[02/11 7:27 AM] My 2nd Mtn: A *FIKRA WRITERS ASSOCIATION* *5/2/2019* *Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah SWT da Ya bani damar fara rubuta wannan labari. Ina addu’a Allah Yasa yadda na fara lafiya na gama lafiya kuma ni daku mu amfani da abinda ya kunsa. Kuskuren da yake ciki kuma ALLAH Ya yafe min. Amin* *HAKKIN MALLAKA* ©Batul Mamman *Wannan labari da duka abinda ya kunsa mallakar BATUL MAMMAN ne. Ban yarda wani ko wata ya juya min ko da shafi daya ne batare da izini ba. Sannan ban yarda a yada min wannan labari ta kowace siga ba ta kafofin sa da zumunta, bugawa ko karantawa. Sabawa hakan zai janyo daukar mataki akan duk wanda aka samu da laifin. Nagode.* *FARKON FARI* *1992* Gidan Mal Ali Gidado babban gida ne a cikin karamar hukumar Sumaila dake Kano. Attajiri ne wanda Allah Ya azurta da dabbobi masu tarin yawa. Garken shanu, tumaki da awakinsa bazasu kirgu ba saboda yawansu. Wata katuwar gona ya samu a can bayan gari ya zubesu yana kula da kayansa da taimakon mutane kalilan saboda bazai juri biyan da yawa ba. Bafillatani ne na usuli dan siriri ba kiba ko kadan amma kallo daya zai tabbatar maka an zuba kyau zamanin kuruciya. Mutan gari da iyalinsa suna kiransa Malamijo. Duk tarin arzikin Malamijo kusan kowa ya sanshi a matsayin rikakken mai mako da bakar rowa. Kudinsa basa tabuwa indai ba aure ya tashi yi ba. To a nan fa yarinya da iyayenta zasu ci su tada kai. Idan anyi auren ma amarya ita ce tauraruwa taci mai kyau tasha mai kyau. Gidan gabadaya hannunta sai dawo har zuwa lokacin da Malamijo zai gaji da ita ko tayi ciki. Daga nan fa ita da babu duk daya don gwani ne wurin wulakanta mata da cin zarafinsu saboda shima ya sani kudinsa suke aure. Malamijo ko suturar kirki baya sakawa saboda kada ya kashe kudinsa. Sau tari zaka ganshi cikin kodaddun kaya yana yawo don bai taba yarda yayi dinki daidai jikinsa ba saboda gudun raini. A halin yanzu ‘ya’yansa goma sha biyar amma shida ne kadai da iyayensu mata a cikin gidan. Sauran taran basu da gata suna ga Allah suna ga Yadikko mata ta biyu a jerin aure auren Malamijo wadda har yau ya kasa sakinta saboda mace ce da ta gagare shi juyawa. Bata taba haihuwa ba kuma nata mahaifin ma da arzikinsa lokacin da akayi aurensu. Duk da haka dai auren nasu yana da tsahon rai domin kuwa duka ‘ya’yan Malamijo akan idonta aka haifesu. Idan ya saki uwar yaran tana kokari matuka wurin kulawa dasu sai dai rashin wadatasu da yake yi yasa itama abubuwan sai a hankali. Yaran da suka ci sa’a suma sun taso da nasu iyayen a gidan to duk abinda aka kawo wawaso ake dasawa mai uwa a gindin murhu ya tsira da abin arziki. Wanda babu tasa kuma ya koma gefe yasha kallo. Duk bakin hali na Malamijo yaransa sun tsira da abu daya wato ilimi na zamani da na arabiya. Wannan ludufi da suka samu ya samo asali ne daga shawarar da abokinsa da suke kai dabbobi kudu tare ya bashi na cewa idan sunyi karatu shine zai mora domin zasu sami aikin gwamnati kuma a matsayinsa na mahaifinsu shine zaifi kowa jindadi da samun yaran. To dayake zuciyar ta nema ce kawai ba musu ya amince. Shi kuwa abokin nasa Mal Kallamu yayi haka ne domin ya taimakawa yaran da suke walagigi a cikin gari. Shawara dai irin ta abokai yana kokarin bashi bakin gwargwado akan tsarin rayuwarsa amma yaki ji. Banda Mal Kallamun ma waye ya isa ya fadawa Malamijo magana irin wannan kai tsaye batare da ya auna masa rashin mutumci ko da rabin kwano bane ya kai masa har kofar gida. Yau yake dawowa daga kudu inda ya kai motoci uku na dabbobi. Duk yadda aka san Fulani da son dabbobinsu haka yake a wurinsa sai dai kudi ya fiye masa komai. Kuma gashi da nasibi don yana samun alkhairi sosai kamar yau din da ya dawo. ‘Ya’ya da matansa haka suka yi ta fitowa ana masa barka da dawowa yana faman hura hanci kada wata tayi gigin neman karbar jakarsa. ‘Yan mata biyu ne a daki daya tana kwance akan yamutsatsiyar katifa dayar kuma mai alamun ta girmeta tana daga tsaye a kanta. “Wai bakiji shigowar Malamijo bane?” Siririn tsaki taja tana juyawa daya bangaren “naji mana” Yayarta ta da suke daga iyaye mata daban ta zauna a gefen katifar tana rage murya “Mairama kinsan idan bamu je ba duk abinda yazo dashi su Inno karbewa zasuyi ko?” Cikin bacin rai Mairama ta juyo “Adda Salame ban fa hanaki zuwa ba.” Batare da kosawa ba sanin halin kanwarta ta sake murmushi “Mairama ki dena wasa da iyaye babu kyau” Tasowa tayi a harzuke sai dai ko kafin ta fara magana ta soma kukan abinda yake ci mata rai “Adda har kin manta ranar da zai tafi yace mana mun cika masa gida kamar ‘ya’yan Allah bani, wato irin wanda ba’a kaunarsu an dai haifemu bisa lalura. Gara ma ke kina zuwa wurin Innarki, ni kuwa da kasa ta rufe idon tawa bani da wani gata” Kuka Mairama take sosai Salame tana bata baki. Yarinya ce mai zuciya shiyasa abubuwan rashin adalcin gidan nasu suke ci mata tuwo a kwarya. Ada da suke makarantar kwana idan suka tafi ko marmarin hutu bata yi. Gashi yanzu sun gama harda watanni. Da yake sune manya Salame mahaifiyarta ce uwargidansa ita kuma Mairama tata ita ce ta uku. Dukkaninsu babu wadda ta budi ido da mahaifiyarta a gidan. Yayin da Salame take da mugun sanyin hali ita Mairama saurin fushi gareta musamman akan yanayin gidan nasu. Labulen dakin aka bankada Hajjo mai mulkin gidan a yanzu saboda ita ce amarya kuma yayinta bai kare ba ta sakar musu harara. “To tabbatattu isassu. Kuna kwance a daki Malamijo ya dawo bazaku je ku gaishe shi ba” Da rawar jiki Salame ta mike tana tayar da Mairama “yanzu zamu fito” Tsaki taja ta koma suka fito babu kowa a tsakar gidan sai kannensu maza da mata kusan kowa rike da agwaluma daidai a hannu daga su har uwayensu. Hatta Yadikko rike take da guda tana lailayawa a hannu don taji dadin sha. Kallonsu tayi idanun Mairama jajir. “Me ya hanaku fitowa da wuri har ya gama rabon tsaraba?” Salame taji babu dadi don ranta ya biya. Kayan kwalama irin wannan da wuya yake musu tsaraba sai anyi matukar sa’a. Harara ta gallawa Mairama don ta tuna ya taba kawo musu agwalumar kudun akwai zaki. Tare suka shiga rumfar Malamijo. Fankar kasa ce aka sakar masa a ka yana shan iska kafin a hada ruwan wanka. Tabe baki yayi ya wani juyar da kai. “Malamijo yaya hanya?” cewar Salame ya amsa da kyar. “Barka da dawowa” Mairama tace tana gintse fuska. “Chege ‘yar kunama wai nan fushi kike yi saboda nashe zan dena ciyar daku kafin nayi tafiya? Baffanku Kallamu ne ya fada min kuna gamawa zaku fara aikin gwamnati ku soma daukar albashi kuna yaga min kawai kuma sai naji shiru.” Da mamaki suke kallonsa. Ashe dalilin tijarar da yayi musu kenan a ranar harda kiransu kattin banza ‘ya’yan Allah bani. Don kansa ya saki fuska yace yayi bincike an fada masa ashe sai sunyi wata makarantar ta gaba da sakandire. “Qur’anin Ubangiji ni kuma bazan sake biya muku komai ba. Ku fiddo mazajen aure na kawar daku a sami sarari a gidan nan. Ga kannanku nan rida-rida dasu suma kullum cikin sasake ni suke. Wannan adashin da babu alamun riba na kudin makaranta na soma gajiya” Dije mata ta biyu a yanzu tayi burum ta fado dakin “Yasin Malamijo yarana sai sun gama makaranta. Haka kawai wasu ma suka gama bare nawa kuma maza” Hularsa ya turo gaba yana kankance idanu “Ki shiga hankalinki dani Dije. Sai hegen labe kamar kadangaruwa kullum kina manne da bango. Ina jiye miki kada watarana ki jiyowa kanki sallama” Idanu ta zaro cike da tsoro su Salame suka fita suka barsu. Kwanakin da suka biyo baya gidan bai canja zani ta kowacce fuska ba sai ma tsananin da Salame da Mairama suka kara shiga na rashin kawo mazajen aure. Malamijo har ikirarin hadasu da masu yi masa aikin dabbobi yayi. Yaran nasa ne tubarakallah ga kyau amma fa babu farinjini….da farinjinin dai tsayayye ne babu saboda babu mai kaunar hada iri da Malamijo saboda halinsa kaf babu na zabe. [02/11 7:27 AM] My 2nd Mtn: ********** B ARMY BARRACK SOKOTO Sojoji ne ta kowane bangare a cikin barikin suna gudanar da al’amuran gabansu. Yawancinsu sanye suke da farar t-shirt da dogon wandon khakinsu, kadan ne da cikakkun kayan suna bada umarni a bangarori daban daban. Cikin jerin wadanda suke gudun da aka fi sani da 4-40 wasu matasa ne guda biyu suke magana kasakasa don kada a ji me suke tattaunawa. “zamu din kuwa in fara shiri tun wuri muna gama training” Wanda yake yiwa maganar yayi gajeren murmushin gefen baki “ta fada min tana da kanwa kuwa” Yana kallon yadda farinciki ya bayyana a kan fuskar abokin nasa ya fadada murmushinsa. Baya bukatar wani abu da zai bata masa ranar ta yau domin burinsa bai wuce ya sami damar zuwa tadi wurin sabuwar budurwarsa ba. Mantawa suka yi da wurin da suke suka cigaba da hirarsu sai da suka ji tsawa daga wanda yake jagorantar training din nasu. “Tureta and Murtala fall in” Sun san manufarsa su daidaita kansu da sauran cikin sauri suka ce a tare “Yes sir, sorry sir” Daya daga cikin wakokinsu na sojoji da suka saba suka fara yi tare da sauran suna gudun har lokacin da babban nasu ya dakatar dasu. “Stand at attention ladies” Captain Mustapha yace yana zagayesu. Su biyun ne dai masu surutu dazu suka fara dariya. Ba komai ke basu dariyar ba kuwa sai cewa da suke idan aka kira su ladies wai sai su rinka hango kawunansu da sauran cikin kayan mata. Captain Mustapha ya gaji da halinsu don basa ji kwata kwata gashi a karkashin platoon dinsa suke. Sallamar sauran yayi dama duka a gajiye suke. Da yatsa ya yiwa samarin biyu alama da su cigaba da gudun sai sun sake zagaye uku zasu tafi. Wanda ya fi fitinar ya dube shi hankali a tashe sannan ya kame cikin daga murya yadda suka fi yin magana da na gaba dasu ya roki alfarmar ya daga horon zuwa washegari. Dayan Captain Mustapha ya yiwa kallon tambaya baiyi wata wata ba ya fadi uzurin abokin nasa, wato zance da zaije wurin sabuwar budurwarsa. Murmushi yayi don ya sami damar horasu yadda yake so. “Zayyan Tureta” “Sir” ya sake kamewa. “Za ka sake yin zagayen nan sau biyar” Baki ya bude sai kuma yayi saurin rufe shi don kada ya sake yin laifi. Yana kallo aka sallami abokin nasa don a bata masa rai tunda duka laifukan da suke aikatawa shine ja gaba. Hadir Murtala ya faki idon Captain Mustapaha ya yi masa gwalo sannan ya bar wurin. Ko da zai kare da rarrafe ya sani bin umarni dole ne. Juyawa yayi a matukar gajiye zai cigaba da gudun Captain yace yaje gidansa ya jira shi. Idan ya riga shi zuwa yana bukatar ya dawo ya ga a ina yake. Haka yake so yayi ta yi har sai ya iske shi a gidan. A guje ya kwasa sai bangaren gidajen sojojin yaje ya dawo Captain yana nan inda ya barshi kuma yace ya sake tafiya. Sai da yayi haka sau hudu suna haduwa a kan hanya a wurare mabanbanta a na karshen suka hadu a kofar gidan. Zuwa lokacin Zayyan da kyar yake motsa gabbansa amma a haka ya kame a bayan Captain Mustapha. Murmushi Captain din yayi masa. Yana kaunar yaron saboda kwazo da himma amma rashin jinsa yayi yawa. “Kana jin yunwa na sani. Mu shiga ciki kaci abinci” Mamaki ne ya bayyana a fuskarsa don ba haka ya zata ba. Tunaninsa kullum Captain Mustapha shi yafi tsana duk cikin platoon dinsu. A waje ya jira shi ya fara shiga ya nemi iyalinsa su shirya zai shigo da bako. Wani yaro ne da zaiyi kimanin shekaru bakwai ya fito a guje yana dariya yazo gabansa ya tsaya. “Kaine Tureta?” Sakin fuska yayi don akwai shi da son yara “nine” Sai kawai yaron ya dane jikinsa har suka kusa faduwa yana kyalkyala dariya ya soma surutu “kaine kayi karyar rashin lafiya don kada kaje training? Daddy yace rannan ka sakawa wani kunama a takalmi saboda ya shiga masallaci da takalminsa. Kuma wai ka iya karatu mai dadi amma baka jin magana” Baki Zayyan ya rike yana kallon yaron yana ta zuba da bashi labarin abubuwan da yake na rashin ji tun zuwansa barrack din. Gyaran muryar Captain din suka ji yaron ya nutsu yana rike da hannun Zayyan. “Awwab?” Sunkuyar da kai yaron yayi yana kara matse masa hannu suka yi murmushi tare. Bayan Captain ya bi har cikin falon. Matarsa Hassana da ake kira Mami ta fito fuska a sake ta nuna masa wurin zama da dan tebur a gaban kujerar wanda ta dora tray din abinci da abin sha. Wuri suka bashi yana cin abinci Awwab na masa hira tamkar sun dade da sanin juna. Sai bayan rabin awa Captain ya sake fitowa sanye da jallabiya irin mai gajeren hannu da fadin nan. Zayyan ya dan gyara zama ya fusakance shi. “Awwab ya dame ka da surutu ko? Halinku daya na fitina amma shi matsoraci ne” Dariya Zayyan yayi yana kallon yaron da ya shiga ransa cikin kankanin lokaci. Basu dade suna hira ba Captain ya sallame shi bayan dogon gargadi akan halayyarsa idan ba yana da burin a kore shi tun kafin ya zama wani a cikin sojojin ba. Har Hadir ya dawo Zayyan yana mamakin Captain Mustapha. Mutumin baya magana sosai idan ta wuce karbar umarni da badawa. Kuma baya nuna damuwarsa akan kowa amma ace wai banda sanin halinsa har labarinsa yake bawa iyalinsa. Hannun Hadir yaji akan kafadarsa yana jijjigawa. “Zayyan lafiyarka kuwa? Inata magana kamar baka ji. Nace naje wurin Zainab mun daidaita kanmu” “Na tayaku murna” Cikin yanayin ko in kula yayi maganar hakan yasa Hadir taba wuyansa “zazzabi kake ko ciwon kai? Zainab fa nace mun hada kanmu. Da naje babanta ya fito yana yi min tambayoyi karshe yace in turo. Ina ta kokarin fahimtar dashi ba kai bane sai da ya tafi tace ta amince min itama. Nima kuma na gani ina so….” “Wai kasan yau a gidan Captain naci abinci har muka yi hira? Ashe haka yake da kirki mune bamu fahimce shi ba. Kuma yana da da dan shekara bakwai abin mamaki yayi auren wuri inajin.” Hadir ya kalli Zayyan ya tabbatar kalau yake sai ya rabu dashi. Washegari ne suka sake hirar bayan kowa ya dawo hayyacinsa. Hadir da gaske ya nuna yana son Zainab kamar yadda ta amince masa shi kuma Zayyan jin kansa yake ya kara girma saboda ya fahimci Captain baya kinsa. Kowa da nasa farincikin a haka abokan suka cigaba