dauke, ya numpasa yace idan haka ne na tabbatar kinzo kano ne dan mu hadu mu auri juna ba tare da nayi gibi a karatunki ba, ki daina gaggawar yanke hukunci akan lamarin rayuwa da hakan gara ki zama mai dabar tsara al'amuranki, ina neman alparmar kar ki koreni.kuma ban matsa miki ki so ni ba, amma ki bani dama mu pahimci ko zqmu iya tapia tare. Yanzu idonta cike yake da kwalla saboda takaicin kalaman yushau gidan su kawai take tunawo da yadda take da kima da mutunci a cikin sa. Auwal na ganin kallarta ya dan shiga damuwa amma a nutse ya tausasa murya yace mata idan akwai matsala dan Allah ki pada min kuka na nupin damuwa. A kalamaina banga abin da na pada da zai bata rai ba. Ta kirkiro murmushin karpin hali dole tace masa babu komai Allah Yayi mana jagora. Tun daga wannan ranar Auwal ya zame mata wani barin rayuwa ya kware da samar da mahallan parin ciki a zuciyarta da kirkinsa da kuma yadda yake kula da ita da damuwa a cikin abin daya dame ta. Kullun sai yazo gidan su tare da cewa yana bata mata da yawan lokutai a waya, haka kuma takanas yake binta makaranta ya daukota, babban zunubinsu da ya tsayewa yushau a rai kenan saboda imanin da yayi na cewa duk yarinyar da ta je jami'a sai ta lalace, ya rasa yadda zai pahimtar da hajia da Alh a matsayinsu na wadanda kamar su ke waliyantar da Rumaisau saboda kyan hali. Rumaisau ta para nisa cikin abind a bata zaba tsarabarsa a rayuwar ta ba wato SO, tana ji a ranta ita nakasasshiya ce duk yadda so zai zo mata in ta amince masa wata rana zai zame mata madaciya, amma a yanzu Auwal ya ture wannan tsarin a ranta sai ya barta da zullumin yadda rayuwa zata kasance musu a gaba. Zai rabu da ita ne idan ya san ita sikila ce ko kuwa zaiyi shahadar auren ta? Zabi na karshe ne patanta, sai dai zuciyarta na wuyatantar da yiyuwar sa. A yanzu sun pice watanni uku tare duk wani laulayi da alayin cututtukanta babu wanda auwal bai gani ba, yau kapa ciwo gobe cikim jibi zazzabi, gata mura... Kai shibai taba ganin mutun mai laulayi kamarta ba, amma wannan bai gutsuri komai cikin soyayyarta ba sai ma kari saboda tsabar tausayin da take bashi, kuma laulaye-laulayenta ne ya koya masa tarin hanyoyin da zai nuna mata kulawa, dan haka ya zama dan gida dan gaske a zuciyarta da zuciyar kowa ma a gidan in aka yi gepe daya da murdadden Yushau. Asai dai duk wannan shakuwar tasu ya rasa dalilin da yasa rumaisau taki amince masa manya su shigo maganar, ya bata lokaci ya kara mata amma har yanzu ta kasa gabatar masa da uzuri, sai dai hakan yaki ya dame shi dan yana da yakinin ya kai matsayin da yapi karpin yaudara a zuciyar rymaisau sai kawai ya zuba mata idon ganin gudun ruwa, musamman da yake karatun nata yazo karshe.. . Dan Aunty. July 31 at 8:26 PM · PublicGORAN DUMA 6 . Ya bata lokaci ya 'kara mata, amma har yanzu ta kasa gabatar masa da uziri, sai dai hakan ya 'ki ya dame shi dan yana da ya'kinin ya kai matsayin da ya fi 'karfin yaudara a zuciyar Rumasa'u, sai kawai ya zuba mata idon ganin gudun ruwa, musamman da yake karatun nata ya zo 'karshe. Wata rana sun fice goma na dare suna hira a zahiri daurewa kawai ta ke saboda cikinta da ke ta faman murd'awa. Ta daure din har suka yi sallama ta shiga gidan a birkice, zta wuce ciki Hajiya ta yi kiranta. "Zo nan Rumaisa'u, me yake faruwa na ga kina yamutse fuska?" Ta 'karaso ta zauna a gajiye. "Wallahi cikina ke min ciwo". Hajiya ta dubeta cikin tausayawa, ta ce. "Sannu, sai ki yi 'kokari ki sha magani, Hafsat taimaka ki murza mata tafarnuwar ki ta ce ki kaw mata". Hafsat ta tashi ta 6arin jiki tana yiwa Rumasa'u sannu ta wuce kicin ta d'ebo tafarnuwa masu kyau ta 6are, ta dandaka sannan ta zuba ruwa kofi daya ta tace da rariya ta kawowa Rumasa'u ta shanye. An fi awa daya kafin a samu ciwon cikin ya lafa, wannan ne kuma ya sa Hajiya ta tsokano maganar da ta ke jin yyinta ya zama dole dan ta fahimci Rumasa'u, so ya rufe mata ido tana shirin yin abin da za a ga laifinta. "Rumasa'u kun ta6a maganar ciwonki da Auwalu kuwa?" Alamun damuwa da nadama ya bayyana a fuskar Rumaisa'u, kwalla har ta cika mata ido, ta girgiza kai ta ce. "Ba mu ta6a ba Hajiya". Cikin zura mata ido, Hajiya ta ce. "Tyn farkon ne kika rasa hanyar sanar da shi Rumasa'u?" "Ban san za mu dore tare ba Hajiya". Hajiya ta yi shiru alamar nazari, sannan ta nisa ta ce. "Ni har na fara zargin ko ganin yawan laulayinki ya hana shi turo manyansa. Ga su Hafsa suna ta faman jiranki". Ta matse kwallar idonta tana amsawa. "Ni ce na ke dakatar da shi Hajiya, kuma na kasa sanar da shi dalili". Hajiya ta girgiza kai ta ce. "Wannan kuma ba dabara ba ce kika yi, za ki ta zama haka ne Rumaisa'u? Ai a rashin kira karen bebe yake 6ata, ki kokarta ku tattauna lamarin". Cikin sanyin jiki Rumaisa'u ta ce. "Shikenan zan kokarta Hajiya". Ta gama shin bacci ke nan ya mmako mata waya, ta dauka da kasalar rashin 'karfin jiki. "Auwal ba ka jin bacci?" Muryarsa a d'ashe ya amsa. "Na kwanta ya 'ki zuwa Rumasa'u, abubuwa barkatai sun cushe a 'kwa'kwalwata. Ga kadaici ga matsaloli". Ta dan yi dariya ta ce. "Me ya dami ranka haka Auwal?" Ya sauke numfashi..... "Kafin mu rabu na fahimci kamar ba kya jin dad'i, na taho da tauayinki da neman hanyoyin da zan samar miki waraka ko da na dauke kewa da 'karfafa gwiwa ne, amma duk kin bi hanyoyin da hakan za ta afku kin toshe. Na fara sarewa Rumasa'u dan na fahimci kamar kin raba zuciyarki biyu ne kin bar min daya na sani, dayar kuma kike wahalar dani da ita. Wata irin 'kaunarsa ta dingo bijiro mata, tana nemansa ta 'kwalla, tana kokawar daurewa yana gagara. "Auwal wannan ne zai hanaka bacci? To in dai ni ce ba za a haifi matsalolin da za su 6ata ranka da ni ba. Za mu sami lokaci nan kusa mu tattauna... Amma ina son ka a jiye a ranka soyayyarka ce ke hana ni yin abin da kake hasashe ina jinka da matsayin wani 6angare na jikina, wanda rashinsa zai gutsire rayuwata, amma na 'kure fatan hakan zai gaza faruwa". A raunane ya ce "Saboda me? Rumaisa'u duk yadda nake da matsayi a zuciyarki da sha'kar numfashinki d'igo ne na matsayinki a wata zuciyar, na kuma dami raina da son kai 'karshen buri a kanki kafin mutuwa ta runtse ganina, ke kuma kin kasa gane hakan..." Ta yi saurin tare shi. "Haba me ya kawo zancen mutuwa Auwal?" Shi ma ya tareta da nasa batun. "Ai ya zama dole, 'karuwar burika, cika wasu da su6ucewar wasu alamu ne na kusantar kabari sai raina yake ciwo da hasashen mutuwa zata iya riksta ba tare da na cika burin samunki ba." Ta fara hawaye sosai, dan haka ta jima ba ta tanka ba, har ta fitar da sautin kukanta kadan, sannan a cikinsa ta ce masa. "Ba na fatan dai-dai da kwayar zarra in cutar da kai Auwal, kuma bana son rabuwa da kai.." Ya tare ta a dan 'kuntace. "Shikenan sai ki bar mu muyi ta bulayi a soyayyar da ba ta da rana, wadda ta ki ta zuciya ta saba da ta fatar bakinki, kina sona amma kin kasa ba ni damar mu kasance 'karkashin sunna... wannan makahon so ne..." Ta yi kokarin tare kukanta, ta ce. "Akwai matsala ne Auwal, ni ke nan yau lafiya, gobe babu. Zan zame maka dawainiya in gundure ka, shi yasa ba na son cin karo da kukanka Auwal". Ya yi dariyar da ta fad'ad'a masa 'kirji ya ce. "Wa ya ke dorawa wani lalura Rumaisa? In Allah Ya so sai Ya yaye miki, ai babu cutar da ba ta da magani. Ita kanta cutar ma wani maganin ce, domin tana kankare zunubai... Ni ma da nake son daukar dawainiyarki ladan zan samu idan na kula da ke, duk sanda aka ce ba ki da lafiya sai na ji da tare muke sai na fi samun nutsuwa..." Ta 'kara fashewa da kukan da ya tsorata shi. A rikice ya ce. "Wai don Allah me yake faruwa ne? Rumaisa na kaa canko dalilan wannan kukan naki". Cikin kukan ta ce "Na gode da niyya da fatanka, amma ciwo na mutuwa ce kadai zata raba... Saoda haka aurena da kai yana nufin ka yi ta danniya da hakuri a kaina har 'karshen rayuwata, domin haka Allah Ya halicce ni, haka kuma Ya so ya ganni..." Ya rasa fassarar da zai wa maganganunta, rashin yanke shawarar ya sa shi yi mata tambaya a gajarce. "Wai wanne irin ciwo ne?" Kai tsaye cikin dakewa ta yi karfin halin amsa masa. "Sickle cell" Ya ji kamar ta doka masa guduma a 'kirji, cikin 'yan sakanni wasu miliyoyin tausayinta da fargabar yadda lamuransu zai kasance ya mamaye masa 'kirji, dan ya san ciwon sickle cell ba da wasa ba kasancewar wani abokinsa sikila ne ya dad'e da sanin yadda masu ita suke shan kashi sai dai wannan 'karamar matsala ce idan aka kwatanta da neman makomar 'ya'yan da za su haifa. Duk da a rikice yake bai kasa 'ko'karin tattara kalaman da zai 'karfafa mata gwiwa ba. "Mene ne matsala a kasancewar sickle Rumaisa, ko ke kika yi kanki dan me za ki raba kanki da ni ballatana Ubangijin da Ya yi ni Ya yi ki, ba domin na fiki ba? Ki zama mai tawakkali da ha'kuri da rayuwa sai matsalolinki su zame miki kaffara. In kuma domin wannan kike gina katanga tsakanin da kasancewa tare, to ni ban fahimci gatan da kike son yi min ko kike son son yi wakanki ba". Yanzu ta rage kukan da ta ke, dan a zahiri hankalinta ya soma kwanciya, duk da ta san bai kamata ya kwanta din ba. Ta nisa ta ce. "Kar ka yi gaggawar yanke hukunci Auwal, ka zauna ka yi tunani da kyaun duk matsaloli a kaina ka lissafo suka ga yadda zaka iya tarbarsu, yadda zaka dinga dawainiya da ni, dawainiyar aljihu da ta KWANJI, ha'kuri da ni wajen kukan ciwo da hakurin wasu kulawa daga gare ni lokacin ciwo in duk wadannan sun zama sau'ki a gareka Auwal makomar 'ya'yanmu ba zata zama sau'ki ba matu'kar ba ka kasance wanda ba zai bayar da gudunmowar da ba zaka haifi sickler ba". Ya ja numfashi sosai saboda rashin abin cewa, amma dole ya nemo shi. Ya ja numfashi sosai saboda rashin abin cewa, amma dole ya nemo shi. "Yin daainiya da ke, da kuma hakuri da laulayinki ni ba zan ta6a kiransu matsala ba Rumaisa, ina son ki soyayyar da nake jin ko mugun hali ne a jininki ba zata gaza ba, bare wannan jarrabawar ta Ubangiji da idan kika haye ta da tawakkali, na haye ta da jurewa dawainiya da ke zamu iya samun aljanna da ita. Batun 'ya'yanmu shi ne hanzari, amma wannan zai hana ki aure har abada ke nan Rumasa'u? Kafin haduwa da ni wanne tanadi kika yiwa kanki a fannin aure, me yasa kike ganin zan bayar da gudunmowar da zamu haifi sickler?" Ta amsa masa a raunane. "Ban ta6a fitar da rai zan yi aure ba, sickle cell kuma ba ciwo ne da za a ce ka auri mai shi ya zama waraka ba, domin za ku samar da iyali irinku ne gaba daya, amma dai ban ta6a hasaso aurena da rayuwar auren wani abu ne mai sau'ki ba. Ina sonka Auwal wallahi ba na fatan duk wani abu da zai cutar da kai, na san kuma ko yaya ne aure na zai iya zame maka matsala ko ta fannin 'ya'yanmu..." Ya tare ta da sauri. "Shi yasa na tambaye ki, wacce irin gudunmowa zan bayar da kike ala'kanta ta da haihuwar sickler?" Ta jima cikin shiru, sannan ta ce. "Idan ka ji a ranka zaka iya aurena, kuma a gidanku za a barka, shi ne zamu tuntu6i likitoci dan samun shawarwari, a iya maka gwaji kuma a gano kai waye, ta nan zamu iya sanin makomar 'ya'yan namu". Yanzu ya fara samun nutsuwa, saboda haka cikin doki ya ce. "In Allah Ya so cikin satin nan sai mu je asibitin, amma ki sani duk yadda bincike zai nuna ba na ji zai iya yi min katanga da aurenki. Ki cire shakku daga ranki Rumasa'u, ina yi miki soyayyar d aban san matsaloli a tare da ke". Ta yi shiru tsawon wasu sakanni sannan ta ce. "Abin da na fi so da kai Auwal ka fara tuntu6ar magabanka shawara a kaina, kar ka biyewa soyayyar zuciyarka ka yi abin da ransu ba zai ji dad'insa ba...q Ya tare ta kamar a 'kufule "Rumaisa'u sickle cell ne yakai girman da ba za a auri mai shi ba? Haba! Wannan maganar banza ki ke..." . Dan AuntyGORAN DUMA 7 . . Ita ma ta tare shi a tausashe "Auwal babu yadda za a yi ni da kaina in 'kir'kiro abubuwan da zai nesanta mu da juna, amma duk abin da yake matsala ina guje mana shi kasancewara sickler na san da yawanmu irin matsalolin da suke fuskanta a rayuwa, ciki har da tsangamar da dangin miji ke masu matsaloli (sicklers) da za yi ta faman dawainiya da nauyi akan mijinsu ko kuma haihuwar dawainiya da su. Auwal wani lokacin ma mazajen ke tsangwamar matan akan sun zame musu nauyi... Kai wata ba sikilar ba ce idan suka taru ita da dangin mijin suka haifi sikila sai ya tattara laifin ya dora mata, wata mahaifiyar sikila da na sani ta ta6a bani labarin yadda mijinta ya fito kai tsaye yake 'kalubantarta akan cewa matansa hudu, amma ita kadai ta ishe da haihuwar sickler duk da cewa tare da mijin suka haifeta. Amma ka fahimta ba gudu nake a tsangwame ni ba ko ko kuma a 'kalubalance ni, na rantse maka babu wata wuya da ba zan iya jurewa ba, kawai dai bana sn ka yi abin da magabatanka za su yi kuka da kai. Idan aure zai shiga tsakaninmu ya kamata mu kori duk wani abu da muka san 'kalubale ne a rayuwarmu ta gaba dan a gaban ba mu da lokacinsa abin da ke gabanmu ma ya ishe mu". A sanyaye ya nisa, ya ce. "Na fahimce ki, in Allah Ya so zan yi abin da kika ce, amma dai dole mu hanzarta zuwa gwajin, ina son yin tanadin dukkanin wata juriya a kanki". Ta yi murmushin karfin hali cikin saduda ta ce. "To shikenan, Allah Ya za6a mana abin da fi alkhairi Auwal". Ya amsa cike da farin ciki. "Amin Rumaisa'u, Allah Ya sa mutuwa ce zata raba mu". Ta yi dariya ta ce. "Kuma ya zama ni zan rigaka mutuwa, na tabbatar rayuwa zata yi min 'kunci idan babu kai". Shima ya yi dariyar, ya ce. "To kin ga gara ni na riga ki mutuwar, saboda ni ba zan iya jure rayuwar da babu ke din ba". Da dad'i ya cikata kawai sai ta amsa masa da cewa. "Ina sonka Auwal!" Ya nisa cikin wani irin shauki ya ce. "Ni na san ina yi miki abin da ya fi So Rumaisa'u". Babu abin da ya motsa dan jua baya akan soyayyar da Auwal ke mata, sai ma wani 'karin tattali da tausayi da yake mata. Ya daura d'amarar sanin duk wani abu da ake gudunsa ga sickler, nisali ko a ina yake idan iska ta taso a wajen sai ya nemi Rumasa'u a waya, idan ta shiga motarsa sai ya zuge gilasai tsab, sannan duk wata sabga ta aljihu da zai mata ya juyar su kaf akan abubuwan da zai taimaki lafiyarta, dangin kayan sawa masu kauri da rufe jiki, dogayen riguna, hijabai, ni'kab har da safar 'kafa da hannu. Haka nan 6angaren abinci mawuyacin abu ne ya je mata ba tare da wani abinci da zai amfaneta ba, ko da mafi 'kan'katarsu ne wato rake. Tun daga nan hankalin Rumaisa da na iyayenta ya kwanta, suke ganin lallai ta sami mijin marainiya, Auwal ya zama dan gida a nan Kano, Rogo har ma da Abuja kowa a dangin Rumaisa'u. A nasa dangin ma Rumaisa'u, saboda haka na'am da girman gidan su Rumasa'u, saboda haka har sun amince da aurensu. Auwal ya kasa tarar mahaifansa ya sanar da su Rumasa'u sickler ce, saboda ta tsorata shi da yadda iyaye ke kar6ar lamarin dansu ya auri sickler, sai ya ke shakkar goyan baya daga nasa iyayen, musamman da yake shi kadai suka haifa, yadda suke zumudin aurensa ya fahimci yadda suka dora masa burin tara 'ya'ya saboda haka ya yi kirmisisi ya 'ki sanar da su, haka ma zuwa gwajin ya share shi saboda fargabar da ta cika ransa, alhalin ko me ma suka samo ba zai iya karya masa gwiwar auren Rumaisa'u ba. A haka manyansa suka je nemar masa auren Ruma aka yi duk yan hidimomi bisa al'adunsu aka sanya musu rana, in ta kammala karatu za'ayi. *BAYAN SHEKARU BIYU* Wata biyu ya rage aurensu, wanda za a had'a da na Hafsat da angonta Sani. Zancen duniya da ba ya 6uya, sai ga batun cewa, Rumaisa'u sikila ce a kunnen mahaifan Auwal. Kwatsam wani dare ya bar wajenta ya koma gida, ya shiga wajen Innarsa neman ruwan zafi, mahaifinsa ya yi kiransa fuska babu walwala a fuskarsa ko kad'an. Ya nemi guri ya zauna cikin sanyin jiki, mahaifin nasa ya ce. "Daga ina haka?" Sai ya ji tambayar ba wai, saboda babu irinta tsakaninsa da mahaifin nasa ko da can ma da ba shi da gurin zuwa ba a fiye tambayar ina ya je da dare ba ko dan yanayin aikinsa. Amma yau shi ne ake tuhumarsa inda ya je. Kawai sai ya yi 'kasa da kai, dan bai san abin fad'a ba, yana ji a cikin ransa nan da wata biyu Baban nasa ba zai ganshi a wannan lokacin ba ma bare ya tambate shi. Mahaifiyarsa ta shigo da fulas har da farantin kayan shayi ta dire a gabansa, zata fara hada masa ya yi sauri ya kar6e ta yana godiya. Ta nemi guri ta zauna, shi kuma jiki a sanyaye ya fara bude gwangwani yana sauraron mahaifinsa da ya dora. "Yaya me jikin?" Ya dago da sauri ya dubi mahaifinsa hankalinsa a tashe, amma fuskarsa ta kasa nunawa. Ya tattare 'kululun da ya taso masa a ma'kogwaro ya kora shi ta hanyar hamud'ar madarar ya hadiye sannan ya ce wa mahaifin nasa. "Abbba ina ka san ba ta da lafiya?" "Zancen duniya ai ba ya 6uya". Abban ya fada cikin rashin kulawa tun daga nan Auwal ya sha jinin jikinsa, kawai sai ya ci gaba da hidimar gabansa. Abban ya gyara zama ya ce. "Wato Auwal ka san yarinyar nan sikila ce ba ka sanar da mu ba, dan kawai ka na son abin da zaka sanya mu 'karanta?" Auwal ya dago cikin bugun zuciya ya dubi mahaifinsa bakinsa na rawa ya ce. "Abba... Mene ne 'karantar a auren sickler?" Cikin 6acin rai Abba ya ce. "Auren sickler ba 'karanta ba ne, kantafi ne kawai da rayuwar 'ya'ya da ta aljihu... In da 'karantar ta fito shi ne zuwan da zamu yi mu ce mun janye..." Tuni har hawaye ya fara zuba a idon Auwal, wanda ke kallon mahaifinsa garau da alamun rashin kwanciyar hankali bare kimtsa maganar da zuciyarsa ya kamata ta haifa, bakinsa kuma ya furta hakan ne kuma ya sa Innarsa ta sami sararin shiga maganar. "Wannan d'an ka yi wauta in dai ka san cewa yarinyar nan sickler ce, amma ka juya wa matsalolinta baya zaka aure ta... Muna zaune 'kalau ka kawo mana sickler dangi..." A yanzu ya sami ga6ar abin cewa wanda ra'ayin kansa da na zuciyarsa suka yi tarayya yana 'kokarin tsayar da hawayen ya tare mahaifiyarsa. 'Idan dai zan iya haihuwar da Rumasa'u, to lallai zan iya haihuwar sickler da wata mai lafiya wadda ba sickler ba ce..." Shi ma mahaifinsa da yake zazzafan mutum ne sai ya tare shi. "Idan Allah Ya hukunto hakan na tabbatar idan za ka haifi sickler goma da Rumaisa'u idan wata ce sai Allah Ya ta'kaita ka haifi hud'u..." Auwal kawai sai ya yi shiru ya ci gaba da shan shayin da ya fi kama da shan magani, 'kwalwarsa ta tsaya cak! Da 'kirkirar mafita ko ta 'kofofin da duk ransa ya raya masa har ya gama kushe masa aure da Rumasa'u tsab ya 'karkashe batunda da haramta aurem. Auwal dai bai tanka ba, har mahaifin nasa ya diga aya sannan cikin rashin hayyaci ya tashi ya fice daga falon. . Dan Aunty.GORAN DUMA 8 . . Tsawon daren nan ba zai iya dorar da wani abin kirki da ya yi ko lissafinsa ya yi ba dangane da yadda zai 6ullowa al'amarin, ya san dai ya gurji kukan da tsananin 'kauna da tausayin Rumasa'u ya haifa, kuma su suka hana shi hasala komai bayan ya 'koshi da ji a ransa duk tsanani ba zai iya rabuwa da Rumaisa'u ba. Sai 'karshen dare ya sami runtsawa saboda haka bai sami sallatar asubahi ba, 'karfe shidda dai-dai wayar Rumasa'u ta farkar da shi. Yana ganin sunanta kan wayar sai da 'kwalla ta taru a idonsa, ya daga yana kokarin gyara muryarsa saboda daskarewar bacci da kuma ta ma'ka'kin tausayinta da ya ma'kale maasa a ma'kogwaro. "Rumaisa'u" Muryarta tar ta ce "Duk wadannan gaibu ne Abba, babu wanda ya san abin da gaba zata haifa, kamar yadda ba mu isa za6ar abin da muke so mu 'kyale wanda tanmu yake hasashen hadari cikinsa ba. Da dan Adam na da iko akan za6in abin da yake so na matar da ta zarce Rumaisa saboda abin da nake mata ya fi so, shi yasa ban san ko wacce irin matsala ba a kanta, amma da yake na san ba dukkan abin da mutum ke so yake samu ba, tun bayan umarninka na jiya na kwana ina gwajin yadda zan iya rayuwar da babu Rumaisa'u. Na yi ta cin karo da gazawa, har ta fara barazanar keta min zuciya. Ban fitar da rai zan iya din ko kuma zan kasa ba, na san a biyu daya ce zata faru, ko in iya d'in in wanzu bisa tsarin da ka za6a min, ko kuma in gaza ta dalilin in bijire maka ba, wanda babu irin haka a tarbiyyar da ka ba ni... Abba kar ka damu da yadda ka ganni har in mutu in Allah Ya so ba zaka had'u da abin kuka ta silata ba..." Yanzu hawaye ya fara cin 'karfinsa, kuma shi ne ya tilasta shi diga aya ba don ya rasa abin cewa ba. Duk jikin mahaifinsa ya yi sanyi, sai kallon Auwal yake shi ma kamar ya yi hawayen, amma wata zuciyar na tuna masa siyasar Auwal ta dadin baki da sadaukarwa har ka yi masa abu ba tare da kana da niyyarsa ba, wannnan ne yasa ya daure ya ce. "Abin har ya yi zafi haka Auwal? Ba zaka iya fitar da yarinyar nan a ranka cikin ruwan sanyi da dalilin matsalarta a rayuwarka da ta 'ya'yanka ba?" Auwal ya muskuta da murmushin ya'ke alamar akwai magana fal a cikinsa, sai dai yadda zai furta ya yi girma, don haka ya hadiye ta kawai ya bi mahaifinsa da shiru, har mahaifin nasa ya gaji da jiran cewarsa ya nemi guri ya zauna idonsa akan Auwal. "Tun farko ka san Rumasa'u sickler ce?" Auwal ya kad'a kai, mahaifin nasa ya dora wata tambayar. "Wanne mataki ka dauka akan yadda za ku rayu tare, ko kaucewa yadda za ku haifi 'ya'yan sicklers?" Auwal ya jima kafin ya tattaro abin cewa. "Ta yi 'kokarin hana ni aurenta tun ranar da muka had'u na dage. Duk matsalolin da ka lissafo min da bakinta ta lissafo min su, amma ba su gigita ni yadda suke gigita ku ba... Da ta ga haka sai ta shawarce ni yin gwaji dan sanin makomar 'ya'yanmu, na amince a sannan amma sai na ga gwajin 6atawa kai lokaci ne da tanadar wa kai fargaba, don na ji a raina ko wane irin sakamako gwajin zai haifar ba zan iya barinta ba, saboda haka na ce ta bar maganar gwaji". Mahaifinsa ya jima cikin shiru yana jiya maganganunsa, kafin ya yanke hukuncin d ayake jin shi ne na 'karshe. "Gaskiya ta yi hange mai kyau saboda haka shawararta ita ce abin bi. Ka je ka yi gwaji idan akwai matserar 'ya'yanku sai ku yi aure, idan kuma babu, to ku dubi girman Allah ku ceci 'ya'yanku ta hanyar ha'kura da juna". Duk da Auwal ya ji maganar mahaifinsa da kamar maimaici kawai, ma'ana babu wani sassauci haka ya cije a ladabce ya gyad'a kai. "To na gode Abba". Ya m'ke kuma salin-alin ya fice ya shiga 'kwan'kwasa falon Innarsa. Auwal bai 6oyewa Rumaisa'u komai ba dangane da yadda suka yi da mahaifinsa da hujjarsa ta sanin kukanta nasa ne, kukansa ma nata ne. Tuni suka yiwa juna wannan al'kawarin na tarayya akan matsalolinsu dan nemo hanyar araka. Rumasa'u ta jima ba ta yi magana ba, ba dan rashin abin cewa ba sai dan saisaita maganar don gudun kada tayi muni a kunnen Auwal ko kuma ya zama wani mataki na karyar masa da gwiwa. "Kin 'ki cewa komai Rumasa?" Ya fada bayan ya gaji da jiran cewar tata. Ta gyara tsaiwarta ta 'kara jingina sosai da motarsa saboda tana jin jiri. Ta yi murmushin 'karfin hali ta ce. "Abin da Abba ya yi shi ne ya kamata Auwal, so ne tun farko ya ke runtse mana ido alhalin wani dad'in gushi ne kawai a cikin rayuwar aure, wanda ake 'kulla si domin kammaluwar iyali. Ya wajaba ne mu samarwa iyalanmu makoma ta gari, ba ya kamata ba Auwal". Shi ma ya yi murmushin 'karfin hali bayan ya ji a ransa kawai 'karfafa masa gwiwa ta ke so ta yi ba ainihin abin da ke cikin ranta ke nan ba, ya ce. "Kamar ke da Abba kuna mantawa ba a yiwa Allah wayo, ke kanki aya ce Rumasa'u, Innarki da Abbanki babu sickler ciki, amma suka haife ki..." Ta tare shi da dariya. "Ba 'kokarin yin wayo ba ne, 'ko'karin amfani da hankali ne, wanda Ubangiji Ya hore mu da shi dan za6ar abin da zai amfane mu da gujewa abin da zai cutar da mu, abin da ya faru da mu cikin akasi mun yarda daga Ubangijinmu ne ba tare da sakacinmu ba, sai mu yi fatan zamowarsa kaffa". Auwal ya yi zuru kawai yana kallonta sannan ya nisa ya ce. "Ban sna me yasa duk cikin lissafinku ba kwa duba uban yaran da samun su yake 'kila wa 'kala ba, sa ku kuka himmata sarayar da shi alhalin shi ne a hannunku. To zan fada miki abin d ana fada Abba jiya na kwana da 'kokarin lissafa yadda zan yi rayuwar da babu ke, na ji kamar numfashina zai yanke daga lissafin kawai ba tare da fitar da sakamako ba, amma dai ban cire rai daga rahamar Ubangiji ba, duk za6in da ya yi min ina fatan rahma da jin 'kanSa a ciki". Ta zuba masa ido, dauriyarta na kokarin 'karewa. Kasa gajiya da kalonsa da ta yi ne ya sa ita ma ta tabbatarwa kanta wa'ka kawai ta ke, amma tursasa kanta za6ar tsaka-tsakin al'amura, sai dai kuma ta kasa hana zuciyarta rauni da son nuna gazawa da ta tsaya kawai ga bayyanawa ta hanyar 'kura masa ido cikin hawaye. Haka suka tsaya ita kuka, shi hawaye, har daga 'karshe ya zagaya mota ya shige yana cewa. "Zo mu je asibitin". Ta yi saurin duba agogon hannnunta da ya nuna 'karfe sha daya da mintoci sha hud'u. Ta bude motar ta sunkuya a tausashe ta ce masa. "Bari na sanar da Hajiya". Ya yi saurin tare da fadin. "Rumaisa'u kar ki sanar da kowa matsalarmu fa, umarni ne da kuma kokarin kwantar da hankalinku ke da Abba zai kai ni gwaji, ba dan na yarda da iya raba ni da ke ko ya yi wani abu a cikin sonki ba. Ya kamata ki ri'ke wannan kada ki yi 'kokarin raba ni da kanki, son da nake miki mutuwa ce kawai zata iya raba ni da shi". Ta sororo cikin sanyin jiki tana kallonsa. Ta hadiye kwallarta ta ce masa. "Auwal wai me yasa ka damu da kira mana mutwa? Ai ba sai ka kirata zaka bayyana min kana sona ba,.." Ya tareta cikin kyalkuala dariya. "Me yasa ba kya so na kirata? In akiranta ne dan na sna ita ce mai YANKE 'KAUNA, duk yun'kurin raba mu da kuke ni dai na tabbatar ita kadai ce zata iya raba ni da son da nake miki. Amma na san ba ni da karfi ko dabara a cikin aurenki yadda Ubangiji Ya so haka zai yi". Ta murza yatsu tana dariya, ita ma ce. "Shikenan. In Allah Ya so ni da kai mutu ka raba". Ba ta jira cewarsa ba ta wuce. Ya bi ta da kira, ta tsaya ba tare da ta juyo ba, ya dan daga murya. "Na fa gaya miki kar ki fad'a". Sai kawai ta kad'a kai ta wuce tana dariya. . Allah sarki soyayya... Sai gobe in shaa Allahu. Dan AuntyGORAN DUMA ****9 Akwai wani lokaci da Alhaji ya sanya shi kai ta taronsu na masu cikon sankarar jini (sickle cell) ya jirata har aka tashi taron. A hanya sun taho yana faman cikarsa da batsewa, har ya fashe da cewa. "Inda za ka san ciwon shifcin gizo ne har a wata 'kungiya, wai dan tsabar lalacewar zamani ciwon ake wa 'kungiya, kowa ya san ba ciwon ne ya dame ku ba, wata hanyar neman kud'i kawai kuka mayar da ciwon!" Rumaisa'u ta yi murmushi tana kallon tagar motar kafin da kyar ta samo abin cewa. "Yaya Yusha'u kamar yin 'kungiyar zai fi rashinta amfani. Ni dai nan na 'kara min imani da godiya ga Allah wanda Ya halicce mu yadda Ya so ba dan 'kiyayya ba, sai dan Ya zamo jarrabawa a gare mu. Kawai dai ka yi mana fatan ya zamo kaffara". Yusha'u ya yi wani gajeran tsaki, sannan ya tsuke bakinsa. Shekararta ta 'karshe a B.U.K, Hafsat ta kammala N.C.E har ta fara aiki, mahaifanta sun dawo Abuja da zama. A wannan shekarar ne ta hadu da gwarzon masoyin da ta ke jin har duniya ta nad'e ba zata yi irinsa ba. Ba wai tana rasa masoya ba tuni, sai soyayyar ba ta wani nisa sabo rashin goyan bayanta, ko kuma in sun san matsalarta su kauce. Sun hadu a wata laraba ne tana tsaye a bus stop cikin B.U.K ner site tana jiran motar da zata kai ta old site, ita kadai ce tsaye a wajen, sai fama ta ke da ri'kon tafkekiyar lema (umbrella) a hannu saboda hadarin da ya fara d'aurewa, zai iya zubar da ruwa bagatatan, saukar ruwa a jikinta kuwa wani tushen tashin hankali ne da zai iya motsa ciwonta. Dai-dai wannan lokacin AUWAL ya zo giftawa ta gabanta da motarsa. Ta bi motar da kallo cikin tunanin yadda suke kwashe da Mominta a hutun da ya gabata. Wani Uziri na son tsaida ni, Amman zan yi 'kokarin kammalawa da wuri naci gaba.... Shekararta ta 'karshe a B.U.K, Hafsat ta kammala N.C.E har ta fara aiki, mahaifanta sun dawo Abuja da zama. A wannan shekarar ne ta hadu da gwarzon masoyin da ta ke jin har duniya ta nad'e ba zata yi irinsa ba. Ba wai tana rasa masoya ba tuni, sai soyayyar ba ta wani nisa sabo rashin goyan bayanta, ko kuma in sun san matsalarta su kauce. Sun hadu a wata laraba ne tana tsaye a bus stop cikin B.U.K ner site tana jiran motar da zata kai ta old site, ita kadai ce tsaye a wajen, sai fama ta ke da ri'kon tafkekiyar lema (umbrella) a hannu saboda hadarin da ya fara d'aurewa, zai iya zubar da ruwa bagatatan, saukar ruwa a jikinta kuwa wani tushen tashin hankali ne da zai iya motsa ciwonta. Dai-dai wannan lokacin AUWAL ya zo giftawa ta gabanta da motarsa. Ta bi motar da kallo cikin tunanin yadda suke kwashe da Mominta a hutun da ya gabata. "Rumaisa'u da zaki iya tu'ko a Kano sai na sai miki mota, saboda yau da gobe, duk safiyar Allah da yammaci sai na tuno yadda za ki fita, ko za ki dawo gida. Sai na dinga jin kamar zan yi tsuntsuwa na zo na dauke ki, na san wahalar da d'alibai suke sha". Ta dubi mahaifiyarta cike da so da 'kauna, ta ce. "Momi ai kina min addu'a in Allah Ya so ba zan ta6e ba". "Duk da haka zan iya siyen motar?" Ta kad'a kai ta ce. "In hankalinki zai fi kwanciya ki siya mana..." Momin ta tareta da fad'in. "To wacce iri kike so, fad'a min idan kud'ina ba su kai bai in nemi taimakon Daddynki". Rumaisa ta yi dariya, ta ce. "Ta daidai kudinki nake so". Momi ma ta sake yin dariya ta ce. "Shikenan, zan ba ki mamaki". Auwal ya kula da kallon da Rumasa'u ta bi motarsa da shi ta madubi, kasancewar shi ma ya sa mata ido, kawai sai ya taka birki, sannan ya yo baya ya risketa. Ganin hakan ya sa ta dauke fuskarta zuwa kallon wani guri daban. Ta ma ajiye lema ta bude jaka ta ciro golas ta 'kwama. Auwal da ta 'kara jan hankalinsa, sai ya bude mota ya fito ya zagayo wajen tana share fuska. Ya dubeta sama da 'kasa ya ce. "Mece! Mace akwai waskiya, yadda kika yi fuskar nan ba dan na ga sanya kika zubo minido ba, in na kwana dubu ina rantsewa babu wanda zai yarda idan na ce kin 'kyasa". Da sauri ta dago ido ta dube shi, sannan ta dubi motar a ta'kaice, ta ce. "Ba kai nake kallo ba..." Ya tareta da sauri. "Wa kike kallo?" Ta nuna masa motar tana cewa. "Ga ta, ai ta fi ka kyau". Ya dan ja da baya baki bude na alamar shan mamaki. Ya kalli motar tasa, sannan ya dubi kansa yana gyara kwalar riga tare da gilashin idonsa, cikin dariya sosai ya dafa motarsa ya ce. "Yanzu wannan ta fini kyau don Allah" dube ni fa ki gani son kowa 'kin wadda ta rasa, ni ba dogo ba, ni ba gajere ba, ni ba fari ba, ni ba ba'ki can ba. Ga ido, ga dogon hanci, shape d'in ba irin na maza, komai ya ji fa kar ki bari ki yi asara yarinya. Mota ki kyaleta in kina raye sai ki ga kin yi wadda ta fi ta... Ni fa na ma tsaneta daga yau... Dan kishi ne da ni..." Yanzu ta daga kai suna duban juna ita da shi, kai tsaye ba za zummar komai cikin ranta game da shi ba, sai game da maganganunsa, kasancewarta mai sanyin hali tana son mutum mai barkwanci. Ba ta sami abin cewa ba, ya rigata da fadin. "Ya ya na ji zaki d'an yi manejin tafiyar da ni?" Karon farko ta yi murmushi ta girgiza kai. "Ka yi ha'kuri a fatar bakina kawai kalmar ta tsaya, na bi motarka da kallo. Amma zahiri ba ita din nake nazari ba, wata duniyar tunanin na tafi daban ka san ana haka ko?" Ya kada kai yana murmuashi. "Na sani, amma dai kin ji na ce bana son kishiya". Ta sunkuya tana murmushi ta dauki lemarta ta mi'ke tana fadin. "Ko dai kishiyi?" Suka yi dariya su duka. Ya kar6i lemar hannunta. "Zo mu tafi kin ga ruwa na shirin sauka, kar ya daki fuskarki ya yi mata illa". Ta girgiza kai tana murmushi. "Na gode kwarai, amma ba na hawa lift.." Da sauri ya tareta. "Wa ya fada miki lift za ki hau? Ke da motarki... Na ramtse zaki iya shafe komai a duniyata saboda haka ke ce alfarmar tawa ba ni zan zama alfarmarki ba". Ta 'kara dubansa da kyau, a sanyaye ta ce. "Wannnan dokin fa? Daga ganin sarkin fawa sai miya ta yi..." Ya sake tare da fadin. "Wata 'kila ina daga masu afkawa rijiyar so farad' d'aya. Tun daga nesa fa na hango ki inuwarki kawai na kalla na ji wata 'kwa'k'kwar zumunta ta sar'kafe zuciyata, da na 'karaso na kalli fuskarki sai kawai na ji mun zama JINI DA TSOKA d'aya. TA Sake dubansa da kyau tana dariya, abin da ta ke ji a ranta game da shi, shi ne ya iya dad'in baki, da ba ta dandani shekaru da yawa a duniya ba, farat d'aya zai wafce imaninta. Ta lumshe ido kai tsaye, ta ce. "Ba na son 6ata maka lokaci ko juyar da karramammun kalamanka. Ga shi ciki dole na za6i daya". Kai tsaye shi ma ya amsa. "Kin za6i 6ata min lokacin in dai ba kishiya ne da ni ba, karramammun kalamaina kar ki wani kalli karamcinsu, yadda ya kamata su fito a kunnenki, wallahi ban tsara su dan in burge ki ba, zo mu tafi don Allah". Bai jira cewarta ba ya bud'e mata 'kofa. Ta d'an yi jim, sai ta kasa tankwa6ewa ta shiga motar.....GORAN DUMA ******10 Ya rufe sannan ya zagaya ya shiga yana mi'ka mata lemarta ya tashi motar. Har suka zo bakin gate kalma daya ta had'u su. "Mene ne sunanki?" Kai tsaye ta amsa masa. "Rumaisa'u Aliyu Ahmad". Ya ce, "Sunanki mai dad'i. Ni sunana Auwal Ibrahim Hadi". Ba ta tanka ba, shi ma bai kuma tankawa ba har suka zo bakin gate, wata iska mai 'karfin gaske ta taso da alamun yanzu ruwa zai sauka. 'Kirjin Rumasa'u ya fara dukan uku- uku cikin matsananciyar fargaba. Ta dubi maza da matan da ke tsaitsaye cikin tashin hankali. Ta tatabar duk yadda hankali zai tashi bai fice fargabar za su yi mura ba, ita kuwa in ruwa ya daketa zai wahala ba ta yi ciwon da ya kusantarta da ita da kabari ba. Rage gudun da Auwal ya yi ya sa fargabar ta 'karuwa, saboda zaton sauke zai yi, amma sai ta ga ya nufi titi zai haura. Ta sauke ajiyar zuciya, muryarta na sar'kewa ta dube shi ta ce. "Da ka taimaka ka dauki matan can, na san ba za a rasa wad'anda za su yi hanyar da zaka yi ba. Za ka sami lada idan ka taimake su". Ya d'an ja fasali yana duban titi, ba tare da ya dubeta ba. Ya ce. "Allah Ya kawo mai taimakonsu, ni ba na daukar mata a motata". Ta d'an juma tana dubansa, duba na rashin fahimta, sannan ta ce. "Ni ba ka gane nawa jinsin ba ne?" Ya yi murmushi ba tare da ya dubeta ba. "`Ka'k'karfar ala'kar da zuciyata ta 'kulla da ke ya kori wancan 'kudurin nawa daga naki jinsin. Kin zama 'yar gida a zuciyata da duk wani abu da na mallaka". Ta gaji da kallonsa ta kawar da kai, ruwa ya fara sauka da 'karfi. Cikin sauri ta 6alle jakarta ta fito da rigar sanyi ta saka tana 'kumbiya-'kumbiya. Bai tanka mata ba, amma dai hankalinsa na kanta duk da idonsa na titi, tana bayyana alamun jin sanyi, amma kawaicinta ya hana ta 'karasa zuge gilashin 6angarenta, kuma da hakan yasa ya yi mata aikin da ta kasa yana cewa. "Na lura kunama ce ke, kawaicinki kuma na son hana ki abin da kike so..." Ta yi 'yar dariya ta amsa. "Ni da na zo ci rani har ga Allah bai kamata in za'ke ba". Ya watsar da wannann batun nata, ya ce. "Ina zan kai ki?" Ta yi dira-dira alamar canki-canki, sai ta kasa za6ar gurin zuwa ta yi shiru kawai sanyi na kad'ata. Hankalinta ya yi gida, amma ta ina zata bi ta je? Ina za ta fake ta sami motar? Ya juyo ya yi d'an nazarinta, cike da mamaki ya ce. "Ina zaki je?" Muryarta na rawa ta ce. "Ai na kasa za6a ne. Bana son santi, ruwa in ya dake ni illa yake min. Da makaranta zan je amma na fasa saboda sanyi. Yanzu in ka sauke ni kafin na sami motar ma ruwan ya yi min abin da ya ga dama". Ya ci gaba da kallonta cikin nazari, bai fahimci abin da yake son fahimta ba. Ya kad'a kkai ya ce. "Ni ma ba zan iya ajiye ki ruwan ya dake ki ba. Ina da ganawa 'karfe uku, sai dai a yi min uzurinta. Ina ne unguwarku?" Muryarta ta ci gaba da rawa, saboda laifin da ta ke jin zata yiwa kanta da gidansu. A ganta saurayi ya auketa kamar zubar da mutumci ne, amma kamar wannan za6in ya fi dukan ruwan. "Na gode Allah ya saka maka da alkhairi, a Gandun Albasa nake". Ya ce, "Hanyarmu daya ke nan, ni a Na'ibawa nake, ziyara na kawowa wani malamina, shekaru na biyu da barin makarantar na yi digiri na a nan na fara aiki a 'karkashin gwamnati. Ya kamata na ajiye iyali Allah bai kawo ba, sai yau Allah Ya yi min katarin d'aura d'amba". Rumaisa'u ta yi d'f! kamar ruwa ya cinyeta. Tausayin kanta ne ya hanata nazarin amsar da zata ba shi. Ta ji 'kaunarsa a ranta, sai dai ta 'ki yarda irin 'kaunar da ta ke d'orewa da aure ce, 'kauna ce kawai irin wadda d'an Adam ke wa wanda yake zaton mutumin kirki ne, ko kuma wanda ya yi maka alkhairi? Ta yi sororo tana kallonsa kawai yana jin kallon da ta ke masa a jikinsa, amma ya had'iye sn ya juya ya kalleta. Ta juya a hankali ta bi shi da kallo tare da sauke ajiyar zuciya, ba ta ce komai ba. "Ba ki da abin cewa akan abin da na fad'a?" Ta girgiza kai a nutse ta ce. "Kar ka 6atawa kanka lokaci na san ban cancanta zama iyali ba". Ya yi saurin yi mata duban rashin fahimta, amma ya ta'kaita zar6a6i wajen ce mata. "Ai ina tsammanin ba a yin komai babu hujja ko? Ki fada min dalilin zan duba na gani". Ta muskuta ta ce da shi. "Don Allah ka yi ha'kuri". Ya ya yi kasa'ke yana kallonta, sannan ya ce. "In dai ba laifi zan wa Allah ba, to ba zan iya hakura ba.. Ta tare shi ta fadin. "Ina fatan nan gaba ba zaka zarge ni da rufa-rufa ko yaudara ba?" Ya 'ki daukar maganarta da muhimmanci. Ba tare da nuna damuwa ba ya ce. "Ina saka rai Alkhairi ya biyo baya, idan kuma akasinsa ya samu zan dogara ga Allah, amma ki sani akwai laifinki ciki Allah ne ba za barki ba, musamman da yake a rufe kike ba ni uzirinki". Ta yi shiru kawai shi kuma ya share wannan maganar ya shiga tambayarta karatu da wasu abubuwa da yake jin suna da muhimmanci a cikin ala'kar da yake son 'kullawa da ita. Cikin ikon Allah sun wuce Gadon Kaya babu ruwan babu iska, ko hadarin ma babu, saboda haka ta ji ranya ta afu da son ta sauka ta hau motar haya ta 'karasa, amma ta kasa yi masa magana har sai da aka kira shi a waya ana nemanta wajen taro ya bayar da uzirinsa, yana sauke wayar ta ce. "Kawai ka sauke ni a nan na shiga mota na 'karasa, sai ka wuce sabgoginka". "Da yake tun farko na ke kika 'kirkirar min sabgogin ba, kar ki yi mamakin in na 'ki bin umarninki". Dole ta yi dariya ta share zancen. Ya tsayar da motar a harabar gidansu yana d'an zuba mata ido saboda yadda ya ga kamar ta kad'u da ganin wani da ya tsaya da motarsa kusan lokaci daya da su. Da sauri ya kalli motar dan ganin tana rawar jikin ficewa. Ta juyo ta dube shi da duban rashin fahimta. Ya nuna Yusha'u yana fadin. "Wane ne wancan?" Ta dubi Yusha'u sannan ta dube shi, a takaice ta ce. "Yayana ne". Ya yi zuru yana kallon Yusha'u, haka kawai ya ji hankalinsa bai kwanta da shi ba. Ya kad'a kai bisa dole ya bude 'kofar suka fita lokaci guda. Da sauri ya nufi Yusha'u da ke 'kokarin rufe mota ya yi masa sallama tare da mi'ka masa hannu. A wula'kance Yusha'u ya amsa idonsa na kan Rumaisa'u, sannan ya ce. "Yaya kuke da wannan?" Auwal ya yi zuru yana kallon Yusha'u da Rumasa'u yadda Yusha'u ya yi mata magana fuskarsa babu walwala ne ya ba wa Auwal damar nutsuwa ya karance shi. Akwai alamar nutsuwa a tsaiwar Rumasa'u, sai dai a rikice ta d'ebo masa amsa. "Dan ajinmu ne... Ya taimake ni ne saboda ruwan da ya tare ni.. Hanyarsa ke nan shi yasa ban nemi sauka ba da muka wuce inda ake ruwan. A gadarance Yusha'u ya ce. "Kina fad'a min hanyarsa ce dan kin shirya kullum ya dauko ki yana kawo ki ko? Ban san iyakar tsawon lokacin da zan dinga fad'a miki nan Arewa ba kamar can Kudu ba ne. Babbar 'kazanta ce mu a nan mace ta dauki namiji aboki..."GORAN DUMA *****11 Ganin yana neman tsinkata ta tare shi. "Lalura ce yaya Yusha'u, na yi gudun dukan ruwa ne". Yusha'u ya yi tsaki tare da yin gaba yana cewa. "Duk illar da dukan ruwan yake da shi, ai bai kai na sarayar da mutumci ba, koda yake wayewarku ta halatta muku haramci". Rumaisa'u ta yi suguri ranta ya yi mugun 6aci. Ta san Yusha'u bai iya magana ba sam! Haka yake yinta kamar kashi, amma a yau ta fara shakkar dan ta zo cin arzi'ki gidansu ne. A sanyaye ta dubi Auwal da ya yi shiru rungume da hannu yana kallon 'kasa, ta ce. "Na fa gode zan shiga ciki". Ya dago da alamun tunani ya dubeta. "Me yasa kika 'ki fad'a masa gaskiyar matsayin da na za6a mana? Sai kika ala'kanta mu da jabun dangantaka?" Ta dan ja numfashi, sannan ta amsa. "Har yanzu kai kake kid'a da rawarka. Da zaka bi ta tawa za mu yi sallama ne mu rabu har abada. Karatu ya kawo ni garin nan, ya kamata na ji da shi shi kad'ai... Mts! Ni bana son hargitse-hargitse wallahi". Ya fahimci cikin 6acin rai ta ke, saboda haka sai da ya shirya kalaman da zai mata. "Kina da wanda kika tsayar? Ta girgiza kai, fuskarta a daure. Ya numfasa ya ce. "Idan haka ne na tabbatar kin zo KANO ne dan mu had'u mu auri juna ba tare da na yi gi6i a karatunki ba, ki daina gaggawar yanke hukunci akan lamarin rayuwa. Da hakan gara ki zama mai dabarar tsara al'amuranki, ina neman alfarmar kar ki kore ni, kuma ban matsa miki ki so ni ba, amma ki ba ni dama mu fahimci ko zamu iya tafiya tare". Yanzu idonta cike yake da 'kwalla saboda takaicin kalaman Yusha'u, gidansu kawai ta ke tunowa da yadda ta ke da kima da mutumci a cikinsa. Auwal na ganin kwallarta ya dan shiga damuwa, amma a nutse ya tausasa murya ya ce mata. "Idan akwai matsala dan Allah ki fad'a mi kuka na nufin damuwa. A kalamaina ban ga abin da na fad'a da zai 6ata rai ba". Ta 'kir'kiro murmushin 'karfin hali dole ta ce masa. "Babu komai, Allah Ya yi mana jagora". Tun daga wannan ranar Auwal ya zame mata wani 6arin rayuwa, ya 'kware da samar da muhallan farin ciki a zuciyarta da kirkinsa da kuma yadda yake kula da ita da damuwa a cikin abin da ya dameta. Tun daga wannan ranar Auwal ya zame mata wani 6arin rayuwa, ya 'kware da samar da mujallan farin ciki a zuciyarta da kirkinsa da kuma yadda yake kula da ita da damuwa a cikin abin da ya dameta. Kullum sai ya zo gidansu, tare da cewa yana 6ata mata da yawan lokutai a waya, haka kuma takanas yake binta makaranta ya daukota, babban zunubinsu da ya tsayawa Yusha'u a rai ke nan saboda imanin da ya yi na cewa, duk yarinyar da ta je jami'a sai ta lalace. Ya rasa yadda zai fahimtar da Hajiya da Alhaji a matsayinsu na wadanda kamar su ke waliyantar da Rumasa'u saboda kyan hali. Rumaisa'u ta fara nisa cikin abin da ba ta za6a tsarabarsa a rayuwarta ba, wato SO, tana ji a ranta ita nakasashiya ce duk yadda so zai zama in ta amince masa wata rrana zai zame mata mad'aciya, amma a yanzu Auwal ya ture wannan tsarin a ranta, sai ya barta da zulumin yadda rayuwa zata kasance musu a gaba, zai rabu da ita ne, idan ya san ita sickler ce, ko kuwa zai yi shahadar aurenta? Za6i na 'karshe ne fatanta, sai dai zuciyarta na wuyatantar da yiyuwarsa. A yanzu sun fice watanni uku tare, duk wani laulayi da alayin cututtukanta babu wanda Auwal bai gani ba. Yau 'kafa ciwo, gobe ciki, jibi zazza6i, gata mura... Kai shi bai ta6a ganin mutum mai laulayi kamarta ba, sai ma 'kari saboda tsabar tausayin da ta ke ba shi. Kuma laulaye-laulaye nta ne ya koya masa tarin hanyoyin da zai nuna mata kulawa. Dan haka ya zama dan gida, dan gidan gaske a zuciyarta da zuciyar kowa ma a gidan in aka yi gefe da daya da murd'ad'd'e Yusha'u. Sai dai duk wannan sha'kuwar tasu ya rasa dalilin da yasa Rumasa'u ta 'ki amince masa manya su shigo maganar. Ya bata lokaci ya 'kara mata, amma har yanzu ta kasa gabatar masa da uziri, sai dai hakan ya 'ki ya dame shi dan yana da ya'kinin ya kai matsayin da ya fi 'karfin yaudara a zuciyar Rumasa'u, sai kawai ya zuba mata idon ganin gudun ruwa, musamman da yake karatun nata ya zo 'karshe. Wata rana sun fice goma na dare suna hira a zahiri daurewa kawai ta ke saboda cikinta da ke ta faman murd'awa. Ta daure din har suka yi sallama ta shiga gidan a birkice, zta wuce ciki Hajiya ta yi kiranta. "Zo nan Rumaisa'u, me yake faruwa na ga kina yamutse fuska?" Ta 'karaso ta zauna a gajiye. "Wallahi cikina ke min ciwo". Hajiya ta dubeta cikin tausayawa, ta ce. "Sannu, sai ki yi 'kokari ki sha magani, Hafsat taimaka ki murza mata tafarnuwar ki ta ce ki kaw mata". Hafsat ta tashi ta 6arin jiki tana yiwa Rumasa'u sannu ta wuce kicin ta d'ebo tafarnuwa masu kyau ta 6are, ta dandaka sannan ta zuba ruwa kofi daya ta tace da rariya ta kawowa Rumasa'u ta shanye. An fi awa daya kafin a samu ciwon cikin ya lafa, wannan ne kuma ya sa Hajiya ta tsokano maganar da ta ke jin yyinta ya zama dole dan ta fahimci Rumasa'u, so ya rufe mata ido tana shirin yin abin da za a ga laifinta. "Rumasa'u kun ta6a maganar ciwonki da Auwalu kuwa?" Alamun damuwa da nadama ya bayyana a fuskar Rumaisa'u, kwalla har ta cika mata ido, ta girgiza kai ta ce. "Ba mu ta6a ba Hajiya". Cikin zura mata ido, Hajiya ta ce. "Tyn farkon ne kika rasa hanyar sanar da shi Rumasa'u?" "Ban san za mu dore tare ba Hajiya". Hajiya ta yi shiru alamar nazari, sannan ta nisa ta ce. "Ni har na fara zargin ko ganin yawan laulayinki ya hana shi turo manyansa. Ga su Hafsa suna ta faman jiranki". Ta matse kwallar idonta tana amsawa. "Ni ce na ke dakatar da shi Hajiya, kuma na kasa sanar da shi dalili". Hajiya ta girgiza kai ta ce. "Wannan kuma ba dabara ba ce kika yi, za ki ta zama haka ne Rumaisa'u? Ai a rashin kira karen bebe yake 6ata, ki kokarta ku tattauna lamarin". Cikin sanyin jiki Rumaisa'u ta ce. "Shikenan zan kokarta Hajiya". Ta gama shin bacci ke nan ya mmako mata waya, ta dauka da kasalar rashin 'karfin jiki. "Auwal ba ka jin bacci?" Muryarsa a d'ashe ya amsa. "Na kwanta ya 'ki zuwa Rumasa'u, abubuwa barkatai sun cushe a 'kwa'kwalwata. Ga kadaici ga matsaloli". Ta dan yi dariya ta ce. "Me ya dami ranka haka Auwal?" Ya sauke numfashi.....GORAN DUMA ****12 "Kafin mu rabu na fahimci kamar ba kya jin dad'i, na taho da tauayinki da neman hanyoyin da zan samar miki waraka ko da na dauke kewa da 'karfafa gwiwa ne, amma duk kin bi hanyoyin da hakan za ta afku kin toshe. Na fara sarewa Rumasa'u dan na fahimci kamar kin raba zuciyarki biyu ne kin bar min daya na sani, dayar kuma kike wahalar dani da ita. Wata irin 'kaunarsa ta dingo bijiro mata, tana nemansa ta 'kwalla, tana kokawar daurewa yana gagara. "Auwal wannan ne zai hanaka bacci? To in dai ni ce ba za a haifi matsalolin da za su 6ata ranka da ni ba. Za mu sami lokaci nan kusa mu tattauna... Amma ina son ka a jiye a ranka soyayyarka ce ke hana ni yin abin da kake hasashe ina jinka da matsayin wani 6angare na jikina, wanda rashinsa zai gutsire rayuwata, amma na 'kure fatan hakan zai gaza faruwa". A raunane ya ce "Saboda me? Rumaisa'u duk yadda nake da matsayi a zuciyarki da sha'kar numfashinki d'igo ne na matsayinki a wata zuciyar, na kuma dami raina da son kai 'karshen buri a kanki kafin mutuwa ta runtse ganina, ke kuma kin kasa gane hakan..." Ta yi saurin tare shi. "Haba me ya kawo zancen mutuwa Auwal?" Shi ma ya tareta da nasa batun. "Ai ya zama dole, 'karuwar burika, cika wasu da su6ucewar wasu alamu ne na kusantar kabari sai raina yake ciwo da hasashen mutuwa zata iya riksta ba tare da na cika burin samunki ba." Ta fara hawaye sosai, dan haka ta jima ba ta tanka ba, har ta fitar da sautin kukanta kadan, sannan a cikinsa ta ce masa. "Ba na fatan dai-dai da kwayar zarra in cutar da kai Auwal, kuma bana son rabuwa da kai.." Ya tare ta a dan 'kuntace. "Shikenan sai ki bar mu muyi ta bulayi a soyayyar da ba ta da rana, wadda ta ki ta zuciya ta saba da ta fatar bakinki, kina sona amma kin kasa ba ni damar mu kasance 'karkashin sunna... wannan makahon so ne..." Ta yi kokarin tare kukanta, ta ce. "Akwai matsala ne Auwal, ni ke nan yau lafiya, gobe babu. Zan zame maka dawainiya in gundure ka, shi yasa ba na son cin karo da kukanka Auwal". Ya yi dariyar da ta fad'ad'a masa 'kirji ya ce. "Wa ya ke dorawa wani lalura Rumaisa? In Allah Ya so sai Ya yaye miki, ai babu cutar da ba ta da magani. Ita kanta cutar ma wani maganin ce, domin tana kankare zunubai... Ni ma da nake son daukar dawainiyarki ladan zan samu idan na kula da ke, duk sanda aka ce ba ki da lafiya sai na ji da tare muke sai na fi samun nutsuwa..." Ta 'kara fashewa da kukan da ya tsorata shi. A rikice ya ce. "Wai don Allah me yake faruwa ne? Rumaisa na kaa canko dalilan wannan kukan naki". Cikin kukan ta ce "Na gode da niyya da fatanka, amma ciwo na mutuwa ce kadai zata raba... Saoda haka aurena da kai yana nufin ka yi ta danniya da hakuri a kaina har 'karshen rayuwata, domin haka Allah Ya halicce ni, haka kuma Ya so ya ganni..." Ya rasa fassarar da zai wa maganganunta, rashin yanke shawarar ya sa shi yi mata tambaya a gajarce. "Wai wanne irin ciwo ne?" Kai tsaye cikin dakewa ta yi karfin halin amsa masa. "Sickle cell" Ya ji kamar ta doka masa guduma a 'kirji, cikin 'yan sakanni wasu miliyoyin tausayinta da fargabar yadda lamuransu zai kasance ya mamaye masa 'kirji, dan ya san ciwon sickle cell ba da wasa ba kasancewar wani abokinsa sikila ne ya dad'e da sanin yadda masu ita suke shan kashi sai dai wannan 'karamar matsala ce idan aka kwatanta da neman makomar 'ya'yan da za su haifa. Duk da a rikice yake bai kasa 'ko'karin tattara kalaman da zai 'karfafa mata gwiwa ba. "Mene ne matsala a kasancewar sickle Rumaisa, ko ke kika yi kanki dan me za ki raba kanki da ni ballatana Ubangijin da Ya yi ni Ya yi ki, ba domin na fiki ba? Ki zama mai tawakkali da ha'kuri da rayuwa sai matsalolinki su zame miki kaffara. In kuma domin wannan kike gina katanga tsakanin da kasancewa tare, to ni ban fahimci gatan da kike son yi min ko kike son son yi wakanki ba". Yanzu ta rage kukan da ta ke, dan a zahiri hankalinta ya soma kwanciya, duk da ta san bai kamata ya kwanta din ba. Ta nisa ta ce. "Kar ka yi gaggawar yanke hukunci Auwal, ka zauna ka yi tunani da kyaun duk matsaloli a kaina ka lissafo suka ga yadda zaka iya tarbarsu, yadda zaka dinga dawainiya da ni, dawainiyar aljihu da ta KWANJI, ha'kuri da ni wajen kukan ciwo da hakurin wasu kulawa daga gare ni lokacin ciwo in duk wadannan sun zama sau'ki a gareka Auwal makomar 'ya'yanmu ba zata zama sau'ki ba matu'kar ba ka kasance wanda ba zai bayar da gudunmowar da ba zaka haifi sickler ba". Ya ja numfashi sosai saboda rashin abin cewa, amma dole ya nemo shi. Ya ja numfashi sosai saboda rashin abin cewa, amma dole ya nemo shi. "Yin daainiya da ke, da kuma hakuri da laulayinki ni ba zan ta6a kiransu matsala ba Rumaisa, ina son ki soyayyar da nake jin ko mugun hali ne a jininki ba zata gaza ba, bare wannan jarrabawar ta Ubangiji da idan kika haye ta da tawakkali, na haye ta da jurewa dawainiya da ke zamu iya samun aljanna da ita. Batun 'ya'yanmu shi ne hanzari, amma wannan zai hana ki aure har abada ke nan Rumasa'u? Kafin haduwa da ni wanne tanadi kika yiwa kanki a fannin aure, me yasa kike ganin zan bayar da gudunmowar da zamu haifi sickler?" Ta amsa masa a raunane. "Ban ta6a fitar da rai zan yi aure ba, sickle cell kuma ba ciwo ne da za a ce ka auri mai shi ya zama waraka ba, domin za ku samar da iyali irinku ne gaba daya, amma dai ban ta6a hasaso aurena da rayuwar auren wani abu ne mai sau'ki ba. Ina sonka Auwal wallahi ba na fatan duk wani abu da zai cutar da kai, na san kuma ko yaya ne aure na zai iya zame maka matsala ko ta fannin 'ya'yanmu..." Ya tare ta da sauri. "Shi yasa na tambaye ki, wacce irin gudunmowa zan bayar da kike ala'kanta ta da haihuwar sickler?" Ta jima cikin shiru, sannan ta ce. "Idan ka ji a ranka zaka iya aurena, kuma a gidanku za a barka, shi ne zamu tuntu6i likitoci dan samun shawarwari, a iya maka gwaji kuma a gano kai waye, ta nan zamu iya sanin makomar 'ya'yan namu". Yanzu ya fara samun nutsuwa, saboda haka cikin doki ya ce. "In Allah Ya so cikin satin nan sai mu je asibitin, amma ki sani duk yadda bincike zai nuna ba na ji zai iya yi min katanga da aurenki. Ki cire shakku daga ranki Rumasa'u, ina yi miki soyayyar d aban san matsaloli a tare da ke". Ta yi shiru tsawon wasu sakanni sannan ta ce. "Abin da na fi so da kai Auwal ka fara tuntu6ar magabanka shawara a kaina, kar ka biyewa soyayyar zuciyarka ka yi abin da ransu ba zai ji dad'insa ba...q Ya tare ta kamar a 'kufule "Rumaisa'u sickle cell ne yakai girman da ba za a auri mai shi ba? Haba! Wannan maganar banza ki ke..." GORAN DUMA *****13 Ita ma ta tare shi a tausashe "Auwal babu yadda za a yi ni da kaina in 'kir'kiro abubuwan da zai nesanta mu da juna, amma duk abin da yake matsala ina guje mana shi kasancewara sickler na san da yawanmu irin matsalolin da suke fuskanta a rayuwa, ciki har da tsangamar da dangin miji ke masu matsaloli (sicklers) da za yi ta faman dawainiya da nauyi akan mijinsu ko kuma haihuwar dawainiya da su. Auwal wani lokacin ma mazajen ke tsangwamar matan akan sun zame musu nauyi... Kai wata ba sikilar ba ce idan suka taru ita da dangin mijin suka haifi sikila sai ya tattara laifin ya dora mata, wata mahaifiyar sikila da na sani ta ta6a bani labarin yadda mijinta ya fito kai tsaye yake 'kalubantarta akan cewa matansa hudu, amma ita kadai ta ishe da haihuwar sickler duk da cewa tare da mijin suka haifeta. Amma ka fahimta ba gudu nake a tsangwame ni ba ko ko kuma a 'kalubalance ni, na rantse maka babu wata wuya da ba zan iya jurewa ba, kawai dai bana sn ka yi abin da magabatanka za su yi kuka da kai. Idan aure zai shiga tsakaninmu ya kamata mu kori duk wani abu da muka san 'kalubale ne a rayuwarmu ta gaba dan a gaban ba mu da lokacinsa abin da ke gabanmu ma ya ishe mu". A sanyaye ya nisa, ya ce. "Na fahimce ki, in Allah Ya so zan yi abin da kika ce, amma dai dole mu hanzarta zuwa gwajin, ina son yin tanadin dukkanin wata juriya a kanki". Ta yi murmushin karfin hali cikin saduda ta ce. "To shikenan, Allah Ya za6a mana abin da fi alkhairi Auwal". Ya amsa cike da farin ciki. "Amin Rumaisa'u, Allah Ya sa mutuwa ce zata raba mu". Ta yi dariya ta ce. "Kuma ya zama ni zan rigaka mutuwa, na tabbatar rayuwa zata yi min 'kunci idan babu kai". Shima ya yi dariyar, ya ce. "To kin ga gara ni na riga ki mutuwar, saboda ni ba zan iya jure rayuwar da babu ke din ba". Da dad'i ya cikata kawai sai ta amsa masa da cewa. "Ina sonka Auwal!" Ya nisa cikin wani irin shauki ya ce. "Ni na san ina yi miki abin da ya fi So Rumaisa'u". Babu abin da ya motsa dan jua baya akan soyayyar da Auwal ke mata, sai ma wani 'karin tattali da tausayi da yake mata. Ya daura d'amarar sanin duk wani abu da ake gudunsa ga sickler, nisali ko a ina yake idan iska ta taso a wajen sai ya nemi Rumasa'u a waya, idan ta shiga motarsa sai ya zuge gilasai tsab, sannan duk wata sabga ta aljihu da zai mata ya juyar su kaf akan abubuwan da zai taimaki lafiyarta, dangin kayan sawa masu kauri da rufe jiki, dogayen riguna, hijabai, ni'kab har da safar 'kafa da hannu. Haka nan 6angaren abinci mawuyacin abu ne ya je mata ba tare da wani abinci da zai amfaneta ba, ko da mafi 'kan'katarsu ne wato rake. Tun daga nan hankalin Rumaisa da na iyayenta ya kwanta, suke ganin lallai ta sami mijin marainiya, Auwal ya zama dan gida a nan Kano, Rogo har ma da Abuja kowa a dangin Rumaisa'u. A nasa dangin ma Rumaisa'u, saboda haka na'am da girman gidan su Rumasa'u, saboda haka har sun amince da aurensu. Auwal ya kasa tarar mahaifansa ya sanar da su Rumasa'u sickler ce, saboda ta tsorata shi da yadda iyaye ke kar6ar lamarin dansu ya auri sickler, sai ya ke shakkar goyan baya daga nasa iyayen, musamman da yake shi kadai suka haifa, yadda suke zumudin aurensa ya fahimci yadda suka dora masa burin tara 'ya'ya saboda haka ya yi kirmisisi ya 'ki sanar da su, haka ma zuwa gwajin ya share shi saboda fargabar da ta cika ransa, alhalin ko me ma suka samo ba zai iya karya masa gwiwar auren Rumaisa'u ba. A haka manyansa suka je nemar masa auren Ruma aka yi duk yan hidimomi bisa al'adunsu aka sanya musu rana, in ta kammala karatu za'ayi. *BAYAN SHEKARU BIYU* Wata biyu ya rage aurensu, wanda za a had'a da na Hafsat da angonta Sani. Zancen duniya da ba ya 6uya, sai ga batun cewa, Rumaisa'u sikila ce a kunnen mahaifan Auwal. Kwatsam wani dare ya bar wajenta ya koma gida, ya shiga wajen Innarsa neman ruwan zafi, mahaifinsa ya yi kiransa fuska babu walwala a fuskarsa ko kad'an. Ya nemi guri ya zauna cikin sanyin jiki, mahaifin nasa ya ce. "Daga ina haka?" Sai ya ji tambayar ba wai, saboda babu irinta tsakaninsa da mahaifin nasa ko da can ma da ba shi da gurin zuwa ba a fiye tambayar ina ya je da dare ba ko dan yanayin aikinsa. Amma yau shi ne ake tuhumarsa inda ya je. Kawai sai ya yi 'kasa da kai, dan bai san abin fad'a ba, yana ji a cikin ransa nan da wata biyu Baban nasa ba zai ganshi a wannan lokacin ba ma bare ya tambate shi. Mahaifiyarsa ta shigo da fulas har da farantin kayan shayi ta dire a gabansa, zata fara hada masa ya yi sauri ya kar6e ta yana godiya. Ta nemi guri ta zauna, shi kuma jiki a sanyaye ya fara bude gwangwani yana sauraron mahaifinsa da ya dora. "Yaya me jikin?" Ya dago da sauri ya dubi mahaifinsa hankalinsa a tashe, amma fuskarsa ta kasa nunawa. Ya tattare 'kululun da ya taso masa a ma'kogwaro ya kora shi ta hanyar hamud'ar madarar ya hadiye sannan ya ce wa mahaifin nasa. "Abbba ina ka san ba ta da lafiya?" "Zancen duniya ai ba ya 6uya". Abban ya fada cikin rashin kulawa tun daga nan Auwal ya sha jinin jikinsa, kawai sai ya ci gaba da hidimar gabansa. Abban ya gyara zama ya ce. "Wato Auwal ka san yarinyar nan sikila ce ba ka sanar da mu ba, dan kawai ka na son abin da zaka sanya mu 'karanta?" Auwal ya dago cikin bugun zuciya ya dubi mahaifinsa bakinsa na rawa ya ce. "Abba... Mene ne 'karantar a auren sickler?" Cikin 6acin rai Abba ya ce. "Auren sickler ba 'karanta ba ne, kantafi ne kawai da rayuwar 'ya'ya da ta aljihu... In da 'karantar ta fito shi ne zuwan da zamu yi mu ce mun janye..." Tuni har hawaye ya fara zuba a idon Auwal, wanda ke kallon mahaifinsa garau da alamun rashin kwanciyar hankali bare kimtsa maganar da zuciyarsa ya kamata ta haifa, bakinsa kuma ya furta hakan ne kuma ya sa Innarsa ta sami sararin shiga maganar. "Wannan d'an ka yi wauta in dai ka san cewa yarinyar nan sickler ce, amma ka juya wa matsalolinta baya zaka aure ta... Muna zaune 'kalau ka kawo mana sickler dangi..." A yanzu ya sami ga6ar abin cewa wanda ra'ayin kansa da na zuciyarsa suka yi tarayya yana 'kokarin tsayar da hawayen ya tare mahaifiyarsa. 'Idan dai zan iya haihuwar da Rumasa'u, to lallai zan iya haihuwar sickler da wata mai lafiya wadda ba sickler ba ce..." Shi ma mahaifinsa da yake zazzafan mutum ne sai ya tare shi. "Idan Allah Ya hukunto hakan na tabbatar idan za ka haifi sickler goma da Rumaisa'u idan wata ce sai Allah Ya ta'kaita ka haifi hud'u..." Auwal kawai sai ya yi shiru ya ci gaba da shan shayin da ya fi kama da shan magani, 'kwalwarsa ta tsaya cak! Da 'kirkirar mafita ko ta 'kofofin da duk ransa ya raya masa har ya gama kushe masa aure da Rumasa'u tsab ya 'karkashe batunda da haramta aurem. Auwal dai bai tanka ba, har mahaifin nasa ya diga aya sannan cikin rashin hayyaci ya tashi ya fice daga falon. GORAN DUMA BY M.I.S.B *****14 Tsawon daren nan ba zai iya dorar da wani abin kirki da ya yi ko lissafinsa ya yi ba dangane da yadda zai 6ullowa al'amarin, ya san dai ya gurji kukan da tsananin 'kauna da tausayin Rumasa'u ya haifa, kuma su suka hana shi hasala komai bayan ya 'koshi da ji a ransa duk tsanani ba zai iya rabuwa da Rumaisa'u ba. Sai 'karshen dare ya sami runtsawa saboda haka bai sami sallatar asubahi ba, 'karfe shidda dai-dai wayar Rumasa'u ta farkar da shi. Yana ganin sunanta kan wayar sai da 'kwalla ta taru a idonsa, ya daga yana kokarin gyara muryarsa saboda daskarewar bacci da kuma ta ma'ka'kin tausayinta da ya ma'kale maasa a ma'kogwaro. "Rumaisa'u" Muryarta tar ta ce "Duk wadannan gaibu ne Abba, babu wanda ya san abin da gaba zata haifa, kamar yadda ba mu isa za6ar abin da muke so mu 'kyale wanda tanmu yake hasashen hadari cikinsa ba. Da dan Adam na da iko akan za6in abin da yake so na matar da ta zarce Rumaisa saboda abin da nake mata ya fi so, shi yasa ban san ko wacce irin matsala ba a kanta, amma da yake na san ba dukkan abin da mutum ke so yake samu ba, tun bayan umarninka na jiya na kwana ina gwajin yadda zan iya rayuwar da babu Rumaisa'u. Na yi ta cin karo da gazawa, har ta fara barazanar keta min zuciya. Ban fitar da rai zan iya din ko kuma zan kasa ba, na san a biyu daya ce zata faru, ko in iya d'in in wanzu bisa tsarin da ka za6a min, ko kuma in gaza ta dalilin in bijire maka ba, wanda babu irin haka a tarbiyyar da ka ba ni... Abba kar ka damu da yadda ka ganni har in mutu in Allah Ya so ba zaka had'u da abin kuka ta silata ba..." Yanzu hawaye ya fara cin 'karfinsa, kuma shi ne ya tilasta shi diga aya ba don ya rasa abin cewa ba. Duk jikin mahaifinsa ya yi sanyi, sai kallon Auwal yake shi ma kamar ya yi hawayen, amma wata zuciyar na tuna masa siyasar Auwal ta dadin baki da sadaukarwa har ka yi masa abu ba tare da kana da niyyarsa ba, wannnan ne yasa ya daure ya ce. "Abin har ya yi zafi haka Auwal? Ba zaka iya fitar da yarinyar nan a ranka cikin ruwan sanyi da dalilin matsalarta a rayuwarka da ta 'ya'yanka ba?" Auwal ya muskuta da murmushin ya'ke alamar akwai magana fal a cikinsa, sai dai yadda zai furta ya yi girma, don haka ya hadiye ta kawai ya bi mahaifinsa da shiru, har mahaifin nasa ya gaji da jiran cewarsa ya nemi guri ya zauna idonsa akan Auwal. "Tun farko ka san Rumasa'u sickler ce?" Auwal ya kad'a kai, mahaifin nasa ya dora wata tambayar. "Wanne mataki ka dauka akan yadda za ku rayu tare, ko kaucewa yadda za ku haifi 'ya'yan sicklers?" Auwal ya jima kafin ya tattaro abin cewa. "Ta yi 'kokarin hana ni aurenta tun ranar da muka had'u na dage. Duk matsalolin da ka lissafo min da bakinta ta lissafo min su, amma ba su gigita ni yadda suke gigita ku ba... Da ta ga haka sai ta shawarce ni yin gwaji dan sanin makomar 'ya'yanmu, na amince a sannan amma sai na ga gwajin 6atawa kai lokaci ne da tanadar wa kai fargaba, don na ji a raina ko wane irin sakamako gwajin zai haifar ba zan iya barinta ba, saboda haka na ce ta bar maganar gwaji". Mahaifinsa ya jima cikin shiru yana jiya maganganunsa, kafin ya yanke hukuncin d ayake jin shi ne na 'karshe. "Gaskiya ta yi hange mai kyau saboda haka shawararta ita ce abin bi. Ka je ka yi gwaji idan akwai matserar 'ya'yanku sai ku yi aure, idan kuma babu, to ku dubi girman Allah ku ceci 'ya'yanku ta hanyar ha'kura da juna". Duk da Auwal ya ji maganar mahaifinsa da kamar maimaici kawai, ma'ana babu wani sassauci haka ya cije a ladabce ya gyad'a kai. "To na gode Abba". Ya m'ke kuma salin-alin ya fice ya shiga 'kwan'kwasa falon Innarsa. Auwal bai 6oyewa Rumaisa'u komai ba dangane da yadda suka yi da mahaifinsa da hujjarsa ta sanin kukanta nasa ne, kukansa ma nata ne. Tuni suka yiwa juna wannan al'kawarin na tarayya akan matsalolinsu dan nemo hanyar araka. Rumasa'u ta jima ba ta yi magana ba, ba dan rashin abin cewa ba sai dan saisaita maganar don gudun kada tayi muni a kunnen Auwal ko kuma ya zama wani mataki na karyar masa da gwiwa. "Kin 'ki cewa komai Rumasa?" Ya fada bayan ya gaji da jiran cewar tata. Ta gyara tsaiwarta ta 'kara jingina sosai da motarsa saboda tana jin jiri. Ta yi murmushin 'karfin hali ta ce. "Abin da Abba ya yi shi ne ya kamata Auwal, so ne tun farko ya ke runtse mana ido alhalin wani dad'in gushi ne kawai a cikin rayuwar aure, wanda ake 'kulla si domin kammaluwar iyali. Ya wajaba ne mu samarwa iyalanmu makoma ta gari, ba ya kamata ba Auwal". Shi ma ya yi murmushin 'karfin hali bayan ya ji a ransa kawai 'karfafa masa gwiwa ta ke so ta yi ba ainihin abin da ke cikin ranta ke nan ba, ya ce. "Kamar ke da Abba kuna mantawa ba a yiwa Allah wayo, ke kanki aya ce Rumasa'u, Innarki da Abbanki babu sickler ciki, amma suka haife ki..." Ta tare shi da dariya. "Ba 'kokarin yin wayo ba ne, 'ko'karin amfani da hankali ne, wanda Ubangiji Ya hore mu da shi dan za6ar abin da zai amfane mu da gujewa abin da zai cutar da mu, abin da ya faru da mu cikin akasi mun yarda daga Ubangijinmu ne ba tare da sakacinmu ba, sai mu yi fatan zamowarsa kaffa". Auwal ya yi zuru kawai yana kallonta sannan ya nisa ya ce. "Ban sna me yasa duk cikin lissafinku ba kwa duba uban yaran da samun su yake 'kila wa 'kala ba, sa ku kuka himmata sarayar da shi alhalin shi ne a hannunku. To zan fada miki abin d ana fada Abba jiya na kwana da 'kokarin lissafa yadda zan yi rayuwar da babu ke, na ji kamar numfashina zai yanke daga lissafin kawai ba tare da fitar da sakamako ba, amma dai ban cire rai daga rahamar Ubangiji ba, duk za6in da ya yi min ina fatan rahma da jin 'kanSa a ciki". Ta zuba masa ido, dauriyarta na kokarin 'karewa. Kasa gajiya da kalonsa da ta yi ne ya sa ita ma ta tabbatarwa kanta wa'ka kawai ta ke, amma tursasa kanta za6ar tsaka-tsakin al'amura, sai dai kuma ta kasa hana zuciyarta rauni da son nuna gazawa da ta tsaya kawai ga bayyanawa ta hanyar 'kura masa ido cikin hawaye. Haka suka tsaya ita kuka, shi hawaye, har daga 'karshe ya zagaya mota ya shige yana cewa. "Zo mu je asibitin". Ta yi saurin duba agogon hannnunta da ya nuna 'karfe sha daya da mintoci sha hud'u. Ta bude motar ta sunkuya a tausashe ta ce masa. "Bari na sanar da Hajiya". Ya yi saurin tare da fadin. "Rumaisa'u kar ki sanar da kowa matsalarmu fa, umarni ne da kuma kokarin kwantar da hankalinku ke da Abba zai kai ni gwaji, ba dan na yarda da iya raba ni da ke ko ya yi wani abu a cikin sonki ba. Ya kamata ki ri'ke wannan kada ki yi 'kokarin raba ni da kanki, son da nake miki mutuwa ce kawai zata iya raba ni da shi". Ta sororo cikin sanyin jiki tana kallonsa. Ta hadiye kwallarta ta ce masa. "Auwal wai me yasa ka damu da kira mana mutwa? Ai ba sai ka kirata zaka bayyana min kana sona ba,.." Ya tareta cikin kyalkuala dariya. "Me yasa ba kya so na kirata? In akiranta ne dan na sna ita ce mai YANKE 'KAUNA, duk yun'kurin raba mu da kuke ni dai na tabbatar ita kadai ce zata iya raba ni da son da nake miki. Amma na san ba ni da karfi ko dabara a cikin aurenki yadda Ubangiji Ya so haka zai yi". Ta murza yatsu tana dariya, ita ma ce. "Shikenan. In Allah Ya so ni da kai mutu ka raba". Ba ta jira cewarsa ba ta wuce. Ya bi ta da kira, ta tsaya ba tare da ta juyo ba, ya dan daga murya. "Na fa gaya miki kar ki fad'a". Sai kawai ta kad'a kai ta wuce tana dariya.GORAN DUMA 15 . . Dr. Hadiza ta gyara zama ta janyo wani fayil cikin murmushi ba tare da dubansa ba ta ce. "Soyayyar da kake mata da amincewarka na aurenta a matsayinta na mai sikila shine matakin farko na magance matsaloli ko yi musu kallon 'kanana a cikin aurenku, idan duk kun yarda da wannan to kamata ce ku zo min tare, duk abin da zan fad'a tare zai amfane ku, idan ma 'karfafa gwiwa ne tare zai 'karfafa muku". Auwalu ya jima bai tanka ba, sannan ya ja numfashi cikin kasa hankula barkatai ya amsa. "Haka Allah ya tsara na riga na taho ni kadai d'in, amma na daura damarar zantar da ita komai kamar yadda kika zantar da ni, hikimia ko ta aro ce zan aro in yi 'kokarin fahimtar da ita". Ofis din ya dauki shiru sai 'karar takardun da likitan ke bud'awa da kuma bugun zuciyarsa da ya cika masa kunne da rud'u. Likita ta dago kai ta dube shi da wata takarda a hannunta tana juyawa. "Sakamakon gwajinka ya nuna cewa, kai AS ne, ma'ana zaku iya haihuwar mai AS za kuma ku iya haihuwar mai SS, wato ranar da ka bayar da A ta bayar da S dinta za ku samar da d'a irinka (AS). ranar kuma da ka bayar da S din ka dama ita abin da zata bayar ke nan, to za ku samar da d'a SS (sickler) irinta. Abin da zan 'karfafa muku gwiwa da shi a nan shi ne, ku shiga cikin hankalinku ku kyautata zaton alkhairi ga rayuwar 'ya'yan da zaku samu a gaba, wanda Ubangiji ne kadai Ya san yadda za su kasance. Idan Allah Ya ga dama sai ya azurta ku da 'ya'ya goma babu sickler ko daya a ciki, ikonSa ne Ya umarce ka ka yi ta bayar da A dinka har ku gama haihuwarku, idan kuma Ya si zai iya jarabtarku da haihuwar sickler, Allah babu yadda bai iya ba. Kai kanka zaka iya haifar sickler ba tare da ka auri Rumaisa'u sickler ba. Idan wadda ka aura din AS ce kamai ai za ku iya tarayya wajen bayar da S zalla ku samar da sickler. Abin da ya ke a rubuce dai babu wanda ya isa kankare shi, dukkanmu ba dan ba damarmu muke, Ubangijin da Ya yi ka AS shi ya yi A. Ba don ya fi sonsa da kai ba. Kuma shi ya yi S.S ba dan Ya yi masa laifi ba, sai dan haka Ya so, haka Ya ga dama. Dan haka babu wani dalili da zamu dogara da shi wajen hana aurenku ina fatan ka fahimce ni? A 'karshe ina shawartarka da kwantar da hankali da mayar da lamari ga Allah, na tabbatar zai saka maka da dubun alkhairi idan ka dogara da shi ka auri wannan baiwar Allah ba tare da ka guje ta ka gadar mata da takaici a zuci ba, kai kuma ka saka 'karfi da dabara a cikin taka rayuwar ba, yadda kake nuna wa ina fahimceka da cewa ka dauki ciwonta naka, wannan ko wanne sickler ke bu'kata. A yarda da rauninsa, a tausa masa idan ciwonsa ya taso, a yi masa uziri a taimake shi ta wadannan hanyoyin kula da maganinsa, kaucewa abin da zai motsa ciwonsa, hana shi aikin wahala tare da 'karfafa masa gwiwar cutar da yake bautar Ubangiji ce. Idan ya yi tawakkali ladansa ba zai lissafu ba. A yarda in an haifi d'a sickler da shi ba shi kadai ya haifa ba, da sauransu. Duk wadannan dabi'un taimakon na zace su a kai malam Auwalu dan Allah ka yi 'ko'kari kar ka ba ni kunya". Tunda ta ke magana hankalinsa ya kasu uku, daya a kanta, daya akan batun mahaifinsa (ka je ka yi gwajin idan akwai matserar 'ya'yanku sai ku yi aure, idan babu to ku dubi girman Allah ku ceci 'ya'yanku ta hanyar ha'kura da juna), daya kuma wanda ya ke da kawo mafi tsoka akan 'kauna da tausayin Rumaisa'u, wanda a yanzu shi ya sa shi fitar da 'kwalla bayan Dr. Hadiza ta dire, zuciyarsa ta dame shi da son ya fad'a mata 'dama can ba ni ne matsala ba, mahaifina ne'. Sai kuma ya ga fada matan wani rage karsashi ne a dogon lokacinta da ta 6ata tana ba shi shawarar rayuwa da Rumasa'u, wanda ko ba a shawarce shi ba, abin da burika da ra'ayoyinsa ke zartarwa ke nan. Ya hadiye duk wata damuwarsa ya yi mata godiya sosai, tare da nuna 'karfin imanin babu abin da zai raba shi da Rumasa'u, suka yi sallama dukkansu suna yiwa juna godiya. Bayan ya fito asibitin ya yi mazantakar wucewa ofis dan gwada 'karfin hali da na zuciyarsa da koyawa kai jarumta cikin lamarin d ake fin 'karfin iyawa, mahaifinsa ne abin jinsa, wanda alamu ke nuna yana son saka 'karfinsa wajen taruwar iyalai da babu tahalikin yadda za su samu. Rayuwarsu zata kai ga haihuwar ko zata gaza, za su haifa din ko ba'kararru ne su? Duk wadannan gaibu ne babu wanda ya san shi sai Allah, idan ya sa wa kansa damuwar rana guda a kansu ya had'a wautar da zata kamanta shi da rashin hankali. Suna zaune a falon da suke hira, idan sun so jimawa suna hirar ke nan, idan ba za su jima ba dama a motarsa suke jingina su yi tad'insu. Rumaisa'u ri'ke da takardar sakamon gwajinsu tana juyawa, idan akwai abin da ya fi 'kunci da d'aci to ranta shi ya yi. Abin da ke shirin faruwa da ita zuciyarta ta 'ki yarda zata iya daukarsa duk yadda ta yi 'ko'karin gwadawar. Auwal ma ko da gwaji ya kasa ce mata wani abu. Tunda ya ba ta takardar har sai da ta gaji ta tsinka, cikin yi masa kallon kai tsaye. "Auwal ban ta6a jin kaico da nadamar kasancewa ta sickler ba sai a yau. Na tsani kaina da duk wata tawaya da ta ke son raba ni da kai Auwalu..." Ya tare ta cikin dakewar 'karfin hali. "Kar ki yi sa6o Rumasa'u, wannan wacce irin wauta ce? Ki shiga cikin hankalinki, duk yadda za ki so ni bayan Ubangijin da ya halicce ki ya wajabta in bi. Tsanar kanki da tsanar kasancewarki yadda Ubangiji Ya tsaro ki tawaye ne da butulci gare Shi..." Ta dam'ke bakin da ya yi mata amfani biyu, hana sautin kukanta fitowa da nuna nadamar abin da bakin ya fad'a, cikin raunanniyar muryar kuka ta ce. "Astagfirullah, Allahumma gafirni war hamni..." Ta zare da shesshekar kukanta. Shi ma duk yadda ya so ya daure sai dauriyar ta fi 'karfinsa ya fara hawaye, ba dan yana zatar musu rabuwa ba, sai dan shaukin yadda suke son juna da tausayin Rumasa'u wadda ake son raba su ta dalilin aibun da ba ita ta 'kaga wa kanta ba. Mace mai sanyin halin da ta kasa fitowa kai tsaye ta ga laifin mahaifinsa da ke son raba su, 'karfinta da yaji ta ke juyawa aibata mahaifinsa baya. Sun jima suna 'yan koke-kokensu kafin ita da ta fi shi sharafin damuwa ta kuma soko wata kato6arar. "Da za a ba ni za6in rayuwar da babu kai ko mutuwa, Auwal da gudu zan za6i mutuwar, har yau ni ban san ta inda zan fara rayuwar ba, shi yasa ka ji na kasa 'karfafarka bin umarnin Abba don Allah ka yi min wannan uzirin... Ina sonka ban san babu a kanka ba Auwal, wannan ciwon ya fi sickle cell ciwo a raina..." Ya tare ta cikin kasa tattara kalaman da za su fidda ma'ana sosai, saboda rud'ani. "Ba zamu rabu ba Rumasa'u ki daina ambato mana rabuwar... Ni duk maganar nan ma ta gundure ni wallahi". Ta dago ta bi shi da kallo cikin hawaye. "Haka ne burina Auwal, amma ba zan yaudari kaina na dorar da shi da fatar baki ko ture abin da ya kamata na duba ba". Suka kuma daukar shiru sannan ta goge hawayeta 2a fuskance shi "Ka sanarwa Abba?" Ya yi saurin girgiza kai yana kallonta sararo. Ta 'kokarta ta ce. "Sai ka yi gaggawar sanar da shi, ya yanke mana hukuncin da Ubangiji Ya za6a mana, fara shirin zama tare ko kuma shiga makarantar koyon juriya da rashin juna, ko wanne Ubangiji Ya za6a mana muna fatan ya zama alkhairi a gare mu".Ba ta jira cewarsa ba ta mi'ke zata bar falon.... . Dan Aunty August 4 at 9:12 PM · PublicGORAN DUMA 16 . . Ya yi saurin dakatar da ita da cewa" Duk kurin da na gama yi na cewa babu abin da zai sauya a cikin soyayyarmu da auren kin fayalar da shi kenan, dama kin tura ni gwaji ne dan ki rabu da ni Rumasa'u?" Ta yi saurin dawowa gabansa ta dur'kushe tana girgiza kai cikin hawaye. Ta kasa magana sai kallonsa da hawayen, shi ma ya motsa baki, ya yi maganar amma ya kasa, har sai da ta gama nata alayin ta riga shi samo abin cewa. "Ina sonka Auwal... aurenka shi ne babban burin da da ace ina da iko zan kusantar da shi tunda ba ni da ikon na yi imani aurenko rashinsa da ni kaina da kai duk muna shawagi ne cikin hukuncin Ubangiji, zai iya kusantar da shi dan rahamarsa a gare mu da ni'imarsa. Zai iya tankwa6ar da shi dan isarSa a kanmu da zartar da abin da mu ba mu san da shi ba, dan haka duk abin da ka ji na fad'a kar ka yiwa ubangiji biyayya da faranta ran Abba, a wani hannun kuma da 'kin biyewa zuciya sakokinta... Ina sonka Auwal".... Ya kai 'kololuwan rauni da tausayin Rumaisa'u wanda ya 'kara masa miliyoyin kaunarta, ma'kogwaron ya cunkushe da shu, shi yasa duk yadda ya yi 'kokarin ya ce wani abu ya kasa, kawai sai ya dauki takarda ya nemi hanyar fita. "Ba zamu rabu ba Rumaisa'u ki daina ambato mana rabuwar... Ni duk maganar nan ma ta gunudure ni wallahi". Ta dago ta bi shi da kallo cikin hawaye. "Haka ne burina Auwal, amma ba zan yaudari kaina na d'orar da shi da fatar baki ko ture abin da ya kamata na duba ba". Suka kuma daukar shiru sannan ta goge hawayenta ta fuskance shi. "Ka sanarwa Abba?" Ka yi saurin gaggawar sanar da shi, ya yanke mana hukuncin da Ubangiji Ya za6a mana, fara shirin zama tare ko kuma shiga makarantar koyon rashin juriya da rashin juna, ko wanne Ubangiji Ya za6a mana muna fatan ya zama alkhairi a gare mu". Ba ta jira cewarsa ba ta mi'ke zata bar falon. Ya yi saurin dakatar a ita da cewa. "Duk kurin dakatar da na gama yi na cewa babu abin da zai sauya a cikin soyayyarmu da auren kin fatalar da shikenan, dama kin tura ni gwaji ne dan ki rabu da ni Rumaisa'u?" Ta yi saurin dawowa gabansa ta dur'kushe tana girgiza kai cikin hawaye. Ta kasa magana sai kallonsa da hawayen, shi ma ya motsa baki, ya yi maganar amma ya kasa, har sai da ta gama nata alayin ta riga shi samo abin cewa. "Ina sonka Auwal... aurenka shi ne babban burin da da ace ina da iko zan kusantar da shi tunda ba ni d aiko na yi imarin aurenko rashinsa da ni kaina da kai duk muna shawagi ne cikin hukuncin Ubangiji, zai iya kusantar da shi dan rahamarsa a gare mu da ni'imarsa. Zai iya tankwa6ar da shi dan isarSa a kanmu da zartar da abin da ba mu ba mu san da shi ba, dan haka duk abin da ka ji na fada kar ka danganta shi da kanka Auwal, danganta shi ga son yiwa ubangiji biyayya da faranta ran Abba, a wani hannun kuma da 'kin biye zuciya sakokinta... Ina sonka Auwal". Ya kai 'koluluwan rauni da tausayin Rumaisa'u wanda ya 'kara masa miliyoyin 'kaunarta, ma'kogwaron ya cunkushe da su, shi yasa duk yadda ya yi 'kokarin ya ce wani abu ya kasa, kawai sai ya dauki takardarsa ya nemi hanyar fita. Ba ta takura kanta da binsa ko kiransa ba, kawai sai ta raka shi da mafi sau'ki cikin abin da zata yi, wato binsa da kallo har ya fice, sannan ta durkushe ta fara kuka mai dalilin. Kwana biyu babu labarin Auwal, babu wayoyinsa. Ta yi 'kokarin kira duk a kashe. Ta yi tunani ta yi issafin duk ta kasa cankar dalilin 6uyansa ko kuma abin da ya 6oye shi, duk canki-cankin da ta ji yana neman tafiya da numfashinta. Auwal ya janye neman aurenta, hasashen da ke kusan tafiya da numfashinta. Auwal ba shi da lafiya, zargin da yake tilasta mata son lallai ta san halin da yake ciki. Kwana na uku ya kama alhamis, ba ta yi shawara da kowa ba ta wanke 'kafa da yammaci ta dauki Hafsat suka tafi Na'ibawa gidan su Auwalu. Tun a hanya Hafsat ke tambayarta abin da ke faruwa, musamman ganin yadda hankalinta ya yi matu'kar tashi ba kamar a lokuta baya ba, inda ko ya shafe kwanaki bai zo ba bata damuwa. Rumasa'u ba ta 6oye mata komai ba ta zayyana mata yadda suka yi. Hafsat ta ce, "Ina ganin gara mu fadawa Inna gaskiyar lamari idan muka je". Rumasa'u ta dafe 'kirji ta ce, "Wai rufa min asiri, kada a ga za'kewata da wawancina." "Ba wawanci ba ne, Rumasa'u, yarda ce da nuna bu'katuwar al'amarin nan." Kallo daya Innar Auwal ta yiwa Rumaisa'u ta gane ta, duk da ba su ta6a haduwa ba. Amma ta yi mata farin sani a hotuna dan haka ta sauke su da rawar jiki kamar zata goya su. Kasala da kunyar da Rumasa'u ke bayyanawa ya sa Innar Auwal jin wani irin tausayinta ya ishe ta. Ta zauna suka gaisa cikin girmama juna. "Duk manyan naku lafiya ko?" Inji Innar Auwal, Hafsat ta amsa "Lafiya kalau". Rumaisa'u kai na 'kasa. Suka dauki shiru kowa da abin da zuciyarsa ke sa'kawa, Rumasa'u na jin tsanar kanta da kankambar zuwa gidan surukai, surukan ma wanda auren d'an nasu da damuwa da 'kila wa'kala, amma 'kaunar dan nasu da sanin halin da yake ciki ya kore nadamarta mai taurin kan da ta 'ki 'karuwa, sai ta tsaya suke ta damun zuciyarta tare. Yanzu abin da ta fi d'ko shi ne, ta ina labarin Auwal zai 6ullo mata? Can Inna ta nisa ta ce. "Ku sha lemon don Allah, Nuraddin nake jira ya shigo ya dubo shi ko ya farka, yanzu da abokansa suka zo duba shi suka ce yana barci". Wani irin tashin hankali ya bayyana a fuskar Rumasa'u. Ta dago ido ta dubi Inna, amma ta kasa cewa komai sai bakinta ne ya ke rawa. Hafsat ce ta yi mata abin da ta ke son yi cikin jimami da sanyin murya, ta ce. "Ayya ba shi da lafiya?" Inna ta jinjina kai, ta ce. "Ba shi da lafiya, na yi tsammanin ma dubiyarsa kuka zo, kwana biyu ke nan yana fama da wani matsanancin ciwon kai". Rumaa'u a rikice ta ke amma ba ta fasa tambayar Inna ba "Inna dama yana yin irinsa?" Cikin nuna jimami Inna ta ce. "Dama yana da yawan ciwon kai, tun yana 'karami ya yi san'karau shikenan yawan ciwon kai ke bibiyarsa, sai dai bai taha tsananta masa irin wannan lokacin ba, amma yau da sau'ki ba kamar jiya ba. Yau har ya ci abinci an yi hira da shi, ftowar mu ke nan bacci ya dauke shi". Rumaisa'u ta sauke numfashi cike da dukan zuciya, duniyar gaba daya ta yi mata 'kunci ba ta san lokacin da kukan zucinta ya fito fili ba, had'e da hawaye har da shessheka. Hafsat da Inna suka bar yiwa juna jajen rashin lafiyar suka koma rarrashinta. Jikin Inna na 6ari ta mi'ke ta fita tana cewa. "Bari na sanar masa da kaina, ki je ki ganshi, jiki fa ya yi kyau". Bayan Inna ta fita Hafsat ta ci gaba da tausar Rumasa'u, yayin da Rumaisa ta d'ago da hawayen ta ce. "Hafsat ni kadai na san yadda na ke jin Auwal a kirjina, duk wani abu na illah ko mai nuna salwantarwa a Auwal ba na iya jure masa, ina son Auwal, kawai shi ne abin da na sani". Hafsat tsakaninta da Allah ta ce. "Yadda na ke addu'ar Allah ya bar ni da Sani, haka na ke addu'ar Ya barki da Auwal ko ma fiye, don na tabbatar kun yi dacewar da abokan burmi irinku su ke wahala". Shigowar Inna ya tsayar da maganar Hafsat, ta ce. "Yauwa ku 'karasa, ya farka na same shi yana sa wayarsa caji". Rumasa'u ta riga tashi suka fita cikin jagorancin Inna, har dakin Auwal, sannan ta yo baya.... . Dan AuntyGORAN DUMA 17 . . "Na yi zaton kin manta da ni". Da kalmar da Auwal ya tare ta ke nan duk da ya ga hankalinta a hargitse, sai kallon sa ta ke kamar in ta dauke ido daga kansa zai 6ace mata ne, saboda haka har ta zauna ba ta cikin hayyacinta, ta dai sami kanta da amsa masa. "Dan na yi maka wanne laifi kake ganin zan manta da kai Auwal?" Dole ya basar da zancen kasancewar da Hafsat a wajen ba ya son su dire zancen da matsalarsu zata bayyana kanta. "Hafsat yau ku ne a gidanmu?" Abin da ya ce ke nan, Hafsat ta nisa idonta a kan Rumasa'u ta ce. "Ai dole ce mai sa wa a kwana a ido Auwal, kamar Rumaisa'u ta san ba ka da lafiya kwana biyun nan in na ce maka ba ta cikin hayyacinta kar ka musa". Ya yi zuru yana kallon Rumasa'u da idanuwansa masu aika mata wasu sa'konni masu dad'i da marasa dad'i, da ta kasa jurewa kallon sai kawai ta yi kasa da ido 'kwallah ta cika ido taf! Ya ri'ke kai saboda taruwar hawaye, take ya ji ciwon kansa ya dawo sabo dal, ya fara kokawar ri'ko juriya tana silalewa har ya yi nasarar dam'karta, cikin son nuna jarumta ya ce. "Yi ha'kuri Rumasa'u...." Ta tare shi a raunane. "Ya ya jikin?" Jikinsa a sanyaye ya amsa. "Na ji sau'ki ai... sai godiyar Ubangiji, kin san rai da jini". Ta kada kai tare da nisawa dukkanin hankalinta na kansa. "Anya Auwal ba damuwa ka sa wa ranka ba har ta janyo maka ciwon kai? Inna ta tabbatar min ba ka ta6a ciwon kai kamar haka ba, ka ga kuwa yadda ka rame Auwal?" Ya koma kujera ya yi rigingine ya dafe kai da hannun hagu sannan ya dafe 'kirjinsa da hannun dama saboda yadda ya ji shi ma ya dauki ciwon nan take fuskarsa na 'kokarin 6oye ciwonsa ya ce mata. "Sai da dalili Ubangiji zai jarrabi abin halitta Rumasa'u? Ki taya ni mu yi fatan zama kaffara kawai dole ya yi 'kokarin tashi zaune ya dubeta murya a sanyaye ya ce. "Rumasa'u idan ba ki dalafiya haka nake sanya ki gaba mu yi ta kuka, ko ciwona ne ya fi na kowa?" Ta yi saurin girgiza kai. "Ina jin abubuwa da yawa marasa dad'i a raina Auwal duk suna nuna min yadda ba zasu iya jure rashinka ba". Ya yi mata inkiya da Hafsat a wajen abin da ya fahimta matsalarsu ce a maganarta, saboda haka ya goce ta da cewa.. "Da ciwo ya san in da rai ya ke Rumasa'u ai da tuni kin tsufa a can, rayuwa da mutuwa duk Allah ne, kuma da yawan abubuwa na faruwa ne ba yadda mutum ya zace su ba, ni yanzu so nake ki kwantar da hankalinki mu yi hirarmu mu fanshe kwana biyun da muka rasa, kinga sai ta zame mana ta tarihi ko? Ina jin tunda muka had'u ba mu ta6a kwana uku ba mu ga juna ba". Ya 'kare maganarsa ne da dariya sai Hafsat ce ta taya shi, ta kalli Rumaisa'u taga fuskata a cunkushe. Tunanin halin da take ciki na rashin lafiyarsa da 'kila wa 'kalan aurensu, ba ta ga wani abu da zai ba ta dariya ba. Fahimtar hakan da Auwal ya yi yasa ya dinga daurewa yana ta tsaokano ta da hira, har saida ya ga abin ya faskara sannan ya dubi Hafsat ya ce. "Hafsat don Allah ki ba mu minti biyar akwai wata wuta d ana hura nake son kashe ta". Hafsat ta mi'ke tana dariya ta ce. "Ni ma na yi niyyar hakan cikin raina, ina da bukatar Rumasa'u ta sami nutsuwa." Ta wuce Auwal bin ta ya yi da cewa. "Yauwa Gimbiyar Sani, Allah Ya barku tare". Hafsat na fita ya baro kujerar da yake ya zo gabanta ya zauna cikin raunin murya ya ce. "Fad'a min abin da ya fi damunki yanzu na wanke miki shi Rumasa'u, idan dai ciwona ne aikin ga na ji sauki ko?" Ta goge hawayenta sannan ta sauko daga kujerar duk suka zauna a kafet suna fuskantar juna, tana ta faman goge hawaye, sannan da kyar ta 'ko'karta ta ce. Me yasa ka kashe wayarka?" Ya 'kura mata ido kawai ya kasa cewa komai har ta kuma dorawa ba tare da ta dube shi ba. "Ya ya kuka yi da Abba?" Kai tsaye cikin dakewa ya amsa mata. "Wannan rashin lafiyar tawa ta sa ba mu zauna mun tattauna ba, amma dai na nuna masa sakamakon gwajin". "Me ka fahimta a tare da shi?" Kai tsaye ya amsa mata "Fuskarsa ba zata iya bayyyana abin d ke fake ba, duk yada zai nuna 'karfi ko hangen nesansa ba zai sauya ba ko ya yi abin da Ubangiji bai nufa ba, zai sauya ba ko ya yi abin da Ubangiji bai nufa ba, na ba shi sakamako na kuma fad'a masaain da ke raina, ke ce farin cikina dan kin haifi 'ya'ya irinki na shirya zan tanada su a ha'kuiri na da juriyata da kuma yin tattalin aljihu iyakar iyawata ina da wannan burin a raina, na niyyace shi duk wani abu sa6anin haka idan haka idan ya faru haka Ubangiji Ya 'kaddara mana, ke ma ki yi min uzirinsa". Rumaisa'u ta yi sakato tana kallonsa, saboda har yanzu ba ta tsinci abin da ya kamata ya faranta mata rai cikin maganarsa ba, idan al'kawuran sonta d akyautata mata ita da 'ya'yanta ne tun ta saba jinsu a bakinsa, tana kuma da ya'kinin daga zuciyarsa suke tasowa saboda haka yanzu abin da ya dame ta shi ne ya ya za su yi su kai ga cimma burin kasancewa tare bare har ta jefa wad'ancan al'kawaran nasa cikin abubuwan da ta ke jiran kasancewarsu a rayuwa? "Zan tafi". Abin da ta iya ce masa ke nan cikin hawaye. Ya d'an runtse ido cikin girgiza kai ya ce. "Yanzu sai ki tafi ki bar ni Rumaisa?" Ta mi'ke tana ci gaba da goge hawayenta ta ce. "Wata'kila gobe in dawo idan ba ka murmure ba, sai dai ka ba wa Inna ha'kuri wata 'kila ta ga rashin kunya ta da za'kewa ta, ni ma haka na tsinci kaina, in dai abu ba haramun ba ne, don sakaf nake ganinsa a fuskarka". Shi ma ya mi'ke yana dariya ya ce. "Inna za ta fahimce ki Rumaisa, kin ta6a zuwa gidanta ban da yau? In Allah Ya so ma goben ni zan zo ba ke za ki zo ba, ai idanuna sun ganki sun yi kwari". Ita ma ta yi dariya ta yi ajiyar zuciya. "Hum...!" Alamar har yanzu ba ta ware ba, suka jima suna kallon juna, sannan ta kad'a kai cikin hawaye ta wuce, jirin da yake ji ya hana shi yi mata ko taku daya da sunan rakiya, daga nan tsayen har ta je bakin 'kofa sannan da murya 'kasa-'kasa ya ce. "Rumaisa'u... Ina sonki, kar ki manta da wannan". Ta tsaya tare da juyowa suka yiwa juna murmushi, sannan ta fice, shi kuma ya haye kujera a gajiye yana lumshe ido, yana son Rumaisa'u tana sonsa, har yau bai ta6a yanke 'kaunar za su gaza kai wa ga burinsu ba. Ta sami Hafsat da Inna suna ta hira ko a fuska babu wanda ya nuna mata wani abu. Ta zauna a sanyaye cikin hawaye, wannan ya sa kowa ya yi dif a dakin tsawon kusan mintuna biyu, sai can Hafsat tayi ajiyar zuciya ta nisa ta ce. "Inna ashe tun tuni Auwal bai sanar da ku cewa Rumaisa'u sickler ba ce ko? Tuni kuma ta shawarce shi ya sanar da ku, amma bai yi hakan ba har sai da kuka ji a gari. Tabbas ba mu kyauta har da ni, amma don Allah Inna ku yi mana uziri, sun fiye son kansu ne shi yasa su ke juyawa matsaloli fuska... Auwal da Rumaisa'u sun fara son juna da radin kansu amma yanzu ga shi sun ya gaza rabuwa. Inna don Allah ki fahimtar da Abba kar ya raba su.. Zaku iya neman wata mafitar ta samarwa Auwal wasu 'ya'ya ba nata ba... Na tabbata za su iya lamuntar haka, raba sun ne kawai muke jinsa wani abu da na ha'ki'kance numfashinsu ya gaza dauka..." . . Dan Aunty.GORAN DUMA 18 . . Rumaisa ta yi sororo hawaye na kwarara daga idanunta. Wadannan kalamai ne a bunne cikin ruhinta, amma baki ya gaza furta su. Inna ta dubi Rumaisa'u da ke shesshekar kuka. Inna ta yi dif damuwar duniyar nan ta bayyana a fuskarsta, duk da tuni ta san da sha'kuwa a tsakaninsu raba su abu ne mai wahala wanda ko ita ba ta mafarkin haka duk da dangar da ta ke hangowa iyalansu a gaba, a yau sun ba ta tausayi su duka har ta fara jin sallamawa cikin ranta. Cikin 'karfin gwiwarta ta ce. "Ku manta wannan maganar, iyakacin Abba fad'ar da kuma nuna yun'kurin da zai iya ba dan nuna 'kiyayya ba, sai don gujewa wahalhalu a gaba. Amma komai ai sai Allah Ya kasantar 'yar nan, ko shi kansa na san yana shakkar ta inda zai kwaso ya hana ko ku aure, auren da ya rage kwanan wata guda da 'yan lamarinmu ga Allah, Allah Ya tabbatar mana da alkhairansa kin ji? Ni ban so ma ya sanar da ke ba wallahi". Yanzu hankalin Rumaisa'u ya kwanta ta kuma sami nutsuwa a cikin ranta, har ta saki wani raunannan murmushi. Suka yi shiru ba wanda ya iya furta wani. A 'karshe sai sallama suka yi da Inna suka nufi gida. Mahaifin Auwal na tare da Innar Auwal bayan dawowarsa da dare yana cin abinci ya ce mata. "Ya ya jikin danki?" Ta yi dariya ta ce. "Wai yaya jikin danki, to ya sami sauki har ya je masallaci sallar isha'i". Ya ce, "Ko kuma ya tafi zance ba". Ta yi saurin girgiza kai. "Ba na tsammanin hakan,dan juria kawai na hanga a idonsa, ciwon kan nan yana matsaya masa, ka je wajen likitan da ka ce zaka je neman 'karin bayani a kan auren nasa?" Cikin fuskar jimami ya ce. "Na je, labarin babu dad'i Asma'u. Likita ya tabbatar min mafi rinjiyaen 'ya'yan da zasu iya haifa da kashei 70% za su zamo sikila ne, sai dai wani hukuncin Ubangiji. Amma duk da haka dan sabar son kai ya ke shawartata kar a hana su aure. Yanzu tsakani da Allah hana su aure ba jihadi ba ne? Su a wahale 'ya'yan da za su haifa a wahale? Mene ne aibun dan ya auri mai lafiya ita ma ta nemo wand aba zasu haifi 'ya'ya masu cuta ba?" Inna ta sauke numfashi cikin alhini ta ce. "Ka bar su kawai Alhaji, yaran nan sun fara ba ni tausayi, ai dazu ta zo duba shi, in ka ga yanayinta sai ka tausaya mata, na tabbatar yadda ya damu da ita haka ta damu da shi. Nan gurin ta zaune min tana neman in ro'ka ka kar ka raba su, har tana bayar da 'kofar yana iya auren wata da zata haifar masa lafiyayyun 'ya'ya... Yarinyar ta ba ni tausayi wallahi sannan ina tsoron makomar da za su fad'a idan aka raba su, dan ni ina shakar babu taimakon wannan jumurd'ar cikin tsanantar ciwon kansa, ka san yawan tunani cikin damuwa babu abin da ba ya haifarwa". Abban ya jima cikin jan numfashi, sannan ya hadiye abin da ya tara, ya cigaba da cin abincinsa, har ya kammala can ya ji motsin shigowar Auwal, saboda haka ya kira shi a waya. Ya shigo idonsa zuru-zuru saboda rama, a yanzu haka ma da 'kyar yake sauke numfashi saboda azabar ciwon kai. Ya nemi guri ya zauna cikin sanyin murya ya gaishe su. Mahaifin nasa ya zura masa ido tsawon wani lokaci yana kallonsa cikin tausayawa a zuci, sannan ya yi gyran murya ya ce. "Auwal tuni na yi maka shaidar tawakkali, me yake son sauya ka har ka dami kanka cikin abin da ban isa in sa ba bare in hana?" Auwal ya yi masa shiru yana masa kallon rashin fahimta, saboda haka mahaifin nasa ya dora. "Fadata fadar Allah ce dan na kawo ra'ayina akan aurenka zaka dinga neman kashe kanka Auwal?" A sanyaye ya ce masa. "Me na yi Abba?" Abban ya nuna Innar Auwal din ya ce. "Ga ta nan, yanzu nan ta gama zargin shigata lamarin aurenka ke jaza maka ciwon kai. Ni ma na gaskgatata, ai duk yadda kake ciwon kai ba ka ta6a fita hayyacinka irin haka ba". Auwal ya 'kokarta ya yi murmushi, ya ce. "Wallahi ba haka ba ne Abba, hankalina a kwance yake da ina da ya'kinin in dai ni mijin Rumaisa'u ne, babu abin da zai hana ni aurenta, ko ina da damuwa ba zata wuce na tausayinta saboda rauninta na mace da kuma lalurarta ba, wanda wannan zai raunana zuciyarta ya iya yi mata illa. Ina kuma cike da tausayinta idan ban zamo mijinta ba yadda na ga ana gudun aurenta, ina tsoron mata auren wanda zai kasa kyautata mata da kyautata rayuwarta... Gaba daya damuwata akan yadda Rumaisa'u zata samu rayuwarta ne.... Na san kuma wannan bai isa dalilin jaza min lalurar da Allah bai gadar min ba, saboda haka ku kyautata zato a gare ni, ku cika ni da addu'arku ta fatan alkhairi, har kullum ina alfahari da kasancewar iyayena. Ni addu'arku kawai nake bu'kata da cire zarge-zarge a cikin jarrabawar da Ubangijina ke min". Su duka jikinsu ya yi sanyi, kaunar Auwal ta 'kara mamaye zu'katansu, Auwal dan halak ne wanda akwai wahala ka ji sharri ya fito bakinsa, duk yadda kake jin abu mummuna ne in ya gifta shi ba zaka ji raknsa ba, kuma ba zai sauya masa manufa ta son zuciya ba, mutum ne shi mai jarumtar mayar da lamari ga Ubangiji. "Allah Ya yi maka albarka, Ya rabaka da duniya lafiya ka ki". Innarsa ta riga mahaifinsa magana, tana direwa shi ma mahaifin nasa ya dora da cewa. "Allah Ya kyautata rayuwarka duniya da lahira Auwal, Ya rabaka da 'kuncin duniya da lahira, Ya 'kara fadada 'kirjinka da halayen kwarai, da son Allah da ManzonSa. Ta shi ka je, Allah Ya ba ka lafiya Ya hore maka dukkan alkhairan da kake ha'ko". Ya dan dakata yana musu godiya, sannan ya tashi ya fita cike da dokin kiran Rumasa'u a waya ya ba ta albishir, dan ma kansa na mats amasa da ciwo saboda haka ya fara shan magani, sannan ya kishingid'a na wasu mintuna wai ko kan nasa zai dan sassauta ciwo, amma da hakan ba ta samu ba, sai ya kira wayarta a haka, sai dai kash! Wayarta a kashe ta ke, amma da yake ya 'kagu da jin muryarta haka ya yi ta gwadawa har bai san adadi ba. *** Washegari da hantsi 'karfe goma da minti hamsin Rumaisa'u da Hafsat da Hajiya suna tare a falonta suna hira, Rumasa'u dai ta kasa hankalinta fiye da dari ma idan ana kasawa, a hirarsu a tunanin lafiyar Auwal, aurensu, 'ya'yansu, da kuma wayarta da duk bayan minti biyar sai ta kira wayar Auwal din, ta yi ta faman rurinta bai daga ba. Tun asuba ta ke nemansa a waya bayan ta kunna wayarta ta tarar da 6oice mail na ya kirata kusan ashirin, tun sannan ta ke gwada kiran wayarsa har kawo wannan lokacin da 'kila in ya zo zai tarar da 100 missed calls. Babu itin tunanin da ba ta yi ba, ya saka wayar a silent, ko kuma jikinsa ne ya matsa masa, sai dai wata zuciyar tata na kore wadannan hasashen da wasu hujjojin, su ne. Idan jikinsa ne ya matsa masa, ina wadanda ke tare da shi da ba za su daga wayarta ba? Da wadannan dalilai ta dogara ta kasa cira 'kafa dan nemo wani hasashen, kuma gabanta ya dinga 'kuntata zuciyarta. Haka ta ke zaune cikinsu tana yake da faman kiran wayar Auwal, har ma lokacin da Hajiya ta dubi agogo ta sauke numfashi ta ce. "Oh ni 'yan nan kawaici ne fa ya fara 'karewa, Alhaji tun fita sallar asuba bai shigo ba, Yayanku ma bai shigo cin abinci ba, Murabak kuma da shirme na tambaye shi ya tsaya min shirme, wai abokinsa ya bi suka fita". Rumasa'u da Hafsat suka yi saurin duban agogo, Hafsat ta riga magana da cewa. "Kin kira shi a waya kuma?" Hajiya ta ce, "Yo ai a gida ya bar wayoyin na fada miki tun sallar asuba". Cikin alhini Rumasa'u ta ce. "Wani lokacin wayar ma ai hoto, kun ga tun safe nake neman wayar Auwal tana shiga amma ba amsa..." . Jama'a ku bani shawara, Ina shirin shiga neman auren Ruma tunda naga da Auwal kamar da wuya kuma gashi jini na A.A ne, daman na jima da jin son ta har cikin xucia ta, gudun kada na raba kauna da Auwal ne na danne xuciar, amma yanxu abun ya xo min har wuya . Ko ya kuka gani? Lol. . Dan AuntyGORAN DUMA 19 . . Kafin ta rufe baki sai ga Alhaji ya yi sallama ya shigo fuskarsa na kokawar 6oye sa'konnin tashin hankali iri-iri, komai nasa a birkice ya ke, sai dai akwai alamun yana tilasta kansa gayyato nutsuwa. Duk suka yi masa barka da zuwa, Hajiya ta dora da tambayarsa cikin kulawa. "Alhaji lafiya kuwa?" Ya wuce zuwa ciki yana cewa. "Lafiya mana, me kika gani?" Ta bishi cikin sauri suka shige falonsa a tare. Ya nemi kujera ya zauna cikin dafe kai hannu biyu. Nan take jikin Hajiya ya dauki 6ari ita ma ta silale kujera ta zauna tana sakin numfashi cikin sauri ba ta katsi hanzarin shirinsa ba, saboda haka ta raka shi suka yi tare". Tsawon wasu mintuna, sannan ya mi'ke ya je ya murzawa 'kofa mukulli sannan ya dawo cikin kasala, ya zauna ya dubi Hajiya ya ce. "Allah ne Ya yiwa yaron nan Auwalu rasuwa!" Tsawon wasu mintuna, sannan ya mi'ke ya je ya murzawa 'kofa mukulli sannan ya dawo cikin kasala, ya zauna ya dubi Hajiya ya ce. "Allah ne Ya yiwa yaron nan Auwalu rasuwa!". Hajiya ta dauke numfashi tana dubansa. "Alhaji wanne Auwalun?" Ya amsa mata yana kallonta. "Auwalun Rumaisa'u". Sai ga Hajiya a tsaye cikin wani matsanancin firgici, sai dai ta had'a shi da fadin. "Innalilahi wa'inna ilaihi raji'un, Alhaji hatsari ya yi, dama ba shi da lafiya?" Alhaji ya yi zuru yana kallonta tsawon fiye da minti daya, ita kuma tana ta faman kai wa da komowa tana ambaton innalilli wa inna ilaihi raji'un har sai da ya fahimci ta kai adadjin da ya kamata ta nemi wani abin, sannan ya tare ta. "Zauna mana, wannan muryar da kike son ki daga mana zata 6allo mana ruwa". Ta koma ta zauna amma kuka mai keta zuciya ya bijiro mata, sai dai ta hana shi fitowa ya sake. "Alhaji ba shi da lafiya ne?" A sanyaye Alhaji Ya amsa mata. "Wai Hajiya sai mutum ya yi cuta Allah ke kar6ar ransa? Ji nake lokacin mutum na cika yake komawa ga Ubangijinsa? Irin wannan tambayoyin ba su da wani hurumi tunda ba za su ta6a dawo da wanda ya tafi ba tare da cuta ba". Hajiya ta ci gaba da kuka cikin jero kalmomin yabo tare da kururuta halayen Auwal na kwarai, tana had'awa da nemo masa rahamar ubanhiji. Tsawon wani lokaci Alhaji ya yi dif cikin tsabar alhini, har sai da ya sami ga6ar abin cewa da ta fara sambatun halin da Rumasa'u zata shiga. Alhaji ya sauke numfashi ya ce. "A halin yanz abin da ya fi zafafa zuciyata ke nan, ko bayan dawowarmu ma'kabarta duk san da mahaifinsa ya dube ni cikin kuka ya ke maimaita min. Rumaisa'u ta yi rashin masoyi... duk wanda zai yi kukan rashinsa bayanta zai bi... maganata ta 'karshe da shi a kanta ne, inda yake ce min...idan ina tare da damuwa ba zata wuce na tausayinta saboda rauninta na mace, da kuma lalurarta ba. Wanda wannan zai iya raunana zuciyarta ya iyayi mata illa, ina kuma cike da tausayinta idan ban zamo mijinta ba yadda na ga ana gudun aurenta... Ina tsoron mata auren wanda zai kasa kyautata mata ya kyautatawa rayuwarta... Gaba dayan damuwata akan yadda Rumasa'u zata sami rayuwarta ne..." Hajiya ta 'kara fashewa da kuka ta ce. "Yanzu zancen da nake maka tun safe ta ke neman wayarsa, in ka ga yadda hankalinta yake tashe sai ka rantse ta sami labarin rasuwar tasa ne..." Innalillahi wa inna ilaihi raji'un". Alhaji ya fad'a cikin dafe kai, sannan ya dago ya dubi Hajiya ya ce. "Yanzu yaya za mu yi?" Hajiya ta ware hannu cikin kuka. "Ban sani ba Alhaji". Falon ya 'kara daukar shiru, ya mi'ke ya shige wanka, har ya fito Hajiya na zaune gurin tana faman sharar hawaye, shi kansa ya rasa da kalmar da zai ce ta yi hakuri har ya kintsa ya zo ya kuma zauna wa. Falon ya 'kara daukar shiru, ya mi'ke ya shige wanka, har ya fito Hajiya na zaune gurin tana faman sharar hawaye, shi kana ya rsa da kalmar da zai ce ta yi hakuri har ya kintsa ya zo ya kuma zauna. "Ki bar kukan nan haka, mu taru mu samo wa yarinyar nan mafita, ta ina za a shero mata wannan mummunan labarin? Ina tsoron shide mana wallahi, ga ta dama ba mai isasshiyar lafiya ba". Hajiya ta dago ta dube shi idanunta jawur ta ce. "Mu 6oye zuwa gobe, ko jibi kafin sannan mun samo abin cewa". Alhaji ya yi kasa'ke, sannan ya ce. "A yi waya a sanar wa mahaifinta, inda hali su zo nan mu taru mu san ta inda za mu 6ullo mata". Hajiya ta yi saurin gyada kai cikin amincewa. Hafsat da Hajiya sun wuni suna kuka a 6oye, yayin da Rumaisa'u ta wuni cikin muguwar kasala da hasashe iri-iri akan Auwal, wanda wayar da ta ke masa ma ta daina shiga, ma'ana an kasheta ko da kashe kanta. Ko kwayar abinci ba ta kai bakinta ba, hana rantsuwa ta wuni tana makar ruwa sai rake ga6a hhudu da ta sha. Su kansu saboda lalurarta ta damu da shan su bisa dole. Bayan sallar la'asar dai hakurinta ya 'kare, tana sanye da hijabin da ta yi sallar ta za'kulo Hafsat a can dakin baccinsu tana kudundune akan sallaya ta soke kai cikin 'kafafu. Rumasa'u ta zauna bakin gado tana ce mata. "Hafsat yau ma fa sai kin agaza min kin raka ni duba Auwalu. Na rantse yau idan na kwanta ban san halin da yake ciki ba, sai zuciyata ta buga". Wani malalacin kuka ya bijirowa Hafsat, amma ta yi jarumtar danne shi a ma'koshi, ba tare da ta dago ba ta ce. "Ni ma ba ni da lafiya Rumasa'u". Cikin jimami Rumasa'u ta ce. "Ayya! Sannu, me ke damunki?" Hafsat ta hada da sautin kukan da ke yun'kurin fitowa ta ambata. "Zazzabi..." Rumasa'u ta yi saurin mikewa tana cewa. "Kuma sai ki zauna ki ta kuka Hafsat, bari na kawo miki magani ki sha sai ki kwanta ki huta, ni zan ira Mubarak ya dawo mu je mu dubo Auwal, jikina yana ba ni Auwal yana cikin wani hali wallahi". Wannan maganar tata ta sa Hafsat 'kara kecewa da kuka. Ta fita ta dawo mata da ruwa da panadol ta bata ta sha, tana kuma mata sannu, Hafsat ta kwanta ita kuma ta zauna bakin gado tana faman kiran wayar Auwal cikin tsananin damuwa. Rashin samun nasa ya sa ta shiga hasashen wanda zata kira ta ji halin da Auwal ke ciki. Da yake ya bata lambar wayar Innarsa, kai tsaye ta kira amma ita ma a kashe. . Allah sarki, hasashe dai sun nuna Ruma ta dan Aunty ne . . Dan Aunty.GORAN DUMA 20 . . Rashin samun nasa yasa ta shiga hasashen wanda zata kira taji halin da yake ciki, da yake ya bata lambar wayar innar sa kai tsaye ta kira, amma ita ma a kashe, a karshe sai ta kira abokinsa Sulaiman cike da karsashi, '' sulaiman yaya gida, ya iyalin??? Abinda tace masa kenan lokacin da ya daga wayar da sallamarsa, murya kuma a dashe , a rude ya amsa mata lapia Ruma, yaya jikinki ? Cikin sauri ta amsa Alhamdulillahi sulaiman, don Allah idan baka da zazzapan azuri ka leka ka dubo min Awwal, tun sape nake kiran wayar sa a kashe, jiya mun rabu bashi da lapia duk hankalina a tashe ya kasa kwancia, ka jeka dubo min shi don Allah, mubarak nake jira ya dawo ya raka ni na dubo shi. Sulaiman ya dinga jan numpashi cikin matsanan cin jin tausayin Rumaisau sai ya da dauke kwalla a idon sa sannan ya kwaso in'ina yi mata karya '' lah bana gari Rumaisau, ina kaduna a halin yanzu.... Cikin tsananin damuwa tace Hasbunallahu wa ni'imal wakil.. To Allah Ya dawo dakai lapia, ina ganin kawai zan tapi ni kadai. Yayi saurin tare ta da padin, a'a ki zauna bari na yiwa wani makocinsu waya. Bai jira cewrta ba ya kashe wayar, ta tashi ta koma palo tana paman jiran kisan sa shiru har piye da mintuna ashirin, da ta kuma binsa sai ta tarar ya kashe wayarsa , kawai sai ta mike ta nupi kicin inda hajia ke tsaye cikin shirin pita sanye da hijabi tana kuka da mai aikinta Talatu tana goge kular da aka shakare da abinci. Rumaisau ta jingina jikin durowa saboda kasala a raunance tace hajia na raka ki gidan gaisuwar mana, sai mu biya mu duba Auwal, ina tsammanin jikin sa ne yayi zaapi shi yasa bai bi ta kan wayar sa ba. Hajia tayi dira-dira sannan ta samo abin padi cikin in'ina sai dai ban sanarwa Alh ba, kila yayi pada, jiya ma da na sanar masa zuwanku sai da yayi ... Kiyi hkuri zuwa dare in bai kira ba sai in tura Mubatak ko yayanku, rumaisau ta jima tsaye ba tare da ta tanka ba kawai sai ta juya a hankali ta pice daga kicin din, hajia da Talatu suka kawar da kai daga kallon ta suna dauke kwalla, har kwana biyu ana paman kwana-kwana da ita, saboda tsabar damuwa itama sai da ta kai ga.... . Kuyi hakuri da jina shiru jiya en wasu uzuri ne suka rike ni, yanzu ma rubutun ba yawa , . Dan Aunty na Ruma.. August 10 at 8:25 PM · PublicGORON DUMA (P 20**2) . . Har kwana biyu ana faman kwana kwana da ita, saboda tsabar damuwa ita ma sai da ta kai ga kwanciya. Akwana na biyu da rasuwar, Innarta da babanta suka zo gaisuwa, mahaifinta ya koma ya bar Innarta da aka fake mata da cewa zata zauna ne saboda 'yan shirye-shirye. Akwana uku da rasuwar tana kwance cikin zazzafan zazza6i, Innarta da Hajiya da Hafsat da Mubarak duk suna zaune ana 'yar hira. Can hajiya ta ce. "Hafsat debo magungunan Rumaisa'u ki ba taa". Sai da Hafsat ta zo da maganin sannan Rumasa'u ta daga kai ta kalle su cikin kwalla ta ce. "Hajiya wai me yasa kuke son ku damu da yi min abin da ba zai amfane ni ba? Na yi kawaici amma kamar ba ku san ina yi ba, amma da kuka ganni a gefen kabari me yasa ba za a gayyato min Auwal mu yi sallama ba?...... Na ga idan an yi hakan kamar za a sami lada, ba a bar ni na mutu da zafi da radad'in son ganinsa ba". Cikin daraba Hafsat ta silale ta bar falon gudun kecewa da kuka a gaban Rumaisa'u. Hajiya da Innarta an sara mai amsa mata, sai Mubarak ne ya 'ko'karta ya ce. "Mutuwa ai lokaci ne Anti, an fada miki Auwla yana kwance asibiti, amma ana rad'e-rad'in yau za a sallamo shi, idan Allah Ya kaimu gobe ba sai mu je ki duba shi ba". Ta yi zuru tana kallon Mubarak, sannan ta amsa. "Wato da na ce ka je ka dubo shi ba ka je ba kake min maganar rade-radi?" Ya yi saurin cafewa da fadin. "A can fa na ji". Sai ta kawar da kai ba ta ce ce komai ba. TA FARU TA 'KARE! Sai da Auwal ya sami kwana biyar da rasuwa Rumaisa'u ta sani, ta hanyar wata 'kawarta. Tun safiyar ranar ta tilastawa 'karfin zuciya da na jiki domin ta samu ko sulalewa ne ta yi zuwa dubo Auwal, saboda haka ta wuni babu kwanciya. Da yamma bayan sallar la'asar ta yi shirin fita, tana tsaye falo gaban madubi ta ji 'karar shigowar sa'ko a wayarta. Da sauri ta ciro wayar cike da doki da fatan Allah ya sa Auwal ne. Ta fada a sarari sai dai kash! Sai ta tarar da shaidar da ke tabbatar mata da Auwal ya bar dniyar turo sa'ko. Ga abin da ta tarar: Salam Lallai duk wani mai rai matafiyi ne, wanda ba shi da garanti na lokacin da tsawon tafiyarsa zai 'kare, bukatarsa kawai tanadin guzuri mai kyau domin samun masauki mai kyau lokacin da ya cimma zangi. Ina tayaki alhinin rashin Auwal, Rumaisa'u Ubangiji ya haskka kabarinsa ya sanya mutuwarsa hutu ce mu kuma in tamu ta zo ta riske mu da imani. Nan take numfashinta ya nemi daukewa zuciyarta ta fara bugawa da 'karfi, kuma nan take hankali da zancinta suka tsaida aiki. Saboda haka ganin kanta ta yi kawai a falon Hajiya, wadda ke tare da Innarta da Yusha'u. Cikin muryar rashin hayyaci ta ke nuna su da wayar. "Umma, Hajiya yanzu kun san cewa babu Auwal a doron duniyar nan kuka bar ni nake 6ata lokacina a cikinta.... Kaico! Ban ga wani da ya ta6a zabga asara irin tawa ba, na rantse da Sarkin da Ya yi ni..." Hajiya da Umma suka taso a lokaci daya suka nufota, amma kafin su 'karaso tuni aikin gama ya gama, dan nan take ta sulale 'kasa ta fad'a kan girkakken teburin gilas din da ke tsakiyar falon, ta datse goshi nan take jini ya fara gudu a wajen, ita kuma tuni ta suma. *** *** *** Ba Hajiya da Umma wadanda dama Rumasa'u ke kwance a zuciyarsu ba, hatta Yusha'u da yake hangenta sama- sama sai da ya shiga matsanancin tashin hankali da abin da ya faru da ita kamar kiftawar ido, shi da ya ke zaune sai ga shi ya riga su isa gare ta ya dago ta yana ambaton. "Innalillahi wa inna ilaihiri raji'un". Hajiya da Umma duk suka gigice, sun ma rasa kalmar da za su fada duk wadda suka kamo sai ta guntule, Yusha'u kuma kawai sai ya sureta ya yi waje da ita, Hajiya babu ko mayafi ta bi shi cikin salati, Umma kuma sai ta shiga cikin hankalinta inda ta yi sauri ta kira mijinta ta ce. "Daddy Ruma don Allah ko me kake yanzu ka sake shi ka biyo jirgin 'karfe biyar ka taho Kano,Ruma ta gamu da wani had'ari na tabbatar za a nemi jinin 'kara mata, ka zo ka ba ta jini". "Subhan Allahi, garin ya ya?" Sai a sannan ta fara shesshekar kuka, ta amsa masa. "Ta sami labarin rasuwar nan a waya, shi ne ta fada kan gilasgi... Ba ta iya 'karasawa ba ta kece da kuka mai buga zuciya. Ta bazama waje jikinta na rawa, tana zuwa motar Yusha'u na ficewa daga harabar gidan. Sai a ka barta da Talatu da Hafsat suka koma cikin gida suna faman kuka, musamman da Hafsat din cikin kuka ta labarta musu hirarsu ta 'karshe ranar da su ka je gidansu duba shi inda ya ce mata. "Rumaisa'u idan baki da lafiya haka nake sa ki gaba nayi ta kuka? Ko ciwona ne ya fi na kowa?" Ita kuma ta amsa da cewa. "Ina jin abubuwa masu yawa marasa dadi a raina Auwal. Duk suna kwatanta min yadda ba zan iya jure rashin ka ba". Shi ma ya kuma amsawa da cewa...... Ya kamata ace yanzu kuna commnts da likes, masuyi muna godia, wanda basayi nake magana, bawai babu masu karantawa bane, idan mutun bazai iya commnts ba ko da like yayi mana, mutuwar gidan nake dubawa, ada da bamu kai haka yawa ba ana samun commtns kusa da 100 zuwa saman sa yanzu kuma pa? Idan da za'a na commnts da like rubutun ma zan kara shi saboda a samu a gama shi da wuri, amma ina bata sama da awa daya zuwa biyu ina typing dan kawai commnt din da bazai wuce minti daya ba sai ya gagara? Idan kun lura a parkon littapin napi yin sa da yawa amma rashin commnts din ku ya kashe min gwuiwa na rage hanu dan nima nake hutawa. . Dan Aunty. GORAN DUMA (P 21) . . "Da ciwo ya san ind arai yake Rumasa'u da tuni kin dade a can, rayuwa da mutuwa duk na Allah ne, kuma da yawan abubuwa na faruwa ne ba yadda mutum ya zace su ba. Ni yanzu so nake ki kwantar da hankalinki mu yi hirarmu mu fashe ta kwana biyun d amuka rasa, kinga sai ta zame mana ta tarihi ko? Ina jin tunda muka hadu bamu ta6a kwanaki uku ba mu ga juna ba". Haka dai suka yi ta tuntuni suna ba wa kansu yajin da ke saka su kuka, Innar Rumasa'u daga 'karshe ma sai ta fara furta kalaman da ke nuna ta cire rai da gudan jinin tata. Sai da awa daya ta haura sannan Yusha'u ya kirasu a waya ya sanar da su suna asibirin Narassarawa, sannan suka shirya suka rungud'a suka tafi asibitin. Rumaisa'u dai tana cikin wani mawuyacin halin da ko ma'kiyinta ya ganta sai ya tausaya mata kuma lalura ta 'karu a kan ta da, wato buguwar da ta yi a ka ya sabbaba mata katsewar wayoyin turo sa'konni daga kwakwalwa zuwa wani sashe a fuskarta inda suka daina aiki sam! Ga kuma bukatar jini a jikinta, saboda haka kafin ma mahaifinta ya zo wanda rukunin jininta ne, yawancin lokuta ma idan bu'katar 'karin jini ta taso mata shi yake ba ta. A wannan karon kafin ya 'karaso har Yusha'u ya bata leda daya. Wannan dangi dai haka suka kwana cikin tashin hankali, suka tashi da shi yayin da mahaifan Auwal suka zo asibitin ake yi da su. Mahaifin Auwal ya fi kowa shan kuka dan yana ji a ransa kamar shi ya yi sanadiyyar rasuwar Auwal wanda Allah Ya nuna masa ishara, ya dauke shi mai 'koshin lafiyar da ya ke tun'kaho da shi, ya bar Rumasa'u da yake kallon gawa-ta'ki-rami, duk da ita ma gata nan rai 'kwa'kwai, mutu 'kwa'kwai. Shi yasa duk lokacin da ya yi arba da ita sai kuka ya su6uce masa, ya kuma dinga ba ta hakuri tare da addu'ar Allah ya tashi kafadunta duk da ba ta san yana yi ba. Haka ma Innar Auwal wadda kusan son da ta ke wa Auwal ya dawo kan Rumasa'u, musamman idan ta tuno da ro'kon da Hafsat tayi mata lokacin da suka je har gidan. "Auwal da Rumaisa'u sun fara son juna da rad'in kansu amma yanzu ga shi sun gaza rabuwa . Inna don Allah ki fahimtar da Abba kar ya raba su... Za ku iya neman wata mafitar ta samarwa Auwal wasu 'ya'ya ba nata ba... Na tabbata za su iya lamuntar haka, raba sun ce kawai muke jinsa wani abu da na ha'ki'kance numfashinsu ya gaza dauka..." Ashe dukkan su da gaske suke, Auwal ya bar duniyar Rumaisa'u ta nad'e k'afar wando zata bi shi. . BAYAN SATI UKU Allah mai yalwata zu'katan bayi da farin ciki ra raba su da 'kuncin zuciya, Shi ya kyautata zuciyar Rumaisa'i, bayan farfadowarta ba ta da aiki da ya fice kuka da kiran mutuwa, kuka kuwa mai 'kona zuciya da kusan hadiye ta, duniyar da duk alatun da ke cikinta suka zame mata wani ba'kin duhu mai cike da rashin aminci, duk mutumin da ta kalla sai ta dinga yi masa kallon wanda bai san komai ba a ba'kin cikin duniya kuma bai rasa komai ba a cikin arzi'kin duniya, sa6anin ita da ta zama wata ganga babu rufi. Lokacin da ta fahimci 6arin fuskarta ba ya aiki ko daya abin bai d'ad'ata da 'kasa ba, kusan ma shi ne abin da a halin yanzu ke faranta mata rai, dan shi yake nuna mata sauran 6angarori a jikin nata ma suna dab da tafiya su bar wannan duniyar maimduhun tsiya, duniyar da duk babu Auwal to labudda ita hoto ce a wajenta. Amma da yake ba ita ke tasifirin kanta ba, sati biyu ba ta rufe ba sai da kaso hamsin cikin dari na zafin zuciyarta da ta ke ji ya ragu, sai burbudin kashi hamsin na kewa da tausayin kai saboda yanke 'kaunar ta yi asarar da ba zata ta6a mayar da ita ba, wannan ya sa ko daya ba ta damu da yadda tafiya ta yi mata 'karanci ba, ta ke ganin ma kamar ba ta 'kawar da ta fice cutar tunda ita ke kusantar da ita ga 'kaura a duniyar. Sati uku, hud'u, sau'ki ya fara samuwa a 6angaren fuskar tata da ya dauki hutu, ta fara motsawa kad'an-kad'an bayan likitoci sun tabbatar da ba ta cikin wani had'ari a lafiyar jikinta da ta wadatar jini a jikinta, sai suka sallameta da tarin sharud'ai na kwantar da hankali da 'karanta tunani domin kwakwalwa ta samu hutu ta mayar da abin da ta rasa. Komawarsu gida ne ma ya famo mata ciwo, dan akwai abubuwa da yawa a gidan da ke tuna mata Auwal wajen Innarsu a haraba inda yake ajiye mota, a falo inda suke hira, wayoyin hannunta guda biyu wadanda duk shi ya sai mata su, turarenta da kuma da yawa a cikin kayan kwalliyarta da tufafin sawarta, kai ko magani ta zo sha sai ta tuno shi, duk san da ya zo cikin gaisuwarsu sai ya binciki ta sha magani, duk da cewa takanas yake yo mata waya ya ce mata idan ba ta sha maganinta ba ta dauka ta sha. Wannan dalilin da ya sa ta ji gaba daya Kanon ma ta gundureta, a cikinta ta hadu da Auwal, kuma a cikinta suka rabu. Kwana biyu da komawar mahaifiyarta gida ta cimma Hajiya a daki bayan ta ji a ranta lallai ba zata iya ci gaba da rayuwa a Kano ba. Cikin in'ina ta debo maganar. "Hajiya jibi nake son komawa gida". Hajiya ta dan yi sororo tana kallonta, a kallon