da zaman barikin suna horowa akan matakan kariya da tsaro. A gefe daya maganar su Hadir tayi nisa yana shirye shiryen idan sun sami hutu zaije Kano ya sanar da iyayensa su zo su nema masa aurenta. Zayyan kuma wata nutsuwa ce take sauko masa don ya burge Captain sannan ga shakuwa mai karfi tsakaninsa da Awwab da kannensa mata biyu. Kimanin watanni biyar sun shude kafin aka basu hutun sallah wanda ba wasu kwanaki bane na azo a gani. Duk da haka sun karba da godiya kowa yayi nasa wuri. Hadir mutumin Kano ne dan cikin gari unguwar Madungurun. Shi kuma Zayyan dan wata karamar hukuma ne a cikin Sakkwato, wato Tureta wadda ta zama inkiyarsa a barikin amma gidansu yana cikin garin Sakkwaton. Sun tafi gida da murna da abinda suka samu a matsayin albashi kasancewarsu a mukami mafi karanta a cikin sojojin Nigeria, Second Lieutenant. Su biyun da mafiya yawa daga cikinsu sun zabi shiga aikin soja ne domin zama ababen alfahari ga kasar da basu da kamarta. Nigeria kasar da manya manyan dattawa daga bangarori daban daban suka hadu suka hada karfi da karfe wurin kwato mata ‘yanci. Wadannan matasan sojoji zukatansu sun tafi ga ganin sun zama kariya ga al’ummar kasarsu batare da duba da bambancin yare, addini ko al’ada ba. Da wannan kyakkyawar manufa su Zayyan suka baro jindadi da kwanciyar hankalin da suke samu a gaban iyayensu suka sadaukar da kuruciyarsu don samarwa na baya kasar da zasuyi alfahari da ita. ********** Tamkar ba soja ba tun da ya nufo gidansu yake jin faduwar gaba. Don ta shi a datse hutunsu saboda babu abinda yake tsinta a gidan nasu da ya wuce bacin rai da bakincikin matar uba da ya’yanta. Zayyan maraya ne ba uwa ba uba. Mahaifiyarsa mutuniyar Nijar ce ‘yar kabilar Tamasheq a cikin Agadas, mahaifinsa ne Basakkwace. Sun hadu a yawon fataucinsa na dabino da cukwi da yake zuwa sarowa. Soyayyar lokaci guda ce ta kamasu shi da Alheran bai kuma sha wahala ba babanta Alh Ghousman Agali ya amince masa kasancewarsa kwastomansa da aminci ya dade da wanzuwa a tsakaninsu. Mal Muhammadu Tureta a lokacin yana da matar aure guda daya Jume da yara shida, maza uku mata uku kuma shima kasuwanci yana damawa dashi kafin daga baya karayar arziki ta same shi. Wani mummunan zama akayi tsakanin Jume da Alheran. Da fari Alheran ta kwantar da kai sosai tana bin Jume sau da kafa duk da irin wulakanci da cin kashin da take yi mata ita da yaranta. Allah ma Ya taimaketa tana jin Hausa saboda cudanya da suke yi da Hausawan kasar tasu. Bayan wani lokaci tana hadiyar bacin rai ita kadai ga gorin haihuwa ta ajiye kawaicin a gefe suke bugawa. Idan Jume ta shirya makircinta Alheran zata fidda kanta da kissar da wahala ta sanya ta koya karfi da yaji. A shekara ta uku da aurensu Allah Ya bata ciki. Sunyi murna ba kadan ba ita da maigidanta. Yadda yake matukar sonta haka yake son abinda yake cikin nata. Wata tara da kwanaki kadan Allah Ya sauketa lafiya aka sami Zayyan. Kafin suyi arba’in Alh Ghousman ya rasu. Alheran tasha kuka Mal Muhammadu ya dauketa suka tafi Nijar. A can ya barota bayan yayi kwana goma sai da ta shefe watanni biyu domin bayan anyi ar’bain aka zo rabon gado kanin Alh Ghousman yayi tsallan badake yace dukiyarsa ce kaf yayansa yake juyawa. Aka buga aka raya ya dauko shaidun karya harda barazanar kai iyalan dan uwan nasa kara. Rigima gagaruma akayi karshe suka hakura ya basu abinda yayi niyya cikin dukiyar mahaifinsu ya handame sauran. Da wannan bakincikin ta dawo Sakkwato sai mijinta ne yake ta kokarin kwantar mata da hankali. Zayyan na da shekara uku ta sake samun ciki. Wannan karon tana laulayi mai wahalarwa wasu lokutan ko yatsa bata iya dagawa, amma duk da haka bata tsira daga kaidin Jume. A haka ta shiga wata tara. Wata asabar ta tashi da nakuda gashi Mal Muhammadu yayi sammakon fita ranar yaran duka su ma basa nan. Tana cikin wannan yanayi ta rinka kiran Jume tana jinta tayi biris abinta. Cikin tsananin azaba Alheran ta soma yunkurin haihuwa abinda ke cikinta kansa ne kawai ya leko Allah Ya karbi ranta. Shima kuma wahala bata barshi ba bai jima ba ya koma. Jume ta ma manta da cewa ta ji Alheran tana kiranta wanda tasan haihuwa ce tayi kwanciyarta tana bacci. A yashe a kasa Mal Muhammadu ya dawo ya riski Alheran rai yayi halinsa. Yayi kukan rashinta ba kadan ba. Jume tayi rantsuwa kwando kwando kan cewa bata ji ko da tari daga dakin Alheran ba. To dayake abin da tayi ya dameta a rai shine ta dauki Zayyan ta rike. Riko ne dai irin na matar uba da bata son dan kishiya amma dai duk tsiya tana kulawa dashi. A haka ya taso gatansa daya mahaifinsa. Maikudi shine babban da namiji a gidan wanda ya kasance na uku a wurin Jume kuma tashin hankalin gidan gabadaya. Shekara biyu kenan da rasuwar Mal Muhammadu, Jume da iyalinta suka tattare duk wani abin arziki suka boye. Dan wanda aka fitar shine aka raba musu tare harda Zayyan. Sauran Maikudi yaki fito dasu tun ‘yan uwansa suna magana har sun ja bakinsu sun rufe. Bashi da kirki ko kadan Jumen ma tsoronsa take ji. Dakin Jume ya fara shiga daga dawowarsa ya gaisheta. Kamar kullum amsar dai babu yabo babu fallasa. Haka ya tashi a sabule yana fatan kada ya gamu da Maikudi. Yayi babbar sa’a kuwa don kwanansa biyu basu hadu ba. A kwana na uku ne Kawunsa Ghoumar kanin Alheran yazo daga Nijar. Kafin ya iso gidan ya aika aka kirawo masa Zayyan suka hadu a gidan wani abokin Mal Muhammadu wanda tare suka sansu a lokacin da suke zuwa fatauci Nijar din. Zayyan yayi murnar ganinsa sosai saboda ba kasafai yake samun ganin dangin mahaifiyar tasa ba. A gaban abokin Malam din Ghoumar ya dauko damin kudi ya mikawa Zayyan. “Wannan shine kasonka na gadon Alheran. Sai da cutar ajali ta kama Baffanmu ya tuba ya dawo mana da dukiyar mahaifinmu. A ciki an fitar da kason Alheran shine aka raba muku kai da Mal Muhammadu bisa doron shari’a” Kudin Zayyan ya shiga juyawa duk da bai kirga ba ya tabbatar suna da yawa. Ghoumar yayi murmushi “kasan mahaifinmu yana da rakuma da dabbobi sosai. Sune aka sayar aka raba naku saboda na sani babu abinda soja zaiyi da rakumi” Dariya suka yi ya cigaba da yi musu bayanin cewa kason Mal Muhammadu da yake hannunsa kuma zai kai gidan a lokacin za’a raba shi ne tsakanin Jume da su yaransa dukkansu. Abokin Mal Muhammadu yace sun zabi bashi nasa a kebence ne saboda sanin halin Jume da Maikudi. Shawara suka bashi ya tabbatar ya boye domin sun sani wannan kudi ba karamin gata zai masa ba. A nan hannun aminin mahaifin nasa Mal Aminu ya bar kudin kafin yayi shawarar me zaiyi dasu. Daga nan suka wuce gidansu tare. Kamar yadda ya sanar da Zayyan haka Ghoumar ya sake yi musu bayani. Liman aka kira da wasu malamai biyu suka kasafta kudin tsakanin Jume, ‘ya’yanta shida da Zayyan. Ana mikawa kowa nasa Maikudi ya tashi yana kumfar baka. “Yanzu kuke cewa Zayyanu akwai nasa kason a matsayinsa na danta. To kuma banda tsantsar mugunta me zai sa rabon mahaifinmu a sake kasaftawa dashi?” Ghoumar ya harare shi “rabon gado ba da ka ake yinsa ba malam. Abu ne da Allah Ya tsara da kanShi. Zayyan yaci rabon kasancewarsa danta sannan yana da rabo a kason mahaifinsa” Rigima ce ta kaure inda Jume da yaranta musamman Maikudi suka dage akan baza’a raba da Zayyan ba. Da ya ga abin yaci tura yace ya yafe amma Ghoumar da Mal Aminu suka ce sam sai ya karba. Tsiya tsiya aka rabu babu dadi. Ghoumar rai a bace yace idan ya kuskura ya basu wani abu a wancan kudin nasa na shi kadai bai yafe masa ba. Dariya ya bawa Zayyan ya dai yi masa nasiha da kuma horonsa da rikon zumunci duk da yasan yanayin aikinsa abin zaiyi wuya. Suna tafiya kuwa Jume ta kira shi dakinta suna zaune ita da Maikudi sai kumburi yake shi kadai. “Zayyanu munyi magana da yayanka tunda kai a bariki kake rayuwa ka bashi kasonka ya cigaba da juya maka” Magana ce ta rainin hankali ya gode Allah da wayonsa sarai amma sai ya biye mata “to Jume amma da na riga na barwa Kawun ne ya yi min kiwon a can Nijar” Tsuke fuska tayi “kana nufin kai ba kudi aka baka ba?” “Rakuma ne da dabbobi” Maikudi ya tashi kamar zai buge shi don zuciyarsa na fada masa karya Zayyan din yake. Wani kallo mai firgitarwa Zayyan ya watsa masa allurer soja ta motsa. Da kansa yayi lakwas ya koma ya zauna yana kallon Jume. “Kina kallo a gabanki yaron nan yake min kallon banza ko Jume?” Bata kula shi ba ta sake kallon Zayyan fuska babu walwala “abinda za’ayi sai ka kawo wanda aka baka a gabanmu ya hada ya juya muku din” A ladabce yace “Gobe da safe in Allah Ya yarda zan je wurin Mal Aminu na karbosu.” “Shi ka barwa don kana bakinciki da karuwata?” Maikudi yace yana kallonsa shekeke. Bai tanka shi ba yana sauraron Jume tana fada masa gobe da sassafe yaje ya karbo kudin ya kawo mata. Daren ranar har bacci ya kwashe shi yana mamakin wannan karfin hali da iko da aka ki dena nuna masa duk da ya mallaki hankalinsa. Washegari yaje wurin Mal Aminu ya fada masa yadda suka yi da shawarar da ya yanke game da kudin. Goyon baya ya bashi suka yi sallama ya kwashi dukiyarsa sai Kano gidansu Hadir. [02/11 7:27 AM] My 2nd Mtn: C Washegari yaje wurin Mal Aminu ya fada masa yadda suka yi da shawarar da ya yanke game da kudin. Goyon baya ya bashi suka yi sallama ya kwashi dukiyarsa sai Kano gidansu Hadir. *********** “Ka koma ka fadawa wadda ta aiko ka na fada na kara ‘yata bazata tafi kwadayi gidan kowa ba.” Cewar Malamijo yana karkada dan jikinsa duk don ya nuna da gaske fa yake. Yaron wanda ya kasance kanin Salame da suka hada uwa ya tashi ya bar wurin Salame na zubar hawaye. Wata tsawa Malamijo ya daka mata ta shi babu shiri jiki na bari. “Kwalamammiya tashi ki bani wuri. Ku babu mijin babu wata sana’ar kawo dari da kwabo sai dai aci a cika min shadda da bayan gari. Mtww Kallamu kwoi mugu, ya rinka rudata sai da na kaiku bokon banza bokon hofi gashi ban ga komai a kasa ba” Mairama da ke wanki a tsakar gidan ya nuna da bakinsa da yake turawa saitinta “ke kuma sai bakin hali ba uhm ba uhmm uhmm kinbi kin tsaneni ina mahaifinki. Ko rokona abu ba kya yi. To duk jarabar mutum dai ba’a sake uba. Nine nan dai uban naki don ko makaho ya shafaki ya shafani yasan akwai jini. Da namiji kika fito ma sunana zan maida miki Yasin” Wankinta ta cigaba tana yi hawaye na diga a cikin bokitin ta jiyo muryar Yadikko daga dakin girki. “Ka dai ji kunya Malamijo, kana abu yana damunka shine ka rasa da wadda zaka rinka wannan magana kamar wata sa’arka sai ‘yar cikinka. Rashin roko tayi min daidai. Masu yi din banda bakar magana me kake tsinana musu bayan sun gama keta billensu” Hularsa ya turo gaban goshi a karkace “mutum dai ya shiga taitayinsa dani don ni dadewa bazata sa na kasa sallamar ‘yan hamayya ba” Daidai nan Nene kanwarsa da ta kawo musu ziyara daga wani kauyen Gaya inda take aure ta idar da sallah. Magana take da niyyar yi masa akan yadda yake yi da gidansa duk da dai ba yau farau ba suka ji an banko kofar gidan. Ta Madina ce babar Salame ta shigo ko sallama babu “gani nazo da kaina a bani ‘yata Malamijo ko in nuna maka ba kai kadai aka haifa a watan tijara ba” Tuni tsakar gidan ta kaure da ‘ya’ya da matansa an fito kallo. Salame jikinta har bari yake tana kuka. “Yanzu ke baki ji kunyar shigo min gida ba? Koda shike naji labarin yanzu ma zawarci kike kina neman mafaka” Daga murya tayi cikin fada ta nuna shi da yatsa “Ali ba tsoronka nake ji ba. A bani ‘yata biki zamu na ‘ya’yan ‘yar uwata a Kano” “Bazata ba” yace a takaice. Fada Innar Salame ta soma yi Nene ta sa baki “Ke Salame wuce ki hado kaya kizo ki bi mahaifiyarki. Malamijo idan baka bari yaran nan suna rabar dangin iyayensu mata za’a sami matsala nan gaba” Wani karkataccen kallo ya bita da shi kafin ya kada baki yace “ke da kika lallabo cin arziki ina ruwanki da iyalina bayan baki san zafin haihuwar ba?” Jikinta ne yayi sanyi ta dukar da kai “Malamijo ni???” Shima sai yaji nasa jikin ya saki don kuwa yana ji da Iyalle ko a cikin dangi “ba haka nake nufi ba. Ke Salame zo ki bi uwarki kuma sati guda na bada aka dara ban yafe ba” Innar Salame tana tsaye tana karkada kafa daya tana jiranta ta fito. Mairama tana rakube a jikin bango wurin da suke shanya tana jin inama ita ce zata je wurin dangin tata mahaifiyar. Sai dai ina zata sami wannan damar. Mutanen da suke fulanin tashi basu nan basu can. Auren ma da Innarta anyi ne kawai saboda sauke bashin da Malamijo yake bin babanta a lokacin. Hangota Innar Salame tayi sai taji yarinyar ta bata tausayi. “Mairama kema ko zaki bimu ne?” Malamijo yayi wani tsalle sai gashi a gaban Mairama “wannan kuma kinyi tsararo Ta Madina, babu inda zata je” Iyalle da kanta tazo taja hannunta ta kaita dakinsu “hada kayanki ki bisu zanyi maganin abin” A tsorace Mairama ta hada kayan saboda gudun kada ya hanata tafiya. Basu dade ba a dakin Yadikko ta kwala musu kira suka tafi dakinta. “Ni da Nene mun roka muku alfarma ya bari kuyi kwana goma. Idan kunje ku tabbatarwa da kanku bazaku wuce lokacin da aka dibar muku ba” Murna a wurin Mairama kai kace bikin na dangin tata mahaifiyar ne. Salame kuwa har ta gama tsoro bai bata damar sakin jiki ba. Da zasu tafi kashedi Malamijo ya rinka yanka musu kusan minti goma yana abu daya. Nene da Yadikko sunyi masa shigar sauri sun kuma hade masa kai ba don haka ba Ta Madina bata isa ya bata Salame harda karin Mairama ba. ********** Kano ta Dabo tumbin giwa, birnin na Kano a yau yayi manyan baki daga garin Sumaila wato Salame da Mairama. Wata unguwa da basu san sunanta ba suka wuce zuga guda ta ‘yan biki daga Sumaila. Yadda Mairama ta saki jiki cikin mutanen sai ta baka mamaki da tausayi. Tun tasowarsu ita dai bata taba zuwa wani wuri da zata ji dadi da sa’anninta ba sai makaranta. A can ma ba wani sakin jiki gareta ba saboda tana ganin kowa yafi karfinsu. Gasu dai da uba mai kudi amma daga kayan makaranta da akwati baya basu komai. Dan siyayyar nan ta provision sai dai su gani a kwanar