nata ne kuma ta fahimci da gaske ta ke. A sanyaye Hajiya ta ce mata. "Gida kuma Rumaisa'i?" Ta kada kai kanta na kallon 'kasa, Hajiyan da Hafsat suka 'kara kallon juna, Hajiya ta riga magana. "Na yi tsammanin za ki jira bikin su Hafsat Rumasa'u? Ki daure ki samawa zuciyarki filin ajiye farin ciki, duk abin da Ubangiji ya tsarawa mutum dacewarsa shi ne ya rungume ya yi gadiya cikin tsoron Allah". Rumasa'u ta daddage ta yi murmushin ya'ke, amma ta kasa cewa komai, sai Hafsat ce ta katsa kame kunnenta da cewa. "Haba Rumasa'u ko ba a garin nan kike ba ai duk inda kike kin taho tun yanzu dan mu yi shirye-shiryenmu tare, bare kina garin me za ki koma gidan ki yi sati biyu ki dawo? Haba Rumasa'u me ya yi zafi?".. . . Allah sarki masoyiya, ba dan jikin nata ba ai da nayi magana an hada bikin mu da ita.lol. Dan Aunty na Ruma..GORAN DUMA (P 22) . . Nan da nan idonta ya cika da kwalla, ta kawar da kai tana nad'ewa. "Ni garin ne kawai ya yi zafi, na tabbatar idan na yi nisa da shi zan sami sau'kin 'kunan zuciya... Don Allah Hajiya ki bar ni in tafi, lokacin auren na dawo..." Hajiya ta tari numfashinta dan ta ga tana shirin rikicewa. "Shikenan za mu tattauna maganar da Alhaji zan sanar da ke zuwa dare, sai ki fara shiri ko?" Ta kad'a kai, fuskarta ba ta bayyana abin da zuciyarta ta ji da maganar Hajiya ba; dad'i ko ba yabo ba fallasa? Alhaji ya 'kurawa Hajiya ido cikin rashin hayyacin batun da ta gama zantar da shi, akwai alamun ya kasa hankalinsa fiye da yadda ya kamata ya kasa shi, can ya nisa ya ce. "Kin san abin da raina ke raya min game da yarinyar nan?" Hajiya ta girgiza kai kawai tana kallonsa, ya 'kara jan numfashi sannan ya sauke ajiyar zuciya ya ce. "Da kamar ace ka isa da d'an yau, sai in saka Yusha'u ya maye gurbin Auwal a yi auren nan kamar yadda aka tsara. Ina cike da tausayin yarinyar nan ko daya ba na 'kara kaunar ta shiga hannun da zata wahala, ko hannun da bai san darajarta ba, samun irin marigayi Auwal wani abu ne mai gajiyar da numfashi shi yasa na cika da tsoron hannun da zata fad'a". Hajiya ta jima kafin kwanyarta ta fanso kanta daga firgicikin da ta shiga, Yusha'u nata ne, amma ta tabbatar hada shi aure da Rumasa'u wani ganganci ne, musamman idan ba da amincewarsu ba, har ga Allah ba ta shakkar Rumasa'u saboda sau'kin hali da taushin zuciyarta, mace ce da duk yadda ka kai da ba'kin hali da wuya ka gundurar da ita, har ka gani a fuskarta, amma Yusha'u wani irin mutum ne mai juyayyen hali da kin fahimtar mutane da jujja ko da gangan. Saboda haka kullum ra'ayinsa yake tfy, kowa bai iya ba, ita kanta ta san ba don Yushau yy sa'ar tsayayyen uba ba, da su kansu iyayensa sai sun yi kuka da shi. Amma da yake babu 'yar musu tsakaninta da mijinta sai ta binne wannan zargin ta kawo wani da ta ke jin zai musu ma'ana, wato ta sanar da Alhaji labarin Hafsat ta baya na yun'kurin hana Auwal auren Rumasa'u da mahaifinsa ya yi. Ta 'kare da cewa. "Yanzu babu abin da ya fi tsaye min a rai irin wannan, auren Rumasa'u nan kusa zai taimaka wajen mantar da ita Auwalu, ta ya ya hakan zata kasance idan ana gudun auren sickler?" Kai tsaye Alhaji ya tare ta da fadin. "Ni ma daya ne cikin dalilaina na son Yusha'u ya aureta, 'yar uwarsa ce ya san darajarta kuma ya san matsalarta. Ina ji a raina duk wani da zai yi tattalinta bayansa zai bi, dalilina na biyu shi ne, kawo 'karshen zaman wannan tuzurancin nasa ba tare da dalili da 'kosai-kosai da shi. Shi ba dan zuhdu ba, ba komai ba ballatana a kalli abin a matsayin ya hana shi aure, kullum maganarsa daya ke nan bai ga wadda ta yi masa ba. To ga 'yar kirki nan ya zo ya aura na san duk 'kawar da yake a mace ba zai zarce hangen irin Rumaisa'u ba... ke ni Allah Ya had'a kansu, rasuwar Auwal din wata aya ce a cikin fatara". Hajiya dai sai sauke ajiyar zuciya ta yi ta ce. "Allah Ya tabbatar da abin da ya fi alkhairi". Ya amsa da, "Amin". Lokacin da ya ke laluben lambar Yusha'u a wayarsa, sannan ya ce. "Ki rarrashe ta ta bani sati daya, zan tattauna da wadanda suka kamata akan maganar Yusha'u, in akwai yiwuwar hakan ina ganin ba sai ta koma gida ba ko?" Hajiya ta yi dariya ta ce. "To ai ni ban ma san abin da zan ce mata ta kwantar da hankalinta ba, yadda ta ke nunawa zamanta anan zai ci gaba da tuna mata Auwalu". Ya kara wayar a kunne yana amsa mata. "Ki fada mata na ce sai nan da sati daya, zata fahimce ki". Da dare Alhaji ya ji muryar Yusha'u a palon Hajiya, ya tabbatar kuma Rumasa'u na falon tare da Hafsat da Mubarak, kawai sai ya nufi falon kai tsaye da niyyar sanya ido ya ga yadda suke mu'amalar juna wata'kila ya san ta inda zai fara tunkararsu. Kowa na zaune ana hira cikin sakewa, amma Rumaisa'u na kwance kan doguwar kujera ta yi dif kukan zuci ta ke, domin tana hana hawaye zuba a idonta. Duk lokacin da idonta ya kai kan agogo ta ga karfe tara zuwa goma har sha daya na dare, sai ta ji wadannan lokutan ne ta tarar da missed calls din Auwal, daren da zai mutu, kaiconta shi ne ina ma ta daga ta ji abin da zai fada mata, wanda ta ke jin ya matsu ya fada mata tunda ya dinga jero mata kira sama da ashirin duk abin da yake son fada mata ta tabbatar da ya sameta ya fada matam da yanzu ya zame mata wani rubutu da zata dinga karantawa yana rage mata d'imi. Idanun Alhaji a kanta, ta muskuta ta dan goge kwallar da ta fi 'karfin zuciyarta ta fito ba tare da ta lura Alhaji na kallonta ba, ta janyo wayarta ta fara dubo sa'konnin Auwal a wayar tana goge hawaye a sace. Alhaji ya yi gyaran murya ya ce. "Rumaisa'u yaya dai na ga kina 'yan 'kananan hawaye?" Ta yi saurin basarwa ta juyo ta dube shi, amma ta rasa abin cewa, har sai da Hafsat ta dube ta a nutse ta ce. "Tunani ko?" Ta yi saurin girgiza kai ta kama ciki, ta ce. "Cikina ke ciwo". Alhaji ya yi saurin duban Yusha'u wanda ko juyowa bai ba, yana ta faman ji da kayan marmari, sannan ya juya ya dubi Rumasa'u cikin tausayawa, ya ce. "Ayya kin sha maganinki kuwa?" Ta kada kai ba tare da ta samu damar maganar ba. Alhaji ya kuma juyawa ya dubi Yusha'u ya ce. "To ko asibiti zaku tafi, Yusha'u tashi ka kaita asibiti". Yusha'u ya ji wani irin takaici ya tokare masa ma'koshi, da kyar ya sami wani dan sarari bayan ya hada takaicin da lemo ya hadiye, ya kokarta yana duban Rumasa'u ya ce. "Toh, tashi mu tafi"..... . Ni yau rai na ma ya baci, ya za'a hada Ruma da mudadden namiji bayan tace ni take so? Sai bayan sati biyu ma kawai.lol. Dan Aunty. . . Ta yi saurin girgiza kai tana duban Alhaji. "Ai bai yi tsanani ba Alhaji, akwai maganin da zan sha". Hajiya ta shiga maganar. "Tafarnuwar za a jajjaga miki?" Dole ta kada kai cikin ajiyar zuciya, Hafsat da ta san aikin ta ne sai ta mike tana cewa. "To bari na kawo miki, Mubarak zo mu je ka taya ni 6arewa". Alhaji ya yi saurin tarewa. A'a! Debo tafarnuwar ki kawowa Yusha'u ya yi aikin". Rumaisa'u ta dubi Yusha'u da sauri, amma ba ta iya karanta komai a fuskarsa ba, amma dai fuskar tasa ce ta 6oye, domin ya shiga rudanin cewar akwai wata a 'kaasan zuciyar Ahaji saboda haka dagewa ya yi murmushin karfin hali ya ce. "Alhaji ai ba na son warin tafarnuwa". Alhaji ya tsare shi da ido ya, ya ce. "To ai haka zaka koya ka saba, misali idan ka haifi sickler zare hannunka zaka yi ka bar matar da dawainiya?" Da yake Yusha'u ba yaro ba ne, nan take ya kamo tashar, gumin goshi ya fara masa sallama, dan sanin waye mahaifinsa akan a'kida, sai ya yi 'kasa da kai kawai yana hirji a zuci. hafsat takawo masa tafarnuwa da ruwa da kofi ta zauna zata tayashi alhji yace tashi ki bar shi. Haka yagama komai ya ce mata to taso ki amsa taje ta amsa ta kafa kai ta shanye.yauwa haka ake idan wani nakusa dakai bashi da lfya taimaka masa zakai..alhji ya ko ma nashi yushau ya jima yakasa tashi yaje kiran mahaifin nasa saboda kiran mahaifin nasa yasan auran ruma ake son likamasa dukda yasan imma hakan ta tabbata baisa ya bijiremasa ba..ya isa dakinsa alhji ya ce wani dan sharar fagge naimaka dazo akan danwani aiki danake son baka wanda na tabbata zakaji dadi. dan ALLAH kai wani tunani akan Ruma kasama mata wata makoma dazata iya zama da zata iya zama mata masalaha dangane da halinda ta tsinci kanta..naimaka hakan ne danganin kaine babba dagani har abbar ruma in muka mutu dawainiyar ya yan mu zai iya hawakanka..nandai alhi yaitamasa bayanin yanda zai fahimce shi amma daga kar she sai yushau ya ce inaga alhji komawar ruma gidansu yafi mata kwanciyar hankali.. daga kar she dai alhji ya ce kai nakeso ka maye gurbin auwal.. A dukkan maganar Alhajin babu ga6ar da Yusha'u zai karya ya shigar da nasa 'korafin saboda haka ya hau rawar baki. "An ji, ita an ji daga gare ta ne?" Kai tsaye Alhaji ya amsa masa. "Ba na jin yarinyar nan. Ai Rumaisa'u ta haifu". Gugar zana kawai Yusha'u ya dauki maganar Alhaji, don haka ya yi 'kunar bakin waken fitowa ya fadi abin da ke ransa. "Dan Allah a yi min afuwa Alhaji, wallahi ni Rumaisa'u ba ta daga cikin irin matar d anake son aure.... akwai na'kasu da yawa a Rumasa'u da ba zan iya jurewa ba". Alhaji ya 'kura masa ido fuskarsa ba ta nuna yadda ya kar6i maganar Yusha'u ba, ya ce. "Uhum! Lissafo min abin da ta rasa ko wanda ya yi mata yawa a matar da kake so".. kodaya bana da ra ayin auran macen da iliminta yadara na sec. sannan ALLAH yasa banasan shagwababben mutum.kuma aganina duk kokarin mutum zataga ya gaza. cikin tsananin ba cin rai alhji ya ce duk wadan nan hujojjun naka ba bu wanda yaikama dana addini.alhji ruma fa tafini zurfin karatu duk yarinyar dataje jamia idonta a bude yake.ganin mazansu suke kaidaya dasu basu isa dasuba.kila kuma kawai ta wafto rigimar kunbi kun shagwabata ciwon nan nata kamar wani kayan alfarma ya zamemata.alhji ni ga badayama banasan auran dangi alhj ya ce yanzu ne na fahimci bada zahiri kake amfani ba son zuciyakawai.alhji ya ce da zuciya daya na za barmaka ruma a matsayin iyali bayan na cika zuciyata dafatan zaku zamewa juna alkhairi kuma idan ina da hakki akanka abinda na zabarmaka kenan amma idan kaki sai inSaka maka ido shikenan alhji ALLAH ya tabbatar mana da mafi alkhairi badan ransa yaso ba.. awashegarin ranar ne kiran alhji ya risketa hankalinta kwance dan a tunaninta zaimata nasi hane kamar yanda yasa ba kila kuma ta bankwana.amma bayansun gaisa sai yana ta tattalinta tare da kutsamata maganar yusha u cikin da bara irin tasa ta manya. Abba ya ce mata rumaisau yushau ne yazo mana da wata magana yanaso ya maye gurbin auwal.ayadda ya cemin ya jima yanasanki ganin kinkarbi auwal yasa ya hakura.nima kuma dama inada muradin hakan kimanta da wata ibtila i dakika sami kanki aciki. rumaisau kizama mai godiya ga ubangiji.ki amince ayi auran nan kamar yadda aka sanya da mari gayi.idan rumaisau karkaf abushe take kallon alhji to mizataima kuka ko tashin hankali.duk wata damuwa ko abinsanya kuka dazata ci karo dashi a duniyarta mutuwar auwal ya isa akira shi matakin kar she.idan kuwa wannan bakincikin baikasheta ba yakamata kowani tashin hankali ya zamar mata gada ta ce masa alhji badan ka bayar da goyo n bayanka a maganar nan ba alhji dana nemi hanzari.ya ce ina jinki ruma ta ce masa alhji da baka goyi bayansa ba harshensa ne yaimazuciyar sa karya takowani bangare nasan yaya yushau baida tsarin auran irina.baikamata mutum lafiyayye kamar sa yakare a auran nakasasshiya irina ba nanda ruma ta bi duk wata hanya tagama aibanta abinda aka gani ake son hada auranta da yushau.. alhji ya ce mata duk wata lalurarki ta sikila idan har bata hanaki auran auwal to bazata hanaki auran yushau ba.yadade yanai mata nuni da abubuwa dasuka sanya yakesan ayi auranta da yushau yanzu kam Ruma tana tunanin KARA,KAWAICI, SADAUKARWA, yakamatne tsakaninta d.a alhji da hajiya wadanda suke karramata daidai da mahaifanta..ko sudasu zata iya dogara ta dubi yushau matsayin mijin aure Shirye shiryen biki ya kankama innar ruma ta iso ana sauran kwana biyu amma kafinhakan tunda alhji yajizatazo ya tura su yushau rogo saboda bayaso umman ruma ta fahimcin rashin jituwar dake tsakaninsuhaka yushau yayarda sukatafi badan yaso ba ahanyarsu ta tafiya rogo bawanda yaimagana acikinsu.saidai ruma ta karbi sakonninda take ta suka sata hawaye idan ta shiga motar auwal sai ya zuge glassai tsab ya rufe, yakuma kashe A.C sannan a motar sa baya rabo da CAR HEATER saboda ita,ga tuki cikin natsuwa,ko da a hanyar da bata da kyau ne saboda kar tajigata,bugu da kari yakan umarcetatada fito da hijab a jakarta tasa idan da mayafi ta shiga motar.... . Dan Aunty. GORAN DUMA (P 24) . . duk wadannan gatancin sun kufcemata ko kallo bata ishi yushau ba bare ayi maganar tattali danhaka taiyi ma kanta gatadakanta ta rufe gilasan.shiko sai zuba gudu yake a hanya ya cika mata kune da wakar ala wanda idan ta rantse saurare kawai yake amma baya duba maanar wakar. sunkusa karaye aka bugo mata waya wannam karan ya rage karar wakar ta daga wayar ta sada zumuncine da gaisuwa daga TAHIR wani member ne a kungiyar su ta masu sickle cell. yaimata gaisuwar auwal tare da jajantawa yushau ya ce mata wanene kukai waya da shi? tajima kafin ta ce sunansa TAHIR TAFIDA MUHAMMAD tana rufe baki ya watso mata wata tambayar yakuke dashi? memberne a kungiyarmu ta sickle cell acan muka san juna muke zumunci. ammadai kina da kudurin idan munyi aure zaki bar kungiyar? dayake na kwana sanin aurena ba zai rabani da sikila ba,sai ban ta ba tunanin zan bar kungiyar ba. amma nasan kin san duk lalacewa kinsan cewa mijinki yana da ikon hanaki duk wata muamala da yake da shakkunta ko? duk yadda kike jin wayewa nasan kinsan mijinki yana da karfi akanki. ruma tajima kwarai maganganunsa nayi mata ihu aka.saidai tayi jarumtaR boye kaico da hawaye,saboda haka ta shirya magana ma sai ta kori rauni a zuciyarta wata sha afa da mukai kenan nida kai da iyayen mu a kaida duk wanda zai auri mai sickle cel ya kamata a zauna a tattauna dashi bayan gwaji yaji matsalolinsu yaga abin juriya akai in zai jure din, yushau ya ce dan na ce ki bar kungiya idan kinyi aure? ko ruhin ciwon naki makale yake da kungiyar da idan an hanaki ya tsinke Ranki duk dai taji zafin maganar amma a sanyaye ta girgiza kai shikuma ya sami damar dorawa cikin zafin rai kiyi kokari ki fahimceni karki dinga sauya min magana kina hada min ita da ciwo.yanzu dai naji kina waya da wani wanda ba muharraminki bane... a raunane ta amsa da cewa ban dauki fadan hakan laifi bane sannan ban shirya karya ta shi ga tsakanina dakai ba Idan hakane sai ki yanke hulda da abinda kikasan banaso,dankar kifada min gaskiya inki fahimtarki kiji ciwo.inkuma karyar kike yimin ALLAH ne shaidata,kamar yanzu dakika cemin dan kungiyarkune ai bansan gaibuba,in bayan dangatakarku ta kungiyancin akwai wata dangatakar yaya zansani kaitsaye ta amsa tana duban titi. kobaka sanidinba rashin sanin ba zai cutar dakai ba,ko da cutarwar ta fargaba ce tunda kasan ciwon sikila ba kanjamau bane da ake bukatar mai shi ya auri dan uwansa mai shi shi sikila so ake ya nemo lafiyayye ya aura dan dorewar haihuwar yayansu masu lafiya.saboda haka karkadamu kanka da dangantakata da wani sickler ko kuma ka saka mana zargin dangantakar soyayya afusa ce ya juyo ya dubeta idan na fahimceki umarni kike minko?kawai saitasami kanta da tuntsi rewa da dariya tana kare masa kallo kaitsaye ta ce. "Haba dai, yaushe zan maka umarni? Na ga dai kamar bai kamata mu dore a gizago da biyayyar babu ji babu gani ba. Ya wajaba mu tattauna matsalar ciwona da kai a yanzu kafin nan gaba ka ce an baka a rufe". Karkacewar da bakinta ya yi wajen dariyar da take, yasa tausayinta ya danne takaicin dariya da ma'anar maganar da ta yi masa. Ya kawar da kai ya bi titi da kallo, sannan murya 'kasa-'asa ya ce. "Tunda ba fasa auren za a yi ba idan na ji abin da bai yi min ba cikin abin da za mu tattauna din ai barin tattaunawar ya fi..." Ta tari numfashinsa da fadin. "Me yasa za a kasa fasawa in kuma ka ga ba ka muradi? Duk sickler ya san a saka aurensa a fasa ba wani ba'kon abu ba ne, saboda haka babu abin da zai fari dan ka fasa". Ya jima kwarai yana sa'ka maganar da zata fito bakinsa kafin ya barta ta fito. "Da zaki ajiye bokonki waje guda, in sami kawwamammen matsayi a wajenki irin wanda nagartattun iyayenmu mata ke ba wa mzajensu, to ina jin zan zama mai hakuri da tuntuninki ga Auwal. Dan haka ba kya bukatar 6ata lokacinki wajen yi min umarnin in aure ki ko in fasa tare da sanin fasawar tawa ba zata rage ki ba, ko ta amfane ki, tunda wani za ki aure ba Auwalu ba". Ta yi shiru kawai tana juyawa maganganunsa, kaasa fahimtarsu sosai ya sa martaninta ya bi ruwa. Shi da ya damu da jin ta bakinta sai ya tuna mata yana mai kallonta. "Ba zaki ce komai ba?" A sanyaye ta amsa masa. "Ga6o6in maganganun naka ne da yawa, yadda kowace na karya za tashi guda in kuma jata ta yi tsawo, saboda haka kar ka zaci muhimmin abin da kake son jin bakina a kansa." Kai tsaye ya amsa mata. "Kar ki dauki kanki wata tsiyar saboda kin yi zurfin karatu, ki zauna da ni zaman bauta kwatankwacin yadda kika ga iyayenmu na yi. In kika yi hakan shine kika ba ni karramammen matsayi wanda zai wanke min dukkan tsatsa a raina na auren mai zurfin ilimi da ban ta6a shiryawa rayuwata ba". Ta dinga jan numfashi kafin ta amsa masa cikin dakewa. "Ina jin da taka karramawar zaka sai wancan matsayin da kake ambatawa, in kuma ka cire zace- zace da zarge-zarge ka kuma cire garaje cikin mallakar matsayin da 'karanta rainuw da kuma sau'kaka fahimta, wannan shi ne". Ya yi dif kamar ruwa ya cinye shi da harshensa ya yi niyyar fada mata abin da zuciyarsa ta fahimta a maganarsa. To abin da zai gaya mata shi ne bokon da yake gudu ta yi masa. Bashi da za6i, dole ya yi shiru ya kyale ta, ai a kan sharafinta take tunda tana da Alhaji me tsaya mata. Har suka shiga cikin garin Rogo babu wanda ya tanka wani, suka sauka a gidan kakaninnsu, duk da tuni kakannin sun 'kar, sai 'ya'ya da jikoki. Haka kowa ya dinga sanya musu albarka, Yusha'u na shan albarkar yarda da ya yi ya auri Rumaisa'u da nakasarta, Rumasa'u na shan albarkar ajiye jimamin rasuwar Auwal da ta yi a gefe ta yarda ta kar6i dan uwanta. Sun wuni a nan gidan, sai dab da la'asar suka nufi gidan Goggo. A gidanta Yusha'u ya yi mafi rinjayen zamansa saboda sha'kuwarsa da 'kaunar da 'yan uwa da Allah Ya zuba mata. 'ya'yan wa da 'kani da mahaifinsu. Son danginta neyasa duk sa'adda ta kwashi Auwal suka je Rogo, to a gidan Goggo zata sauke shi, su yi hira su yi barkanci tare da Goggo. Wannan dalilin yasa suna shiga gidan yanzu gaba daya jikinta ya yi la'asar, musamman da Goggo ta baza musu tabarma wajen da ta saba shimfida musu in ta zo da Auwal, sai ta kasa zaman kan tabarma ta koma kan 'karamar kujera ta zauna tana kokarin hadiye kwallarta. A haka suka gaisa duk tana rikice, a karshe dauriyarta ta kai 'karshe lokacin da wasu rukunin zabbi suka gifta, ta tuno lokacin da suka zo da Auwal an kyankyaso jariran zabbi fiye da ashirin reras abin sha'awa, ya daga kai ya dubeta ya ce. "Don Allah zabbin nan ba su burge ki ba Rumaisa'u?" Ta bi zabbin da kallo tana murmushi, sannan ta ce...... . Dan Aunty. GORAN DUMA (P 25) . . "Ba na jin sun burge nikamar yadda suka burgke ka, tun dazu fa na ankara kana ta faman satar kallonsu..." Ya tare ta cikin dariya yana kallon Gaggo. "Satar kallo kuma? In zan kalli zabbi sai na saci kallonsu kamar ke zan kalla a gaban Goggo?" Shi ma Goggon ta tare shi da fadin. "Dan ma ita din ba satar kallon nata kake a gaban nawa ba, 'karfi da yaji kun mayar da ni kakarku". Suka tuntsire da dariya su duka. Auwal ya ce. "Kar ki sami damuwa Goggo, ko barewa a daji da danta ta ke wasa. Ina son zabbin ya ya zaki yi da ni?" Goggo ta yi murmushi ta ce masa. "Ka zo garin nan ka siya a yi maka kiwo. Ya kuma bin zabbin da kallo, sannan ya juyo ya dubi Rumaisa'u. "Har yanzu ba su fara burge ki ba Rumasa'u? Anya kuwa zabbin nan ni ma sun burge ni? Duk abin da ya burge ni fa ya kamata ya burge ki". Ta bi zabbin da kallo suka zuba musu ido tare, sai can ta juyo ta dube shi cikin murmushi ta ce. "Wallahi sun fara burge ni". Da tausasshiyar murya ya ce mata. "Haba ko mu fa". Sai suka bar Goggo da sallalami suna yi mata dariya. Yanzu da Rumaisa'u ta 'kurawa Zabbin ido cikin kwalla nan take ita ma Goggo ta tuno tunowar da ita ma ta tilasta mata kwallar, sai suka bar Yusha'u galala yana kallonsu da kwanon ruwa a hannu. A karshe kukan zucin Rumaisa'u ya ki 6oyuwa sai da ya ta fashe da kukan bayan ta sunkuya kamar zata shid'e. Da sauri Goggo ta 'karaso wajenta ita ma nata kukan ya 'ki 6oyuwa ta ru'kota duk suka rafke da kuka cikin kuka Goggo ta ke cewa. "Manta Auwalu a zuci wani abu ne da ba zai ta6a yiwuwa ba, dan cikin rayuwarsa ya guji abin tir, babu yadda zamu yi haka zamu ci gaba da daurewa muna yi masa gatan da ya fi bu'kata yanzu, wato addu'a". Ga mamakin Yusha'u sai ya ji wani matsanancin kishi ya turnu'ke masa 'kirji, ya sababba masa fusatar da ya ajiye ruwa ya tashi a fusace ya fice daga gidan. Hakan ya basu dama cin karensu babu babbaka, suka ci kukansu, Rumaisa'u na maimaita. "Kin ga yadda Allah Ya yi da ni ko Goggo, na rantse da mafarki ne abin da ke faruwa da ni idan na farka bacci ba zan 'kara bacci har abada". Sun jima cikin wannan damuwar, da koke-koken har sai da mutam gidan suka fara zagayowa kewayen Goggo dan gaishe da ba'ki, Goggo ta ari juriya ta hau yiwa Rumaisa'u ga yiwa Auwal addu'a da sadaka su ne gatan da zai iya samu daga gare ki a halin yanzu." Rumaisa'u ta yi namijin 'kokarin gyada kai da sauri cikin gintse kuka lokaci daya zuciyarta na halarto da aikatawa Auwal dukkan Wani gata da kwanjinta zai iya in dai zai taimaka wajen sada shi da rahamar Ubangiji amma ta ji a ranta mantawa da Auwal ne har abada ba zata iya ba. Ta tuna da auwal dake firar dasuke ya ta hallakane akan matsalar ruwa inda tatuna wani zuwansu rogo yake cemata abu nafarko dazansaka agaba bayan hidimar bikin mu ita ce insamu yan kudi inzo garinnan in gina rijiya ko bayan raina sai ladar ya amfaneni farad daya tafara tunanin hanyar dazata bi ta cikamasa burinsa duk zuwan dazasui da auwal indai akwai lokaci sai sunje kan dutse.saboda haka ta shirya tama gwoggo sallamar fita zuwa kan dutse duk da tasan zuwannata sai gadar mata da kunan zuciya ahaka takasance har rana tagama yinja tafara sauka a hankali tayi kuka hartakasa gajiya duk wanda yaganta a wannan halin sai ya tausayamata.bata hango yushau na zuwa ba motsinsa kawai taji tajuyo taga fuskar sa ba annuri wai anan zaki kwanane? aranta ta ce abune mai matukar wuya ta taRe da giRman ciwo a ce tarasa mai tattali da fara a kamar gonar auduga ace ta bige da auran mai kyaliya da gizago kamar zaki. ta tashe ta bi bayansa tana mai share hawayenta..har suka iso kano tara saura babu wanda ya tanka acikinsu Suna faka mota tafara kicikicin bude motar amma a kulle danhaka saitai shuru dan bazata iya dubansa ba balle ta nemi dalilin yin hakan.yajima yana huci san nan ya sauke cikin gyaran murya Sannan ya ce bawai gudun laifinake ba illa gudun daukaR bakuna,in ma laifine yakamata a tuhumeni da wanda nake da ruwa da tsakinsa,ba lallai agida su san haka ba,kiyi kokarin gyara wannan hawayen wofin dakike zubdawa dan karki janyo a dora min alhakinsa bata tankamasa ba tagoge hawayenta tsab ta rabka tagumi.ki kwance jaka ki shafa hoda ta cemasa dazan fito ma ban shafa hoda ba ta muskuta cikin tsananin kuncin zuciya ta cemasa shafa hoda tana nufin farinciki ko jin zakin rayuwa,nikuwa duk nayi bankwana dasu.a fusa ce ya fice daga motar yana cewa au na shafa cewa a cikin takaba kike wanda baikamata na manta hakanba itama ta fito ta wuce dan tuna cewa yaufa mominta zatazo tana isa ta ga innarta ga kuma balaraba yayarta harda kari ma wato da innar auwal. Maimakon ruma taiwajen innarta saita nufi innar auwal tafada cinyarta tafara rera wani irin kuka mai tsuma zuciya.inna data gama wani kukan sai ga zuwan ruma.inna nanata kukan ruma na nata kukan mai keta zuciya ke akaima rasuwa ruma kekikai rashin auwal.Allah ya baki hakuri da dangana Allah yajikansa kekuma ya baki wanda ya fishi.wadan nan kalaman nata ne suka kara kular da yushau.da ya shigo yanzu,yakada kai yai waje baitsaya.ba balle ya gaida bakin a can falon alhji wani takai cin yatararmmahaifin auwaldin yatarar tare da alhji suna hira.hirar kuma ta auwal da ruma game da yan matsalalolinda suka taso gab da auren.akar she hirar ya rufe da cewa dake shi ALLAH babu ruwansa sai ya saukar da ayar sa gareni.ya karbi auwal mai lfyar alhalin shikadai na haifa.yayanke min hanzarin 'ya'yan dana tara burika akansu.nake kuma tafaman hura hanci akansu.alhali bani da sani akan Samuwar su ko rashin samuwar su. hakadai har yushau yadaure yagaida su tare da alhji.danhaka alhji yanuna yushau ga mahaifin auwal tare da cewa ga wanda ze maye gurbin auwal. ya ce masha ALLAH karike ta da kyau yarinyar tsakani da ALLAH yaimasa nasiha kwarai.... . Daga uhum sai uhum baki na dai har yau a kulle yake.. Dan AuntyGORAN DUMA (P 26) . . RUMAISAU DA MOMINTA CIKIN DARE. har sha biyun dare ruma,hafsat tare da balaraba da momin ruma da barci ya ciyo idan hafsat,kuma taga alamun nuna tausayinta ga ruma kuma kamar tanasan kebewa da yartata.saboda haka taimusu sallama ko minti biyar bataida fita ba momi tadubi Ruma da kyau ta ce.inafata ba matsa ma kanki da zuciyarki kikai ba kika aminta da auran yushau.? ruma tajinjina kai tare da murmushin yake ta ce bazan iya zabar mijiba momi dantagama zancenta yaya yushau zai shi go rayuwartane dan rashin zabina bai zama karewar numfashina ba baikuma kankare aure daga cikin ayyukan da aka rubuto a allon abinda zanyi a duniya ba,rashin auwal ne matsala a rayuwata ba auran waninsaba.momi ta ce to ALLAH yajikansa yasa aljanna ce makomar sa.kekuma ki rage yawan damuwa kinsan yanayin ciwonki.balarab kawai kallonsu take yi saboda tsabar tausayi takasa cewa komai.ruma ta shaRe hawayenta ta ce ina tilastawa kaina musamman danganin bakincikin rashin auwal ya isa ya karar da nawa numfashin.amma gani a raye ALLAH Ne kadai yasan abinda yake boye yaSa ya barni araye bataRe da auwal ba saidai ina neman wata alfarma wadda nake ganin zata taimaka min narage tuna auwal cikin kunan zuciya,illah in na tuno shi nai farinciki umma da balara ba cikin doki tare da hada baki wa ce alfarma?momi kiyimim alfarma na sayar dawasu hannun jarinda kika saimin da kudin motar da alhji ya hanaki siyamin.kikuma banidama na sayar da sarkokina ahadamine kudin da dangin auwal suka barmin ko a siyar dawasu da wasu daga cikin kayan lefan... Cikin kaguwa momi ta ce aime da kudin? Ruma ta shaida musu yadda sukai da auwal dakuma bukatar cikamasa burinsa.asanyaye balaraba ta ce amma dai zaki iya dorewa dayimasa addua samun rahamar ubangiji ruma ba saikin salwantar da dukiya mai yawa ba..momi tai saurin dakatar da ita ta ce a a balaraba ba salwantar wa ba ce,ya kamata tunanindatai auwal yafi karfin komai agurinta,ba komaikarki samu damuwa za ayi zanfadawa dadynki idan kudin basu cika bama zancikamiki. cike da farinciki ruma t.ai godiya momi taji farinciki ya cikata dan tada de bataga farincikin ruma kamar na yanzu ba tun kafin rasuwar auwal sunata hira har suka fado kan yush.u anan ne ruma tafadi wata alfarma momin su alhji sundauki yaya yushau dan gida a ciwona suna ganin kamar babu wani bukatar a tattauna matsalar ciwona dashi dan haka ba a tattauna dinba.bana son a share wannan batun kirjin momi yaf.ara lugude dan haka tai zuru tana kallon ruma ta tabbatarw kanta akwai dalilindayasa ruma wannan maganar kasancewarta mace mai zurfinciki da karanta korafi.ta ce fadamin gaskiya saboda ALLAH mekika hanga kikawo wannan maganar? A sanyaye ruma ta shaida ma ummanta yadda sukai da yushau bayanta amsa wayar tahir tafida muhammad takare da cewa bazan iya dorar da yadda yaya yushau ke karbar alamurana ba,amma ko ma menene baya karbar .alamura da sassauka fahimta yazuwa yanzu momi ta rafka tagumi sannan damuwa tattare da fuskarta momi ta ce kunya da nauyin alhjh. nake ji ruma da badan haka ba bazan bawa yushau aurenki ba cike da tawakkali ta dubeta badam nadaga miki hankali kodan in sanyawa ranki rashin natsuwa cikin aurena da yaya yushau ba.nandai suka ci gaba da tattaunawa daga karshe ruma ta ce ki kyau tata zato a aurena da yaya yushau,.. washegarin ranar alhamis kenan ya shigo gaida umman ruma..nan ya taddasu harda ummansa haryatashi zaifita umman ruma.ta ce masa idan babu damuwa kadawo kamar karfe sha biyu don ALLAH inason kakaini yankaba wajen aunty fati . Yusha'u ya hadiyi wani irin yawu wanda ya taimaka masa hadiye 'kuntata masa ran da yake jin an yi, ya dubi agogo ya ce. "Babu damuwa Momi, zan yi 'kokari in dawo din duk da akwai tarin ayyuka a gabana kasancewar jiya ban sami sararin zuwa kasuwar ba, amma dai komai runtsi zan yi 'kokarin dawowa zuwa azahar... Ko kuma na yiwa direban Alhaji maganar ya zo ya kai ki...?" Ta yi saurin tare shi da girgiza kai. "Kai nake so ka kai ni..." Hajiya ma ta yo kansa ta fada. "To wai umar me kake a kasuwar me shegen nauyi haka?" Nan da nan ya karya murya ya ce. "Babu matsala zan dawo, ku shirya zuwa sha biyun". Hajiya ta juya kai, Momi kuma ta yi saurin cewa. "To Allah Ya dawo da kai lafiya na gode". Ya amsa, "Amin." Sannan ya fice ransa na yi masa wani irin 'kuna, takurar da yake fuskanta daga mahaifansa akan wannan auren bai san dalilinta ba. Sai ka ce shi ya dau ran Auwal? Dole kafin sha biyun ta cika ma ya dawo gidan ya dauki Momi, kasancewarsa mutum mai saurin fahimtar abin da mutane ke yi, ko shirin yi yasa shi zargin akwai abin da Momi ke nufi da ya kai ta 'Yankaba tunda ya ga ita kadai ta fito. Saboda haka da suka dauki hanya bai dauki furucinta a ba-zato ba lokacin da Suna tafiya daga cikin harabar gidan t. a cemasa yushau waikuwa kunje sickle cell counselling centre kaida ruma? yushau mutum ne da bai iya karya ba danhaka kaitsaye ya ce a.a bamuje ba,jiyannan dai ruma taimin magana.nikuma inagai idandai zuwa neman shawaran bazai sauya komai na yuwuwar auren mu ko rashin yuwuwar hakanba.inaganin babu bukatar batawakai lokaci momi ta ce masa neman shawara zai iya rushe aurenku.amma idan kunso..yushau yakurawa titi fuskar sa ba ya bo ba fallassa ya ce OK. hakan yasa takauda kai ta ci gaba da bayanani tundaga matakin farko har iya idan take ganin zai fahimci komai.tadade tana masa bayani daga kar she tadaka ko zaice wani abu kafin ta dora da.... Gwajin ba ya daukar wani dogon lokaci, za a dauki jininka ne a sirijni sai shigar cikin na'ura ta musamman domin wannan aikin. Gwajin zazzabin maleriya ma ya fi gwajin sikila jimawa. Sannan komawa asibitin ko sickle cell couseling center ga me shirin auren sickler a karo na biyu, shi ma wani gingimen muhimmi ne cikin dukkan matsayin da gwaji ya nuna mutum, AS ne ko AA, in AS ne zai je neman shawara tudu biyu ne, wato matarsa da kuma 'ya'yansa ko 'ya'yanta da zata haifa ko zai haifa. Cikin shawarwarin likitoci nunawa abokin zama yadda ciwon sickle cell yake kamar yadda na fara yi maka bayani a baya alamomin tashin ciwon, kulawar da ya kamara ciwon ya samu a gida idan ya tashi da kuma abubuwan da ya kamata a kiyaye dan kar ciwon ya tashi, da kuma abin da za a yi a gida in ciwon ya suman a garzaya asibiti, juriyar zuwa asibiti duk wata, sannan da tanadin kudi saboda ciwonsu, ko mutum AA ne ya kamata ya kwana da wannan Sani..... . Dan Aunty. GORAN DUMA (P 27) . . . In kuwa AS ne zai 'kara da tanadin kudi dan hidimar ciwon sauran sickler duk da zai haifa, tunda ciwon sickler ba ciwo ne da ake warkewa ba, yadda Ubangiji ya halicci mutum ke nan haka Ya so da ganinsa ba dan yana 'kinsa ba, illa iyaka dai ya kamata mace ko miji su sani ba mutum daya ke gadar da sickle cell ba, ma'ana ba dan mace sickler ba ce kawai ta ke haihuwar sickler ko ba dan miji sickler ba ne aka haifar masa sickler ba, a'a duk su biyun mata da miji ke karo-karo su haifi sickler..." Momi ta dan dakata ko Yusha'u zai ce wani abu kafin ta dora da zayyana masa yadda sicklers ke jin ciwo a jikinsu da kuma matakan da ake bi wajen taimakon gaggawa, ciwon ya sauka amma sai jikinta ya yi sanyi, domin ko kadan fuskar Yusha'u ba ta sauya da tausayi ko mamaki ba, kusan ma kamar a gundure ya ce. "Allah Ya sawa'ke, kuma maganar gwaji ma ai ta wuce kamar yadda na fada, in dai zuwa gwajin ba zai tankwa6e Alhaji hana shi daura auren ba... Ni ban ma dauki ciwon Rumaisa'u wata martsala a cikin aurena da ita ba..." Momi ta jima tana kallon tagar mota cike da matukar takaici, sannan ta daure ta ce. "Yusha'u ba ka son auren nan, Alhaji ya matsa maka ko?" Ya yi girgiza kai cikin murmushin ya'ke ya ce. "Ni ba matsa min ya yi ba wallahi, bamban muka sha da ku kawai, abin da kuke kallon shi ne matsala ni a gurina ba shi ne matsalar ba". Har yanzu Momi sha'ke ta ke da takaici, sai dai wayewarta ta hadidiye takaicin, ta nisa ttace. "Yusha'u me yasa ba ka yi tunanin mun fi ka gaskiya ba tunda mun rinjaye ka". Ya jima cikin shiru kafin ya tanka. "Momi ai duk ba wasu abubuwa ne masu zafi da za yi ta tashin hankalu a kansu ba...." Fuskar Momi cike da damuwa ta girgiza kai ta tareshi. "Don Allah Yusha'u me yasa ba ka bijirewa auren Rumasa'u ba tunda akwai matsala a cikinsa abin da ba ka fahimta ba shi ne, kai ba ka kallon ciwon Rumasa'u matsala, ni kuma a duniyar nan ba ni da matsalar da ta fi shi girma, ko tattalin ciwon Rumasa'u nake, to na tabbatar ina yi masa tattalin da yake wa rayuwarta amfani dan ina kokarin kore dukkan abin da zai motsa mata ciwo saboda ina jin ciwon cikin matsalolin da ke daga hankalina. To kai ba ka dauki ciwon matsala ba ta ya ya zaka iya kare shi? Abin da kake dauka shine matsala wata'kila ni da Rumasa'u mu 'ki kula da shi, dole ne wadannan bambance-bamncen fahimtar su gadar mana da matsaloli a gaba akan wannan Yusha'u na so ace ka 'ki auren nan... Ina da juriya akan komai amma Allah Ya sani ba ni da ita akan Rumaisa'u, ina fada maka gaskiya ne dan ba zan iya fitowa in hana ka aurenta ta dalilin bambancin al'kibla ba". Nan da nan Yusha'u ya gane kato6arar da ya yi, wadda ya ke tsoron zuwanta kunnen Alhaji, dan haka ya yi sauri ya gyara muryarsa da ladabinsa. "Haba Momi ba ki fahimce ni ba ne, ko Rumasa'u ba ta aure ni ba, ai ni mai zage kwanji in kare mata abin cuta ne, balle ni in zame mata cutar, don Allah ki kwantar da hankalinki ki bi mu da addu'a... Ni fa babu wanda ya matsa min aurenta". Momi ta yi shiru kawai da alama zuciyarta ta fara sanyi, sai can jimawa ta ce. "To maganar zuwa asibiti?" Tana direwa ya amsa cikin kwantar da kai da murmushi. "A kyale maganar gwajin kawai, ko ya ya zata haifar min 'ya'ya ina son su haka zan kuma tanade su". Momi ta dan juyar da fuska ta ce. "Ko 'ya'ya zaku haifa dai ai na fada maka mutum daya ba ya haihuwar sickler". Cikin irin karya wuyan nan na to da hausawa suka ce ba ta karya wuya ya ce. "Ko 'ya'ya zamu haifa Momi, ku yi mana addu'ar Allah Ya ba mu ikon kula da su". Yanzu ta fara saukowa sosai, ta ce masa. "Amin. Amma tilas ne ka je ga mashawartan sickler dan jin irin dawairniyar dake gabanka da kuma abin da zaka yi hakuri a kai. Adddu'a ma ibada ce, amma akwai ayyuka tu'kuru kamar yadda aka ce, aljanna ba ta samuwa da wayo ko dabara sai da aiki". Nan ma cikin rawar murya ya ce. "Zan je gobe da sanyin safiya cikin yardar Allah. watakila anan motar ya zubda shawarar data basu.dan tunda sukai haka da ummanta baikara bi takanta ba har aka shi ga hidimar biki sosai.ruma duk wani farincikinta da ita da ummanta da balaraba duk yake suke kawai. aka daura auren ranar lahadi akakai hafsat gidanta dawaki road aka kai ruma nata gidan sallari kowa ya watse aka bar su da halinsu. kamar kowa ce amarya abokan ango sunkawo ango sunkuma danyi barkwanci sukai sallama da amarya suka tafi.ruma takasayin komai illa data tuna auwal amma a a wannan karan taki zubda hawaye musamman data tuna cewa ummanta taimata batun sayarda abunda ta ce ayi wannan kadai ya wuni yana faranta ran ruma agundure ya cemata ALLAH ya sauwaka kuma maganar gwaji ma aita wuce kamar yadda nafada,indai zuwa gwajin bazah. tankwabe alhji hana shi daura aurenba.... nibandauki ciwon ruma wata matsala ba a cikin auren.a da ita.. momi tajima kafin ta iya magana yushau bakasan auren nan alhajine ya matsamaka ko? cikin murmushin yake ya ce aa niba matsamin akaiba,kawai a inda muka sha banban ku abinda kuka daukeshi damuwa ko matsala ni awurina ba matsala bane. Momi fuskarta cike da damuma ta cemasa dan ALLAH yusha u meyasa baka bijirewa auren ruma ba tunda akwai matsa a cikin auren? abinda baka fahimta ba shine,kai baka kallon ciwon ruma matsala,nikuma a duniyar nam banida matsalar datafi shi girma,ko tattalin ciwon ruma nake,to na tabbatar ina yimasa tattalinda yake wa rayuwarta amfani dan ina kokarin kore dukkan abinda zai motsamata ciwon saboda inajin hakannyanadagamin hankali nandai yushau yagane yayi katobara kuma idan hakan yaje kunnen alhji da matsala danhaka ya gyara zancensa "Haba Momi ba ki fahimce ni ba ne, ko Rumasa'u ba ta aure ni ba, ai ni mai zage kwanji in kare mata abin cuta ne, balle ni in zame mata cutar, don Allah ki kwantar da hankalinki ki bi mu da addu'a... Ni fa babu wanda ya matsamin aurenta". Momi ta yi shiru kawai da alama zuciyarta ta fara sanyi, sai can jimawa ta ce. "To maganar zuwa asibiti?" Tana direwa ya amsa cikin kwantar da kai da murmushi. "A kyale maganar gwajin kawai, ko ya ya zata haifar min 'ya'ya ina son su haka zan kuma tanade su". ta ce koya zaku haifadai angaya muku mutum daya dai baya haifar sikila. hm..ya ce ko yaya zamu haifa momi kui mana adduar ALLAH ya bamu ikon kula dasu.. (kaji gulma kamar dagaske) ta ce amen amma tilasne kaje ga mashawartan sikila da jin irin dawai niyar dake gabanka. ya cemata zanje gobe da sanyin safiya insha ALLAH.... . To ai banda Yushau ko da mace lapiyar ta kalau ba sickler bace tana bukatar tattali da kulawa piye da yadda sarauniyar ingila take bukata, pls take note my guys. . Dan Aunty. GORAN DUMA (P 28) . . . watakila anan motar ya zubda shawarar data basu.dan tunda sukai haka da ummanta baikara bi takanta ba har aka shi ga hidimar biki sosai.ruma duk wani farincikinta da ita da ummanta da balaraba duk yake suke kawai. aka daura auren ranar lahadi akakai hafsat gidanta dawaki road aka kai ruma nata gidan sallari kowa ya watse aka bar suda halinsu. kamar kowa ce amarya abokan ango sunkawo ango sunkuma danyi barkwanci sukai sallama da amarya suka tafi. ruma takasayin komai illa data tuna auwal amma a a wannan karan taki zubda hawaye musamman data tuna cewa ummanta taimata batun sayarda abunda ta ce ayi wannan kadai ya wuni yana faranta ran ruma Ango da amarya wato ruma da yushau,shi kallon tv ita kallom yatsun hannunta fiye da minti sha biyar .rumaisau dai bata da abin cewa amatsayinta na mace da akasani da karancin azarbabi da yawaita kunya yushau ne mai abin cewa inyayi kuma yai masa kyau amma girman kai da tattalin shugabanci yahana shi motsi a kar she saikawai ya mike yana nuna mata leda ya ce ganaman nan samo faranti kibani nawa. ta yunkura jiki a sanyaye ta je kitchen ta samo faranti biyu .yan shila ne guda shidda,ta zuba masa uku muryar sa narawa ya ce biyu ya isheni. ya wuce yana cewa to saida safe ALLAH Yatashemu lfya amsar data bashi kenan bayan fitar sa, kaitsaye bazata ce taji ciwon abinda yaimata ba.in ma hartaji ciwon to bazai wuce na bar mata sarari mai katon fadi ba wanda zataita sukuwar tunanin auwal da lissafin DAMA ACE (SUNAN WANI LITTAFI.) haka tawuce kitchen ta aje naman a frige dan tarasa abin ci ta garkame kofarta... tayi kuka iya yinta inda daga baya ta tuna da hudubar mahaifiyarta ayaudin kafin akawo ta gidan miji. babbar ALFARMAN DAZAKIMIN RUMA ITA CE MANTAWA DA AUWAL A FURUCI DA HAWAYENKI GABAN MIJINKI,KO BAYAN IDONSA,KIBAR GANIN BABU RAN AUWAL DAN HAKA BAI ISA A YI KISHI DA SHI BA,INA TABBATAR MIKI KO BAYAN KO BA TA BA AUWAL BA BAKINKINE YA KIRKIRE SHI YUSHAU ZAIYI IYA KISHI DA SHI ,MATAKIN DAZAI DAUKAKUMA WANI SANADI NE NA KORE ZAMAN LFYA A TSAKANINKU WANDA HAKAN KEME ZAI DAMI DUNIYARKI..DON ALLAH RUMA KARKI BANI KUNYA BANTA BA ZATON DUK WANI ABIN TIR A CIKIN SHAANINKIBA.DON ALLAH KICI GABA DA KORESHI A ZAMANKI DA YUSHAU KITOSHE DUK WATA BARAKA DAZAIKUKA DAKE MUSAMMAN TA KORAFIN KIN MALLAKAWA AUWAL ZUCIYARKI KINBAR MASA GANGAR JIKINKI.. SHIDAI AUWAL TASA TAKARE MUNA SAKA MASA RAN DA CE DA RAHAMAR ALLAH wannan nasihohin sune sukafi tsayamata a rai tsawon kwanaki bakwai abinda ke faruwa kenan tsaka. Tsawan wadannan kwanakin hajiya ke tada mubarak ya kaimusu abinci safe rana da dare.saboda haka ruma batakowani irin aikin wuya inbanda wanke wanke da shara saiko tafasawa yushau ruwan shayi a duk sanda yai umarni hajia nada azancin na dauke musu nauyin abinci,hikimar hajiya shine,daga cikin babban abinda yake motsawa sikila ciwonsu shine aikin wahala ko yin aiki mai yawa a lokaci guda.a wasu lokuta wasu dayawa ba asanin sikilane sai sunyi aure.dalili .anan shine.aure yasa dawainiya ta hau kansu na kula da gida da hidimar maigida.sannan basu saba kwanciya da namiji ba,kwatsam sai su wayi gari cikinta.musamman idan suka hadu da namiji mai yawan bukata.sai abin yafi karfin yanda zasu iya dauka.. a azancin hajiya babu da cewar akai ruma da mai aiki a halin yanzu ga amarci gakuma rashin fahimta dake tsakaninsu duk wadannan uzurorine dake bukatar kadaici saboda haka hajiya tadau nauyin basu abinci har na sati biyu sannan tai maganar yar aiki kuma duk lokacinda mubarak zaije takan masa kashedin idan yaje yaimata share share kuma yana kwatantawa to saidai abinda hajiya takewa hidimar shi kamar baima kama hanyar faruwar hakan tsakaninsuba danta koina kofofin alama a damke suke.shiyana takama da girmankai da tattalin shugabanci. hakadai suka cigaba da zama.ALLAH cikin ikonsa kuma saiya kwantarmata da ciwonta saudaya mukamukinta ya tayarmata da ciwo,kuma data shafa CONFO bai dauki lokaci ba ya saki. lokacin data dauki kwana shadaya a washegarin ranar waadin komawar ta asibiti game da ciwonta ya cika duk da barunta tarasa hikimar dazata fadamasa fita saboda taji aranta idan babu kofar dazasui nishadin jima'i to batun zuwa asibiti zai iya bada kofar dazasu kara tsanar junansu ita bazata iya hakura da batun ba haka bazata iya tsaga idonsa ta tambaye ba kawai saitakira hajiya suka gaisa taimata jajen jiki takuma sanya mata albarka.a ladabce ruma ta ce hajiya gobene nake ganin likita ko inyaya yushau yazo zaki tunamasa hajiya taji wani irin jiri na dibarta.lallai daliline kuma mara dadi zaisa mace ta biyo ta wata hanyar dan sanar da mijinta wani batu,alhalin tare dashi take kwana take tashi.bakin hajiya na rawa ta ce meyasa bazaki sanar masa ba? ruma tai dariya wanda hajiya taji kamar ta kunya ta ce wallahi hajiya narasa da hikimar da zanfada masane ba zan iya ba dan ALLAH kifadamasa. hajiya ta cemata to harma yazo yatafi amma zan masa waya waiko satinda wuce kinje ganin likita da gashin fuskarki kuwa? a sanyaye ta amsa a.a to meyasa? tafada adan fada ce.ruma tai shuru kintambaye shine ya hana? ta ce a.a bantambayeshi ba amma zandi ga tambayar sa. hajiya tai shuru tana tunani tajima da sanin ruma akan kawaicinta bata yinsa cikin abinda ya zama dole sai idan anfi karfinta saitaimata nasiha akan cewa tafi kowa kusanci da mijin ta. ta ce zankiyaye hajiya kitaimin addua cikin tausayamata hajiya ta ce ALLAH yaimiki albarka. da yamma yushau yadawo gida kamar yadda ya saba ya kulle dakinsa yadan huta yai wanka yana shirin fita hidar abinci wajen ruma sai ga hajiya takira shi a waya kana lissafe da cewa gobe ruma zata ganin likita ko? oh fuskarta ko? da wannan tunanin na shi go gida yanzu mts!ina ganin ma zamu sauya asibiti...kada ka cemin bakwa zuwa gashin fuskar ni akan sikilarta nake magana yaji wani bakin ciki da takaici ya rufeshi. . Dan Aunty. GORAN DUMA (P 29) . . kai tsaye dakin ruma ya nufa yana kwankwansawa ta bude a ladabce tai masa sannuda zuwa tanakokarin ta fito,amma sai ya tureta kadan ya wuce falon nata, ta bisa da kallo,har saida ya zauna.jiki a sanyaye..takara gaidashi haka yake ta kallonta bako kyafta ido itakuma saita buge da wasa da yatsun hannunta tsoro duk ya cikamata zuciya saida yagaji da kallonta zuciyar sa kuma tadan sassauta kunan laifin dayake ganin tamai. kawo min abinci.asanyaye ta mike tare da mamaki aranta.tamike harta wuce baidorar da abinda zuciyar sa take rayawa game da ita ba ammadai abine yasani shine sanyin jikinta, ya dauki hankalinsa yadade da sanin ruma kasaitacciyace ta nunawa gaban sarki,.amma baita ba kula da sanyin jikinta ba,in ma matantakarta takeson nunawa tabbas taci wasan dankuwa ta nunu. Ya ce mata abinda kikemin na tabbata baki taba ganinsa gurin alhji ko hajiya bako? ta ce menaimaka? ya ce tunda kikazo gidan nan na taba fita kin min .adawo lfya? ko indawo kimim sannu da zuwa? abincima saina roka balle insaka ran zaki zubamin ko ki zauna gabana inacin abinci ina kallanki. tagama cika damamaki da wannan tsabar karfin hali natake laifinkai.da abokin mayar da maganarta ne sai itama ta tambaye shi KATABAGANIN ALHJI KO DADY YA FITA BA TARE DA SANIN MATAR SABA? IDAN YADAWO BATA KUSA SAI YA NEMO TA WATAKILA SHIYASA TAKE ZAMA A GABANSA YA CI ABINCI,KO BA .HAKA BA. todake bazata iya fadi infada dashi ba saitaja bakinta ta kulle ta ce to ni menake dashi daza a kallah.? yajima yana kallanta tare da murmushi a fuskar sa..meyasa kika watsar da korafina na farko kika za bi amsa ta karshe kikaimasa sharhi? ba watsarwa naiba,abinda nadauka kawai shine rashin sabo ne.murmushi kamar a mafarki ya tausasa murya ya ce kuma bakyaso musaba ko? Nayimamaki ace waike dakanki bazaki iya min maganar zuwa asibiti ba saikin sanarma hajiya,kuma kisan da wuya , na fahimcima ke gabadaya wannan fuskartaki bata damunki.niko bakiji yadda nake tausayinki akanta ba, tai shuru..danko maganar tausayin ce ruma bazata daUKeta ba. yana tausayintane zata kwana go ma sha a gidansa amma baita ba yimata ko sannu akan ciwan ba. badan ransa yasoba washegari yakaita asibiti tagama yadawo da ita ya tafi Sabgoginsa. haka dai suka ciga ba da zama .duk dare adakinta ya ke cin abinci.haka zaita takalo hira ita kam amsawar atakai ce dukkansu sai suke wa kansu kallan girman kai shiyanaganin dan bai isa bane tanashare shi.itakuma tanaganinsa a mai daukar dala ba gammo na kwanciya yasami soyayyar mace da mulkinsa daya saba shikenan sai suka zarce a cinaka in ci nawa , watansu guda ta fara shi ga matsalolinta na yau fari gobe baki.amma baisan tanayiba saboda rashin kulawa.agida idan tawayi gari da ciwo kamar yadda ka'ida yake,zata garzaya asibiti amma agidan yushau babu wannan dantawayi gari taga idanta yazama dorawa daya daga cikin alamar tashin ciwanta kenan.haka tai shirin zuwa asibiti da zumar zuwa tanajin motsinsa taje suka gaisa tafadi matsalarta amma sai yaki daukar hakan da mahimmanci.saiya ce ba wani abubane shawara ce zantaho miki magani baiko saurareta ba yai gaba saida tai kuka musamman ma data tunada auwal tun ma kafin yasan ita sikila ce. akwai lokacin dayazo ya taradda idanta yai hakan cikin tsananin kulawa ya ce ya kyautu kije asibiti wannan sauyawar idan naki ya wuce a ce shawara ce tadanyi murmushi batare da ta tankaba.ya ce inbabu damuwa muje inkaiki asibiti.tacemasa babu matsala gobe zanje asibiti akwai magungunan danake sha.watakila kafin goben makaga idon ya washe kaitsaye ya cemata mekika sha ta ce ina zuba glucose a cikin ruwan dazansha,inyawaita shan ruwa,da rake..ALLAH ya sauwake. dan bawan ALLAH washegarin dazai dawo sai gashi da gwangwanin glocuse,biyar da yankakkun rake Auwal ALLAH YAJIKANKA.. tare da kokarin yanke tunaninta.dan tana tuna asarar data tafka na rashin auwal. haka ta hakura ta zauna ta tilasta wa kanta shan ruwa bako glucose din a ciki. dan wanda tazo dashidin yakare da dare sai gashi da tulin magunguna shawara iri iri.dan takaici tana karba tai kitchen ta watsa su friege tadawo hannunta nadukan cinya taizaune tana karatun jaridar aminiya. yana gamawawda abincinsa ya cemata da anayiwa na miji kishiya da sai ince ko kukan ina da kishiyoyi jaridun nan ko kunya bakyaji kullum ni ina zaune ke kina karatun jaridun nan Yushau ya ce ina magungunan naga kin aje ko ciwan be dameki bane? ransa yai mugun baci,itama ta hadiye duk wani bacin rai ta ce masa irin wadannan magungunan da matsala a jinina na gazawa wajen tace abinci shine dalilin taruwar abinda kagani a idona.innasha illah zaimin. ya cemata amma kinsan hakane kika barni na siyo? batare data dubeshi ba ta amsa baka bani damar naimaka bayani ba kana yanke hukunci kai tafiyarka.hakane ammadai bayan natafi kya kirani ki gayamin.taimurmushi kawai ya ce mata ruma kinki sakin jikinki dani ko?bansan yadda kike kallan hukuncin ALLAH a tsakaninmu ba. a zuciyarta ta ce yakasa gane matakin datake dauka haka ta kasa gane abinda yake nufi a yanzu.a farin sanin dataimasa ba bu dadin baki ko agidansu a tsakaninsu dalilin kirkirar su a yanzu kuma takasa gano danya amfanetane.hawayen ta ne yai dalilin baro nasa mazaunin zuwa inda take idan wani laifi nake miki sai ki gayamin wata irin rudewa da kidima yau ya bayyana atare da ita yau ita ce a jikin wani namiji wanin ma yushau? sai tarasa inda zata tsoma ranta,a kidime ta ce ba bu wani laifi in ma akwai nayafe yushau baidamu da kidimewarta ba saiya kamo hannunta yana murzawa Da yawan lokuta ciwanta na tashi.amma idan yushau yakai kololuwar nuna kulawar sa kawai ya ce mata ruma daurewa zakiyi dayawan mutane inzasu samii gado da likita kwanciya zasui,nikaina nan bakiji yadda nake fama da abu kaza ba..... . Ina yiwa en uwa barka da shan ruwa, Allah Ya amsa ibadun mu da addu'oin mu na khairi baki daya. Allah Ya sa muna daga cikin bayin da aka enta su xuwa Aljannah, Aamiin. Dan Aunty GORAN DUMA (P 30) . . nikaina nan bakiji yadda nake fama da abu kaza ba..... hakan shine kadai furucinsa. watansu biyu da aure hajiya takawo musu ziyara ganin yadda ruma tai muguwar rama kuma takara kasalancewa saboda gigitar ayyuka ba yan ta ko ma gida da yushau ya zo taimasa magana kan yanema wa ruma yar aiki, ransa yai mugun ba ci saiya tattaro korafinsa yayo gida da niyyar karewa akan ruma Tunda haushin ruma yakeji ko kallan dakinta baiyi ba itakam aranar ta wuni zazzabi.ammadake tasan uzurin ciwo agurin yushau ba uzuribane haka ta daddage tai abinci jalof din taliya da lemon kwakwa ta ri ga ta aje abincin adakinta dataji shuru saita kaddara ya hadiyotane saboda haka ta kokarta ta kwashi kayan abincin ta bishi dashi. ya fito wanka ta gaidashi ya amsa fuska ba ya bo ba fallasa suna zaune shuru har yayi rabin plate sannan yadaga kai ya dubeta yanzu dan ALLAH ruma mene ne abin wahala a irin wannan girkin sai 'yan wanke kwanuka da aka ci.? tai shuru tana kallansa kirjinta na bugawa ta ce masa meyafaru? cikin gatsali ya cemata kinfini sani.kuma niba wannan yadameni ba.wai duk lokacindakike son wani abu saikin hadani da hajiya? kodake kinsan ba bu gaskiya a batun in samo miki 'yar aiki ina kudan yake balle romonsa? dan ALLAH ina aikin yake a gidan nan bare a nemo wata mai hidima mamaki da takaici ya ishe ruma amma dake jaruma ce sam fuskarta bata nuna ba.kamar cikin jimami ta ce dashi kaga kuma bani naimata maganarba.rannan datazo ta tarar banida lafiya ina aikin gida a wahalce watakila wannan ya sanyata hasashen samo mai aikin amma bani nasa ta ba yaya yushau. kunya taso takamashi amma dake sarkin ki fadine.sai ya maza yai fuska. Ya ce mata babu wata mai aiki da za asamo kodan saboda dalilai biyu,kisami damar mike kafa,shawara takara samun gurin zama a jikinki,ko kuma kici gaba da mike kafa kina abinda na tsana.wato karatun jarida ta hadiye ciwan maganar sa cikin sanyin murya tace to naji abar maganar. haka ta kwashe kwanukan taje ta kwanta gashi jikinta da zazzabi,ga sanyin iskar fankar dake kadata gashi ba dama taRAGE DAN Yushau mutum ne mai matukar jin zafi shiyasa yake kallon nata gudun iskar a matsayin wata tsirfa yana shan lemon kwakwa ya dubeta meyasa baki yi lemun shinkafar nan ba yafi wannan dadi.? murmushin yake kawai tai aranta ta ce yushau komai kai baka burgeshi ranar datai na shinkafar ma cewa yai wannan menene marabansa da kunun zaki.? ya cemata akwai nama dana shi go dashi kiyima farfesu. tai shuru tana tausayawa kanta yushau baisan yakamata da kawaici ba. yaya yushau wallahi inafama da zazzabi, kadan min uzuri zuwa gobe. baiko dubeta ba ya wuce yana cewa aidaurewa zakiyi, bari nakawo miki PANADOL karfi da yaji kin mayar da kanki 'yar kwaya..yakawo mata tare da ruwa tasha tanufi kitchen tafara aikin.dan yanzu ruma talura indai tana son lallai sai yushau ya damu da lalurartane to ranta yadunga baci kenan.... gab da sallar magarib ta kammala yushau yashigo kichen din da shirin zuwa masallaci. Har kingama ya shigo yafara dauraye kwanunka yana kifewa..yana cewa laulayinki idan aka biyemasa sam baza a morekiba..tai shuru bata tanka ba tana ta numfarfashi har tagama wanke wanken dayaga shurunta yayi yawa yasa yakai hannu wuyanta yaji zafin zazzabin cikin jimami ya ce zazzabin yakaru ruma sannu.kawai saitaji kwalla na zuwamata amma haka ta daure tahana kwallar fitowa can sai gashi ya shigo da maganin boska ya mikamata yana cewa maza balla biyu kisha yanzu zakiji zazzabin ya sauka.ta amsa ta aje gefe ta cemasa na cemaka banashan magani kaitsaye batare da umarnin likita ba sai kilu tajawo min bau idan nai ganganci. ALLAH yasauwake ya ce sannan ya koma kan abincinsa itakuma tashi ge dakinta yana cin nama tunaninsa nakanta kullum mace babu lfya da aurensa amma yana hada kafada da gwauro duk yadda yake da bukata sai dai bukatun subi ruwa sai lokacin barci ya shiga dakin ya tadda tai barci yataba wuyanta yaji haryanzu da dumi ya dinga shafa kanta har saida tafarka... duk abinda zai saukar da zazzabin kin koreshi, kiyi wanka da ruwan sanyi kinki,kisha boska kinki,yanzu dankinsha sau daya sai wani abu yafaru? itakam takasa magana sai yarike mata hannu yana matsamata zuwa kafada .tasan dukkan manufar sa saboda haka takawad da kai cikin bata fuska. haka yadafa ruwa ya tilasta mata wanka dashi. data fito wanka zazzabin yadan sauka.hakan kuma ya bama yushau damar ji da ita.iyakar yadda yaso wanda ko mai cikakkiyar lfya ce zataji a jikinta.yahau barcinsa ya barta da mayar da numfashi adaidai. hakadai suka ci gaba da zama wanda yushau saiyana da bukata yake lallabarta tare da tattalinta.har kullum ruma kukanta bai wuce naganin zata kare rayuwarta cikin Rashin 'yanci dasafe ruma tatashi. da matsanancin ciwan baya hartakai saidai yushau yaimusu karin kummalo amma ya bar na ruma a kichen. yasame ta adaki kidaure kitashi ga abincinki can akitchen kidanci kisha magani ninatafi kasuwa haka ruma tadaure duk wani bacin rai tace masa adawo lfya. kogama ficewa gidan baiyi ba tarushe da kuka..tunda ta auri yushau ko saudaya bata taba zuwa taronsu na sikila ba kwatsam tawayi gari da zaton tana da ciki saboda rashinganin aladarta. . Eh uwa barkan ku da sallah, da fatan ana shan shagali da hidiman sallah lafiya, Allah Ya amshi ibadun mu Ya maimaita mana, Aamiin sannan barka da sallah na, ban daukewa kowa ba ina jira ehe.. Dan Aunty. GORAN DUMA (P 31) . . Ruma tai kuka hartagaji kamar ranta zaifita.dan ta tabbatar a yadda yushau ke tafiyar da ita,lallai rayuwarta na cikin hatsari domin mace in sikila ce a duk lokacinda tasami ciki tun cikin na na wata biyu zata kasance karkashin kulawar likita duk bayan sati biyu har zuwa watannin sannan tako ma antenatal. wajibine ba bu ita ba bu aikace-aikacen masu nauyi da yawa kuma wajibine ta haihu gaban likita saboda matsaloli barkatai musamman game da jini Duk wad'annan dokokin suna nufin gata, ita kuwa ta san bata dashi, Yusha'u ba mutum ne mai fahimta ba duk yadda ake fahimtar da shi ba a sauya masa ra'ayi da fassara. Har cikin ya yi wata biyu tana cikin halin kuka da damuwa ta kasa sanar da kowa, mafita a wajenta ita ce ta sanar da Hajiya, amma idan ta tuna jan idon da Yusha'u ya ke idan Hajiya ta yi masa wani Umarni bisa tunaninta a kanta, ya kan zo ya yi ta zabga mata gori da goruba, to ina ga yanzu ta sanar da ita. Da ta rasa mafita kawai sai ta yiwa Innarta waya cikin kuka ta sanar da ita tare da neman shawararta. Hankalin Mahaifiyarta ya yi mugun tashi duk da dama a tashen yake kasancewar duk 'karshen wata sai ta ziyarci Rumaisa'u, kuma ganin da ta ke mata tana tabbatarwa Rumasau ba ta cikin kwanciyar hankali da 'koshin lafiya. Cike da 6acin rai Mummy ta ce. "Ni dama na san sai auren Yushe'u ya cutar da mu, Yusha'u mutum ne mai mugun girman kai, babu wanda ya iya sai shi". Rumasa'u ta kasa cewa komai sai shesshekar kuka, dan ta san gaskiya Innarta ta fada. Momi ta yi dogon tunani, sannan ta ce. "Ki kwantar da hankalinki, zan same shi a waya". Rumasa'u ta tsayar da shesshekar kukanta tare da fadin. "A'a Momi ki ba ni shawarar yadda zan fahimtar da shi, ba na son ya yi ta tuhumata da maganar ina kai 'kararsa...." Ita ma Momin ta tare da fadin. "Dole hakuri zaki yi ki bar ni na yi masa magana, Yusha'u na da raina mutane ko ni din ma ba lallai in yi nasarar ya ji maganata ba amma dai na san duk tsiya zan fi ki, tunda zan iya bibiyarsa idan na nemi ba'asi idan ya 'ki abin da na ce". Rumasa'u na cikin fargaba, amma dai dole haka ta yarda da batun Momi suka yi sallama kowa rai babu dad'i. Yusha'u na kasuwa wajen azahar Momi ta yi masa waya, cikin zaton faruwar wani abu ya daga wayar dan sanin da ya yi Momi ba ta kiransa a irin wannan lokacin. Ta fi kiransa da daddare ko da safe lokutan da ta tabbatar yana gida. Ya gaishe ta cikin ladabi da ci-da-zuci, ita kuma ba ta ja masa rai ba ta fadi abin da ke tafe da ita. "Cikin Rumasa'u ya cika watannni biyu ko? Ya wajaba lallai ku je asibiti ka san sickler mai ciki preterm labor ce, watau kullum tamkar cikin na'kuda take. Dole sai da kulawar likita zata raini cikin dan ceto ranta da na abin da ke cikinta". Ya ji maganar banbarakwai wai namiji da suna Hajara, dan shi dai bai ma san Rumasa'u na da ciki ba, kuma bai iya boyewa ba ya ce wa Momin. "Ni walllahi ban ma san tana da ciki ba". Ba tare da ba wa maganarsa muhimmanci ba Momi ta ce. "Allah Sarki, ka san Rumasa'u da kunya, ni kaina ba dan akwai wannan dalilin ba na tabbatar ba zata sanar da ni ba. To don Allah ina rokon arziki kar ka yi wasa da lafiyarrta ku je asibiti a shirya mata fayil, kuma abi dokokin likita". A sanyaye ya ce mata. "Babu komai, in Allah Ya so za a yi, Allah Ya inganta, Ya sauke ta lafiya". Momi ta amsa, "Amin". Sannan suka yi sallama. Ya wuni da abubuwa biyu, tsabar murnar cikin Rumasa'u saboda dokin samun magaji, da kuma takaicin yadda Rumasa'u ke yawan hada shi da iyayensu. Da ya dawo gida da yamma ya jima a dakinsa Rumaisa'u ba ta shigo ba, saboda haka ya sameta a dakinta, sai ya tarar da ita a bandaki tana kwara amai, dole ya sassauta 6acin ransa ya yi tsaye a bakin kofa yana mata sannu, har ta gama aman, ta gyara wajen ta wanke baki sannan ta wuce firji ta ciko tambulan da ruwa ta zuba glucose ta shanye sannan ta dawo ta zauna yana bin ta da kallon da ya sanya ta tsarguwa shi yasa ta kasa hada ido da shi, shi kuma ya 'ki tanka mata. Can ta mi'ke ta kawo masa lemo da fura sannan ta koro masa bayani. "Don Allah ka yi hakuri yaya Yusha'u, wallahi na sha ciwon 'kafa dazu shi yasa ban sami sararin yin abincin ba". Ya jima cikkin shiru sannan ta tsinka bayan ya tsiyayi leman ya sha. "Ya ya zan yi Rumasa'u, tururuwa ta yi jidon banza ma ballantana ranar garar 'yarta". Tana 'kila wa 'kalan fahimtar inda maganarsa ta dosa duk da ko ta fahimta din ba ta da kalmar amsa masa dan haka ta kyale kanta da damuwa da sai ta fahimta. Sai da ya gama shan furar sannan ya dubeta da kyau, ya ce. "Yanzu tsakani da Allah Rumaisa'u kina dauke da cikina in rasa arzikin ki sanar da ni? Duk lamurana ba kya daukarsau da muhimmanci idan ba wandanda ba ki 'kudurta kai ni 'kara wajen mahaifanmu ba". Ta yi shiru 'kirjinta sai bugawa yake saboda tsoro, bakinta sai rawa yake ta kasa samo hanyar kare kai saboda haka shi kuma ya sami sararin fitar da dukkan zargin da zuciyarsa ta sa'ka masa. "Tun kafin auren nan fargabar a ta dame ni ke nan, ni na san zurfin iliminki ba zai barki daukata wata tsiya ba bare ki kimanta ni, duk wani abu na ha'k'kina ko naki kina ganin na yi tsororo ki cika min shi ko ki gabatar min. Babu wani abin arziki da nake tsinta a wajenki sai na 'korafi da kaiwa iyayenmu magana... Takardar jarida ko mujallarki ta fi ni kima da daraja..." Yanzu kwallar da ta taru a idonta ta fara saukowa, cikinta kuma ta dago ta dubi Yusha'u murya a raunane ta tare shi. "Wallahi Yaya Yusha'u ban ta6a kai 'korafinka ko 'kararka ba, wannan kuma da na fadawa Momi ba 6ata ka nake nufin yi ba, kawai dai na yi tunanin ita zata fi iya fahimtar da kai matakin da za a iya dauka a kaina. Yadda aurenmu ya zo bagatatan ne duk ya janyo wannan matsalar, tun kafin mu yi aure ya kamata ka san yadda rainon cikina zai kasance..." Ya tare ta a zafafe. "Karki sauya min magana ko ki yi min gori Rumasa'u, yadda aurenmu ya zo ni ban ta6a daukarsa wani daban da yadda ya kamata aurena ya kasance ba, Allah ne Ya za6a min ke ban kuma yi butulci ba na kar6a, na ri'ke ki da iyakar adalcin da zan iya. Duk wani abu daban sai dai in a wajenki ya ke, ba kuma a baibi kike ba ni yadda na kabari ya fi ni daraja a wajenki ba..." Sai ta bude baki cikin tashin hankali tana dubansa, kuka ya dinga fizgirta, amma ita ma ta dinga hadiye shi, a karshe cikin rawar murya ta ce. "Yaya Yusha'u me nake yi na zafi haka?".... Dan Aunty. GORAN DUMA (P 32) . . Ya tsare ta da ido, ya ce. "Tsakaninki da Allah idan Auwal ne za ki zauna da cikinsa tsawon wata biyu ba ki sanar da shi ya yi farin ciki ba?" Takaici da rauni ya cikata, dan haka ta saka masa ido ta kasa tanka masa. Ya ce. "Ki amsa min mana!" Ta girgiza kai tana dubansa kai tsaye da alama ya fara 'kure ta. Ta ce masa. "Idan na amsa wata'kila kai tsaye ka yiwa amsar tawa kallon wautacciya, in daga zuciyata kai tsaye amsa zata fito." Cikin gadara ya ce. "Idan ma a haukace zata fito ina jiranta. Na kuma tabbatar ba zata sauya daga yadda na zace ta ba". Hawayen idonta ya fara gangarowa, tana kallonsa kai tsaye ta ce. "In da Auwal ne ba zan kai tsawon wata biyu da ciki ba tare da ya binciko da kansa da kansa ba, cikin wata biyun nan wanne irin amai ne bana yi, wanne irin zazza6i ne ba na yi, wacce irin kasala ce bana yi? Yaya Yusha'u duk sanda zan gabatar maka da wadannan matsaloli 'kar'kari ka ce min ok Sannu, Allah Ya sauwa'ke sai ka ga na galaibata ne kake kawo min maganin shawara, ko kuma tarkacen magunguna daga kyamis... Saboda haka ne sam ba ni da 'karfin gwiwar sanar maka da wani abu da ya dangance ni..." Rumaisa'u bata kula ba ne, tuni Yusha'u ya zo wuya taf! Tana direwa kuma ya fara zubar da bala'in da ya 'kunshe. "Ka ji ba! Rumasa'u ni kike fadawa wannan maganganun saboda rashin ladabi ko? Saboda tsabar ke butulu ce wacce irin kulawa ce bana yi miki? Duk namiji ne zai jure wannan jarabar laulayin naki amma ina iyakacin kokarina kina nuna min na gaza, kuma saboda tsabar raini ki keta idona ki nuna Auwal ya fi ni matsayi a gurinki?... Dadin abin ya gama yi miki nisa, duk yadda kike jin fitsara dai ba zaki dauko gawarsa ki gina mata daki a cikin gidan nan ki ce kishiya ne shi ba...." Bai ko saurareta ba fuuu! Ya fice ya bar dakin sai ya bar ta da binsa da kallo, lokaci guda kuma hawayenta ya dauke saboda maimaita kalmar KISHIYATA da Yusha'u ya ambata tare da tuno yadda Auwal yake ambaton kalmar da KISHIYI. Kusan sati guda Yusha'u na gaba da Rumaisa'u, ba gabar magana ba har da na dauke hannu a shigo mata da abubuwan masarufi dangin ciye-ciyen kayan gina jiki, kaza, balangu, kifi da kayan itaciya, ''Inko hakane gwara ya daina fita. Don ni ban ga amfanin dukiyar da iyalina ba zasu amfaneta ba'' wadanda su kadai ne ba ta rasa ba a abin da ya kamata kada sickler ya rasa su, saboda haka 'kan- jikinta ya 'karu, ga nata na asali ga na raunin ciki sannan ga na 6acin rai. Suka sake share wasu sati biyun a haka, bayan muguwar rama yanzu ta fara d'ashewa alamun jini ya yi mata 'karanci, babu ciwo dai sosai, sai yawan kwanciya da bin sanyi wanda shi ma alamu ne na 'karancin jini a jikin sickler. A karo na hudu da Innarta ta kirata dan ta ji batun zuwansu asibiti, sai ta fada mata gaskiya don 'karya ta kan fada mata cewa 'mun je', yau cikin kuka sai ta fada mata. "Wallahi Momi ko soron 'kofar gida ban taka da sunan asibiti ba, a halin yanzu kuma ina cikin wani hali dan ina ganin alamomin rashin jini... Amma don Allah Momi mu nemi wata shawarar kar ki yiwa Yaya Yusha'u magana, tuhumata yake da kai 'kararsa." Momi ta rasa abin da zata ce saboda mugun takaici, kawai sai ta ja numfashi ta ce. "Shikenan, ba ni awa daya na yi tunani zan kira ki". Ba ta ko jira cewar Rumasa'u ba ta kashe wayar, kai tsaye kuma ta kira Yusha'u cikin tsananin fushi, ko gaisuwarsa ba ta amsa ba, ta ce. "Yusha'u ka tuna na ta6a fada maka cewa, ina da juriya akan komai amma ban da akan Rumasa'u? Zan iya yi maka kawaici akan komai amma ban da na wasa da ranta, mun shiga sati na uku a maganar da na yi maka ba ku nemi hanyar asibiti ba, yanzu da na tuntubeta ta tabbatar min tana tare da alamomin 'karancin jini. Wallahi Yusha'u ba zan iya zuba ido ka yi min sanadin Rumasa'u ba..." Muryarsa a tausashe, amma maganarsa zazzafa dan cewa ya yi. "Ai babu mai iya kashe wani sai Allah!" A fusace Momi ta ce masa. "Au haka ka ce? Shikenan Allah Ya kaimu gobe ni kuma zan zo in nuna iyawata akan hanawa ka zama silar Rumaisa'u, in ma ka 6oye manufar shirya kasheta ne saboda an aura maka ita bisa tilas ni zan yi maka gatan rabaka da aurenta..." Ba ta ko jira cewarsa ba ta kashe wayar, nan take ya hada gumi kashir6an dan ya san Momi ba wa'ka take ba, zazzafar mace ce shigen mahaifinsa. Tsab zata zo kuma ta dauke Rumaisa'u dole kuma maganar ta je kunnen mahaifinsa, wanda zai iya mummunar sa6a masa. Bai yi dogon nazari ba ya hau kiran Momi tana 'kin amsa kiran nasa, shi kuma ya nace cikin tsabar dakan zuciya, amma yana mita. "Mahaifin Rumasa'u ya zama hoto, dama yawancin masu d'amarar nan matansu ke juya su, haba me za a yi da auren 'yar mace?" Ire-iren mitar da ya dinga yi ke nan yana nacin kiran wayar Momi, kusan sau ashirin sannan ta daure ta daga. A ladabce ya ce. "Don Allah Momi ki yi hakuri, wallahi za a yi yau din nan ba zamu kwanta ba sai an je asibiti, na rantse miki". Ta sauke hucin 6acin rai, sannan cikin lumana ta ce. "Yusha'u ka yi tunani da kyau, bai kamata sai an yi yun'kurin gwada maka 'karfi zaka tausaya wa 'yar uwarka ka yi mata abin da ya kamata ba, ko babu igiyar aurenka akan Rumaisa'u ai abar ka tausaya mata ce, yanzu ta ce min jininta ya yi 'kasa sosai, idan aka sake nan da kwana biyu, sai dai ka ji batun yi mata 'karin jini". Cikin 'kas'kantar da murya ya ce. "In Allah Ya so ba za akai wannan matakin ba Momi, ki yi hakuri". Cikin sakewar Murya ta ce."To na yi, Allah Ya yi muku albarka". Da ya koma gida da yamma, Rumasa'u ta kawo masa abinci a dakinsa sai ya dinga satar kallonta. Ta yi mugun ramewa, sannan ta yi wani irin fari, idanunta kuma sun yi wani 6ulu-6ulu sun kukkunbura. Ta zauna jim amma kafin ya 'karasa cin abincin sai ta tashi ta koma dakinta ta kwanta, yanzu babu abin da yake mata dad'i sai kwanciya, hatta dan karance-karancen jaridu da mujallun da ta ke samun yi a da yanzu gagararta yake, duk da ma dai Mubarak me daukar nauyin kawo mata jaridun jarabawa ta 6oye shi. A haka ta jiyo motsin shigowar Yusha'u, haka kawai sai ta ji gabanta na faduwa dan ta ha'ki'kance da kyar idan ba gadar mata da wani takaicin ya kawo shi ba. Sai dai ya shigo dakin cikin sakin fuska ya nemi stool ya zauna idonsa a kanta, ta dan dube shi da kyau sannan ta lumshe ido. Ya yanke shirunsa da cewa. "Kwanciyarki ta yi yawa, ko yaushe ke kenan a akwance". Ta bude ido ta dube shi, amma ta kasa cewa da shi komai. Ya sauke numfashi ya ce. "Jaridancinki dai a gidan aurenki da mijin aurenki kike sauke shi. A zamanmu dad'i da wahalarmu gaba daya babu na sirri kunnen iyayenmu da 'kawaye kaiconki Rumaisa'u, wallahi ba ki morre hali ba..." . Dan Aunty.GORAN DUMA (P 33) , , Ta kokarta ta tashi zaune ba tare da ta shirya ba ta ji kuka ya kwace mata babu kakkautawa, yana kallonta zuru yana dokin ta yi shiru har kukan nata ya fara ta6a ransa, babu shiri ya cimmata ya fara rarrashi. "Ki yi hakuri ni ban fada dan cin fuskarki ba, na fada ne dan ki ankara da laifi da cutarwar da ki ke min fisabilillahi ina mutunci a ce duk sirrin gidanmu a kunnen Hajiya, Momi da sauran dangi da 'kawaye..." Ta dakatar da shi cikin kuka. "Ba gudun cin fuska ya ba ni kuka ba Yaya Yusha'u, illa mummunar shaidar da ka yi min a matsayinka na mijina har kana tir da halina.... rayuwar nan ba ta da garanti musamman ta mutum irina... Idan Allah Ya kar6i raina yanzu wannan shaidar 'kila ta yi tasiri a kaina... Dole in yi kuka dan ban san yadda zan gyara ka yarda da ni ba". Ya 'kara tausasa murya ya ce. "Ki daina kai 'karata gurin Momi ko Hajiya, ki dinga 6oye sirrin gidanmu ba fa jahila ba ce ke Rumasa'u, kin sani yana daga nagatar mace 6oye sirrin mijinta..." Ta jima tana kallonsa cikin hawaye, sannan ta kwace kafadarta ta koma ta kwanta alamar ta ma rasa abin da zata ce. Ya yi saurin dagota ya ce. "Babu abin da zaki ce?" Yana rufe baki ta amsa. "Idan in ce dan in kare kaina ne ba zan ce din ba, dan kar mu ci gaba da 6atawa juna lokaci, amma zan iya cewar da zata iya zame maka wani nauyi a ayyukanka biyu na duniya da lahira cewar tawa ita ce, duk matsananin halin da zan shiga kuma duk yadda Momi zata kwakkwafe ni ta ji matsalata ba zan kuma fada mata ba, in ka kula da ni kanka Yaya Yusha'u, in ka yi sakacin da na rasa raina sai ka shirya amsa tambaya wajen Ubangiji fa'kat!" Yusha'u ya yi wuri-wuri ya rasa abin da zai ce mata, sai da kyar ya lalubo shi. "Abin da kika fadawa Momi ke nan ina sakaci da ranki? Amma sam ba ki yi min adalci ba Rumaisa'u". Ta goge hawayenta duk da wasu sun kuma kunnonwa, ta dube shi ta ce. "Kana dai so sai na kare kaina ko? To ka san dai mutum ba zai rayu ba sai da jini? Dube ni". Ta shiga gwale idonta fatar ba'kinta tare da nuna masa tafukan hannayenta, sannan ta dora. "Jinina ya yi 'kasa sosai, da ko ba ni da ciki dab nake da shiga mawuyacin halin da zai kai ni matsayin 'karin jini. An yi maka batun fa'idar zuwana asibiti tun sayi biyu da suka wuce ba ka dauki batun da muhimmanci ba, ban yi tsammanin zai zama laifi ba dan Momi ta binciki halin da nake ciki na sanar mata ina da matsalar rashin jini, ko babu komai ya fi sama ta ka a ce musu ga ni kwance ana 'kara min jini... ko su zo su bayar da jini a 'kara min". Da ya rasa bakin magana sai ya fanshe akan kalamanta na 'karshe. "Lokacin da ba ki karkashin ikona ma na ba ki jini Rumasa'u bare ki yi min gori... in leda goma ne zan iya baki ba leda daya ko biyu ba". Yana rufe baki ta amsa masa. "Rigafi ai ya fi magani". Ya ce, "Me kike nufi?" Ta amsa masa, "Ka yi tattalina kar na rasa jini ya fi burgewa akan ka bar ni na rasa ka bayar da leda goma a 'kara min". Yanzu ya rasa abin da zai ce mata bilha'k'ki, sai ya 6uge da duban agogo lokacin da aka rera kiran sallar magriba, ya wuce kai tsaye batare da ya kare kansa ba. Abin mamaki ba ya 'karewa a duniya, karfe tara na dare Yusha'u ya shigo mata da Dan'Isiya mai kyamis a nan unguwarsu dauke da akwatin magunguna da allurai. Dan Isiya ya tsare ta da lacca da hudubobi bayan ya gama karade ta da tambayoyin da ake wa sababbin zuwa awon haihuwa, mata masu lafiya ba sicklers ba. Kallonsa kawai ta ke kamar wani duron ya'kin neman za6e, wani lokacin kuma ta sauke ganinta akan Yusha'u wanda ya hakimce shi a dole ya yi abin arzi'ki. A karshe Dan Isiya ya ce, tun da cikin bai kai ko wata uku ba ba sai an yi awo ba, yanzu zai dauki jininta ya tafi da shi lab. gobe zai kuma yi mata allura yanzu sannan ya bata magunguna musamman na 'karin jini. Duk Rumaisa'u na kallonsa bambarakwai har ya fito da sirinji ya zu'ki jininta, sai da ya zu'ko allurar da zai mata ne sannan ta magantu. "Tun safe ban ci abinci ba bai kamata a yi min allura ba, zai fi kyau a bari sai gobe". Dan Isiya ya mayar da ruwan allura cikin kwalba yana cewa. "Eh gaskiya ne, in Allah Ya kaimu goben sai na zo na yi miki". Yusha'u kuma ya ce. Amma kina kallonsa ya zu'ko? To ya zauna ya jira kici abincin mana ya yi miki..." Ta girgiza kai ba tare da ta dube shi ba, ta ce. "Nidai sai gobe". Dole ya kyale ta, ya mayar da hankali ga Dan Isiya da ke zube masa magunguna yana masa bayaninsu. Yusha'u ya ce. Ina fatan akwai na 'karin jini?" "Akwai". Yusha'u ya ce masa. "Yauwa, ka hada mata da maganin kasala da na 'karfin jiki ba ta da aiki sai kwanciya". Nan ma Dan Isiya ya ce. "Duk akwai". Ya dure musu magunguna tuli a leda ya mi'kawa Yusha'u, shi kuma ya mikawa Rumasa'u ya wuce raka Dan Isiya. Ya dawo mata da gasasshen nama da nonon roba mai sanyi. Da kansa ya nemi faranti a kicin ya zuba naman ya kawo ruwa da lemo ya zube, sannan ya ce mata. "Ki zo ki ci ki samu ki sha magani". Tun da ta ga 6arin jikin da ya ke ta san ba na Allah da Annabi ba ne, tattalin raya darensa kawai yake, dan haka ta zage ta yiwa naman cin 'koshi cikin 6oye 6acin zuciya, dan ta san idan ma ba ta taimaki kanta ta ci ba babu abin da Yusha'u zai raga mata, gara ma ta kori yunwa ko ta rage wa kanta wahala. Har ta gama cin naman da fargabar abubuwa biyu, wato yadda zata ji jiki a shimfidarsu da kuma yadda zata gujewa shan wadannan magungunan da wata 'kila in ta sha su yi ajalinta. Bayan ta gama ya dauke farantan da tarkacen kayan da ta sha lemo da yagot, sannan ya dawo ya janyo ruwa ya janyo ruwa ya tsiyaya mata a tambulan kana ya janyo ledar magunguna ya fara 6alla. Kijrinta sai dakan uku-uku ya ke ta dube shi ta ce. "Yaya Yusha'u har na gaji da gaya maka ba na shan maganin da duk ba likita ne ya rubuta min ba". Ya tsayar da 6allo maganin sororo yana kallonta, cikin hadiye bacin rai ya ce. "Da yake nan ya ba ki wadannan magungunan? Dauko miki shi da na yi har gida bai zama garkuwar da zaki zarge ni da shi ba musan abin da muke ba?" Ta girgiza kai a raunane, tace. "Likita daban mai kyamis daban Yaya Yusha'u, in ya san abin da yake yi na tabbatar ba lallai ya san yadda ya kamata tafiyar da sickler ba...." Ya tare ta da alamar rarrashi, Rumaisa'u bata zargi karya ba, ya yi kewarta yana kuma son ya fanshe a yau, dan haka ya 'ki su yi fada, ya ce mata. "Tun da kin iya karatu kin kuma san kan magungunan me yasa ba zaki dube su ki gani idan ya yi miki ganganci ba?" Tun da an ce Mutum ba ya 'kin ta mutane, ta mika hannu ta kar6i magungunan na farko da ta dago sai ta tarar capsil ne na 'karin jini. Ta daga maganin tana duban Yusha'u fuskarta cike da takaici ta ce. "Daga inda ya dauki maganin karin jini ya ba ni na san bai san aikinsa ba..." Yusha'u ya tareta cikin tsabar mamaki. "Amma dai ke kika ce kina da 'karancin jini ko?" Ta amsa masa cikin sabawa da takaici. . Abbas Abdulkadir Hada Hada ( Dan Aunty.) GORAN DUMA (P 34) . . Ta amsa masa cikin sabawa da takaici. "Ba zan iya 'kirga sau nawa na yi 'karancin jini daga haihuwata zuwa yau ba, amma ko sau daya likita bai ta6a ba ni maganin 'karin jini ba, sickler ba ya bu'katar maganin 'karin jini, domin cikin kowanne irin maganin yana dauke da sinadarin Iron, su kuma sicklers suka sha maganin 'karin jini to jininsu zai daskare kamar gasara, abin da zai faru da su kuma Allah ne kadai zai iya faru da su kuma Allah ne kadai zai iya iyakance shi". Yusha'u ya yi shiru kawai yana kallonta, ba wai bai yarda a ita ba, amma in ya bi ta kamar ya fadi, sai dai dole faduwar zai yi, dan a yanzu rashin dabara ne ya jagula mata rai, sai ya daure kamar wani soko ya ce. "Shikenan sai ki duba sauran". Ta mayar da maganin 'karin jini cikin ledar, tana cewa. "Ka yi hakuri Yaya Yusha'u, babu maganin da zan iya sha a ciki, in na sha na jefa rayuwata cikin hatsari". Yanzu Yusha'u ya kasa hadiye 6acin ransa, dan har ga Allah yana ganin Rumasa'u amfani ta ke da zurfin iliminta tana nuna masa iyakarsa, komai ya yi bai iya ba dan tsabar rainin hankali ita da ta karanci jarida wai ita ce zata kushe wanda ya karanci lafiya. Ta kushe wannan ta kushe wancan komai cikin gadara kamar wata uwar mutane. Ya yi kokari ya rage zafin 6acin ransa a muryarsa, ya ce mata. "Amma dai idan kin yi min haka ba ki yi min adalci ba, kawai dan ki nunawa duniya kina iko dani, kina kallo in kawo mutumin duk ba ki musa ba sai bayan tafiyarsa ki ce ba kya son aikin in mayar masa da magungunansa? Wannan ai ya yi kama da wulakanci..." Ta katse shi a sanyaye. "Yaya Yusha'u idan na katse hanzarinka a gabansa shi ne wulakanci, gara in bari ya tafi muyi komai mu biyu... wai ma don Allah Yaya Yusha'u har sau nawa zan fada maka ba na shan magani kai tsaye? Tsawon zama a gidanku ka ta6a ganina a kyamis...?" Shi ma ya tare da tsawa. "Ban sani ba! Ni dai kin wulakanta ni, abin da nake ta gudu ke nan, duk mai zurfin karatu ta 'kalubalanci mijinta, ta yi jayayya da shi, ko ta raina masa azanci sunnarta ce, kamar ni ma ban ta6a allin nan ba.... Haba! Ban da kaddara me zai kai ni? Ba gara ma mutum ya tafi kauye ya auro ba". In dai da sabo ya kamata Rumaisa'u ta saba da wannan gori da cin fuskar, duk kuma 6igiren son zuciya da rashin gaskiya. Tun kafin abin ya yi tsawo ai ta mi'ke ta bar masa falon ba tare da ta ce ci-kanka ba, ta shiga bandaki ta wanke baki, sannan ta bi lafiyar gado tana addu'ar Allah Ya sa ma ya yi zuciya ya tafi dakinsa ta huta. Sai dai addu'ar tata ba ta kar6u ba, dan ko mintuna ashirin ba ta yi da kwanciya ba ya shigo ya sauya kayan kwanciya, ya zauna bakin gado ya ce mata. "Yanzu ya ya kike so a yi?" Ta dan zura masa ido sannan ta ce. "Da me?" Ya ce, "Da maganar 'karancin jinin bana son a kai ga maganar sai an 'kara miki jini". Ta yi murmushin gajiya da abu daya, ta ce. "Idan ba zan yi laifi ba kuma ba zai zama umarni na ba ka ba, asibiti ya kamata na je gobe". Ya janye mata abin rufa ya fara murza tafin kafarta yana cewa. "To ya ya zan yi? Ai kawai na zama mijin ta ce sam-sam ba na yi miki kwarjini. In Allah Ya kaimu gobe sai mu je asibitin." Ta janye kafarta tana 'karamar dariya. "Allah Ya kai mu goben. Yanzu sai ka tashi ka tafi dakinka..." Ya tare ta lokacin da ya fara nade su cikin bargon. "Haba yarinya kin ma isa, ai rashin kwanjin nawa bai kai nan ba". Da sapiyar ranar sai ya nemi hanzarin cewa na manta yau akwai ni da zuwa rogo, satin da ya wuce Alh yayi min maganar kaddamar da wata rijiya da yake a waya ne bai min cikakken bayani ba, sai naje naji, ki bari idan na dawo da yamma sai muje asibitin, ta kada kai da sauri cikin bugun zuciya , rijiyar Awwal ce ta kuma tabbatar idan Yushau ya jiyo gaskiyar maganar Allah ne kadai ya san yadda zai tashi hankalinsu. Saboda haka ta wuni cikin zullumi da tashin hankali gami da pargaba, lallai kuwa' yushau ya shigo gida karpe goma na dare puskar nan tasa kamar an saukar masa sakon mutuwa ko hutawa baiyi ba ya para surparta da bala'i irin wanda bai taba yi mata kamar sa ba, tun tana kokarin kare kanta har ta zubo masa ido tana kallo cike da tsabar bakin ciki a tsukun wannan lokacin da za a kawo mata tayin mutuwa babu abin da zai hana ta amsa, sai sha daya da kusan rabi ya hakura ya tapi dakin sa yana ta mita, wai don me tana auren sa tana auren soyayyar wani har da irin wadannan sadaukarwar da ya rantse kuma ko kwatar abin da tayiwa Awwal shi bazata iya yi masa ba, lokacin da yake bala'in idon Rumaisau a kekeshe yake babu alamun kuka saboda masipar bacin rai, sai bayan pitarsa ta samu kukan ya goce mata, ta dinga yi babu kakkautawa dan ta hakkake duk rashinsa ya jepata cikin wadannan masipun auren Yushau ke wa sila. Da akwai Awwal kila da yanzu tana daga cikin matan da za a lissapa su a sahun parko na jin dadi da sa'ar miji, amma yanzu ratuwarta da lapiyarta na wani hali na tsaka mai wuya, wajen karpe biyun dare ta nupi dakin kwana saboda jin numpashinta na shakewa, da zummar tilasta kanta bacci dan ta manta wadannan bacin ran ko dan kai lapiyarta ta sami nakasu. Sai dai da alama ta makara dan numpashinta yaci gaba da shakewa lokaci daya kuma cikinta yayi wani irin juyawa tape da ciwo sai ga damshi-damshi ta sami kanta a ciki, nan da nan ta para ambaton Innalillahi wa inna ilaihi raji- un . Ta san lallai tana cikin tsaka mai wiya, bari zatayi, zata bubar da jini alhali dama bai ishe ta ba, ta barke da kuka ta isa bandaki kamar dama ana jiran ta shiga bandalin ne jini ya balle , tun tana tararradin rasa gudan jininta (wato danta) har ta dawo pargabar tsira da ran ta, saboda yadda xiwon ciki ya addabe ta ,jini kuma yaki tsayawa har numpashinta na neman daukewa. Da rarrape ta sawo dakinta ta janyo waya sai ta rasa ma wanda zata buga ta sanarwa , ko yushau bai gargade ta sanar da iyayen su halin da take ciki ba, ita kuma tai alkawarin ko zata mutu ba zata kuma sanar da su din ba. To idan ta kira wani a yanzu ta pada masa wannan mummunan labarin sai sun tuhumi ina yushauu ? Ko wacce irin laya za a yi musu sai sun parke. Numpaninta na kokarin kubucewa ta dinga kiran yushau yana kallon kiran yana sharewa, kusan sau goma sai da kyar ya daga cikin tsaki sai dai a wannan lokacin ta para pita hayyacinta sai ta kasa magana illa wata irin sheshsheka,,,, nan da nan yushau ya dawo cikin azancinsa da gudu ya watsar da wayar ya doshi dakinta ya same ta kwance gaban gado cikin jini a sume. Halin da ya same ta shi kansa ba dan yana jar zuciya ba kila ya sume cikin tsabar rikita da barin jiki ya dago ta yana padin na shiga uku zan kashe yar mutane,babu bata lokaci ya janyo durowa ya dauki ID card dinta na shaidar kasancewarta sikila da gudu ya pice ya pita da mota, sannan ya dawo ya dauke ta ya nupi asibitin nasarawa, da yake akwai group din jininta a jikin Id card dinta ba a tsaya jiran diban na yushau ba aka makala mata wani. Har azahar na washegarin ranar Rumasa'u tana cikin wani hali na kasa gane kai, Yusha'u ya yi nadamar abin da ya yi matu'ka, musamman da ya sami tabbacin cikin Rumasa'u ya zube, hannun agogonsa ya koma baya a matsayinsa na mai dokin ganin dan kai. Tun sha biyun rana Mummy ta sauka cike da tashin hankali wanda ta yiwa Yusha'u kallon tsana a fakaice ba, babu wanda ya san tana yi idan ka dauke shi Yusha'u. Da azahar da suka sami damar shiga dakin kowa cikin jimami, Hajiya da iyalanta kaf in ka dauke Mubarak da tilas ya je makaranta, ga Alhaji ga Mummyn Rumasa'u tare da Balaraba. Ko zama Mummy ta kasa yi tana tsaye rungume da hannnu ta 'kurawa ledar jinin da ake 'karawa Rumasa ido, idon Mummy ya fara fitar da kwalla saboda tsabar tausayin 'yarta. Ta ji a ranta akwai sakaci cikin hatsarin da ya faru da 'yarta, sakacin da ta tabbata ba 'karshensa ke nan ba, za a kuma wani dan Yusha'u mutum ne mai taurin kai da wasa da al'amura cikinsu har da rai. An dai gaya mata silar hatsarin daga bakin Hajia iya ma kamar yadda Yusha'u ya fada mata cewa. "Ana dan zafi, ita kuma kin san ba a kunna mata fanka, sai na ce ta tafi dakinta ni ina son kunna fanka. Ina bacci kwatsam ta kira ni a waya na ji muryarta cikin wani hali kafin na 'karasa dakin na tarar da ita a sume." Sam Momi ta kasa gamsuwa da wannan fatawar. Ranta kuma ya yi mugun 6acin da ta ke jin lallai sai ta bude kwanji a kan 'yarta in ba haka ba Yusha'u zai yi mata sanadinta ko da yake cuta ba mutuwa ba ce, amma zai iya yiwuwa ta 'kare rayuwarta cikin wahala saboda rashin kulawa. Idonta cike da kwalla ta sauke ganinta a kan Yusha'u da ke zaune kan kujerar da ke gaban gadon Rumaisa'u, ta ce masa. "Yusha'u me ya faru ne wannan tsausayin ya afku?" Yusha'u ya kasa hada ido da ita, ya kwaso in'ina. "Wallahi Mummy... Muna kwance ta tashi ta.... shiga bandaki kawai ta fara kwala min kira kafin na farga ta fadi a nan wajen..." Hajiya da su Atika suka ware ido suna kallonsa, tun daga nan jikin Hajiya ya yi sanyi ta tabbatar akwai wani abu da Yusha'u ke 6oye wa tunda har ya yi baki biyu haka, Alhaji ma ya dan kalli Hajiya ya basar cikinsu babu wanda ya tanka. Mummy ta 'kara tayar da ganinta sosai akan Yusha'u, ta ce. "Shin kun je asibiti kuwa kamar yadda na ro'ki alfarmarka a waya?" Nan ya shiga kame-kame cike da borin kunya. "Ranar ban koma gida akan kari ba. Jiya kuma mun je bikin bude rijiyar nan... Damadai yau na ke shirin ta je asibitin..." Alhaji da takaici da fargaba ya fara kaiwa bango ya tare shi ta hanyar shiga maganar ya cewa Mummy. "Wai me yake faruwa da kika sanshi kina Abuja mu ba mu sani ba?" Kai tsaye cikin raunin murya ta fada masa. "Lokacin da cikinta ya yi wata biyu ta kira ni ta fafa min, amma da sigar neman shawarar yadda za a yi ta je asibiti kasancewar sickler kullum cikin na'kuda suke, na ce ta sanar da mijinta da kanta, sai ta nuna min tana jin nauyi. Ni na kira Yusha'u a waya na fada masa, na kuma sanar da shi dukkan hatsarin da ke tattare da rashin zuwanta asibiti ya amsa min za a je, amma har tsawon sati kusan uku ba a je asibitin ba. Rannan na kirata ina bincikar lafiyarta, sai tana kuka ta sanar min a halin yanzu ma jininta ya yi 'karanci. Na kuma kiran Yusha'u na gargade shi. Yau kwana uku ke nan jiya kwana biyu wannan hatsarin ya faru, Yusha'u bai nemi asibiti ba ni ban san wanne irin sakaci ba ne wannan". . To zamu shiga hutun sallah daga yau, sai kuma bayan sati biyu. Dan Aunty.GORAN DUMA (P 35) . . Ran kowa a dakin ya 6aci, musamman Alhaji da Hajiya, Alhaji ya yi kwafa cike da takaici da 'kunar rai kamar ya hadiye zuciya, ya ce. "Sakaci ko ganganci, 'kila so ya ke ya kasheta tunda na aura masa ita bisa tilas". Dannewa kawai Mummy ta yi ta amsa cikin sanyin murya. "Alhaji maganar duk ba ta yi zafin haka ba, amma dan kyautawa gaskiya Yusha'u ba ka kyauta ba. Ba a kan wannan lamarin ba Yusha'u na sha sanar da kai irin hatsarin da yarinyar nan ke ciki, dan na yi wasa da hankalinka ba zan dinga fada maka 'karya ba. Yarinyar nan na bukatar taimako ba na komai ba na taya ta kiwon kar ciwonta ya tashi. Ko ba 'yar uwarka ba ce ba kuma matarka ba ce ai ka yi mata taimakon musulunci, wanda ya hori musulmai da taikamon juna da yaye damuwar juna". SABODA tsabar takaici Yusha'u kasa magana ya yi, sai ya yi kwafa kawai ya kawar da kai, Hajiya ce ma ta cika shi da kallon tuhuma, Hafsat kuma take satar harararsa, dan ita kadai ta san wanne irin zama Yusha'u ya ke da Rumasa'u, gidan Rumaisa'u gidan zuwanta ne kwarai da gaske, tana kallon rashin shakuwar dake tsakaninsu tana kuma kallon yadda Rumasa'u ta ke fama da dawainiyar aiki tana da lafiya ko ba ta da ita, shi babu abin da ya shafe shi. Bayan wannan ta kula da jarabar ma'kon da Yusha'u ke yi ko a wajen abinci da kayan masarufi ballantana a sami Rumasa'u da kudi, bare a yi batun ta bugi kirji ta kai kanta asibiti. Yusha'u bai ta6a tsanar auren Rumasa'u irin yau ba. Ya fahimci Rumaisa'u ake so ta mallake shi ta dinga shimfida masa doka ba, a'a danginta ma so ake suna daga nesa su za su dinga tsara masa yadda zai yi a gidansa, shi yake hakuri da Rumasa'u ta ke juya shi son rai, ya ke hakuri da masifar laulayinta, ya ke hakuri da ita ya ke mata adalci alhalin ya san ba shi ne cikin zuciyarta ba. Duk wadannan manyan aibu ne ya ke jurewa sun kuma isa ya ci fuskar Rumasa'u a kansu, amma bai ci din ba ya ke kawar da kai amma duk da haka ana nuna gazawarsa, ba a dangin Rumasa'i ba ba kuma a nasa dangin ba. Wannan abu da yawa yake mutuwa ta je kasuwa! Rumaisa'u ta yi kwana biyar a asibiti aka mayar da ita gidan Hajiya, ta yi sati uku a can ta warware sosai ta kuma murmure kamar ba ta yi cuta ba. Sannan aka mayar da ita gidanta bayan Alhaji ya wanke Yusha'u tas da nasiha da gori, ya nuna masa lallai Yusha'u na shirin ba su kunya a wajen iyayen Rumasa'u, kunyar da ta fi tun karfo ya tubure ya ce ba zai auri 'yarsu ba. Zaman ya sauya salo da wata irin rayuwa mara dadin labari, Yusha'u ya bude kofar zuwa asibiti da kashi saba'in cikin dari sai dai shigen je-ka-na-yi- ka, wato ba ya bayar da kwabonsa zuwa asibiti bare a kai batun siyo magani, ya kuma toshe dukkan kofar da zata iya tambayarsa saboda tsabar gizagonsa ya camfa Rumasa'u ta raina shi, kuma matakin da zai iya dauka a kanta shi ne ya toshe kofofin rainin ta daina ganin hakoransa a waje balle ta nemi kawo masa wargi. Ai kuwa sai ya kwana bakwai Rumaisa'u ba ta ga hakorinsa da sunan dariya ba, babu doguwar hira sai dai numfarfashi da bayar da umarni, in ta debo masa dogon batu sai ya numfasa da kyar ya ce mata, "To". Ko kuma, "Na ji". Gaba daya rayuwar Rumaisa'u ta kuntata, jikinta babu dadi, zuciyarta babu dadi sai gaba daya gidan ya zame mata kamar kurkuku, duk da tana iyakar kokarinta wajen ganin ta ribato Yusha'u. Cikin haka ta kuma wayar gari da ciki bayan watanni uku da komawarta gidan. Wannan karon ta yi jan namijin tuknararsa da maganar cikin tun kafin ya cika watanni biyun. "Allah Ya inganta, Ya raba lafiya. Ina fatan za a yi min hanzarin mu wayi gari lafiya kafin mu je asibiti?" Abin da ya fada mata ke nan cikin rashin walwala ba tare da ya dubi idonta ba. Sai dai fa yana neman shayar da ita mamaki, dan yanzu ya 'kara sauya taku na mayar da ita aljihun baya, kuma ba a bakin komai ba, sannan yanzu kullum ya dawo kasuwa zai fesa wanka da sabon dinki ya feshe jiki da turrare ya cife kullm cikin sabon dinki da daure fuska ya ke, sai kuma ya kai goma na dare har zuwwa sha daya a waje babu halin ta nemi ba'asi yanzu sai abin ya zame musu rigima, domin kuwa sai ya hau kanta da bala'i. "KO KE da nake da ikon in hana ki fita ban sami wannan sararin ba bare ni da duk lalacewa ba ke kike ciyar da ni ba balle ki iya saka wa 'kafata kwado". Ba'kar magana a tsakaninsu ta zama abin adon da kamar alfajari Yusha'u yake idan yana ya6a mata, komai na laifi da korafi ne, duk kuwa yadda ta zage masa da kyautatawa kullum bakin cikinsa ta ke hadiya tana korawa da ruwan hakuri, amma tamkar zuga shi ake yana 'kara gadara da izza tare da munana mata. Rannan ya dawo gida karfe goma kamar yadda ya saba, da sauri ta cimmasa a dakinsa ta yi kwalliya kamar 'yar tsana, amma bai ko yarda ya 'kare mata kallo ba, sai wani kawar da kai yake yana hura hanci. Ta yi masa sannu da zuwa ta gaishe shi, sannan ta ce. "Wanka zaka fara ko in kawo maka abinci?" Ya yi kicin-kicin ya daure fuska ya ce. "Wannan wacce irin tambayar rowa ce Rumasa'u?" Ta dan dube shi a sanyaye ta kawar da kai, ta kasa cewa komai, shi kuma ya ci gaba da mita. "Ina jin haushin tambayar nan da kike min kullum! Ki kawo min mana idan ba na bukata ba sai na barshi ba?" Ta jima kanta a sunkuye, sannan ta yi murmushin takaici ta ce. "Allah Ya ba ka hakuri". Jiki a sa6ule ta wuce ta kawo masa abincin sannan ta nemi guri ta zauna har ya gaji da hararar abincin sannan ya zauna ya fara ci. Ita kuma ta ci gaba da satar kallonsa tana tuna yadda suka yi rannan. Ya dawo da yamma ya fito da kudi yana kirgawa ta kawo masa abinci, kawai sai ya hau ta da masifa. "Wallahi matsi ne ba na so. An gaya miki babu abin da na zo yi duniya sai cin abinci? Ke babu arzikin da zaki yiwa mutum sai dai ki yi ta tura masa abinci?" Idon ta rau-rau ta ce. "Yaya Yusha'u kamar me zan yi maka yanzu? Ka dawo na yi maka sannu da zuwa, na kawo maka ruwa kai da ka fita tun safe sai in kasa kawo maka abinci? Haba Yaya Yusha'u!" Ya kara tarar numfashinta a 'kufule. "Amma dai lissafi kika tarar ina yi ko? Idan abin kirki ne sai ki zauna ki taya ni ba wai ki yi ta tura min abinci ba". Ta dube shi da kwallarta ta ce. "Ka tuna ranar da ina hada kayan wankinka na ciro kudi a aljihunka na ajiye maka ka zo kana tuhumata da cewa, ba su ke nan ba? Har kana min gargadin kar na 'kara ta6a maka kudi?" A nan sai ya yi zugudi, kuma da yake uwarsa ba ta rasuwa ita kadai sai ya yi fuska ya ce. "Ni ba na son 'kullaci". Dan haka yanzu da ya yi mata maganar rowa ke sa ta yi masa tayin abinci ya sa ta tsaya tana ta faman satar kallonsa, shi dai wanda ke 'kinka babu abin da za ka yi ka iyar masa. Zuciyarta ta 'kara rauni da ta kula da yadda yake ta faman muzurai kamar mai zaune da mayya, kawai sai ta ji hawaye ya su6uce mata, can ma sai shesshekar kuka. Ya dago ya dubeta cikin muguwar 'kufula, ya ji ransa ya yi mugun 6aci dan babu abin da ya kaddara shi ne, ta tuno marigayi Auwal. Ya jima yana mata kallon tuhuma me kuma ya tuna? Oho! Sai ya sauke kai murya a sar'ke ya ce. "Haka Allah Ya 'kaddaro min, Alhaji kuma ya jaza min, ina aurenki zuciyarki na auren wani ko? Hmm MUTUM DA ZUCIYARSA ko? Ba zan gaji da gaya wa Allah neman Ya bi min ha'k'kina ba". Ta tsayar da kuka ta zuba masa ido kamar numfashinta zai dauke saboda takaici ta motsa baki da niyyar magana sai kuma ta hadiye abarta ta yi 'kasa da kai tana girgizawa. Sai kuma ya sha jinin jikinsa ya dan kafa mata ido, sannan ya ta6e baki ya ce. "Ki fadi duk abinda ranki ya raya miki, kar ki 'kullace ni. Abin da na fada gaskiya ce idan kina da wadda zata tankwa6e ta ba sai ki kawo ba, in ma rashin kunyar da kika saba za ki yi min ai ba wani saban ba ace a gurina ki yi iyakar son ranki ran da na kawo wadda zata bi ni sai 'kila ta zame miki darasi" . Allah sarki Ruma. Mata Allah Ya raba ku da na miji irin Yushau, Aamiin. . Dan Aunty GORAN DUMA (P 36) . . Ta hadiye dun'kullallen ba'kin cikin da ya tokare mata a 'kirji, da murmushin 'karfin Hali ta ce. "Ba na tuna Auwal a hurimin muzguna maka Yaya Yusha'u, domin ban aure ka ta silar so ko kuma ta dole ba, na aure ka ne dan na yi bautar aure wato bautar Allah, saboda haka ban ta6a hada zaman gidanka da wani 'kyalli ba. Halin da na sami kaina a cikin gidanka da irin ri'kon da kake min wani nufi ne daga ubangiji. Yadda kake nuna munin halina da kasawata a cikin rikon da nake maka Allah Shi ne shaidata ina kuma ro'konSa kafin Ya dau raina ya nuna maka 'kir'kirarmin munin hali kawai ka yi ba dan ya cancance ni ba. Sai dai duk yadda na ke da 'karfin halin tsayar da zuciyata a kanka kar na tuna baya in wuya ba na kasa tuna Auwal tunda MUTUM DA ZUCIYARSA bashi da iko da ita, sai dai ina ro'kona wata alfarma, ko ma dai menene, Auwal ya mutu babu komai tsakanina da shi, sai fatan alkhairi. Ina ro'kon ka janye shi daga cikin al'amuranmu, mu muka saura a duniyar muke taka irin rawar da muke so a cikinta, kuma ha'ki'katan ta ishe mu riga da wando...." Cikin kuka ta tashi ta bar masa dakinsa, in da ta bar shi da shanya baki yana kallon wajen da ta tashi. Ya yi niyyar ya share ta, amma da ya tuno tashin hankalin da suka yi har ta kai ga 6ari sai ya sauya shawara, ya gaggauta shiryawa ya sameta a dakinta. Hankalinsa ya dan kwanta da ya same ta ba cikin kuka ba kamar yadda ya yi zato, sai ya same ta a zaune bakin gado tana murza confo a gwiwar hannu tana cije le6e, akwai alamun hannun ne ya motsa. Ya zauna kan sofa yana binta da kallo fuskarsa babu yabo babu fallasa. Ya jima yana shan 'kamshi kafin ya taro abin da zai ce. "Ki yi hakuri na daina sako Auwal a lamuranmu, amma magana ta gaskiya ba zan ta6a lamintar..." Ta yi saurin dakatar da shi cikn muryarta da ke sha'kewa saboda son fashewa da kuka da kuma alamun zafin ciwo. "Yaya Yusha'u ka taimake ni ka tashi ka koma dakinka ciwon hannuna ya kori ciwon da zuciyata ke ji saboda takaicin da kake 'kunsa mata. Bai kamata ka biyo ni ka kuma daga min hankali ba, in dai baka dokantu da na bar maka duniyar a yanzu ba" Bai yi mamakin yadda ta ke magana cikin fada ba. A sanin da ya yi mata in dai tana ciwon hannu ko 'kafa ya ta6ota harshenta kan yi kaifi a wadannan lokutan, Allah basshi idan ta warke sai ta ba shi hakuri ta ce zafin ciwo ne. Sai ya yi shiru ya tsaya yana kallonta, ta ci gaba da mur'kususu tana 'kugi, nan da nan ta hada gumi sharkaf! Dole zuciyar musulunci ta sanya shi zuwa ya ri'keta yana mata sannu yana ta faman shafa mata confo a hannun. Sun fi awa daya suna abu daya, ba ita ba ba shi kansa sai da ya yi muguwar jigata saboda ri'kon da ta ke masa. Ya tambayeta ta sha magungunanta na kullum? Ta nuna ba ta sha ba, ya nemi ya bata sai wajen karfe daya ta samu runtsawa a cinyarsa ta barshi da sa'ke-sa'ke da 'kare mata kallo, har ta kai shi ga lissafin tsawon lokacin rabonsu da kusantar juna kamar haka, lissafin kuma da ya tuna masa kishinta har ya kai ga farkar da ita. Amma Rumaisa'u 'yar halak duk da gajiya da baccin da ya cika mata ido ba ta 'ki amsa tayinsa ba. Sai dai tir! Lokacin da ya fara gigicewa sai ya ke ambaton sunan wasu mata. "Sumayya, Sumoli, Ummi". Tuni ta kwaci kanta da ambaton. "Lahaula wala 'kuwata illa billah". Ta barke da kuka lokacin da ta tattaro bargo ta tashi zaune. Ya bi ta da kallo cikin fuskar mamaki ya ce. "Kan ki daya Rumasa'u, lafiya kike?" Ta ci gaba da kuka cikin tsare shi da ido, sannan ta kattse shi cikin shesshekar kuka, ta ce. "Abin da ka yi yau ba ka da sanin yana daga nau'in zina? Wace ce Sumayya, Sumoli, Ummi? Mene ne hukuncin kawo mana su a shimfida?" Zuciyar Yusha'u ta yi wani mugun bugu da ya fahimci abin da yake rayawa ya fito fili, amma da yake ya iya fargar jaji, sai yayi fuffukar borin kunya. "Kin ga malama bana son sharri, wacce mace na sani bayan ke? Kawai ki ce min kin zaci kowa ma irinki ne da kike suffanta ni da na kabari...." Ta toshe baki ta tashi tsaye cikin tsananin tashin hankali tana kallonsa. Da sauri ta juya ta shiga bandaki ta turo 'kofa ta fashe da kuka. * Bakwai safiya bata cika ba, Yusha'u ya silale ya buga mota ya bar gidan inda ya doshi gidansu kai tsaye. Ya kamata ya ture shakka ya bude kwanjinsa dan yin abin da yake so ba wanda ake so masa ba, wanda ya dace da shi ba wanda aka datar masa ba. Kai gara ma ya tunkari Alhaji kai tsaye ya sanar da shi zai yi aure tun kafin kwa6arsa ta zaureye tunda a yanzu dai ta fara ruwa. "Alhaji ina neman amincewarka ka yarje min na 'karo aure, ina da muradin hakan sannan na kamu da son wata yarinya, bugu da 'kari auren zai taimake ni ya taimaki Rumaisa'u a matsayinta na mai yawan larura ba ta ko iya daukar nauye-nauyen kanta balle ta dauki na wani". Ran Alhaji ya 6aci gaya, sai dai ya hadiye shi a ciki. Ya yiwa Yusha'u wani kallon wulakanci ya ce. "Cikin dalilai ukun da ka gabatar min wanne ne kake jin ya fi gamsar da kai na lallai ka yi aure?" Cikin karfin hali Yusha'u ya ce. "Duk Alhaji ina son in 'kara auren, ina son yarinyar, sannan dan in taimaki ita Rumasa'u" Nan da nan Alhaji ya ci mur, ya tare shi. "Ni karya ce ba na so, kawai dai kana muradin ka yi aure yanzu ne ka sami matar da kake so ba wadda ake so maka ba, kar ka 'kara sako Rumasa'u a cikin dalilanka". Yusha'u ya dauko buhun rantsuwa ya fara saukewa, Alhaji ya tare shi. "In ka rantse min zan iya kwada maka mari a banza a wofi Yusha'u, kana son taimakonta ka kasa nemar mata 'yar aiki? Hajiya ma ta yi zuciya ta kai muku 'yar aikin, ka ke neman korarta da mugun hali? Duk halin da kuke ciki ina sane Yusha'u zuba maka ido kawai na yi na ga iyakar gudun ruwanka, in gani shin da gaske kasheta kake shirin yi, ka sami sararin auro wata.....?" Yusha'u ya tari numfashin mahaifinsa da doguwar rantsuwa. "Na rantse da Allah Alhaji ba 'karamin hakuri nake da munanan halayen Rumasa'u ba...." "Kafin ya sauke huci Alhaji ya sharara masa wani bahagon mari, Yusha'u ya dafe kuncin, wani irin radadi ya isa har kwanyarsa ya hadu da bakin da zuciyarsa ta yi suka sabbaba masa zubar hawaye. Yaushe rabonsa da dorar da zafin duka gemai-gemai da shi? A dake shi akan matar da yake zaman laurara da ita? Sai ya ji ya 'kara tsanar Rumaisa'u, zuciyarsa ta 'ke'kashe, ya dubi mahaifin nasa cikin kwalla ya ce. "Alhaji ni na san matsalolin da nake shiga a cikin auren Rumaisa'u, idan dai ina da damar in auri wata bayanta to don Allah ka amince min auren nan..." . . Yushau dai dakikine inji wani a gidan nan, idan kuna so ku bani dama na sheke shi kamar yadda nayiwa Awwal kowa ya huta da bakin cikin sa... Abbas Abdulkadir Hada Hada (Dan Aunty) GORAN DUMA (P 37) . . Alhaji ya hadiye rud'anin da ya shiga cikin zafin murya ya ce. "Ba ka da damar! Ka tashi kuma ka bar min gida, sannan ina maka godiyar halaccin da ka yi min. Na aura maka Rumasa'u dan ka ji 'kanta ashe kai auren je- ka-na-ka ka yi da ita, kake zage 'karfinka da iyawarka kake muzguna mata dan ta gaji da kanta ta ce ba ta aurenka ta jure, sai kake son kinkimo aure dan ka nuna mana iyakarmu. Auren da kadan ya haure shekara daya kake shirin dan'kara mata kishiya? To ban laminta ba, in kuma ka ga na laminta to ciki aikinka ka yi ka sako min Rumaisa'i, fa'kat! Ka 6ace min da gani na gaji da ganin mummunar fuskarka". Yusha'u bai wami karfin gwiwar wucewa kasuwa ba saboda zafin zuciya, fushi, 6acin rai da radadin a fuskarsa ta ke. Ya shiga gidan shiru babu motsin Rumasa'u ko na talabijin dinta, sai Adama da ke kara-kainar aiki a kicin, ya yi tsaki 'kasa-'kasa ya wuce dakinsa cike da dokin Allah Ya kawo Rumasa'u ta ta'kalo shi ya sauke mata kwandon rashin kirki. Amma fiye da awaya biyu babu ita babu motsinta, ga yunwa na addabarsa saboda ko karyawa bai yi ba, ga ciwon kai da zafin mari ya sabbaba masa. Amman fiye da awa biyu babu ita babu motsinta, ga yunwa na addabarsa saboda ko karyawa bai yi ba, ga ciwon kai da zafin da marin ya sabbabasa masa. Da kyar ya lalla6a da azahar ya je sallah ya dawo ya kuma kwanciya yana sanyo idon shigowar Rumaisa'i. Da gangan ya dinga kaki da gyaran murya a tsakar gida dan ta san da zuwansa, amma har la'asar ba ta shigo ba. Bayan ya dawo sallar la'asar sai ya wuce dakinta kai tsaye cike da fushi. Ya same ta a zaune gaban sofa tana jinyar hannunta wanda ya yi ciwo jiya, yau ya kumbura suntum, da ya kalli fuskarta sai da gabansa ya fadi saboda yadda ta yi wata muguwar rama idonta kuwa ya jeme da kuka. Sai dai yana tuno yadda ya sha mari a kanta a wajen Alhaji sai ya ji kamar ma ya yi mata Allah Ya 'kara. Ya nemi guri bakin gado ya zauna ya dubeta fuskarsa a daure. "Ki tashi ki dafa min abin da zan ci yunwa na ke ji". Cikin wahalallen kallo ta dan tsura masa ido, muryarta a dashe. "Yau daya Yaya Yusha'u.... ina neman alfarmar ka ci abincin Adama, lallai ina takaicin kasa tashi in girka maka abinci. Ba zan iya ba Yaya Yusha'u, dubi hannuna ya dame ni da matsanancin ciwo kamar na cire shi na jefar..." Ya tareta cikin halin ko'in kula. "Wallahi ba zan ci girkin Adama ba, dole ki tashi ko abu mai sauki ki dafa min. Taliya ko ki soya min dankali da kwai, na ba ki minti talatin." Bai ko saurari hanzarinta ba ya fice ya barta. Dole ta mike tana kuka ta sami dankwali ta daura a wuya, ta tare hannunta ta nufi kicin. Ta dinga aiki da hannu daya cikin matsananciyar wahala da zubar da hawaye, in ciwo ya ishe ta ta tsaya ta yi mur'kususu da 'kugi har sai ya lafa sannan zata tashi ta ci gaba. Da yake jalob din taliya babu wahala ba ta dauki wani dogon lokaci ba ta gama, ta iske shi daki ta kai masa. Ya nuna mata firji. "Ki dauki fura ki dama min". Ta daure hawayen da ya cika mata ido tana duban hannunta ta ce. "Sai dai in da hannun hagu zan dama maka, kada furar ta samu matsala.... hannuna yana ciwo." Ya kawar da kai yana ta6e baki. "Yaushe za ki dama min fura da hannun hagu? Yanzu duk girkin nan da hannun hagu kika yi? Damun fura sai ya gagare ki....?" Da ta dan tsura masa ido ta ga ya soko maganganu a 'kasa sai ta fahimci shi kansa bai yarda da kansa ba. Ba ta ce masa komai ba dan haka ya kuma samun ta cewa. "Ina son in sha furar nan da gaske, ki lalla6a hannnun ki dama min..." Cikin 'kufula akan rashin tausayinsa ta tare shi da cewa. "Ba zan iya ba wallahi". Ya dago kai cike da haushi da 'kufula ya dube ta amma ba ta bashi sararin cewa wani abu ba, ta tashi ta bar masa falon. Wannan abin da ta yi ya 'kara 'kufular da shi. Ya fito zai je sallar magriba ta fito tsakar gida cikin hawaye ta tare shi. "Don Allah Yaya Yusha'u in ka yi sallar ka dawo ka kai ni asibiti..." "Ba zan iya ba wallahi". Ya tari numfashinta da irin furucin da ta yi masa dazu yana ta faman hura hanci. Cikin raunin murya ko zai tausaya mata ta ce. "Don Allah ka taimake ni Yaya Yusha'u". Ya yi gaba cikin fuffuka ba tare da ya tanka mata ba. Ta ce. "To na je ni kadai...?" Ya sake tare ta da fadin. "Allah Ya ba da sa'a". "To ba ni kudin magani". Ta fada cikin tsananin tausayin kanta. Ya fice abinsa yana cewa. "Ba ni da su". Kawai sai ta dur'kushe a wajen ta rushe da kuka ta jima tana yi sannnan ta koma daki tana kuka tana ambaton Allah, babu halin ko Hafsat ta kira a waya ta taimake ta saboda al'kawarin da ta yi na ba zata 'kara sanar da wani halin da ta ke ciki ba ko zata mutu. Har sha daya na dare tana cikin tashin hankali, sannan Yusha'u ya shigo amma shi da kansa ya san bai kyauta ba, tare kuma da tsoron 'kila Rumasa'u ta kira wani ta sanar da shi yadda suka yi, 'kila Alhaji ya la'ance shi, yana kuma cike da tsoron wannan dan rikicin da suka yi kar ya yi sanadin zubewar cikinta kamar yadda ya faru a cikinta na baya. Wadannan dalilan suka sa bayan ya gama shirin bacci ya doshi dakinta ya same ta cikin mawuyacin halinta. Girman kai da masifar haushinta da yake ji ya hana shi yi mata kulawar kirki, ya dai yi mata sannu, ya ajiye wayarsa kan durowa ya haye gado ya ja bargo. Rumaisa'u na zaune har sha biyu da rabi sannan ta samu hannunta ya rage zogi, zuciyarta kuma ta dau nata ciwon na zama da ma'kiyi wanda ba ya tausayin dan Adam, duk hawayen da ta ke a yanzu na wannan takaicin ne. Cikin haka ta ji take shigowar sa'ko a wayar Yusha'u, haka kawai ta ji ta cika da dokin ganin sa'kon. Ban da tana cikin halin ciwo wanda kan mantar da ita tuna wasu tunane-tunanen duniya babu yadda za a yi ta kasa lissafinta da Sumoli, Sumayya, Ummi. Duk lokacin da ciwo ya sake ta tunanin matan nan da ala'kar da ke tsakaninsu da mijinta ta ke. Cikin sand'a ta janyo wayarsa ta budo sa'kon cikin doki da dukan zuciya ta bud'a. 