wasu. Shiyasa an rainasu sosai musamman Salame da sunanta ya dace da halinta. Anyi Kamu a ranar da suka sauka da daddare inda amare aka kunshesu a daki tsakiyar ‘yan mata kawayensu da ‘yan uwa, dangin angwayen su ka zo aka feshesu da turare. Washegari kuwa lanchin (luncheon) za’ayi a filin wani katon gida mallakar kanin baban amaren biyu. Salame ta sami kaya kala biyar sababbi, biyu daga yayar innarta uwar amare sai uku daga Ta Madinan. Guda ta cire a ciki ta baiwa Mairama tace ta saka kada ta fita daban tunda su dai ba wasu suturun arziki na shiga taro garesu ba. Mairama sai murna da godiya ta sanya atampar da akayi mata dinkin riga da zani buba anyiwa rigar cin baki da irin lace dinnan na adon kaya a wuya da hannaye. Tayi kyau abinta gwanin sha’awa haka itama Salamen. Motoci bus bus ne aka haya suka rinka kwasarsu aka kaisu wurin bikin. Salame tana manne da kanwarta duk da cewa dai tana sakin jiki da ‘yan uwanta suna hira. Teburinsu su bakwai ne da yake a zagaye yake suna fuskantar juna ana ta tsokanar wata cikinsu da tayi saurayi daidai kofar shigarsu gidan. Karaf idanun Salame suka sauka akan Zayyan ya nisa suna magana mai matukar mahimmanci da Hadir. Daya daga cikin angwayen dan uwa ne ga Hadir din. Iyayensu maza ciki daya suka fito. Shiyasa da Zayyan ya iso Kano aka sanya shi cikin abokan ango. Cinikin fili suka gama kafin zuwansu nan a unguwar gandun albasa. Shi dai Zayyan ya ga wurin babu gidaje sosai amma dillalin yana ta cika masa baki cewa nan gaba kadan unguwar zata hade harma a rasa filin saidawa. Shima da yake ba mazauni ba sai ya amince ya biya kudi bisa shawarar Hadir. Zancen gini kuma a hankali zasu yi tunda har yanzu ko rabin kudin da aka bashi bai taba ba. Takardun filin ne kwafi biyu da sa hannayensu ya mikawa Hadir daya yace gata nan ya ajiye masa shi kuma zai aje daya a wurinsa. Sai da suka gama komai duk motsinsa akan idon Salame sannan su ka koma cikin samari ‘yan uwansu. Ba karamin tafiya yayi da imanin Salame ba lokaci guda taji sonsa ya game zuciyarta. Mairama kuwa an sami sake hira tayi hira an kawo abinci kowa plate dinta shake da jallof din shinkafa da yankan naman sa da aka soya sai salad, tumatir da albasa. Wayyo dadi jikinta har tsuma yake kuma wai aka kirga su aka sake ajiye musu ledar tsire ga kuma lemon kwalba. Kar kaso ka ga idanun Mairama hankalinta yayi kwano na Salame kuma yayi kan Zayyan da bai san da zamanta a wurin ba. Police band suna wakarsu amma kusan kowa abinci yake ci babu ‘yan rawa. Kwalbar fanta chapman Mairama ta faki ido ta daga tana kwankwada asalin dadi da sanyi yana ratsata ta manta da kunyar idanun jama’a. Bata samu ta sauke kwalbar mai 35cl ba sai da ta shanye shi tas. Daga lokacin da ta soma waige ta tabbatar babu mai kallonta har zuwa sanda ta ajiye kwalbar Zayyan yana gani. Baki ya rike yana kallon yadda ko da ta shanye sai da ta sake daga kwalbar ta kwakkwafeta a bakinta. Kasa cin nasa abincin yayi komai tayi sai yaji ya burge shi shi kadai ya rinka murmushi. Teburin kusa da nasu Mairama ne duka matan dama su uku ne su ka tashi a tare. Mairama tana ji suna cewa sallama zasu yiwa amaren su tafi. Tana ganin sun bace cikin jama’a ta wayance ta tashi da kwalbar lemonta ta ajiye a wurin ta dauki wata mirinda da ko rabinta ba’a sha ba. Plate din nasu ma basu wani ci sosai ba ga nama sun bari. Kamar ta dauka shima sai dai ta hakura lemon yafi mahimmaci a gareta. [02/11 7:28 AM] My 2nd Mtn: D Banda wanda ta dauka sai da ta dan kurbi na kusa dashi sannan ta juya da sauri da taji ana kiran sunanta. Hadir ya tabo Zayyan da yake kyakyata dariya shi kadai da ya hango Mairama tana zaro idanu. Matan da suka bar teburin ne suka dawo daya ta soma cigiyar lemon da ta bari. Mairama tayi tsit don kuwa saura kadan ma ta shanye mirindar. “Kai lafiyarka kuwa?” Idanu ya lumshe yana kallon kyakkyawar bafulatanar ta tsure karshe ta kuma rungume kwalbar ta boye cikin lullubinta. “Mata nayi” Hadir ya tura kujera baya da sauri “nuna min ita muje mu tsarata wallahi” Zayyan ya mike da sauri “naki din, kai fa satar budurwa kake yi” Sauran mazan wurin suka sa dariya shi kuma ya kwashe lemuka uku da ba’a bude ba yayi gaba. Salame tana ganin ya nufosu ta tattaro dukkan nutsuwarta tana murmushi don tun dazu suke hada ido yana murmushi a zatonta ita yake yiwa yayin da hankalinsa kacokan yana kan Mairama ne. Sallama yayi musu matan teburin gefen ana ta masifar rashin ganin lemo ya mika musu biyu sanna ya dubi Mairama da tsoro ya hanata motsi ya mika mata chapman irin wadda ta fara sha. Dan rausayo kai yayi ya duku wurin kanta. “Kanwata ga wannan ki kara” Sai lokacin ta dena jin mitar wadancan matan ta tsuke baki batare da ta juya ba “rike kayanka bana so” “Haka ma zaki ce? To ki shirya kuwa don zan tona” yace yana rage murya sosai daidai kunnenta. A firgice ta waiga idanunta suka sauka cikin nashi. Ko ma me tayi niyar cewa makalewa yayi a wuyanta ta sami kanta da manta a ina ma take na ‘yan dakiku. Lallausan murmushi ya sakar mata wanda ya sake fito da kyaunsa da cikar sa. “Muje can na fada miki me da me na gani” ya nuna can jikin katanga wurin wata katuwar bishiyar darbejiya. Ko dogon nazari bata tsaya yi ba ta bi bayansa kuwa don ta gama tsorata kaddai ace ya ga lokacin da ta dauke musu lemon. Wani mugun daci ne ya taso ya tokare wuyan Salame har suka isa bakin bishiyar tana binsu da kallo. Me yake shirin faruwa tsakanin kanwarta da mutumin da take jin bata taba son wani abu makamancinsa ba a rayuwarta. Kallon da yake yiwa Mairama kadai ya isheta amsa. Sauran ‘yan mata kuwa sai shewa itama zasu kwana suna tsokanarta kenan. Suna isa wurin bishiyar yace “da farko dai sunana Zayyan, ni soja ne” Idanunta suka yi kwalkwal da hawaye suna barazanar saukowa. Murya na rawa ta fito da kwalbar da ta boye cikin mayafinta “me yayi zafi ni ‘yasu. Daga shan lemo sai dauko sojoji. Ni wallahi nayi zaton sun tashi kenan. Don Allah kuyi hakuri kada ka kamani” tace tana kallon Hadir da ya iso inda suke. Maganarta dariya ta bashi ya mikawa abokinsa hannu da nufin gabatar dashi a gareta “Zayyan Tureta…” Wani kallo ta watsa masa tsoron yayi nasa wuri ta yatsina fuska za ta gwada musu tsiwarta “ya tureni? To Bismillah dan halak ka fasa. Mutum ya tabani ba hakura zanyi ba” Kasa cewa komai suka yi sai dariyar da suke yi mata tana karkada hannuwa. A ranta tana jin tsoronsu zaratan samari irin haka amma kuma bata so ta basu damar cutar da ita. “Kinga ‘yan mata sunansa Zayyan Muhammad Tureta ba tuureta na hankadewa ba, garinsu ne a Sakkwato” Kunya taji sosai ta rufe fuska “lahhhhh” Shima Zayyan sai ya biye mata yace “lahhhhh” Hadir yana dariya ya basu wuri Zayyan ya kura mata ido “yaya sunanki” “Mairama” ta amsa da karamar murya. “Kamar Maryam yake?” “Haka dai aka saka min a gida ni” “To fillo ni dai Mairam zan ce. Ina ne gidanku?” Kallonsa tayi na dan lokaci tana son yin nazari shin kamata zaiyi ko kuwa dai wani abin ne daban. “Ba kamani kazo yi ba?” “Kwantar da hankalinki babu mai sanin kin saci mirinda” Yadda yayi maganar yana kasha mata ido ya sanya hankalinta ya kwanta itama harda dariya. Kwatancen gidansu ya nema daga gareta da bayanin kansa sannan yace duk da karancin lokaci yana son ganawa da mahifinta domin ya nemi aurenta. Kunya sosai ta lullube Mairama don itama a ‘yar hirar tasu har ya shige zuciyarta. Ta fada masa gidan da suke yanzu da kuma kwatancen gidansu yace zai zo da daddare su sake fahimtar juna. Kusan da gudu-gudu ta koma teburinsu ‘yan matan suka soma zuba mata tambayoyi. Jiki na rawa ta fada jikin Salame tana dariya. “Bazaku ji komai ba sai ma gama shawara da Addata” Wani murmushin yake Salame tayi a ranta tana nadamar tahowarsu da Mairama. Ita kuwa dadi ya cikata ta fada mata yadda suka yi. Cikin gatse tace “kice dai wannan tafiyar taki ce” Bata fahimta ba shiyasa tayi murmushi “gaskiya tawa ce, yace zai tambayi gidan da muke sai yazo anjima. Ai tare zamu fito ki ganshi da kyau. Hmmm Hausarsa sai ta baki dariya, sakkwatanci yake” Kamar wanda ta hadiyi kota Salame tace “umhumm” Taro ya watse amare da angwaye suna farinciki, Zayyan da Mairama suma suna nasu. Bayan isha ba dadewa kuwa sai ga aike cikin gidan ana sallama da Mairama. Ta Madina tayi dariya tace idan al’amari ya kankama tukwuicinta mai tsoka ne tunda ita ta kawota. Kunya ce ta kama Mairama taje ta janyo Salame wadda taso nokewa suka fita. Maza uku ne a wurin. Zayyan, Hadir sai kuma wani abokin Hadir din tun kuruciya layin gidansu ma daya Salisu. Tunda suka fito shi kuma ya kyallo Salame shima tasa zuciyar ta lula kogin kauna. Gaisawa suka yi a mutumce Hadir ya sake yi musu bayanin waye Zayyan da manufarsa akan Mairama. Zuciyar Salame kamar ta fashe don bakinciki a ganinta cin fuska ne ma suke mata. Bayan an gama bayanin Salisu yace shima fa yaga matar aure nan dai aka hau gabatar da kai. Salame ko kadan bata yi farinciki ba. Salisu dan kasuwa ne a kantin kwari tun da kuruciya yake da zafin nema bata sani ba yana da arziki sosai. Mairama da Zayyan sun rabu akan cewa jibi kafin ya bar gari zai sake zuwa don a hada shi da mai yi masa rakiya Sumaila wurin Malamijo. Idan ya tafi zai gabatar da maganar ga magabatansa don bashi da burin a ja lokaci. Salisu ne dai bai wani sami hadin kan Salame ba hanlinta yana kan hirar su Zayyan yace Mairama ta taya shi neman fada. Bayan sun tafi a cikin gidan ana ta tsokanar Mairama ta kuwa biye musu tana yi tana sako yayarta aciki. Salame kunci da bacin rai ya sanya ta fashe da kuka mai cin rai. Shiru kowa yayi Mairama tayi juyin duniya taki cewa komai. Ta Madina aka sanarwa tazo itama tana tambayarta sai cewa tayi wai gida take son komawa. Ashar Ta Madina ta kunduma mata “ke har wani gida gareku a Sumailan kike son komawa?” Fuskarta har ta soma kumbura tace “ni dai tafiya zanyi tsoro nake kada mu koma Malamijo yayi fada don baiso muka zo ba” Ba wani abu ke cinta ba face zallar kishi da kanwarta. A ganinta idan tasa su ka koma gida Zayyan bazai san gidansu ba bare yabi Mairama shikenan kowa ya rasa. Abu kamar wasa Salame ta tubure sosai. Ran Ta Madina a bace tace gobe da sassafe zata sakasu a mota kuma ta kwana da sanin cewa bazata sake neman daukota ba, idan Malamijo zai cinyeta ne a gidansa babu ruwanta. Dayake ido ya rufe maganar ta inda ta shiga ta nan ta fice. Mairama a daren bata damu ba sai da ta tuna Zayyan yace zai zo hankalinta ya tashi. Har daki ta kira Salamen ta roketa alfamar ta bari su sake kwana. Kallon da bata taba yi mata ba ta jefeta dashi wanda ya haddasawa Mairama tuhumar kanta ko ta bata mata rai ne. “Kinzo kin wani shige cikin danginmu sai wani cusa kai kike yi. Dadin abin dai duk tsiyar mutum da danginsa na jini zaiyi tinkaho. Mu dai munyi sa’a muna da dangin uwa” Mairama sai taji ranta ya baci itama “nima ba daga sama tawa uwar ta fado ba. Idan don nazo bikin danginku ne Allah Ya baki hakuri bazan kara ba” “To dama waye zai gayyaceki?” Kasa bata amsa tayi ranta a jagule ta karasa hada kayanta ta dauko wanda Salamen ta bata na taron da akayi da rana ta saka ta mika mata. Bata damu ba ta karbe duk da a farko niyarta ta bar mata kyauta ne. Tasha aka kaisu suka hau mota suna harare hararen juna. Mairama ita gorin da akayi mata ne ya bata mata rai don bata san me tayiwa Salame haka da zafi ba. Sun isa gida kafin azahar Malamijo yana gidan gonarsa wurin dabbobi. Babu wanda ya aikesu bare yayi murnar dawowarsu gidan. Basu rufa awa guda ba ma Dije ta taso Mairama tazo tayi mata aikin fura da take yi ta sayarwa saboda ciyar da yaranta. Tana tsaka da aikin Inno ta kira Salame ita kuma aka bata surfen masara. Haka suka yi ta aikin babu mai yiwa ‘yar uwarta magana. Mairama ke satar kallon Salame cike da damuwa, ita kuma da sun hada ido sai ta galla mata harara. Washegari wuraren goma na safe aka aiko wani yaro wurin Malamijo. Dan aiken da ne ga wanda yake taya shi aikin kula da dabbobinsa. Yaron yana haki don gudu yayi zuwa gidan ya sanar dashi wani katon san sa yana neman kasawa ya bada izini a yanka shi. Tamkar an soki kahon zuciyarsa ya zabura zai bi bayan yaron sai ya tuna babu takalmi a kafarsa ya koma ciki da sauri. Lokacin da ake sanar dashi san ya kasa dan sa daya na wajen Inno mai suna Habibu yana ji ya juya cikin gidan kafin ya ankara da tsayuwarsa. Inno tana gaban murhu za ta hada wutar girki yazo yana haki. “Inno yau kece a turaka?” ya tambaya babu alamun damuwa a fuskarsa sai ma farinciki. Yaran gidan musamman masu uwaye sun san ranakun girkin iyayen nasu saboda abincinsu yana fin na sauran ranakun auki. “Idan bani bace uban me zanyi a nan da zafin ranar nan kwal a kaina” Dariya ya saki har wawulunsa na gaba su ka bayyana “san Malamijo ne ya kasa Inno yau akwai cin nama.” Kamar wadda aka bawa kujerar hajji Inno ta saki dariyar farinciki ita ma. Su da nama sai dabba ta kasa. Gashi ya fada girkinta sai yadda tayi kenan. Bakin dan nata ta toshe lokacin da yake cewa ta cire musu manyan tsoka idan an soya irin na wancan karon. “Allah Ya sa wani ma ya kasa mu samu da yawa” ya kare da addua. Tsaf Malamijo ya gama jin me suke cewa ya shiga tafa hannuwa “ba amin ba, billahillazi baa min ba. Kuji min ‘yan bakinciki masu fatan tsiya. Idan ba kun jawowa kowa wallahi mahauta zan saidawa bazaku ci ba” Yaron sai ya kama kuka nan da nan iyalan gidan su ka cika tsakar gidan. Don kada ayi biyu babu Inno ta fada musu sa ne ya kasa kuma wai baza’a kawo musu kamar yadda aka saba ba. Iyaye mata suka hau jimami yaransu harda masu dan wayo suna kuka. Kuka na gaske suke ana rokonsa ya taimaka. Shi abin nasu tsoro ya bashi ma ya ja baya ya manne a jikin bango yan raba idanu. “La-e-lafi qureshin wallahi idan ku mayu ne Allah Ya fiku” yace yana tottofe na kusa dashi “ko ku matsa ko na dauko sarkin mayu yazo ya kama min ku kafin ku karasa ni. Haba ko da naji, kullum zukewa nake