'Ya Habibi, wani mafarki na yi mai 'kayatarwa, mun yi nutso cikin burikanmu, mun tabbatar da mafarkanmu na mallakar juna. SUMOLINKA'. RUMAISA'U ta maimaita karanta sa'kon nan ya fi sau ashirin masa'ki, hade da kallon 'keyar Yusha'u da ya juya mata baya yana sharar baccinsa. Yanzu tunaninta ya fi tafiya juya maganganun sa'kon tare da misalta daga irin macen da ya kamata su fito. Sumoli! Sunan ya yi kama da na wadanda ba Hausawa ba 'kila kuma ba musulmai ba. To karuwa ce? Tana shakkar in karuwa ce dan Yusha'u ba shi da kamannin neman mata ko ta ina aka juya shi.... . . To da ganowa idon ta, shi yasa yanzu naji ance an daina yiwa mata padan komai idan za'ayi auren su sai padan ''kiyi hakuri, banda duban wayan sa' lol. Dan Aunty.GORAN DUMA (P 38) . . In Sumoli ba karuwa ba ce mecece? Ba ta ta6a kawo matar da Yusha'u zai nema da aure zata zo da irin wannan sunan ba bare a same ta da irin wadannan maganganu a tsakiyar dare haka! Abin ya daure mata kai matu'ka. Ana cikin haka sai ga lambar sa'kon ta kwado kira, Allah Ya sanya wayar a silent ta ke, kawai sai ta suri wayar ta yi falo, ta daga wayar ba tare da ta tanka ba. Sai mai kiran ce ta fara magana cikin yau'ki da sautin 'karamar dariya. "Yi hakuri na tashe ka bacci ko? Zuciyata ce ta kasa hutawa da begenka. Ka ga sa'kona? Wani mafarki mai dad'i na yi mana tunda na farka na kasa komawa....." Zuciyar Rumaisa'u ta dinga bugawa fat-fat! Hannunta ya dinga karkarwa ri'ke da wayar, amma da yake tana da dauriya sai ta amsa muryarta tar! "Ayya! Shi kam kin ga har ya fara jan rago, amma idan ya farka da safe zan sanar da shi". Ba ta jira cewar Sumoli ba ta kashe wayar ta zube a kujera cikin haki tamkar wadda ta yi gudun famfala'ik, abin da ya cunkushe mata numfashi ta ma rasa ta inda zata kwashi wannan 'kalubalen yadda zai zame mata maslaha. Da safe Yusha'u bai sami sararin fita kasuwa ba saboda kansa da ya matsa masa da ciwo. Da Adama ta iso kasancewar da safiya take zuwa, ta zauna har la'asar, yau da ta zo sai Rumasa'u ta sallame ta da cewa sai gobe yanzu zata je asibiti daga can kuma ta wuce gida sai dare zata dawo. Ta sami Yusha'u da maganar asibiti kamar jiya dai ya furje. "Ki dawo lafiya, ni ma ba lafiyar ce da ni ba in zan sami mai kai ni asibitin albarka zan sa masa". Ta yi murmushi kawai ta yi masa sallama ta fice duk da kuwa dari da hamsin ne a jakarta, ko cikakken kudin a daidaita sahu ba ta da su daga Sallari zuwa asibitin Nasarawa, ga shi safiya ce bare ta je banki ta fitar da kudi. Amma dai da yake gidan zafi yake mata sai ta jefa katin ATM dinta a jaka ta fito daga gidan ta kama tafiya a 'kafa zuwa titi ta sami adaidaita sahun da zai kai ta asibiti a kudin jakarta. Akwai tazara tsakaninta da titi saboda haka hutunta hudu a hanya, tana na hudun ne kan wata kwalbati kamar daga sama Hafsat ta tsayar da motarta kusa da ita tana matsa mata hon. Cikin farin ciki da goge gumi ta mi'ke ta nufi motar Hafsat ta bude mata cike da mamaki tana tambayarta. "Daga ina zuwa ina?" Bayan Rumaisa ta shiga motar ta daure cikin murmushin ya'ke tana cewa. "Daga gida zuwa asibiti, ke kuma daga ina kika fado mana da sassafe haka, ko ba gidana za ki ba?" Hafsat ta juya motar rabin hankalinta na kan Rumaisa ta ce. "Daga gida nake, jiya Mubarak ya sanar da ni ba ki ji dadi ba, da ke na kwana a raina shi yasa na doko miki wannan sammakon". Rumaisa ta yi murmushin jin dadi ta ce. "Kin kyauta wallahi, kin ceci rai, ina Sani da ya bari kika fito da safe haka?" Hafsat ta amsa mata tana dariya. "Ya fita shi ma, da dai ya kwaso min mita sai kuma ya mayar da ita gori, wai gara na dinga zuwa ina ganinki ko na yi zuciya in taya 'kokarinsa in karb'i baby". Rumaisa ta tayata da dariya ta ce. "Sani ba dai ba'a da zare-zaren magana ba". Hafsat ta murgina kai, ta ce. "Ai fa..... Hafsat ta murgina kai, ta ce. "Ai fa, me kike zaune kan waccan kwalbatin?" Cikin son a basar da maganar Rumaisa ta ce. "Hutawa nake, wai 'karfe nawa?" Hafsat ta dan kalleta da kyau sannan ta mayar da kallonta ga titi ta ce mata. "Tambayar da na so in miki kenan, da sanyin safiyar nan kika fito a yanayin jikinki kuma har da tafiyar 'kafa, ina Yaya Yusha'u?" Cikin hadiye 6acin rai Rumaisa tta ce. "Yana gida, kansa ne yake ciwo..." Da sauri hafsat ta tare ta. "Yadda har ba zai iya tu'ki ba kuma ba zai iya fitowa ya nemar miki adaidaita sahu ba?" Sai Rumaisa'u ta kasa amsawa, wannan ya sabbaba shiru a tsakaninsu, saboda kowa da abin da zuciyarsa ke sa'kawa. "Mu 6ulla ta zoo road ko zan samu fitar da kudi a Sahad". In ji Rumausa'u cikin rashin nutsuwa dan ta san fada kawai ta yi dan kar kai tsaye ta roki Hafsat kud'i, amma ta san yanzu ba zata iya fitar da kudi ba. Hafsat ta dan harareta ta ce. "Da wannan safiyar?" Rumasa'u ta yi shiru kawai, ita kuma Hafsat ta dora cikin zafin rai da 'kufula. "Mubarak ya fada min hannunki ke ciwo har ya fara kumbura, mu gani". Rumaisa'u ta janye hijabi cikin d'ar-dar ta nuna mata yadda hannun ya kumbura kamar yana dab da jan ruwa. Hawaye ya cika idon Hafsat ta janye ido tana cewa. "Yaya Yusha'u ya san haka hannunki ya yi?" Ita ma Rumaisa sai da ta goge kwalla saboda tuno yadda suka yi jiya akan girkin abinci da damun fura, sannan ta amsawa Hafsat. "Ya sani, na fada miki kansa ke ciwo". Hafsata ta sauke fushinta akan Rumaisa'u cikin zafin rai ta ce. "Wai Rumasa'u me yasa kike damuwa da kare azzalumi irin Yaya Yusha'u ne? Kina son wawantar da mutane game da yadda yake danne hakkinki. Ni kuma ban ga ribar da kike samu a kan haka ba... har gara ki bayar da 'kofar a kwato miki 'yanci idan ba haka ba yana dab da kai ki kabari..." Kuka ya su6ucewa Rumaisa'u cikin shessheka ta ce. "Ni wallahi da zan mutu ma sai ya fiye min, ni ban ga zaman duniyar nan ya kar6e ni ba..." Sai su duka suka kama kuka. Haka suka je asibiti jugum- jugum, sun 6atar da kimanin awa biyu a asibitin, Hafsat kuma ta 6atar da kudi masu yawa, sannan ta dawo da ita gidanta da zummar zata dawo da yamma su tattauna wata magana. Ba ta sami Yusha'u a gida ba, saboda haka ta dan sami kwanciyar hankali, a 'kalla ba ita babu 'kyara da tsangwama da kuma sa aikin rashin tausayi. Wajen 'karfe biyar ta fito da darduma a baranda ta shimfida dan ta sha iska, dakin akwai dan zafi, kuma tana tsoron kunna fanka ko kadan din ce dan kar garin neman 'kiba ta samo rama. Ta daga waya ta kira Hafsat, sai ta ce mata tana hanya. Tana sauke wayar ta ji tsayuwar motar Yusha'u, sai gabanta ya yi wani mummunan faduwa da ba ta ta6a jin irinta ba, kawai sai ta kama ambaton Allah a zuci. A haka Yusha'u ya fado gidan cikin mayen 6acin rai saboda haka nan take jikinta ya dauki 6ari, ta sami kanta da tashi zaune tana ture farantin rake da ke gabanta. "Rumaisa'u wanne karanbani ke sanya ki yi min bincike a waya, kina gane min sirri kuma ba'kin cikinki ya sanya ki wargaza kyakkyawar dangantakar da ke tsakanina da su?" Ta hadiye dukkan fargaba da takaicinta ta dube shi da sanyaiyiyar murya ta ce. "Ban gane na gane maka sirri ba Yaya Yusha'u, bayan cewa ni ce sirrin naka, kuma barrgonka malullu6ar asirinka". . Sai gobe idan Allah Ya kaimu. Dan Aunty na Ruma.GORAN DUMA (P 39) . . Ya fara kumfar baki. "Allah Ya kiyaye, a ina kika zama sirrin nawa bayan cewa zuciyarki ma6oyar sirri ba ni ne a cikinta ba, amma dan 6ata baki ki ce ke ce..." Ta tare shi da 'karfin halin kyautata murya har ma da d'an murmushi ta ce. "Duk yadda ka dauke ni mara amfani a rayuwarka ba zai hana na zama sirrinka ba, misali jiya 'karfe nawa ita Sumolin ta turo sa'ko kuma ta kira wayarka? Karfe daya da 'yan mintuna ta kira wayar shaidar ni ce sirrinka tare ta same mu, ita tana can tana faman juyi da filo tana mafarkin ido biyu. To bari ka ji, ni ba kishi nake da ita ba dan ba aikin banza na zo yi a duniyar ba bare na tsaya 6ata lokacina wajen wula'kanta kaina da jera kafad'a da wata mara mafad'i ba". Ya tsattsare ta da ido fuskarsa a jagule. "Ke wace ce mara mafadin?" Yana rufe baki ta amsa masa kai tsaye. "Ita Sumolin mana! Matar kirki ce zata kira namijin aure karfe dayan dare har tana wasu maganganu na rashin tarbiyya..." Kawai sai Yusha'u ya wanketa da wasu zafafan tagwayen mari a cikin sakanni kadan abubuwa biyu suka faru, hancin Rumasa'u da ya 6arke da jini da kuma shigowar Hafsat gidan, ta samu Yusha'u tsaye yana surfa masifar borin kunya dan shi kansa ganin jinin ya yi mugun kad'a shi. Hafsar ta tsaya cak cikin tashin hankali tana kallon Rumaisa'u da ta durkushe ta tara hannayenta jini na zuba cikin kuka tana ambaton innalillahi wa inna ilaihi raji'un. A bayyane yake yanzu ba ta zafin marin ta ke ba, ta jinin da ta ke asara ta ke wanda ta tabbatar 'kila rashinsa ya janyo mata wata matsalar. "Haba Yaya Yusha'u, don Allah ina abin duka a jikin Rumaisa'u?" Hafsat ta fada cikin 'kumewar takaici tana duban Yusha'u cikin tsana, shi kuma ya tare ta da nade tabarmar kunya da hauka. "Fita! Fice min daga gida, 'yan iska dama ku ne masu zuwa har gidan mutane kuna kashe musu aure... Fita!. Kar na 'kara ganin 'kafarki a gidan nan". Ta zabga masa hararar da ta ku6uce mata, ta ce. "Amma dai ai ka bari na taimake ta ko?" Ya yi kanta kamar zai rufe ta da duka. "An 'ki ki taimake ta, tun wuri ma ki fita idan ba jiran naki dukan kike ba...." Ta yi baya ta fice tana 'kun'kuni. "Allah Ya kiyaye, ai ni mai dukana sai ruwan sama, ita ma Allah Ya isa." Hafsat ta tsaya cikin mota ta kira Alhaji cikin kuka ta ke fada masa. "Alhaji ka taimaka ka shigo lamarin Rumaisa'u Yaya Yusha'u zai yanke maka danyen hukuncin, ya kashe Rumasa'u ya janyo maka masifa..." Alhaji ya katse ta cikin dukan zuciya da si'kewa. "Ke bana son jaye-jayen bala'i, me ya faru?" "Na zo gidan na tarar ya yi mata tsinannen duka, yanzu haka ina 'kofar gidan dan ya hana ni shiga, ita kuma tana cikin gidan ba ka ga yadda jini ke fita ta hancinta ba". Cikin firgici Alhaji ya ce. "Subhanallah, lallai zai yanke min danyen hukunci, ki jira ni ina nan Ibrahin Taiwo Road, amma gani nan zuwa gidan yanzu" Da farko Yusha'u shigewa daki ya yi saboda tsabar 'ki fad'i, ya san lallai ya 6allo ruwa, amma bai san ta ina zai tare shi ba, saboda girman kai shi dai ba zai ba ta hakuri ba, to ai babu ma sararin ba ta hakurin dan ya fahimci Rumaisa ta dauki lamarin da girma, yadda ta ke ambaton innalillahi ririta jinin nan kamar zata mayar da shi jikinta ya san ta zuzuta abin, ko da yake dama ita da lamarin jini babu dama. Ya sauya riga ya dauki mukullin mota tare da niyyar yin 'kunar ba'kin waken zuwa ya kai ta asibiti, amma kamar a mafarki sai ya ji muryar mahaifinsa a cikin gidan cike da tsananin 6acin rai. "Basirar Yusha'u ta toshe da yake tunanin sai ta hanyar mutuwa kawai zai iya rabuwa da Rumaisa'u, idan ya saketa wanene zai matsa masa sai ya zauna da ita.....? Babu komai Hafsat shiga ki hado min kayanta. Cikin sanda da tashin mukulli yana ta zabga da na sani. Ko cikakken minti talatinba a yi ba ya ji sun fice, sai tashin moticinsu ya ji. Hafsat ta wuce Gandu da kayan Rumasa'u, Alhaji kuma ya doshi asibiti da Rumaisa'i, dan tana ganin abin da ta fara ce masa shi ne. "Alhaji a kai ni asibiti, ha6o yana daya daga cikin abin da ake gudarwa sickler". Da muryar tausayi ya amsa mata. "Na sani Rumaisa'u, yanzu za mu je asibiti, ki yi hakuri don Allah, duk ni na janyo miki. Amma Allah Ya sani na yi tsammanin na isa da Yusha'u, ashe shi bai dauke ni mahaifi ba, Ba karamin zafi lamarin nan ya yiwa Alhaji da Hajiya ba, musamman kuma da suka sami zugar Hafsat wadda ke kwance musu duk wani abu da ta sani na muzgunawa da Yusha'u yake wa Rumasa'u har da 'karin gishiri. Kwana biyu, uku Alhaji na zura idon zuwan Yusha'u amma ya 'ki zuwa. Da farkon shi Alhaji ke 6oye hanyar da za su hadu a kasuwa, amma da ya ga Yusha'u ma share kunne kullum in ya kalli Rumaasa'u a gida sai ya ji takaici ya sha'ke shi, wannan ya sa ya bude hanyoyin da zasu hadu, amma shiru har sati biyu. Alhaji ya koma neman Yusha'u a waya, amma sai dai wayar ta 'karaci burarinta Yusha'u bai daga ba. Daga nan ne kuma Alhaji ya tabbatar Yusha'u ya shirya nuna masa iyakarsa. Wannan neman da Alhaji ke masa ne kuma 'kara 'kular da shi. Mugun son kansu yake gani, sun aura masa 'yar dangi sun ce auren zobe ne babu shi babu wani auren , ko da son wata zai kashe shi sannan wadda suka aura masa ba ta cika macen da za a so ba, mace kullum tana gado sai shegen kaifin harshe. A ta6ata kuma cibi ya zamo 'kari, 'kila ma da gangan ta fito da wannan jinin dan dai ya san shi dukan da ya yi mata ba wani taka kara ya yi bare ya karya ba. Yau ya je gidan su Sumoli ya dawo da 6acin ran takurar ya fito, wadda Innarta ta ke masa. Ya dawo Alhaji ya ishe da kira a waya, da haushi ya ci gaba da 'kume shi kawai sai ya shirya fanshewa a kan Rumaisa'u. Karfe sha dayan dare ya kira ta a waya. A tsorace ta dau wayar cikin karkarwar murya ta gaishe shi. Ya amsa a gundure, sannan ya 'kara 6ata murya ya ce. "Wai ke zaman me kike a gida?" Ta shiga numfarfashi ta kasa cewa da shi komai. Ya kara nisawa cikin gadara ya ce. "Ya kamata ki san abin da zaki fada musu su dawo da ke dakinki, ni dai wallahi ba zan zo bikonki ba, malama ba dan ke kadai aka halicce ni ba da zan zauna bakin cikinki ya kashe ni ba. Kafin a sami namijin da zai jure wannan jarabar laulayinki sai an tara dubu, ni na jure dan me za a hana ni auro wadda zata share min hawaye? To kina jin dai abin da na ce, ba zan zo ba, in kin yi dabarar da suka dawo da ke dakinki kanki za ki taimaka, kina ganin dai yadda zawarcin zamanin nan ya ke, bazawarar da ta shekara biyu ko uku a gida ta sami miji sai an ba ta makin distinction balle ke mai dagawa kabari hannu, mutum na ta abinci yana ta maganinki...." Tun da ya faro cin zarafinsa ta ke hawaye, sai da ta ga abin babu 'yan uwantaka ko sanayyya da arzi'ki sannan ta tare shi tana kuka. "Yaya Yusha'u da kana shaye-shaye sai in ce wadannan maganganun a cikin maye kake min su, ka manta ne idan na tashi daga matsayin matarka ni 'yar uwanka ce, jininka? Bari yi min barazana da saki da zawarci duk abin da Ubangiji ya rubuto min sai ya same ni. Da can na ta6a za6arwa kaina aurenka ne? Na san ni nakasasasshiya ce. Duk wanda ya aure ni alfarma kawai ya yi min, saboda haka na gode da alfarmar d aka yi min a baya Yaya Yusha'u, kuma a yanzu duk abin da yake ranka a kaina ka zartar da shi kar ka damu da abin da zan za6a ni amfane ni ko zai cutar da ni, ni duk abin da Allah Ya za6a min zan yi biyayya a gare shi in gode. .. . Kuka ya hanani karisawa, ganin masoyi cikin wani hali babu dadi... Idan kuna so a kara yawan rubutu sai an kara yawan comments da likes. Dan Aunty. GORAN DUMA (P 40) . . A karshe ina son yi maka nasiha, ka daina ta'kama da ciwona wanda ka la6e a bayansa kana cin mutuncina. Ka san ina dauke da cikinka, gwaje- gwaje sun nuna mace ce, Yaya Yusha'u babu tabbacin lafiyayya ce ko sickler, Allah babu yadda bai iya ba, Yaya Yusha'u idan ta kasance sickler wanne tanadi zaka yiwa aurenta? Ka mayar da hankalinka ya kamara ka karrama dan wani dan ko bayan ranka a karrama naka". Ta sauke wayar cikin kuka, kuma ta kasheta gaba daya. Kamar Alhaji ya san da faruwar haka a tsakaninsu, da sanyin safiya ya aikawa Yusha'u sa'kon kar ta kwana kamar haka. ""Ba alfarmar da na saba nema a wajenka zan nema ba, lallai ina son ganinka yanzu kafin ka fita, na shirya kawo 'karshen matsalarka da Rumaisa'u a yau, in ka 'ki zuwa zan iya yanke hukuncin da na za6awa kaina ko da kuwa na kai ka kotu ne."" Ba 'karamin kada Yusha'u wannan sakon ya yi ba, daga ganin kalaman sa'kon ya san Alhaji ya yi fushi, fushi mai tsanani dan haka sam bai yi tunanin gocewa ba. Jikinsa babu nauyi ko wanka bai yi ba ya kintsa ya fice. Tun daga gurin Hajiya ya fara ganin dauke wuta, kar6ar da ta yi masa ko karen makota bai ta6a ganin ta yi masa ita ba. Ya riski Alhaji a falonsa yana lissafe-lissaffe da raskwana yana shigarwa. Ya amsa sallamarsa fuska babu yabo babu fallasa, suka gaisa a haka. Yusha'u ya tattakure yana lalubo kalam ban hakuri, bai gama kammala su ba ya fara shirin rero su, kafin sannan ma har Alhaji ya 'kosa ya dago ya dube shi ya ce. "To ranka ya dade ina jinka". Ya muskuta zai rero abinda ya sa'ka da rawar murya. "Alhaji don Allah.... a yi hakuri... wallahi..." Alhaji ya yi saurin tattare fuska ya daga masa hannu. "Ji nan Yusha'u, ba abin da na kiraka k yi ba ke nan, kar ka dauke ni wani masoyin zuciya mana! Haka kawai zan gayyatoka ka zo ka ba ni hakuri ni din banza?" Jikin Yusha'u ya 'kara daukar 6ari, zai yi magana Alhaji ya tare shi. "Yusha'u ban gayyyatoka dan mu yi tanki-in-tanka ba, ka saurara min kar ka cika ni na sharara maka mari ka zage kwanji ka rama, dan na san ba kyalewa zaka yi ba, tunda babu Rumasa'u a gida wadda zaka koma ka rama a kanta kamar yadda ka yi rannan". Galala Yusha'u ya 'kame baki, ya san halin Alhaji tabbas idan ya yi magana zai iya tafka masa marin, idan ya yi kuma ya tabbatar da laifin da aka li'ka masa na rama mari akan Rumaisa'u. Kamar daga sama Alhaji ya ambata dalilin kiran. "Za6i zan ba ka, sabon aurenka ko kuma zama da Rumasa'u bana son dogon surutu, maza ka za6i daya ka tashi ka ba ni guri". Yusha'u ya ji maganar kamar a mafarki, zuciyarsa ta dinga bugawa numfashinsa na kamar zai 'kwace, da rawar murya ya ce. "Duk ina sonsu Alhaji laifin Rumaisa'u ne... Na ce mata ta daina ba ni abu da hannun hagu.... Na yi magana kuma ta nemi zagina... ban san lokacin da na mareta ba wallahi.... Marinta kawai na yi...." Takaici ya yi mugun 'kume Alhaji, ya tare shi cikin fushi. "Kai Yusha'u duk ri'karka ka san na fi cikin za6in da na ba ka mu kashe wannan maganar". Yusha'u ya dinga juya takarda tsawon mintuna goma, duk sa'kar da ya kamata ya yi ya kwatanta masa zama da Rumaisa'u wanda ba ya tare da komai sai kasawa da wulak'anci, sannan yana ganin ko ita din ya za6a wasu wahalhalun dokokin za a kafa masa, har gara in ya rabu da ita ko su Alhaji sun yi fushi za su sauko su huce. Ya daddage ya yi ta cizawa, amma ko sau daya bai hura ba, ya dage ya rangadawa Rumaisau saki a takarda ya ninke ya mi'kawa Alhaji. Sai da kwalla ta cika idon Alhaji bayan ya ware ya tarar da. "Na yanke igiyar aurena daya da Rumaisa'u, idan ta haihu ta sami miji ta yi aure". Sai da Alhaji ya yi 'kokarin mayar da kwallarsa, sannan ya dago ya dubi Yusha'u. "Da ko 'yar taka tana haifa maka shi ta mi'ke maka amaryarka zata shayar da shi?" Yusha'u ya yi dira-dira ya ce. "A'a Alhaji, ta shayar da shi sai mu yi jinga kamar yadda musulunci ya tsara". Alhaji ya kada kai ya ce. "To da kyau, sai ka fara da jingar renon ciki kafin a kai ga ta shayarwa, wannan zai fara ne daga yau, ya kama daga abincinta zuwa maganinta. Ina fatan ka fahimta?" Yusha'u ya yi sororo dan ganin tsabacewar ta yi yawa, sai ka ce wanda ba a san daga inda ya fito ba? Bai gama shanye wannan mamakin ba Alhaji ya watso masa wani. "Ka je ka fara shirin aurenka, komai da ya kamata a kai ka kawo za mu jagorance ka mu kai, abin da na san za mu iya ke nan ni dai sisi ba zan iya taimakonka da shi ba, wanda na yi maka na baya ma idan ba ka gode ba kana iya dawo min da kayana. Tashi ka bar min gida". Zabu-zabu Yusha'u ya fito ko sallama bai yi wa Hajiya ba, ya fice ya bar gidan. Wuni Alhaji na nu'ku-nu'ku da sakin da Yusha'u ya yiwa Rumaisa'u, ko Hajiya ya kasa sanarwa bare Rumasa'u illa dai ya kira dan uwansa. Mahaifin Rumaisa'u ya sanar da shi cikin kuka da nadama, sai mahaifin Rumasa'u ne ya dinga ba shi hakuri yana tuna masa ai kowanne bawa ba ya kaucewa kaddararsa, a 'karshe ya nemi a bar Rumaisa'u ta taho Abuja, ama Alhaji ya nuna karaya da cewa. "Kun ga na gaza ko? Ku yafe min ba laifina ba ne wallahi...." Ya 'kare maganarsa cikin hawaye. Babu shirin mahaifin Rumaisa'u ya janye maganarsa. "Sam ba haka nake nufii ba Yaya, amma dan hankalinka ya kwanta na janye maganata, na bar maka Rumasa'u ka yi duk abin da ka so a kanta, ai 'yarka ce ba tawa ba Yaya". Daga haka ya kashe wayar. Sai dare Alhaji ya sami Rumasa'u da Hajiya da zancen, bayan doguwar nasiha wadda ke nuna nadama da kwane-kwanen son fadae laifi a karshe dai dole ya fada amma cikin neman afuwa. "Ki gafarce ni Rumasa'u, na zaci alkhairi a aurenki da Yusha'u, ban ta6a kawo sharri ba amma tawa na yi Allah Ya yi tasa, na cutar da ke don Allah ki yafe min... Yau Yusha'u ya nuna min iyakata ya rubuta miki saki daya ya ba ni.... Ina rokon alfarmar kar ki yi nadamar kasancewata uba gare ki..." Numfashin Rumaisa'u ya so ya dauke saboda gigitar zafin sakin da Yusha'u ya yi mata. Ba ta jin dadin auren Yusha'u, amma ba ta6a hararowa kanta zai saketa ba, sakin ya yi mata ciwo kusan ta kwantana shi da mutuwa, sai dai wannan akwai nutsuwa da son cusawa kai tawakalli, musamman ta dalilin sanyayan kalaman Alhaji masu katse hanzari. Ta isa gabansa cikin rauni da hawaye. "Ka daina fadar haka Alhaji, babu bawan da ke iya kaucewa 'kaddararsa, na dogara ga Allah, sakin da Yaya Yusha'u ya yi min bai ta6a komai cikin darajoji da kimarka ba Alhaji, sai ma 'kara su da ya yi. Sannan ya 'kara min nutsuwa da yak'inin gata da tsantsenin mutum ba ya katange shi daga 'kaddararsa...." Ta mi'ke 'kafafunta na harhard'ewa ta bar falon zuciyarta na wani irin zafi... Ina ma ta san inda mutuwa ta ke! Tabbas da ta bi ta ta yafitota ta nuna mata kanta. (Tashin Hankali!.... Masoyan Rumaisa'u na murnar mutuwar aurenta. Ita kuma na cigiyar Mutuwa saboda radadi da zafin sakin.....) . YA HADU DA SUMOLI Lokacin da yake Ganin Bekin Iyayansa Da Kullamasa Auran Ruma Dayake Ganin Gangancine Auren Mai Zurfin Ilimi Yana Shago A Kantin Kwari Kyakkyawa Sumoli Fara Tas Mai Tsawo Da Kiba Sunzo Sayen Kaya ZANBAKU TARIHIN HADUWAR SU DA YUSHAU IN BRIEFLY DANKU FAHIMTA******* Suna Ta Hira Da Kawarta Indashikuma Yushau Yaketa Aikinsa Kuma Yanasauraron Hirarsu Sumoli Tadubi Kyallen Shaddar Dasuka Zo Siya Ajakarta Tafito Dawasu Kananun Litattafi Waisu Text Message Guda Uku Wasu Litattafaine Wadanda Matasa Masujin Sharafin Soyayya Kan Zauna Su Rubuta Sakonnin Soyayya Daga Masoyi Zuwa Masoyiya Kawarta Hadiza Naganin Littafin Tai Kuwwa Ta Ce Kai Sumayya Wadannan Littafan Fa? Sumoli Ta Saci Idon Yushau Tare Da Kallon Kudin Hannunsa Sanna Ta Kifta Mata Ido Tana Mayarda Littafin A Jakarta Wallahi Na Adduoine Najido Zanfara Allah Yakawo Miji Nagari Yanzu Auren Yazama Abin Tsoro Dole Ne mu dage Mukaiwa Ubangiji Kuka Tai Hakan Dan Yushau Ne Kuma Hakika Har Ta Shako Wuyansa Yadansaci Kallanta Kawarta Tace Oh Hakane,yanzu Dan Kinaso Ki Gayamin Daga J,s 3 Kingama Karatu? Nasan Yayan Gidankufa Basawuce Aji Uku A Sakandiri Wallahi Kuwa Yayyena Uku Duk A Haka Aka Aurar Dasu Yayata Umma Ce Kawai Tasamu Miji Mai Shaawar Karatu Ya Barta Ta Zarce A Gidanta Amma Babanmu Duk Kwakwarki Ason Karatu Ba Zai Lamunta Ba Haka Sukaita Basajar Zancensu Mahaifinki Ya Burgeni Sosai Nandai Suka Kulla Soyayya Tsakaninsu,dukan Kayandasu Sumoli Suka Dauka A Aljihun Yushau Tundaga Wannan Ranar Yushau Yadaura Dambar Neman Sumoli, Sumoli Su Biyar Ne Adakinsu Duka Mata Ne An Aurar Da Sauran Saura Itakadai Mahaifinta Yafizuwa Kudu Daga Arewa Kayan Gwari Yake Siyarwa Lokacinda Girma Yakamashi Gashi Fitinar Matar Sa Tatasa Shi Danhaka Ya Tattara Komatsansa Yakoma Kudu Watan Yushau Biyu Suna Soyayya Da Sumoli Iyayata Suka Matsamasa Ya Turo Hardai Yasaketa Adaren Ranar Duk Yadda Ruma Taso Ta Basar Damaganar Sakinda Yaimata Takasa Darar Ranar Saiyazamemata Tamkar Daren Samun Labarin Rasuwar Auwal Indatake Tunani Lallai Da Kyar Idan Rayuwa Zata Kara Budemata Shaf Idan Rayuwa Zatakara Budemata Shafi Mai Haske Koda Kuwa Za A Dan Gutsiro Kyallinsa Ne Daga Shafi Irin Na Auwal Kilamashafi Masu Duhu Za A Yi Ta Bude Mata Kukanta Na Abincikintane Waddata Hakikance Irintane Wato Sikila Tunda Yai Sanadiyar Barin Rabinda A Baya Wanda Shine Kila Zaizo A,S Tausayin Abincikinta Wasa Wasa Ranar Nan Da Sanyin Asuba Saida Alhji Ya Kwashi Ruma Zuwa Asibiti Suna Zuwa Aka Basu Gado Wannan Yadawo Da Ciwan Abinda Yushau Yai Danye A Zuciyar Mahaifansa Da Surukansa Musamman Innar Ruma Wadda Karamcin Mahaifin Yushau Kadai ke taka Mata Birkin Kiran Yushau A Waya Taimasa Allah Ya Isanta Malyria Tafara Cinkarfinta Ga Jininta Yafara Hawa,ciwan Mukamiki Ya Motsa,nandanan Sai Ga Ruma A Hanyar Lahira,wai Gidan Sauro Ma Kunrasa Arzikinsa Ruma? Kwananta Uku A Asibiti Yushau Ya Cika Aljihu Da Kudi Yadoshi Gidan Nasu,gidan Cike Da Kannensa Mata Dukkansu Tare Da Hajiya Suna Shiri Da Alama Shirin Fita Wani Guri Suke,yai murnar Rashin Ganin Ruma Haryaji Haushi Indai Samun Mijin dazai kula Da Ita Kamar Shi Abi Ta Wajen Alhji Yafara Zuwa Wanda Yaimasa Irin Saukar Dakewa Maroki Ga Mutumin dasam Baiyi Niyyar Kyau Ta Ba,meyafaru? Alhji Yatambayeshi Cikin Fuskar Shanu,yafito Da Kudi Yamikawa Alhji Tare Da Koro Bayani Gasu Alhji Sai A Ciri Wanda Za A Kai Kudin Aure,,a Ware Sadaki,akaimusu Harnadanyi Wani Karanbani Nasanardasu Kunanantafe Ranar Sati,. tundakaika Haifemu Ko? Kawai Tunkudar Keyarmu Zakai Ka Ce 'ya'yan Nan Zoku Kai Kudinnan, ayi Hakuri Alhji Dama Dan Sun Matsane Alhji Ya Kalleshi A Kule,ammadai Yashanye Bacin Ransa Ya Ajiye A Gefe Yadau Wayar Sa Kan Tebur Yana Latsawa To A Fita A Siyo Min Kati Zansa A Waya Akira Yanuwa Masu Kai Kudin Auren Suzo Sukai,mamaki Da Mugun Takaici Suka Gallabi Zuciyar Yushau Yaje Mota Yadauko Katin Dari Hudu Yakawo Ma Alhji Fuskar Alhji Ba Walwala Za A Raba Kudin Akai Rabi Hakane? Daga Baya Kuma Akai Sadaki Ko?Alhji Baijira Cewar Sa Ba Ya Ce To Ranar Asabar Din Zakazo Kakaisu Ko Kuma Kudin Ma Zaka Bayar Na Ara Mota A Zuba? Rannan Naimaka Maganar Daukan Nauyin Rainon Cikin Ruma Alhji Ya Ce Rannan Naimaka Maganar Jinyar Cikin Ruma Kasameta Kunyi Maganar? Ban Ganta Ba Ranar Har Na Bar Gidannan Amma Yau Zansameta To Alhji Yafada Cikin Halin Ko In Kula Ya Ce Tadanyi Jinya Sosai Cikin Kwana Biyun Nan Wanda Nauyin Cikim Bakin Cikinka Dakuma Guggubin Wahalardata Taho Da Ita Daga Gidanka Suka Hadu Suka Jazamata Talasarmin Kudi Sosai Dan Saidatasha Ledar Jini Biyu Saboda Malyria Takamata Da Zafin Kasansu Sickle Malyria Ba Karamin Hatsari Ba Ce Atare Dasu Ince Ko Arzikin Ne Ko Na Maganin Sauro Batasamu A Gidanka Ba Yushau Yakasa Magana Zuciyar Sa Kamar Ta Fashe Saboda Takaici Ta Ci Kudi Sama Da Dubu Hamsin Don Mundanje Asibiti Mai Kyau Ne Idankafita Ka Karbi Rasidai Gurin Hajiya Kaduba Dan Allah Inasan Kudina Gobe Alhji Nasane Kallan Mamaki Yushau Yakemai Danhaka Yafice Yana Cewa Kakokarta Kuyi Jinyar Nan Saura Kuma Kasanya Zalunci Ciki In Hakan Ta Faru Tozan Fitar Da Ita A Alamarin Ni In Shiga A Fusace Ya Fice Yana Kunkuni A Zuciyar Sa Allah Bazai Hanani Yadda Zanyiba Yakarade Gidan Bai Ga Ruma Danhaka Saiyadawo Falo Ya Taddasu Suna Shirinfita Ransa A Baceyake Harma Yanafakan Idan Hajiya Yana Hararar Hafsat Wanda Ita Ma Take Murguda Masa Baki To Malam Fitafa Zamui Hajiyatafadama Cikin Wata Murya Mara Dadi, To A Dawo Lfya Inkin Rike Adadin Rasitan Asibitin Nanda Waccen Yarinyar Ta Ci nawane? Alhji Ya Ce Na Kawo Masa Kudinsa Gobe,yafadi Hakan Ne Waiko Hajiya Zataga Rashin Kyautatwar Alhji,ko Ma Ta Taushi Zuciyar Sa Ya Janye Amma Sai Ga Shi Hajiyata Fadi Abindayanuna Tamafi Alhji Kulla Gabadashi To Idan Aron Kudin Zaizame Masa Da Rashin Burgewa Aisai Yadinga Nemoka Duk Lokacinda Bukatar Irin Hakantataso Kazo Asibitin Ka Biya Kaitsaye Basai Ka Sanya Wani Akin Yahada Maka Lissafiba,ko Kuma Kaji Haushin Wana Ya Ranta Maka, Allah Yabaki Hakuri Niba Hakane Nufina Ba Batatankashi Ba Ta Wuce Dole Ya Biyo Bayansu Suka Kebe Da Mubarak Ya Kirga Dubu Ashirin Ya Damkawa Mubarak Ransa A Bace Man Allah Idan Waccen Malalaciyar Yarinyar Tatashi Daga Bacci Ka Bata Ka Ce Na Rainon Cikine Yawuce Mubaraka Ruma Kwance A Gadon Asibiti Yammacin Kwananta Biyu A Asibitin Idanta Biyu Kuma Cikin Hayyacinta Fes Amma Ta Runtse Idonta Alamun Tana Bacci Tunanuwa Barkatah Na Ruda Kwakwalwarta Alhji Da Hajiya Da Mominta Kadai Ke Ciki Suna Sirri Acewar Su Itakadai Ce Ba Aso Taji Mominta Cikin Damuwa Ta Ce Alhji Acikin fargaba Nake Dan Allah Karka Boyemin Komai Melikitan Ruma Yakebe Dakai Yafada Maka Ya Ce Abinda Kika Riga Kikasanine Fa!Na Cutar Da Ruma Dana Gadata Da Wanda Baisan Darajarta Ba Duk Wannan Yawuce Alhji Ba Bu Wanda Yaisa Kankare Abinda Allah Ya Riga Ya Rubuta Yanzu me Likita Ya Ce Yaimin Tambayoyi Sosai Game da Asibitin Da Ruma Kezuwa Awo Na Sanardashi Amma Saiyanuna Mamaki Kwarai Da Yadda Batasami Isashiyar Kulawa Ba Momi Ta Girgiza Kai Cikin Takaici Sam Ba Laifin Asibitin Bane Dazu Ma Safe Nai Hira Da Ita Shigen Wannan Amma Yadda Na Fahimta Shine Tana Fashin Zuwa Asibitin A Kaidar Da Likita Yaimata Sannan Ba Bu Isashen Kudin Da Ake cajinta Irin Yadda Ake Cajin Sikila,hakane Alhji Ya Ce Tare Da Takahcin Yusha'u.... . To sai kuma gobe idan Allah ya kai mu. Na dan kara rubutun. Masu commnts da like godia marar adadi, wanda basayi ya kamata ku para koda like ne kapin ku pita a gidan. Dan Aunty. GORAN DUMA (P 41) . . Likita Yasanar Dani Ce Malyria Taiyawa Ajikinta Wanda Yake Ganin Harda Sakacin Liikitanta Na Baya Da Bai Zurfafa Bincike Ya Gano Cewa Yara Biyune A Cikin nata Ba,yan Biyu? Hajiya Da Momi Suka Fada Cikin Firgici Nandanan Hawaye Yafara Zarya A Idon Momi Ta Dora Hannu Biyu Aka Tana Kallon Ruma Dake Bacci A Gado Cikin Raunanniyar Murya Ta Ce Allah Kaika Halicci Ruma Kafimu Sonta Allah Ka Tsallakar Da Ita Ka Saukaka Alamuranta Kaimata Albarka Duniya Da Lahira Daga Hajiya Har Alhji Cikin Raunaniyar Murya Suka Amsamata Alhji Ya Ce Karkidamu Aita Dawo Hannunmu,muba Zamu Yi Sakacinda Yushau Yai A Baya Ba Zansami Ma Likitan Naimasa Bayanin Komai Cewa Sakacin Daga Garemu Ne Badaga Likitanta Na Baya Ba, Haka Har Sukai Shuru Da Maganar Da Suke Zaton Sirrine Amma Komai A Kunnen Ruma Sukayi Dan Haka Dasuka Yi Shuru Saitata Zuciyar Ta Hau Nata Aiki Na Fargaba.Tausayi,da Nadama zuciyarta Takai Kololuwar Ciwo Da Jin Inama Daga Wannan Kwanciyar Adau Gawarta Su Huta Da Radadin Rayuwar Wannan Kuntatar Duniyar,basu Ankara Ba Haka Da Safe Likita Yazo Duba Ta Hajiya Da Mominta Da Hafsat Ne A Dakin Suka Mike Suka Fita Itakuma Mominta Talike Ganin Likita Bai Koro Momi Ba Yasanya Ta Dubi Momi Cikin Sanyin Murya Ta Ce Momi Zan Iya Magana Da Likita Momi Ta Ce Menene Ke da Na Cancanci A Boyemin Shi Ruma Murmushi Tai Kawai Likita Yanuna Mata Hanya Tare Da Cewa Dama Yanzu Nake Shhrin Korarki Ta Ce Likita Ya'ya Biyu Ne Acikina Ko? Cikin Muryar Kwantar Da Hankali Ya Ce Hakane Ta Ce To Inajin ba Damuwa Ke Asassa Hawan Jiniba,da Ita Ce Sila Lallai Daga Jiya Zuwa Yau Da An Sami Labarin Cewa Yan Biyu Zan Haifa Yakamata Atarar Da Jinina Yai Bindiga Don Me? Don Ba Kya Murna Da Rahamar Da Allah Yaimiki Ta Kyautar Ya'ya Biyun? Ta Ce A A In Zanyi Murnar Na Haifi Ya'ya Biyu Ya Kamata Na Hada Ta Da Fargabar Kai Na Haifi Wahalallu A Rayuwa Irina Wannan Kuma Yin Allah Ne Ruma Likita Inaso Aimin Prenatal Diagnosis Gynotype Don Insan Makomar 'ya'yan Gwajine Da Ake Zukar Ruwan Da Jariri Ke Kwance A Ciki Yayinda Ciki Yakai Sati Goma A Gwada Ana Samun Sakamako Dan Gano Gynotype A Razane Likita Ya Dubeta Meyasa Ruma? Nafadi Dalili Inasan Insan Makomar 'ya'yana Matsayinki Na Musulma Baikamata Kinemo Wannan Mafitar Ba Inkinga Su Waye 'ya'yanki Mezakiyi? Kizubar Dasu? Ai Ina Tsammanin Kinsan Ko Haka Ne Lokaci Yakuremiki Tunda Bazaki Zubar Da Dan Da Ko Yanzu Kika Haifeshi Zai Izaci Gaba Da Rayuwa Ba, Ba Abinda Nake Nufi Ba Kenan Inason In Sami Murna Da Natsuwa Idan Abinda Zan Haifa Ba Sikila Bane Inason Yin Kuka Da Nadama Idan Bincike Ya Gano Sikila Zan Haifo Inyi Tir Da Kaina Danake Ganin Abin Danai Na Kirkine Bisa Auren Mahaifinsu Wanda Yaki Yarda Ayi Gwajin Gynotype Dan Sanin Matsayinsa Da Sanin In Munyi Aure Me Zamu Iya Haifa Indai Ba Kashesu Zaki Ba Kuma Ba Sauya Su Za Ai Daga Sikila Su Koma Masu Lfya Ba Ko Kamar Gara Ma A Bar Su Suzo Duniyar Ki Gani Ruma Musamman Dakike Maganar Kuka Da Nadama Idan Har A Ka Tarar Da Cewa Sikilane Lallai Kuwa Inhar Aka Barni Ba A Gano Ba Zuciyata Zata Iya Bugawa Kafin Na Hai Hu Duk Abinda Sakamako Zai Nuna Shinakeso Likita Inasan Yin Kukan Murnar 'ya'yana Sun Kubuta Kuma In Sun Girma Bazan Ji Ciwon Zaluncindanai Musu Na Kawo Su Duniya Yadda Suka Sami Kaiba Haka Ma In Kukan Ne Inasonyi Tare Da Godiya Ga Allah Wanda Yake Jarrabani Nida Ahalina Sanin Sikila Zan Haifa Bazai Tawayi Lfyata Ba,amma Zaisamin Karfin Gwiwar Data Wakalli To Shiken Karkidamu Za Ayi Ma Yardar Allah Haka Ruma Ta Ci Gaba Da Kwanciya A Asibiti Kudi Kam Ana Cinsu Komai Aka Nema Da Gudu Alhji Kan Bayar Haka Ko Zuwa Yayi Ya Tarar Da Wani Ya Bayar Saiya Mayar Masa Da Abinsa Ammafa Akwai Dirowa Ta Musammasan Daya Ware Yana Adana Wa Yushau Wanda Hidimar Aure Ta Dauke Wa Hankali Abin Haushi Ko Sau Daya Baije Asibiti Da Suna Duba Ruma Ba Yasan Tana Asibiti Bai Sani Ba Oho! Su Dai Sundage Suna Ta Kakkare Mata Musamman Maganar Aurensa Dasuke Sayawa Wai Ba Sontaji Itakuma Tanai Musu Kallon Rashin Sanin Dawan Gari Tare Da Mayar Da Allura Garma Shin Ita Data Mallaki Irin Auwal Tarasa Bata Mutuba,dan Irin Yushau A Doron Duniya Ya Saketa Ya Auri Wata Saitai Ciwon Kai,? Andaura Auren Yushau Da Kwana Daya Sannan Aka Bama Atika Alhakin Sanarma Ruma Tagayamata Kuma Taimusu Fatan Alkhairi Inda Sukuma Su Atikan Sukaji Haushin Abinda Ruma Ta Ce Akan Hakan Mominta Ta Sanarmata Da Sakamakon Likita Akan Gynotype Din Akwai Yuyuwar Duk Yaran Sikilane Saidah Kinsan Babu Yadda Allah Bai Iya Ba,sai Ki Ga Ya Sanyo Su Lafiyayu Ba Kamar Yadda Bincike Yanuna Ba Tayi Mutuwar Zaune Da Hawaye Tana Kallon Momi Nata Zuba Mata Maganganu Na Kwantar Da Hankali Ta Ce Ki Tuno Shekaruna Mana Momi Yakikejin Za Ki Binne Tunanina Da Abinda Bazai Yuwu Ba Tafarakuka Karki Yaudareni Da Cewa Zan Iya Haifar 'ya'yan Da Ba Sikila Ba,gara Kizo Kitaya Ni Mui Jimami Mui Kaico Da Nadamar Yadda Muka Amince Da Auren Yaya Yushau Alhalin Ta Ko Ina Bai Cancanta Ba Tabbas Mun Zalunci Yaran Dazan Haifa Indai Zasuyi Rayuwar Su Cikin Jinya Da Jin Ciwo Irin Wanda Nakeji,ruma Tasake Barkewa Da Kuka Tausayin 'ya'yan Cikinta Kamar Zai Kekketa Zuciyarta Momi Takasa Daurewa Danhaka Itama Tafara Tayata Momi Nason 'yarta Ruma Tanajin Tausayin Halinda Take Ciki Dakuma Wanda 'ya'yanta Dake Shirin Zuwa Duniya Zasu Shi Ga Ruma Na Tausayin Kanta Amma Ga Abinda Yafi Shi 'ya'yan Dazata Haifa Irin Rayuwarta Zasuyi Rayuwa Mai Wahala Irin Wadda Ko Makiyarka Bazakayi Wa Fatanta Ba Yan Biyu Zan Haifa Kuma Duka Sikila Momi Tausayinsu Zai Illantani Indah Irin Jinyar Da Nake Zasui Momi Nayi Nadamar Hakurina Da Biyayyata Wadanda Suka Saukaka Min Auren Yushau Harmuka Dau Wannan Hakkin Na Haifar Yara Masu Ciwo Haka Dai Ruma Taita Sumbatu Har Saida Wata Nurse Ta ShiGo Taita Musu NasiHa Yushau Kam Ana Cin Amarci Har Dakansa Yadinga Jin Asarar Rayuwar Auren Dayai A Baya,dakuma Sara Wakansa Wajen Kafewa Neman Dayazamo Masa Alkhairi, Dole Yakoyi Tattali Da Kalaman Kwantar Da Hankali Da Bayyana Soyayya,cikin Satin Bikinsu Da Aure Suka Zama Wasu Laila Majnun Duk Da Cikin Wadannan Sati Biyun Abubuwan Mintsinin Zuciya Akan Sumoli Tuni Sunfara Bayyana,amma Yanajin Jarumtar Sadaukar Da Son Ransa Ga Soyayya Wadda Ta Afko Masa Rana Tsaka Batare Daya zaci Abin Mamaki Ya Manta Da Komai Da Kowa Kaiko Bangajiya Baijewasu Alhji Dakuma Hajiya Ba Wata Safiyar Lahadi Yafarko Yatarar Da Missed Calls Din Alhji Dakuma Na Hajiya Gabansa Yadinga Faduwa Da Fargaba Tare Da Zargin Kila Ba Bu Lfya,kokuma Kiransa Ya Ke Yi A Nuna Masa Iyakar Sa Akan Ruma Hakan Yasa Ya Share Kiran Ya Ci Gaba Da Sabgoginsa,sunkarya Kumallo Kowa Cikin Kwalliya Suna Zaune Ana Hira Amma Dai Yushau Na Satar Hararar Kwanukan Da Suka Gama Da Abinda Ya Riga Ya Saba A Gidansu Ana Gama Cin Abinci Ake Kwashe Kwanuka A Wanke ,ruma Ma tana Kwatantawa Yaddako Bata Wanke A Lokacinba Musamman Lokacin Sanyi Saboda Ciwanta Takan Kwashe Ta Adanasu A Kichin Amma Sumoli Da Sauki,dayagaji Da Hararar Kwanukan Saiya Shirya Yimata Jirwaye Dakamar Wanka Inda Ya Kwashi Kwanukan Ya Nufi Kicin Yana Fitowa Tsakar Gida Sai Ga Almajirai Biyu Yadanji Takaicin Ganinsu Dantaimasa Maganar Daukan Almajiran Aiki Sudinga Yimata Aikace AikaCe Suka Gayamasa Cewa Aunti ce Tadaukesu Aiki Kullum Sudunga Zuwa Sunaimata Shara Da Wankewanke... . Hhhh... To pa. Yushau welcome to the world.. Yanxu aka para wasan. Muje zuwa.. Dan Aunty GORAN DUMA (P 42) . . Yaushe Kuka Fara Wanke Wanken,? satin Mu Daya Kenan Yaji Wani Mugun Amai Nataso Masa Ya Ce To Dan Allah Fita Bana Bukatar Sake Ganin Kowa Agidana Tuni Sumayya Na Tsaye Jikin Taga Tana Jinsu Haushin Duniyarnan Ya Isheta Ta Lalubo Mai Kudi Ta Aura Wanda Yakamata A Ce ta fantama Zai Iya Aje Mai Wanke mata Musamman Idanko Da Harabar Ajiyn Motocin Gidan Ubansa Ka Kalla To Amma A 'yan Kwanakinta A Gidan Tafara Tsintar Kamar Ta Gina Ne Bata Shi Ga Ba Ne Mijinta Furar Dankoneya Shigo Rai A BaCe Yadauki Remote Ya Sauya Gurin Zama Kwatsam Ta Jefo Masa Wani Batu Mai Cike Da Rainin Hankali Wani Abu Na Dauremin Kai Darling Sama Da Sati Biyu Da Auren Mu Amma Ban Taba Ganin Wani Ko Wata Ya Zo Gidan Na Ka Gabatarmin Shi A Matsayin Dan Uwanka Ba,duk Sai Tarkacen Abokai Da Makota Ya Ce Sumayya Aini Ki Ka Aura Ba Dangina Ba Saboda Haka Karki Wani Fitini Kanki Da Rashin Ganin Dangina Kai Haba Honey Ni Har Dasu Na Aure Ka Wallahi Ai Abin Alfaharine Ace Mutum Ya Auri Dan Dangi Ba Kamar Wanda Yafado Daga Sama Ba Wani Irin Rudu Yashiga Sai Ga Kiran Alhji Nandanan Ya Daga Ko Dan Shawarar Da Zuciyar Sa Ta Bashi Na Tuntuntuni Akan Amsar Bawa Sumoli Saboda Ma Kar A Fitar Da Gurbin Raini Ko Kuma Aci Amanar Soyayya Alhji Ya Ce Kaga Malam Ba Alfarma Zan Nema A Wajenka Ba Ruma Ce Ba Bu Lfya Tunjiya Zuwa Yanzu Dai Ta Hai Hu Muna Son Ganinka Da Gaggawa Ya Katse Wayar Yushau Ya Cika Da Farincikh Ruma Ta Haifamasa 'ya Amma Gauraye Da Fargabar Ance Bata Da Lfya Yana Tsoron Ta Mutu Yanzu Ba Bu Makawa Dangi Sai Sun Masa Sharrin Shiyakasheta A Rude Ya Dinga Kiran Alhji Yaki Dagawa Darling Me Ke Faruwa? Kishirya Muje Gidan Mu Yanzu Inki Ka Ga Gidan Kila Kisan Dan Dangi Kika Aura Ba Wanda Ya Fado Daga Sama Ba Kadauki Maganar Da Zafi Allah Ya Baka Hakurh Darling ,Tadan Bugi Shi A Kafada Ta Wuce Tana Dariya Bari Na Shirya Cikin Ransa Ya Ce Meyakamata Ya Tunana Akanta Kodayake Yaudarar Kansa Kawai Yake Tuni Ya Tunanadin Abinkuma Ya Tunoshi Ne Sumoli Kuma Wadda Ko Secondry Bata Cika Ba Ita Ce Burinsa Amatar Aure,yakuma Dace Ya Aura, Gata Kyakyawa Ma Amma Abinda Abinda Yakasa Ganewa Wanda Yake Zato Da A Budewar Idon Bokone Yanzu Ya Fara Shakkar Kamar A Dabi'ane Wato Rashin Jin Kunyar Miji Da Fadamasa Magana Kaitsaye Sumoli Na Iya Kallon Kwayar Idansa Kaitsaye A Kowanne Irin Lokaci Tafada Masa Ko Wanne Irin Magana Ta Soyayya Har Na Can Karshe Wanda Duk Dadewar Sa Da Ruma Bata Taba Iya Bude Ido Tafadamasa Ba To Anji A Bar Wannan Dama Ruma Bata Sonsa Amma 'yan Boko Akasani Da Lakabawa Miji Sunaye.Darling. Dear.Honey,sweety Da Sauransu Da Sunayen Nan Take Kiransa Tun Ma Kafin Suyi Aure Dan Haka Ya Cire Su A Layin Halin 'yan Bokone Dan Kawai Abin Na Burge Shi Duk Daya Kasa Cinkar Dalilin Burgewar To Amma Tsayayyar Da Sumoli Taimasa Dazufa? Yafi Zatonta A Mace Data Gama Wayewa Wadda Mata Dauki Kanta Daidai Da Mijin Itakuma Dabiar Ina Sumoli Ta Fincikota? Baisan Haka Ba Saida Sumoli Ta Fito Cikin Shirin Fita Fuskarta Cike Da Kwalliya Kamar Mai Shirin Fita Gasar Sarauniyar Kyau Tasha Matsatsun Riga Da Siket Na Leshi Ga Kuma Yalolan Mayafi Ta Yafa Tana Ta Taunan Cingam Yaji Haushi Kamar Ya Kashe Shi Ya Ce Amma Bada Wannan Shigar Zamuba Ko? Ta Ce Haba Sweety To Gidan Naku Masallacine Daza Ce Bazanje Haka Ba? Ba Masallaci Bane Haka Zalika Ba Mashaya Bane Tajuya Adan Kufule Tadawo Sake Da Mayafi Wanda Yadan Fi Na Dazu Yafito Dauke Da Key Yana Cemata Wai Duk Ina Mayafan Dana Zuba Miki A Lefe Haba Wadannan Saika Ce Wata Matar Limami Washegarin Ranar Da Akakawosu Na Mayar Dasu Kasuwa Na Sauyosu, Ya Tadda Gidan Ba Bu Kowa Sai Megadi Ya Basu Tabbcin Duka Suma Asibiti Ance Ruma Ta Sauka Ko? Ansami 'yan Biyu Allah Ya Raya,yan Biyu? Yushau Ya Tambaya Cikin Farinciki AlhamduliLlah Megadi Yaimusu Kwatance Da Cewa Aitana Asibitinsu Datake Kwance Tuntuni YuShau Kam Ya Girgiza Dakin Ruma Tadade A Asibiti Na Gyadi Gyadine Yushau Kam Yasan Zaiji Ajikinsa Aljihu Zai Yi Bayani Gashi Hidimar Biki Dayayi Ba Bu Mataimaki Kasuwa BaBu Ciniki Bugu Da Kari Alhji Neke Bashi Kaya Kwasha Kwasha Tunda Ya Sakarmasa Ruma Ya Make Hannu Satin da yawuce Ma Hanashi Bashi Yai Wai Sai Ya Bayar Da Kudi Kamar Kowa,, Fice Yushau Ya Zagayesu Da Ido Saida Yaji Fitsari Na Neman Kubcemasa Inka Cire Su Hafsat Gaba Daya Manyan Surukansa Ne A Dalilin Ruma Saboda Rashin Kyautatawar Da Sukejin Yai Musu Mahaifansa Biyu Na Ruma Biyu Goggo Daga Rogo Saikuma Wadda Baiji Dadin Ganinta Ba Innar Marigayi Auwal Yadda Kafafuwansa Suka Sarke Hakama Na Sumoli Saboda Kwarjinin Da Mutanan Sukaimusu Tare Da Jin Raunin Karbar Ko Inkula Da Akaimusu,haka Dai Aka Gaisa Inka Cire Goggo Dataimasa Barka Da Momin Ruma Dataima Sumoli Fatan Alkhairi Tare Da Bayar Da Hakurin Rashin Halartar Zuwa Ganin Amarya Dakin Yai Tsit Saboda Rashin Sanin Halinda Take Ciki Hardai Lokacin Sallah Tai Maza Suka Fice Sumoli Tayo Alwala Cike Da Fargabar Wanda Zata Tambaya Aron Hijabi Kinyi Sallarne Hijab Nake Jira Su Aramin Momin Rumaisau Ta Mika Mata Wani Yayinda Hafsat Karaf Wanda Dama Tadade Tana Jifanta Da Harara Nifa Farkon Shigowarkima Na Zata Budurwa Ce Wallahi Sam Bakiyi Kama Da Matar Aureba,hajiya Tatare Ta Rai A Dan Ba Ce Kai Ke Dai Hafsat Kincika Shishigi Kowa Bada Yanda Yaza Barma Kansa Rayuwa Ba Yushau Ya Kule Da Haushin Hafsat Wadda Yake Ganin Ta hadashi Da Mahaifansa Amma Hakan Ma Yasa Hafsat Takara Matsawa Tana Hararar Yushau Ta Ce To Hajiya Ai Gara Afadawa Mutum Gaskiya Dankar A Zageshi A Bayan Idansa Yushau Kam Yakasa Magana Sai Ga Alhji Ya Shigo Yamikamasa Takarda Cajin Dasukaimana Na Yanzu Kenan Maza Jeka Biyasu Abinsu Yushau Kam Yaga Kudi Sama Da Dubu Hamsin Yadago Ya Dubi Alhji Baki Na Rawa Alhji Ai Yau Lahadi Ba Bu Bankuna Alhji Ya Ce Baka Aje A Gida Ba,yanzu Yaya Za Ayi, Sum Sum Ya Fice Daga Dakin Goggo Ta Yunkura Ta Ce Tsaya Kaci Abinci Alhji Ya Ce Barshi Munan Yaushe Rabon Mu Da Abinci,yushau Dama Baiyi Niyyar Tsaya Wa Ba Danyasan Anyi Niyyar Tsinkashine, Nan Ya Bar Sumoli Dan Yasan A Gida Ko Cikakkiyar Dubu Ashirin Baida Ita Saiwajen Bayan Isha'i Yadawo Cike Da FargaBa Ya Taradda Hafsat Momi Da Alhji Ko Zama Baiyiba Alhji Ya Ce Ka Biyasu Ko? Ya Kada Kai, Kuma Sai ka dawo Mana Hannu Na Dukan Cinya Kana Nufin Hakan Yaran zasu Zauna Bako Rigar Sawa Yushau Yadaga Kai Yadubi Alhji Saboda Yadda Maganar Taimasa Ciwo Ya Ce Aima Bansan Abinda Akasamu Ba Cikin Zafin Rai Alhji Ya Ce Kuma Bakaso Kasaniba Kila Donkar Kai Wahala Sai Can Momi Ta Ce Kanemo Masa Alfarma Mana Ya Shiga Ya Dubasu Ya Cemata Ya Cemiki Yanason Ganin sune? Dankar Na Cika Damunkune Yasa Ban Tambaya Ba Amma Dama Na Matsu Nasan Halinda Suke Ciki Alhji Yai Tsaki Momi Ta Tashi Tadawo Tadubi Yushau Cike Da Kulawa Ta Ce Kashi Ga Hafsat Ta Mike Da Sauri Nifa Momi? Kibari Ya Fito Karkuje Kuiwa Mutane Hayaniya Inji Alhji,jikin Yushau A Sanyaye Ya Tura Kofar,ruma Kam Kwance Take Magashiyan A Gado Tan Karbar Karin Jini A Gefe Ga Jarirai Biyu Bisa Kananan Gadaje Nade Cikin Lallausan Farin Bargo Daga Wani Barin Kuma Ga Nurse Tanaganin Yushau Ta Ajiye Wayarta Tataso Da Sauri Tanamasa MaraBa Murya Kasa Kasa Ya Amsa Ta Dauko Masa Na Farko Yadauka Yana Lallabawa Kamar Kwai Mace Ce Ko Namiji? Fuskar Sa Dan Firit Bata Da Mara Ba Dana Ruma Da Kallonsa Ansan Bashi Da Koshin Lfya, namijine Ga Macen Nan Yajima Yana Kallon Yaron Dake Maida Numfashi Daidai Yamaidashi Yadau Macen Da Kwarin Guiwa Ganin Tafi Namijin Kuzari Yaga Alamar Cutar Tafiyawa Ga Namijin Akan Macen Canyaji Ruma Na Magana Kasa Kasa Dasauri Yadubi Nurse Ya Ce Kinji Magana Take Ta Ce A Tausaye Sambatu Take Kawai,cikin Nannauyan Bacci Take, Kamarfa Ana Iya Gane Abinda Take Cewa Hakane Kakarasa Kusa Da Ita Zaka Iyaji Yamikamata Yaran Yakara Sa Kusa Da Ita Farat Daya Yaji Ta Ce KUYI HAKURI BANSO HAKA BA,BAN SHIRYA HAKA BA,DAN ALLAH KU YAFEMIN.. a Razane Yadube Nurse Din Meyafaru Dawa Take? Saida Nurse Tadauke Kwallah Ta Nuna Yaran Da Yaranta Take Tana Tausayinsu Da Nadamar Ta Haifesu Sicklers Amma Ba Abin Mamaki Ba Ne Kasancewarta Sikila Ita Kadai Tasan Azabar Datakesha... . Ayya masoyiya ta Allah Ya baki lapia.... Ba komai ya tsaida ni ba illa tausayin ta.. Sai jibi muci gaba kapin nan ta dan samu sauki.. Dan Aunty GORAN DUMA (P 43) . . Ita Ce Kadai Zatafi Tausayamusu,a Razane Ya Bar Gadonta Yakoma Na Yaran Yahau Kallonsu Yadaga Kai A Gigice Ya Ce Dukansu Sikilane? Ai Ba Dauka Ake Ba, Uwa Da Uba Ke Tarayya Su Haifi Sikila Ita Kadai Bazata Iya Haihuwar Sikila Ba Sai Idan Mijinta Ma Nada Irin Wannan Nauin Jinin A Sakarce Yace Gaskiya Ni Lfyata Kalau Nurse Kam Tafara Lissafin Daga Kauyen Dayafito Da Kyau Ta Daure Ta Tambayeshi Au Kaine Mijinta Yakada Kai Amma Dai Kafin Aurenku Baku Ziyarci Mashawarta Sikila Ba Kilama Bakui Gwajin Gynotype Ba,kuma Bayan Auren Ma Baka Shiga Lamarin Asibitinta Sosai Ba Kunya Ta Hana Yushau Amsawa Yana Ma Fargaba Kar Allah Ya Jefo Wani Cikin Danginsa Yaji Haukar Wannan Matar Donsu Ma Haka Suke Girmama Asibiti Tamkar A Can Aka Buso Wa Ruma Rai Ya Fice A Can Kuma Alhji Yatareshi Dawata Bakar Magana Kaganka Da Sikila Har Kala Biyu Ko? Allah Kenan Sai Mugani In Haka Rami Zakai Ka Binnesu Ko Kuma Suma Zaka Ce Shagwabar Ce,yushau Kam Yakasa Magana Yaimusu Sallama Yatambayi Ina Sumoli Aka Ce Tabisu Hajiya Gida Dan Takaici Kiranta Yai A Waya Tafito Suka Tafi,a Hanya Ne Ma Yadinga Samun Karin Haske Gurinta Yaji Tun Washegarin Ranar Dayasaki Ruma Take Kwance A Asibiti Yaji Cewa Tasha Wuya Lokacin Haihuwarta Sannan Bayan Haihuwar Tasami Karancin Jini Kuma Ga Jininta Ya Hau Ba Bu Halin A Yimata Karin Jini Har Sai Ya Sauka Ya Ji Cewa Har Kukan Mutuwarta Anfasa Sai Daga Baya Aka Fahimci Da Ranta Likitoci Sukai Kokarin Shawo Kan MatsalarTa Har Jininta Yakoma Daidai Aka Hau Yimata Kari,kuma Tafara Dawowa Hayyacinta,haka Kuma Yakarajin Yaran Basa Da Koshin Lfya Musamman Ma Na Mijin Wanda Aka Haifa Da JUNDICE Ajininsa Dayawa Har Ake Tunanin Kila In Ba Ai Sa A Ba Sai Anyimasa Juyen Jini Da Sauran Wasu Labaran Duka Kuma Sun daga masa Hankali Dan Daliline Wanda Dangi Zasu Kara Tsanarsa Wahalar Aljihu Da Tashin Hankali Na Wuyar Da 'ya"yansa Zasu Sha Kokuma Suke Kanci Amma Me Suna Gab Da Wuce Wani Store Sai Sumoli Ta kara masa Wani Takaicin Honey Mubiya Store Dinnan A Sai Kayan Abinci Ya Dubeta Da Shakka Amma dake Ance Amarya Bata laipi, Buhun Shinkafa Daya,katon Din Taliya Biyu,indomi Katan Din Madara,galan Din Mai Uku,fari Da Ja Da Sauransu Wai duk A Cikin Sati Basu Kai Ukun Nan Ba Muka Hadiye A Cikinmu? Kai Abin Kamar Mafarkifa,fuskarta Ta Sauya Zuwa Dan Tsoro Tsoro Amma Tashare Kasan Dai Ba Araba Gidan Amarya Da Baki Ko Taron Idine Suke Zuwa Maiya Hadasu Da Kayan Tea Ko Sabulun Wanka Dana Nema Dazun BaBu? Kaga Allah Ya Baka Hakuri Bansan Abinda Kake Nufi Dani Kenanba Suna Karasowa Wani Kanti Ya Shiga Bai ko Dubeta Ba Kijirani Nafito Dan Ba Bu Kudi Sosai,yadauko Karamin Buhun Shinkafa,25kg Garwar Turkey Daya,sukari Rabin Kwano.A Leda,peak Gwangwani Uku Kayoyin Sabulu Uku,yana Kallan kifin Gwangwani Ya Wuce Bai Siya Ba,yadauki Kwallin Kus Kus faya Fahimci Taimugun Tsanar Sa Sai Bread Kwaya Daya Jal,ashe Sumoli Ta Shaka Da Safe Karin Kumallon Saita Tafasa Ruwan Zafi Kawai Ko Kayan Kamshi Ba Bu Tajuye A Fulas Ta Hada Madara Guda Ta Dire Masa Tare Da Tilon Bredin Daya Sawo Sukarin Ma Haka tadire Masa A Leda Takirashi Karin Kumallo Haka Sumoli Taita Satar Kallansa Dantaga Yadda Zaiyi,amma Yushau Ko Ajikinsa Ya Kwance Leda Ya Debi Sukari Ya Juye Fiye Da Rabin Madarar Sannan Yaja Bredi Yafara Cinsa Hankali Kwance Takaici Yai Mugun Shake Sumoli Ta Zuba Tagumi Tana Hararar Abincin Har Saida Yakusa Kammalawa Ya Ce Wai Ke Ba Kyajin Yunwane? Idan Inajin Yunwa Sai Inci kar in Mutu? Ci Karki Mutufa Kika Ce?Ba Ke Kika Girka Da Kankiba? Yo Dafa Ruwan Zafi Kawai Honey Haba Saika Ce Wasu Mayunwata Tea Da Gayan Bread Ya Ce Ba Bu Dai Kyau Fariya Wani Kamar Haka Yake Nema Baisamuba,nan Ma Takaici Ya Rufeta Ya Nunamata Kudi Naira Dari Uku,ki Bayar Asawo Maki Tumatir Da Magi Tunda Kince Ba Bu Zan Aiko Da Nama Ayi Farfesu Tadinga Juya Kudin Kamar Ta Watsamasa A Fuska Ammadai Kasan Dai Ba Bu Maganar Sayen Wani Abu Ainaga Ka Kan Bani Sama Da Dari Uku Na Sallamar Baki Bare Bamu Da Komai A Dangin Kayan Miya Yai Gaba Ya Ce Ai Juyin Duniyar Dana Gama Yimiki Magana Akansa Kenan Yanzu Inkin Yi Bakin ki Basu Hakuri Sainadawo, Yau Ko Rakiyar Bataimasa Ba Karfe Goma Sha Daya Mahahfiyar Sumoli Ta Dira Agidan Suka Kacame Da Murnar Ganin Juna Suna Zama Mamanta Tafara Mata Fadar Barin Gida Ka Ca Kaca Wallahi Almajiran Dake Tayani Aikin Ne Yau Basuzoba, Dama Wasu Almajirai Nezasu Miki Aikin Kirki Mezai Hana Ki Shawarci Mijinki Asamo Miki 'yar Aiki Kudinga Biyanta Kawai Akawota Cike Da Murna Sumoli Tace Ba Sai An Shawarce Shi Ba, Har Karfe Daya Momi Na Gidan Suna Hira Sumoli Tamike Tana Dariya To Niyanzu Mezambaki Wai Amrya Guda Azo Gidanta Tadinga Mizata Bada Ni Inkuna Da 'yar Fulawa Dan Sammin Dan Wake Nake Sha Awa Danaje Na Jefa Akwai Ragowa Bari Na Debo Miki Anti Jamila Ce Duk Ta Karbeta Tana Kyallara Ido Taganta Shikenan Ta Huta Zuba Jari Suna Fitowa Tsakar Gida Yaron Da Yushau Ya Aiko Kawo Nama Yazo Bayan Fitar Sa Momi Ta Ce Aidanasan Farfesu Za A Sha Dana Bari Gobe Nazo, to Ko In Dibarmiki Danyene? Ayi Haka? To Ai Bazanki Ba Nan Sumoli Ta Kwashe Rabin Nama Ta Bata Itakuma Ta Karbe Tana Godiya Kamar Gadon Tsohonta,hakama Yau A Asibiti Ya Wuni Dadadi Badadi Ruma Dai Jikinta Yafi Na Jiya,dan Yau Ido Biyu Ta Wuni,kuma Har Akanyi Musayan Gajerun Hira Da ita, ya Ci Gaba Dashan Kyara Wajen Alhji Bayan Kyarar Kuma Yakemiko Masa Duk Wata Bukatar Kudi Da Ta Taso Ya Biya,ciki Harda Karamin Alhaki Pure Water Da Masu Dubiya Zasu Sha,akan Kayan Jarirai Kuwa Da Hafsat Alhji Ya Jonashi,waitayimasa Lissafin Wasu Makudan Kudade Wanda Suka Sashi Mikewa Tsaye Ya Kurma Mata Tsawa,tundani Ba Manajan Banki Bane Irin Mijinki,me Zai Hana Kikai Ni Kasuwa Ki Sayar,kamar Ta Fashe Dadariya,ya Buga Tsaki Yamike Ya Barmata Wajen Tafito Tana Dariya Tana Cewa Ina Ruwan Yaya Bala'i Saika Ce Na Kashe Masa Yar Fari Washe garin Sumoli Tanemi Binsa Asibiti Don Ta Dubo Ruma Baimusa Mata Ba Amma Yau Yayi Niyyar Bazai Wuni A Asibitiba Kasuwa Zai Wuce,ya Ce Mata Inafatan Kinsanya Ragowar Naman Nan A Gidan Kankara A Sanyaye,wanne Naman? Ragowar Na Jiya Mana,dan Nasan Yafi Karfin Cikin Mu Lokaci guda, Cikinta Yakada Kamar Ta Cemasa Eh Yana Gidan Kankarar Saikuma Ta Tuna Kalatar Sa Akan Nama Kila Suna Da Ta Cemasa Ba Bu Wani Ragowar Nama Wallahi Dan Jiya Momi Tazo Narasa Abinda Zanbata To Lokacin An Kawo Naman Nan Kawai Saina Dibar Mata, Saboda Da Kudinki Nasiyoko? Mamaki Ya Cikata Momin Tawa Yushau? Momin Taki Ni Gaskiya Kifadamata Banasan Yawan Zirga Zirga Datakemana A Gidan Nan Ta Dakata Haka,nandanan Sai Ga Sumoli Na Hawaye Bakinta Na Ta Karkarwa Tana Ce Honey,honey,,,ya Cemata Ni Bansan Rainin Hankali Malama Ko Kina Nufin Ni Bawan Gidan Kune? Ke Kanki Kinsan Abinda Ake Min Ba A Kyauta Min Har Yaushe Akai Auren Da Mahaifiyarki Zata Mayar Da Gidannan Na Kawarta? Inafa Sane Tazo Gidan Nan Yakai Sau Takwas To Me Take Zuwa Yi? Sumoli Takasa Magana Kallonsa Kawai Take,dan Bata Taba Tsammanin Lambar Rashin Mutuncin Yushau Yakai Haka Ba Wai Gyatumarta Yake Zagi . Kwanaki Sukadinga Dauki Daidai Suna Wucewa Ruma Nasamun Sauki Yaranta Nadan Warwarewa Duk Da Har Yanzu Ba A Janye Tunanin Yiwa Namijin Juyen Jiniba Dazarar Yakara Wasu Kwanaki,yushau Kuma Nata Cin Kwakwa Wajen Alhji Na Kyara Da Kawo Kawo... . Dan Aunty.GORAN DUMA (P 44) . Dan Ma Har Yanzu Alhjh Bai Debo Masa Maganar Bashi Ba Amma Aljihun Yushau Yayi Mugun Girgiza Ta Yadda Har Kudin Mutane Ya Shiga Tabawa Kuma A Bangaren Sumoli Wadda Itama Take Huro Masa Wuta Wadda Har Zuwa Yanzu Yakejin Kunyar Yaji Nadamar Aurenta Ko Da Acikin Zucine Duk Yadda Yake Zaton Sumoli da Tarbiyya Da Saukin Kai Tare Da Bin Miji Saboda Rashin Wayewar Kan Boko Bata Doshi Nan Ba,amma Har Yau Ya Rasa Dalilin Dayasa Yakejin Kamar Bahaguwar Fahimta Yakemata Yanzu Kam Yakosa A Sallami Ruma Yasamu Sauki Ta Wurin Alhji Ana Gobe sati Da Haihuwar Ne Alhji Yakirasa Takanas Gida Ba Bu Irin Adduar Da Bai Karanto Ba Amma Bata Ciba To Malam Ko Daga Sunan Nan Za Ayine? Banga Hakika Ba Gobe Kuma Sati Da Haihuwar Hakan Kuma Ya Tsorata Yushau Gudun Bacin Rai Ya Ce Yakarka Ce Ya Sheko Karya Alhjh Na Siya Suna Can Kasuwa Na Ce A Bar Su Gobe Da Safe Sai Akawo,alhji Ya Ce To Ko Danaji Saidai Kuma Batun Sunan Daka Rada Wa Jariran Ko Bakai Musu Hudubane,? Alhji Ainazaci Anyi Musu? Uban Waye Zaimusu? Waka Ajiye Bawanka? Cikin Bacin rai Alhji Ya Ce Ai Dama Hakane Sai Mutum Ya Karta Son Zuciyar Sa Yana Fakewa Da Allah,tabbas Komai Nufin Allahne Amma Ka Bar Mutane Masu Hankali Sui Wanna Togaciyar Bawai Irinka Masu Butulcema Rahamar Ubangijiba Ubangiji Yaimaka Baiwar Mace Tagari Dan Ni Na Maka Dolen Aurenta Kasakomin Ita Kazabi Wadda Na Hakikance Fitinace Ga Rayuwarka,wallahi Yushau Ba Dan Umarnin Musulunci Na Haramtawa Musulmi Gaba Ba Da Na Rantse Da Raba Hanya Zanyi Dakai Bani Ba Kai,to Amma Bazanyi Haka Ba,na Barka Da Wannan Duniyar Wadda Tafi Bagaruwa Jima Duk Dakai A Gurinka Tasamu Don Kana Iya Samun Abinda Kakeso Ruma Ce Mun Rike Abarmu Munai Mata Adduar Samun Mutum Na Gari Wanda Zai Ga Mutuncinta Yaga Namu Hawaye Wani Na Bin Wani A Kuncin Yushau Bai Taba Riskar Bakinci Irin Na Yau Ba,kuma Baita Ba Zaton Fushin Da Alhji Keyidashi Yakai Haka Ba Donshi A Ganinsa Laifinsa Baitaka Kara Ya Karya Ba,amma Gashi Har Mahaifinsa Naneman Yimasa Baki Dole Ya Maganu Yadinga Bashi Hakuri Wanda Baiya Cin Galabar Alhjinba Ya Ce Hakuri yazam Dole Yushau Allah Ne Ya Jarrabeni Da Zamowarka Jinina Bayan Na Tsani Mutum Mara Uzuri Irinka,abinda Kawai Zan Tunamaka Shine Mai Kyautatawa Za A Sakamasa Da Kyautatawa Mai Munanawa Kuma Za A Munana Masa, na Mayar Da Ruma Alhji Yushau Yafada Cikin Sheshekar Kuka Haba Alhji Yakara Tunzura Yamaka Masa Harara Ya Ce Zan Kwantara Maka Zagi Wallai Ai Yanzu Ba Matarka Ba Ce Bare Ka Mayar,kaiko Matarka Ce Ka Mayardin Wallahi Saina Maka Ka A Kotu Da Yushau Yakasa Magana Saiyamike Zai Bar Falon Alhji Ya Ce Malam Bakaimin Maganar Sunan Yaran Da Goronsu Ba Ya Tsaya Batare Da Ya Juyo Ba Zanturo Da Goron Da Safe,sunan Kuma A Bawa Ruma Zabi,alhji Ya Ce Bazata Zaba Ba,arasa Abin Arzikin Daza Ayi Mata Sai Zabin Suna? Na Yarda 'ya"yanta Ne Tunda Ita Da Haifo Dan Haka Idan Rabonta Zataiya Haihuwar Goma A Bayansu To Ta Sanya Sunan Datakeso A Inda Akasan Darajarta Saboda Haka Idan Ba 'yan Nanaye Kakeson A Rada Musu Ba Ka Tsaya Ka Zabarmusu Wani Matsanancin Kishi Ya Tokaremasa Kirji Wai 'ya'yan Dayakeji Dasu Kamar Tsoka Daya Amiya Su akema Kishiyoyi Goma Yanzu? Kuma Bama 'ya'yansa Ba, 'ya'yan Wani Gardin,fuskarta Yanuna Bacin Rai Ya Ce Asanya Wa Macen Hamida,namijin A Kirashi Auwal Ba Bu Ubanda Zaisa Masa Auwal Wallahi A Gidan Uwar Wa Ya Ciyo Auwal Din?In Ma Izgili Kake Za A Haifi Auwal Din Ne Amma Bakai Zaka Haifa Ba,yushau Yakara Kulewa Ya Ce To Asamasa Auwal Yai Gaba Tunkafin Yatashi Motar Sa Yakira Wani Abokin Cinikinsa Ya Bidi Bashin Dabbobin Yanka Sannan Ya Koma Agadasawa Ya Siyo Goro Ya Tsaya Wani Kanti Ya Sai Alewa Duk Ya Watsa Bayan Mota Yana Mita Allah Ya Rufamin Wannan Asirin Idan Ma Anayi Ne Don A Tozartani, ****** Wannan Dalilin Ya Sanya Ya Dauke Kafa Daga Gidan Kuma Ko A Waya Baya Gaida Kowa Bare Afadamasa Ba Bu Dadi Ko A Tambayeshi Wani Abu Saidai Fa Rayuwa Na Kara Kuntata Agareshi Dankuwa A Inda Bai Hanawa Kansa Zuwa Bama Wato Gidan Nasa Yanda Sumolinsa Wanda Ya Fahimci Tafi Kashi Doyi Sumoli Raina Kama Kaga Gayya Ce,wadda Kuma Yake Zargin Yafada Tarkonta Na Abindayaketa Yawanji A Bakin Mutane Wato So,ba Ya Iya Tsawatar mata Ruma Da Yaranta Suka Ci Gaba Da Samun Lfya Cikin Horewar Ubangiji Tare Da Kyakyawar Kulawa Da Suke Samu Amma Badinin Zuciyar Ruma Na Mugun Ciwo Dangane Da Banzantarwar Da Yushau Kemusu Ita Da Yaranta,ayanzune Kuma Take Kara Tabbatar Wa Kanta A Boye taSha Saka 'ya'yanta Taita Kukan Rashin Dacen Uba Wanda Baisan Darajar Suba A Matsayinta Na Sikila Ta Tabbatar Duk Sikila Satinta Biyar Da Haihuwa Maimuna Yayar Hafsa Ta Haihu Son Biki Irin Namata Sai Suka Kulla Ai Hadawa Zasuyi A Yi Biyan Bashin Bikin Sunansu Hamida Rana Guda Inda Maimuna Zata Baro Gidanta Lokacin Sunan Su Hadu Anan Gida Ayi Taron Sunan Alhji Badan Yasoyima Yushau Mugunta Ba Ba Bu Abinda Zaisa Ya Laminta Amma Da Sauri Ya Yarda Yakuma Aiki Jakada Mubarak Takanas Yakiramasa Yushau Wanda Ya Amsa Cikin Kaduwar Hanta Da Cewa Gobe Da Yamma Zaizo,ya Manta Dadare Bai Gama kasa Kayan Karin Kumallo Ba, Wato Bai Siyo Madara Ba Asafiyar Ranar Sumoli 'yar Kwaya Saita Tafasa Masa Ruwan Bununsa Ba Bu Ko 'yar Citta Takawo Masa Yaso Yashareta Saiyagama Rashin Hakadai Sukaita Jifan Kawunansu Da Bakar Magana Daga Karshe Takare Ta Ce Yaufa Sauran Kwana Uku Sunan Gidansu Hakane,yaushe Zaka Gidan? Ya Ce Yauma Dadare Zani,ta Ce Idankaje Inkasami Hafsat Ko Asiya Katambayi Su Bayanin Ankon Dazamuyi,ok, Kawai Ya Cemata Ta Ci Gaba Dayimasa Lissafi Ya Fara Bata Amsa Ranshi Inyai Dubu Ya Baci daga Nan Suka Daura Daga Inda Suka Tsaya Hajiya Ta Ce Ashe Da Gaske Kazo Har Ina Karyatawa Ya Gaidata Tare Da Ce Eh Naga Gidan Cike Da Mutane Shiyasa Ban Karasoba,suka Dubi Juna Ita Da Alhji Yo Waye Bakonka A Bakin Alhalin Duk 'yanuwankane, Haba Ke Kuwa Ai Dole Da Kunya Mutum Ya Fita Zakka A Dangi Idan Yana Da Kunyarba Inji Hajiya Alhji Yakuma Cewa Haba Ko Baiji Kunyarmu Kashin Duwawunsa Daya Wulakanta Ba,ai Zaiji Kunyar Uwar Ruma Wadda Ta Wanke Diya Taba Shi Yanemi Kashewa Don bayaso,,wallahi Kuwa Kaga Tun Tanajin Wai Wai Yanzu Taga Dahir Kwananta Biyu A Gidannan Bata Keyar Ka Ba Kazo Ganin Ya'yanka Ko Da Kuwa Kazo Yi Uwar Su Sannu Dashayar Dasu Ba Tab!Ai Sai Mutum Yasan Mutunci Zaiyi Saida Alhji Yainisa Da Cin Abincinsa Yadago Ya Cemasa Karkace Banyimaka Tayi Ba Idanzaka Ci Bismillah Naga Kana Wani Kikkifta Idanu Don Bukata Yushau Na Matukar Bukatar Abincin Amma Yanayin Tayin Ne Yaimugun Kular Da Yushau Ya Girgiza Kai Musamman Daya Tuno Dangantakar Sa Da Alhji A Can Baya Farkon Aurensa Da Ruma Yadda Alhji Kenan Nan Dashi Kamar Abokinsa Ya Bashi Kyautar Kudi Yafi Akirga Yaimasa Wasa Suci Daga Kwarya Daya Amma Ayanzu Alhji Ya Zama Kamar Wani Mugun Ubangida Da Yaronsa,sanda Ya Cinye Abincinsa Tsab Ya Ce Yadai Malam Nifa Zanshiga Ciki Yamike Yakwaso Masa Rasitai Ya Zubemasa Ka Duba Kwanan Wata Da Kyau Iyalanka Din Nan Ne Suka Kokoma Asibiti Idan Yushau Garau Yake Dubasu Sunakara Rikitamasa Lissafi Daya gaza Saiyaje Fasu A Aljihu Yadubi Alhji Ya Ce Shikenan Za A Kawo Kudin Gobe BaBu Laifi Dama Kudin Wancan Asibitin Ma Baka Gama Biyana Ba Inji Alhji Ya Ce Baka Fa Sake Magana Akan Shawarar Nan Ba Tun 'yan Kudin Daka Bayar Baka Kuma Bayarda Ko Sisiba, niyanzu Ba Kudine Dani Ba, "to Waye mai Kudin"? Cewar Alhajin........ . Hehehe... Pls inda mai kudu a hanu ya taimaki Yushau mana.? Ko karokaro zamu masa ne mai biyar mai goma? Lol.z Dan Aunty GORAN DUMA (P 45) . . Kaga Malam Wannanfa Umarnin Ubangijine Ba Bulus Na Kwaso Maka Inci Ba,ruwankane Kayi Ko Ka Bari,kanka Ka Zalunta Bawaniba mu Sai mubarka Da Allah, hawaye Yafara Zarya Yushau Najin Mahaifinsa Na Neman Yimasa Baki Akan Alamarin Da Zai Iya Daukemasa Nauyi Shi Dayake Dancikinsa,wallahi Tallahi Dagaske Nake Banida Kudine, Ba Bayarwa Bane Banasanyi, aishine Na Ce Saimu Barka Da Allah Kokuma Wallahi Ka Kwashi 'ya'yanka Kujeko Nonon Akuya Ne Ku Dunga Tatsowa Kubasu Allah Ya Baka Hakuri Ayanka Min Abinda Akeso Na Bayar A Wata Zandinga Bayarwa, Kasami Hajiya Ta Yankamaka,ya Ce To Godiyanake Allah Yakara Girma Alhji Yakara Koro Wani Lissafin Ga Wata Dawainiyar Ma Data Billo Kasan Mata Da Biki Yaimasa Bayanin Sunan Daza Ayi Kashiga Hajiya Taimaka Lissafin Nidai Ankarbarmin Dubu Ashirin dina Dazu Saika Bani Abina Yanzu Saboda Takaici Ya Zira Hannu Ya Ciro Kudi Yatarar Gabadaya Dubu Bakwaine Ya Zari Dubu Daya Yamikama Alhji Shida Karike Wadannan Zanciko Maka Ragowar Gobe,a A Ka Mayarda Ita Kabani Har Ita Dubun daka Cire Haka Alhji Yahada Duka Bakwaidin Ya Amshe Ya Ce Dafatan Zaka Biyamu Bashinmu Zuwa Gobe Saboda Shi Dai bashi Nauyine Dashi,idan An Sauke A Huta, Yushau Yashiga Gurin Hajiya Taimasa Nata Lissafin Ya Fice Yanazuwa Gida Da Tsohuwar Yunwar Sa Yaga Sumoli Koruwa Bata Bashiba Takwaso Masa Kayan da taje Kasuwa Tasiyo Ya Ce Wakika Tambaya Dazaki Fita? Haba Darling Saika Ce Wata Matar Kauye,aransa Ya Ce Wai Wannance Wadda Ya Zabo Dan Yanason ko Soron Kofar Gidansa Saitanemi Izininsa Kuma Inya Ce Karma Tataka Soron Zata Yarda Ya Isa,ba Abinda Yafado Masa Sai Kalmar Kar She Na Mahahfinsa Wato'WADDA NA HAKIKANCE FITINACE AGAREKA. Saboda Bacin Rai Da Kyar Yake Taunar Abincin Itako Ta Tuntsire Masa Da Dariya,.,kai Honey,ci A Hankali Ba Guduwa Zaiyiba, ******* Ance mai Hankali Baya Damuwa Da Lamarin Duniya Domin Damuwa Da Bacin Rai Basa Gusar Da Masifa,ruma Ta Gwada Wannan Falsafar Kodon Tsira Da Cikakkiyar Lfya Amma Tagaza Iyawa,duk Yadda Taso Ta Fitar Amma Ta Gaza Iyawa,duk Yadda Taso Tafitar Da Wulacinda Yushau Kemata Aranta Ruma Kam Ita Tasan Halinda Take Ciki Allah Ma Yasan Sun Sameta Kuma A Muhallinda Ya Dace Wasu Masu Sikilar Yaya suke Musamman Ma Idan Abin Yahadu Da Rashin Gata Ita Tasan Abinda Suke Bukata Idan Suka Galabaita Ita Tasan Da Cewar Akwai Ciwansu A Duniya Ba Son jiki Bane Lallai Tunda Itasuka Sama Mai Irin Ciwansu Allah Yaimusu Babban Gata BAYAN WATA TAKWAS Allah Mai Yadda Yaso Watannin Su Hamida Tara Cif Da Haihuwa Allah Ya Amshi Ahmad Bayan Jinyar Kwana Daya Baisan Inda Yake Ba Bayan Zace Zacen Akadinga Yi Ruma tashiga Cikin Wani Hali Na Kidimewa Tayi Kuka Sosai Haryakai Ce Iyayan Sun fahimci Ba Kukan Rashin Ahmad Ne Kawai Ruma Take Ba Harda Narashin Auwal Tare Da Wani Abu Na Wulakancin Da Yushau Yakemata Wanda Tunda Ya Daukesu Sau Daya Baikara Daukansu Ba,har Bayan Rasuwar Bata Yarda Tagaisa Da Yushau Ba Haka Dai Ruma Takasance Cikin Jimami Inda Safiyar Watarana Taje Gurin Hajiya Da Kukanta Ta Ce Hajiya Ki Rokarmin Alhji Inason Komawa Abuja Dan Nikam Nasan Kano Bata Karbeni Ba Hajiya Ta Tausayamata Kwarai Alhji Dakansa Yazo Dakin Ruma Inda Yaga Tana Gasa Mata Mukamukinta Ya Ce Yanaga Kina Gasata Ta Ce Masa Ta Dameni Da Kuka Kuma Nan Take Ta Bawa Shiyasa Nake Gasamata Ya Ce Asha Allah Yasauwake Yasa Kaffarane In Angama A Miko Min Ita Tagama Ta Sauya Mata Kaya Tamika Masa Yakarba Yana Zolayarta Bayan Yajima Adakin Har Hamida Tai Barci Ruma Ta Amsheta Ta Kwantar Da Ita Alhji Ya Ce Kwana Nawa Kikesa Ran Zaki A Abuja? Azuciyarta Ta Ce Wai Daga Zuwa Karatu Sai A Kaga Wa Mutum Zaman Dindindin? Takasa Magana Ya Ce Sati Daya Ko Biyu? Yai Gyaran Murya Banji Dadin Yadda Furucin Dakikai Amfani Dashi A San Zuwa Abuja Ba,na Cewa Kano Bata Karbekiba Ki Caje Maganar Nan Da Kyau Zaki Tarar Da Kure A Cikinta, Domin Ubangiji Bai Hukunto Kaddarar Mutum Rataye Da Gurin Zama Ba,jikinta Sanyaye Ta Ce Astagfurullah, yadago Ya Ce Yauma Zansake Zuwa Miki Da Kokon Barar Alfarma Ina Mai Cike Da Yakinin Jincewa Alkhairinki Da Tawakkalinki Bazai Saki Gaza Yimin Ba Gabanta Yafadi Aranta Ta Ce Allah Yasa Alhji Ba Komawa Gidan Yushau Zaice Ya Ce Lallai Kinzo Kano Cikin Farinciki Da Wani Abu Na Koshin Lfya Abubuwa Dayawa Sunfaru Wadanda Allah Ya Tsarasu Danai Sila Kamar Auren Yushau Wandayake Cikin Kaddarorinki Marasa Dadi Har Yanzu Ina Nadamar Da Kasa Yafewa Kaina Kuma Na Tabbatar Nadamata Bazata Gusheba Idan Ba Ganinki Nai Cikin Farinciki Ba Amma Yanzu Ruma Saiki Kinkimi Min Maganar Komawa Gida? Kiyi Hakuri Kimin Alfarmar Ki Bani Lokaci Mui Addua Mumika Wa Allah Kokenmu Mujira Hukuncinsa Nayi Alhji Tafada Cikin Tawakkali Da Rarrauniyar Murya Hakikatan Bataji Dadin Yadda Yake Dora Wa Kansa Laifi Ba Acikin Abinda Yushau Kemata Dantana Da Yakinin In Ana Bada Numfashi Alhji Zai Iya Bata Nasa Saboda Damuwa Da Kulawa Ta Ce Masa Amma Inason Kai Ziyara Wannan Ba Bu Laifi Kijekiyi Wata Daya Ko Biyu Ki Dawo Allah Yaimiki Albarka Amin Kwana Biyu Tsakani Ta Hada Kaya Ta Nufi Abuja, ****** Yushau Yadawo Kasuwa A Gajiye Karfe Shida Amma Har Shida Darabi Ba Bu Alamar Sumayya Allah Kana Gani Cikin Tausayin Kai Goshin Magaruba Ta Shigo Tare Da Almajirai Uku Ta Ce Ma Almajiran Kai Sharemin Tsakar Gidan Da Kicin Kai Gyaramin Falo Ka Goge Tayil,kaikuma Yimin Wanke Wanke Ka Feremin Doyannan Don Wancen Hayatun Saiya nemi Dagamin Hankali Akan Abinci,wata Bakar Zuciya Tataso Masa Amma Haka Yashare Yai Alwala Yatafi Massallaci Dan Yatuna Lokacin Ruma Ko Adama Bata Isa Ba Shi Abinci Ya Ci Ba Amma Gashi Yanzu Ashe Har Girkin Almajirai Yakeci, Bismillah Ga Abinci Yaduba Soyayyar Doya Ce Mai Fulawa An Kawata Ta Da Farin Kwai Dajan Tumatir Tai Shar Kamshi Maidadi Natashia Amma Saiyarufe Yana Toshe Hanci Lfya Kake Wani Toshe Hanci Hayyatar Tawa Batakainan Ba Dahar Zanci Jagwalgwalon Almajirai Nandai Suka Hau Sama Suka Fado Ita Tana Korafin Yaki Kawo Mata 'yar Aiki Shikuma Ya Cemata Ke Wannan Dama Zamanki Kikai Agidanku Kika Mutu Ba Bu Aure Da Gangan Ake Cutar Mutane Ake Damfarar Musu Kudi Azuwan Ba Aso Kui Zurfin Ilimi Ashe Rabuwa Da Ja'ib Ake, tuni Sumoli Ta Barke Da Kuka Ayya Inza Ai Wasa Ayi Darling Amma Banda Tsikarar Uwar Miji, yanzu Dan Allah Audine Zaiwa Talle Gori? Ai Wallahi Garani Iyayena Suna Sona Har Ma Zasu Inganta Rayuwata Sun Damfara Wa Wani Amma Kaifa? In Bandani A Duniyar Nan Kafadamin Wake Sonka,? Kuma Wallahi Sweety Barikaji Ba Fa A Kauye Muke Ba Dazan Zauna Kadinga Cin Zarafin Iyayena Shi Zaman Duniya Susar Jakine Yimin In Maka Allah Inka Ci Gaba Da Zagin Iyayena Zan Rama Don Iyaye Basufi Iyaye Ba,kaima Danaka Iyayen,kewofintar Dakai Kaso Abinka Bareni Da Nawa Ke Lelena, ai Kuwa Zanfara Turamiki Ashar Daga Karamin Alhaki Sweety Da Darling Dindakike Cemin Tamike Tana Dariya Har Da Sunkuyawa Har Takai Dakin Baccinsa Ta Ce To Honey Turamin Ashar Din Mana Iyayenmu Daya Haka Dai Rayuwa Tadinga Tfya Kwanaki Suka Dinga Karewa Har Takai Watara Na Yushau Ya Zarce Gidansu Wanda Rabonsa Da Zuwa Tun Rasuwar Ahmad Dakuma Niyyar Gyara Dangantakar Sa Da Iyayansa Kafin Tunanin Hukuncin Dazai Duka Akan Sumoli, Gaisuwar Sa Ma Da Kyar Hajiya Ta Amsa,yajima Zaune Gabanta Kala Batasake Ce masa Ba Yatuna Ba Buwani Abinda Zai faranta musu Rai Irin Ruma Dan haka Yai Niyyar Yaudarar Su Hajiya Ina Rumaisau Banji Motsinta Ba? Hajiya Kamar Ta Kifa masa Mari Saboda Haushi Anan Tahadiye A Takaice Ta Ce masa "Bansaniba"..... Ya dubo dayan gefen yace Dan Aunty ina Ruma? Hehehe... Jama'a wace irin amsa zan ba Yushau? . Dan Aunty.GORAN DUMA (P 46) . . Yai Dif Jiki A Mace Yanufi Kicin Wajen Talatu, Rumaisau Sunje Unuwane? Eh Suna Abuja, da Mamakinsa Kwana Nawa?Watansu Hudu,yakarajin Rudewa An Tafi masa Da 'ya Batare Da Saninsa Ba,ziyara Ko Zaman Dindin?Daga Ziyarar Wata Biyu Gata Tana Neman Haure Wata Hudu Saboda Kaguwa Da Tambayar Atakaice Take Amsamasa, Saidai Naji Hajiya Nafadin Kila Cikin Watan Nan Su Dawo Yai Sallama Ya Bar Gidan Ya Wuce Gidan Maikudi Abokinsa Yakaimasa Koken Sumoli Yaimasa Nasiha Da Shawarwari Akan Haka, hakadai Sumoli Taci Gaba Da Gara Yushau Yarame Ya Lalace Hartakai Watarana Hatsaniyar Takai Ga Yushau Ya Zageta Tarama Da Kaima Tir Dakai,kawai Kaita Tsinemin Mugun Mutum Kawai Tunda Na shiGo Gidanka Nakasa Gaba Na Kasa Baya Kullum Cikin Zulumin Bala'inka Na Ke Ashe Duk Zakin Bakinka Damin Ina Waje Na Yaudarane Aurenka Cike Yake Da Rashin Kwanciyar Hankali Kayan More Rayuwa Ba Bu Saita Fashe Da Kuka, to Fita Fita Nasake Saki Daya Kitafi Gidanku Ta Ce Wallahi Tallahi Baka Isa Ba,ba Bu Inda Zani Na Rantse Da Allah To Ki Zauna Watarana Zanyi Ajalinki Don Bazan Jure Wannan Rashin Tarbiyar Ba ***** Innar Ruma Ta Kware Dasanin Hanyoyin Hilatar Mutum Da Tattalinsa Ruma Kam Da Hamida Suna Samun Kulawa, Duk Azaman Da Ruma Tai A Abujane Karance Karancenta Yadawo Kuma Daidai Wannan Gabarne Tasami Damar Zama Marubuciyar Tauraruwa Jaridarta Ta Aminiya Tun Tana Abuja Bisa Sahalewar Mominta Alhji Ya Gaji Da Kawaici Yatanka Mata Rumaisau Kin Saba Alkawari Fa Tai Dariya Cikin Satin Nan Ko Na Sama Zandawo, Dazaki Hakuri Kidawo Danafi Kowa Farinciki, Wallahi Zandawo Alhji Amma Ina Neman Alfarmar Barin Hamida Wajen Momin Domin Ta Saba Da Ita Harma Tafi Damuwa Daita Akaina BaBu Laifi Inkin Tsayar Da Ranar Dawowa Kisanar Dani Nazo Na Daukeki Na Gaisa Da Hamida Tunda Nan Za A Barota Sukai Sallama Ranaku Suka Dan Wuce Inda Rayuwar Sumoli Da Yushau Bata Canza Daga Yadda Take Ba Shidai Baikulata Itakuma Tanasan Yamaidata Yushau Kam Baidawo Wa Gida Sai Cikin Dare Itakuma Sumoli Data Lura Da Hakan Safiya Nayi Yafita Itama Ta Dasa Kwalliyarta Ta Shiga Dakinsa Tadauki Kudi Ta Shi Ga Gari Adalci Daya Yaimata Bai Kullemata Sito Ba,kuma Yana Ajiye Kayan Abinci DaiDai Bukata Sannan Yasan Tana Zarar Masa Kudi Dari Biyar Ko Dubu Daya, Duk Yashare Danyaga Bata Daukar Wanda Yafice Kima Sumoli Sunyi Wata Daya A Haka Tafara Laushi Tare dayin Girki Dashi A Wani Rana Ta Boyewata Kawarta Da Sukai Rikici Da Mijinta Yakoreta Gidansu To Tana Tsoron Mahaifanta Kawai Sai Sumoli Ta Bata Mafaka A Gidan Yushau Baisaniba, Inda Bayan Mahaifinta Yagano Tana Gidan sukazo Tafiya Da Ita Da Cewar Zasui Karar Sa Saboda Aje Matar Aure Da Yai A Gidansa Kaitsaye Falon Yushau Ya Dosa Tare Da Iyayan Samira Ya Kwankwansa Kofa Yana Kwada Mata Kira Ta Fito A Firgice Yadaka Mata Tsawa Ina Yarinyar Danagani A Gidan Nan Ta Ce Ai Batanan Tunjiya Au Shekaranjiya Tatafi Yasheketa Da Mari Yashige Falon Ya Tadda Mata Sama Da Goma Sunata Cashewa Duka Yakorasu Itakuma duk Aranar Yushau Yakara Ma Sumoli Saki Daya Takara Daukan Alwashin Bazata Je Koina Ba Ranar Kam Yushau Bai Runtsa Ba,kuma Yatabbatar Alhakin Rumane Yakamashi Ita Yakewa Kallon Masifa Ashe Ita Rahamane In Aka Jerata Da Sumoli,haka Sukaci Gaba Inda Sumoli Takara Canza Salon Karkato Da Hankalin Yushau Gareta Amma Yagagara Haka Yushau Yakara Komawa Ga Abokinsa Maikudi Wannan Karan Gurin Mahaifiyar Ta Sukaje Amma Me Bata Wani Daraja Koken Nasu Ba,tadai Ce Zatai Mata Fada **** Maman Ta Cemata Dazu Da Safe Sai Ga Mijinki Yakawo Kararki Sumoli Ta Ce Ashenan Yayo Aima Haryasakeni Ummanta Ta Ce Ashe Munafikine Inaganinsa Haka Ta Ce Karkidamu Suka Zarce Can Wajen Wani Boka Sai daf Da Magariba Tadawo Tagama Abinci Aka Bade Masa Abinci Da Magunguna Haka Dai Zaman Nasu Ya Ciga Ba Har Suka Sake Share wata Uku Batare Da Anji Kansu Ba Sai Halin Sumoli Yafi Nada Tambaya Zuwa Anguwa Kullum In Ma Bai Barta Ba Zatatafi , Kayan Abinci Taiyanda Taga Dama Dashi Hartakai Sumoli Tanason Yushau Ya Biyamata Makaranta Tadora Daga Indata Ta tsaya To Ashe Dai Tana Jika Tunda Har Sumoli Ta Furta Maganar Komawa Makaranta Hakan Dai Baisamu Ba Danko A Mafarki Bazan Lamunta Ba, Na Lura Idan Na Biyemaki Kwanan Nan Zanyi Mutuwar Tsaye, Awata rana Sumoli Takaremasa Rashin Mutunci Da Gori Kan Kayan Abinci Ya Ce Mata Tir Tir Dake Sumoli Kin Munana Halinki Ni Allah Yayemin Jidalin Aurenki Idan Dagaskeni Bana Rufamiki Asiri Ki Sami Mai Rufamiki Idankuma Ni Ni'imane Atare Dake Allah Na rokeKa Daka Janye Miki Ni Kozaki Hankaltu,na Tabbata Matukar Inatare Dake Kece Ajalina Ya Fice Yafada Motar Sa Yatuno Ruma Yadda Yake Munana Mata Da Dukkan Gabbansa,ya Hantareta,ya Bautar Da Ita,ko Bata Da Lfya,yaki Kula Da Lfyarta,yaki Taimaka Mata Alokacin datake neman Taimakonsa,yaha na Kudin Cefane Koda Bai Aje Kwayar Hatsiba Amma Ko A Fuskarta Bazata Nuna Fushiba Balle Harshenta Ya Furta,kuma Bata Kasa Kyautata Masa Ba Bare Ta Kauracemasa, Unguwa Kamsaita Share Wata Biyu Bata Leka Kofar Gidanba,kuma Dukda Tana Da Alaka Da Masu Hannu Da Shuni Bata Taba Ganin Abu Ta Ce Asaimata Ba Ahaka Take Binsa Saudakafa Har Lokacinda Gangandinsa Takadamasa Kidan Watsar Da Ita Yazabi Sumoli Ya Biyemata Yawatsar Daduk Dangi To Yau Ga Kangin Rayuwar Dayashiga Ya Bata Dakowa Nasa Adalilin Sumoli Waidamezaiji? Da Fushin Mahaifinsa? Ko Da Matsin Rayuwa? Ko Kuma Masifa Da Balain Ta Na Cikin Gida? Yaukam Da Tunanin Ruma Yawuni Musamman Dayake Ganin Akwai Sauran Damarta Nakomawa Tunda Saki Daya Yaimata Kuma Ba Maganar Aurenta Da Wani Allah Yadubeshi Tadawo Rayuwar Sa Ko Farinciki Yadawo Rayuwar Sa Har Yake Ganin Zai Cire Nauyi Da Kunya Da Tsoro Ya Tunkari Alhji Da Hajiya Har Ita Ruma A Gobe Yana Iya Yiwa Abuja Tsinkesu Yanke Masa Duk Irin Hukuncin Dasukeso Indai Zasu Dawo Masa Da Ruma Yaje Gidansu Da jin Kumajin Zai Motsa Kwanji Amma Sai yatarar Da Alhinin anyi Rashi A Rogo Saboda Haka Yahadiye Abinda Ya kawoshi Da Safe Yanufi Rogo Ashe Da Rabon Zai Tsinka Dami Akala Wato Tsinto Ruma... <==KAN DUTSE!==> Karasowar Yusha'u gare ta da 'karar shigowar sa'kon murya karo na biyu a wayarta ya katse mata tunanin JIYANTA wanda ba ta dire ba. Ta kasa hankalinta biyu, kallon Yusha'u da damuwa da sakon wayarta. Ta san sa'kon MAHAUKACIN MASOYI ne, mahaukacin da wani lokaci zuciyarta ke hararo basajar Yusha'u, amma yanzu yana son 'karfafa shakkar in shi din ne, don ga shi a tsaye, ga kuma sakon ya shigo. Yusha'u ya gyara tsayuwa lokacin da ya gaji da cika da dokin abin da ke ranta game da shi ya zarce wannan kallon 'kurullar da ta ke masa. Kamar ta san abin da ransa ya raya masa, ta kawar da kai a sannu tare da shan kunu, sai ya shiga taitayinsa, amma da yake kamar bai gaji iya rarrashi da siyen soyayya ba, iyakar maotsinsa sai ya 6uge da son kyautata murya ya ce. "Ban san al'adar da ke tilasta miki zuwa kan dutsen nan ba, kuma duk sanda kika zo sai an biyo bayanki". Ko kadan ba ta yi niyyar zata amsa ba, sai kawai ta 6uge da zuge jakarta ta zura wayarta, sannan ta fara tafiya tana cewa. "Dan ma ba a dare a gida". Ya biyo ta cikin daga 'kafa saboda son su jera. "Kin fada za ki kwana ne?" Har zata amsa da fatar baki sai kuma ta ga asarar hakan, ta girgiza kai tare da duba agogo.. . Chakwakia.. Ga Yushau ga Mahaukacin masoyi ga kuma Dan Aunty? Ko ya zata kare. Amma dai ni hankaki na akwan ce yake tunda tace in ba niba sai rijiya, lol. Sai kuma gobe idan Allah Ya kai mu. Dan AuntyGORAN DUMA (P 47 ) . . Karfe shida saura kadan za su kai wajen isha'i ke nan kafin su je gida. Ba wannan ya fi yi mata ciwo ba, sai yadda Yusha'u ya yi damarar dole sai sun tafi tare, ba dan Hajiya ta yi mata kashedin kwana ba da babu abin da zai hanata kwana, saboda kawai kar ta jera da shi. Yana ta fuffurzo mata magana da 'karfin hali da na kwanji har suka 'karaso gidan Goggo tana cika tana batsewa suka yi sallama da Goggo mai yi mata nasihar ta saurari Yusha'u a fakaice. Suna fitowa kofar gida dan babur din da ta yiwa maganar ya dawo ya kaita tasha ya karaso. Cikin dakewa kuma ta doshe shi ya karkata mata mashin din a gaban Yusha'u ta haye. Duk yadda ya zo wuya sai ya rasa matakin da zai dauka wanda ya wuce binsu a mota har tashar. Ta salllami mai mashin shi kuma ta yi d'amarar share shi, sai da ya matsa mata da hon sannan kamar dole ta zo ta shiga motar. Sai da tafiya ta fara nisa sannan ya tsinka shirun tsakaninsu. "Na yi miki.....mtsw..... Abu dan gayya, abin da kika yi yau nayi masa kallon gayya..." Wannan karon yana sauke numfashi ta amsa. "Ba gayya ba ce, kamar matsa min ka yi sai mun taho tare, na yi kokarin in hana zuciyata nuna ba ta son biyoka ta gaza, wannan shi ne abin da ka dauka gayya". "Shi ne kika za6i ki sa6i Allah?" Ya fada yana nacin kallonta. Ita ma ta dan yi masa zuru na rashin fahimta, ya mayar da kallonsa ga titi. "Kin ba ni haushin da kika yi niyyar ki ba ni na kuma kar6a cutar da yadda kika so. Wai a gabana ki haye bayan wani 'kato ya goya ki... 'kazantar ta wuce 'kazanta..." Ta tare shi ba dan zuciyarta ta fara zafi ba, sai dan kar ta ba shi sararin da zai ci gaba da nuna mata iko. "Ka daina fadar wani a gabanka, dazu ma da babu kai shi ya dauko ni, kawai ka kaddara rayuwa ce ta 'yanci da rashin mafadi...." Mamaki ya ishe shi, ya juyo yana kallon ita kuma ta maza ta shiga binciko wayarta a jaka saboda 'karar shigowar kira, kafin ta gama fito da ita kiran ya katse. Da ta duba lambar kiran sai ta tarar da 6oyayyar lamba (hidden number). Ta shiga juya wayar tana kallo, shi kuma Yusha'u ya sami sararin magana. "Ni kike fadawa haka Rumaisa'u?" Ta yi saurin dagowa ta dube shi ba tare da fuskarta ta sauya ba. Ta yi saurin dagowa ta dube shi ba tare da fuskarta ta sauya ba. "Ban dauki maganata wani cin fuska ba, na fada ne dan ban ga abin 6oye-6oye ba... In dai mutum ba ya iya hanzartar da wani akan wani abu da zuciyarsa wanin ta 'kulla masa, to kai tsaye gara ya yi abin da ya shiryawa kansa, ya kuma fito da shi kowa ya gani, Allah basshi duk wanda yake jin an shiga hakkinsa sai ya fito ya nema". "Allah Ya ba ki hakuri". Abin da ya ce mata ke nan, ita ma cikin ko'in kula ta ce. "Amin". Ta ciro bututun sauraren magana na kunne (earphone) daga jakarta tana zurawa a wayarta dan ta ji sakon muryar Mahaukacin masoyi, wanda ya shigo mata dai-dai da zuwan Yusha'u kan dutse. Ammma sai Yusha'un ya katse mata hanzari da tambayar. "Ina Hamida?" Ta kuma dagowa ta kalle shi fuskarta babu alamar wasa ta ce. "Wace ce haka?" Cikin bayyana mamaki ya ce. "Hamida nawa kika sani?" Ta dan d'aure gira ta yi 'kasa da ido. "Wadda na sani ba mu ta6a lurarta da kai ba, ban san akwai wata ala'a tsakaninu ba shi yasa na yi mamakin yadda aka yi ka san da rayuwarta a doron 'kasa". Ya yi kasa'ke lokacin da zuciyarsa ta fara bugawa, Rumaisa'u ta sauya matu'ka ba kamar sanin baya da ya yi mata na rashin kullaci da 'kankantar da laifi ba, sannan yanzu harshenta ya yi kaifi, zuciyarta ta yi 'kwari yadda ba ta shakkar fada masa duk wata magana da ta zo bakinta. Hamida 'yata cikinsa Rumaisa'u ke keta idonsa ta fada masa wai ba ta san da wata ala'ka a tsakaninsu ba. Sai dai dole ya share saboda ya fi kowa sanin dalilin da ya sa ta fadar hakan. Dalilin da ba ya son ya tuno bare ya fadi abin da zai sa ita ta tunatar masa. Sai ya watsar da wannan maganar ya kamo wata, duk da a kan Hamidar. "Ya ya jikinta?" Ta juyo masa da fushi, sai dai ya yi dai-dai da latsa ma6allin sauraron muryar Mahaukacin Masoyi da ta yi. -- ''Kamar kina cikin fushi yau, na dame ki ko? In kin dauki abin da nake miki damu kar ki dauke shi zalunci, ko zuciyarki ta raya miki zaluncin ne ki tunatar da kanki fadin Manzon Allah (S.A.W). 'Kada ku bi mutane ku ce in sun kyautata ni ma zan kyautata, in sun yi zalunci ni ma zan yi zalunci... ku tsaya da 'kafafunku in suka yi zalunci ku ku kyautata". Ta yi tsuru idonta akan wayar Yusha'u da ke ajiye lokacin da sa'kon ke maimaita kansa a kunnuwanta. Hakan kuma ya yi tasirin sauke fushin da ta 'kunso a radadin da zata yiwa Yusha'u, 'kari a kan sa'kar da zuciyarta ta yi mata na ta binciki Yusha'u Mahaukacin Masoyi da sa'konninsa. A 'kagauce ta amsa masa tambayarsa. "Da sauki". Zai yi wata maganar ta riga shi cikin sar'kewar murya. "Me yasa kake damuna da yawan turo sa'konni? Duk abin da kake son sanar da ni ai gara ka tunkare ni kai tsaye ka fada min". Wato ta yi masa basaja ke nan. Ya tare girar da ke bayyyana mamaki tare da dafe kirji ya ce. "Ni? Ai kuwa kin san rubutu ba dabi'ata ba ce, layi biyu na rubutu akan na yi shi gara na kashe dari biyar a waya balle na dame ki da wanda zai gundure ki Rumaisa'u". Ya kare da tausasa murya yana dan kallonta. Ta yi saurin kawar da kai tana da na sani. Ta gamsu da ma'anarsa, mawuyacin abu ne ka ganshi yana rubutu, kai ko karanta sa'ko ba cika yi ba, in ka yi masa sa'ko ma ka yi a wofi, koda yake ita kanta ma basirarta ce ta toshe, sakonnin Mahaukacin Masoyi sun yi kama da na dan leken asiri ko wani mai gani har hanji. Ta ci gaba da raba hankulanta uku, kan kallon wayarta sanan ta daga kai ta dubi Yusha'u tarwai, alhalin kuma zuciyarta ta kwarzaheta da haske mata fuskoki kala-kala wadanda ta ke zatawa Mahaukacin Masoyi tare da zuciyoyi iri-iri wadanda ta ke hasaso niyyarsa da manufarsa a kanta, wannan ya yi dalilin da har suka 'karaso Kano ba ta fahimci sabon kundin da Yusha'u ya bude ya fara karata mata ba, kundin da yake son nuna shi ne wanda ta ke 'karkashin mulkin mallakarsa shekaru kusan uku da suka gabata ba, ba shi ne wanda kamar a tsohuwar rayuwarsa ta ke zaton lokacin da aka raba maganganu masu dadi da taushn furuci an manta da shi ba.... Ba shine kaza ba shine kaza ba! Wannan da suke tafe yanzu kamar Yusha'u ne a fuska da riga kawai, amma ayyuka wani ne daban... . Dan Aunty.GORAN DUMA (P 48) . . Lokacin da ta fara barin kunnuwanta su saurare shi sai zuciyarta ta cika da dokin ta san makasudin wannan sauyawar, ga6a kawai ta ke jira ta nemi ba'asi, kuma ta tabbatar masa ita fa ba a sauyata ba, ba a sauya Rumasa'u daga kasancewarta sickler ba, kuma ba ta daina laulaye-laulaye ba, sannan ba a kwashe mata zurfin karatun da yake ganin shi ne tsanar da ya yi mata ba. Ga6ar da zata nemi ba'asin ta zo dai-dai lokacin da suke jiran danja a Gadon Kaya kan titin B.U.K zuwa Ibrahim Taiwo Road, sai dai abubuwa biyu ne suka faru a dai-dai lokacin, wato Yusha'u ya nuna mata Yahya Guasau Road ya ce mata. "Kin ga hanyar gidan da nake gina miki, na san ba zaki so zama gida daya da kishiya ba..." Ta ci gaba da raba hankulanta uku, kan kallon wayarta sanan ta daga kai ta dubi Yusha'u tarwai, alhalin kuma zuciyarta ta kwarzabe ta dahaske mata fuskoki kala-kala wadanda ta kezatawa Mahaukacin Masoyi tare da zuciyoyi iri-iri wadanda ta ke hasaso niyyarsa da manufarsa akanta, wannan ya yi dalilin da har suka 'karaso Kano ba ta fahimci sabon kundin da Yusha'u yabude ya fara karata mata ba, kundin da yake sonnuna shi ne wanda ta ke 'karkashin mulkin mallakarsa shekaru kusan uku da suka gabata ba,ba shi ne wanda kamar a tsohuwar rayuwarsa take zaton lokacin da aka raba maganganu masu dadi da taushn furuci an manta da shi ba.... Bashine kaza ba shine kaza ba! Wannan da suke tafe yanzu kamar Yusha'u ne afuska da riga kawai, amma ayyuka wanine daban.Lokacin da ta fara barin kunnuwanta su saurareshi sai zuciyarta ta cika da dokin ta san makasudin wannan sauyawar, ga6a kawai ta kejira ta nemi ba'asi, kuma ta tabbatar masa ita faba a sauyata ba, ba a sauya Rumasa'u dagakasancewarta sickler ba, kuma ba ta daina laulaye-laulaye ba, sannan ba a kwashe mata zurfin karatun da yake ganin shi ne tsanar da yayi mata ba.Ga6ar da zata nemi ba'asin ta zo dai- dai lokacinda suke jiran danja a Gadon Kaya kan titin B.U.Kzuwa Ibrahim Taiwo Road, sai dai abubuwa biyune suka faru a dai-dai lokacin, wato Yusha'u yanuna mata Yahya Guasau Road ya ce mata."Kin ga hanyar gidan da nake gina miki, na san ba zaki so zama gida daya da kishiya ba... "Kunnuwanta ba su gama kwashe maganganunsaba ta dago a fusace ta dube shi, amma sai aka yirashin sa'a bai san tana yi ba, saboda yana cinikin faifan C.D, duk da haka sai ta ta6e baki tajuyar da kai zuwa kallon tagar mota, sai kuma idonta karaf kan wani matsashi da ke cikin wata Toyota Parado da alamun ya jima yana 'kuramata ido, kafin ta tantance kalolin fuskarsa ko dalilin wannan kallon maitar da ya yi mata Karan Farko A Tsawan Tarihin Rayuwata Naji Yakamata Nai Shawara A Wasu Lamurana,saikawai Naga Zuciyata Taza Beki Dan Ki Zama Abokiyar Shawarar Yushau Yafada Cikin Wata Raunanniyar Murya Da Ruma Bata Taba Mafarkinjinta Daga Gareshi Ba Kodayake Ita Bata Cikin Hayyacinta Batamasan Abinda Yakecewa Ba Ga Badaya Tadinga Waige Waigen Bayanta Tamkar Zata Tsinke Wuyanta Motocin dasuke Biyo Bayanta Sukadinga Yimata Gizo Tadinga Ganinsu Duk Sun Zamemata Toyota Parado Da Alama Game Din Nata Yanada Yawa Domin Lokacin datake Jin Yakamata Ta Zira Kai A Tagar Motar Tadinga Gano Baya Sosai A Sannan Wata Kalmar Yushau Tadaki Dodon Kunnenta,so Nake Na Sallami Sumoli,amma Ina Tsoron Alhji Dan Allah Kibani Shawara Ruma Tadubeshi Da Sauri Tana Neman Tafarka Daga Wannan Rikitaccen Mafarkin Ido Biyun Daya Fizgeta Ba Bu Shiri Can Ga Mahaukacin Masoyi Nan Kuma Ga Mahaukacin Tunani Da Zartar Da Hukunci Cikin Haukansa,saboda Dokinsan Ruma Ta Amsa Masa Tambayar Sa Ya Bita Da Kallo Ta Hana A Kunna A.C Gashikuma Tana Zufa Waimeke Faruwane? Da Yushau Ya CigaBa Da Kallanta Da Kyau Ma Saiya Ji Wata Irin Shakkarta Ta Mamaye Shi Nantake Bakinta Na Rawa Ta Ce Da Akame?Inatakira Kina Watsawa Juji,, tayi Mugun Zuwa Wuya Amma Hakurarriyar Muryarta Ta Taka Rawa Wajen Boye Wa Duk Da Kuwa Katse Mutum Inyana Magana Alama Ce Daga Alamomin Nuna Fushi,wadannan Hirarrakin Naka Waikana Ganin Sunada Amsa Agurina? Ya Jahilce Ta Da Ido Amma Baice Komaiba Har Ita Ce Datakejin In Anbar Maganar Ahaka An Cida Guminta,takara Zunkudo Maganar Cikin Rauni Da Rawar Harshe,kana Laakari Kuwa Da Maganganun Da Suke Fitowa Bakinka Yau Da Kunnen Wadda Suke Zuwa?Rumaisau Fa! Sikila Nan Mai Ririta Ciwo Wadda Tai Zurfin Karatu Ba Pre Boko Ba, Bazawararnan Mara Daraja Wadda Tumatirin Gwangwani Yafita Kima Fuskar Yushau Na Nuna Hakikanin Gaskiyar Sa Kidaina Dawo Da Bara Bana Ruma Idankika Duba Tarin Manyan Sahabbai Duk Zaki Tarar Da Manyan Kafuraine Suka Karbi Hasken Muslunci Badaidaine Ba Don Mutum Yai Wata Barna A Baya Kuma Yadawo Yagane Kuskurensa Ace Sai An Dauwama Masa Waccen Ta Rausayar Dakanta Alamar Mamaki Lallai Kayi Kwatance Mai Kyau Yaya Saidai Kamanta Musulunci Gaskiya Ce Kwaya Daya Tal Wadda Duk Juyinka Haka Zaka Tarar Da Ita Amma Musulmi Kuma Mutane Sun Mallaki Hali Da Halitta Wanda Suke Iya Sauya Wani Su Bar Wani Har Suje Kabari dashi Kamar Kai Kenan Daka Sauya Hali Dagayimin Kallan Wata Yar Ta Adda Zuwa Mata Mai Daraja Wadda Sam Ma Bataimin Kyau Ba,amma Niban Sauya Halitta Ta Kasancewata Sikila Ba,kuma Ilimin Boko Danasamu Ya Sha Kwanyata Kenan Har Mutuwata Lallaikenan Inkai Ansauyaka Da Alamar Niba A Sauyani Ba,ko Ma Kila Baza Sauya Dinba,ya Bude Baki Zaitareta Ta Dakatarda Shi Jinan Yaya Yushau Ba A Sauya Ruma Sikila Ba Saikuma Akasami Hamida Sikila Wakwafinta Kana Iya Bude Kwanji Mu Ga Sauyinta kAkanta Kafin Nina Ga Ko Dagasken Ka Sauya? Ba Lallai Sai Zaka Amfanar Da Abu Zaka Jajirce Nuna Akansa Ka Sauya Ba, yanzu Kam Jikinshi Yai Sanyi Kalau,amma Wani Fushi Da Makakin Kalmar Ji Nan,datake Tabbatar Masa Bai Sauya Din Ba Da Gaske Hakan Ne Yasanya Yajima Bai Ce Komai Ba Naga Na Tambayeki Hamida Kisa Tambayata A Kwandan Shara Nikuma Na Dauka Idan Dai Ka Sauya Ba Ka Bukatar Tambayata, idan Fa Har Dagaske Matsayin Mu Dakai Dayane A Wajen Hamidar Bazan Iya Kirga Sau Nawa Nake Neman Hamida Naganiba,amma Ba Tambayar Kowa Ita Ba,taimasa Maganarne A Kagauce Saboda Gajiya Da Tambayar Sa, yushau Yanaganin Rayuwa Da Ita Ce Farincikinsa Zai Kammala,ya Sheka Smoli Ya Tarar Ba Bu Kwaya Sainake Ganin Baikamata Ba,ki Katseni Akan Matsalar Cikingidana Danakeson Sanar Miki Zan Warwaremiki Wacece Sumayya Tana Bin Wata Toyota Tai Gidan Murtala Su Kuma Suka Karkata Suka Shiga Titin Gandun Albasa Saitaji Zuciyarta Ta Cika Da Mugun Fushi Ta Ce Ashe Lokacinda Zaka Auri Sumoli Danikai Shawara? Kodayake Bakai Shawara Dani Ba Kayi Aikin Dayafi Shawarar Kasakeni Domin Ka Aureta,kabarnida Ciki Batare Daka Taba Waiwayata Lfyata Da Ta Abinda Kecikina Ba,dukda Dai An Matsa Maka Daukar Nauyi Na Haifi Abin Cikina Irina Masu Matukar Rauni Wadanda Bankira Hai Huwar Su Abin Burgewa Ba,ammdai A Matsayinsu ammadai A Matsayinsu Na Tsatso Kamarkoba A Godemin Haihuwar Su Bayakamata A Godewa Allah Ta Hanyar Kuladasu Da Kuma Tausayinsu Har Allah Yai Ikonsa Akan Ahmad Kuma Me?Hamida Ma Tabi Sahuna Nazama Tumatirin Gwangwani,wane Irin Sonkai Ne Wannan Daza A Ce Mu Wannan Iyalin Masu Kama Da Abin Kyama Zaka Kawo Wani Abu Game Da Matar Dakayi Man Wanna Tozarcine Dominta,ta Girgiza Kai Cikin Tsananin Takaici,bazan Iya Zagi Bane Yaya Yushau Amma Tabbas Yaudana Zageka, idan Zaki Zageni Kiji Sanyi Ki Gwadamana Ruma Ammadai ki Saurareni Dakinji Cewa Badan Sumoli Nai Laifindakikejin Yai Girman Dazaki Kasa Yafewa Ila Dai Kuskuren Fahimta Batasan Lokacindata Maka Masa Harara Ba,taso Tai Tsaki Tashareshi Banida Bukatar Ji,ka Bar Abinka Zaimaka Amfani Nima Ka Barni Dan Allah Inji Da Abinda Yadameni,nasan Abindake Damunki Ai,da Sauri Tajuyo Ta Dubeshi Kuma Daidai Lokacinne Yahau Layin Gidansu Daga Gefensu Kuma Ga Toyotar Nan Data Hargitsa Ruma Nafitowa Daga Titin Gidansu Yushau Yanunamata Yana Dariya,wai Ba Wacen Motarbane Naga Ta Gigitakiba ?... . Dan Aunty GORAN DUMA (P 49) , , Dakin Nemi Shawarata Akanta Kila Da Ina Da Abincewa Rudani Da Tashin Hankali Take Kallan Yushau Tana Kuma Waiwayen Motar Harta BaCe maganinta,,shikuma Yushau Yaita Kyalkayata Mata Dariya Har Suka Karasa Giada Bataimasa Magana Ba, Taiwanka Tai Sallah Da Cin Abinci Duk Cikin Alhini Tanemi Guri Musamman Ta Zauna Dantai Tunanikan Mahaukacin Masoyi Takasa Lamarin Nan Mahaukacin Masoyi Yafara Ruda Ta Bayan Rashin Auwal datai A Duniya Nan Ta Cire Rai Akwai Wani Abin Rudu A Cikinta,amma Halittar Mahaukacin Masoyi Naneman Ta Tsoratata Indai Dan Ganine Todazu Taganshi Kumadaga Ganin Dataimasa Ya Zuwa Yanzu Bata Taba Rudewa A Lamuranta Irin Na Tsukun Lokacin Nan Ba,infa Har da gaskene Ba Plan Din Yushau Bane,taga Motar Su A Layinsu Meyazo Yi Gidansu? Menene Manufar Sa Akanta? Menene Alakar Sa Da Yushau? Kawai Saitafada Watsup Dan Rage Kewa Da Tunani Tafara Rage Kewar Da Sakon Friends Data Tadda Sun Turo Mata Kwatsam Sai Hannunta Yafada Kansakon Mahaukacin Masoyi Wanda Takejin Tagoge Lambar Sa Dake Layinta Na M.T.N Ta Adana A Layinta Na Etisalat Wanda Tahau Watsup Dashi Lambar Tasama Waddatake Kaddarawa Cewa Matacciya Ce Agurinta Tunda Ko Ankira Bata Shiga Duk Da Kuwa Akwai Lokutan datake Leka Blacklis ta Ta Tarar An Zare Lambar,kuma Wannan ke Kara Bata Tabbacin Mahaukacin Masoyi Aljanine Ba Mutumba Tunda Dai Ita Ke Rataye Lambar Amma Sai A Sauketa Duk Jikinta Yadau Rawa Kasancewar Sakon Nasa Biyune Akwaina Murya Akwai Na Hoto Tanadubawa Saita Tadda Dandasheshiyar Fulawa Da Wasu Kalolin Baloon Sun Zagaye Ta Daga Kasa Kuma Cikin Wani Rubutu Mai Kyau An Rubuta HAPPY BIRTHDAY MY LOVE WISHING U MANY MORE BLESSED RETURNS OF THE DAY,gabanta Yai Mugun Yankewa Yafadi Cikin Rawar Jiki Tafara Jera Yatsun Hannunta Tana Kirgawa Kamar Sune Zasu Tabbatar Mata Da Cewa Yaufa Sha Shida Ga Watan Febrairu Kuma Ayaudin Ne Take Cika Shekaru Ashirin Da Takwas Cif A Duniya Ita Bata Tuna Hakanba Saida Mahaukacin Masoyi Ne Ya Tunamata TabbaCin Yasanta Dayawa,kila Sanin Ma Da Bataima Kanta Ba Ta Matsa Sakon Murya Taji Ance Rumaisau Ance Abinda Yawuce Tarihine Abinda Baizo Ga Gaibune,amma Yau Tawa Ce Kuma A Cikinta Nake Lallai Masu Wannan Hikimar Sunyi Gaskiya Dan Shekara Ashirinda Takwas Dinki Na Baya Basan Dasuba Sai Kwatsam Na Tsince Su Yau A Cikin Tarihina Danaki Dayake Yaudin Tawa Ce Har Gani Cikin Masu Farincikin Tarihinki,abin Mamaki Na Cika Nawa Shekarun Ban Tuna Ba,amma Naki Tun Sha Biyun Daren Jiya Suka Fado Min Duk Da Kuwa Bana Muhallina Tabbas Ba Bu Karya Na Cancanci Zama Mahaukaci A Soyayyarki Inafatan Shekarun Gaibunki Duk Tsawansu Muyi Su Tare,dafatan Kinje Gida Kalau? Ta Saurari Sakon Yakai Sau Ashirin Mamaki Take Ko Fargaba? Itakanta Tarasa Daya Amma dayake Kamar Mahaukacin Masoyi Natare Da Abinda Zuciyarta Ke Sakawa Kawai Saigashi Ya Zabar mata Fargaba Inda Wani Gajeran Sako Nasa Yafado Mata KISHIRYA DAGA YANZU ZUWA KO WANE LOKACI ZAKI IYA KARBAR SAKONA, firgici Tafara Bin Dakin Da Kallo Cikin Mugun Dauke Numfashi Babu Abindake Motsi A Dakin Amma Saitadinga Jin Lallai Ba Itakadaine Acikinsa Ba Tadinga Adduoi Saiga Mubarak Yashigo Dauke Da Katuwar Leda Tai Sauri Ta Gyara Fuskarta Suka dubi Juna Suna Murmushi,yajiye Yana Bata Bayani Dazu Dabda Zaku Shigo Kikai Bako Bako? Mubarak Ya Bita Da Kallo Saboda Ganin Firgicewardatai Anti Bako Mana Meyafaru? Kokin sanshine? Ta Girgizakai Dasauri Ga Sako Nan Ya Bayar A Baki Waiyana Tayaki Murnar Zagayowar Haihuwarki Baki Bude Take Kallan Mubarak Baki Na Rawa Tadubi Kayan Tadubeshi bai Fadi Sunansa ba,kuma Daga Inayake? Yafada Sunansa Ashir Kuma Tarauni Yake In aka fadamiki Haka Zaki Gane Batagano Komaiba Face Mahaukacin Masoyi Yazo Ya Bide Iyayanta Ta Wannan Sigar Kamar Yadda Yake Gasa Nata Lissafin Da Sauri Tadaga Ledarta Jirkice Shi A Gefe Saitatuna Ya Ce Kishirya daga Yanzu Zuwa Kowani Lokaci Zaki Karbi Sako na baBu Abinda Ledar Takunsa SaitarkaCen Kayan Kwalliya Masu Tsada Tare Da Turarurruka haka Tadinga Karanta Katutukan Happy Birthday Wanda Sunkai Kala Ashirin Batare Da Kwakwalwarta Na Fassara Mata Ma,anar Suba Ta Watsar Cikin Tsananin Rudani Kana Gida Lokacinda Yazo? Eh Ina Gida Kaganshi? Kaga Motar Daya Hawo? Mubarak Ma Yafara Rudewa Dan Baita Ba Ganinta Cikinrudani Haka Ba Dawowata Kenan Ya Shigo A Motar Sa Toyota Wankan Tarwada Ne Yana Ta Tsatsaman Jiki Yana Da Fara A Yanasan Hakadai Yaita Wassafa Mata Shi,tuni Ruma Takasa Magana Saidai Binsa Tai Da Ido Saima Yabata Wani Mugun Tausayi Saboda Yana Tunkahon Yai Hira Da Aljani Kinganeshi? Ka Kalli Yatsun Kafar Sa? A,a Na Tabbatar Daka Kalla Saikaga Kofato Kofato Aunty? Ta Ce E,h Irin Na Doki Ba Dan Inada Yakini Ashir Ba Mutum bane Tagama Hada Kayan Taware Katunan Tamika Wa Mubarak Ledar Dan Girman Allah Fita Da Kayan Nan Ka Sadakar Mubarak Yadubeta Ya Dubi Kayan A Tsorace Waimeyasa Kika Ce Aljanine? Ta Ajiye Ledar Ta Turamasa Wayoyinta, Ta Cemasa Dazaka Shiga Wayata Duk Social Netwok Danake Yi Zaka Tarar Da Manyan Alajabinsa Dake Nuni Kan Abotar Kan Abotar Sa Da Zuciyata Waddayake Sanin Duk Abindayake Raya Wani Lokacin Har Da Abinda Gangar Jikin Ke Aiwatarwa Kamar Daiyanzu Taimasa Bayanin Komai Adaddafe Yakaranta Yayarfar Da Wayar Tamkar Wanda Yarfar Da Maciji Yamike Yana Goge Tafin Hannunsa Da Riga Inna Lillahi Wa Inna Ilaihi Rajiun,anti Tun Yaushe Hakanke Faruwa? Munshiga Uku Gashi Ya Ce Gobe Zaidawo Hakayace? Ya Ce Eh Ammake Dawani Idan Zaki Ganshi? Nima Da Tsautsayi Yahadamu Ina Danasani Ruma Ta Tuntsire Da Dariya Kaifa Sokone Mubarak Saika Ce Ba namiji Ba Tabbas Nikam Ko Ifiritine Inasan Ganinsa, Tunsanyin Safyar Mubarak Yadaka Sammako Ya Bar Gidan Gashi Alhji Da Hajiya Basanan Suna Egypt Sai Gobe Zasu Dawo Dan Tun Adaran Mubarak Baiyi Barcin Kirkiba Babu Irin Shakkar Da Wasiwasin Da Ruma Bataiba A Safiyar Yau Dawani Alajabin Nasa Tatashi Inda Tataradda Makudan Kudi Yaimata Transfer Alayinta Na M.T.N Har Naira Dubu Ishirin,sannan Ya Rubuta To Gashinan Agaisa Da 'yanuwa Masu Taya Murna Aljanu Ma Sunsan Takan Waya Da Internet Harma Da Yadda a Ke Kyautata Soyayyarsa Ta Hanyar Kyautar Kudi A Waya A Tsawan Ranar Ta Saurari Suratul Bakara Yakai Sau Biyar Karfe Hudu Da Rabi Daidai Neman Isonsa Yakaraso Mata Daka Ta Hanyar Mairo Maimusu Wanke Wanke Nandanan Ta Tsorata Fiye Da Mintuna Talatin Tana Safa Da Marwa Saiga Mairo Uwar dakina Kin Manta Da Bakonne? Haba Uwardakina Adinga Daurewa Ana Kara Wa Zuciya Dangana,tajuya Idanta Cike Da Hawaye Kingano Min Yatsun Kafar Sa?Yatsun Ne Kokuma Kofato? Wanne Irin Kofato? Yo Ni Inama Zanga Kafar Sa Akwai Safa Meyakawo Wannan Maganar? Nifa Dukma Kinfir Gitani Nidah Dazaki Iya Dakingano Min Yatsun Komai A Jikin Mairo Rawa Yake Ni Bazan Iya Ba Wallahi Har Gudawa Na Neman Tsinkemin, Duk Da Halinda Ruma Keciki Na Rudewa Saida Dariya Yaso Kwacemata Tadauki Hijabi Ta Doshi Kofa Tana Cewa Ni Zaniya Bara Naje, Haka Tadinga Kalimatush Shahada Gwamma Ma Tazarce Inda Masoyinta Auwal Yaketake Fatan Sui Rayuwa A Aljannah Maimakon Tai Sallama Kawai Sai Ta Rangada Kalmar Shahada Tafada Dakin Wanda Ke Zaune A Dakin Yadago A Firgice Yadubeta Cike Damamaki,itama Ta Tsaya Cak Tana Kallansa Ba Bu Kakkautawa Cike Da nata Mamakin Shiya kasa Magana Itakuma Ta Bige Da Nuna Shida Hannu Tana Kokarin Magana Amma Takasa Ranki Yadade Fuskar Sa Cike Da Faraa Har Kumatunsa Suka Loba Wanda Suke Nunawa Ruma Zallar Kuruciyar Sa,ta Isa Kujera Ta Zauna Tana Kokarin dawo Wa Zuciyarta Doka Da Oda Batasan Yaudarar Kanta Bare Ta Cutu Kota Cutar Dawani Amma Wannan Tabbas Bashine Mahaukacin Masoyiba Ta Cemasa Ashir Manyan Gari,ya Ce Hakadai Kikecewa Ya za ai muzama Hakan Kiduba Fa Shanyar Dakikaimin Har Na Tsawan Kusan Awa Daya.... . Ayi hakuri na rashin ganin post jiya, en wasu abune suka shige min gaba, da patan za ayi min uzuri. Dan Aunty. GORAN DUMA (P 50) . . Kamanta Dan Allah Ya faru ne Bisa Akasi Wai Da Gaske Kaine Bakon Dayazo Jiya Har Ya Bar Sako Ya Ce Eh Wani Abu Ne Yafaru? Ta Ce A.Ah Da Akemin Kwatancenka An Ce Kazoda Toyota Shine Nake Ga Aikamar Ma Mun Hadu A Gadon Kaya Jiyan, kai Banibane,ainafi Wata Banhau Wannan Titinba,anzo Gurin Ruma Tafada A Zuciyarta Kaine Katuromin Sako? Ni Ina Naga Lambar Wayarki Alhalin Kinhana,waimaduk Meyakawo Wannan Tuhume Tuhumen Daga Zuwana? To Inakasan Ranar Birthday di NA? Haka Dai Sukai Ta Hira Har Saida Ruma Tagamsu Ba Ashir ne Mahaukin Masoyi ba Abin Mamaki Suna Zaune Sai Ga Shi Gowar Sakon Mahaukacin Masoyi,ya Cemata Kamar Daikina Cikin Wani Uzuri Ko Mudaga Tattaunawar Mu Sai Wani Lokaci Nazo Datarin Burika Akanki Wanda Nake Wafatan Su Sami Matsuguni A Zuciyarki Da Duniyarki Ta Cemasa Banasan In Wahalar Da Zuciya Ko Gangan Jikin datake Jin Kaunata Ashir Tun Ranarnan Danaga Baka Gamsu Da Abinda Nagayamaka Ba Ba Waka Naso Namaka Ba Dana Cemaka Banida Wata Daraja Da Kamar Kai Zaka soni Kuma Nima Ban Shirya Son Kamarka Ba Hakadai Ashir Yaita Kokarin Kwatanta Mata Irin San Dayakemata Itakuma Ruma Tadinga Gayamasa Illar Dake Tattare Da Aurenta Hardai Sukai Sallama. Wanene Ashir? Kwanakin Bayadasuka Wuce Kafin Mahaukacin Masoyi Yafara Nasa Almarar Ruma Tai Shirin Zuwa Abuja Da Niyyar Jifan Tsuntsu Uku Da Dutse Daya Wato Ziyarar Ofishin Jaridarta Aminiya,dakuma Gaida Iyayanta Da Yayarta Balaraba Sai Kuma Uwa Uba Datake Boyewa Aranta Kadai Wato Dora Sansanyar Kallo Kan Sanyin Idaonta Wato Hamida Anahaka Sai Yayarta Takirata A Waya Taroki Alfarmar Da Taje Gidankawarta Fatima Matar Abu Turab Wandake Tarauni Takarbo Mata Turarurruka Datakawo Mata Daga Dubai,fatima Ba Bakuwarta Ba Ce,dayamma Tadauki Mubarak Yarakata Amma Suna Zuwa Ko Gidan Bai Shiga Ba Yahaumata Magiyar Taimasa Uzuri Yana Da Kallon Kwallo Yadawo Bayan Sallar Magariba Su Tafi,tana shiGa Fatima Tatare Da Murna Suka Gaisa Suna Zaune Sai Ga Baby Hindatu Kyakyawa Kamar Uwatta Ruma Takarbeta Tana Tunanin Tata Gudan Jinin tare Datakaicin Yushau Wanda Ya Nesanta Su Da Juna Lokacin Da Abu Turab Yazo Ruma Taga Ririta Hindatu Gun Mahaifinta Saida Kwalla Yazubo Mata Ta Ce Zata Tafi Fatima Taiwa Abdullahi Kallon Wutsiyar Ido Kinga Badan Wannan Man Dinba Ma Kallon Ne Zai Dauke Masa Hankali Ba Dakawai Inkingama Saimu Kai Baikamata Muci Amanar Momiba Nanda Magariba Saimu Kaita Har Gida Haka Tazauna Dasu inda Ko Minti Goma Ba Ai Ba,sai Ga Bakonsu Ashir Kanin Abu Turab Ubansu Daya, Ashir Yaita Kallon Ruma Tasaci Zuciyar Sa Ya Ce Aunty Hakadai Yafurta Zuciyar Sa Inda Ruma Ta Cewa Fati Da Abu Turab Kundai sanni Datarin Matsaloli Hakadai Har Sukai Sallama Ruma Bata Amince Da Bukatar Ashir Ba Sukakaita Gida, Mairo Tashigo Falon Tasami Ta A Tsaye Takurawa Kofar Fita Daga Falon Ido,a Rikice Mairo Ta Ce,yaya Dai?7 da Sannan Ta tunada Yadda Sukai Da Mero,ruma Ta Tuntsire Da Darya, Yatafi Ashe Mutumne Ba Wanda Nazata Ba Kanin Mijin Anti Fatine Kawar Anti Balaraba Anmmadai Kindau Hakki Uwardakina Tsuguno Na Uku Na Rantse Mubarak Ma Sau Uku Yana Matsamin In Lekaki Hankali Atashe Dakyar Nai Shahada Nataho Ruma Kam Dariyatake Sai Bayanfitan Mairone Ta Tuna Dasakon Mahaukacin Masoyi Saitatafi Kuryardaki Saida Ta Tabbatar Taima Dakin Adduoin Tsari Daga Shaidanu kuma Ta Ceyakamata In Nemi Naurar Satar Bayanai Adakinta Ko Kuma A Zuciyarki Ba Zuciyarta Ta Rayamata Haka Innalhllahi Wa Inna Ilai Hirajiun Tadinga Furtawa INADA TSANANIN KISHI RUMA BAZAKIYIMIN GATANDA ZA A CE DON NIKADAI A KA HALLICCEKIBA? WANNAN Kashedine Ko Gargadi Tatambayi Kanta Sakon Ya Isone Daidai Lokacinda Take Zance Da Ashir Kenan Mahaukacin Masoyi Ya Ganta Da Kishiyarsa Karon Farko Kenan Datun Bullowar Mahaukacin Masoyi Rayuwarta Taji Kwalla Ta Cika Mata Ido Anjima Kadan Ma Sai Ga Kuka Shabeshabe Lallai Ba Kowani Abu Kebata Kuka Ba Musamman Wanda Takeson Nuna Jarumtar Karbar Kaddara Amma Tabbas Mahaukacin Masoyi Yafara Girman Da Jarumtakarta Zata Gaza Boye Sirrinsa Ita Kadai Ko Kuma Kokarin Samowa Kai Mafita Ita Kadai,doletazabi Daya Ciki Kodah Ta Runtse Zuciyarta Mahaukacin Masoyi Yadaina Hango Ciki Ko Kuma Zuciyar Tata Ta Runtse Idanuwanta Masu Mamakantar Da Ita Lamarin Mahaukacin Masoyi Ko Girmama Su Yadda Suke Firgita Zuciyar,kamar Na Biyu Ta Dauka Ta Goge Hawayenta A Fili Kuma Ta Furta Cikin Sarkewar Murya Kai Baka Dasuna? Sai Almajanuni A Soyayya? Lallai Kanada Kishin Abindakake Da Wanda Yafika Kishinsa Kakeson Abinda Yake Da Wanda Yafika Sonsa Wato Ni! Shin Zaka Iya Son Gawa? Ruhin Soyayyata Fankone Bazai Amfaneka Da Komai Ba Gara Ka Adana Haukarka Kozai Amfaneka Gaba Tana Ta jira Taji Sako Sai Ga Wata Gajeriyar Sako BAYAN HAUKA SO NA MAKAHONE,SHARAFINSA YAKE SHA BATARE DA BUKATAR RADDI BA,INASONKI,KARKI MANTA DA WANNAN Nantake Kwakwalwarta Ta Tsaya Da Aiki Cak Komai A Tare Da Ita Ya Koma Sifiri Kafin A Guje Su Harba Can Baya Tuno Mata Da Kalmar Dako Daza A Ce Katondin Benelin Ta Kwankwada Bazatakasa Tuna Daga Wanda Ta Taba Fito Mata Ba Danko Sakon Mahaukacin Masoyi Bashida Bambanci Da Kalmar Datashiga Tsakaninta Ta Karshe Da Masoyinta Auwal,to Ina Mahaukacin Masoyi Ya Samota? Data Rasa Amsa Saitakara GiGicewa Cikin Rudu Tamike Ta Garkama Wa Kofar Dakinta Mukulli Tanemi Guri Na Musamman Ta Zauna Tafara Gurzar Kukan Rashin Auwal A Madadin Kai Tsaye Tazaci Kukan Haukan Da Mahaukacin Masoyi Keneman Zozamatane,tadade Dasanin Tanason Auwal Kamar Yadda Tajima Da Sanin Asarar Data Tafka Na Rashin Auwal Wanda Yatanada Mata Ita Da Iyalanta Duk Wani Farinciki Da Hawayen Share Kuka,kece Farincikina,don Ki Haifi 'ya'ya Irinki Zantanade Su Da Hakurina Da Juriyata Dakuma Tattalin Aljihuna Iyakar Iyawata Inada Wannan Burin A Raina Na Kuma Niyyaceshi Wasudaga Cikin Alkawuran Auwal Kenan Aranar Dazaibar Duniya Ta Zabga Asarar Wannan Alwashi Da Alkawarinsa Ita Da 'ya'yanta Yauga Wani Ibtilainda Auwal Baitaba Hasaso Mata Ba Ya fada mata Duk Wannan Gibine Daga Cikin Manyan Gibinan Da Rashin Auwal Ya Haifarmata Domin Idan Yana Duniya Ko Shaidani Sai Yaji Kunyar Keta Idon Auwal Yazo Mata Da Rudu,mahaukacin Masoyi Yasami Rayuwarta Cikin Rashin Gata shi Yasa Mi Sararin Yimata Wasa Mai Saurin Tafiyar Da Numfashi,amma Menene Hadinsa Da Maganganu Irin Na Auwal? Tafikowa Sanin Auwal Ya Mutu Itamusulma Ce Dake Da Imani Duk Wanda Yamutu Yatafi Kenan Bare Ta Tafi Kan Kirkirar Musu Tsammanin Akwai Fatalwa Haka Ta Ci Gaba Da Kuka Da Tsora Ta Aranta Kuma Tanasan Sanin Shin Waye Mahaukacin Masoyi? 3-2-2013 Takomawa Dabiarta Ta Baya Kauracewa Wayoyinta Tare Da Kauracewa Sakonni Daga Nakan Layin Wayarta Har Gaba Daga Jakar Sakkonninta Na Social Network Inkadauke E-mail Dinta Wanda Batada Damarjuya Baya Kodake Ma Satinta Biyu A Kwance Shikansa E-mail Din Shigar Sauri Take Mai Idanta Yasha Gane Mata Na Mahaukacin Masoyi Amma Saita Share Tawuce Kaurardataiwa Social Netork Shine Gina Katanga Tsakaninta Da Makaranta Shafinta Na Jarida Musamman Dake Satin Daya Gabata Tai Rubutune Dan Gida Wato Kan Mutane Irinta Sickler Amma Saboda GanaWa Kanta Sukuni A Dukkan Kafar Da Sakonsu Zai Risketa Saibata Sami Wasu Ra,ayoyin Makaranta Sosai Ba,saboda Haka Yau Tadauki Kafa Zuwa Gidan Waya Debo Wasiku Saidai Kash Guda Daya Kawai Ta Tarar Ta Juyo Gida Tanashigowa Gidanta Cikaro Da Motar Yushau Tashi Ga Gida A Tsammaninta Zata Taradda Shi Gaban Hajiya A Durkushe Kamar Yanda Ta Saba Ganinsa Idanyazo Gidan Hajiyar kuma Nazaune Tana Gyaran Farce Fuskarta Ba Bu Annuri Gakuna Sumoli Matar Yushau Idanta A Talabijin Hajiya taimata Sannuda Dawowa Da Fara'arta Sumoli Kuma Ta Tsurawa Ruma Idon Danganin Tagano Muninta Itakuma Ruma Nata Kallon Kan Sumoli Uwar Eye Shadow Allah Yaimata Sansa Saika Ce Wadda Aljani Ya Aura..... . Dan Aunty. GORAN DUMA (P 51) . . Ta kuma iya baza Turare Tamkar Mai Shirin Shiga Turaka, adan dogashe Ruma Tazauna Hannun Kujera Aka Gaisa Sannan Tamike Zata wuce Ciki Yushau Yayafito Da Zance Nizanfara Baki Albishir Rumaisau Atika Ta Haihu Dazun Nan Da Sauri Hajiya Da Sumoli Sukaimasa Wani Irin Kallo Sumoli Na Tsarguwa Da Tuhuma Hajiya Na Ganin Kamar Abinda yayima Baimasa Kyau Ba,itakanta Ruma Saitarasa Da Bakinda zata Amsa Ikon Allah Ashe Abinyazo Jiyannan Fa Muka Hadu Tana Tafiya Kafarta Na Hardewa Take Maganar Hartakule Inda Ta Bar Yushau Da Bin Gurin Da Ta Bace Da Kallo Tana Shiga Daki Ta Lalubo Wayarta Cikin Watsar Da Fargaba Ta Ari Farinciki Ta Yabawa Zuciyarta Tana Lalubar Atika Sai Ga Atika Taturo Mata Sako Bayantagaji Dakiran Wayarta Daidai lokacin da take Kokarin Bude Sakon Atika Wani Sakon Yafado Cikin Akasi Ta Bude Shi Batare Data Shirya Ba, Wato Sakon Mahaukacin Masoyi, INADA YAKININ ZAKIN BAKI YA RUDARKI AMMA HAUSAWA SUNCE DUKA YAU,DUKA GOBE,SHIKESA BAKIN BA'AUZINI TAWAYE,SABODA HAKA NAKASA NATSUWA AKAN WANDA NAKIRA YANA FARAUTAR ZUCIYARKI ALHALIN BAIFINI SONKI BA KIBI A HANKALI, MAHAUKACIN MASOYI karon Farko Da Sakon Mahaukacin Masoyi Ya Bata Dariya Itama Bata Hakikance Dalilin Dariyarba.Kawaidai Tajita Tanayine,afili Ta Ce Wannan Halittar Fa Bashida Matsala Ga Dukkan Alamu ni yakeson Gadarwa Matsalar,ana Ga Yaki Yana Ga Kura Tanata Faman dariya Ta kira Atika Sukai Shewar Murnar Su Nasamun Karuwar Atika, Taimata Tsegumin da Aka Saba Ke Mutanenkifa Sunkawo Min Ziyara Suka Tarar Anyi Haihuwar,suwafa?Shagonki Da Pre-bokonsa Mana Yanzu Tagama Yimana Feleke Sukawuce Zuwanan Gidan Ruma Tai Murmushin Yake,ai Har Sunzu Bangane Wadanda Kikenufi Bane,ruma Kunyar Kanta Takeji Idanta Shiga Aka Zagi Sumoli Da Ita Duk Yadda Sumoli Takai Ga Mugun Hali Daitafita Domin Ita Yushau Yaso Harya saketa Akanta Kuma Garunan Shekaru Kusan Uku Suna Zaune Ba Ajikansu Sabanin Ita Da Shekara Dayama Suka Kasa Hadawa Tare,atika Ta Ce Tasami Su Hafsat Anan Sabodata Kawomin Lesunan Nanda Muke Maganar Mui Ankonsu Ranar Suna Ai In Fadamiki Sumoli Nazuwa Takwashi Uku Wai Itama Zatai, hafsat Suna Tafya Ta Zube nata Nan Ta barminsu Wai Indai Sumoli Zatai Ankon Ita Wallahi Tafasa,suka Fashe Da Dariya Ruma Ta Ce Dandai Hafsat Taki Karbar Shawaratane Amma Tuni Nafadamata Tadaina Ganin Bakin Wannan Iyalin Ita Take Dauka Ta Wata Tsiyar Shi Yasa Da Yaya Yushau Yaki Rayuwa dani Take Ganin Bakinsa Amma Har Ga Allah Nasan Tuni Ni Ba Wata Tsiya Ba Ce Dukwanda Ma Zai Aureni Alfarma Yamin Wanda Kuwa Yaga Bazai Iya Hakurin Yimin Alfarmar Ba Wallahi Baikamata Aga Laifinsa Ba Atika Ta Ce Aike Matsalarki Kenan Daga Anfara Magana Saiki Kwaso Wa Mutane Kayan Haushi,kinga Ni Sai Anjima Ni Da Baby Muna Zuba Idan Ganinki Daga Nan Zuwa Gobe Nasankemai Hajiya Idankin Zakifito Yanzu Sai Anyimiki Zancen Zama Ki Huta, "Dan Bani Da miji ne Ma kike Sa Ran Zanfito Yanzu In Taho Gidanki Itama Ruma Ta tareta Da Zolaya Atika Ta Ce Ina kika Kai Mahaukacin Masoyi? Ruma Na Sauke Wayar Ta Zauna Kan Kujera Kuncinta Har Yanzu Murmushi,tarasa Dalilin Jin Farin cikinta Da Yawa Irin Na Daidai Wannan Lokaci Dajin ba Abu Daya Ne Kawai Ya Faranta Mata Raiba,wato Haihuwar Atika Sakon Mahaukacin Masoyi Ma daya sanyata Dariya Farinciki Ba Tashiga Laluben Zuciyarta Don Nemo Dalilin Farinciki Sakon Nasa Tajima Suna Tirzawa Ita Da Zuciyar Tata Sannan Suka Yanke Hukuncin Cewa Sakon Masoyi Yana Nuna Tsantsar Kauna Gareta A Kowanne Lokaci A Matsayinta Na Ba Kowan Kowa Ba Lallai Kowace Irin Halitta Ce Mahaukacin Masoyi Tabbas Masoyine Bata Shakkar Cewa Inbata Fara Shakuwa Da Sakonninsa Ba Sannan Inta Ci Gaba Da Nesanta Kanta Da Sakonninsa Dole Taikewa Kamar Yadda Ita Da Zuciyarta Suka Yarda Sunyi Kewa A Kwanakin Da Suka Gabata Tazauna Tajanyo Wasikar Datakarbo Daga Gidan Waya Adireshin ANNUR MIKYWAY CAFE DAGA ABUJA? CAFE DIN DAKE ABUJA INDA KUMA TASAI WAYOYIN HANNUNTA BIYU TASAI MODERN DINTA INDA TA SAI KYAMARARTA INDA TASAI......... KAI BAZATA IYA KIRGAWA BA. Inhar Taje Hankalinta Baya Kwanciya Tanaji Ajikinta Kamar Tana Da Nasaba Da Gurin, Tanata Tunani Ta Bude Wasikar Ko Kuma Kawai Ta Share Taikarfin Hali Ta Bude Taga An Rubuta ""RAYUWATA ZAN BAYYANA MIKI KAINA, NAKI MAHAUKACIN MASOYI"" TARE DA SA HANNUNSA,ta Ce Wato Mahaukacin Masoyi Daga Annur Mikyway Yake,ya Abinyake? Innalillahi Wa Inna Ilaihirajiun Tanamamakin Yaya Haka Tafaru,,dago Kan Nan Dazatayi Saitaga Alamun Mutum A Inuwar Labule Ta Taga ,yanaganin Ta Dago Da Sauri Ya Bar Wajen,takori Dukan Da Zuciyarta Take Cikin Zafin Nama Ta Isa Tagar Ta Yaye Labulen Tahau Leke Leke Amma Bataga Komai Ba Sai Motocinsu Dake Gurin Kwanyarta Tafara Dawo Mata Da Abindata Karanta A Takardar Mahaukacin Masoyi Zanbayyana Miki Kaina Shine Wato Yanzu Ya Bayyana A Labule Taja Baya Tana Raya Abubuwa Masu Wahalar Fassara Wanda Tagama Hakikancewa Mahaukacin Masoyi Ba Aljanibane Amma Abinda Mahaukacin Masoyi Keyi Yawuce Azaceshi Cikin Mutane,to Waye? Ta Fizgo Hijabi Ta Zira Ta Ce Zan Binciko Waye Kai,abindayakama Naikenan A Farko, kasha Zamanka Zan Nemoka, a Falo Ba Yushau Ba Hajiya Sai Sumoli Tafice Itakuma Sumoli Ta Tsargu Don Haka Ta Mike Ta Hau Lekenta Ta Taga Ruma Nafita Ta Hango Yushau Yafito Ta Tsakanin Motoci Kaitsaye Ya Nufota Take Ta Tsargu Da Ganinsa Kuma Ta Alakanta Hakan Da Mahaukacin Masoyi Fuskarta Daure Ta Tsaya Ina Zaki Haka? Ta daga Takardar Tsakaninka Da Allah Yaya Yushau Bakada Masaniya Akan Wannan Takardar? Yanamata Kallan Rashin Fahimta Ya Karba Yana Nazarinta Cikin Yamutsa Fuska Kirjinsa Na Dukan Uku Uku Basaikin Hadani Da Allah Ba Ruma Wallahi Bansan Komai Akanta Mene yafaru? Ta Amsa Takardar Tana Nazarinta Yanzu Ina Daki Naga Inuwar Mutum Naleke Nata Labule Ko Kaganshi Tunda Tanan Ka Bullo, Kallon Juna Sukai Ido Cikin Ido Wanda Yushau Yake Da Yakinin Hakan Baitaba Faruwa Tsakaninsa Hakanyasanya Masa Muguwar Kasala Kirjinsa Nata Bugawa Da Sauri Taja Baya Ayanzu Kam Tasan Yushau Ya Wanke Hannu Nezai Danna Maballin Kunno Mata Danjar Bakin ciki Wahala Da Kunan Zuciya, Tsoronta Daya Kada Hakan Yafaru Gaban Abbah Dan Zata Iya Keta Idan Alhji Ta Ce Batasansa Tajuya Zata Bar Gurin Ga Mamakinta Saitaji Yushau Ya Ruko Hannunta Yaja Ta Baya Dasauri Suka Shiga Tskanin Motoci Tsoro Da Shakku Tuni Sungama Mamaye Ta Yaya Yushau Menene Haka? Sai Ga Hawaye Daga Idansa So Nake Na Baki Kalmar Da Ban Taba Baki Ba Duk Tazo Kunnenki A Makare Saidai Niyanzu Take Shan Sharafinta A Kirjina Alhalin Ina Cike Da Jin Haushin Ciwan Rashin Zuwanta INASONKI RUMAISAU WALLAHI INASONKI Dasauri Ruma Ta Ce Kadaina Rantsewa Meyasa? Indaza A Laluba Zuciyarka Da Kyau Sai Antarar Da Kaffara Takamaka Bajinsona Kake Ba Illah,,, yatareta Ruma Duk Abinan Danakeji A Kirjina Game Dake Kicemin Baso Bane? Taja Baya Hawaye Suka Fara Zuba Daidai Lokacin Idanta Yakai Kan Sumoli Ta Ce SO DAYANE TAK TUNI NA SADAUKAR DA NAWA GA WANDA YA CANCANCESHI DUK DA UBANGIJI BAI NUFA ZAMUCI GAJIYAR SA NIDA WANDA NASO DINBA,ILLA JIN KUMAJIN RADADIN DANAKE JI YAZAMA KAFFARA,AMMA NAKA SON KAGA INDA KA SARAYAR DASHI,TA NUNA MASA SUMOLI Yakalli Sumoli Baiji Zuciyar Sa Ta Sauya Ba...... Yaitsaki Yamaida Kallansa Ga Ruma, Ruma Ta Ce "Nikuma TAWA RAYUWAR BA A KIRKIRETA DAN TAZAMA FANSAR FARINCIKINKA BA YAYA YUSHAU MURUFE WANNAN CAFTAR AUREN JUNA DA MUKAI A BAYA KUSKURENE DA CIN AMANAR ZUCIYOYINMU WADANDA DUK BA HAKA SUKESO BA HAKA ZALIKA IYALAN DAMUKA SAMAR BA HAKAMUKASO BA NI NAI DANASANIN HAIHUWAR SU DOMIN TAUSAYIN RAYUWARSU KAI KANA BAKINCIKIN HAIHUWARSU DOMIN TAUSAYIN RAYUWAR SU KAIKANA BAKINCIKIN HAIHUWAR SU SABODA BASU FITO DAGA MACEN DATA CANCANCI HAIHUWAR 'YA'YANKA BA, KI Bar Maganar Nan Dan Allah Tafara Tafiya Ya Ce Zansa Karfi Da Lallashi Kidawo Rayuwata Zanbaki Abinda Ban Baki A Baya Ba Wato So Da Kulawa, Takada Kai Ta Ce ToGA HANYA NAN AMMA KAMAR AKWAI WANDA YAFIKA KARFI DA IYA LALLASHI AKAN HANYA WATO DAN AUNTY. . To en gidan nan ku zama shaida Ruma ni take so , kunji dai da bakinta..lol. . Sai jibi ma dora. . Dan Aunty GORAN DUMA (p 52) . . Takada Kai TaCe To GA HANYA NAN AMMA KAMAR AKWAI WANDA YAFIKA KARFI DA IYA LALLASHI AKAN HANYA WATO MAHAUKACIN MASOYI IN ALAMUN KARFI YANAGA MAI KIBA SAI INGA KAMAR ZAI IYA KAYARDAKAI Tunda tai maganar Tai Taga Yanayin Sa Ya Sau Dan taga Ko suna Da Alaka Da Mahaukacin Masoyi,ransa A Bace Ya Ce wanene Mahaukacin Masoyi? Wannan kuwa Ba cin Fuska Bane?Zakijerani Dawani waima Mahaukaci Asan Dan kinga Nafada Sonki Ruma? Saitasami Kanta Dayimasa Murmushin Mamaki Sannan Takauda Kai Batare Data Amsamasa Ba Tawuce Cikingida Ta Barshi Agurin Motocin Sumoli Naleke Ta Window,gabadaya Zuciyar Ruma Ta Zaku Da Sanin Mahaukacin Masoyi,tanazama Adaki Sai Ga Sakonsa Ta Waya Wanda Ke Nuna Shaidar Yagama Kallon Diramarta Da Yushau HANKALINA SOYAKE YA KWANTA ASHE BANI NAKE YAUDARAR ZUCIYATA BA? TAJIMA TANA RADAMIN ZAKI SOMU, Cikin Karkarwar Hannu Tasami Kanta Da tafa Gajeren Sako Taimasa Amsa A Karo Na Farko,WAYE KAI? INA SON IN SANKA, Taitajiran Amsa Har Karfe Goma Na Dare Tadinga Kiran Wasu Layiyyinkansa Bata samuba Taji Afuwar Son Tasan Mahaukacin Masoyi A Yau Tamkar Dandayaso Fitowa Cikin Mahaifiyar Sa Dan Haka Tanemi Abinda Yake Mata Dadi A Duniya Tarasa,sai Ta Hau Social Network Ta Tura masa KALAMANKA NA NUNA JARUMTA A SOYAYYA DA RAYUWA,AMMA AYYUKANKA SUN KASA TABBATAR DA HAKAN,YAKIN BOYE DAGA MUTUM BOYAYYE? LALLAI BUYA YAYIN CIMMA BURI ALAMACE TA RAGONTAKA,IDAN BA A CIKIN RAGWAYE KAKE BA INASON INSANKA, Tafi Awa Biyu Sannan Tasami Gajeriyar Amsa Ta Inbox Dinta A Facebook,LOl! BANSAN NI RAGONE KO JARUMI BA,ABINDA KAWAI NASANI NI MAHAUKACINE A SOYAYYARKI MAHAUKACINDA IN BAI SHIGA SAHUN DAKARU A KWANJI BA DA ADALCI ZA AKIRA SHI BARDE A SOYAYYA,KINA SON GANINA? NAZACI KINCI ALWASHIN GANONI DA KANKI, TANAKARANTA Wanna Sakon Nasa Tamike Zumbur Kawai Saitasami Kanta Da Kwankwasa Kofar Dakin Baccin Hajiya Tsawon Mintuna Biyar,sai Ga Hajiya Tafito Daga Sashen Alhji Cikin Magagin Bacci Fuska Cike Da Tsoro Tana Duban Agogo Wanda Yanuna Sha Biyu Da Rabi Lfya Jikin Ne Ruma? Arikice Take Idanta Fal Da Kwalla Takama Hannun Hajiya Inason Zuwa Abuja Gobe Indawo Jibi,kinemarmin Wannan Damar Wajen Alhji Dan Allah Meyafaru? Wani Abu Kike Da Bukata Kikejin Mu Bazamu Iya Yimiki Ba Sai A Abuja? Kina Girgiza Kai Kina Kuka? Amsarki Na Nufin E,h Da A,a Kenan,ba Abin Kuka Bane Hajiya,raunina Ne Kawai Yakawo Kukan,a Barni Inje Abuja Nai Alkawarin Da Nadawo Zansanar Dake Komai kuma Na Rantse miki Da Allah Sai Kaddarar Ubangiji Inzan Dara Jib Ruma Na Sauka A Tashar Utako Maimakon Ta Dauki Shatar Mota Zuwa Gidantake Wuse,kawai Saita Umarci Dan Tasi Dayakaita Milkway Cafe Bata Da Yakinin Zatajima A Ciki Ko Bazata Jimaba Dan Haka Tasallami Dan Tasi Tataka Cikin Barin Jiki Dana Zuciya Ta Shiga Kantin,babu Abinda Ke Yawo Aranta Irin Sakon Mahaukacin Masoyi Na Safiyar Yau INAJI A JIKINA A YAU ZANGA MASOYIYATA, Kamar Kullum A Milkway Na Baya BaBu Abinda Ya Ragu A Kallon Mayatar Da Ma,aikatan Gurin Kemata Saima Karuwa Datake Tsammanin Yi,itama Ta Dake Ta Janyo Daddatan Magani Ta Ci Kuma Tadinga Tafiyar Kasaita Har Taisa Bangaren Datafi Wayo Wato Yanar Gizo,ina Son Ganin Manajan Gidannan Malam Bayan Sallamar Ko Gaisuwa Bataimasa Ba To Madam Kira Shi Za Ayi Ko Kuma Kai Ki Gurinsa Za Ayi Akaini, Kaitsaye Tafada Cikin Cin Magani Tamike Tana Rataya Jaka,zo Muje,bayan Yagama Jimaminsa,har Ofishin Manaja Tai Arba Dashi Gajeren Mutumin Nane Wanda Ya Ce Kallanta Yafi Kallon Talabijin,suna shiGa Taga Fuskar Rashin Gaskiya Atare Dashi Lfya Garba? Yatambaya Arikice Bayan Tafiyar Garba Office Din Yai Shuru Shiyasakata A Kwandan Shara Yanata Tafa Sako A Wayar Sa Itakuma Tanata Nazarin Ofishin To Hajiya Inajinki, Nazo Ne Inji Dalilinda Yasa In Nazo Gidan Nan Nake Zama Muku Magiji In Ban Manta Ba Kaida Kanka Ka Taba Fadamin Nafi Majigin Dadin Kallo Mudin? Kalmar Dayafada Cikin Alamar Shakansa Ma Baiyarda Da Kansa Ba, Kudinfa Ta Amsa Rai A Bace,yai Kasake Hankalinsa Nakan Waya, Shikenan Abinda Kikeson Sani? A Amsa Min Wannan Tambayar Mana Sai Aji Idan Akwai Wata, Karon Farko Dayai Murmushi, Kin Tsargu Ne Kawai Amma Ni Ban San Munakallanki Kamar Majigi Ba,nidai Kawai Nasan Bama Iya Ganinki Bamu ShiGa Rudani Ba Amma Har Yau Bamu Gano Dalili Ba,duk Da Haka Kiyi Hakuri, ruma Taji Kamar Ta Kwarfa Masa Mari Saboda Haushi Amma Ta Hadiye Ta Balle Jaka Ta Fito Da Takardar Mahaukacin Masoyi Wadda Ya Aiko Ta Gidan Waya Kuma Daidai Wannan Lokacin Sakon Mahaukacin Masoyin Yashigo Wayarta, ASHE DA GASKE KINA SON GANINA DAN ALLAH MEYA KAI HAKA DADI A DUNIYATA TA YANZU? TA Hada Da Wayar Da Wasikar Duba Wasikar Nan Waya Rubuta Ta Agidannan Kuma Sa Hannun Watake Dauke Dashi Duk Taimasa Tambayoyine Cikin Hanzari Da Hadiye Rikitarta Manaja Yafi Minti Biyar Yana Juya Waya Da Wasika Sannan Yadago Muryar Sa Na Rawa Ya Ce,lambar Da Sanya Hannu Duk Na NAZIFI MUHAMMAD NE Nazifi Muhammad? NAZIFI MUHAMMAD? Tasake Maimaitawa A Rude Ganin Yakasa Amsa Mata Kuma Yana Bintada Wani Rudadden Kallo,amma Bakinsa Yakasa Furta Kalma Ko Guda,taja Kujera Datun Tuni Take Tsaye Rike Da Majin gininta Ta Zauna Inatambaya Kayi Shuru? Madam Tambaya Kikayi Kenan?Nazaci Maimaita Sunan kike Domin Yanamiki Dadin Fada? Ta Hadiye Doki Da Mamakinsa Kuma Datakara Saitajanye Dukkan Rudanin Da Fuskarta Ke Nunawa Ta Barwa Zuciyarta Tanaji Dasu,to Ba Bu Laifi Inason Ganinsa,baya Gari Takara Zuramasa Ido Kuri Tsawon Lokaci Ta Ce Menene Matsayinsa A Gidan Nan? Shine Mamallakin Wajen,da Sauri Tajuyo Amma Naji Kakira Sunanshi Kaitsaye? Yadan Fara Dariya Aikamawa Take A Daure Mai Daurewa,hakane Ina Son In Sani Mutum Ne Ko Aljan? Mamaki Ya Bayyana Karara A Fuskar Sa Bakinsa Na Rawa Ya Ce Wanne Irin Aljani Kuma? Dama Aljannu Abokan Huldarmu Ne Dahaar Zan Shaida miki Shi A Mamallakin Gidan Nan, tatareshi Cikin Ci Da Zuci Kukusani Ni Ba Matsayinsa Nazo A Sanar Dani Ba,shinakeso In Sani Dan Haka Karmu Ja Maganar Kasanar Dani Ranar Dazai Dawo, To Kahadani Dashi A Waya Cikin Jimami Ya Ce To Bara Nanemi Izini Agurinsa Yatafa Sako Yaturamasa Sannan Ya Tsaya Dako,can Sai Ga Amsar Amincewa Sannan Ubangida Nasa Yakirashi A Waya,kaitsaye Shikuma Bai Daga Ba Saiyamika Wa Ruma Tare Da Mikewa Yabar Falon Tadaga Wayar Dajin Karfin Gwiwar Juya Harshe Yadda Taso,amma Daga Sallamar Sa Ya Warware Mata Duk Notikan Laka Da Karfin Hali Baki Yahau Karkarwa Jiki Yadauki Bari,duk Da Haka Bata Iya Amsa Sallamar Ba,ranki Yadade Ance Kina Son Magana Dani,?Tattausar Muryar Tasa Takara Dukan Dukan Kunnenta Da Zuciyarta Kawai Saitaji Wani Irin Rauni Ya Mamayeta Dan Haka Batun Tai Maganarma Bata Tasoba Rumaisau Kinajina Kuwa? Cikin Mamaki Tadanyi Wani Nishi, Waye Wa,,,,wa Takasa Direwa Kawai Saita Hakura Rumaisau Yaya Jikin? Kawai Saitasami Kanta Da Sheshekar Kuka Itakanta Takasa Tantance Abinda Yasata Kuka baitankamata Ba Tsawon Lokacin dataji Kamar Bawa Kanta Hakuri Amma Kafin Tafadi Abindata Sak'a Fada Ya Rigata Cikin Wata Irin Murya Mai Rauni, "kin Dauki Hakki. . . Dan Aunty GORAN DUMA (P 53) . . Kin Nemi Tarwatsa Zuciyata Mai Sauraronki Kina Kuka,,dakin San Hakane Da Ba Kice A Hadaki Daniba Gara Yin Umarnin Duk Inda Nake Nazo Nasameki Zanyi Biyayya Nazo Kuma Ina Da Yakinin Inkinga Kaunarki Dake Kwance A Kwayar Idona Zaki Tabbatar Inkinyi Kuka Agabana Zaki Cutar Dani,maganganunsa Sunkara Rudata Ainun,data Lalubi Ilahirinta Sai Ta Tarar Ita Kanta Neman Manta Kanta Take,bare Ta Tuna Maganar Dazata Fadawa Wannan Majanunin Magana Wadda Ta Shafi Jiya Dayau Dinta Shida Ba A Toshe Masa Basirar Ba Saiyaja Sunanta A Hankali Tamkar Yaimata Allura Saigata A Farke,bakinta Yagaji Da Bari Ya Furta Abinda Kwakwalwartata Ta Kera Watakila Ina Kuka Ne Saboda Bansan Da Irin Mutumin Danake Tare Ba,,ina Kuka Bisa Yadda Kake Wahalar Da Zuciyata Tare Da Gangar Jikina Yakatse Ta Cikin Muryar Lallashi Kinga Yi Hakuri Ki Koma Gida Zanzo Nasameki Har Gidan Ya Katse Wayar, Ruma Tai Tsuru Da Wayar A Kunne Batare Data Iya Saukewa Zuciyarta Na Bugawa Fat Fat Hajijiya Na Dibanta Saidai Takasa Motsawa Nanda Can Sai A Manaja Ya Ya Ce Mata Kano Kika Nufa Ko Wuse? Ta Juyo Tana Binsa Da Kallo Da Alamar Tai Mamakin Jin Kanonta A Bakinsa Da Wuse Wannan Ya Tabbatar Mata Duk Shakiyancin Da Ake Mata Yana Da Masaniya Saitaji Ranta Yai Mugun Baci Ta Ajiye Masa Wayar Sa Takarasa Goge Hawayenta Kunnuwanta Kuma Na Sauraronsa Yace Yayi Umarnin Duk Inda Kika Nufa Idan Kina Da Bukata A Bayar Da Mota Akaiki Bata Tsinka Ba Kallan Dataimasa Yana Tattare Da Amsar Banida Bukata Ta Wuce Kai Tsaye Batare Data masa Sallama Ba Ta Bar Office Din, Shikuma Baidamu Da Basarwarta Ba Yatake Mata Baya Ya Rakota Har Bakin Titi Ya Tayata Jiran Tasi,bai Mata Magana Ba Itama Hakan Bayan Sun Tsayar Da Motar Shiya Sallami Mai Tasi Yaimata Bankwana Ita Ko Tankasa Bataiba, Tana Mota Tanata Lissafe Lissafen Yadda Nazifi Yake Da Yadda Har Ya Wuce Makadi Da Rawa A Sha'anoninta Har Dana Tsakaninta Da Zuciyarta Wadanda Suka Yi Kama Da 'ya'yan Cikin GORAN DUMA Wanda Sai Anfasa Za A Iya Lissafawa Tai Shige Da Fice A Duk Lungunan