jiki babu wata mamora kamar ba Ali mai garken dabbobi ba” Magana yake yana kallon jikinsa yadda yake sai tsayi da uwar rama ya kula Mairama tayi murmushi abinda bata saba ba. Tun haduwarta da Zayyan take jin zuciyarta fes babu wannan mugun kuncin na gidansu. Mamaki sosai ta baiwa Malamijo don kullum ya tarasu yana irin wannan hade rai take abinta bata kuka bata bada hakuri kuma. Sai yaji wani dan dadi a ransa haka kawai. Yadikko ce ta bashi amsar maganarsa “ta ina zaka yi kiba ka tara hakkin mutane sun fi talatin a wuyanka” “Ta, ta, ta uwar zance nasan sai kin tanka. Indai sa ne zaku ci amma yau akan idona za’ayi komai har rabawar don bana so ake kwarar wasu. ‘Ya’ya dai duka nawa ne” Gidan tuni ya kaure da ihun murna ya shige ya sako silifas zai tafi gonar kafin su ma wurin aikin naman su kwashi rabonsu su boye. Yana fitowa yayi kicibus da sojoji biyu a kofar gidan da wani yasha shadda sai kyalli take na sabunta. Su kuwa sojojin ya ganesu ne saboda kayan jikinsu wanda suka yi matukar kyau a cikinsu. Sai kuma dan Ta Madina wato kanin Salame da ta aiko rannan. Gaban Malamijo yayi wata irin faduwa baki ya soma rawa. “Uhmm ince dai lafiya ko” Hadir ne ya amsa fuskarsa dauke da murmushi “lafiya kalau dama akan Mairama da Salame ne…” Ko gaisuwar da suke masa bai iya amsawa ba ya koma ciki jikinsa na bari. Wanke-wanke ya hango Mairama tana yi yayi kanta a fusace. “Ashe ba banza ba dazu kike murmushi abinda baki saba ba, wato kunje Kano idon ku ya bude shine kika kai karata wurin hakuma ko?” Dago kai tayi da sauri Salame ma ta fito daga dakinsu don maganarsa ta hasko mata su waye. Kenan batayi sa’ar rabasu ba. Shi kuwa a harzuke yake matuka ya shiga nuna su da yatsa “nasan kece mai bakar zuciya ke ki ka ingiza Salame ku ka kai karar, amma ku sani babu wanda zai kamani akanku, biki ne na barku kunje kuma san nan nace za’a kawo muku ku ci me ya rage” Kana ganinsa kasan a tsorace yake sauran matansa su ma duk sun tsure. Yadikko ce tayi karfin halin riko hannun Mairama “kin san ko su waye a wajen?” Murmushi tayi tare da sunkuyar da kanta Yadikko ta kuma maimaita tambayar. Ganin ta ki magana sai ta sake cewa “kodai surukai ne daga Kanon?” A guje Mairama ta yi hanyar dakinsu cike da kunya. Yadikko ta fadada murmushinta tana yiwa Malamijo da yayi saroro a wurin bayani. Sai gashi yana wani kasaitaccen murmushi yana kada kai. “O’oh kaga su Mairama Daso ‘yar Ma’aikin Allah. Ashe dai da farinjinin ta ban sani ba. Baku ga sojojin ba fa gwanin ban sha’awa. Ganinsu kadai ya sani shauki na tono lokacin da muka fara zuwa gwaji Jaji a can kasar Kaduna…” Hajjo ta tuntsire da dariyar rainin wayo don tasan kawai sakin kwai zaiyi duk labaransa bata taba ji yace yaje barikin sojoji ba. Hankalinsa ya koma ga Salame yana tambayarta ko ita ma da bakonta. Ciwon da yake cin ranta bai bari ita ta gwada kunyar ba kawai ta hade rai ta koma daki. Mairama ya kwalawa kira ita ta bashi tabbacin akwai wanda yake son ‘yar uwar ta ta. Sai ga Malamijo baki yaki rufowa “Ka ga Ummassalama abu yayi kyau. Allah dai Yasa mai shaddar ne naki don bazaki iya da hakuma ba, wannan sai ‘yar kunama. Bari dai na koma wajen bakin” Su na tsaye ya barsu da kokonta sai gashi ya dawo da fara’arsa har babbar riga ya doro akan kayan jikinsa. Tabarma aka shimfida musu a zure shi kuma yana daga kan wata kujerar karfe ya baza riga don ya cika ido. Gaishe shi suka sake yi Hadir yayi masa bayanin komai game da zuwansu da bukatar idan ‘yan matan sun amince ayi komai da wuri musamman saboda su basa samun damar fitowa daga barikin suyi dogowar tafiya batare da dalili ba. Yawonsu baya wuce cikin gari kada a nemesu sunyi nisa. “Ku kwantar da hankalinku Kano dai ba bakuwata bace sannan a can birnin Shehun ma akwai wanda na sani don na taba zuwa garin. Kunsan wani mai kilishi a hanyar Dange shuni? Yana nan wani dan firit haka yace min asalinsa ma mutumin Zaria ne. Kila zai iya tuna ni don naji dadin kilishinsa na sayi da yawa lokacin…” Duk sun dauka wata alaka zai ce tsakaninsu ko karin bayani sai suka ji zancen yakare, Zayyan sarkin dariya tunda yace mai kilishi dan firit ya daga kai ya kalli Malamijo sai kawai ya kunshe dariyarsa kada ya jawowa kansa. Sun ji dadi ya ce ya basu yaran sai su fara shiri. Tashi yayi yace su jira zai turo su ko gaisawa suyi tunda su Zayyan a ranar zasu koma Sakkwato. Kusan a shirye Mairama take kira kawai take jira yayin da Salame ta nade akan katifa wai zazzabi ke damunta. Mairama tayi mata sannu ta bi bayan kanwarta da ta sanar da ita Malamijo yace taje wurin bakin. Sai da tazo bakin kofar da zata sa da ta da zauren da suke, kunya ta hanata shiga. Da Hadir ya hangota, ya fara zolayarta cewa ko sune bata son gani bari su basu wuri. Kai a kasa ta rufe fuska ta shiga ta gaishesu. Salisu yana cigiyar gimbiya Salame ta sanar masa bata da lafiya. Yanayin fuskarsa ya nuna baiji dadi ba. “Ki dai taimaka min naga alama so take ta saka min ciwon zuciya” Zayyan da Hadir ne suke kwantar masa da hankali har suka fita don a bar Zayyan suyi magana da Mairama. “Mairam tafiya ba sallama ko?” Kanta a kasa ta amsa “kayi hakuri” “Nayi tunda zuwan nawa ya haifar da da mai ido gashi an bani ke” Wata matsananciyar kunya ce ta shigeta ta sake dukar da kai. Shima yasan a hanya suke shiyasa bai ja ta sosai ba yace zaiyi kokarin dawowa kafin magabantansa su zo. Yau a hanya suke suna sauri. Wata leda ya mika mata, yayi yayi, taki karba sai ya tashi ya barta a wurin. Iyakarta bakin kofa tayi musu sallama da kyakkyawar addu’ar tafiya. [02/11 7:28 AM] My 2nd Mtn: E *TUN RAN GINI…* Tana shiga daki ta sami Salame a tsaye sai safa da marwa take saboda zulumi. Yanzu shikenan abinda take so sai ta hakura dashi saboda Mairama. Gaskiya bazata iya ba domin son da take masa ba kadan bane. Kuma ma dai ai ita ce ya kamata yaso tunda danginta ne, Mairama kara kawai akayi mata. Ta nisa a cikin tunani taji Mairama tana mata magana. “Adda jikin ne dai? Ko na sanar da Yadikko a fadawa Malamijo?” Hade rai tayi ta koma ta zauna akan tabarma “ke yanzu banda rashin kamun kai me ya kaiki dadewa wurin saurayi daga zuwansa na farko? Mutumin da ba wani saninsa ki ka yi ba don iya zubar da aji.” Kwarai Mairama tayi mamakin kalaman Salame don a iya sani da kuma shaidar da za’ayi mata a gidan tafi kowa saukin kai da dadin mu’amala. To amma meye ya kawo wannan zantuka haka? Kasa daurewa Mairama tayi ta koma bakin katifarsu ta zauna ita ma. “Adda Salame wai me nayi miki ne haka don Allah? Kwana biyu kenan sai kiyi ta harara ta kina fada min maganganu” “Ji rainin wayo ki min kwace kizo kina min dadin baki” tace a ranta amma a zahiri sai ta daure tayi mumushi “gani nayi daga yin saurayi kin haukace a kansa ko tunanin idan kin bar gidan nan da wa zan zauna ba kya yi?” Jikinta sai yayi sanyi ta sake matsowa kusa da Salamen “kai Adda me ya kaiki wannan tunanin? Shine kike ta fushi…ohh ni wallahi duk kin tayar min da hankali na damu. Kema ga Salisu ba sai mu bar gidan tare ba.” Turo baki Salame tayi “dena min zancensa wallahi baiyi min ba, ke dai kinyi sa’ar Zayyan kawai kina murna” Rarrashinta Mairama ta soma yi a zatonta da gaske tunanin rabuwarsu a gaba ke damunta. Sauran kannensu mata babu sa’anninsu, maza biyar ne su ke binsu. Koda Salisu ta shiga yi tare da bata sakon gaisuwarsa ta yi tsaki da gaske dai bata son zancensa. “To na bar zancen nasa Allah Ya kawo wanda ya fishi alkhairi. Shima yace na gaisheki da jiki kuwa” “Shi wa?” Salame ta fada cikin gatsali wanda Mairama duk ta sawa ranta duk a cikin rashin son su rabu ne. Tambayar kunya ta bata ta soma inda-inda ba ta san da me za ta kira shi ba. Sunansa dai da wahala ta iya fada a yadda take matukar jin nauyinsa. Zungurinta Salame tayi da kafa tana mata wani irin kallo mai tattare da kishin da ake kokarin sakayawa. “Zayyan kike nufi?” Kai ta gyada ga mamakinta sai ta ga fuskar Salame ta washe sosai tana murmushi “ashe bai manta ni ba. Me yace? Ina nufin da yaya ya baki sakon? Ki gaishe da Salame yace ko me?” Dadi taji ganin sauyi a tare da yayarta ta kuwa biye mata tana fada mata yadda yace da zai bada sakon gaisuwar. Har dare ranar Salame motsi kadan sai ta tuna wai Zayyan yace a gaisheta, sai taji wani dadi yana ratsata. ********** Matafiya sun sauka a cikin garin Sakkwato lafiya. Ba wata gajiya su ka yi ba don sun dade da fara sabawa da wahala suna jure mata sosai. Gidansu Zayyan su ka wuce zai dauki kayansa da ya bari sai su koma barrack dinsu. Gidan yanzu dama daga Jume sai Maikudi, Rayyan da Badaru wadanda sune Zayyan yake bi dukkansu babu mai aure. Matan kuwa Fiddausi, Mubaraka da Hafsatu duk suna dakunansu. Kwasar tuwo Jume take yi Badaru yana zaune akan turmi da ya kifa sai Maikudi kwance a kofar daki yana faman firfita su ka ji sallamar Zayyan din. Babu wanda ya amsa masa cikinsu sai harara da suke binsa da ita. Dakinsa ya wuce kai tsaye ya dauko jakar kayansa a ransa yana bakincikin halayyar ‘yan uwan nasa. Ba haka ya bar jakar ba alamu sun nuna an bude an yamutsa masa kaya wurin neman abin da yake zaton kudi ne, sai dai ko kwandala bai bari a ciki ba. Ratayo abarsa ya yi ya fito ya kulle dakin. “Sai Allah Ya sake dawo damu ni zan wuce” yace daga tsaye yana dan rissinawa Jume. Maikudi ya tashi zumbur yana kallonsa, ita ma Jume ta juyo da kujerar da take zaune a kai yadda za ta fuskance shi da kyau. “Zayyanu ni zaka wulakanta a gidan nan? In baka umarni saboda ba uwarka bace sai kasa kafa ka take. Kwana nawa ina sawa a dubo ko gidan Aminun ka makale babu kai babu labari sai yau. Shine har kake da bakin cewa zaka wuce.” Baya son ya kai ga yi mata abinda zai zo yana nadama nan gaba ga darajarta na matsayin wadda ta rike shi kuma matar babansa, da idan ya fada mata wata maganar ko hanyar da ya bi bazata so ta sake bi ba. “Jume Kano naje biki ba maganarki naki ji ba” Maikudi ya dawo kusa dashi ya miko hannu kamar wanda ya bawa ajiya “ina kudin da tace ka karbo a wurin wancan tsohon munafukin?” “Yanzu aminin Baba kake kira munafuki?” “Kaga kafin ka fara dogon surutu bani kudin ka wuce bana son rigima da al’murun nan” Jume ta fada tana kara tamke fuska. Dago idanu yayi ya zube mata a kanta sai gashi jikinta ya yi lakwas. Rayyan da Badaru ma kowa ya sha jinin jikinsa. Maikudi ne kawai hankalinsa bai kai wurin ba. “Jume!” “Eyye” ta amsa a dan tosrace. “Kudi dai gadona ne ni kadai kamar yadda a gabana aka bawa kowa nasa...” “Kai, rashin kunya za ka yi mata a gabanmu?” inji Maikudi. “Idan na fahinceka Zayyanu kudin ne ba za ka bani ba saboda ban isa in nemi abu a wurinka in samu ba?” Tausayi ta bashi yadda ta hakikance akan rashin gaskiyarta bata ko tunani sai son bukatarta ta biya. Hannu ya zura cikin aljihun wandonsa ya zaro naira dari ‘yan ashirin guda biyar ya mika mata. “Ga wannan ku kara cefane” yace cike da nutsuwa, bai kuma jira cewarta ba ya fice waje inda Hadir yake jiransa. Yana fita Maikudi ya warce kudin a hannunta yana jaddada mata tasan yadda zata yi ta karbo musu ragowar idan ba haka ba shine zaiyi ajalin Zayyanu sai ya ga ta inda zaiyi amfani da kudin. “Banza shashasha to sai ka dawo, kafin kayi ajalin nasa shi zaiyi naka. Har mamaki kake bani yadda kake manta zuciyar Zayyanu da kuma kasancewara soja. Yanzu idan yasa aka kamaka duk duniya bana jin kana da wanda zai fito da kai. Nima kaina tsoronsa nake ji dan jakar uba, daurewa kawai nake ina masa barazana. Amma muje zuwa sai na dawo dashi tafin hannuna. Uwarsa ma mai suna kamar na tsuntsaye bata iya karawa dani ba” ********** Sati uku da dawowarsu a tsukun lokacin iyayen Hadir sun zo daga Kano an daidaita maganar aurensa da Zainab. Kullum ya dawo ya ishi Zayyan da labarin hirarsu ko maganar biki. Ranar da ya bishi kuwa yadda ya kula suna son juna musamman Zainab da duniya bata ganin kowa da gashi sai Hadir sai yaji muguwar kewar Mairama. Ranar lahadi ya samu da babu training sosai ya fita yaje ya sanar da Mal Aminu da mutum biyu cikin ‘yan uwan mahaifinsa game da auren da yake nema. Sunyi farinciki da alkawarin bayan ya koma Kanon ya fadawa mahaifin yarinyar zasu je bayan sati daya da zuwan nasa. Godiya yayi musu ya nemi matar Mal Aminu mai suna Gwaggo Ladi matar da ta maye masa gurbin uwa wurin kulawa da bashi abinci da sauran abubuwa lokacin da kowa ya gane gashin kuman da Jume take yi masa. Kudade ya bata da yake so a fara siyayyar kayan aure ta yadda idan zasu tafi zasu je ne a shirye saboda nisa. [02/11 7:28 AM] My 2nd Mtn: F Sai da ya nemi izinin fita na kwana biyar, da kyar kuwa bukatarsa ta biya saboda ba kasafai ake son suna yin nesa da barikin ba. Ranar da zai tafi sai da ya bi ya sallama da Captain Mustapha. Yanzu alakarsu tamkar wa da kani ga kuma yaransa sun mayar da Zayyan uba na biyu. Shi Captain Mustapha asalinsa da Katsina ne daga shi har matarsa don auren gida ma su ka yi. Asubancin fita yayi ya shiga cikin gari gidajen dangin Mal Muhammadu. Daga can ya wuce tasha sai Kano. Yayi sa’a masu kilishi sun fito ya sayawa Malamijo. Shi dai a dan zamansu na farko bai hango komai a tattare da shi ba sai barkwanci. Kwanakin da suka gabata Salame ta dami Mairama wai me ya hana Zayyan dawowa saboda Salisu ya matsa lamba kuma Malamijo ya riga ya bashi. Ganin akwai kudi yaron ya kara shiga ransa. Salame so take ta tabbatar Zayyan bazai dawo ba sai ta amince masa ko babu komai zata huta. A haka tana tsoron saurin amincewa ya dawo a bashi Mairama ita kuma ta rasa. Akwai ranar da ta tambayi Mairaman ko ta fadawa Zayyan yanayin gidansu. “Kinsan boye-boyen babu amfani gara yasan wa zai aura kada Malamijo ya nuna masa hali” Bata rai Mairama tayi “yau da kanki Adda Salame kike cewa Malamijo zai nuna hali? Ni dai soyayya bazata sa na kwashe sirrin gidanmu na kaiwa saurayi ba. Idan bai aureni ba shikenan ya gama sanin komai nawa. Kuma ko yaya Malamijo yake ai babanmu ne dole mu so a mutunta shi” Waskewa Salame tayi amma a ranta tana ganin ta sami hanyar rabasu “irin wannan sharhi ba wani abu nake nufi ba, abar maganr dai” Yau kamar daga sama sai ga dan aike wai ana sallama da Mairama inji Zayyan. Wanka take yi lokacin ta gama aikin fura Salame ce taji sakon. Jikinta har bari yake tsabagen murna ta fada dakinsu da sauri. Kaya ta sauya da sauri ta shafa hoda harda janbaki ta sako daya daga cikin kayan da Ta Madina ta dinka mata. Komai da azama take kada Mairama ta fito ta sameta. Tazo fita ta koma ta cire mukullin sif din kayansu bayan ta kwashe duk wani kayan sawa ta saka a ciki ta jefa a karkashin sif din ta fita tana dariyar mugunta. Bata yiwa kowa sallama ba don basa tsakar gidan ta fice zaure. Dama niyarta da an tambayeta ina zuwa tace wurin Innarta zata je. Kamshin turare wanda Salisu ya kawo mata zuwansa na karshe ya fara ji kafin ya ganta. Ta gumbuda turaren sosai kuwa a ransa yaji dadi ba Mairamansa bace take wannan aika-aikan. Fuska ya saki yana mata murmushi. Ta sunkuyar da kai tana ‘yar dariya don jin kanta take kamar yau take sallah saboda ganin Zayyan. “Babban bakonmu barka da sauka, yaya hanya?” “Lafiya kalau Saude ya mutanen gida” Wani abu taji ya soki zuciyarta, wato ku sunanta bai rike ba. Bata nuna damuwar a fuska ba sai ma wani kasha murya da ta tsiri yi “Salame dai ko, baka ma rike sunana ba saboda baka damu dani ba” Banbarakwai yaji zancen nata “Afuwan kada ki fadawa Mairama tace ta fasa na yiwa Addarta ko ince Addarmu laifi” “Ba wani abu ai, ita ma bata soma fada ba yadda ta matsu tayi auren nan. Allah Ya dube mu, masu gudunmu saboda Malamijo zasu sha kunya” Zayyan mutum ne mai saurin dago ina mutum ya dosa idan suna magana, yanzu ma tuni ya fahimci akwai abinda Salame take son fada masa tun hirar bata tsawaita ba. “Ban gane masu gudunku saboda Malamijo ba, ba babanku bane?” Hannu ta dora akan bakinta kamar gaske tana ware idanu “ba dai Mairama bata yi maka bayani ba? Irin haka ai da wuri ake fada saboda toshe matsala don kada kaji a waje. Idan na koma zan fada mata gara ta sanar da kai komai da wuri zai fi. Sai ka danyi hakuri ta gama aikin furar sayarwa ne ta shiga wanka” Wai shi za ta jawa rai, kawar da kai yayi abinsa yana kallon waje. Haka nan bata yi masa ba tun haduwarsu ta farko a gidan Gwaggonta da akayi bikin yaranta. Sai tayi ta wani kifi-kifi da idanu amma sau goma idan zai dago kai sai sun hada ido. Yanzu da ta ji bashi da niyar tambaya sai ta sake salo. Jan hanci yaji tana yi alamun tana kuka. Dawo da hankalinsa yayi gareta da sauri. “Ya dai?” Goge hawayen da ko digonsu babu tayi sannan ta dan tabe baki duk yana kallonta “gara kawai na fada maka don abin zai yiwa Mairama nauyi” Halin Malamijo kaf da yanayin zamantakewar gidansu ta kwashe masa. Hatta dangin mahaifiyar Mairama sai da ta kwancewa zani. Jinjina kai kawai yake yi yana kara tausayin Mairama sosai. Yanayin rayuwarta kusan daya da tashi wato dukkansu basa jindadi a gidan iyayensu. Salame sai ta dauki sauyin yanayinsa a matsayin tarkonta ne ya fara kamu ta dan murmusa “nasan rashin dangin uwa lokacin aure a kusa da ciwo…..” ta dan ciji labbanta “…uhmmm ni kaga dangin Innata suna garin nan kuma bikin da muka hadu ma nasu ne, Mairama kara kawai aka yi mata” Yanzu ya gama gane manufar wannan dogon sharhin. Kaurara murya yayi ya hade rai “Salame!....” Bai karasa maganar ba sai ga Mairama ta fito da sassarfa sanye da kayan da tayi aikin furar ta makale a bayan kyaure. “Adda” ta kira Salame tana kunyar fitowa. Zayyan ne ya amsa yana mai jindadin ganinta “Mairam yau a nan zamuyi tadin?” Kai ta sunkuyar ta sake yafito Salame sai kawai tayi gaba abinta ta fice don tasan me take nema. Kusan minti goma tun bayan fitowarta take ta neman mukullin sif din bata gani ba. Baki ta saki ganin ta fice bayan tasan kiranta take. Duk sai taji ta muzanta saboda Zayyan ma ya gani kuma baiyi mamaki ba duk da bai san me take bukata a wurinta ba. “Nima in zo bayan kyauren ne?” “A’a ina zuwa don Allah kaya zan sauya” Hannu ya daga ya dakatar da ita “dawo abinki nima nan kayan jikina sun sha wahala da kurar hanya amma na kasa hakuri ko masauki ban nema ba nayo nan” Jikinta ta kalla musamman zanin taji babu dadi. Zayyan ya matsa mata akan ta fito ba zai dade ba sai dare zai dawo. Busu-busu haka ta fito kayan jikinta masu saurin nuna datti ne dama saboda haskensu. Kanta ta sunkuyar tana kallon kasa ta gaisheshi ya amsa fuskarsa a sake. Lura yayi a takure take sai ya mika mata ledar kilishin Malamijo yace ta shiga gida sai anjima zai dawo. Yana tafiya a hanya amma zuciyarsa ta fada kogin tunanin kalaman Salame da kuma yanayin da ya ga Mairama. Yana da yakinin Salame ko dai tana son sa ko kuma kawai bata son cigaban kanwarta ne. Ko ma meye zaiyi kokarin sanin wacece Mairama Ali kafin ya koma bakin aikinsa. A cikin gidan kuma Mairama sake komawa tayi neman mukulli har ta hada gumi amma ta rasa ina ya fada. Da ta gaji da nema ga rashin sanin ina Salame ta tafi sai kawai ta cire kayan jikinta taje ta wankesu. Dije ce ta kasa hakuri tace mata me take yi da daurin kirji ta fada mata bata ga mukulli bane. “Kin tambayi Salame?” “Ta fita” “Taje gidan uban wa?” suka ji Malamijo ya daga murya yana fada. Tsoro taji da tasan zai shigo gidan a lokacin bazata fada ba. Tsawa ya sake yi mata “baki da baki ne?” Da ya ga bata da niyyar amsawa saboda rashin sani da kuma kokarin rufa mata asiri sai ya mayar da akalar tambayar ga Dije. Hannuwa ta yarfe “ina dakina ina zan sani, dama tunda yaron nan mai kudi ya fara zuwa daga birni naga take takenta so take tafi karfin kowa” “Babu mai fin karfina a gidan nan, idan ta dawo a turo min ita inji da izinin wa ta fita” Zai shiga dakinsa Mairama tayi saurin dauko masa kilishin “Malamijo gashi yace na baka” Ledar ya karba da sauri yana lekawa. Ganin kilishi yayi gari guda ya soma dariya “soja yazo kenan Mairama” Kanta ta kawar gefe tana murmushi ya bantaro mai dan girma kamar tafin hannunsa ya mika mata “gashi kema ki taba, ko ya baki?” Sai da ta karba din tace masa nasa ne kawai. Dije tuni yawu ya tsinke tayi kasake tana jiran ya bata amma sai ta ga bashi da niyya. “Bani nawa mana zan fara aikin tuwo ne” Harararta yayi yana kanne ido “iyayen kwadayi ungo kafin a tara min taragutsan nan su fara min kallon nama” Wani dan guntu ya bata ta jefa a baki a kan idon Hajjo. Fitowa tayi itama tana bata rai “ko a bani ko na gayyato jama’ar gidan nan” Bashi da zabi haka ya dangwara mata a tafin hannunta. Jefashi tayi duka a baki sannan ta daga murya tace kowa ya fito Malamijo yana rabon kilishi. Ai kan kace kwabo sun soma taruwa mutum kadan ne basa nan. Malamijo kamar ya hadiyi zuciya haka ya rinka yafita musu yana badawa ba da zuciya daya ba. Ana tsaka da kiran magariba Salame ta shigo gidan. Can wurin Ta Madina da taje bacin rai kawai ta karo don sosai take fushi da ita har yanzu saboda abinda tayi mata a Kano. Sallama tayi a dakin Mairama ta amsata ciki-ciki. Tsaki ta doka ta ajiye gyalenta ta fita yin alwala. Bayan tayi sallah ne Mairama ta tambayeta ko ta ga mukullin sif din. “Ajiya kika ban ko me?” Zuciya ta soma cin Mairama saboda ta tabbatar dazu da gangan Salame ta fita duk da tasan kiranta take yi. Wai ma me ya kaita wurin Zayyan din. “Shikenan” “Shikenan me?” Maimakon amsar fatar baki sai gani tayi Mairama tasa iyakar karfinta tana jijjiga kofofin sif din tana neman ballesu. Da saurinta ta mike don ta dakatar da ita. “Meye hakan?” “Dame yayi miki kama? Balleta zanyi tunda mukullin ya bata in nemi kayan sawa” “Saboda saurayinki zai zo?” Salame tace da kaushin murya. “Adda Salame idan wani abu nayi miki ki fito fili ki fada min amma ba ki zauna kullum kina jin haushina kina min tsaki ba. Kin sani wallahi ba don ke Addata bace ….” “Sai ki dakeni ko ba haka ba” Wata fuzga ta kaiwa kofar sai gata ta bude ta dauko kayan da zata saka bata sake kula Salame ba. Gefe ita ma ta koma tana ta hucin kishi ganin yadda Mairama ta zage tana kwalliya saboda Zayyan. “Aikin banza ki gama adon yace ya fasa tunda yanzu yasan daga wane irin gida ki ka fito.” A tsorace ta waiwayo “fada masa kika yi?” Salame sai ta tsame kafarta tayi waje. Tana zaune tana jira a raba tuwon gidan na al’ada a bata nata Mairama ta fito bayan an fada mata dawowar Zayyan. Da tazo wucewa tana jin uban tsakin da Salame taja har sai da Dije ta soma sababi ko da ita take. Hira suka yi cikin nutsuwa rabi duk shi yake maganar saboda kunya irin ta Fulani. Tana son tambayarsa game da abubuwan da take zargin Salame ta fada masa amma ta gaza. Kamar ya sani kuwa da kansa ya shiga bata labarin asalinsa da rayuwarsa ta baya zuwa yanzu. Tausayinsa taji har idanunta su ka ciko da kwalla. “Bana so yanayin rayuwar gidanku ya sanya ki fara tunanin zan gujeki ko hakan zai shafi zamantakewarmu. Gidajen da muka fito daban, sannan gidan da zamu samarwa kanmu da ‘ya’yan da nake burin ki haifa min shima daban.” Tamkar kasa ta zage ta hadiyeta taji saboda kunyar kalaminsa na karshe. Da dabara ya samu ya rinka kwantar mata da hankali da kwadaita mata irin tanadin da yake mata idan ta zama mallakinsa. Ba shi ya bar gidan ba sai tara da rabi na dare. Washegari ya sake zuwa kuma a ranar ne ya sanar da Malamijo zuwan kawunnansa idan ya koma. “Abin da nake so da kai shine ka fada musu su taho da sadakinsu ayi komai a kare. Yaran nan sun zaunu babu dalilin ayi ta jan lokaci. Budurwa kamar Mairama ta bawa shekaru shatakwas baya harda watanni ina kallonta tana kallona. Ga yayarta ita ma zan fadawa yaron nan Salisu sai ayi a lokaci guda” Dadi maganar ta Malamijo tayi masa yayi na’am da ita. Ana gobe zai koma yana jiran fitowar Mairama sai ga Salame da ta shiga tashin hankali sakamakon gabatowar aurenta da Salisun da bata so. Hanyar waje tayi a daidai inda yake zaune ta jefa masa takarda ta fita. Ba nisa tayi ba tana layin bayan gidansu tana jiran ya karanta wasikar yazo ya sameta. Layuka kadan ya karanta inda take sanar dashi son da take masa da kuma jiransa da take a bayan layi idan ya amince yazo ya sameta. Mairama ce tayi sallama sai kawai ya yayyaga takardar ya dunkuleta a hannunsa. Sun jima suna hira yana fada mata haduwarsu ta gaba ta zama tasa tana dariya a hankali Salame ta dawo kamar kububuwa. Ta kwashi awa guda da doriya tana jiransa bai zo ba. Yanzu da ta shigo takardar hannunsa ya watsa a iska ko kallonta baiyi ba. Zuciyarta kamar za ta fashe saboda bakinciki ta wuce ciki. Bahaushe ma yasan babu wanda ya isa ya sauya kudurar Ubangiji ga bayinSa shiyasa mu kan ce wai tun ran gini….Bayan duka wasu shirye shirye da hassada daga bangaren ‘yan bakinciki irin su Jume da ‘ya’yanta da kuma Salame mai son maso wani, da azahar din wata asabar aka daura auren Zayyan Muhammad Tureta da Mairama Ali Gidado. Sai kuma Salisu Lawan da Ummusalma Ali Gidado. Kowacce cikinsu angonta yayi bajinta gwargwadon aljihunsa ya yi mata kayan lefe. Ko ba’a fada ba kayan Salame sun kere na Mairamu duk da Zayyan din ma baiyi kasa a gwiwa ba, amma a haka Salame ta dauko ido ta sakawa kayan Mairama a ganinta da ita su ka fi dacewa. [02/11 7:28 AM] My 2nd Mtn: H ********** “Kasan Allah Malamijo idan naje Sakkwato haka zikau Allah shi tsinan” Fuskarsa a murtuke kamar zai kai mata duka ya tashi daga kwanciyar da yayi “ wai ni dake waye ya haifi yarinyar nan ne eyyee?” Yadikko ta galla masa harara “kaine ubanta wanda na sani da ana sakewa wallahi bana jin ko tsinken ashanar gidan nan zai so a alakanta shi da kai. Me kake yiwa yaran bayan haihuwarsu? Nan haka muka kaita gidan miji abin kunya babu wani kayan arziki wai kuma ‘yarka ce, kai da garin nan kowa ya shaida arziki gareka” “Sa ido, sa ido…kowa zaiyi ya bari tunda ba da uban mutum muke kiwon ba” “Ba sai ka zageni ba, gaskiya ce dai dole na fada maka. Mairama baka fitar da ita kunya da biki ba dole kayi bajinta ita ta fara kawo maka jika a gidan nan. Ka kuma hada da gara tunda ba’ayi musu komai ba da bikin. Salame ba don mahaifiyarta tana kusa ba itama da haka za ta tare ba garar” Malamijo ya mike yana kada hannuwa yana kumfar baka saboda an bukaci kudi “garo ba gara ba, idan sai na bada kudi kunyi mata gara zaku je don Allah kuyi zamanku na yafe. Yo dangin uwarta ma suka bace bat a doron kasa basa waiwayarta tunda ta rasu balle ku” “Laifin waye to idan bana ka ba? Kowace mace ka gani kana so saboda zalama. Kuma ba dole su bace ba. Kayi auren biyan bashi tana haihuwa kace ka saketa kuma sai sun biya rabin kudin. Tsoro yasa sun gudu bakinciki kuma ya kashe yarinya karama ta bar marainiya” Yadikko kin hakura tayi sai da kyar da sudin goshi Malamijo ya bata dubu uku da kuma tinkiya guda daya “gashi nan a tafi a kaiwa ‘yar kunama kafin na fara ganinki cikin bacci na. Ke dai da mayya ce da tuni na dade a tukunya” Warce kudin tayi a hannunsa “fadi ka kara, aradu da ina maita da tuni an dade da raba gadon ka” Hanjin cikin Malamijo ne ya kada da gaske furucinta ya bashi tsoro. Ko dai mayyar ce ne? shiyasa kullum baya gaba sai dai baya kamar kudin guzuri. ********** Kwance take akan doguwar kujera a falonta lokaci lokaci ta dago kai ta tsartar da miyau a duk inda ta ga dama tana faman yatsina fuska. Salisu ne ya shigo da langa cike da gurasa da tsire irin wanda take so. “Salame tashi kici abincin” Kallonsa tayi ta watsar tana kokarin zubar da wani yawun ya taho da sauri ya mika mata kurtun da ya ciko da kasa “zuba a nan kinji don Allah Salame na” yace da rarrashi. Kamar bazata zuba ba sai kuma ta tofa ya mayar ya ajiye jiki na rawa ya miko mata langar ta amshe ta soma ci don yunwa take ji dama. Ta dauko yanka na biyu ya saki fuska yana dariya “yau da albishir na dawo, me zaki bani tukwici?” “Rike kayanka indai sai na bada wani abu zaka fada” Baiyi fushi ba don ya saba da halinta. Bata boye masa kiyayya har yanzu da take dauke da ciki