Zuciyarta Dakuma Magabatan Alamuranta Musamman Cikin Rayuwarta A Abuja Dakuma Milkway Danta Gano Ko Ta Taba Cin Karo Da Wannan Mai Kiran Kansa Mahaukacin Masoyi,amma A Sunan Manajansa Ya Shata Masa Wai Nazifi? Ta Shafa Sosai Ba Ta Tuna Shi Dinba Sai Can Ta Dan So Ta Tunano Shi Bayanta Tariyo Sha Biyar Ga Watan Nuwamba Na Shekarar Dubu Biyu Da Sha Biyu A Kwakwalwarta Shugaban Milkway Ya Fado Mata,amma Acikin Basaja Yadda Yanzu Zata Kasance Cikin Shakkunshine Nazifi Kokuma Wani Daban 15 Nov 2012 Sunyi Da Nusaiba Kanwar Mijin Yayarta Balaraba Zatazo Raka Ta Milkyway Dan Ta Siyo Ipad Satika Kadan Da Fara Rubutunta A Jaridar Aminiya Don Saukaka Mata Aiki,sai Nusaiba Taimata Waya Cewa Suhadu A Milkyway Ta Tsayar Da Motar Innarta Honda A Harabar Milkyway Tanemi Kiran Nusaiba A Waya Amma Saita Tarar Wayarta Ba Bu Ko Kobo Haka Tajima Zaune Cikin Motar Tana Waige Waigen Shigowar Nusaiba Dazama Yafara Gundurarta Saita Fito Ta Rumgume Hannu Ta Jingina Da Motar Tana Ta Faman Baza Idon Kan Motoci Da Mutanen Dake Shige Da Fice A Wajen,cikin Haka Wata Shudiyar Jeep Ta Shigo Harabar Milkyway Hade Da Tagumi Ta Tsura Mata Ido Har Tazo Ta Gifta Ta Kadan Tatsaya Kafin Kuma Ta Gifta Ta Din Ne Suka Hada Ido Da Matukin Motar,wani Matashi Baki Mai Dogon Hanci Da Fararen Idanuwa Yana Sanye da Bakin Wando Da Shudiyar Tshirt Da tambarin Mikyway Cafe Ta Kawar Da Kai Saidai Jikinta Ya Ci Gaba Da Batashi Baidauke Idanuwansa Daga Kanta Ba Harya Wuceta Kamar Mintuna Goma Bai Bude Motar Sa Yafito Ba Tana Tsaye Tana Ci Gaba Da Waige Waigenta Har Idonta Yazo Zagaye Kan Motar Sa Adaidai Lokacin da taGa Yana Gyaran Madubi Da Alama Ita Yake Karewa Kallo,ranta Yai Mugun Baci Har Ta Zabga Masa Harara A Duhu Tayi Tsaki Tare Da Duban Agogo Cikin Takaicin Nusaiba Asannanne Tasami Azancin Shiga Ciki Tasanya Kati A Wayarta Dan Kiran Nusaiba Ta Rufe Motarta Tanufi Ciki Agurguje Ya Rufe Mota Ya Biyo Bayanta Don Haka Takara Daga Kafa Dab Da Isarta Ta Waiga Saitaga Manaja Nadan Rusunawa Matashin Nan Yana Masa Barka Da Zuwa Tasake Hada Ido Da Shi Tadan Motsa Baki Alamar Bataji Dadi Ba Ka Share Yallaban Nan Yau Malam Kakira Ni Da Muhammd Kawai Domin Acikin Tarko Nake Neman Maitayani Yakin Kubuta Nake Batare Da Daddawar Da Na Kamo Ta Subuce Ba,bata Damu Da Zantikanta Da Suka Biyo Baya A Tsakanin Matashin Da Manaja Ba Domin Zaurance Suke Harma Da Sauya Harshe Zuwa French Wanda Gaisuwa Kawai Ta Iya Dashi A Cikin Zafin Nama Kuma Sai Gasu Gaban Kantar Lokacin da take Mika Dubu Dayan Katin Sun Dauke Hankalin Mai Bata Katin Dayimasa Zance Shima Cikin Harshen Da Bata Lakanta Ba Dan Haka Yakasa Dauko Mata Katin,ranki Yadade Barka Da Yau,inji Matashin Nan Wanda Yadamu Da Kallonta Bayan Yazo Dab Da Ita Ya Tsaya,,yauwa Barka Dai Kamar Nasan Fuskar Nanfa Afuwa Cankowa Nakeson Nayi Yasa Nadamu Da Kallanki, Ta Gyara Tsayuwa Da Kyar Ta Ce Hmm,,kamar Munyi Karatu Da Kyar Ta Ce,,hmm,,kamar Munyi Karatu Tare?Bata Tankamasa Ba,hm,,,bani Katin Mana,,, yadan Yi Turus Cikin Kallanta Sannan Ya Ce Ranki Yadade Kozaki Miko Min Wayar Na Kwashe Miki Lambobin Ansami Matsala A Katin munan Idan Ba Ai Taka Tsantsanba Batai nazarin Komai Ba Tamika Masa Wayar Karaf Manaja Ya Amshe Wai Shizai Samata Da Alama Na Takuramiki Ko? Ba Haka Bane Wai A Ina Mukai Karatun Tare? Alamar An Kureshi Ya Ce A Bayero Univer Sity Mun Karanci Aikin Jarida Wannan Yasa Tadan Sauko Harda Murmushi Hakane Yaya Bayan Rabu Sai Alkhairi Tuna Min Suna Ta Ce Cikin Kwanciyar Hankali Rumaisau Aliyu Ahmad Haka Kuwa Na Tuna Takara Dubansa Da Kyau Da Alama Tanada Shakku Saidai Yadda Yayi Fuska Saitaji BaBu Bukatar Ta Tambaye Shi Kokuma Tayi Ja Inja Dashi To Hausawa Sunce Bata Karya Wuya To Kuwa Ta Yafo Ta Harzuwa Lokacinda Za A RaBu Saura Dame? Sai In An Kuma Haduwa Haka,nikuma Sunana Nazifi Muhammad To Madallah Ta Tattara Dukan Hankalinta Ga Abokinsa Gajere Wanda Take Tsammanin Abinda Yake Da Wayarta Ya Wuce Loda Kati Ta Tsuke Fuska Ta Ce Masa Malam Yayadai? Kar Ka Wuce Gona Da Irifa!Yaki Dagowa Ya Dubeta Yana Bata Amsa Habadai Aimu Bamu Da Irin Ma Shimuke Nema Madam Yana Rufe Baki Yamika Mata Wayar Ta Karba Tana Tura Baki Bata Tanka Wa Kowa Ba Ta Bar Gurin Kwaji Dashi Tafada A Fili Ta Fice Daga Farfajiyar Tana Neman Nusaiba ,nusaiba Takaraso Suka Shiga Sayen Wayar Inda Batasamu Siyen Ipad Din Datai Niyya Bama Sakamakon Garabasar Waya Mai Tsada Da Suka Yi A Kananun Kudi Abinda Ta Iya Tunowa Kenan A 15 Nov 2013 Amma Tayi Ta Tuno Fuskar Sa Takasa Ballantana Ta Iya Tuno Ko Ta Kalli Kafarsta Taga Kofato Shiyasa Data Tuno Hakan Baiwani Sanyaya Mata Raiba Yadda Ranta Ke Jagule Saitaji Inama Ace Ta Wuce Kano Yau? Duk Tsiya A Yanzu Kano Tafi Abuja Kwanciyar Hankali Domin Basajar Kano Ta Waya Da Social Network Kawai Ake Mata Amma Ta Abuja Bayan Rainin Hankali Tattare Dake Databa Rai, Ta Karkare Ta Hadiye Damuwarta Bayan Ta Tarad Da Gudan Jininta Hamida Ba Bu Lfya Wani Kurji Ya Fito Mata A Kirji Tanata Faman Jinya Saita Fake Da Tausayin Hamida Ta Hada Kukan Tausayin Da Basajar Mahaukacin Masoyi Ta Ci Kuka Ta Koshi A Zuwan Ciwon Hamida Ki Gode Allah Kawai Da Ba Kauye Kika Bayar Da !Yar Riko Ba,munyi Tunanin Huda Mata Kirjin Nana A Gida Amma Muka Nufi Asibiti ashe Damunyi Hakan Da Danyen Hukunci Muka Yanke,inji Momin Ruma Ruma Ta Tsayar Da Kuka Tazaro Ido Cikin Mugun Kaduwa Lallai Allah Ya Tseratar Da Hamida Domin Da Anyi Hakan Akwai Matsala Saita Biyewa Momi Wajen Hamdala Ga Allah Har Washegarin Momi Najiran Jin Wani Abu Daga Ruma Akan Zuwanta Abuja Domin Hajiya Tasanar Mata Komai Amma Ruma Taki Tankawa Duk Da Cewa Ko Gabadaya Aka Duba A Jikinta Tana Nuna Damuwa Da Kasala Amma Iyakarta Haka Cikinta Mai Hadama Ya Hadiye Shi Kadai ya Hana Bakinta Furtawa Sai Ga Tama Tana Shirin Komawa Kano Momi Takasa Daurewa Saita Tareta Da Zancen Tunjiya Nake Kawaici Inajiran Jin Kin Furta Abinda Ke Damun Zuciyarki Da Rayuwarki Amma Ga Alama Kina Son Na Karya Billena Na Tambaya, Ruma Tayi Walai Da Ido Tana Murmushin Yake Lah! Mekika Gani Momi? . . Dan Aunty. GORAN DUMA (P 54) . . Ni Ba Bu Abindayake Damuna,kinganki Kuwa? Komai Naki Yana Nuna Damuwa Inana Ture Wayar Damukai Da Hajiya Kenan,ruma Tayi Kasake Bata Da Ta Cewa Tunda Hajiya Ta Burma Mata Ciki,momi Ma tadan Ja Fasali Fadamin Ruma Meke Faruwa? Naso Ace Saida Kikazo Gidan Nan Sannankika Nufi Sabgar Taka Kawoki Abuja Nayi Niyyar Sanyawa Abiki A Boye Aga Abinda zakiyi,amma Saikika Shammaci Niyyata Har Yanzu Ruma Bata Da Niyyar Tankawa So Ma Take Ta Fashe Da Kuka Saboda Tunano Yadda Tayi Kwanar Jinya Da Zuciyarta Kowa A Kuntace,kame Kamen Tashoshin Ainihin Mahaukacin Masoyi Ya Cunkushe Wa Kwakwalwar Amma Har Cajinta Yakare Bata Canko Wadda Zata famata Shi Tar Tar Ba Anya Wannan Rayuwar Zata Dore Ciki? Ta Ina Zata Bi Ta Kubuta? Kawai Sai ta sami Kanta Cikin Hawayen Momi Kam Tausayin Da Rauninta Akan Ruma Tana Hadiyewa Har Taci Nasarar Data Bata Kwarin Gwiwar Yimata Nasiha Zanyi Murna Idan Ba Tarkon Soyayya Kika Fada Ba Ruma Dan Banasan Kifada Tarkon Son Mutumin Da Bai Cancanta Ba Dan Baisan Muhimman cin ki Ba Haryaja Ragamar Rayuwarki Cikin Son Zuciyar Sa Kawai,mace Irinki Datafi Sauran Mata Rauni Tana Bukatar Taka Tsantsan Acikin Soyayya Kinfi Kowa Sani,aranta Ta Ce Kamar Momi Nasan Cinka Abinda Ke Wakana A Tsakaninta Da Mahaukacin Masoyi Saidai Kurkuren Lis Cewa Ita Tafada Tarkon So Ba Wata Hallitar Ce Tafada Tarkon Son Nata Ba Kila Momi Bata Taba Hasaso Ko Tarkon Sonka Aka Fada Kana Iya Shiga Hadariba Ta shiGa Goge Hawayenta Batare Data Kammala Tunaninba Inafatan Dazara Kinkoma Zaki Cikawa Hajiya Alkawarin da kika Daukar mata? Da Sauri Ruma Tadago Tayi Ma Momi Duban Rashin Fahimta Momi Tamike Tana Shirin Barin Wajen Tana Amsa Mata Tafadamin Kin Mata Alkawarin Kina Komawa Zaki Sanar Da Ita Dukkan Abinda Ke Akwai Ruma Tashi Ga Gyada Kai Batare Da Hayyaci Ba To To,,,,dama Bazan Karya Alkawari Ba, ************ tana Isa Kano Daidai Lokacindatake Shiga Harabar Gidansu Sakon Mahaukacin Masoyi Nafado Kasancewar Wayar Na Hannuta Cikin Dukan Zuciya Ta Kashe Ido Ta Hau Dubawa BARKA DA ISOWA RANKI YADADE,IDANKIN HUTA KILA ANJIMA NA SHIGO MUGA JUNA MAHAUKACIN MASOYI Bataji Bakinciki Kofargaba Game Da Sakonsa Ba Tadai Samikanta Cikin Saurin Shigewa Cikingida Wanda Batafara Mamakin Neman Dalilinsa Ba Sai Gata Tashiga Gidan Mutangida Nata Hidimar Murnar Yimata Maraba Rashinki Ko Na Awa Dayane Agidan Nan Kufai yake Mayaimin Da Gidan,inji Mubarak Koyai Dariya Amma Ruma Murmushin Yake Hajiya Tun Daga Shigowar Ruma Tadora Mata Ido Ta Cemasa Idan Tai Aure sai Muga Yadda Zakai Mubarak Zaiyi Magana Tatare Shi Kajira Nai Sallar Magariba Bar Tadin Ka Wuce Alwala Yawuce Yana Dariya Aima Zan Barta Ta Huta Sai Gobe Zamu Fanshe Hirar Kiyi Sallah Kici Abinci Muzauna Ko? Fuskarta Ba Bu Alamar Wasa Kilatayi Hakan Ne Dan Kar Ruma Takawo Mata Wargi Hakanyasa Ruma Tadinga Komai Cikin Fargaba Tana Saka Yadda Zata Sanar Da Hajiya Murdadden Labarinta Da Mahaukacin Masoyi A Kar She Tatarar Da Bata Da Zabi Illai Tasanar Mata Komai Tinda Tai Alkawari Da Wayarta Akai Tattaunawar Tadinga Nunawa Hajiya Komai Na Sakonninsa Duk Da Hajiya Takidime Amma Bai Hanata Magana Anutse Ba Meyasakika Ci Gaba Da Rike Wannan Abin A Zuciyarki Kekadai? Kuma Mekikaje Yi Abuja? Hajiya Taimata Karin Bayani Ikon Allah HajiYa Tafadi Cikin Jinjinawa Tare Da Nanata Kalmar Duk sunyi Shuru Zuciyar Kowanne Tai Nisa A Saka Wani Aikinda Zuciyartata Ta Hada Cikin Lissafin Shine,fargabar Allah Yasa Anjima Din Nasa Karta Zamo Tsakar Dare Dan Karya Bayyanar Mata Abinda Tafi Zatonsa,wato Aljani Ko Kadan Batason Ya Bayyana A Haka Batare Da Dalilin Tsoronsa A Aljani Ba Saitare Da Dalilin In Aljanin Ne Sun Rabu Kenan,inkin Amince In Sanar da Alhji Wanna Katon Labari In Ganin Dole Maza Su Shigo Ciki Hajiya Ta Katsewa Ruma Tunani Duk Da Ita Ma Bata Hattama Nata Tunanin Ba,amma Tasanya Masa Karfi,mujira Yau Da Gobe Da Jibi Dan Ganin Abinda Zai Biyo Baya,karmu Tashi Hankalin Kowa Hajiya Kila Lamarin Baikai Natashin Hankali Ba,yaya Zanyi Da Mominki Mai Jiran Nakai Mata Kanun Matsalarki? Hankalin Momi Atashe,,,rumaisau Rumaisau Tamike Cikin Alamun Son Ficewa Daga Falon Fuskarta Na Nuna Gajiyar Jiki Data Zuciya Ki Kyale Ta Kawai Hajiya Yadda Momi Take Damuwa Cikin Matsalolina Inason Duk Abinda Zataji Akaina Indai Zan Iya To Taji Mai Dadi,,shikenan hajiya Ta Fada Badan Taso Ba Ta Bi Ruma Da Kallo Har Ta Kule Tanadan Dingisa Kafarta Wadda Kem Bayan Kwanar Fargaba Tare Da Tsammanin Bango Zai tsage Mahaukacin Masoyi Ya Bullo Ruma Batasami Bacci Ba Saikarfe Hudu Saura Hakan Ya Janyo Da Kyar Ta Iya Katse Bacci Ta Gabatar Da Sallar Asuba Akan Lokaci Sannan Ta Koma Ta Ci Gaba Da Ramuwar Bacci,karfe Tara Daidai Wayarta Ta Farkar Da Ita Da Shigowar Kira Saidata Koshi Da Kallon Agogo Har Kiranya Katse Sannan Tasami Taba Wayar Daidai Lokacin Wani Kiran Yasake Shigowa Ta Daure Ta Hadiye Kasalarta Ta Daga Tare Da Sallama Yushau Ya Amsa Cikin Kuzari Nayi Ta Baza Ido Inganki Gidan Atika Jiya Har Dare Bangankiba Kuma Naji Atika Ma Na Mitar Baki Zo Dubata Ba,ta Basar Ta Ce Yau Zanje,yushau Yadan Jinkirta Sannan Ya Ce Karfe Nawa? Ina Son Mu Hadu Ne Akwai Muhimmiyar Maganar Danake Son Mu Tattauna,bansan Lokacin Dazan Shiga Ba Tafada A Raunane,amma Ta Raunana Muryar Tatane Dan Ta Basar Da Zuciyarta Wadda Ta Dauki Zafi Inta Bar Muryarta Dazafi Kila Ya Rage Mata Kima Shikuma Saiya Marairaice Kidaure Ki Tsara Lokaci Shigar Taki Ko Saboda Ni, Ba Lokaci Zanzo In Batamiki Ba Ruma Ragowar Rayuwarmu Nakeson Muyi Wa Garambawul, tayi Iyakar Bakin Kokarinta Tai Magana Amma Takasa Don Kar Ta Cika Rashin Mutunci Da Kyar Ta Ce Ok Yushau Baidamuba Yasake Zagewa Da Rarrashi Ko Wuni Zakiyi? E,h Wuni Zanyi Toki Saka Idan Ganina Bayan Laasar Yayi Kyau Ta Amsa Masa Ta Kashe Wayar ******* A Gaggauce Yushau Yahau Shirin Fita Alhali Ya Shaidawa Sumoli Yaukansa Ciwo Yake Kodake Da Biyu Ya Ce Haka Dankartadameshi Yasamu Damar Yin Tunani Hanyar Dazasu Samo Masa Ruma Na Biyu Kuma Mugun Haushinta Yakeji,jiya Ya Dauketa Yakaita Gidan Atika Da Kwadayin Haduwa Da Ruma Yadinga Zarya A Gidan Tsammanin Ganinta Amma Har Dare Ba Bu Labarinta Ta Ce Masa Kaikuwa Dan Allah Ko Bazaka Sauya Motar Nan Ka Daure Kakai Ta Gareji Adan Kwaskware Injinta Ayimata Sabon Fenti Fisabilillahi Kai Ko Kunya Bakaji Kowa A Danginka Shar Shar Da Motocin Nunawa Sa,a Amma Kaikana Fama Da Karfen Shekaru Aru Aru Haka Zuciyar Yushau Ke Tafarfasa Daidai Yadda Sumoli Take Masa Magana Tunda Uban Wani Bai Sayi Shar Ya Baniba Sai A Kalleni Da Wanda Allah Ya Bani Sai Dai Idan Anga Ban Cancanci Zama A Irin Wannan Duniyar Da Wannan Motar Ba To A Iya Kokarin Rufe Ido A Bude Kar Aganni, ai Bakafadi Ba Yushau Idan Ka Saka Wa Ubana Da Zagi Da Cin Fuska Tunda Yadauki Aure Yabaka Da Wuya Ba Bu Dadi Ina Zaune Ina Rufa Maka Asiri Yakada Kai Cikin Fushi Sumoli Takara Da Cewa In Ma Sake Zagina Zakai Yushau Zageni Mana,,,, insauran Gashin Kumarka Bai sanyani Kuka Zaginka Ai Bazai saniba Karamin Misali Auranmu Kusan Shekaru Uku Banta Ba Batan Wata Ba Amma Dan Masifar Mammako Sha Katafi Kakasa Kai Ni A Nemo Dalilin Rashin Haihuwata,,.,,ta Dawo Cikin Kwalliya Malam Inakake Shirin Zuwa Bayan Kace Bakajin Dadi Ya Cemata Yasamu Kiran Gaggawa Daga Office Ta Ce Bara Nadauko Mayafi Mufita Tare Inba Gidanku Zakaje Ba,gidan Dakana Rabe Rabe Kana Komai Amma Baka Kasa Motsa Kwanjin Son Zawarci Ba,yafice Bai Tanka Ba Tadawo Da Mayafi Ya Ce Wai Malama Ina Zakibine? Muje Kasaukeni Gidan Atika mana Kashiga Ka Biya Kudin Lesunan Ankon Suna.... , dan kari, ni ma dole naje gidan Atikar nan nasha kallon yadda zata kaya, ko da akwai pasinja anan gidan?? . Dan Aunty. GORAN DUMA (P .55) . . Dubu Nawa? Dubu Arbain Da Takwas Mana Ta Amsa Masa Kai Tsaye Tana Taunar Cingam Kas Kas,cikin Tsawa Ya Ce Daga Dubu Goma Bazan Karamiki Ko Ficika Ba In Baki Da Kudi Ki Mayar Musu Kayansu Ba Bu Jimawa Sai Gata Tadawo Dauke Da Lesunan Ta Zube Masa Kan Gado Cikin Fusata Gasunan Katafi Dasu Ka Mayar Bani Dubu Goman Zanbi Wata Hanyar In Samo,ai In Na Ce Dakai Zan Dogara Har Abada Araba Danni Zan Tabbata Bai tanka Ba Ya Kirga Dubu Goman Ya Zubemata Kan Durowa Ya Kwashi Lesunan Yafice Sannan Ta Kwashi Kudin Tajefa Ajaka Ta Kulle Gidan Ta Fice Sai Gidan Wata Kawar Mominta Hajiyar Dubai Da China Ta Kwaso Lesunan Bashi Ta Wuce Gurin Dinki Ta Bayar Da Dubu Goman Yushau A Kudin Dinkin, gidan Abokinsa Mai Kudi Ya Nufa Inda Matar Sa Tasha Fada Masa Matsalar Sikila Da Bukatar Su Ayanzu Kam Yanade Hannu Zaitafi Neman Iliminsa Kaga Na Jaruma Sumayya Mai Zizar Sunan Sumoli,kaga Mutum Na Musamman Wanda Kiyayyar Ruwa Kesashi Kiba Soyayyar Sumoli Ke Sanyashi Rama,, irin Wannan Kirarin Maikudi Abokinsa Kemasa Yushau Kam Kasa Magana yayi. Haka Dai Tazage Tana Bashi Bayanin Masu Ciwan Sikila Saboda Sunadasu A Danginsu Inda Duk Wata Alama Yushau Yaji Tafada Yanaganinsa Ga Ruma Hartagama Yatafi Abinsa Tare Da Yunkurin Komai Zai Daidaita Tunda Yagano Bakin Zaren, ********* garin Rana Sosai Ruma Damai Adaidaita Sahunta Keke Napep Suka Hau Titin Layin Gidan Atika A Unguwar Hotoro Ruma Na Cike Da Dokin Akarasa Gidan taga Dangi Taga Kuma Sabuwar Bakuwar Dasuka Samu,dahaka Tadinga Binne Mahaukacin Masoyi Da Matsalar Sa Koda Na Wuni Dayane Tall,wato Taje Tadawo,basui Nisa Da Hawa Titinba Sai Ga Adaidaita Sahun Ya Mutu A Titin,subhan Allahi Kabiru Meyafaru?? Karfen Nan Yagaji Dani Hajiya Shekaran Jiya Fa na Karboshi Daga Gurin Mai Gyara Inda Yacimin Naira Dubu Ashirin Da Takwas Amma Tunjiya Yafara Yimin Mahangurba,ruma Tadan Yi Dariya Kalmarsata Karshe,ta Duba Agogo Taleko Kai Tana Kokarin Hango Kabiru Wanda Yadawo Ya Shi Ga Turata Gefen Hanya Inda Ya Tsayar Da Shi Gefen Wani Mota B,M,W, Series 5 Wadda Ke Kafe Gurin Tun Kafin Keke Napep Dinsu Takaraso Nan Dukda Akwai Dan Duhu Gilashin Motar Ana Iya Gane Matashin Direban Dake Kwance,mazauninsa Yana Sauraren Wakar The Power Love,maitashi Kasa Kasa Daga Bakin Celine Dion,sama Da Mintuna Goma Ruma Na Cikin Adaidita Sahu Zafi Da Ciwon Jira Na Dimarta Har Ta Kosa Tafito Ta Tsaya Akan Kabiru Wanda Yake Tabe Tabe A Injin BaBurdin,haryanzu Dai Kabiru?Wallahi Kuwa Tundazu Nake Faman Taremaki Adaidaita Din Dazai Karasa Dake Amma Kinga Duk A Cike Suke Zuwa,ikon Allah Tabi Titin Da Kallo Tana Rayawa Aranta Inama Zata Iya Data Karasa A Kafa Ta Huta Da Tsayuwar Ta Dora Da Zolayar Sa To In Hakane Kuwa Zanbaka Hutu Tunda Ga Ya Shirya Hadamu Yayimana Mahangurbar Tare Yau Wannan Zafinda Ake Kwadawa Idan Ya Rikide Yazama Hadari Yazubda Ruwa Fa? Kabir Yafara Yunkurin Tare Wani Adaidaita Dayashigo Layin Yana Amsamata Nima Haka Nafara Tunani Ai Karshen Watan Nan Ma In Allah Yaso Zan Sauya Yana karasowa Sukaga Ai Cike Yake Da Mutane Ruma Ta Rungume Hannu Ta Ce Bar tarewa Ka Koma Ka Lallaba Ko Zai Hakura Ya Bari Ka Karasa Dani, Dukansu Sukai Dariya YakoMa Yana Tabata Mintuna Biyar Tsakani Matashin Nan Ya Bude Motar Sa Yafito Ya Riski Kabiru Baidamu Da Kallon Rumasau Ba Sam,kamar Yadda Itama Bata Mayar Da Hankali Akansa,saida Maganar Sa Taja Hankalinta Ranka Yadade Meyasami Keken Naka Dazaka Shanyata Arana Haka? Abinda Kabiru Ya Kaddara Shine Ruma Tasan Matashin Danhaka Ya Amsa Da Kar Sashi,tsautsayine Yallabai Kuma Muna Ta Kokarin Tare Wanda Zaikarasa Da Ita Bamu samuba,ya Dago Suka Gaisa Yacigaba Da Duba Injin Din,sai Ya Bar Ruma Da Tunanin Ina Tasan Matashin Saurayin Baki Mai Dogon Hanci Da Fararen Idanu,? Bata Canka Ba,takuma Kasa Kojin Kunyar Kallon da take Masa Bare Ta Hakura Cikin Faduwar Gaba Da Raunin Zuciya Iri Iri,can Yajuyo Yadubeta Duban Da Bai Nuna Mamaki Ko Tuhumar Kallan Datake Masa Ba Yadago Ya Dubeta Aransa Yana Mamakin Kota san shine Takemasa Kallo Haka Yanuna Motar Sa Kinga Muje Inkarasa Dake, Tajima Mamaki Yadda Yake Kokarin Bata Umarni Irin Na Yaya Da Kanwa Amma Hakan Bai Hana Ta Daure Gira Ta Cemasa Bisa Wace Hujjar,,? Ragowar Maganar Tamakale A Makoshinta Bayan Tagane Motar Data Dan Gifta Su Kadan Yanzu Ta Yushau Ce Kuma Da Alamu Ya Ganta Dan Gashi Can Yana Kokarin Samun Guri Ya Tsaya Nantake Taji Haushi Da Kyashin Ya Ce Tazo Yakaita Kuma Itama Ta Bishi Suje Gidan Mutane Da Kowa Yagansu Tare Zai Ga Bakinta Arashin Zuciya Kawai Saita Zabi Bin Matashin Nan Wanda Zuciyarta Ta Darsa Mata Kila Irin Kannen Mijin Anti Atikane,tunda Gashi Yasan Ta Ita Kuma Tanai Masa Kallon Sani,to Nagode Tasami Kanta Da Fada Tare Da Kada Kai Alamar Amincewa Ta Dubi Kabiru Ka Kyale Shi Kaje Ka Nemo Mai Gyara Idan Na Dawo Da Yamma Kazo Kasameni Da Sauri Ta Bi Bayan Saurin A Zuwan Bataga Yushau Wanda Ya Bude Mota Ba,da Alama Shima Matashin Kamar Yagane Abinda take Gudu Cikin Zafin Nama Yadaga Motar Suka Bude Yushau Da Kura,daidai Lokacin Dayake Daga Musu Hannu, matashin Ya Figi Motar Kamar Mai Shirin Tashi Sama Fuska Ba Yabo Ba Fallasa Idansa Ga Titi,hakan Kuwa Ya Kada Hantar Ruma Tafara Zargin Kanta Da Gangancin Kaikanta Makasa, Har Suka Kusa Gidan Anti Atika Ba Wanda Yai Motsin Ha,inci Atare Dashi Bai Dubeta, Ba Illa Yanata Hidimar Tukin Motar Sa Yanabin Wakar Sa,can Yajuyo Yana Rage Karar Sautin Au Namanta,ruma Yayajiki,nauyin Da Zuciyarta Tai Wajen Kokarin Ta Gano Inda Tasanshi Kokuma Tasan Muryarsa Ya Sanya Ta jinkirin Amsa Masa,da Sauki,dafatan Iyali Da Kowa Lfya,ta Kara Da Cewa Muryarta Na Rawa,akwai Alamun Ya Shanye Mamaki Lokacin Dayake Amsamata Kowa Lfyar Su Lau,kayi Hakuri Banfa Ganeka Ba Wallahi,, murmushi Kawai Yai Ya Basar Har Suka Karaso Batare Datamasa Iziniba Yanemi Guri Ya Tsaya Da Mota,adan Zuciye Zatafita Bakiji ba? Da Sauri Ta Tsaya Bayan Tafitarda Kafarta Na Farko,yanawasa Da Key Holder Inkinshiga Dan Allah Ki Gaidamin Mai Jegon,takarasa Ficewa Cikin Fusatarta Wadda Kuzarin Gangar Jikinta Ce Kawai Kenunawa Ta Rufemasa Motar Nagode Wazance Yanamata Barkar? Idanta Akan Makullin Motar Dayake Kadawa Cikin Sakanni Kadan Hantar Cikinta Yai Mugun Kadawa Sukadinga Lugude Abubuwa Biyune,wani Irin Kallo Dayake Mata,sannan Da Da Tambarin Milkyway Datagani Manne A Key Holder Sa,batagama Rudewa Ba Bare Tanemi Mafita Ya Tashi Motar Yafara Ja Sannu Yana Amsamata Cikin Murmushi MAHAUKACIN MASOYI Da Sauri ta Janye Jiki Tare Da Kokarin Tantance Shi Duk Da yaja Motar Aguje Haryana Neman Bugeta Ita Ma Kamar Zubin Haukar Bana Ta Diba A Guje Cikin Gida Daidai Lokacinda Yushau Ya Tsayar Da Motar Sa Inda Mahaukacin Masoyi Yadaga A Kidime Tafada Falon Atika Wanda Ke Cike Da Dangi,asiya MAIMUNA HAFSAT,DA YA'YAN KANWAR HAJIYAR SU HASANA DA HUSAINA,jiyo Sallamar Ta Kafinta Shigo Falon Ya Sanya Kowa Yadau Murna musamman Hafsat Wadda Tatashi Yiwa Ruma Oyoyo,amma Ina Ruma A Birkicetake,tana Zuwa Ta Suri Wayar Asiya Komai nata Rawa Sai Gashi Takarde Dakin Da Muryar Abdullahi Madarut Acikin Suratul Bakara Ta Ajiye Akan Kujera Taja Jiki Gefe A Hankali Ta Zauna,,falon Yai Tsit Cikin Alamar Tambaya Kuma Danta Gajarta Musu Aiki Saita Hada Tambayoyin duk Ta Amsa A Kalmomi Kadan,motar Aljani Na Hau Shiyakowani Har Kofar Gida Suka Dinga Duban Juna Anrasa Wanda zai yi magana..... . Dan Aunty GORAN DUMA (P.56) . . Hafsat Ta Ce Shine Wannan Ya Shigo Ta Girgiza Kai Toyaya Akai?Kowa Saitambayarta Yake Sai Ga Yushau Da Kyar Suka Kori Rudu Aka Gaisa Idan Aka Cire Ruma Wadda Take Takure Tana Karkarwa Yushau Yakore Kunya Da Nauyi Cikin Kishi Da Fargaba Da So,cikin Rada Hafsat Ta Matsa Kusa Da Ruma Ko Yaya Yushau Ne Aljanin? Ruma Ta Girgiza Kai ,to Ku Kashe Karatun Mana Kunata Faman Sheka Surutu Kuma Kun Ware Kuna Sheka Kuka Suka Kashe,,,kekuma Kalau?Yanzufa Naganki Lfya Harkina Shuka Min Wulakanci Ki Barni Tsaye Yanzu kuma Gaki A Burkice,duk datana Cikin Rikita Bata fasa Jin Haushin Son Nuna Mata Iko Da Yushau Yakeba Waita Wulakan tashi? Dan kawai Ta Guji Hawa Motar Sa Ta Ce Kai Yaya Yushau Kadaina Mayar Da Allura Garma Wulakancin Mena Shuka Maka? Amma Nasanar Dake Takanas Yau Zan Zo Gidan Nan Donke Daidaine Acce Kin Ganni Kin Shareni? Saima Budeni Da Kurar Dakikayi?Bisa Wani Dalili Zakazo Gidan Nan Domin Ni? Cikin Dacin Murya,kowa Kallansa Kawai Yake Yakore Kunya Kan Tsinkawar Da Ruma Taimasa Gaban Kannansa Inkin Kwantar Hankali Tunda Nazo Ai zan Fadamaki Dalili,, cikin Ci Da Zuci Ta Ce Saidai Wani Lokaci,ni Wallahi Yanzu Banda Sukuni, ran Yushau Ya Baci Sosai,amma Dole Yashanye Yana Nazarin Ruma Saikawai Ya Kaddara Aljanarta Ce Ta Bijiro Take Masa Rashin Kunya A Fahimtar Dayaima Matar Maikudi Amininsa Kenan Amma Tuniya Kwana Da Sanin Ruma Ba Halinta Ba,amma Dai Makakin Kishin Saurayin Ruma Ta Hawo Motar Sa Ya Gallabi Zuciyar Sa Ya Ce Wanne Shegen Ne kika Hawo Motar Sa Ya Badamin Kura? Ta Dauki Lokaci Bata Amsa Ba Kowa Yai Tsit Inka Cire Hafsa Wanda Dukkan Alamunta Kenuna Ita Idan An Bar Ta Zata Iya Bada Amsar, Kamar Aiken Amsar Daga Mahaukacin Masoyi Sai Ga Sakon Tex Dinsa Yafado Wayar Zuciyarta Tadinga Azalzalawa Ta Karanta Kozata Ga Abinda Zai Bata Tabbacin Kasantuwar Sa Jinsin Aljanu,INA MAIYIMIKI RANTSUWA DA ALLAH NI NAFI KOWA CANCANTAR ZAMOWA JAGORANKI,BA A SO KAWAI BA HAR DA BARAZANAR KAMUWA DA CIWAN ZUCIYA IDAN AN SOKEKI KO A TUKUICINE KAWAI BATARE DA SO BA,KI TAIMAKA AKARE NAWA MUTUNCIN KAR KI BARI A AIBATA MIKI NI. NAKI MAHAUKACIN MASOYI BA SHEGE BANE DAN HALAK NE! Tasami Kanta Da Kallon Tsakiyar Idansa Cikin Kuka Ta Ambata,a Maimakon Tasanar Dashi Cewa Aljani Ya Dauko Ta Bayan Ta Ga Tabbacin Aljanancinsa A Sakonsa,amma Aljanin Baiyi Tasirin Komai A Zuciyarta Da Fargabarta Ba,illa Zuciyarta Data Yi Mugun Raunin An Ce Masa Shege Bata Hana Ba,wani Mugun Kishi Ya Turnuke Yushau Yanata Kallanta Kallan Dake Son Dawo Da Ita Hayyacinta Tagane Cewa Ta,addanci Fatakewa Zuciyar Sa A Kokarinta Nafifita Wani A Kansa,amma Maimakon Haka Sai Ruma Takara Wani Taddancin Cikin Kuka Ta Maimaita Kalma Daya WALLAHI BA SHEGE BANE, yushau Dayaji Ashar Naneman Kwace Masa Saiya Fice Daga Falon ,falon Yai Tsit Illah Sheshekar Kukar Ruma Sai Can Hassana Tafasa Shirun Cikin Yanayi Na Zolaya Da Nuna Tausayi, ABIN TAUSAYI WALLAHI,YAYA YUSHAU YA FARKA DAHDAI LOKACIN YAKUSA MAKARA YASAMI WANI MAI KWANJI YAYI FASHIN ZUCIYAR, Hakan Yasa Kowa A Falon Yah Dariya Ruma Kuma Ta Tsagaita Da Kuka Takoma Hidimar Goge Hawaye,dan Allah Wai Yaya Akaine? Kin Barmu Cikin Duhu.Da Gaske Aljanine Yakawoki Kuma Shi Kika Zaba Kikabar Yaya Yushau? Maimuna Ta Cehaka ,hafsat Ta Zabga Mata Harara,a Kayan Miya Meyeshi Yaya Yushau Da Baza A Barshi Azabi Waniba? Zuciyar Ruma Kam Arude Take, Tamike Ta Isa Ga Usaina Ta Amsa Jaririn Tana Amsa Tambayar Maimuna A SURA KYAWAWAN DABIU DA SHIRYA KALAMAI MUTUM NE BA ALJANBA,AMMA A WASU AYYUKA YANAKAMA DANA ALJAN,NASHIGA WANI HALI,WANDA YASANYA NIKAINA NAKE MAMAKIN ZUCIYATADA IDAN BANYI KARYA BA ZAN FADI TA FADA TARKON SON ABINDA BATASANI BA,KO ALJANINE WALLAHI NAFADA TARKON SONSA,CIKIN TSANANIN RAUNI TAKARASA MAGANAR Duk Suka Tsagaita Da Alama Bada Wasa take Ba Hafsa Ta Ce Waiwanene? Mahaukacin Masoyi,lahaula Wala Kuwata Illah Billah,kinganshi Da Idanki? Shiya Daukoni Yakawoni Nan, Bayan Ta Zayyanamasu Yadda Haduwar Su Takaya Tare Kuma Da Cewa Tariski Sakonsa Akancewa Na Yana Dab Da Bayyana Mata Kansa,kun Barmu A Duhu Ku Warware mana? Inji Asiya, hafsat Takalli Ruma Kallan Neman Izini,ruma Tamike Tadauki Jariri Tana Ce Kisanar Dasu, Ta Wuce Kaitsaye Dakin Barcin Atika Kozata Samu Damar Wassafo Surar Mahaukacin Masoyi, Amma Tana Sauraran Hafsa Datake Basu Labarin Mahaukacin Masoyi Da Nuna Musu Tex Din Sa A Wayarta Bayan ta gama Kowa Ya Jinjina,wasu Suka Shiga Rudu,amma Abu Daya Ya Karfafamata Guiwa Maganganun Da Hafsa Take Kuma Cikin Yakini Da Gasgata Kai,na Bawa Kaina Sati Biyu Da Izinin Allah Sainabinciko Mutuminnan Haka,kawai Bazai Zautamin Yaruwa Ba Wallahi,ta Wace Hanyar? Atika Ta Tambaya Kin Manta Mijina Dan sandan Cikine? Lambobin Wayar Sa Nadauka Sun Isa Nagano Indayake, ********** Bayan Wuni Cikin Sake Sake Yushau Ya Yanke Shawarar Daukan Kwaryar Ban Hakuri Zuwa Ga Alhajinsa Bisa Abinda Yafaru A Baya Da Kokon Barar A Mayar Masa Da Ruma Yagyara Aurensa,yagama Shakulacin Bangaransa Wajen Hajiya,haryakai Ga Isa Ga Alhji Wanda Yasanyashi A Kwandan Shara,yajuyo Ya Fuskantanceshi,NASO NA TUNA WANNAN FUSKARKUWA? YALLABAI DAGA INA? Duk Dakuwa Wutar Dake Zuciyar Sa Tana Raya masa Kuka Yakamata Yayi Danhakan Kadai Ya Isa Nuna masa Saiya Wahala Malam Banfa Ganeka Ba Daga Ina?Kawai Sai Yushau Yasami Kansa Da Fashewa Da Dariya Yana Kallon Alhji Wanda Ko Kadan Dariyar Batasa Shi Ya Sassauta Damarar Dayai Wa Fuskarsa Ba,saima Yakawar Dakai Yaitsaki,hakan Ne Yasanya Yushau Yadan Shiga Taitayinsa,yadinga Kokawar Gyara Zama Yafara Bada Hakuri Na Tsawan Minti Gowa Sha Biyar,alhji Na Saurarensa Har Saida Takaici Ya Sanya Shi Tare Yushau Cikin Sarkewar Murya Dan Allah Malam Bari Batawa Kanka Lokaci,wai Hakuri Kadaine Kawai Yakamata A Rayuwa? Bashi Kadai Nara Sa Ba,abubuwa Da Yawa Wadanda Na Sasa A Bangarenka Wadanda Sukafi Su Muhimmanci Suna Fi Bukata,,,cikin Zumudi Yushau Yatare Shi Saboda Yana Zaton Alhji Zaice Ya Mayarda Auren Ruma Amma Sabanin Haka Kaitsaye Cikin Muryar Tura Haushi Alhji Ya Amsa,biya Na Kudaden Dasuke Wuyanka Mana,wadanda Nadinga Hidimar Iyalinka Dasu Tun Bayanda Ka Saki Uwar Su ,saima Ka Daukemin Kafa Da Aljihu Ka Barni Da Nauyi Danka Tabbatar Lallai Bazan Iya Kaisu Bola Na Zubarba! Ka Yi Ta Banzar Yushau Domin Komai Na Nan Arubuce Na Na Adana Ko Mutuwa Nai Na Sanar Da Magada Sunemi Hakkinsu A Wajenka,,, cike Da Rauni Yushau Yatare Shi,,kayi Hakuri Zan Biya Alhji,a Bani Adadi Sainafara Biya Daga Wannan Watan, daka Kyauta Wa Kanka,cikin Ko Inkula Alhji Yafada,falon Yai Tsit Inbanda Bugawar Zuciyar Yushau Wadda Ke Tattara Dukan Kafofin Da Zata Sauke Karfin Halin Data Wanko,akarshe Dai Da Ya Hattama Sai Bakinsa Ya Karbi Karfin Halin Yafurta Cikin Sarkewar Harshe,idan Rabuwa Da Ruma Ne Ya Nisanta Ni Daku? Kuma Har Shine Yaisa Abin Sanyawa Ka Manta Kamannina Alhji Ina Neman Alfarma Kadawo Dani Kusa Daku,,ku Mayar Da Diyancina Dan Haka Inaso Ka Sanya Albarkarka Ka Bani Dama Na Mayar Da Aurena Da Ruma... tunkafin Ya Dire Akwatin Tara Fushin Alhji Ta Cika,ya Yunkuro Da Fushi Yatareshi,,,wallahi Tallahi Danasan Maganar Dazakai Minkenan Na Rantse Da Allah Da Samsam Ban Saurareka Ka Sarayar Min Da Lokaci Ba,saboda Haka Idan Ba Son In Sassaba Maka Kamannin Ka Ba,to Ka Digawa Wannan Maganar Aya, yushau Yai Tsita Cike Da Fargabar Ta Inda Zai Billowa Alhjin.. Dan Girman Allah Alhji Ka Bani Dama Na Fahimtar Dakai Akasin Da Aka Samu Cike Da Takaici Alhji Yake Kallon Yushau Cikin Yanayi Nata Gina-ba-ta-shiga Ba Ya Cemasa Ahau!Inajinka Yushau Ya Gyara Zama Jiki Na Bari Ina Son Ruma Alhji Duk Wata Mace a Duniya Bayanta Zata Bi A Zuciyata,ban Fahimci Hakan Ba Sai Bayan Rabuwarmu Amma Fushin Da Kuke Ciki Ya Dinga Tsoratani Yana Hanani Kawo Kaina..... . Dan Anti. . . Sannan Sai Gurguwar Fahimtar Dana Yiwa Ciwonta Wanda Shine Kashi Casa'in Na Rashin Jituwarmu,ayanzu Kuwa na Nemo Iliminsa Na Tabbatar Matsala A Dalilinsa Takare Kuma Idan An Bani Dama Na Ci Alwashin Sai Ruma Ta Rabu Da Ciwon Nan Haihata Haihata Cikin Izinin Allah, oh Kana Da Kudin Daza a Canza ,mata Bargo Ko? Alhji Yakatse Shi A Shashance Cike Da Ladabi Yushau Ya Amsa A Iyakar Gaskiyarsa,a Binciken Danayi Nagano Shafar Jinnu Ce Naci Alwashin Daganan Har Saudiya Zandauki Nauyinsa Ayimata Rukiya, alhji Yafara Yiwa Yushau Duban Mahaukaci,da Kyar Ya Hadiye Wani Yawu Daya Cikamasa Makogwaro,yanunawa Yushau Kofa,tashi Ka Barmin Gida,,,,,,,,!,, Nima Ina Da Malaminda Zan Nemo Yaimaka Rukiyar Dankafi Ta Bukatar Rukiya,,, yushau Yai Funfurus Yakitashi Sai Shi Alhjin Yamike To Ni Barina Barmaka Dakin Kafin Yushau Yai Magana Tuni Ya Fice Danshima Ya Mike Jiki A Sanyaye Yana Kokarin Ficewa Zuciyar Sa Na Karkatar Dashi Cewa Kawai Yadage Ya Nemo Kan Ruma Dakanta Inta Kawo Wa Alhji Maganar Komen Ai Bazai kiba, *********** Kwanaki Uku Da Suka Biyo Baya Mahaukacin Masoyi Ya Bace A Rayuwar Ruma Ta Zahiri,wato Ba Bushi A Sakonninsa Kuma Ba Bu Shi A Zahiri Kamar Yadda Ya Billo A Matsayin Direban,dayakai Ta Gidan Atika Amma A Badininta Yananan Yana Ninkaya,wuni Da Kwana Yana Shige Da Fice A Zuciyarta Mai Wassafa Kamaninsa Tanakara Kawata Wa kanta Shi,abuna Biyu Kuma Tana Canke,canken Mutum Ne Shiko Aljan Sai Abu Na Uku Tana Tunanin Koma Waneneshi Wato Mutum Din Dai Ko Aljan Dinshine Wannan Nazifi Muhammad Daga Milkyway,sai Abu Na Karshe Shine,tanason Ganinsa A Fili Rayuwarta Ba Irin Yanzu Daya Ke Kan Katangarta Ba,kowace Irin Rawa Zaitaka A Fili Saita Cika Kanta Tsakar Dare Ana Gobe Sunan Jaririn Atika,bacci Ya Kaurace Mata Fau-fau Bayan ta gama Laluben Mahaukacin Masoyi A Dukkan Kafar Daya Taba Lalubota Bata riskeshi Ba,kama Daga Kiran Waya Akwatin Tura Sako,social Network Da Sauransu Amma Shiru Ba Bu Alamar Shi,da Bacci Ya Kaura Cewa Idanta Sai Gata A Zaune Tanakaranta Wasikar Jaki,kamar Daga Sama Wayarta Tayi Tsuwwa Cikin Razana Da Barin Jiki Ta Wawurota Amma Sai Taga Hafsat Damamaki Ta Daga Da Sauri Ko Sallama Batai Ba Hafsat Lfya? Cikin Doki Ta Ce Lfya Kalau Nakasa Jiran Wayewar Gari Da Tsegumina Meyafaru? Ruma Tatare Ta Cikin Doki Hafsat Ta Ce Sani Munafikine Yasan Abubuwa Dayawa Dangane Da Mutuminnan, Wanne Mutumin? Hafsat Ta Ce Harkin Manta? Mahaukacin Masoyi Mana Sai Ga Ruma A Tsaye Cikin Tsananin Rudani Ta Ambata Da Gaske? Yanzu Dama Canda Sa Hannun Sani Abinda Mutumin Nan Kemin? Hafsa Tatare Ta Cikin Sauri Ko Daya Satin daya Gabata Shima Yasani Ruma Ta Sauke Kakkarfar Ajhyar Zuciya Innalillahi Wa Inna Ilai Hirajiun To Mutum Ne Ko Aljani?Kuma Meye Takamar Sa? Hafsat Na Shirin Amsamata Sani Ya Karbe Wayar Ya Ce Haba Shekara Uku Ba Bu Aure Wasane? Kin Manta Cewa Katon A Addancin Ne Ka Bugowa Amare Waya Tsakar Dare Irin Haka Ko Baki Duba Agogo bane? Su Waye Amaren Waiku? Tafada Cikin Zolaya Tare Da Jin Ciwom Yayankemata Samun Haske Akan Majanuninta Sani Ya Ce Mu Mana! Saida Safe Kafin Ka Ajiye Saika Amsamin Tambayar Danaimata Sarkin Kulle Kullue Kanaganin Ana Neman Kasheni Da Raina Amma Ashe Kaine Mai Bada Gudumawa,saiki Hau Duro Ki Fada Ya Ce Cikin Zolaya Yakashe Wayar Gabadaya,tafada Gado Tana Ambatan Allah Wato Mahaukacin Masoyh Mutum Ne Ba Aljani Kamar Yadda Tayi Tsammani Ba Indai Sani Yasanshi To Ta Tabbata A Duniyar Su Ta Mutane Yake To Amma Tayaya Yakemata Sidda Baru? Tajima Tanakokarin Amsa Tambayar Amma Takasa Saita Hakura Ta Kamo Tashar Wadda Ta Tarar Da Shiryayyun Wasu Tambayoyin Ba Bu Amsa Wato Mene Ne ManuFar Sa Akanta? Yana Da Masaniyar Cewa Ita Sikila Ce? Kamar Amsa Ga Tambayoyinta Sai Ga Wani Kira Daga Hafsa Da Sauri Ta Amsa Ta Ce Yi Saurin Amsamin Kafin Kafin Sani Yadawo,cike Da Zolaya Hafsa Ta Ce Aiyana Kusa Kwalar Rigarsa Naci Ya Sallama Na fada miki Wani Abu Daya Da Zai Kwantar Miki Da Hankali Inajinki, hafsa Tai Kasakasa Da Murya Ta Ce Mahaukacin Masoyi Wato Nazifi Muhammad Mutum Ne Kuma Da Gaske Mahaukacikine A So,yayi Nisa Fiye Da Yadda Kike Tsammani,kuma A Nawa Tsammanin Ba A Ta Ba Sonki Kamarki Haka Ba Rumaisa"u Karyakike Hafsa,ruma Tafada A Fusace Cikin Sauri Maitafe Da Kuka Mai Tuna Baya Ni Ban Taba Wani Kamar Auwal Ba,kuma Ban Yarda Za A Sami Wanda Zaiso Ni Fiye Da Shi Ba Tanason Zarcewa Da Kuka Hafsa Ta Tareta Cikin Rudani Rage Kukan Karki Janyo Hankalin Iyayenki Gobe na Sha Luguden Fada,duk Da Tuntuni Maganar Taje Kunnen Alhji,rumaisa Tanemi Dauke Numfashi Cikin Rudani Amma Kafin Ta Tanka Hafsata Ta Rigata Indai Za A Sami Mai Son Naki Zuciyarki Ta Yarda Da Haka,ba Wai Angama Samun Mai Sonkine Kwata Kwata Ba,kidan Bude Wa Wannan Dan Tahalikin Zuciyarki Kadan Yasami Guri Ina Mai Tabbatarmiki Lokaci Kadan Zai Gawurta Harki Gane Nisan Fifikonsa Da Au... Ke Tafi Can Ruma Tafada A Fusace Ta Kashe Wayar Cikin Zafin Zuciya,kwana Tai Safa Da Marwa Da Rashin Barci,saboda Damuwa Da Rikita Yajanyo Mata Wani Matsananchn Ciwon Kafa Da Misalin Karfe Takwas Na Safiyar Ranar Inda Ciwon Kafa Da Misalin Karfe Takwas Na Safiyar Ranar Inda Ciwan Yadinga Shan Sharafinsa Har Fiye Da Awa Daya Saida Kowa A Gidan Hankalinsa Yatashi Ita Ruma Mai Ciwon Kuka,mairo Mai Tausayi Kuka Hajiya Da Alhji Da Mubarak Ba Bu Wanda Hankalinsa Ke Kwance Har Saida Ciwan Ya Lafa Alhji Yatafi Da Ita Asibiti,daga Asibitin Ne Kuma Taki Yadda Amayarda Ita Gida Saidai Mubarak Yakaita Gidan Suna Kawah Duk Da Kuwa Bata gama Wartsakewa Ba Ana Dai Abinda Yafi Ciwo Ajikinta Shine Zuciyarta Dake neman Gazawa Da Lissafin Mahaukacin Masoyi,hayaniya Bata Barta Ba Dole Atika Ta Waremata Falon Mijinta Ta Kwanta Jefi Jefi Wasu Kanshi Go Su Dubata Balaraba Yayarta Ta Shigo Ta Cemata Wai Wanene Wancen Da Sani Keta Faman Nunawa Mutane A Matsayin Mijinki? Abin 'yar Hakane Ruma Kinyi Miji Ko Albishir Ba Bu? Cikin Rudani Ruma Tatashi Zaune Ban Sanshi Ba nima,balaraba Takalleta Sororo Har Nawasu Lokuta Ta Ce Dagaske? Ruma Takoma A Kasalce Ta Kwanta Balaraba Tamike Cikin Sanyin Jiki Ban So Haka Ba Gaskiya Naso Ace Kinsan Shi,kuma Kece Kika Bashi Damar Yazama Mijinkh Saboda Nutsuwar Sa Da Kalamar Sa Dakuma Abinda Bani Kadai Na Hango Ba Wato Tarin Kaunarki Atare Da Shi,duk Kwakwar Balaraba Takasa Fahimta Abinda Ruma Ke Rayawa Aranta Balaraba Tafara Tfya Tana Cewa Nadanyi Hira Dashi Har Na Fahimce Shi Dan Hadejane,kuma Mazaunin Abuja,yaushe Kakayi Hirar Dashi? Cikin Hanzari Ruma Tafada Tana Dagowa Balaraba Hannu Alamar Dakatar Da Ita Barin Falon,saboda Kasalar Gangar Jikinta Yanzunnan Balaraba Ta Amsa ,au Ance Ma Nasanarmiki Zai Shigo Ya Dubaki,cikin Kuluwa Ruma Ta Amsa Ba Bu Laifi Ta Koma Ta Kwanta,balaraba Ta Fice Daga Falon Batare Da Ta Canka Dalilin Kuluwar Ruma Ba Duk Da Tana Tunanin Ce Wa Marigayi Auwal Ta Tuna Ruma Takasa Cankar Inda Zuciyarta Fada Dokin Gani,fargaba Kojin Kallan Mahaukacin Masoyi? Yau Kuma Yanzu? A Haka Tajiyo Takun Sawaye Tare Da Muryar Sani Yana Karadin Hirar Sa Ta Dora Idanta Kir Akan Kofa Cike Da Dokin Ganin Inta Ga Nazifi Muhammad Kar To Taga Kafar Sa Da Kofato Dan Kuwa Idanta Na Kan Inda Kafafunsa Zasu Duro,sani Ne Yafara Shigowa Cikin Yanayinsa Na Faraa Da Kuzari Kamar Koda Yaushe Nazifi Biye Da Shi Cikin Matsananciyar Kasala Mai Alamun Tasowa Daga Zuciya,ba Kamar Ko Yaushe A Ganin Dataimasa Cikin Kananun Kaya Ba,yau shiGar Manyar Kaya Yayi Na Shadda Ruwan Toka Yar Ciki Da Babbar Riga Bata Damu Da Zolayar Sani Ba Ahankali Ta Dauke Idonta Daga Kallansa Zuwa Wani Wajen ... . Dan Aunty Al-Hada Hada Hausa Book stories GORAN DUMA (P 58) . . Sani Yadubi Ruma Wannan Wace Irin Tarba Ce? Karkuma Ki Kalawa Ciwo Dan Fuskarki Tanuna Da Sauki,takalli Sani Garau Ta Shiga Gyara Mayafi Wanda Ta Lullube Kafafuwanta Dashi Tun Lokacin Dataji Takun Shigowar Su Dahaka Ta Bar Tambayar Sani Tabi Ruwa,hakan Yasa Sani Da Nazif Sukai Murmushi Nazifi Ya Ce Ankuma Ce Tun Tuni Kina Dokin Ganina Ni Ma Ban Zaci Wannan Tarbar Zansamu Daga Gareki Ba Sai Yanzu Ta Fahimci Kwakwalwarta Ta Tsaya, sani yatafi yabar Ruma da nazifi alamu yanuna a tsorace take tundaga fitar sani daga falon nazifi ya mike cikin kwarin guiwa a tsorace cikin zafin nama sai gata a zaune tana kallon kofar cikin Gyara wuyar Riga yakaraso tsakiyar falon ya zauna kan teburin dake girke a tsakiyar dakin Wanda ya basu Damar kallon juna ruma cikin tsananin so da farin cikin ganin masoyin Ruma tafara kauda kai cikin cin magani yace najima INA kaucewa haduwa dake idan kina cikin rudu ALLAH bai nufa ba amma dai nayi nasara ba wani na ya rudaki ba nida kaina na rudaki yatsayar da maganar saboda yaga bakinta na motsi alamar zatai magana amma yana rufe baki sai yaga ta hadiye yaya jiki? Nanma kallonsa kawai tayi ta kauda kai yace nasan abinda yajanyo fushinnan lokacin da kika so ganina naki ki ganni ba fushi ya dace kiyi ba Ruma kamata yai kinemi ba'asi cikin karkarwar murya tace wa yace maka inason ganinka? kaitsaye ya amsa cikin daga gira kintashi daga kano takanas zuwa abuja din kiganni cikin tilastawa kai wani fushin face duk yafarune cikin kuskure Yanzu najanye saboda haka kana iya tafiyarka idan kazone domin na ganka takaj da raunanniyar murya yace badon kiganni nazoba nine nazo don na ganki domin nikadai kesonki nakuma cika son kai Dan banbaki damar kisoni ba a tsammanina nawa son ya wadatar tace masa wannan bayanin naka sunyi hanzari domin kai yakamata nafara sani ba kalaman soyayyarka ba amma idan kagama boye boyen kenan nagama yafada da sauri shiyasa nacemiki nafiye son kai na boye mini kaina yayinda na zurfafa a sonki har nakai bigiren da raina kejin in an raba shi da sonki bazai iya cigaba da nunfasawa ba nantake kwalla tacika mata ido domin maganarsa tatuno mata da auwal babu alamun shakku ta amsa masa rashin masoyi baya kisa dayanayi dabaka ganni a Raye ba har ka soni. nazifi ya dauke wuta dad fuskarsa da gangar jikinsa sun nuna damuwa kishi yajima cikin kallon shimfidar falon kamar yadda taciga ba da kallon talabijin zuciyarta a auwal batare da nadamar maganar dataiba said a ta hangi inuwar nazifi a tsaye tajuyo ta dubeshi lokacin yakusa kofar fita falon tagama yanke kaunar sai fice baice komaiba amma sai ya jiyo a sanyaye yace nasan ba zafafa cimma burina ne yasanya nijin cewa ALLAH ya karbi ran Auwal ya barmin me ba don nafishi cancantane.na fishi sonki na kuma fishi cancantar zama mijinki RUMAISA'U sikila..,. watakila sai lokaci yayi zaki fahimci hakan tai shuru tana kallonsa da alama kamar laluben ta inda yafi Auwal cancanta take zanwuce masaukina yanzu badon zantakura mikaba danazo gidan yau da dare gobe don inanan kano har safiyar jibi itadai kam hawaye take face masa jimana tareda karfin halin mikewa tsaye yajuyo ya kalleta tadanyi kamar xatafadi a kokarinta na gyara tsayuwa da sauri yadaga mata hannu , a, ah koma ki zauna ta koma ta xauna tace maasa kafin goben inasan sanin kai waye I na tsammanin a duniya babu abinda ya shige min gaba kamar son sanin amsar wannan tambayar akwai wani suna dazan sake amsawa ne banda MAHAUKACIN MASOYI? wannan sanin yakamata ki rike ba na tsammanin zakisami Wanda yafishi da gaske ne ni MAHAUKACIN sonkine ba wannan nake tambayaba ai tundazu akan haka muke magana tambayata anan itace ta wace hanyar kake shiga zuciyata? tawace idon kake kaina hatta a lokutan da nakasance nesa da idon kowa yakada kai yana dariya au hakanefa duk naji zarge zargen dakikemin wajen sani zargi ne wato ba gaskiya bane? ta tambaya cike da mamaki kwarai da gaske ya amsamata shikenan saika tabbatarmin da gaskiyar yanzu. ya CE a irin wannan lokaci n dakika cakuda min zuciyata da takaici ? INA girmama Auwal don darajar zuciyarki tasoshi ni kuma masoyin kine ke da komanki amma girmamawar taki shafe kishina ya fice ya var falon tunbayan fitar MAHAUKACIN MASOYI Gidan sunan yaimata zafi tatashi tashiga cikin jamaa inda ake ta kayakaya murna da daukan hotuna kozata manta amma hotunan MAHAUKACIN MASOYI a cikin zuciyarta musamman daidai lokacin da yake cewa NASAN BA ZAFAFA CIMMA BURINE YA SANYA NAJI CEWA ALLAH YA KARBI RAN Auwal YABAR MINKE BA DON NAFISHI CANCANTANE NAFISHI sonki KUMA NAFISHI CANCANTAR ZAMOWA MIJINKI RUMAISAU sickle INA GIRMAMA Auwal DON DARAJAR ZUCIYARKI TASOSHI NI KUMA MASOYINKINE KE DA KOMANKI AMMA GIRMAMAWARKI TAKI SHAFE KISHINA wadannan zantukannasa sunki bacewa daga zuciyarta da alama duminsu ne yake ta faman kyankya sar son ubangidansu wato MAHAUKACIN MASOYI a kirjinta ta yarda ya iya so tunda ya iya sonta ita da son dataiwa waninsa AUWAL kuma kishinsa ya na nan daram amma baya runtse masa I do ya ya mayar masa da sonta kiyayya ,tabbas ko yayane zai iya zama waziri a fadar so da kaunarta yayinda auwal yake sarkin sarakuna , ##**************** Dan rumaisau yushau ya isa gidan sunan da gamma da sunan wai yaje daukar sumoli wadda ta mayar da kanta amarar biki da karfi da yaji yayi katari an kwakolo rumaisau da kyar zuwa wajen daukar hotuna a harabar gidan sai gashi dayin abinda babu shi a cikin tsarinsa wato shiga sabgar bikin mata ya rungume hannu ya tsaya kusa da kanin mijin atika yana satar karewa Ruma kallo Wanda kaf Cikim matan dasukazo sunan sinfita daukan ado amma a haka it'a kadai kallon ta ke buga masa zuciya musamman daya hangota da sumoli fara tas kuma ko aljana ta shafa mata lfya wajen caba kwalliya NASA wasane baidau kallon Ruma kadai buga masa zuciya ba komai daya shafeta ma buga masa zucuyar yake ba said a kunnensa ya kwaso masa muryar Hassana NA cewa rumaisau amma dai baki da kirki tun safe kin kulle a daki har mijin naki yazo ya tafi ai kamata yai Ku kafa tarihin kwasar hotuna a ranarnan,,,, acikin rudu YUSHAU yake amma kunnuwansa sunjiyo amsar ruma tace fadar miji a baki baya muku wuya babu Wanda ya danka min sadaki amma Ku daga ganin sarkin fawa sai miya tai zaki hassana tabar gurin tana amsamata nasan yayi nasara ya gama din mai irin fuskarsa da zuciyarsa sun cika saurin nasara, fiye da awa daga YUSHAU na jinyar zuciyarsa da Neman mafita har SUMOLI tagama sallamarta tasameshi a mota babu magana kawai yatashi motar ya fice sumoli TAGaji da shan kamshi Dan haka ita ta tankashi tana taunar cingam ranka ya Dade lfya kuwa ? lfya mekika gani? saida ta jero kwa say uku cikin gwaninta tace naganka a firgice ne sannan yinin yau kadai naga kakara ramewa,badon kaidin kai bane aidanakaika asibiti ko ruwa adan samu daura maka Leda guda inka yarda nakaika gurin kawata FAUZIYA D SULEMAN takara mka nasan kyauta zataimaka in kudin kakeji yushau Yasan Iskancin tane Ya Motsa Amma Tunda Bai Shirya Masa Ba Sai Ya So Basar Da Maganar Da Cewa Inatare Da Hayaniyarki Aina Bar Kiba Sumayya Ke Ai Gashi Nan Kina Shirga Kiba, Wallahh Tallahi Ba Bu Ruwana Tsabar Ma makon kane Yake Ramar Da Kai Ni Din Ma Kibar Godiyar Allah Ce Ba Dan Haka Ba Nasan Sai An Kirga Kashi A Kirjina Inya Ci Gaba Da Takaici Yasan Sai Ya Haifar Masa Da Ciwan Zuciya Sumoli Bata Damu Ba Dan Haka Yaja Bakinsa Yai Shuru Daganan Ta Ci Gaba Da Zuba Har Ta Cemasa Yau Kusan Sati Biyu Kenan Bata Ga Aladarta Kuma Tana Jin Kasala Da Tashe Tashen Zuciya Kila Cikine Tare Da Cin Alwashi Na Rantse Da Allah Nima Ina Haihu Saina Yi Wadannan Bidioin Andaina Barina A Baya Tayi Jiran Amsa Harta Kule Ta Cemasa Haba Malam Kokana Da Yakinin Cikinannan In Natashi Kwado Zan Haifa Aikataya Ni Murna Ko Na Ganin Idoce Maimakon Haka Sai Cin Magani Kake Yayi Murmushi Ya Ce Kece Da Wauta Wallah Tun Kafinki Tabbatar Da Cikin Harkin Fara Lissafin,, tatareshi Tana Dariya To Meza A Fasa? Ya Ce To Allah Ya Inganta Amma Dai Kidaure Ki Haifo Nimiji Mai Kama dani.... . Dan Aunty GORAN DUMA (P. 59) . . summaya Tazaci Yabo ne Cikin Tuntsira Dariya Ta Ce,insha Allah Namiji Zan Haifo Lafiyayye Ammame Kama Dani Don Nafika Kyau Ya Kada Kai Kawah Da Alama Hankalin Nacan Ga Ruma Sumoli Ta Ce To Waimeyasa Ka kE son Namiji?Bawai Namijin Nafiso Ba A A Kece Kawai Har Abada Banaso Ki Haifo Mace Dan Me? Cikin Doki Da Tashin Hankali Ya Ce Dan Banason Ki Haifi Mace Ta Gado Halinki Na Zamo Kullum Cikin Kiran Mubarak Ya Daura Mata Aure In Kuma Ba A Yi Sa'ar Maikai Zuciya Nesa Dazai Saketa Cikin Sauki Ba Saiya Nadamata Na Jaki Kafin Ya Sakota Kai Dan Giya Ne Ma Nasan Saita Janyo Abinda Kullum Zai Sa Ya Yanke Tada Muka,... sumayya Tai Mugun Zuwa Wuya Danhaka Takasa Maida Martani Har Saida Tagansu A Tsakiyar Gidansu To Allah Yasa Namijin Kar Ya Biyo Halinka Wallahi Har Nafara Tausayama Matan Dazasu Aure Shi A Waje Acan Amma Dasun Shigo Ko Gizago Da Mammako Ya Ishesu Oho Dai Yafada Cikin Dariya Sannan Yajuya Yafice Daga Gidan A Guje Yana Dariya Yanufi Masallaci.... Yushau Kaitsaye Bayan Dawowar Sa Daga Sallar Ishai Kaitsaye Yakoma Gidan Suna,ba Bu Yadda Atika Batai Da Ruma Ta Zauna Ta Kwana Ba Amma Taki Yarda Haba Aunty Atika Menene Bambamcina Da Hafsat Ita Bakice Ta Zauna Ta Kwana Ba? Cikin Raha Ta Cema Atika Kowa Na Dariya Atika Ta Kada Kai Babu Bambamci Sadakine Kawai Ba Miko Waliyyai Sun Daura Auren Ba,wato Yadda Take Da Kifinta A Gora Haka Kike Danaki, oho Kuma!Ruma Tafada Cikin Dariya Ana Haka Sai Ga Mubarak Ya Shigo Yana Wata Dariya Wadda Tasha Bambam Da tasu,ruma Ta Nuna Masa Kofa Karka Zauna Muje Ka Kaini Gida Naga Aunty Atika Ta Dage Sai Ta Mayar Dani Arha,,, mubarak Yatareta Yana Dariya Ya Ce Ai Bata Kai Yaya Yushau Ba,shi Da Duk Ma Yakeson Siyenki Baki Ga Fa,kamar Zai Rushemin Da Kuka Yake Rokona Na Rokeki Da Girman Allah Kifito Ki Saurareshi,ruma Na Takaici Su Asiya Na Shewa Asiya Ta Ce GORAN Ruma Fa Manyan Kamu Ya Yo Guda Biyu Dazu Ya Kamo TIGER SHARK YANZU KUMA YA KAMO KAWARA Dakin Yafara Gaurayewa Da Dariya Hafsat Ta Ci Magani Dazu Harda Kwanciya Akasa Amma Dai Aunty Asiya Kin Iya Yanka Lasa Nawa Tiger Shark Zai Wa Kawara?Yaya Yushau Ne Ya Zama Haka A Wajenki? Suna Ta Dariya Kamar Abin Arziki Maimuna Tarike Hannu Ruma Kamar Abin Kirki Tanajan Ta Zuwa Kofar Daki Allah Sarki Wallahi Kawaran Can Ya Fara Bani Tausayi Jeki Ganshi Ko Na 'yan Mintunane, Itakanta Ruma Sai Suka Bata Dariya Ta Yafito Mubarak Tana Cewa Zo Mu Wuce Daga Nan Mubarak Mubarak Yai Dariya Ya Ce A,a Ki Daije Anti Kawararnan Mu Karfasa Ta Ke Zame Mana Ba Muya Ta Bude Kayar Baya,ruma Ta Fice Ta Bar Su Cikin Rashin Kwarin Guiwa Dajin Takaicin Shi Ga Hanci Da Kudundune Da Yushau Kemata Tasameshi Tsaye Jikin Motar Sa Mubarak Yasanar Dani Kana Nemana Baiji Dadin Yadda Ta Daure Fuska Ba Dan Haka Yajima Baice Komai Ba Yanumfasa Ya Ce Yaya Gajiyar Taro? Alhmdlah Ta Amsa Masa Cikin Kokarin Tilastawa Kai Dazun Har Natafi Bamu Gaisa Ba Duk Da Cewa Takanas Domin Na Ganki Nazo,ta Dauki Maganar Nasa Rainin Hankali Amma Cikakken Nata Hankalin Ya Shanye Nuna Bacin Rai Saita Ce Hakane Tokasan Komai Sai Allah Tabbas Yafada Yana Kokarin Dorawa Amma Saita Rigasa Zarcewa Yanzu Kuma Dare Yayi Sai Wani Jikon Kenan? Muzamu Wuce Gida Kedawa? Cikin Rashin Jindadi Nida Mubarak ne,in Ba Bu Damuwa Me Zai Hanaki Zona Kaiki Gidan? Akwai Wasu Muhimman Batutuwa Danakeso Mu Tattauna Dake A Hanya Tadanjima Alamar Ranta Baisoba,kome Kika Gani? Kaje Kawai Ma Hadu Wani Jikon Har Waya Nayi Wa Mubarak Yazo Daukana Bazaiji Dadi Ba Idan Na Bar Shi Yakoma Shi Kadai Indan Shine Barina Nemi Afuwa Kafinta Tare Shi Har Yafara Magana Da Mubarak A Waya Afuwa Mubarak Zan Wuce Da Ruma Zuwa Gida Kataho Kai Kadai Ya Budemata Kofa Ya Zagaya Bata Da Zabi Dole Ta Shi Ga Motar Zuciyarta A Kuntace Yushau Yaita Kalatarta Da Hira Dazata Budemasa Damar Gabatarmata Da Kudurinsa A Saukake,amma Ruma Tai Fuska Kalmominta Tamkar Sai Ya Siya Kamar Yadda Dariya Da Murmushinta Sukenuna Karara Sunfi Karfinsa Saida Yaga Haza Sannan Yai Wa Shirin Nasa Kutse Ruma Ina Muka Kwana? Dame Fa? Yajima Yana Tunani Wajen Kirkirar Kalamai Masu Dadi Wanda Baima San Ya Iyasu Ba Bansan Komai Ba A Yanzu Sai Sonki RUMA KOMAI NAWA RARRAUNA NE SABODA SO KARFIN GUIWATA KADAN NE SHINE GANIN ALLAH YA JINKIRTA MIKI AURE DOMIN NA DAWO MIKI A MATSAYIN MASOYI MAI SHAFE KOWANNE IRIN AIBU NAKI, ya Tsagaita Amma Shiru Kakeji Saidai Kawaicintane Kawai Ya Boye Mugun Takaicin Da maganganunsa Suka Kunsa Mata,musamman Daya Tuno Wani Kurarin Zawarci Dayaimata A Can Baya Kafin Ya Saketa Wanda Ya Tabbatar mata In An Sake Bazata Auru Ba Sai Shi Daya Saba yimata Alfarma Yadawo Zai Sake Yimata Wani Alfarma Ta Kada Kai ta Sake Amma Ta Hadiye Komai Saidai Ta Bar Hawaye Nashan Sharafinsa A Fuskarta Dayake Fitilar Motar Bata Cika Haske Ba Kuma Wani Kaso Na Hankalinsa Nakan Tuki Bai Lurada Hawayenta Shurunta Kuma Yakara Masa Karfin Guiwa Ci Gaba Da Magana Dan Ki Tabbatar Da Cewa Da Gaske Nake Duk Surukutar Dake Tsakanina Da Alhji Kwanakin Uku Da Suka Gabata Na Nade Kunyata Najemasa Da Maganar Yayi Farin Ciki Kwarai Saidai Ya Bani Damar Na Nemi Hadin Kanki A Ganinsa Wannan Ne Horo Gareni Bisa Kurarkuren Dasu ka faru, Mu Dauko Hamida Mu Rike Abarmu Zan Sake Rantse miki Da Allah Na Shiryawa Dukkan Lalurarki Ke In Takaita Miki Ma Har Na Fara Nemar Miki Magani, tun Lokacin Daya Ambaci Zuwansa Wajen Alhji Ta Watsar Da Kallon Windon Motar Ta Koma Kansa Cikin Dauke Numfashi Bata Kuma Kara Fahimtar Maganganunsa Ba Tun Bayanda Ya Fadi Sharadin Alhji,tayi Shakkun Sharadin Wanda Ke Cike Da Danne Hakki,wanda Tana Kara Jaddada Shakkar In Zai Fito Daga Alhji,a Hankali Ta Dauke Kai Daga Kallonsa Ta Cemasa Nayi Farinciki Tunda Alhji Ya Bayarda Damar Yarda Tana Hannuna Dan Haka Ina Mai Baka Hakuri Tare Da Tunatar Dakai Ni Da Ayyukana Bamu Sauya Ba Ciki Har Da Zuciyata Mai Bijiro Da Kudirori Ta Sanya Gangar Jiki Aiwatarwa Lallai Kafin In Aureka Na Zaci Banida Zabinko Mawazan Aura Tunda Na Rasa Wanda Zuciyata Keso Amma A Yanzu Na Fahimci Aure Ba Hakkin Kaina Ni Kadai Bane,lallai Ko Na Sarayar Da So A Cikinsa Dole In Nemo Wa 'ya'yana Da Zan Haifa Lafya Da Farinciki Bangane Abinda Kike Nufiba? Tawa Rayuwar Baata Da Sauran Tanada Na Zuci Ko Na Gangar Jiki Amma Dolene Inyi Aiki Tukuru Dan 'ya'yan Dazan Haifa Su Zamo Masu Lfya Ba Irina Ba Cikin Matakin Kuwa Harda Hakura Da Aure Idan Ban Sami Mai Nau'in Jinin Dazan Haifi Masu Lfya Ba, sun Isa Harabar Gida Yajanyo Wata Leda Dama An Fadamin Kune Kuke Daurewa Aljanu Gindi Ta Hanyar Manta Kaidinsu Kuyi Tamika Wuya Ga Asibiti, Cike Da Mamaki Wato Mai Hali Duk Inda Ya Juya Baya Sauya Halinsa Ko Ta Ina Yushau Ya Bullo Saiya Nuna Shi A Baude Yake,fitsarin Rakumi Ne Ance Maganin Sikilane Karafiyan Idankin Gama Shansa Zanzo Muje Amiki Rukiya Ba Gaggawa Nake Ba Ruma Inkin So Saikin Warke Garau Zaki Koma Dakinki Koda An Daura Auren Tuni Ruma Taiwa Kwalbar Rikon Tsantsani Shidai Kallan Mahaukaci Karafiyan Takemasa Kamar Magani Karfiyan Din Daya Kawo Mata Kinyi Shuru? To Nagode Da Kokari Allah Ya Bar Zumunci,tatashi Zatafice Daga Motar Ya Ce Baki Ce Komai Ba Ai? A Lalace Ta Ce Da Me? Game Da Hujjojin Dana Kawowa Hanzarinki Na Nema Wa 'ya'yanmu Makoma Mai Kyau Takarasa Ficewa Mujinkirta Tattaunawar Har Saina Gama Maganin Munga Abinda Haliyai,to Ba Bu Laifi Yafada Cikin Karsashi Dajin Farincikin Ruma Tadawo Rayuwar Sa Tagama Indai Wuyar Ciwo Shine Kasa Gano Maganinsa Sukai Sallama Yafice Tashi Ge Gida Kulallen Kanta Dauke Da Yushau Tsohon Miji,tare Da Mahaukacin Masoyi Sabon Miji, Daidai Lokacine Alhji Ya Saki Labulen Falonsa Shima Nasa Kan A Rude,shine Yake Kishin Ruma Da Rayuwarta Ita Bata Kishin Kanta Harda Bazata Iya Gane Yushau Dan Ta Adda Bane A Rayuwarta, bayan Share Dare Cikin Raba Daidai Tsakanin Bacci Da Ido Biyu Bayan Sallar Asuba Tasamu Ta Runtsa Karfe Takwas Da Rabi Mairo Ta Farkar Da Ita Da Zummar Ta Amsa Kiran Alhji.. . Hhhh.. Wai dan ta adda? Lallai kuwa Yushau dan ta adda ne Naziri kuma dan Kidnapin. Dan Aunty kuma Masoyin Ruma... . Dan Aunty. GORAN DUMA (P 60) . . Tun Data karasa Farkowa Ta Shiga Rudani Da Fargaba Dan Tana Da Yakinin Banza Batakai Zomo Kasuwa A Gurguje Takarasa Shiryawa Ta Iske Shi Afalonsa Yadda taga Fuskar Alhji Kuma Ya Kara Bata Tabbacin Da Sauki Lfya Suna Gaisawa Bai Tsaya Bata Lokaci Ba Yace Jiya Naga Yushau Yakawo Ki meke Tsakaninku? Kayan Cikinta Suka Kada Ba Komai Alhji Ko Dai Bakyaso In sani? Rauninta Yasanya Alhji Ya Rage Gizagon Fuskar Sa,kwanaki Yazo Yasameni Da Maganar Yanaso Ya Mayar Da Aurenki Atakaice Bamu Rabu Ta Dadi Da Shiba Sai kuma Abin Mamaki Da Takaich Jiya Sai Na Ganku Tare Kila Kin Karbi Tayinsa Kenan Gaskiyar Magana Abin Baiyin Dadi Ba Sam! Ruma Taji Wani Irin Tausayin Alhji Ya Rufeta Ashe Sharri Yushau Ke masa Daya Ce Wai Ya Amince Ta Natsu Kafin ta Amsa Dan Bata Manta Tsakanin Da Da Mahaifi Sai Allah Duk Abinda Za Ai Lallai Baikamata Ta Wuce Gona Da Iriba Muna Shirin Tahowa Gida Da Mubarak Ajiya Yazo Yanemi Alfarmar Dan Allah Inzo Yakaini To A Hanya Dai Ya Nuna Min Manufar Sa Kamar Yadda Ya Sanar Dakai Amma Ban Amsa masa Da Komai Ba Cike Da Doki Alhji Ya Ce Yauwa Kinyi Kyan Kai Dan Ni A Wajen Batun Komawa Auren Yushau Ma Sam Bata Tasoba Wanda Hakan Yasa Har Nadanyi Miki Karambani Ban Sani Ba Ko Dadi Zaiyi miki Kokuma Daci Ta Dago Cikin Muguwar Fargaba Meta Zata? Wani Yaro Mai Hankali Da Mutunci Kuma Dan Babban Gida Shekaran Jiya Nan Yazo Min Da Kokon Barar Aurenki Ni Kuma Nai Masa, Har Yanzu Ta Kasa Dauke Ido Alamar Dukkan Furucinsa Suna Sauka Inda Yakama A Kwanyarta,anyi Masa Amanna An Bashi Auranta Kenan,wanene Wannan Ya Dace Da Ita Zallarta Mai Amsa Sunar Ruma Kuma Mai Dogon Numfashi A Matsayinta Na Sikila? Tambayoyinda Sukemata Yawo A Makogoranta Kenan Amma Ta Tabbatar Bata Da Muhallin Furtasu Nayi Masa Amanna Ai Ba Sadakinsa Na Karba Nakira Shaidu Ba Ruma Kamar Yadda Na Fada Miki Hankalinsa Na Yaba Dakuma Gidan Da Yafito Saikuma Tarihin Son da Yake Miki Wanda Naji A Bakin Sani,, Waye Shine? Kaitsaye Ya Ce NAZIFI MUHAMMAD Aiya Cemin Kinsan Shi Kamar Ta Girgiza Kai Cikin Rudewar Kwakwalwa Amma Saita Cije Rudunta Yasha Sharafi A Kwanyarta Kadai Muryarta Na Rawa Ta Ce, Nasanshi Daga Nesa, shima Hakan Ya Cemin Inji Alhji Yafito Daga Hadeja Ta Jihar Jigawa Daga Shahararren Dan Kasuwar Nan Alhji Muhammad Hadi Da Mahaifiyar Sa Hassana Haifaffiyar Kano Da Rano,yayi Digirinsa Na Daya Sanin Halayyar Dan Adam Na Biyu Ya Karanci Kasuwanci Amma Daya Bangaren Yanada Nasibi Sosai A Bangaren Na,ura Mai Kwakwalwa Saiya Hada Taura Biyu A Baki Ya Ke Taunawa Ji Da Harkokin Kasuwancin Mahaifinsa Da Kuma Nasa Harkokin Na Aiki Karkashin Kamfanin Layin Waya A,T,S Dakuma Shagunan Sayar Da Kayayyakin Da Suka Danganci Sadarwa Daya Daga Ciki Shine Milky Way Cafe Dake Abuja Ya Samarmin Ma Anan Ya Ganki Bayan Wannan Yana Da Kamfanin Ginin Website Tare Da Ma,aikata Shekarunsa Talatin Da Biyar Yataba Neman Aure Sau Biyu Allah Bai Nufa Ba Dan Haka Ya Jingine Maganar Auren Wadda Bata Tashiba Sai Akanki Atakaice Ta Ture Duk Wani Shi Ga Ukun Data Shi Ga Farinsani A TariHi Amma Baimasa A Shige Da Fice Ba Wanda Yake Bashi Damar Kama Da Aljanu A Ayyuka,kila Dukkan Aiyukansa Ko Na Neman Aurensa Kawai Kila Matahaka Matan Kan Kubuce Ciki Har Da Ita Alhji Ya Ce Nayiwa Mahaifinsa Farin sani Haka Dai Yaita Bata Tarihin Nazifi Ciki Harda Wahalar Da Mahaifiyar Sa Ta Sha Wajen Haihuwar Sa Inda Dole Likitoci Sukaiwa Mahaifiyar Sa Tiyata Aka Ciro Nazifi Wanda Daganan Aka Ciremata Mahaifa Saboda Haka Nazifi Shine Danta Na Fari Kuma Autanta Saida Mahaifinsa Yataya Ta Karajin Alkunyar In Ya Kara Aure Zatai Tsammanin Haihuwa Yake nema Har Zuwa Yau Bai Zubar Da Makaman Karar Nan Tasa Ba Ruma Wannan Halaccin Nasa Ma Yana Daya Daga Cikin Abinda Nake Fata Nazifi Ya Gada Kisami Danshi Ruma, ruma Tayi Nisa Zuciyarta Na Rage Nauyi Tana Kara Mata Damun Fuskokin Nazifi Da Kallo Ba A Mai Suddabaru A Waya Da Sakonnin Test Ba,a Fuskar Da Alhji Kawai Yasanshi Dakuma Cuda Jiyanta Da Yau Mai Auwal Da Yushau Sannan Goben Ta Wadda Nazifi Keson Shiga. Kije Kiyi Nazari Zaizo Yau Ku Tattauna Kuma Ba Bu Dole A Ciki In Baimiki Ba Ko Ke Banason Ki Cuci Kanki Ki Karbe Shi Bare Ni Nayi Miki Kuka, TaCe masa Yasan Ni Sikila Ce? Yasan Ni Bazawara Ce? Yasanki Ciki Da Bai Kafin Yazo Neman Aurenki Alhji A Yanzu Nasan Ba Kyan Hali Ko Na Asali Kawai Nake Nema A Miji Ba Ina Neman Nagartar Lafyata Ko Ta 'ya'yan