na wata biyu. Tsiyarta take tsulawa a gidan tana cin karenta babu babbaka kawai don tasan Salisu yana masifar son ta. “Mairama ta sauka yau kwana hudu an sami mace” Naman da take shirin hadiya ne ya makale mata a makoshi ta soma tari. Ruwa ya bata ko kalla bata yi ba bare ta karba. “Me kace?” “Mairama….” “Dakata malam, wannan har wani labarin fada ne?” Mamaki ya kama shi “ke, Mairama kanwarki nake nufi” Zuciyarta ce take tafasa da bakin kishi. Yanzu Mairama har ciki Zayyan yayi mata ta haihu. Saboda shi tafi wata uku Salisu bai sami kanta ba sai da ya hada da fin karfi. Rigima sosai suka kwasa kamar auren bariki tana ta yi masa Allah Ya isa. Ganin babu sarki sai Allah daga baya ta hakura ba don tana son sa din ba sai don kawai ba ta hango mafita daga kaddararren aurensa ba. Da ciki ya bullo kamar ta zare don bata kaunar komai tsakaninsu lokacin da za ta kasha auren ta nemi hanyar shiga gidan Zayyan. Indai soyayya na saka hauka, kan Salame ya dade da kwancewa akan mijin kanwarta. Kuka ne ya kwace mata mai cin rai da zuciya. Mairama ta rigata samun abinda take muradi. Salisu ya tsaya kallon ikon Allah yadda take kuka haikan. “Yanzu meye abin kuka bayan kema kina da cikin nan” a tunaninsa ko don ta riga ta haihuwa ne. “Allah Ya sauwake nayi kuka don ta rigani haihuwa” tace cike da tsiwa. Tsareta yayi da idanu “to kukan me kike yi?” Gabanta ne ya fadi ta soma inda-inda “banda abin Mairama da kwarewa a rashin kunya daga auren sai ta bashi kanta. Wannan ai zubar da mutumci ne. A lissafina sai nan da kwana hudu ma zamu cika wata tara da aure amma gashi ita ta haihu. Anya ma kuwa cikin nan….” “Ke Salame! Shiga taitayinki. Kanwar ta ki kike neman jifa da kazafi saboda wani shirmenku na banza da hofi. Na dade da kula ko sunanta na ambata ko agidan ku aka ambaceta sai fuskarki ta sauya. Idan ma wani abin ne ya hadaku ki shirya jibi zamu wuce Sakkwaton sai ku sasanta” Kallon wulakanci ta jefa masa duk da taji tsoron tsawar da yayi mata “ba zani ba idan ka matsu da ganinsu kaje kai kadai” Ransa ne ya soma baci shima “na fasa a gobe ma zamu tafi, haba yarinya mai nutsuwa da kunya baki da aiki sai na kusheta da jifanta da bakaken kalamai” “Da kasan tana da halayen kirki me ya hana ka nemi aurenta ka barni na auri wanda nake….” Tasss taji saukar mari a kumatunta sai da ta ga haske, rai a matukar bace Salisu ya nunata da yatsa “bar ganin ina lallabaki wallahi sai nayi miki shegen duka a gidan nan. Ke wace irin mutum ce ne? Kina ta abubuwa ina kawar da kai to amma tura ta kai bango tunda har jininki baki raga musu ba. Ki shirya gobe zamu tafi sannan ki tashi ki hada ruwan omo da dettol ki bi duka gidan nan ki goge min. Su bayan kofofi da kujeru duka ki tsaftace min gida ko ina warin yawu ya isheni. Idan na sake kamaki kina tofa yawu nan ba a wancan abin ba wallahi jikinki ne zai gaya miki. Tashi ki bani wuri ni” Ba karamin tsorata tayi ba ta kai mai hakuri bango. Tsoro ne da ita tun da can, soyayyar Zayyan da ta bari a zuciyarta da kyashin kanwarta su ne suka maidata haka. Jiki na rawa ta tashi yace ta dawo sai ta gama cin abincinta tukunna. [02/11 7:28 AM] My 2nd Mtn: 9 *KANA NAKA…* Shirye shiryen tarbar bakin da zasu zo suna ya kankama. Zayyan ya dage a gidan mahaifinsa za’ayi taron duk da cewa kawunansa da Mal Aminu sun ce gara ya yi a nasu saboda gudun bacin rai da ga Jume ko ‘ya’yanta. Ya riga ya gama tsara yadda zai bi da su domin gujewa hakan. Gidan yaje har daki ya same ta ta hakimce tana taunar goro. “Hutawa akeyi ne Jume? Kawarki tana gaisheki” Tabe baki tayi tana kallonsa ya zauna a kan yagaggiyar ledar dakin “kawarsu dai wadanda aka haifawa. Ni a su wa kuma?” Basarwa yayi ya tankwashe kafafu “dama alfarma nazo nema, ina son ayi taron sunan a gidan nan ne” “Dama jiranka nake naga iya gudun ruwanka tun da aka fara shigowa da bokatan fenti dazu. Ita matar taka basu da dangi ne da bazata koma gidansu ba? Naga haihuwar fari ce, ya dace ace tana gaban iyayenta. Tsabagen rashin ta ido ka barta a gidanka kuna kwana daki guda.” “Cikin masu zuwa sunan akwai matar babanta da zata zauna har ayi arba’in tare da ita. Ni zan koma wani gidan a cikin barikin kafin su gama” Maikudi ne ya shigo fakam fakam ya sami guri ya tsaya ayi zancen dashi. Zayyan ya sake fada mata yana son sauke baki da ga Nijar da kuma mutanen Sumaila a gidan nasu tunda babba ne. “Ince ko ka ga nayi kama da baiwar gidanku da zan zauna tarbar baki. Kaga Zayyanu tun wuri ka san me kake ciki da bakinka” Murmushi ta ga yayi maimakon ya tashi ma sai ya gyara zama “to babu matsala zan yiwa su Kawu magana. Sai abu na biyu nace idan an kawo kudin rakuman wace sana’a Maikudi zai fara?” A tare su ka taso masa kamar zasu zaune sh. Maikudi ya zauna a gefensa yana fara’a kamar gonar auduga, hakansa zai cimma ruwa. Jume ma sai ta saki fuska kamar ba ita ba. “An sayar da rakuman naka ne?” Maikudi ya tambayeshi da zumudi. “Eh, zasu taho min da kudin, jibi nake sa ran isowarsu” ya bashi amsa. Sai ga Maikudi ya tashi jiki na rawa “Bari na kira yayyenka malalatan banza su zo a fara gyara gidan nan, mu gidanmu da yake da wadatar dakuna kamar ramin bera, Jume yaushe zaki ce sai ya nemi su Kawu don iya tonawa kai asiri” Matsowa tayi kusa da Zayyan tana dariya “shima yasan wasa nake yi masa. Ka nemi masu fentin su zo ayi a gama da wuri sai a share dakunan ayi shimfida.” Mayar da kansa wawa yayi suna ta bidirinsu yana biye musu. Maikudi da son banza harda cewa an hutar dasu yin fenti tunda su ma baifi wata uku ya rage dukkansu su ukun zasuyi aure ba. ********** Cikin ikon Allah baki sun iso an kaisu masauki, washegari za’ayi taron suna. Zayyan ya wadata iyalinsa da duk abin da ya dace. Wani hadin kai da ga bangaren sojojin su ma sun hada masa gudunmawa sannan matayensu sun zage dasu ake komai kamar yadda su ka saba idan dayarsu ta haihu ko wani taro ya tashi. Salame da Nene Marka kanwar Malamijo a gidan zasu kwana sauran kuma duka suna gidansu Zayyan. Su Nene sun riga isowa ga yamma jama’ar gidan sun watse sai ita da Mairama da Zainab. Mami ta wuce gida Fauziyya tana fama da zazzabi. Salisu na tsayar da mota a harabar gidajen da suke jere a wurin ta fito da sauri gabanta yana faduwa ta barshi yana yiwa security din da yayi musu rakiya zuwa gidan godiya. Ciki ta shige tana fatan yin tozali da Zayyan. Sai dai idanunta akan na Mairama su ka sauka tana shayar da jaririyarta. Wani kululun bakinciki ya taso ya tsaya mata a wuya. Mairama tayi wani mugun kyau ta ciko ko ta ina. Kallo daya zaka yi mata kasan cewa hankalinta a kwance yake. Da sauri ta cire yarinyar da ga bakin abincinta ta tashi ta fada jikin Salame tana murna da tsalle sai da Yadikko tace tayi a hankali saboda yanayin jikin haihuwa. “Wayyo Adda Salame nayi kewarki sosai ashe kina hanya. Ina yayan namu?” Da kyar ta amsa “yana waje, ki tura mijinki ya bashi masauki” Tsabar murna duk ta rude ma tayi hanyar daki neman mayafi sai ta jiyo muryar Zayyan din suna magana da Salisu. Salame cikin zakuwa ta juya “bari naje mu gaisa da angon karni” Nene ce ta dakatar da ita “wa yake ta angon karni baki ga ‘yar taki ba, dawo kiyi zamanki nasan zasu shigo” Ba haka taso ba amma dolente ta zauna. Mairama ta gabatar da Zainab wadda ta tashi tana tayata hadowa su Salame abinci da sha. Daga nan Zainab din tayi sallama ta tafi Yadikko kuma ta shiga wanka. Baby tana kwance akan wani bargon yara mai kyau Mairama ta sake komawa kitchen ta soma kuka. Har wannan lokacin Salame dama bata yi karar cewa a bata ita ba bare ta dauketa saboda bata ma son ganinta har ranta. Kukan ya tsananta Mairama tana ji ta kasa cewa ta dauketa tunda ai ba kurma bace sannan tana jin nauyin ta fito ta dauketa a ga tayi rashin kunya. Nene tana da ga bandaki kukan ya isheta tana tunanin me ya sami yarinyar. Harara Salame ta jefa mata sannan tasa hannu tana dan taba gefen jikinta wai rarrashi. Daga sama ta bayan kujerar ta ga an zuro hannuwa an dauketa. Waigawa tayi da sauri idanunta su ka gane mata Zayyan Tureta. Sanye yake da khakinsa ya zura hularsa cikin wani abu da aka yiwa maballi daga kafadar rigar. Yayi matukar kyau da haske aure ya sake gyara shi. A kafada ya dora ‘yarsa yana shafa mata baya. “Waye ya taba min mamana? Sojoji basa kuka fa ‘Yar soja” “Zayyan ina wuni?” Salame tace cikin sanyin jiki. Bata san zai shigo ba da ko don ta burge shi ta dauki ‘yar. Tamkar bai ga mutum ba ya shareta ya shiga kwalawa Mairama kira. Tana tsaye dama daga kofar kitchen din duk abinda Salame tayi ta gani tunda kujerar ta bata baya ne. Mamakin wannan mummunan canjin daga ‘yar uwarta take yi. Ashe ko me ya hadasu tun kafin suyi aure bai kare ba har yana son shafar ‘ya’ya. Hawaye taji ya soma sauko mata tana kallon bayan Salame a inda take zaune kamar gunki saboda yadda taji kunyar abinda ta yiwa jaririyar a gaban babanta. Hawayen nata Zayyan ya gani ya matsa gareta da dayan hannun da yake shafa babyn ya janyota jikinsa da karfi ya rungume da hannu daya. “Kada na sake ganin kin bar min yarinya ita kadai a falo. Idan babu kowa ki goyata ki shiga kitchen din…kinji” “Kayi hakuri baza’a kuma ba, na ga Adda tana wurin ne” tace tana karbarta daga hannunsa. Salame ta juyo kamar mai ciwon wuya tana neman kalaman wanke kanta. Kamar bai ji ba sai cewa yayi “Taimaka ki hada min abinci da zan tafi dashi inda zamu kwana da Salisu. Zan kaishi yayi sallah da wanka na dawo na dauka. Amma ki fara cikawa wannan sojar ciki” Hannunta daya ta dora a gefen ido tayi masa salute “Yes Sir” Matsowa yayi yana neman sumbatarta ta goce tana dariya. Mutuwar zaune Salame tayi. Shi kuwa Zayyan da biyu yake yi don ji yayi ya kara tsanarta. Ba don ta hada jini da Mairamansa ba da sai ya saka ta a guardroom ko na sa’a daya ne ya huce kukan ‘yarsa. Da ya fita Mairama ta kawo mata sauran kayan abincin batare da ta sake yi mata magana ba ta zauna bawa ‘yar nono. “Ki kwashe ba ci zanyi ba don yanzu ba komai ke zauna min a ciki ba” Wai nan so take ta sanar da ita itama tana da cikin. Sai Mairama ta gwada mata halin matar soja da ta fara koyon yadda yake juya zance musamman idan ya fuskanci abu kake son sanar dashi da dabara don ka bashi haushi. "Adda yaya hanya? Ya zaman Kano?" Sai da Salame ta kara kallonta irin baki ji me nace dinnan ba sannan ta chanja zancen tace lafiya. Zaman kurame su ka koma har Nene ta fito tana tambayar me ya sami baby dazu take kuka. Babu wadda ta amsa mata a cikinsu duk sun daure fuska sai ta kyale su ta sa tv a gaba tana kallon tashar NTA. Zaman ne ya ishi Salame ta tashi ta shiga daki wai zata yi wanka. Mairama ta bi bayanta taji ko akwai abin da zata bukata. A tsaye ta sameta tana karewa dakin kallo tana tabe baki. "Af...ke fa gadon da Malamijo yayi mana dashi aka kawoki ko? Amma naga labulayen kamar sababbi ga TV ma a falon da firij. Kin fara sana'a ne ko Zayyan din kike tatikewa?" "Yo Allah na tuba Adda mace da mijinta har sai kinji yaya ake kudi ke fita har a gyara mata gida? Dadin zama ne kawai da iya tafiyar da miji" Ta fadi haka ne saboda gorin da Salamen ke shirin yi mata. Ita kuma Salame sai ta dauka cin fuska ne ko ta gane ta son sa. "Ki dai bi a hankali maza basu da tabbas. Canja mace a wurinsu ba wata tsiya bace" Zaro idanu Mairama tayi da mamaki. Har fatan aurenta ya mutu kuma Salame take yi? Indai haka ne dole ta kama kanta don bata ga me ta tsare mata ba da take nuna mata hassada irin haka. Kowa ya shaida mijinta yana da kudi ta rasa gane bakincikin na meye. Karfe goma na safe a gidansu Zayyan tayi musu. Anyi taron suna na kayatarwa don Zayyan ya sakar musu yadda zasu fita kunya. 'Yan uwansa mutan Agadas sunyi masa halacci duk da rashin mahaifiyarsa sun zo da yawansu tare da gudunmawa mai yawa. A cewarsu basu sami bikinsa ba dole a fanshe yanzu. Gashi jaririya ta gaji sunan 'yar uwarsu. Mutan Sumaila ma sun sha kallo ganin irin suturar da Zayyan ya wadata Mairama da su na fitar suna. Abin nasu ya burge sosai musamman da wata kanwar innar Zayyan ta kawo kayansu na gargajiya na kabilarsu ta Tamasheq ta bawa Mairama. " 'Yata ga wannan ku saka ke da maigidanki da jikarmu ayi hoto. Dashi nake son tafiya saboda wadanda basu zo ba su ganku." Mairama sai godiya take su Zainab suna tayata. Riga ce fara kamar buba ta zarta gwiwa da kadan gaban ta sha aiki da shudin zare sai zani shudi. Ga kuma sarkoki da yari duka irin nasu da abubuwan sakawa a ka. Mami ce ta karbi Radhiya yayin da wasu 'yan mata biyu kusan sa'annin Mairama su ka ja ta dakin da su ka kwana. Da taimakonsu ta shirya komai su suka yi mata. Abin hannu da na wuya da kunne harda hanci kowanne yayi mata cif. Na gashin kuwa sai da daya ta yi mata kalba kananu guda uku-uku a gefe da gefen kunnenta ta zubo mata dogon gashin irin nasu sannan aka dora mata shi ya zauna daga gaba kai kace wata sarauniya ce. Hatta fuskarta kwalliyarsu aka yi mata leben nan ya sha fenti yayi baki. Da yake fara ce ba karamin kyau tayi ba ta saje dasu. Wata guda ta soma ji daga tsakar gidan aka dora mata shudin yadi irin na zanin wani irin yafawa yadda suke yi sannan su ka rike mata hannuwa aka fito da ita. Turus tayi ga wata irin kunya kamar sabon aure da su ka hada idanu da Zayyan. Yayi kyau har bata san yadda za ta kwatanta ba. Shima kayan gargajiyar ne a jikinsa na ciki farare babbar rigar da kuma rawani duka shudi. Kanta a kasa shi kuwa ya zuba mata idanu, manya cikin 'yan uwan nasu suna ta guda. Da shirinsu suka zo da sunan yi masa nasu bikin. Taro ya kayatar da jama'a ba kadan ba duk da iyakarsu cikin gidan. Salame tamkar ta bude ido ta ganta a matsayin Mairama. Ganinsa cikin wannan kaya ba karamin sake fama mata ciwon son sa da yake nukurkusarta yayi ba. Mai hoto aka kira yazo akayi ta dauka. Gwaggon Zayyan tace suyi su uku zata kai hoton gida. Days suka dauka a tsakar gidan a tsaye tana rike da Radhiya shi kuma a gefenta. Dayan kuwa dakin Innarsa yace su shiga a kan tsohon gadonta ya zauna da 'yarsa a hannu ita kuma a kusa dashi. Daga nan ta kira danta Awwab ta dora masa kanwarsa tana tallabe da kanta daga bayansa ta dan duka aka yi musu sannan Zayyan ma ya shiga. Ranar idan ka gansu dole su baka sha'awa. Mutan Agadas har irin abincinsu sun dafa duk na bikin dansu Zayyan da murnar haihuwar Alheran Radhiya. A gidan maijego ta kwana ranar tare da danginsa ana ta bata labarin 'yan uwansu da irin yawan danginsu. Gwaggon Zayyan tace mata cikin gurbatacciyar hausarta da ace Zayyan ba soja bane gida Nijar suka so komawa dashi bayan rasuwar Mal Muhammadu. "Idan ya sami saukin aiki ku kawo mana ziyara kinji Mairama. Zayyan dan gata ne saboda yana zagaye da dangi masu kaunarsa saboda maraicin uwa. Da mahaifinsa ya amince min naso tun rasuwar Alheran na dauke shi." Hawaye ta ga dattijuwar tana gogewa shiyasa taji zuciyarta ta karye "In sha Allahu zamu zo" "Allah Ya nuna mana" Mairamu a ranar tayi kwanan farinciki da bakinciki duka lokaci guda. Soyayyar da ta samu daga wurin dangin mijinta ta tsaya mata a rai tayi matukar farinciki. Sai kuma tunanin dangin Innarta da babu wanda zata iya nunawa tace nata ne ta wannan bangaren. Sun manta da ita da shafin rayuwarta saboda rashin uwa da tsanar da suka yiwa Malamijo akan rikon sakainar kashin da ya yiwa 'yar uwarsu a gidansa. Asubar fari aka fara tashi saboda masu shirin komawa. 