Dazan Haifa,,tuni Na Sakawa Raina Zuwan Mijin Da Zan Haifa 'ya'ya Masu Lfya Ko Da Kuwa Cikin Jiran Mutuwata Zata Riskeni, ban Fahimcekiba Tajima Cikin Girgiza Kai Da Rausayawa Idonta Cike Da Hawaye Ta Ce Ina Nufin Ka Bani Sati Biyu Na Tattauna Da Nazifi Tattaunawa Dangane Da Ciwona Sannan Muje Asibiti Nasan Matsayinsa In An Sami Akasin Da Lfyar 'ya'yan Dazamu Haifa Zata Shiga Gararin Jihadi Ne Mucetosu Ta Hanyar Hakura Da Auren juna In Kuma An Dace Nayi maka Alkawari Sakeyi Maka Biyayya Akaro Na Biyu Alhji Ma Yaji Hawaye Naneman Kwacemasa Na Gamsu Insha Allah Ba Za Akara Samun Akasin Da Aka Samu A Baya Ba,tamike Ta Bar Falon Daidai Lokacinda Wayar Hannunta Ta Kad'a, Hello Akayi Shuru Da Alama Anajinta Saita Sake Maimaitawa Rumaisau Nazifi Yakira Sunanta Cikin Yanayin Nutsuwa Da Kuma Damuwar Yadda Yaji Muryarta Tai maza Tajanyo Natsuwa Na Am Barka Da Safiya Barkanki Dai Yaya Naji Muryarki Kamar Kina Cikin Damuwa Yadan Gitse Murya Ko? Zuwa Yanzu Nasan Kinsan Waye Mahaukacin Masoyi Kuma Waye Nazifi Muhammad To Don Allah Mu Ajiye Game A Gefe Guda Muyi Abin daya Kamatarmu Ina Cikn Rudun so Ruma Ba Bu Abinda Zai Warware Ni Sai Shiga Zuciyar Wadda Nakeso Nasamo Aminci Kuma Naji Matasayi Na Ina Sonki Ruma Karkiya Wasa Da Alamarina Bokanci Ko Aljananci Datake Zata Masa Ya Dawo Sabo Ta Ina Yasan Alhji Yasanar Da Ita Kansa? Wannan Yasa Ta Tare Shi San Dataji Zaizarce Da Maganar Abinda Ya Riga Yafara Samun Gurbi A Yuciyarta Wato Sonsa Gyara zancenka Dai Nasan Nazifi Muhammad Amma Har Yanzu Bansan Mahaukacin Masoyi Ba Yai Karamar Dariya Ai Bakiso Ki Gani Bane,,to Ina So Insanni Yaushe? Duk Lokacin Daka Shirya, Nasanar Dake Yau Kawai Nake Da Ita A Kano Kin Lashi Lokatai Da Yawa A Hutu Cikin Rashin Kulawa Ta Ce Ba Bu Matsala Muna Iya Daga Sanin Har Zuwa Lokacin Dazaka Samu Lokaci Kai Tsaye Ya Amsa Ko?To Dama Nakira Kine Inji Karfe Nawa Kika Shirya Zuwana? Dazaka Zo Din Kakemin Lissafin Na Lashi Lokuta Saboda Haka Zaka Buga Sammako Gobe E,h Ai Maganar Aurena Zata Kawo Ni Ba Maganar Mahaukacin Masoyi Ba Ruma Tadan Rausaya Kai Na Gajiya Da Yawo Da Hankali Inkaji Wani Abu A Bakina Dangane Da Aurenka Malam Ai Ka Kaddara Kawai Ba Daga Zuciyata Yataso Ba Ta Yaya Zan Auri Mutumin Da Ban sani ba? Au Yanzu Baki San Nazifi Muhammad Ba Alhalin Nasan Alhji Bazaimiki Kwange A Tarihina Ba Ta Cemasa Nida Mahaukacin Masoyi Nake Magana Yanzu Shine Kuma Bansaniba,yaCe mata Shikenan Kishare Mahaukacin Masoyi Ki Saurari Nazifi Muhammad Kawai Ki Sanar Da Ni Lokacin Da Zanzo Don Allah Karo Nafarko Datayi 'yar Dariya Shikenan Kazo Bayan La,asar Ka Saurari Maganganun Fatar Bakina Wadanda Suka Sha Bambam Dana Zuciyata Zaka Fara Sanin Gaskiyar Zuciyatane Daga Ranar Dana Sanka A Hakikanin Sunayenka Biyu Nazifi Muhamma Da na Mahaukacin Masoyi Nidai Bukata A Saurareni Yafada Yana Ci Gaba Da Dariya Har Ta Kashe Waya Bai Ankara ba, . Pls. Amin uzuri rashin jina kwana biyu. Kauyen namu ne wutar ta baci, babu caji... . Dan Aunty. GORAN DUMA (P 61) . . Katin Zamowarta Sikila Tagani A Hannunsa Wanda Da Alama Tayi Murna Da Ganin Haka Ya Zauna A Kujerar Kusa Da Ita Ya Ce Kinama Gamsuwa Da Sanin Dakika Yiwa Nazifi Ko Kina Bukatar Kari? Ruma Tadubi Shi A Takaice Cikin Yanayin Kasala Da Sanyin Jiki Amma Rudu Ya Hanata Tankawa Dole Ta Kawar Dakai Tana Dan Kebe Baki Na Rashin Madafa Nazipi Ya Mike Ina Zuwa Ya Ajiye Card Din Itakuma Tana Tunanin Miyaja Raayinsa Haka Bata Canki Adadin Lokaci Ba Yadawo Falon Hannunsa Dauke Da Wasu Takardu Kai Tsaye Ya Karaso Gareta Yamika Mata,hannunta Na Karkarwa Ta Karbi Takardun Tafara Kirgasu Da Ido Guda Uku,sannan Cikin Sa Wa Azarbabi Karfi Ta Fara Nazarin Ta Farkon A Natse Dukkan Takardun Sunfito Daga Asibitin Koyarwa Na Aminu Kano Takardar Farko Ta Sakamakon Gwajin H,I,V NE Kanjamau Wanda Yanuna Ba Bu Cutar, Batasan Abinda Ya Rudata Ba Da Sauri Cikin Bugun Zuciya Tajanyo Takarda Ta Biyu Itakuma Sakamakon Gwajin Ajin Jini Ce Blood Group Wanda Sakamakon Yanuna Rukunin Jinin Nazifi B Ne Ganin Hakan Yakara Mata Dokin Na Ukun Wanda Takesa Ran Nan Makomar Aurenta Yake A Takarda Na Ukun Indai Dagaske Nazifi Yasan Ita Sikila Ce Da Gaske Ita Ce!Taji Gabanta Yasake Tarwatsewa Cike Da Tsoro Tabi Takardar Da Nazari Sakamakon Gwajin Gynotype Ne Kamar Yadda Tazata Tako Yi Dokin Ta Tarar Duk Wani Nauin Da Ake Wa Duba Da Nazari Tayiwa Takardar Nan Tayi Na Fargaba Tayi Na Doki Tayina Shakka Tayi Na Tabbatarwa Tayi Na Murna Sakamakon Gwajin Nazifi Yanuna 'ya'yan Jininsa AA NE Akar She Ta Daga Ta Dube Shi Cikin Zubar Da Hawaye,zuciyarta Da Kwakwalwarta Basu Tattauna Bataji Sun Aiki Bakinta Na Yanke Hukunci Mekake Nufi? Tafada Cikin Rauni Wanda Hawaye Ya Taimakawa Nuna Kai Nazifi Ya Zube Gabanta Cikin Kuzari Ya Dafa Hannun Kujerar Datake Zaune Maimakon Hannayenta Da Inda Halacci Su Suka Kamata Yadafa Shima Idansa Suncika Da Kwalla Amma Ya Kyalesu Ya Bayyana Daga Makyankyasar Soyayya Suka Taso Bana Rauni Ko Farin ciki Irin Nata Ba Yazura Idonsa Cikin Nata Ya Ce Ina Nufin Nazifi Ya Cancanta,,,na Cancanta Ruma Kizo Mu Rayu Tare Tayi Baya Cikin Tarairayarmu A Matsayin Ma Aurata Taimakon Junane Ruma Ko Wannan Yakamata Kituna Inasonki Ruma Idan Kin Aureni Kin Yi Taimako Kuma Kin Ceto Dan In Ba Haka Ba Kila Son Naki Ya Iya Kisa In Narasa In Na Aureki Na Taimakeki Dan Rauninki Na Bukatar Mai Sonki Irina Lfyarki Tana Bukatar Mai Sadaukar miki Da Komai Irina Ya'yanki Suna Bukatar Sirkin Jinina Wanda Zai Cetosu Daga Zama Gundarin Sikila Taji Tana Neman Barkewa Da Kuka Sai Rausaya Kaikawai Take Ta Ce To Idan Hakane Kaine Kawai Zaka Iya Taimako Bandani Domin So A Aure Yakamata Ne Ba Wajibi Ba Zaman Lfya Da Kwanciyar Hankali Kan Riskar Da Kyakyawar Manufa Kammaluwar Iyali Masu Koshin Lfya Da Kyakyawar Zuciya Sune Manufar Iyali So Ne Zai Jagoranci Haka Ko Hakuri Da Sadaukarwa Yanzu Hankalin Nazifi Yafara Kwanciya Yanzu Zuciyar Sa Ta Canja Bugu Daga Fargabar Yada Manufa Saboda Ta Shinshino Nasara Yanzu Bugunta Na Cin Nasarane Dakuma Wanzuwarta A Fagen Da Masoya Ke Taka Rawa Sabanin Da Can Ba Da Take A Matsayin Masoyiya Ita Kadai Kuma Take Taka Rawarta, Yamike Tsaye Yana Nazari Ya Ce Sam Bazan Yarda Da Raayinki Ba Abubuwa Da Dama Nacin Albarkacin So Ni Shaidane Zuciyata Babban Masaki Takai Aka Cika Mata Da Sonki Ba Shine Dalilin Dazan Iya Sadaukarmiki Da Komai Ba? Tun Da Dadewa Nasan Type Din Jinina B Ne Amma Banta Ba Daukar Sa Wata Tsiya Ko Ya Sanya Ni Murna Ba Saida Na Tarar Danaki Type Din AB Wanda Da Aceni AB Ke B Kila In Dauwama Cikin Rauni Da Kukan Bazan Iya Biyan Hakkin Soyayya Ba Alokacin Dakike Bukatar jini Tanadin Zaman Lfya Da Kammaluwar Iyali Ne Ko Kuma Tanadin Sadaukarwa So? Ruma Kamrauninta Yasa Ta Sheshekar Kuka Kwakwalwarta Ta Gaza Nazifi Ya Durkushe A Gabanta Ni Inkin Danganta Son danake Miki A Tanadin Aure Kawai Kin Yiwa Son Kwange Ina Sonki Da Kyau Zan Iya Sadaukar Da Komai Dominki,in Ban Aureki Ba Ma Ba Fasa Sonki Zanyiba,dan Haka Nasan Sonki Ba Shiga Zuciyata Dan Bukatar Aure Kawai Ba Yadda Nake Jin Sonki Ba Haka Na Saba Ganin Maza Nason Matayensu Ba,takasa Magana A Cikin Tunaninta Abu Uku Kacal Ne Aranta Amma Masu Fadi A Tarihinta, "Auwal Yadawo,tafada Acikin Ranta Yayinda Kamar Nazifi Yasan Tunaninta Ya Ce Nafi Auwal Sonki Ruma Ina kasan Auwal? Kai Tsaye Nazifi Ya Amsa Komai Ake Nasani Ruma Wannan Zai Baki Shaidar Ban Fara Sonki Da Wasa Ba Ta Cemasa Duk Lokacinda Ka Shirya Nasan Sirrin Mahaukacin Masoyi Saikadawo Ka Karbi Amsata Cikin Dariya Ya Mike Tunda Kince Duk Abinda Zanji Daga Gareki Yau Na Fatar Bakine Na Yarda Da Maganarki Ta Yanzu A Fatar Baki Acan Cikin Zuciyarki Nasan Kin Binne Amincewa Dani Duk Ranar Dakika San Mahaukacin Masoyi Saikin Baniko? Nayarda Zantafi A Hakan Wato Da Gaske Har Yanzu Zakaci Gaba Da Wasa Da Hankalina!Haka!Bazaka Tausayaminba? Da Gaske Ruma Bansan Mahaukacin Masoyin Dakikeson Saniba Baya Gani Da Nake Tsaye Gabanki Ba,har Yanzu Nakasa Gano Abinda Ya Baki Mamaki Ko Yake Rudaki A Mahaukacin Masoyi Ko Sunan Ne? Wato Mahaukacin Masoyi? In Shine Abokina Mas!Ud Ya Rada Min Tun Bayan Ganin Haukan Son Danakemiki Daga Gani Daya Kacal Sannan A Lokacin banda Sunanki Da Lambar Wayarki Daya Ban San Komai Akan kiba, Kaine Bakasan Ni Ba Anya? Ta Ina Ka Bi To Kasanni Da Har Kake Iya Sani Nani Da Abinda Zuciyata Take Rayawa Taina Kake Kallon Halinda Nake Ciki Har Kayi Tsokaci Akai? Ban Manta Ba Kayimin Ganin Farko Ne Ranar 15th Nov Kuma Ina Tsammanin Tun Wajen 18th Nov Nafara Samun Sakonninka Wadanda Suke Nuni Kana Ganin Duk Motsina Da Gaske? Cikin Bayyana Mamaki Kinsan Da Haka Kika Kasa Sanar Dani Saida Lokaci Ya Kure? Kinga Yanzu Za Akira Sallar Magariba To Naji Kwantar Da Hankalinki Kibani Sati Biyu Inje Gida In Rago Ayyukan Gabana Indawo Takanar Inzo Muwuni Kina Nuna Kwarewar Aikinki Akaina Wato Jaridanci Na Ci Alwashin Ba Bu Amsar Da Ba Zan Bayar Bisa Zahirin Gaskiya Ba,,,, kayi Alkawari? Nakusa Ta Ce Ba Bu Laifi Allah Yakaimu Ina Rokon Alfarmar Kafin Satin Biyun Kibani Damar Turo Manya Su Share Fagen Neman Aurena,,na Karanceki,,kuma Bakinki Ma Bai Furta Sharadin Aurena Jigine Yake Da Sanin Mahaukacin Masoyi Ba,, to Yanzu Na Furta Tafada A Hanzarce Da Alamun Matsawa Kanta Da Dakewa Shikenan Ma Na Samo Amsar, Ita Ce Ba Haka Bane Tundakin Tabbatarmin Furucin Bakinki Dabanda Kudurin Zuciya Dole Tasami Kanta Cikin Dariya Tana Kada Kai Kawai Shima Yana Tayata Sai Sannan Hankalinta Yadawo Kan Abincin Saukar Babban Bakon Da Aka Jeremasa Bakaci Komai Ba? Wayafada Miki? Tarakashi Har Wajen Motar Sa Dan Tafiya Suka Tsaya Suna Dan Hira Yana Bugun Cikinta Danjin Kalmar Amincewa Daga Fatar Bakinta Kamar Daga Sama Yushau Ya Jefo Tambaya Daga Bayanta Rumaisau Wanene Wannan? Ta Shanye Cikin Firgici Sannan Tajuya Ta Dubi Nazifi Wanda Ke wasa Da Makullin Mota Yana Cillawa Sama Yana Cabewa Yanayinsa Yana Nuna Banza Ya Baiwa Ajiyar Yushau Tun Datana Dayakinin A Sanin Da Yaimata Bazai Kasa Sanin Yushau Cikin Rayuwarta Ba Sau Uku Tana Kallon Mutanen Biyu Dake Gabanta Daya Bayan Daya Tamkar Mai Canki Cankin Wanda Zata Fifita Ko Wanda Zata Kaskantar Yushau Yazo Wuya Kamar Sunaso Su Yarfashine,kai Bakasan An Mata Miji Bane? Ruma A Firgice Tajuya Tare Da Dora Hannu Aka Kuma Da Shirin Kurma Ihu Musamman Data Ga Nazifi Na Dunkula Hannu Murya A Tausashe Nazifi Ya Amsa Aini Ne Mijin Ranka Yadade Sannan Yashiga Motar Sa Yanadaga Ma Ruma Hannu Zamuyi Magana A Waya Daga Yushau Har Ruma Sunyi Mutuwar Tsaye Kowa Danasa Dalilin Mutuwar,nazifi Na Bacewa Yushau Ya Farko Ta Hanyar WaiGowa A Fusace Ga Ruma Dan Ya Sauke Mata Fishinda Ya Tattara Amma Yana Waigowa Yagawayam Tuni Ta Bace Cikin Rashin Hayyaci Shima Ya Ruga Tasa Motar Ya Figa A Guje.. . Dan Aunty GORAN DUMA P( 62) . . Masud Na Kwance Rigingine Kan Gado Da Laptop Gabansa Yana Shawagi A Shafin Zumunci Na Facebook Nazifi Nata Faman Kai Komo A Tsakiyar Falo YazaBuro A Fusace Ya Fusge Laptop Kamar Zai Bugata Kasa Saikuma Yafasa Ya Dangwarar Da Ita Kan Sofa Yajuya Cikin Hargagi, Wallahi Zan Kashe Kada Mari Malam Nazo Da Matsaloli Amma Ka Hana Kwakwalwarka Ta Tayani Neman Waraka Da Wannan Latsetsen Takaici Ya Ishi Masud Yayi Zugui Yana Kallon Nazifi Sai Can Ya Basar Cikin Ko Inkula Ya Ce Aume Ma Ka Ce Menene Matsalar Ya Ce Da Alama Tarkona Yagama Kama Ruma Harma Nayi Azarbabin Sanar Da Ita Kafin Sati Biyu Zanturo. Munfito Zataimin Rakiya Muka Ci Karo Da Wannan Banzan Mutumin Yushau Alamunsa Sun Nuna Lallai Yanzu Tauraron Ruma Haske Yake A Idonsa,,ina Tsoron 'yan Ubanci Da 'yan Uwanci Masud Za A Iya Yankan Bayana Bayana Idan Nayi Wasa,,kasamo Wata Dabarar? Da Sauran Aiki Masud In Nayi Nasarar Samun Fage A Damar Auren Ruma Yaya Zanyi Da Kwanjin Yan Uwantakarta Da Wancen Karen Yushau? Ummanan Da Tata Rigimar Wanda Zata Hanani Na Ci Da Zafi Kar Rabon Wani Ya Shiga Masud Yayi Kasake Yana Sauraron Nazifi Tamkar Tausaya Masa Yake Amma Yana Direwa Sai Ya Saki Tsaki Ya Janyo Computer Sa Zo kagani Abinda Nagano Maka Shegen Ci Da Zucinka Yahana Ka Gani Jikin Nazifi Na Bari Yatafi Da Sauri Yakurawa Allon Computer Ido Masud Ya Budo Status Din Ruma Wandatai Mintina Talatin Da Biyar Da Suka Wuce Gajeren Sako Ne Amma Mai Dauke Muhimmanci KOKARI SHI KE BUDE KOFAR DAKE KULLE SANNAN BABU ABINDA KE MIKAR DA SANDARKA SAI NACIN DADDANNAWA Shine Sakon Na Ruma Wanda Nazifi Yadinga Karantawa Yana Maimaitawa Tundaga Kan Rubutun Wanda Idonsa Yakema Ganin Tamkar An Zana Da Ruwan Goal Ya Ce Kai Abokina Narage Maka Labari Kasan Ruma Kallan Aljani Ko Mutumin Boye Takemin Duk A Dalilin Basajar Daka Bayar Da Shawarar Ayimata Dagaske To Meyafaru Nan dai Suka Gama Hirar Su A KarShe suka Ce Mu Kulla Shawarar Yadda Umma Zata Amince Akan Kari Yadda Bazaka Saba Alwashin Daka Ci Na Tura Manya Kafin Sati Biyu Ya Cemasa Tunfarko Kayi Raguwar Dabarar Sanar Da Umma Cewa Ruma Bazawara Ce Kuma Ka Zabeta A Wadda Zaka Juyewa Dukkan Cikinka Akan Ruma Ya Ce Kaima Dai Masud Kai Ka Dauki Zawarci Kuren Daza A Dinga Faman Boyewa Allah Na Tuba Ni Zawarci Bashi Yaimin Riga Wando Inba Donshi Ba Na Isa Inga Ruma Ballena So? Mahaukacin Masoyi Inji Masud Cikin Dariya Lokacin daya ga Nazifi Ya Fitittike Yana Wanke Zawarci Kawai Ta Inda Zamu Bulluwa Umma Ta Gane Hatsarinda Nake ciki? Masud Yasake Lulawa Tunani Nazifi Ma Haka Amma Sai Yari Ga Farkowa Oh Na Tuno Wata Hikimar Zan Gwada. , BAYAN WATA UKU Nazo Ne Karakani Gidan Wani Shahararren Boka Dakasani Maikudi Kai Ko Matsafine Ni Dai Bukata Kayimin Rakiya Gurinsa Yushau Ke Fadawa Abokinsa Maikudi Cikin Tsanani Tashin Hankali Maikudi Cike Da Mamaki Harda Tsoro Ya Ke Kallon Yushau A Lfyarka Kake Kuwa Yushau Badan Nafi Kowa Sanin Tsantseninka Bana Ranste Da Allah Ba Abinda Zai Hanani Rantsewa Sholisho Ka Shaka Yushau Ya Furzar Da Numfashi Bayyana Takaici Da Tsananin Damuwa Banta Ba Zata Ba,banta Ba Ganiba,banta Ba Jin Labariba,na Rantse Da Allah Kuma Ko Za A Mutu Bazan Laminta Ba Maikudi Yakara Duban Yushau Yafara Zargin Hauka Yushau Ya Ci Kuka Yakoshh Yafara Share Hawaye Iyakar Cin Mutunci Da Wulakanci Anyimin Maikudi Wai Inje Gidan Mujiya Sai Na Tarar Da Taron Biki Har Andaura Aure Shekaranjiya,,maikudi Yatare Cikin Zumudi Da Fargaba Daurin Aurenwa? A Zafafe Yushau Ya Amsa Daurin Auren Ruma Dana Niki Gari Har Niger Kwana Goma Sha Biyu Dan Nemo Mata Magani Sikila Nayi Asarar Kudi Nayi Asarar Lokaci Na Har Kasar Haihuwa Duk Dan In Nunawa Ruma Zan Iya Rasa Rai Dominta, Amma An min Adalci Idan Na Dawo Na Tarar Ta Auri Wani? Banta Ba Ganin Iyayen Dakekin Jininsu Da Gaske Irin Nawa Ba Sun Sallame Ni Kuma Nima Yanzu Zan Nade Kafar Wando In Sallama Su Maikudi Ya Kadakai Cikin Jimami Babu Dadi Amma Da Yardar Ruma Katafi Niger Kuma Tasan Maganinta Zaka Karbo? Cikin Tsawa Ya Amsa Tasani Tasan Komai Jinake Kaika Sanar Da Ni Inda Zan Samo Fitsarin Rakumi Bada Kaimuka Jeyawo Neman Kunkurunba? Dawa Mukaje Gidan Sarkin Baka Karbo Magani Nine Sikilan Nina Kesha? Ba Ita Nake Kaiwa Tana Sha Ba?Kuma Tasan Dalilin Hakan Harma Da Shirinta Na Cewa Intaga Ta Fara Samun Sauki Zata Sanar Dani Ranar Da Zanje Niger Din Ma Ai Na Jemata Sallama Tasan Kuma Ko Kuda Bani Da Shi A Niger In Ba Maganinta Ba Uban Me Zanjeyi? Yasake Fashewa Dakuka Ba A KyauTa Maka Ba Maikudi Yafada Yake Maimaitawa Amma A Fatar Baki Amma Cikin Zuciyarsa Yanajin Hakkike Dawainiya Da Yushau Allah Yaimasa Niima Amma Sai Yajefa Hankalinsa Dawa Bai Ankara Ba Sai Da Niimar Ta Subuce Yayiwa Kansa Tsirara,shine Yanzu Zaizo Yayiwa Mutane surutu. Ina Kace In Rakaka? Yushau Ya Tsayar Da Fyace Hanci Yakara Daure Gira Gurin Rikakken Boka Ko Matsafi Zaka Kaini Ya Farraka Tsinannu Abin Haryakai Haka Yurhau? Maikudi Yafada A Raunane Yushau Ya Ce Banga Mafitar Datafi Wannanba Idan Na Kyalesu Kashe Nizasu Yi Allah Sarki Inji Maikudi Ya Ce Bangane Ba Yushau Kana Tsoron Mutuwane Wadda Tazame Maka Dole Dankanajin Dadin Wannan Duniyar Kokuma Domin Son Dakakewa Ruma? Ban Banbanta Da Kowa Ba Maikudi Rayuwar Duniya Wahala Ba Kuma A Kaunar Mutuwa Yo Kowa Ma Baiji Dadi Ba A Duniyarnan Bare Ni Mai Somoli Dariya Taso Kubcewa Maikudi Amma Ya Hadiye Amma Kasan Dahaka Kake Kokarin Jefa Kanka Wata Musibar Ta Fishin Allah Wajen Bin Bokaye Alhalin Inzaka Tuna Fishin Iyayenka A Hakkin Ruma Ne Yarataya Maka Sumoli Yatari Shi A Fusace Wanne Hakkin Ruma Na Danne? Karka Fadamin Maganar Banza Mana In Baka Da Abin Cemin Ni Ina Dashi A Fusace Yakarkade Rigar Sa Yatafi Maikudi Nata Kira Yaki Dawowa Bai Zame Koina Ba Sai Falon Gidansu Bayan Yasami Tabbacin Dukkan Baki Sun Darare. Kaiko Hajiyata Cika Da Mamakin Yadda Yau Dinnan Yushau Ke Gaisheta A Tsaye Dan Haka Ma Tasaki Baki Tana Kallansa Kaitsaye Ransa Abace Sai Faman Huci Yake Murya Ya Daure Hajiya Ta Ce Kaiwai Lfya? So Nake Aje Abuja A Daukomin Hamida Na Fasa Kyautar Dama Ai Bada Izinina Aka Kyautar Da Ita Ba Hajiya Tafahimci Ba Cikin Hayyacinsa Yakeba Tsabar Kishine Kawai Ke Wajigashi Dan Haka Ta Sanya Masa Ido Yadinga Sakin Maganganu Son Rasa Saida Ta Lura Yana Neman Wuce Gona Da Iri Sannan Tata ka masa Burki Malam Kar Kasake Ka Zageni Yai Tirjiya Kamar Mai Shirin Barkewa Da Kuka Ba Zaginki Zanyi Ba Hajiya Kawai Ni A Karbo Min 'yata Da Sauki Ai Indai Ba Ruma Za A Dauko Maka Ba 'yarka Za A Dauko Maka Gaskiya Da Sauki Inji Hajiya Hawayen Dayake Ta Rikewa Ya Subuce Masa Yana Murza Ido Yana Tafiya Da Baya Zuwa Zanyi Na Dauko 'yata Ku Hadamu Ku Kimu Tare Yana Maimaita Kalma Daya Ya Fice Daga Falon Cikin Rudu, ******** Yashafe Sama Da Sati Hudu Yana Jinyar Zuciya Wanda Jiki Yataya Ta Da Zazzabi A Wannan Dan Tsukin Ne Kuma Yakara Tabbatar Duniyar Tajuyamasa Baya Da Kyau Ba Bu Dangi Ba Bu Ruma Sumoli Da Yazaba Kuma Takara Nisa Dashi A Zatonsa Yanajinyar Nan Zata Rage Gantali Ta Zauna Takula Dashi Amma Ba Bu Abinda Yaragu Sannuma Saitagadama Takemasa Intsiyartama Yatashi Har Tsiyatakemasa Tawon Wata Daya Ya Warware Yafi Sabgoginsa Cikin Ikon Allah Kuma Sai Ga Sumoli Ta Kwanta Tanata Jinyar Alaye Iri Iri Na Ciki Ita Bai Risketa Ba Saida Cikin Yafara Girma To Mai Waina Ruwa Bare Yasami Mai Ai Nan Sumoli Taga Bakin Halin Juya Baya Domin Shiko Samun Na Rainawar Ma Baya Yimata Tun Tana Daukar Lamarin Wasa Harta Fara Tuna Masa Kanta Da Mawuyacin Halinda Zata Iya Shi Ga Wata Rana Mominta Ta Yasar Da Zuciyar Datai Na Dauke Kafa Daga Gidansu Tun Da Sumayyan Ta Bata Labarin Yushau Yai Tawayen Adaina Zuwa Masa Gida Tundaga Tsakar Gida Tafara Cin Karo Da Bola Har Tsakiyar Gado Inda Sumoli Ke Kwance Kangayau A Kasalce Mominta Yar Da Mayafi Ta Dago Tana Salati Tamkar Zata Fasa Kuka Na Shiga Uku Ummi Haka Aka Wulakanta Minke? Ina Yushau? Yatafi Kasuwa" cewar Ummi..... . Yo ai gwanda Yushau yasan makomar sa, ko da yake ni sadaukarwa nayiwa Nazifi na daga masa kafa, . Abbas Abdulkadir Hada Hada ( Dan Aunty ) GORAN DUMA ( P 63) . . Tsawan Lokaci Suka Dauka Suna Kwashewa Wa Yushau Albarka Sannan Takira Wani Dan Makwabtansu Yakai Sumoli Asibiti Tagama Yimata Hudubar Tsiya Tare Da Jaddada Mata Lallai Inyadawo Ta Cemasa Tana Nemansa Tundaga Kofar Gida Yushau Yasan Ansami Canji Saidai Ko Ajikinsa Wai Antsikari Kakkausa Ya Ratsa Kamshin Daya Turare gidan Ya Wuce Dakinsa Baijima Dazama Sumoli Ta Riskeshi Cikin Karfin Hali ta Zauna Hannun Kujera A Dogashe Baiko Dubeta Ba Ya Ce Sannu Dajiki Ta Tabe Baki Jiki Aiya Kusa Warkewa Maganar Data Kawo Ni Gurinka Kenan Inajinki Ta Dauke Kai Nayanke Shawarar Kawai A Zubar Da Cikin Nan Ina Tsammanin Kwayoyin Maganin Da Kike Banka Sunfara Zamemiki Kwayoyin Maye Naji Idan Ma Daga Turu Aka Kunto Ni Cikin Dai Ajikina Yake Da Ko Ya Koma Ko Na Haifa Da Alama Kaina Zan Haifawa Ba Wani Shegen Ba Batadireba Yakifa Mata Mari Kena Dai Na Raga Maki Sumayya Idan Maguzawane Suka Haifeki Dan Allah Kullum Kidinga Gaisheni Da Ashar Nikuma Nayi Alkawarin Amsa Miki Da Mahangurba Ba 'yan Dambe Suka Haifeni Ba Amma Sabodake Zan ara in yafa, "Duka? Ta katseashi, In Na Zage Ka Hukuncina Duka Da Fasa Baki? To Ina Na Zubar Da Cikin Mene Hukuncina? Dan Wallahi Ba Bu Tsinanne Da Zai Sanya Ni In Haifeshi Yayi kokarin Kawo Mata Wani Bahagon Marin Amma Ta Goce A Guje Tayi Kofar Daki A Tsaya Daga Bakin Kofa Tana Harararsa Kika Zubarmin Da Ciki Sumoli Na Rantsemiki Da Allah Saina Daure Ubanki Wanda Bai Baki Ilimi Da Tarbiya Ba Allah Sarki Aini Da Sauki Tarbiya Ce Ma Gaba Daya Ba A Baniba Wani Shegen Bashi Aka Yiya Tankwabe Kuma Wallahi Kasake Zagin Ubana Saina Rama Dan Uba Bai Fi Uba Yadda Yushau Yatunzura Yasan Idan Ya Biyemata Saidai Adau Gawarta Kificemin Daga Daki Ta Cemasa Kuma Momi Ta Ce Kaje Tana Son Ganinka A Tunzure Ya Ce Ba Bu Inda Zanje Wallah Idan Kuma Za A Daukeni Akai Sai A Gwada karfe Goma Na safiya Ruma Tafarka Cikin Kasala Ta Waiwayi Makwancin Nazifi Ta Tarar Ba Bushi Da Sauri Tayi Kokarin Korar Kasalar Ta Hau Lalubensa A Bandakuna Kafin Takoma Sauran Dakuna Da Falo Ba Bushi A can Teburin Cin Abinci Ta Tsaya Fakare Tana Bin Kayan Abincin da kallo, Alamu Sun Nuna Yaci Nasa Yafice Kwakwalwarta Ta Karade Da Tunanuwa Barkatai Har Daga Karshe Daya Daga Ciki Ya Bata Kwallah Shine Yushau Ya Sha Muzanta Mata Da Dogaronsa Akan Kasalarta Tayi Yawa Bata Kula Dashi Yadda Yakamata Duk Da Cewa Tana Iyakar Kokarin Tashi Taji Da Shi Kafin Yatafi Harkokinsa To Nazifi A Tsawon Zamanta Dashi Na Watanni Kusan Biyu Bata Taba Farkawa Ranar Aiki Ta Tarar Ya Fice Batare Daya Bar Mata Duk Wani Gibin Aikin Dazata Sami Lada Ba Wato Ya Cikamata Gida Da Masu Aiki Mata Har Kala Uku Mai Share Share Da Wanke Wanke Ga Kuma Mai Girki Daban Banda Maza Masu Aiyukan Karfi Irinsu Wanki Da Kula Da Farfajiyar Gida Yanuna Rashin Amincewar Shigar Masu Aikin Dakunan Baccinsu Amma Bata Ta Ba Farkawa Ba Tatarar Da Dakunan A Gyare Ba Ma'ana Shiyake Gyarawa Kenan Kasala Da Cututuka Sun Taka Rawa A Tsinke Aurenta Na Baya Idan Antafi Ahaka Kuwa Nazifi Bazai Dayo Yatsaneta Ba Duk Da Dumbin Sondayake Mata?Kwanakin Can Ta Taba Yanke Shawarar Hana Idonta Baccin Safe Bayan Azkar Din Safiya Kasancewar Kullum Nazifi Kan Dawo Masallaci Yasamu Ta Koma Bacci Ranar Saiyasameta Farke Cikin Kulawa Yafara Nazarin Ta Har Da Bincikarta Hannu Da Kafafu Ina Fatan Lfya Ruma? Banjin Dadin Yadda Kullum Nake Farkawa Ban Tarar Da Kai Ba Ban Sami Ladanka A Komai Bako Da Karamine In Fesa Maka Turare Yayin Shirin Fitarka Tafada Cikin Tausasa Murya Tadan Kishingida A Kirjinsa Hakandatai Nekuma Ya Tabbatar Masa A Kasalcenta Take Ta Sadaukarne Kawai Danta Faranta Masa Rai Ya Kwantar Dakanta A Kafadar Sa Yana Shafar Gashin Ta A Hankali Shine Yanzu Kike Hana Idanki Bacci Dankiyi Me? Mu Gaisa Kuma Intayaka Shirin Fita Ai Nafasa Yau Ba Bu Inda Zani Yafara Matsamata Gabobi Cikin Shakku Ta Ce Habadai Ammafa Jiya Harkarfe Biyu Kana Fama Da Aiki Kuma Ka Ce Min Sammako Zakayi Ka Fita Dashi Nafasa Ya Cemata Yana Gyara Bargo Ya Kwanta Ruma Tayi Sakare Tana Binsa Da Kallo Kamar Yadda Nasa Idon Ke Kallonta Yamiko Mata Hannu Bacci Nakeji Sosai Zoki Tayani Ba Musu Domin Abinda Take Bukata Kenan Tajeta Kwanta Ba Bu Jimawa Bacci Ya dauketa Bata Farka Ba Sai Goma Da Rabi Nankuma Ta Shafa Ba Bu Nazifi Data Bincika Sai Ta Tarar Tun Bakwai Yafita Batafi Rabin awa Da Komawa Bacci Ba Kenan Wannan Yasanya Tafara Shakkun In Gaskiya Yafadamata Daya Baya Saita Canja Dabarar Inda Saita Alarm A Wayarta Dan Tadinga Tayar Da Ita Karfe Shidda Da Rabi A Ranar Nazifi Na Dawowa Gida Abinda Yafara Tambayarta Kenan Mizaki Dinga Yi Karfe Shidda Da Rabi Na Safiya Dakika Sanya Kararrawa Tadinga Tashinki? Tadubeshi Cike Da Tsoro Da Zargi Baki Bude Da Kyar Tasamu Amsa Masa Waya Fadamaka? Yai Gaba Alamar Nadamar Furucinsa Amma Sai Yai Fuska Ruma Saikin Nuna Min Dole Ke 'yar Kano Ce? Amsa Nake Bukata Ba Tambaya Ba Tawuce Kichen Ta Shiryamasa Kayan Jika Makoshi Takawo Masa To Sannu Allah Yaimiki Albarka Yafada Bayan Yadire Tambulan Ya Lura Da Ita Cikin Tsarguwa Ta Zauna Kan Coffe Table Daga Gefensa Na Hagu Tanajan Yatsunta Cikin Fuska Ba Yabo Ba Fallasa Mahaukacin Masoyi Mamaki Ya Shige Shi Dakyau Amma Ya Daure Ya Basar Yana Binta Da Ido Tsawon lokaCi Na fada maka Matsala Ita Ce Banajin Dadin Yadda Muke Sallama Da Juna Da Dare Ko Da Asuba Shi Ne Dalilin Saita Kararrawar Yadan Yi Jim Sannan Yakawar Dakai Daga Kallonta A Tausashe Ya Ce Shikenan Ki Bar Abarki Kar Kicire To Amsa Min Tawa Tambayar Inakasan Na Sanya Alarm? Dazu Na shiGo Kina Wanka Ankira Wayar Na Zo Amsawa Nagani Tasan Karya Yaimata Hakkum Amma Yanada Kwarjini Da Bata Iya Musu Dashi Dan Haka Tai Murmushi Ta Rausayar Dakai TaCe Ok Tana Ci Gaba Dajan Yatsun Hannunta Suna Kara Yakamo Hannunta Yana Dubawa Cikin Kulawa Meya Sami Yatsun? Ba Komai Tafada Cikin Kasa Hankali Tana Sane Wane Ne Mahaukacin Masoyi Ta Aura Amma Bata Taba Tsammanin Lullubin Birin Zai Zarce Har A Cikin Zaman Aurensu Ba Gashi Dai A Yanzu Tana Da Kusanci Dashi Yadda Take Caje Shi Ciki Da Bai Bata Tarar Da Alamun Zamowar Sa Jinnuba To Ta Ina Yake Samin Boyayyun Al'amuranta? Tayi masa Wannan Tambayar Tafi Sau Ashirin Yana Wawantar Da Ita Kin Tabbata BBu Komai? Ya Katse Mata Tunani Lokacinda Yafara Taya ta Jan Yatsun Ta Bi Yatsun da Kallo, Inafata Kinsha Magungunanki? Na sha Ta Amsa Atakaice Ya Bita Da Nazari Sannan Yajata Jikinsa Fadamin Meya Bata miki Rai Ina Tambayar Sanya Alarm Ceki Yafemin Naimiki Alkawarin Bazan Sake Ba Kinji? Da Sauri Takada Kai Duk Da Bai Bata Wannan Damar Ba Saita Sami Kanta Cikin Kwalla Baka Da Abinda Zai Batan Rai Kwata Kwata Nazifi Amma Ina Bukatar Ka Yarda Dani Dari Bisa Dari Ban Fada Tarkon So Irin Naka Ba Amma Ni tun Asali Rayuwata Tagaji Rashin Manta Alkhairi Halittar So A Cikin Zuciyata Mai Saurin Mika Wuya Ce Ga Kyautatawa Kawai Dan Haka Ka Zaci Kirjina Cike Yake Da Kaunarka Da Zata Yi Haihuwa Ka Kyautatamin Ko Baka Kyautata Ba Ya Rungumeta Da Kyau Bukatarki Kenan? Aina Yarda Dake Dari Bisa Dari Ruma Kyautatawata Ba Dalilinta Kenan Ba Watoki Soni Dalilinta Yasamu Ne Karkashin Tausayi Da Soyayyar Dani Nake Miki Ko Yaya Kike Haka Nake So Ko Yaya Zanyi Dawainiya Haka Nakeso Kin Fahimceni? Ya Dago Fuskarta Yana Duba Wani Irin Shaukin Sonsa Yakara Mamaye Mata Kirji Har Yai Tasirin Hana Ta Cigaba Da Neman Sanin Mahaukacin MASOYI . Dan Aunty. GORAN DUMA (P 64) . . Ina Tune Hafsat Kasalata Da Ciwona Sun Taka Rawa Wajen Jawo Min Tsana A Gurin Yaya Yushau Kila Har Yake Ganin Ba Bu Asara Inya Rabu Dani In Nazifi Ya Dauki Wannan Matakin Akaina Bana Tsammanin Zan Iya Jurewa Da Kyar Zan Iya Rayuwar Da Babu Shi,, hafsat Ta Ce Cikin Tausasawa Karka Cika Wa Kwakwalwark Tunani Da Zargi Mara Tushe Ruma Bai Kamata Ki Sanya Kuka So Yasa Ki Ba Ruma Ta Ce Nafadamiki Hujjata, Hafsat Ta Ce Aina Fahimceki Abinda Kika Kasa Tunawa Shine In Yaya Yushau Bai Yarda Da Sikila Ba Yana Mata Kallon Gaibu Ko Shafar Jinnu A Wajensa Daidai Ne Ya Tsani Kasalarki Amma Nazifi Yasan Sikila Ciki Da Bai A Dalilinki Ta Yaya Zai Karyata Yadda Rayuwarki Take? A Ganina Zaton Hakan Dakike Masa Ma Kaskantar Da Son Dayakemikine? Ruma Ta Sauke Wata Doguwar Ajiyar Zuciya Karfafa Mini Gwaiwa Daikike TaCe mata Sonda Yakemiki Baikai Haka Ba Baya Sona Kawai Nake Bukata Ba Yaita Sona Har Abada Nake Nema Hafsat Dan Son Dayakemin Yana Da Tarin Alfarma Da Aminci A Kulliyar Rayuwata Wanna Yana Cikin Jerin Adduoina Danake Miki Ruma Wata Kwallar Farinciki Ta sauko daga idonta. Daga Hirar Da Ruma Tayi Da Hafsa Sai Ga Kiran Nazifi Ya Shigo Ta Daga Ta Cemasa Ranka Ya Dade Zanyi Fushifa Muryar Sa Da Alamun Damuwa Ya Ce Oh Kezaki Fara Yin Fushi Konizan Fara? A Rikice Ta Ce Da Akayime? Nazifi Inkayi Fushi Ba Bu Rumaisau Menayi Ya Amsa Kina Raina Son Danake Miki Har Kike Danganta Rawarsa Da Kasalarki In Yushau Ya Tsane Ki Dalilin Kasala Har Takai Ga Yasake Ki Kila Ya Aureki Ne Donkiyi Masa Hidima Nikuwa Na Aureki Ne Don Ina Sonki Tunkafin Haka Na Shiryamiki Hidima Kaico Har Zuwa Yau Ruma Baki Ga Na Cancanci Kar A Hada Kafadata Data Yushau Ba? Zuciyarta Ta Nemi Dakatar Da Aiki Amma Wasi Wasi Ya Hana Hakan Tafara Waige Waige Ko Nazifi Ya Boye A Wata Kafar Ne Har Yasan Tayi Hirar Sa Da Hafsat Amma Takasa Gano Amsar Ta Cemasa Nazifi Ina Sonka Tasake Maimaitawa Kaji Alfaharin Ban Taba Furtawa Yushau Wannan Kalmar Ba Kai Kuwa Na Sha Furta Maka Bin Hakki Da Gaskiya Nan Ma Taji Jiran Amsa Cike Da Fargaba Ta Cemasa Kadaure Karkai Fushi Yace Bazanyi Ba Amma Ina Sonki Sani Indai Ruma Ce Ina Sonta Badai Ruma Dai Ruma Sikila Ba? Ko Mai Amsa Zallar Sunan Ruma Da Mai Amsa Zallar Sunan Sikila Bazanta Ba Tsana Ba Bareke Ki Dinga Tuna Haka Ta Ce Na Rike Ya Katse Wayar To Muwuni Lfya A Wani Bangaren Kuma Farin ciki Yanata Faman Kwatarta Aminci Da Alfarma A Mahaukacin Masoyi Yaugata Da Tankasaheshen Gida A Unguwa Mai Daraja Har A Garki Area I11 **** ******* Lokacinda Cikin Sumoli Yai Wata Takwas Saida Yushau Ya Gwammace Daya Barta Ta Zubar Saboda Azabar Lissafe Lissafe Ga Matsaloli Sunyi Masa Yawa Ga Basussuka Sun Masa Yawa A Wata Juma,a Yana Kasuwa Wajen Kasuwancinsa Aka Doko Masa Waya Daga Ofishin 'yan Sanda Na Unguwarsu Wai Ana Son Ganinsa Hankali A Tashe Ya Tafi Sai Ga Sumayya Tafito Tana Tura Ciki Tun Kafin A Sanar Dashi Dalilin Kawota Yafara Hargagin Nade Tabarmar Kunyarsa Da Hauka Meyasa Aka Kawo Masa Mata Ba Tare Da Saninsa Ba? Ta Inda Yake Fita Bata Nan Yake Shiga Ba Sam Yaki Yarda Da Saurari Bayaninda 'yan Sandan Suke Masa Sai Ma Ya Fice Ya Bar Ofishin Yan Sanda Hargagi Kuje Ku Hadiyeta Babu Abinda Zanyi Kai Karama Zankai Ku Yawuce Yai Tafiyar Sa Kwananta Uku A Rufe Wata Daga Kawayenta Tayi Belinta Ba Dai Wani Abu Ya Kaita Hannun Hukuma Ba Sai Kudin Matar Nan Data Ci Na Ankon Sunan Atika Wanda Ta Kasa Biya A Kofar Gida Taga Motar Yushau Taita Buga Kofar Yaki Budewa Dole Taja Jiki Taje Gidansu Ta Kwashe Komai Tasanar Ma Ummanta Haka Taita Mata Hudubar Banza Da Zagin Yushau Bayan Sallar Magariba Suka Yi Kofa Gidan Tsinke Yana Masallaci Suka Zauna Zaman Jiransa Canwajen Karfe Tara Sai Gashi Yadawo Da Take Away Dinsa A Hannu Yana Ganinsu Yai Turus Kamar Ya Juya Amma Idan Momi Yai Masa Katanga Yashiga Yimata Maraba A Cunkushe Ya Shige Ciki Sunjima A Dakin Sumoli Suna Jiran Yazo Gaishe Da Suruka Amma Babu Shi BaBu Alamunsa Momi Ta Ce Lallai Wannan Takadarin Kansane Tasameshi A Dakinsa Momi Najiranka Fa Tana So Tatafi Waike Don Allah Zaki Barni Kuwa Na Karasa Shekarun danazo Yi Duniya Da Sauran Lfya? Wane Irin Bala'i Ne Tunda Kika Shigo Rayuwata Kin Dagula Ta Gaba Daya Har Nafara Manta wani Abu Waishi Farinciki To Yanzu Dai Kayi Hakuri Kazo Ka Fara Gamawa Da Mominka Ga Dare Yafarayi Kaji Yushau Ya Hayayyako Da Bala'i Toko Abincin Ma Bazanci Bane? Allah Ya Baka Hakuri Bayan Yakammala Ya Karasa Ya Zauna Dab Da Kofa Ko Gaisuwa Ba Bu Ya Ce Gani Ita Kanta Baki Na Rawa Ta Ce Masa Saikuma Kasamu Wanman Mummunan Labari Yai Banza Da Ita Ta Bige Da Bashi Hakuri Saboda Ta Lura Baida Niyyar Amsawa Tagama Surutanta Ta Wuce Tana Fita Yadubi Sumoli Ya Ce Kinsan Allah Sisi Bazan Biya Ba Idan Sungadama Suzo Su Kara Damkeki Ai Bani Na Aikeki Ba Yafice Haka Suka Ci Gaba Da Zaman Doya Da Manja Yushau Fishi Sumoli Kuma Tana Dannewa Tana Ladabi Har Yafara Saukowa Kwatsam Ranannan Yasami Kiran Gaggawa Daga Mahaifinsa Ta Hannun Mubarak Wanda Yazo Har Gida Ya Ce Yatafi Dashi Tunda Yaje Mahaifinnasa Kemasa Wani Irin Kallo Me Alaka Da Tausayi Har Dai Yakare Da Cewa Wai Kai Baka Da Lfyane? Ramarka Fa Tai Yawa Saika Ce Maifama Da Cutar Cida Lfya Lau Alhji Yanayin Rayuwane Kawai To Allah Ya Gyara Dama Nakiraka Ne Naji Inda Aka Haihu A Ragaya Harka Lalace Wajen Cinyewa Mutane Kudadensu Ni Danazaci Nawa Kawai Kakeci Amma Kusan Mutane Biyar Nakawo Min Kararka Akanka Hakadai Yushau Yadinga Kamekame Tsakani Da Allah Yushau Ka Fada Min Gaskiyar Abinda Ke Faruwa Da Rayuwarka Dan Da Dai Ba Haka Kakeba Kokafara Shaye Shayene? Ku Yafemin Alhji Nasan Tabbas Fishinku Na Tasiri A Rayuwata Kuma Sakayyar Abinda Nayi Muku Ne Yasanya Aka Jarrabeni A Cikin Abinda Na Zaba Na Barku Wai Matarka? Alhji Ya Ce Cikin Mamaki To Meye Nata A Kudin Da Mutane Ke Binka? Nandai Ya Kwashe Halin Zamansu Da Ita Yafada Masu Alhji Ya Ce Har Yanzu Banji Hannunta A Kudin Mutane Ba Yushau Inbaka Dauka Ka Bata Ba Aiba Daureka Zata Yi Ta Ce Saika Bayar Zata Sakeka Ba Nandai Yushau Yaimasa Karin Bayani Akanka Alhji Ya Cemasa Yanzu Kenan Kaga Shaidar Cewa Ba Zurfin Ilimi Ne Ke Hana Tarbiyaba? Na Tabbatar Idan Na Rantse Bazanyi Kaffara Ba Duk Cikin 'ya'yan Gidan Nan Ba Bu Wace Zata Iya Haka Agidan Mijinta Sannan Duk Wahalar Dawainiyar Da Zata Duk Dawainiyar Da Zaka Yida Ruma Sikila Ina Da Tabbacin Bazata Wahalar Dakai Kamar Wannan Matar Ba Tun Daga Kunan Zuciya Zuwa Aljihu Duk Na Fahimci Kurena Ina Mai Neman Gafararka Kaida Hajiya Ba Bu Komai Ya Wuce Abu Biyu Ya Burgeni A Alamarinka Hakurinda Kayi Na Kaucewa Yimata Saki Uku Bare Inkayi Sakin Taki Tafiya Ku Fada Halaka Dakuma Yadda Ka Iya Rike Babunka Ba Tare Da Ka Zubarda Kimarka Wajen Roke Roke Ba Yushau Kam Yakara Natsuwa Kuma Kaima Ka Tsarkake Zuciyarka Kayimata Rikon Gaskiya Sannan In Allah Ya Sauketa Lfya Karkai Wa Danta Ko Diyarta Rikon Dakaiwa Hamida Bana Tsammanin Zuciyar Yushau Na Dukan Uku Uku Wallahi Duk Zan Gyara In Allah Yaso Cikin Satinnan Zanje Abuja To yayi Kyau Alhji Yafada A Gajarce Kuma Yatashi Yadauko Cek Ya Hau Signing Yushau Na Kallo Yana Hadiye Yawu Ga Wannan Kadan Toshe Wata Kofar Sauran Basussukan Kuma Ka Barni Zanji Dasu Inji Alhji Farat Daya Yushau Ya Kirga Kudin Dake Cek Din Naira Dubu Dari Biyar Ne Nanfa Yafara Godiya Kuma Na Yafemaka Kanemi Gafara Wajen Mahaifiyarka. . Iyaye kenan, duk wanda ya sabawa umurnin su bazai ga da kyau ba, dunia ma kadai ta isheshi. Allah Ya sa mu gama da iyayen mu lafiya Ya sa albarka a rayuwar mu baki daya. Aamiin, Dan Aunty... GORAN DUMA (P 65) . . Dubu Dari Uku Ya Zaunar A Asusunsa Ya Kwashe Dubu Dari Biyu Ya Doshi Gida Dasu Cike Da Cin Alwashin Indai Kudi Na Siyo Soyayya Da Zaman Lfyar Sumoli Abin Takaici Bai Sameta A Gida Ba Yadinga Tsaki Ya Bude Drwer Ya Watsa Kudi Yafice Ya Bar Gidan Hartadawo Tamai Sannu Da Zuwa Kwana Hudu Suna 'yar Gaba Da Ita Sumoli Tai Halinnata Na Rashin Riko Dake Shima Yaso Hakan Sai Ya Bada Kai Bori Ya Hau Cikin Wannan Satin Sukaje Asibiti Awo Likita Ya Tabbatar Musu Sufara Shirin Amsar Bako A Hanyar Su Ta Dawowa Yayi Mamakin Da Batafara Yimasa Lissafin Abinda Za A Kashe Ba Yafara Hamdala Shiriya Tazo Mata Kamar Yanda Shima Yazo Mata Kwamfa! Cike Da Tsananin Mamaki Da Sanyin Jiki Yagama Hargitse Dukkan Maajiyar Kudinsa Bai Tarar Da Dubu Dari Biyun Daya Ajiye Ba Yanemi Guri Dirshan A Falo Ya Zauna Yana Faman Hada Gumi Yana Tunanin Yadda Kudinnan Suka Yi Tsuntsuwa Suka Tashi Dole ya Kira Sumoli Ya Tambayeta Kudindana Ajiye A Drawer Dakina Nake Nema Sumoli Ta Yatsina Fuska Wanne Irin Kudi Ya Cemata Banason Tambayar Raini, Naira Dubu Dari Biyu Ne Kudin Eye!Amma Dai Da Mamaki Yushau Ko Mafarki Kake? A,a A Sume Nake Haka Sukadinga Casa Bala'i Har Na Kwana Biyar Cur Kamar Su Kashe Kansu Ranar Kwana Na Biyar Dinne Yana Shirin Fita Sallar Azahar Aka Dinga Murza Kararrawar Gidan Can Sai Ga Sumoli Tana Takawa Da Kyar Fuskarta Akumbure Saboda Kuka Ta Cemasa Don Allah Ka Bude Momina Ceta Zo Meta zoyi? Ni Nai Mata Waya Na Sanar Da Ita Komai In Ma Biyan Kudin Ne Nasan Zata Biyaka Tunda Kace Ni Na Dauka Tsinanniya Kawai A Firgice Sumoli Ta Ce Wa! Niko Ita? Yakawar Dakai Rai A Bace Oho Miki Yamike Yazari Key Yana Budewa Momi Kofar Ko Kallonta Baiyi Ba Yajuya Ciki Abinsa Can Sumoli Tazo Waikazo Inji Momi,babu Indazani Ku Gama Kintsa Gulmarku In Ma Miko Min Kudina Zatayi Sannan Tatafi Dake Inajira Har Sumoli Zata Tanka Da Tsiwa Tana Tuna Marin daya Zabga Mata Shekaran Jiya Saita Hadiye Can jimawa Yai Alwala Kamar Mai Zuwa Masallaci Yafita Amma Saiyadawo Ya Labe Musu Muryar Momi Yafara Jiyowa Ai Duk Laifinkine Ummi Tunda Kin San Wutar Cikin Mijinki. Ni Dakinyi Shawara Dani Tun Lokacinda Kika Dau Kudin Dakinzo Munje Wajen Malam Ya Kulle Bakin Ja"iri Naje Fa Tun Kwana Daya Da Daukar Kudin Malam Ya Cemin Indai Yushau Zai Iya Tunawa Da Kudin Nan Tozai Tuna Ranar Da Aka Haifeshi Kema Momi Kin Manta Taurin Kan Mugun Mutumin Nan Ne Kawai Asirin Muke Kamar A Bayan Farcensa Yake Makalewa Mts! Aikin Banza Yo Dole Saita Hanyar Asiri Za Aci Kudinsa? Banda Ma Dai Ke Sokuwace Doluwa Kawai In Nice Ina Ganin Wura Wura Zai Gane Na Taba Kudin Ba Sai In Kunna Masa Gobara Ba Ya Isa Ya Ce Kudin Wutar Bazata Kone Suba,wallahi Danasani Hakan Nai Masa Akalla Da Baitashi Hankalina Yanzuba Yushau Yadinga Hirji A Zuci Ciki Tashin Hankali A Iyakar Zace Zacensa Baita Ba Zaton Taurin Kan Sumoli Yakai Haka Ba **** ***** Doctor Aiki Yasha Kaina Ban Sami Rako Matata Ganinka Ba Nazifi Ke Fadawa Likita A Waya Hakane Batafi Minti Goma Sha Biyar Da Barin Asibitinnanba Ya Cemasa Ammafa Kusan Sati Biyar Kenan Tanafama Da Yawan Laulayi Ai Satindaya Wuce Da Mukazo Ma Na Sanar Daka, To Gaskiya Har Yanzu Ba Bu Sauki Jiya Cikin Darema Saida Ta Kwara Amai Shima Likitan Cike Da Doki Ya Amsa Waida Bari Nayi Tafara Baka Albishir Naga Kamar Taso Haka Wane Albishir? Tana Dauke Da Juna Biyu Na Sama Da Sati Shidda A Firgice Nazifi Ya Ce Kace Me? Da Gaske? Dariya Kawai Likita Yake Yana Jin Nazifi Na Sumbatu Har Daga Karshe Wayar Ta Katse Kwana Biyu Nazifi Na Hadiye Murna Da Farin cikinsa Yanajiran Ruma Ta Bashi Albishir Dinda Kanta Kamar Yadda Likita Ya Gayamasa Amma Ta Share A Kwana Na Uku Yakasa Daurewa Yadawo Da Wuri Ya Ce Mata Na Fiye Sonkifa Da Kalmominda Yajanyo Bakin Zarenta Kenan Ni Mahaka Tare Da Tsura Masa Ido Ban Yarda Ta Zarce Da Dariya BaBu Kyau Rainuwa Fa Babu Kyau Nazifi Ya Kauda Kai Tasha Jinin Jikinta Tajuyo Da Kafadarsa Meyai Zafi Ido Zaici Wuta? Fadamin Laifi Nayiko? Nasani Baka Cancanci Laifiba,ina Neman Afuwa tun Kafin Katuna Min Laifin Yai Murmushi Ainazaci Ninai Laifin Ake Hukuntani Da Boyemin Abinda Yakamata Nasani Tashi Ga Cikin Dimuwa Menake Boyemaka? Ko Menene Banyi Da Gayya вa,a, "Da Gaske?" Aiko Da Mamaki Ace Bakida Dalilin Sanar Dani Kina Da Ciki Har Sai Likita Daga Waje Yafadamin Nandanan Tai Fuska Oh!Wallahi Nazaci Kasani Nasani? A Ina Zansani? Ta Dubeshi Ido Cikin Ido Aina Kake Sanin Abubuwan Danake Yi Lokacinda Bamatare? Yadanyi Kasake Saikuma Yamike Cikin Kuzari Yana Kai Komo A Falon Itakuma Tai Tagumi Kawai Tana Kallonsa Da Sauri Ya Nunata Da Yatsa Wannane Dalilinda Yasa Kika Boyemin Kina Da Ciki? Bare Har Na Rubanya Miki Tattalina Kukasance Cikin Koshin Lfya Keda Bebin? Cikin Dakewa Ta Kada Masa Kai Yajima Yana Kallanta Fuskarsa Ba Yabo Ba Fallasa Yanufi Daki Yana Cewa Ina Zuwa Ta Bishi Da Kallo Cikin Fargaba Tana Hasashen Abinda Zaiyi *** **** *** Yana Dogare Da Kofar Dakin Yawatsa Wa Somoli Takarda Yana Huci Idonsa Akan Mominta Ya Ce Ina Fata Zaku Hada Kare Yanzu Kubarmin Gida A Tafi A Babbakamin Gidan Wani Nidai Allah Ya Kubutar Danawa Dan haka Kudin Da Kuka Dauka Saiku Yi Hidimar Haihuwar Dasu Dama Abinda Zanyi Dasu Kenan Ya Fice Abinsa Cikin razana Musamman Da Suka Ga Saki Uku Momi Ta Dora Mayafi Aka Jikinta Sai Karkarwa Yake Kinga Kwantar Da Hankalinki Kiyi Zamanki Zanje In Sami Boka Tafice A Gaggauce Tabar Sumoli Cikin Mawuyacin Hali Da Nadama Kaitsaye Yushau Gidansu Ya Zarce Ya Kwashe Komai Yagayawa Hajiyarsa Dukda Cewa Ta Razana Dajin Hakan Ta Ce Kaikuma Haka Allah Ya Jarrabeka Da Sakin Mata Kuma Da Ciki Musamman Ma Wadda Take Gargarar Haihuwa ? Cike Damamaki Yake Kallonta Kodayake Mai Daki Shiyasan Inda Yakemasa Yoyo Amma Sumayya Ko Cikin 'yan Dari Take Dashi Ya Cancanta Yaimata Saki Uku Karfe Sha Biyun Dare Yakoma Gidansa Idonsa Akan Dakin Sumoli Yaga Alamar Tanan Cikin Tafasar Zuciya Yanufi Dakin Yakwankwasa Babu Jimawa Ta Zo Ta Bude Kofar Yajima Yanamata Kallon Mamaki Ke Kinsan Allah? Ko Kwalam Ta Koki Ce Ta Kawoki Duniya Saikin Bar Gidannan!Wallahi Sai Kinbar Shi Zama Dakena Haramtawa Kai Har Abada Saboda Haka Nayi Miki Alfarmar Safiya Ki Hada Tsiyarki Kifita Daga Rayuwata Jafa'inki Yafi Karfina Sumoli Ta Daga Kafa Da Kyar A Kokarinta Na Komawa Dakι Sakamakon Wani Matsanancin Ciwon Ciki Dataji Ya Soketa Lokacinda Yushau Ya Bar Gurin Wasa Wasa Ya Zarce Ciwon Mara Batasan Sanda Ta Rarrafa Kofar Dakin Yushau Ba Tana Bugawa Yushau Yadinga Tsaki Yana Juyi A Gado Yanajin Nishin Sumoli Har Na Tsawon Fiye Da Minti Ashirin Yana Kwance Sai Nasihar Mahaifinsa Ta Fado Masa Ka Kyautatawa Kanka Ta Hanyar Bin Umarnin Ubangijinka Bisa Kyautata Mu,amala Tsakaninka Da Matan Daka saki Hakanyasa Ya Fito Kilama Haihuwa Ce Amma Me? Yana Bude Kofar Yaci Karo Da Ita Kwance Cikin Jini Da Alama Ta Mutu! *** ***** Idon Ruma Nakan Hanya Nazifi Yafito Dakin Hannunsa Dauke Da Wayoyi Biyu Yazauna Kusa Da Ita Ta Fahimci Wayartace Da Tasa Wayar Cikin Dukan Zuciya Daitake Binsa Da Kallo Tana Canki Cankar Meyake Nufi Iyakar Zamanta Dashi Bata Taba Ganin Wayarta A Hannunsa Ba Yadago Wayarta Yana Karemata Kallo A Hankali Ya Ce BB PORSCHE Ya Dago Ya Dubeta A Ina Kika Sai Wayar Nan? A Rude Take Ta Ce Milkyway Mana Ai Tunda Kuka Tsafeni Ko katin Waya In ba na Can ba Sai Inga Bashi Da Auki... ᴬˢᴹᵞᴳᵞᴳᴳ Dan Aunty GORAN DUMA (P 66) . . Nawa Kika Siya Ina Tsammanin Ko Dubu Tamanin Ne Ko Saba'in Ne Mts Na Manta Dai Zaki Iya Tuna Ranar Dakika Sai Wayar? Ban Mance Ranar Dana Siya Ba Ranar Sha Biyar Ga Watan Nuwambar Shekarar Dubu Biyu Da Sha Biyune Na Rike Ranarne Lokacindana Shiga Tarkonka Na Bincika Kuma Na Tarar Kaine Nazifin Dana Fara Haduwa Dakai Ranar Danaje Siyen Wayar Kinsan Gaskiyar Kudin Wayarnan? Ta Zuramasa Ido Tana Dawani Farashine Bayan Wanda Na Siya? Kudin Wannan Wayar Yana Kamawa Daga Dubu Dari Uku Zuwa Sama,ruma Ta Saki Baki Kawai Tana Kallonsa Har Tsawon Dayagama Danne Dannensa A Wayar Ya Dago Suka Hada Ido Yasakar Mata Murmushi Itakuma Ta Basar Ta Kawar Dakai Amma Yasanya Ta Dawo Dakan Ta Dubeshi Lokacinda Ya Cemata Inasonki Rumasai Muryarta Na Sarkewa Ta Ce Game Din Bai Kare Ba Kenan? Yadan Kai Mata Dukan Wasa Cikin Raha Wato Game ne? Kai Ka Kirashi Da Haka Ta Fada Yanisa Hakane Ubangiji Mai Cewa Kasance Kuma Ya Kasance Shi Yajefamin Kaunarki Farat Daya A Ganin Farko Danayi Miki A Harabar Milkyway Ranar Sha Biyar Ga Watan, Nasan Zaki Tuna Yadda Naso Nuna Kaina A Wajenki Kika Ki Bani Hadinkai Inda Har Na Kai Ga Yimiki Karya Na Karanta Jarida A Jami'ar Bayero Na Kuma Dace Na Fada Daidai Alhalin Ban Taba Karatu A Kanoba Ta Daga Masa Hannu Alamar Jinjina Tana Murmushi Daga Nan Saime? Yakama Hannunta Yahada Da Nasa Shirine Ni Da Masud Wato Manajana A Karbi Wayarki Da Zummar Za A Sanya Miki Credit Anan Muka Dauki Lambobin Wayarki Ta Zaro Ido Cikin Mamaki Eye!Ai Tukunna Ya Fada Yana Dariya Ta Sauke Ajiyar Zuciya Sannan Ta Zame Hannunta Daga Nasa Ta Mayar Da Tagumi To Cigaba Yakarbi Wayarta Yana Dubawa Wannan Wayartaki Ko Sati Daya Banyi Da Mallakarta Ba Na Siye Ta A Japan Sannan Wani Abokin Karatuna Kuma Kwararre A Fannin Kerekere Yayi Aikin Sanya Mata Wata Software Mai Suna "droid Air Ya Ajiye Wayar Tata Sannan Ya Dauko Tasa Ya Shiga Matso Hotuna Kana Ya Ci Gaba Kinsan Ko Wacce BB Tana Da Blackberry Id Wannan Ne Yake Bayar Da Damarko Ansace Ta Ake Iya Ganota Ta Wannan Hanyar Kuma Ana Iya Ganin Abinda Ke Gudana A Wayar Kamar Aikawa Da Sakonni Kira Da Shiga Internet a Sannan Kuma Ana Iya Gane Inda Take Ruma Tadinga Kallon Wayar Cike Da Doki Bayan Haka Ita Wannan BB Porsche Din Tana Iya Daukar Hoto Mai Ita Ta Tura Wani Guri Daban Idan An Saita Ta Yamika Mata Daftarin Wasu Hotuna Daya Budo A Wayar Sa Hannunta Na Karkarwa Ta Karba Cikin Baza Ido Dantun Kafin Wayar Tazo Hannunta Ta Gane Hotunanta Ne Cikin Rawar Ido Da Jiki Tafara Duban Hotunan Daya Bayan Daya A Abujane A Kano Ne A Motane A Rano Ne A Kan Dutsene Gasunandai Dayawa Yamiko Hannu Ta Bashi Wayar Amma Takasa Kawai Sai Ta Dago Ta Zuba Masa Ido Numfashinta Na Bugawa Da Sauri Da Sauri Ya Boye Damuwar Rikitar Yaci Gaba Dayimata Bayani Waccan Software Da Abokina Yasanya Min Ana Samunta Ne A Irin Wannan Android Din Yanuna Mata Wayar Sa Dake Hannunta Idan Aka Saita Wayoyi Biyu Masu Wannan Software Duk Nisan Dake Tsakaninmu Ko Da Inanan Nigeria Kina China Zaniya Sarrafa Wayarki Yaddanaso,zaniy a Gano Indakike Zaniya Daukar Hoto Zaniya Nado Sauti Zan iya Shiga Mesgs Dinki Hakadai Ya Ci Gaba Da Nunamata Ita Kuma Taita Godiya Ga Allah Dayasanya Bawani Abin Asshan Take Aikatawa Ba A Boye Lokacin da Kike Tsaye A Harabar Milkyway Muna Tsaye Nida Masud Muna Kallonki Tare Da Kulla Yadda Zamu Bullowa Lamarinki Har Lokacinda Kawarki Ta Shigo Kuka Shigo Tare Kawai Sai Ga Sani Ya Rugo Fadamana Ai Ipad Kikazo Siya To Anan Ne Ba Tare Da Dogon Nazari Ba Masud Ya Kawo Shawarar A Siyar Miki Da Wannan Wayar Ruma Ta Rasa Bakin Magana Sai Kallonsa Kawai Take Babu Kiftawa Cikin dariya Ya Hura Mata Iska Ta Wadannan Hanyoyin Nai Tracking Din Ayyukanki Ta Haka Nasan Ke 'yar Jarida Ce Har Nagano Jaridardakike Da Wa Aiki Wanda Hakan Ya Saukakamin Gano Muhallinki Ta Haka Nasanke Sikila Ce Ta Haka Nasankin Taba Aure Har Nasanwa Kika Aura Nasan Kintaba Son Wani Auwal Amma Ya Rasu Nasan Ranar Birthday Dinki Saidai Nasan Ki Da Kyau Daga Nanan Gidanku Abuja Har Mazauninki Na Kano Kafin Nan Tunda Nasan Ke Sikila Ce Na Shiga Neman Sani Akan Sikle Cell Naziyarci Kwararren Likitan Da Ya Shawarceni Tare Da Gwaje Gwajen Har Na Dace Da Cewa Zan Iya Aurenki 'ya'yanmu Su Tsira Saida Duk Na Gama Danan Sannan Na Dauki Hanyar Kano Dan Haduwa Dake Nana Kum Nayi Katarin Haduwa Da Sani A Matsayinsa Na Abokin Abokina Shi Kenan Yaimin Tsanin Haduwa Da Alhji Wadda Nan Ma Na Sake Katarin Ashe Yasan Mahaifina Wannan Katarin Ma Yakara Saukaka Min Samin Aurenki Musamman Ta Bangaren Mahaifiyata Waddata Kyamaci In Auri Bazawara Amma Mahaifina Na Jero Mata Lissafin Daga Gidan Dakika Fito Saita Saki Ya Tayar Da Kallo Akanta Cikin Dage Gira Wannan A Takaice Kenan Kin Gamsu? Jiki A Sanyaye Da Kuzarin Karfin Hali Ta Girgiza Kai Sannan Ta Shiga Cikin Wayarta Ranar Sha Daya Ga Watan Sha Biyune Naje Abuja Dan Tsira Daga Basajarka Ta Kano Nakuma Zarce Milkyway Da Zummar Tura Wasu Ayyuka Ta Yanar Gizo Tunda Na Sauka Abuja Na Fahimci Mutane Na Binada Kallo Haka Ma A Milkyway Din Kowa Yasamin Ido Miyasa? Mutanen Gari Dake Kallonki Tsarguwa Kawai Kikayi Jama,ar Milkyway Kuwa Duk Sunsan Da Zamanki A Zuciyata Harma Masud Ya Basu Umarni Duk Lokacinda Suka Ganki Su Sanar Masa Ta Kada Kai Alamar Nuna Gamsuwa Sannan Tajefo Wata Tambayar Yaya Akai Kasan Zanyi Rubutu Akan 'yan Maye Ko Zuwana Gidan Hafsa? Na Nadi Sautinku Lokacinda Kuke Hira A Mota Da Mubarak Tare Da Abokinsa Haka Zalika Na Nadi Sautin Farkon Hirarku Da Hafsat Ruma Tajima Cikin Kada Kai Da Tunani Sannan Ta Furzar Anji Amma Tayaya Kake Gane Abubuwan Da Nake Rayawa A Zuciyata? Cikin Zaro Ido Ya Ce Kai Haba!Saika Ce Wani Maye? Sukayi Dariya Su Duka Sannan Tazarce Da Magana Misali Ranar 16th Ga Watan Biyu Dubu Biyu Da Sha Uku 16-2-2013 Ranar Naje Rogo Kuma Na Hau Dutse Sakonka Na Daidai Lokacin Tamkar Kalubalanta Ne Ga Radadin Da Zuciyata Take Dalilin Hasashen Da Kaicon Daya cikata Tana Sauke Numfashi Ya Amsa Mata Idan Ina Son Abu Ko Wane Irine Ina Da Juriyar Nunawa Allah Shi Na Tsananta Addua Akanki Fiye Da Yadda Kike Tsammani A Tsawon Dararena Dan Haka Karkiyi Mamaki Idan Na Dinga Aikin Da Zai Dinga Dacewa Da Abinda Uwar Dakin Zuciyarki Ke Kimsawa Abuna Gaba Kuma Daya Kamata Kituna Digirina Na Farko Halayyar Dan Adam Na Karanta Babu Laifi Ina Iya Karantar Mutane A Yayin Furucinsu Ko Kallonsu Lokacinda Suke Wani Aiki Kamar Dai Yadda Na Kalli Fuskarki Akan Dutse Sanin Kankine Duk Wanda Zai Nufi Daji Ya Kurawa Horizon Ido Cikin Aihini Tabbas Sai An Tarar Yana Jinjinawa Makagin Sammai Da Kassai In Kuma Zai Zurfafa Tunaninsa Sai Ya Dangana Da Mutuwa Ruma Ta Sake Rafka Tagumi Tana Kallonsa Cikin Murmushi Can Ta Sauke Wata Wawuyar Ajiyar Zuciya Wato Abinda Kaimin Kenan,? Kwarai Da Gaske Kyautatawa Nayi Ko Laifi? . Idan an samu isashshen commnts zamuyi post din karshe anjima.... . Dan Aunty GORAN DUMA KARSHE... NA MAIMUNA BELI TARE DA ABBAS ABDULKADIR HADA HADA . . Eh To Uhum Ka Kyauta Din Kenan Kila Ba Dan Kayi Haka Bada Yanzu Bansami Maijin Kaina Nida 'ya'yana Ba Cike Dajin Dadi Yace Ko Banyi Haka Ba Dole Zamu Hadu Allah Ya Hukunto Tuni Cewa Sai Mun Auri Juna Saboda Haka Dole Mu Hadu In Baki Wannan Bebin Tare Da Kannensa Masu Zuwa Ya Shafi Mararta Ko? Tafada Cikin Kunya Da Dariya Toke Yaya Kika Gani? Yatareta Cikin Dole Dan Karta Ci Gaba Da Sharewa Takada Kai Hakane Yadanyi Shuru Zuwa Wani Lokaci Sannan Ya Ce Idan Nasami Lokaci Mai Kyau Zan, Samu In Wargaza Saitin. Ya ShiGa Duban Agogo Sannan Yasake Dubanta Lokacinkine Yanzu Kin Kuma Cinye Shi Da Tuhume- Tuhume Karka Damu Duk A Ni Din Ne Yakura Mata Ido Har Saidata Tsargu Tanemi Baasi Da Ido Ya Ce Wai Da Gaske Zaki Haifo Min Ya'yan Dazasu Janyo Na Kara Sonki? Kuma Nima Idan Na Haifo 'ya'yan Nasan Tawa Zuciyar Zata Iya Tarar Da taka Zuciyar Wadda Ta Shahara A Sona Ya Kame Kafadarta Da Sauri Tokice In Kara Murna Haihuwarki Nafada Ka Kara Murnar Suka Tuntsire Da Dariya Su Duka ********* *** Duk Da Yushau Ya Yanke Kaunar Kawai Sumoli Ta Mutu Bai Kasa Kwasarta Cikin Tashin Hankali Yanufi Asibiti Ba Ananne Aka Tabbatar Masa Da Bukatar Jini Bayan Ta Farko Daga Dogon Sumanta Lokacin Dake Gwada Jininsa Dan Neman Dacewa Da Nata Saida Ya Kawar Dakai Cikin Hawaye Ga Ruma Can Wadda Ta Cancanci A Bata Abinda Yafijini Tana Can Tana Rayuwa Da Jininsa Amma Ba A Matsayinsa Ba Wannan Asarar Da Kyar Zai Iya Mayar Da Gurbinta Jinin Sumoline Ya Hau Abinda Ya Sabbaba Mata Barin Jini Kenan Ta Galabaita sosai, Aka Fara Yimata Karin Jini Da Jiran Cikar Waadi Da Idan Bata Haihu Ba Sai Ayimata Aiki Cikin Ikon Allah Kafin Sfya Ta Haifi Santalelen Danta Namiji Bayan Yai Waya Gidansu Ya Sanar Da Hajiyar Su Haihuwar Saiya Mikawa Sumoli Wayar Wadda Ke Kashangare Tana Kallansa Bakin Cikin Sakin Dayai Mata Ya Hanata Farin Cikin Karuwar Data Samu Ungo Ki Kira Mutanen Gidanku Ki Sanar Dasu Kin Haihu Kai Bazaka Sanar Dasuba? Ta Tambaya Ya Kawar Dakai Yana Kara Bata Rai Idan Kina So Su Sani Kawai Ki Sanar Dasu Kaitsaye Ta Amsa Cikin Kuramasa Ido To Banaso Su Sani Dan Allah Ka Daukeni Mu Koma Gida Na Rantse Zan Rayu Dakai Kai Kadai Batare Da Kowa Ba Kuma Nai Alkawari Zanzame Maka Zallar Farinciki Har Mutuwa Ya Gwasaleta Ya Ce Allah Sarki Bakin Alkalami Aiya Bushe Sukai Shuru Har Tsawon Wani Lokaci Saida Sumoli Ta Ga Babu Sarki Sai Allah Sannan Taiwa Mominta Waya Ta Sanarmata Yushau Na Harabar Asibitin Mahaifan Sumoli Sukazo Tare Dawasu Yayyenta Yana Sane Ya Boye Musu Suka Shige Har Saida Yagano Nasa Mahaifin Sannan Yataro Su, Tunkafin Su Shiga Dakin Suke Jiyo Bambamin Fadan Mahaifin Sumayya Wanda Ya Saci Jin Hirar Anyiwa Sumayya Saki Uku A Dalilin Satar Kudi Tsakanin Momin Da Yayyenta Masifar Dayake Batawasa Ba Ce Yana Nuna Tsananin Bakincikinsa Da Auren Momi Wadda Ta Tarwatsa Masa Rayuwar 'ya'ya Yanzu Zawarawanta Hudu A Gaba Allah Ya Kubutardani Abinda Yushau Ke Maimaitawa Cikin Ransa Kenan Ganin Su Yasanya Mahaifin Sumoli Yin Shuru Saida Aka Gaggaisa Tare Dayiwa Juna Barka Sannan Mahaifin Sumoli Yanemi Komawa Fadansa Alhjin Yushau Yatareshi Ai Alhji Duk Hakuri Za Ai Kai Yushau Daure Ka Mayar Da Matarka Cike Da Karsashi Yushau Ya Ce Ai Saki Uku Ne Alhji Kayi Wauta Yushau Alhji Yadinga Maimaita Cikin Alhini Yushau Kuma Yai Sagare Yana Kallan Alhji Sannan Ya Dubi Sumoli Wannan Kadai Yaisa Tabbatar Da Nufinsa Na Sumoli Tafi Karfin Hakuri Duniya Mahada Duniya Maraba Inji Wani Mawaki Anan Dangi Biyu Suka Hakurkurtar Da Juna Tare Da Alkawarin Kin Yasar Da Zumunci Daganan Kowa Ya Kwashi Nasa Iyalin Akai Gida Dukda Yushau Yadinga yi yana Ta Satar Kallon Dansa A Goye Bayan Sumoli Zuciyar Sa Cike Da Dokin Ya Cika Shekaru Biyu Ya Dauko Abinsa Ba Tare Daya Tashi Gidan Da Ake Rowar Tarbiya Ba. Wani Lokaci Ciwon Ruma Yatashi Yadda Take Murkususun Ciwo Cikin Kuka Haka Nazifi Ke Murkususun Ciwon Zuciyar Tausayinta Cikin Hawaye Sai Bayan Allura Tafara Ratsa Ta Harta Sami Bacci Sannan Ya Kwashi Sanyayyar Gwiwarsa Ya Bar Dakin Da Aka Kwantar Da Ita Ya Cimma Likita A Ofishinsa Likita Wane Aikine Ka Ce Ana Yiwa Sikila A Rabasu Da Ciwon? Likita Wane Aikine Kace Anayiwa Sikila A Rabasu Da Ciwon? Likita Yadan Dubeshi A Razane Baki Na Rawa Ya Amsa "'Bone Marrow Transplant"" Wato Dashen Bargo Kasancewar Ciwon A Ainihin Jininsune Kuma Bargo Ke Samar Dajini Dan Haka Saidai A Canja Shi Da Wanda Zai Samar Dajini Mara Wannan Kantararrun Sel Din To Ina So Ayi Wa Matata Likita Ya Dubi Nazifi Da Kyau Saiya gane Sam Ba Cikin Hayyacinsa Ma Yakeba Saboda Haka Ya Bar Kujerarsa Yadawo Kusa Dashi Yadinga Rarrashinsa Tsawon Lokaci Har Ya Fahimta, " Ka Manta Ne?" Amma Tun Zaman Farko Damukayi Na Sanar Dakai Cewa A Nigeria Ba A Taba Wannan Aikinba Sai A Kasashen Turai Acandin Ma Saiwane Da Wane Akewa Saboda Yana Lasar Miliyoyin Kudi Nazifi Ya Katsi Numfashinsa Nawane Kudin Farashin Yana Canzawa Daga Wannan Kasa Zuwa Wannan Amma Dai Yana Lasar Makudan Daloli Likita Ya Amsa Nazifi Yamike Dafe Dakai Yana Ambatan Innalillahi Wa Inna Ilaihirajiun Sannan Yanuna Alamun Fadawa Tunani Mai Nuna Kwantar Da Hankali Yadinga Safa Da Marwa A Ofishin Cikin Dukan Zuciya Likita Na Kallansa Cike Da Tausayi Sai Can Yaga Nazifi Ya Daga Hannaye Sama Cikin Hawaye Fuskar Sa A Sakeya Ce Ya Ubangiji Ina Rokonka Da Iliminka Nashaida Kaine Ubangiji BaBu Wani Bayan Kai Makadaici Wanda Bai Haifa Ba Kuma Ba A Haifeshi Ba Ubangiji Kaika Ce Duk Wanda Yarokeka Zaka Amsa Masa Ina Rokonka Ka Hore Min Halak Dinda Zan Biya Kudaden Daza Aiwa Matata Ruma Da 'yarta Hamida Aiki Sannan Ka Saukaka Musu Su Da Sauran Sikila Irinsu Tare Da Dukkan Marasa Lfya Allah Ka Sanya Wannan Ciwon Yaimusu sauki, Kasa Yai Sanadin Shi Ga Aljanna In Har Sun Bayar Da Gaskiya Dakai Kuma Ka Bawa Jagororinsu Juriyar Kula Dasu Amin Likitaketa Faman Amsa Masa Cike Da Jintausayi Yana Kallan Nazifi Wanda Ya Goge Kwalla Sannan Ya Juyo Yai Masa Murmushi Yana Daga Masa Hannu Har Yafice Likita Yakoma Mazauninsa Jiki A Sanyaye Cike Dajin Wani Irin Kaye A Zuci Dama Dai Duk Sikila Suna Samun Irin Wannan Gatan Daga Mazaje Ko Iyayensu Dama Hakan Takasance Rayuwa Yacigaba Da Wanzuwa Cike Dajin Dadi Da Kulawar Nazifi Har Allah Ya Sauki Ruma Lfya Tasamu Danta Kyakyawa Maikama Da Ubansa Cike Da Koshin Lfya Batare Da Sikila Ajikinsaba Inda Suka samasa Sunan Mahaifin Yushau Sunakiransa Da Irfan Dan Ruma Tana Alfahari Da Alhji Yajajirce Kwarai Akanta Da Lfyarta Wanda Tai Amanna Koda Mahaifantane Iyakar Abinda Zasui Matakenan. . ALHAMDULILLAH KARSHE Marubucia MAIMUNA IDRIS SANI BELI. . Naso ace an iso wajen da Ruma zata samu lapia , ace koda a cikin dangi ne an hada kudin da za a mata aiki da erta Hamida, ciwon bashi da dadi ko kadan, nasan ciwon, shine sanadin tafiyar kanwata mai bina, yanzu haka karamin kani na yana dauke da kwayan ciwon. Likitoci sun tabbatar ba cuta bace, halittace abun kamar yadda kuka ji a cikin littapin, mace da na miji su suke haipar da irin kwayar cutar a jikin d'an da zasu haipa. Shi yasa yanzu likitoci suke bada shawaran kowa yasan Genotype din sa, tun kapin soyayyar ku tayi nisa kusan makomar ku, ammana kuskure ne sai ana saura kwana 3 aure aje gwajin genotype, da dama basa barin auren su koda an same su da duka A.S , suna duba soyayyar dake tsakanin su alhali basu san illar ciwon ba, a cikin littapin nan kadan aka ambata muku game da illar ciwon , ga wanda suka sani sun sani, ciwon kaman iska, yanzu-yanzu zaku zauna da mutun lapia anjima kadan ya birkice babu lapia. A binciken da akayi a dunia a Nigeria tapi yawan masu dauke da ciwon sikila, kuma arewacin Nigeria ne, saboda ba'a gwaji yayin aure shi yasa muka pi kowa dauke da masu shi ciwon, kwanaki nagani a jarida wasu en mata da aka musu dashen bargo tun suna yara, a lokacin an musu dashen bargon ne ko wacce kimanin 26m a Austrilia, A yanzu kuma kudin ya kama kimanin 100m (Miliyon dari,) a kudancin Nigeria ma wai an para, anyiwa mutun 6 an samu nasaran mutun biyu, lititocin sunce idan ana son abun ya daure dole sai gwamnati ta shiga ciki ta bada nata gudumowar da tura likitoci kara ilimi da kayan aiki. . dan Allah ina kira ga samarin gidan nan da en mata da ku ziyarci asibiti domin a muku gwajin wannan GENOTYPE din saboda koma yasan makomar sa. Ina ganin yadda mahaipiya ta take pama da ciwon, tayi jinyar kanwata, ta rasu 2015, tun tana wata 8 ake pama da jinyarta, san da takai shekara 15 ta rasu, yanzu ma haka ga kanina ana pama da jinyar sa shima tun aihuwar sa, shi da zapin ciwo yana kuka mahaipiya da hawaye.... Kusan kullun haka suke shi da ita idan ciwon ya tashi babu bacci a idon su, haka zasu ini haka zasu kwana. Mahaipiyata kullun tana hanyar asibiti tare dashi.... Ciwon babu dadi ko kadan. Ina mai Addu'ar Allah ya sawaka wa masu pama da cuta komin kankantarta Ya basu lapia Ya yaye musu, mu kuma da muke da lapia Allah Ya kara mana lapia mai albarka. Aamiin . Dan Aunty... Angon Hamida.. Ehem..