'Yan Sumaila ne farkon tafiya aka bar Nene zata zauna wanka idan sunyi arba'in su tafi Sumailan tare. Mutan Agadas ma kaf sun gama shiri wai basa son dorawa Zayyan nauyi idan suka cigaba da kwanaki. Kawunnansa biyu ne a cikin tawagar Ghoumar da Sidi. Shatara ta arziki suka yi masa kyautar kudi da irin abin amfani nasu na can. Kamar kada su tafi haka Mairama taji har kofar gidan inda bus guda biyu zasu daukesu tayi musu rakiya. Daga nan gidanta ta koma tare da Yadikko da Salame su ma a ranar zasu wuce. Manya akwai kaifin tunani da hangen nesa. Cikin kankanin lokaci Nene ta gane manufar Salame akan Zayyan. Tasha mamaki ba kadan ba saboda a da tana yi mata kallon wadda zata iya sadaukar da komai domin farantawa kanwarta. Ashe abin ba haka yake ba. Ta ciki na ciki ne. Jan bakinta tayi ta tsuke bata tona ba sai dai ta jasu su biyun tayi musu fada akan sabon yanayin alakarsu. "Nene gara da ki ka kula, ki tambayeta idan na mata laifi ne na bata hakuri" Kallon Salame Nene tayi ta dauke fuska tare da janyo jakar kayanta tana shan kunu. Nene tace "Salame idan ma da sabani na kula kece kike jansa. Tun zuwanki ina lura dake ko da wasa wallahi baki dauki Radhiya ba." Saurin kallon Mairama tayi don kuwa hakan ne. Mairama tuni ta gane shiru kawai tayi. "Nene bana jindadi tunda nazo garin nan shiyasa. Mairama Allah Ya baki hakuri...shikenan ko" tace a kagauce tana son fita daga dakin. "Juna biyun shine zai sa ki kasa daukar 'yarki? Ki dai yiwa kanki fada don rayuwa bata da tabbas" Mairama bata ma tanka ba ganin za ta rana musu wayo. Da zasu tafi Salisu ya kawo kudi ya bayar a sayawa Radhiya kaya harda cewa inji mamanta Salame. Godiya suka yi masa sun san kuma kara ce kawai yayi amma babu wani inji Salame. Sun shiga gidan Nene ta goya Radhiya ta shige daki wai garin akwai sanyi. Ga gida mai daki daya tana rufo kofar Zayyan ya rungume Mairama harda ajiyar zuciya. "Na wahala Mairam, na wahala sosai" "Taron jama'a ko?" Tace tana kokarin kwace jikinta kada Yadikko ta fito. "Wane jama'a, a kaina suke? Rashinki ne ya addabeni." Murmushi tayi ta sunkuyar da kai ya dago habarta "dadina da mutum kunya. Yaci ace mun wuce wannan matakin fa, ga 'yar soja can kina gani" "Ni dai kazo ka tafi kada ta fito ta sameka" "Kin yarda zaki yi min irin kwalliyar jiya idan ta tafi?" "Na yarda" Rungumeta ya sake yi sosai "Ina sonki Mairam, shigowarki rayuwata ya sanyani farinciki mara misaltuwa. Karo na farko naga da dangin Innata su ka zo da yawa haka saboda ni. Kuma duk a dalilinki ne da kyautar Alheran da kika yi min. Nagode" "Ina fatan Allah Ya bani ikon cigaba da kyatata maka Sojana. Kayi min komai a rayuwata. Ka rabani da kunci da bacin rai. Ka zame min miji, aboki kuma dan uwa" Kashe mata ido yayi "ina ma daga ni sai ke a gidan nan kike wannan kalaman" Ta gano manufarsa ta shiga dariya a hankali. Kofar dakin aka taba ya tashi a guje ya fice ita kuma ta dake fuska kada Yadikko tace me suke yi. [02/11 7:28 AM] My 2nd Mtn: G *….TUN RAN ZANE* Hakan take domin kuwa yau ne za’a kai amaren dakunansu. Dakin Yadikko aka tarasu Malamijo ya shigo zaiyi musu nasiha ta karshe safiyar lahadi. Kallonsu yayi daya bayan daya sannan ya juya wurin Yadikko. "Me ake cewa ne idan za'a kai amarya?" "Ko addu'a ai ka yi musu" Hularsa ya turo gaba "abi miji sau da kafa shine shawarata gareku. Banda tsiwa ko rashin kunya sannan ayi ta hakuri. Duk wadda ta kaso aurenta babu abinda ya shalleni ah to. Allah bada zaman lafiya ku tashi ku tafi kada ayi dare Mairama tana da nisa. Birnin Shehu kwai dan karen tafiya daga nan kamar za'a ya da shege" Wannan magana ma sai da ta taba ran Salame. Babu wanda ya damu da cewa ita ke son Zayyan har ake wani zancen nisan garin. Haka su ka fito suna ta kuka, kowacce da abinda take yiwa. Salame kukan rabuwa da masoyi take yi don tasan an riga an cuceta an rabata da Zayyan. Mairama kuwa kukanta bai wuce na rabuwa da 'yar uwarta da gidan nasu duk da ba dadinsa suke ji ba, sai kuma fargabar sabuwar rayuwar da zata fara. Akori kura biyu ke biye da motocin daukar amaren na kayan dakinsu da aka samu Malamijo yayi. Gadaje daidai ne da saitin kujeru da kuma kayan kitchen. Gidan Salame aka fara tsayawa a Kofar na'isa babban gida ne mai bangare uku na Salisu da 'yan uwansa. Yadikko da Hajjo su ne zasu tsaya a nan ayi jere tare da 'yan uwan Ta Madina. Basuyi mamaki ba ganin har sunyi jeren katon gado a daki daya da kwaba da madubi masu kyau daidai da zamani wanda Ta Madina da 'yan uwanta suka yi. A falon ma sunyi mata kujeru manya da suka fi na wajen Malamijo an malale kasan da leda mai ado da ta dace da labulen da suka yi mata. Kayan da suka zo dasu wani daki guda aka nuna musu suka jera kujerun da gadon ya dauke su tsaf saboda ba wani yawa garesu ba. Kannen Ta Madina suna aiki suna yabawa su Yadikko magana wai kudin Malamijo bai tsinana musu komai ba. To su din ma basu tanka ba tunda idan anbi ta barawo abi ta mabi sawu. Dije da Inno su ne jagora a tafiya kai Mairama nata gidan. Yamma likis suka isa Allah Yasa ba wata gayya ce ba basu fi su biyar ba. Sanin cewa idan ya kaisu gidansu Jume sai ta saka shi jin kunya ya nemi alfarmar kanin babansa zai saukesu a gidan kafin su yi jeren. Nan su ka kwana ana ta tarairayarsu. Mami matar Captain Mustapha ita ma tayi abinci mai yawa suka je aka yi taro a gidan. Jume ko zuwa bata yi ba amma 'ya'yanta mata sun je suna ta yada magana wai kalen dangi ya guji nasa asalin. Haka nan 'yan uwan Mal.Muhammadu sun je da yawansu. Da safe Hadir ne yaje daukosu aka kaisu gidan da aka bawa Zayyan a bangaren gidajen da suke cikin barikin. Daki daya ne kato da bandaki a cikinsa sai falo madaidaici da kitchen karami. Bata zo da komai ba sai iya kayan da Malamijo yayi mata. Anyi jere lafiya a daren aka kawo amarya dakinta su kuma suka koma Sumaila washegari. Zaman Zayyan da Mairama abin burgewa ne da sha'awa ga duk wanda ya sansu kuma yake mu'amala dasu. Babu abinda ya rageta dashi ta fannin soyayya da kyautatawa. Ita ma a nata bangaren tana binsa sau da kafa da biyayya da tattali. Yanayin gidansu yasa ta iya girki bashi da matsala ta wannan fannin ma. Satinsu biyar da aure Zainab ta tare matar Hadir. Mami dadi ya isheta ga hausawa 'yan uwanta a kusa duk da nasu gidajen suna bangare daban. Sunfi girma da kyau. Su Mairama kuwa layinsu daya da Zainab. Hade kai suka yi suna zaman gaskiya da bawa juna shawarwari. Mami ce babba amma Zainab duk ta fisu wayewa. Mairama kuwa dama albarkacin boko ta san wasu abubuwan amma kifin rijiya ce. Idan suna hira abin dariya, Mairama kana jin hausarta zaka gane bafillatana ce, Zainab sakkwatanci ziryan ita kuma Mami Hausar Katsina. Yau juma'a Mairama tana cikin girki kafin dawowar Zayyan taji sallamar Awwab. Kowa yasan dan gidanta ne na gaban goshi. Zainab har ta gaji da mita ta kama kannensa Zahra da Fauziyya a matsayin nata. Kitchen din ya shigo ya sameta tana yanka salad. "Anti kawo in yanka" "So ka ke Anti Zainab ta shigo ta soma tsokanarka ko" tace tana murmushi. "Mami tace in gaisheki kuma zata zo kiyi mata kalba anjima" "Kaje kace mata nace sai ta shigo sannan ka dawo ka ci abinci" Fita yayi zai tafi ya ga ta biyo bayansa a guje ta shige bandaki tana kakarin amai. Awwab ya rasa me zaiyi sai kuka yana mata sannu. Ita ke fama da matsananciyar tashin zuciya da amai kamar zata fitar da kayan cikinta amma kuma ita ke bashi hakuri saboda yadda ya gigice mata. "Awwab ka dena kuka mana" tace cikin rashin kuzari. Kuka yake sosai "to ki dena aman" "Na gama muje ka zuba abincin idan kaci sai ka tafi" Kallonta yayi tana dafa bango tana daga kafa da kyar. Hannunta ya rike har kan kujera yace "In fadawa Mami ko Anti Zainab?" Da sauri ta dakatar dashi "a'a kada ka fadawa kowa na ji sauki" "To kiyi dariya in gani" Dariya ya bata ya kafeta da ido wai tayi dariya. Motsin mutane suka fara ji daga waje ya tashi da sauri ya bude kofar. Zayyan ne da wani security soja sun kinkimo katon kwali ga wasu kwalayen biyu kuma a kasa daga gefe. Yana ganin Awwab yace ya je ya fadawa Mairama ta koma daki zasu shigo da kaya. Ta ji me yace kafin Awwab din ya dawo ta koma ciki ta kwanta. Suna shigo da kayan ya fadawa Zayyan tana amai. Nan fa hankalinsa ya tashi ya bishi dakin bayan sun gama shigo da kayan. A kwance take tana jin ya shigo ta tashi zaune. "Mairam me ya same ki?" Sai da ta harari Awwab ta bashi amsa "ulcer ta ce ta tashi tun dazu da na sha coke kirjina ke suya" "Shine baki taba fada min kina da ulcer ba suk sati nake ajiye miki crate din minerals? To anyi an gama" Bata da wata ulcer a iya saninta amma ta ki jinin asibiti. Kitchen din yaje ya zubo abinci. "Nasan baki ci ba, tashi" Wani aman taji ya taho mata daga ganin abincin ta daure "Awwab baici ba ka bashi zan ci anjima" "Nima bazan ci ba sai kinci" Awwab din yace yana marairaicewa. Zayyan ya janyo hannunsa ya zauna a kusa dashi da kyar ya samu ya karba yana ci yana mata hira. "Kayi min kwacen mata kirikiri yaron nan" Mairam ta soma dariya da Awwab ya dage sai ya fada masa me yake nufi. Sai can yamma ya tafi ya fadawa Maminsa bata da lafiya. Taso zuwa amma tunda Zayyan yana gida sai ta hakura sai gobe. Sai dare Zayyan ya bude kwalayen da suka zo dasu. Daya firinji ne madaidaici mai kofa daya amma da freezer daga sama. Sai kuma TV da bidiyo duka sababbi. Mairama godiya harda kuka don murna. Bayan kwana biyu kullum tana fama da amai da jiri ya kaita asibiti aka basu tabbacin ciki ne da ita. Tamkar ya hadiyeta don farinciki. Gani yake yanzu zai sami abinda zai kira nasa, jininsa sosai. ********** Lokaci yana tafiya al'amura suna faruwa garesu. Captain Mustapha ya sami karin girma zuwa mukamin Major bayan ya dawo daga wani aiki da aka tura shi Warri. Zayyan da Hadir kuma sun zama Lieutenants. Cikin Mairama yana da wata shida amma idan ka ganta sai ka rantse bazata kara kwana ba zata haihu. Su Mami sun gama sadakarwa ‘yan biyu ne a cikin. Bata wani laulayi sosai sai cin abinci akai akai tayi bulbul ta sake kyau da cikowa. Kwakkwaran motsi idan tayi Zayyan ya rinka cewa yaya akayi. Zainab ma cikin gareta wata uku amma ita laulayi yake saka ta don bata iya komai yanzu sai kwanciya duk ta rame abin tausayi. Mazajensu na fita suke tarewa a gidanta su taimaka mata da aikin gida. Mami tayi ta kokarin hana Mairama amma bata ji, tafi ganewa motsa jikin dama kuma haka ake so ga mai juna biyu. Yau litinin suna tare a gidan Zainab su Awwab suka dawo daga makaranta. Tun da suka ga gidan a rufe sun san inda Maminsu ta tafi sai suka bita. A falo suke zaune suna hira yau Zainab din jikinta da kwari ba kamar kwanaki ba. Kowa yana cin abinci an hadawa yaran a tray karami na silver iyayensu su ma sun hada tare. Zainab ce ta kula da Awwab gabadaya idanunsa suna kan Mairama. Idan ta yamutsa fuska sai yayi kamar zaiyi kuka. “Awwabu ya aka yi ne kake ta kallon mamanka?” “Anti baki ga cikinta ba kullum yana kato kamar na maman Ebere” Mami ta tuntsire da dariya “kai kuma baka son cikinta yayi irin na maman Ebere din ne?” Ya gyada kai “saboda fashewa zaiyi watarana, haka Ebere tace na mamansu ya fashe a asibiti.” Zahra ta kai masa bugu a kafada “Kai Hamma haihuwa zatayi fa mu sami baby” Hamma shine sunan da Mairama tace su rinka kiransa dashi don da fari Awwab kawai suke cewa. Maminsu ya kalla a tsorace “kinji tana rashin kunya Mami, ni dai ba ruwana” Tsokanarsa Zainab ta shiga yi tana cewa Mairama danta yakware a wautar ‘yan fari. Da abun ya ishe shi sai ga hawaye Zahra da Fauziyya aka sami na yi. Mairama ta janyo shi kusa da ita. “Kyalesu baby zan dauko maka a asibiti idan nawa cikin ya fashe kai kadai zaka rinka dauka.” Wata dariya ya saki da ta kara masa kyau da nuna kuruciyarsa yana murna, har da yiwa su Fauziyya gwalo. A haka rayuwarsu take tafiya komai nasu cikin aminci tamkar ‘yan uwa na jini. Ranar da nakuda ta kama Mairama Zayyan sun tafi gidan gwamnati shugaban kasa zai kawo ziyara. Nauyi da kunya ya sanya ta kasa fada masa tun gabanin asuba da ta fara ciwon har ya fita. Gashi abu yafi karfinta zamani ba na waya ba bare ta nemi taimako. Allah ne ya kawo mata Awwab tana cikin wannan matsanancin halin ta daure tace yaje gida ya kira Mami kuma ya tabbata ta taho yanzun nan. Ya kusa shekara tara a lokacin shiyasa duk da bata fada ba jikinsa ya bashi ba lafiya ba. A guje ya koma gida sai gasu cikin mintuna kalilan. Tana ganinta tace ya fita ta shiga daki ta taimaka mata su fito kawai ta fara nishi. Mami ta san babu yadda zatayi tun da ta hango kai yana neman fitowa a take Allah Ya sako mata karfin zuciya ta karbi haihuwar santaleliyar yarinyar da Mairama ta haifa. Tubarakallah yarinyar akwai girma da kiba taci ta koshi tun a ciki ga kyau. Kukan da ta chanyara ne ya sanar da gidan da yake jikin nasu an sauka. Matar gidan bayerabiya ce suna kiranta Maman Dolapo ta shigo da sallamarta domin su ma musulmai ne. Awwab aka tura ya kira Zainab itama tazo suna ta murna aka dora musu ruwan wanka. Yarinya tana ta wutsil wutsil kakkarfa da ita. Mami girman yana gareta ita ta yiwa Mairama wanka. Jaririya kuwa Maman Dolapo ta roki alfarmar a barta tayi mata irin nasu na yarbawa. Babu wanda ya hana saboda zaman mutumci suke yi da ita. Sun kuwa ga wanka ba irin wanda suka saba ba. Ta wanke yarinyar nan sosai ga mamakinsu harda manja mai kyau ta dauko daga gidanta ta shefe jikin yarinyar ta mitstsiketa sosai sannan aka fara wankan da kyau ana fitar da datti da maikon manjan. Ko da ta gama yarinya kana tabata jikin nan subul ta kara wani haske kamar jini ya fito. Lallausan kayan sanyi aka sanya mata lokaci na damuna sannan akace Mairama ta bata nono. Nan fa ake yinta kunyar jama’a ko karbarta ta kasa. Zainab ta kamata ta maidata daki. Zata rufe mata kofa Awwab yayi kekam dole ta barshi ya bi bayan mamansa ana musu dariya. Babu abinda makota basu yiwa Mairama ba. Daki ta shiga tayi kukan rashin dangin uwa da basu damu da ita ba. Da kanta ta nemi Zayyan akan bata son zuwa gida wanka saboda ta sani ba wata kulawa da zata samu. Bayan auren nasu sunje sau daya bata ji dadin gidan ba ko kadan. Wani kallo na kyashi ake watsa mata, Yadikko ce kadai mai janta a jiki. Malamijo kuwa zubar da girma yayi gaban Zayyan yana fada masa yadda yake cikin mawuyacin halin kula da iyali. Allah Yasa sunyo musu tsaraba irin ta Sakkwato amma duk da haka sai da ya bashi kudi. Kurewar lokaci yasa basu tsaya a gidan Salame ba. Abin da bata sani ba da gangan Zayyan yayi haka don ko kadan baya kaunar yadda Salamen take yiwa matarsa ita kuma bata gani. Ba su suka dawo gida ba sai daya saura na dare. Lokacin kowa ya watse hatta Mami ta tafi saboda yara sun fara bacci. Mairama da jaririyarta ma baccin suke jiki ya gaji ga wankan da suka sha. Ko ina a gyare tsaf gidan ya bude kofar dakin a hankali don kada ya tasheta ko fitila bai kunna ba. Kayansa ya cire yaje yayi wanka ya fito yana komai a nutse don baya son damunta. Duhun dakin yasa garin neman robar mai ya tunkudu wani abu daga kan madubin ya fado da karfi. Karar ce ta tashi baby din yaji ana inya inyaa. Hanyar kofa ya nufa da fari ya ajiye sojancin na wucin gadi, sai yaji muryar Mairama tana cewa shhhh. Da mugun sauri ya kunna fitila idanunsa a kan gadon. Kyakkyawan gamo yayi. Masoyiyarsa abar kaunarsa ya gani tare da baby kunshe cikin shawul fari tas. Zuciyarsa ce tayi wani irin nauyi ya tako gaban gadon a hankali ya zauna a gefenta. Murmushi ta sakar masa kafin ta dora masa jaririyar a kan hannuwan da ya miko mata. Rungumesu yayi tare yana fidda numfashi da sauri. Mairama sai ta soma hawayen farinciki ta kara shiga jikinsa yana yiwa baby addu’a. Sun dauki lokaci a haka kafin ya bude fuskarta tana tandar baki. “Yunwa take ji ko?” ya kalli Mairama Karbarta tayi ta juya masa baya zata shayar da ita ya hawo gadon ya zagaya gabanta “kada ki cuceni da kunya” Ba yadda ta iya yana ta kallonsu cike da sha’awa kamar wani zai ce ba nasa bane. Bai iya tashi ba har ta gama ya ga babyn tayi bacci ita ma idanu sun fara rufewa. Kwanciya ya gyara musu ya dauko darduma ya shimfida yana nafilar godiyarsa ga Allah. Duk gajiyar da ya kwaso ranar babu wani bacci da ya iya yi sai gadinsu har asuba tayi. A masallaci Major Mustapha da Hadir su ka yi masa barka tare da sauran abokan aikinsu ana taya shi murna. Papa Dolapo ya tsokane shi wai Allah Yasa dai ba mai kiriniya bane kamarsa akayi dariya. Aikinsu bai kare ba zasu koma gidan gwamna. Kafin su tafi Major Mustapha da Hadir su ka je gidan ganin baby da kuma yi mata addu’a. Zayyan ya dan taba Hadir yana yi masa magana da ido. Ya san zancen shiyasa ya dubi Major din. “Sir kaine zaka rada mata suna fa, kayi mata huduba” Wani iri yaji yadda yaran nan suke matukar girmama shi tamkar yayansu na jini “wane sunan zan saka mata?” Shiru Zayyan yayi sai ya koma ciki da sauri wurin Mairama a daki. “Mairam bamu tsayar da shawarar suna ba ga Major can yana jira” “Sunanta Alheran” tace tana gyara daurin zaninta. “Nace sunan Innarmu ta Sumaila zamu fara sakawa” “Don Allah Sojana sunanta Alheran, idan na sake haihuwa sai a saka sunan Innar” Muhawara suke yi sosai ya gaji ya karbi nata “baki da wani suna da kike son a saka mata? Suna biyu nake son a saka” Sarai ta fahimce shi, a dole yana son bata dama ita ma ta sanyawa yarinyar suna. Sai dai duk yadda take son saka sunan innarta tana ganin shi yafi dacewa da ya fara sakawa. Bata yi dogon tunani ba tace “Radhiya”. Murmushi kawai yayi ya fita ya sanar da Major sunan ‘yarsa Alheran Radhiya Zayyan Muhammad Tureta. Hadir yace “mutumina wannan sunaye haka” “ ‘Yar soja ce, ya kamata a komai ta fita daban” ya bashi amsa yana magana a hankali kada a ji. Major Mustapha ya gama yi mata huduba sannan yace ya maidata ciki suyi shirin tafiya bakwai ta kusa. Kwanaki hudu da haihuwa duk wanda ya kamata ya sami labarin haihuwa daga danginsu ya sani. Tasha Zayyan yaje ya bada sakon wasika zuwa ga Kawunsa Ghoumar domin a sanar da sauran dangi abinda aka samu. Sai wasikar ta isa akan gaba suna shirin zuwa saboda aurensa da yazo da gaggawa basu sami damar halarta ba. [02/11 7:29 AM] My 2nd Mtn: ***********10 Kyakkyawar kulawa da gyara Mairama take samu daga wurin Nene Marka. Ita da Zainab da Mami shakuwarsu sai gaba take kara yi. Idan kaga Awwab baya gidan to makaranta ce ta tsare shi ko dare ya tafi yayi bacci. Amma kullum yana wurin Mairama da kanwarsa Radhiya. Zahra da Fauziyya suna shan gori yayi ta cewa su Antinsu bata kawo baby ba har yanzu. Idan ya fadi haka Zahra sai tace ai nata cikin ya kusa fashewa ne su ma bazasu bari ya taba musu baby ba. Zayyan ba karamin kewar matarsa yake ba. Ko yaya Nene ta dan bada wuri sai ya faki ido ya rungumeta yana fada mata yadda yake kewarta da matsuwa ayi arba'in dinnan kowa ya huta. Jaririyarsu Radhiya ta kara yin bulbul gwanin sha'awa. Idan kayi mata kallo daya sai ka rasa wa ta debo cikin iyayen. Bafillatanar mahaifiyarta ko sojan babanta da yake surki tsakanin mutanen Agadas da na Tureta. Yarinya ce mai matukar shiga rai musamman idan tayi murmushi gefen kumatunta na dama ya lotsa. Awwab har yatsa yake sakawa a wurin don kawai tayi masa murmushi. Ranar da su ka cika wata biyu Zayyan ya kwashesu a motar haya sai Sumaila. Mairama bata taba tunanin zata yi kewar gidansu ba sai yanzu. Sun isa yamma likis 'yan uwa ana ta tururuwar ganinsu. Malamijo yana jin isowarsu daga gona ya zari takalmansa ya yo gida. Fadi yake 'yarsa mai auren soja ce ta iso tare da jikarsa. Abin arziki kaza guda ya bayar irin 'yar sati goman nan aka yanka Yadikko ce da girki tayi musu shinkafa da miya. Daki aka gyarawa Zayyan ya kwana. Da safe abin mamaki sai ga Salame wai bazata iya jiran su iso gidanta ba tana kewar Radhiya. Mairama taji dadi balle da ta ga yadda take haba haba da Radhiyan harda su goyo duk da ana hanata saboda nata cikin ya fara fitowa. Zayyan dauke kai yayi saboda shige masa da take yi tana ta so ko magana yayi mata. Allah sai Ya dauke hankalin Mairama daga garesu bata kula ba. Kwanansu biyu sannan su ka wuce Balan a karkashin karamar hukumar Gaya inda gidan Nene yake. Tana da kishiya guda daya mai yara shida. Maigidansu manomi ne babu wani kudi sai rufin asiri. Irin kyautar da Zayyan yayi mata Mairama kanta tayi mamaki. Nene Marka harda kuka tana masa godiya. "Nene mune da godiya, Allah Ya saka da alkhairi. Idan ta sake haihuwa ke zaki dawo ko?" Mairama ta tashi daga wurin da sauri saboda kunya. Nene tayi masa dakuwa tana murmushi "kuji min dan kaniya, wato a gaban nawa kake rashin kunya ko Zayyanu" "Fada nayi fa saboda kada ace wata daban ce za ta zo." Tare su ka yi dariya don ta saba da barkwancin surikin nata. Kofar dakin ta kalla ta tabbatar Mairama tana wurin kishiyarta sannan ta dan matso fuskarta babu alamun wasa "Zayyanu nasan kana sane da son da Salame take yi maka" Gabansa ne ya fadi ya dago kai yana kallonta da kallon kofa "Nene ki bar zancen nan, yau ko Mairam zata fadi ta mutu bazan auri Salame ba. Matar da aure bai hanata nunawa mijin kanwarta soyayya ba" "Tun yaushe ta fara son ka?" "Kafin muyi aure...don Allah bana son kowa yaji. Ni dai babu abinda ya taba hadani da ita" Hankalinta taji ya kwanta "nagode Zayyanu. Ka rike min amanar Mairama. Ga maraici ga rashin dangin uwa har yau mun rasa a wace rugar ma suke zaune. Duk tsiyar Malamijo yana ta kokarin nemansu domin ya faranta mata. Salame kuma ka barni da 'yar banza. Idan ta nemi tada muku hankali da kaina zan gyara mata zama don ba gagararmu tayi ba" Kafin azahar sun koma Sumaila inda ta sake kwana biyu suka bar garin bayan ihsani mai tsoka da ya yiwa Malamijo da matan gidan. Mairama har mamakin ina ya sami kudi haka takeyi saboda ita tasan duka duka albashin nasu babu wata tsokar kirki. Sun baro Sumaila tana sa ran za su wuce Sakkwato sai gani tayi sun shiga cikin Kano zuwa wata unguwa yana yiwa dreba kwatance. Gaban wani gida zubin zamani a wancan lokacin mai kyau da tsari tun a waje aka ajiye su. Mukulli ya dauko da ga aljihunsa ya bata yana dauke da Radhiya. "Bude mana da sunan Allah" Kallon tuhuma take masa yayi murmushi da ka yayi mata alamar ta bude. Ba musu ta bude yana cewa ta shiga da Bismillah. Farfajiyar gidan tana da dan girma daidai mota guda daya. Sai kuma ainihin ginin wanda flat ne gidan. Yana gaba tana biye dashi zuciyarta da tarin tambayoyi har ciki. Wani korido su ka fara bi a karshensa kofa take inda suka tarar da katon falo ga kofofi a ciki. Daya bayan daya suke shiga yana mata bayanin. Kitchen, dakuna hudu, store da kuma bandakuna ko ina da fenti amma babu kaya. Daki daya ne aka shimfide da leda ga katifa sabuwa da filo biyu sai zanin gado a cikin ledarsa ko budewa ba'ayi ba. "Sojana ina ne nan?" "Mairam ga gidan mijinki na halak yau kin shigo" "Gidanka ne nan?" Takowa yayi gabanta ya hadeta da Radhiya ya kankame. "Gidanmu dai Mairam" Zaunar da ita yayi ya mata bayanin kudin gadonsa da ya narkar a wannan gini domin inganta rayuwar iyalinsa. Ya zabi zuwa Kano saboda gujewa fitina daga bangaren su Jume. Dama yanzu matsanancin fushi suke yi dashi saboda an gama taron suna basu ga komai ba. Da Jume da tado zance yace gida dai shima na mahaifinsa ne, idan basa son ya rabesu a raba gado ko dakin mahaifiyarsa a bashi. Sunyi rigima ba kadan ba ya fito musu gar da gar dinsa a soja mara daukar raini ko kadan. Suna ji suna gani dole suka hakura da haram din da suka kwallafawa rai. Addu'a ta rinka jerowa yana amsawa daga nan yace to fa ta shirya jiya da ya taho cikin Kano siyayya yayi musu yana so ko sati suyi a gidan kafin ya koma aiki. Kitchen ta leka ya siyo karamin risho, tukwane biyu da yan kayan bukata. Wani sabon shafin amarci su ka bude a gidan ga diyarsu a gefe tana samun kulawa. Wasa-wasa kwanansu goma sha biyu sannan su ka fara shirin komawa Birnin Shehu. Duk yadda taso kuwa yaki kaita gidan Salame don baya kaunar duk wani dalili da zai sa su hadu. ********** Watansu biyu da komawa Zainab ta haihu. Sai dai ita a gidan iyayenta ta zauna su Mairama da Mami ke zuwa kullum har akayi suna. Jariri yaci sunan kanin baban Hadir da ya rasu gabanin haihuwarsa Ibrahim. Rayuwar wadannan bayin Allah haka ta cigaba da tafiya cikin so, yarda da aminci. A kowane mataki su na kokari wurin ganin sun tsayawa juna cikin dadi ko akasinsa. Da Salame ta haihu ya barta taje ta kwana hudu a Kano inda ta rinka fuskantar Gadara da wulakanci daga wurin yayarta ta. Da yake ta fara sabawa da wannan bakon hali sai ta daure zuciyarta don kada ayi batacciya. [02/11 7:29 AM] My 2nd Mtn: ....ALLAH NA NASA 11. "Ummin Awwab me yake damunki ne kwanakin nan sai wata rama kike yi kamar wadda za'a yiwa kishiya" Dago kai Mairama tayi jiki a sanyaye "Mami ni kaina na rasa gane dalilin wannan rama. Kuma ke shaida ce ina cin abinci sosai" "Kinbi kin dashe kinyi fayau. Jiya ina ji baban Radhiya yana fadawa Hadir wai kinki bari ku je asibiti. Baki ga yadda ya damu ba fa" Mairama tayi shiru ita kanta ramar da take yi tana damunta. Dadinta ma dai Radhiya kullum kara habbaka take. Suna wannan hirar Fauziyya ta shigo da Radhiya tana nishi anyi daukan rungumarni mu fadi. Kafin su shigo kukan Radhiyan ne ya isar da zuwansu. Mairama ta girgiza kai tana takaicin wannan kukan banza na Radhiya. Tana jaririya babu ruwanta amma yanzu rigima da kuka ga fada duk ta iya. Idan ta raina girman mutum ya dauketa sai yakushi tana doke doke duka wataninta tara a lokacin. Zayyan dariya yake yace 'yar Soja bata daukar raini. Wasu lokutan kuma sunanta na gaskiya yake kira idan yana jin nishadi. Har ta gane indai taji Alheran tasan babanta ne. A cinyar Mairama ta ajiyeta ta kalli uwar tasa dariya. Zainab tace "kunji min mara kunya ko? Mu da take gani kullum yanzu dariyar ma sai mun roka. Dadinta dai har Awwab bata yiwa" Homework yake yi a gefe yana jin tsokanar da ake masa ya taso ya kinkimeta yana cewa "Ummi wallahi tayi nauyi da yawa ki dena bata abinci" Me zasu yi banda dariya kuwa. " to sarkin wauta, an taba hana mutum abinci saboda kiba ne?" Cewar Mami Shi dai bai ga aibun maganarsa ba ya dauketa gashi siriri sai tsayi da yake faman yi ya tafi dakinsu Zahra. Kayan wasa ya baje mata yana cewa sai tace Ummi da Daddy. Gajiya tayi da wasan ta soma rigima sai ya dauketa. Duk da haka kukan take masa ya sabata yana haki "gaskiya kin fiye kuka Alheran dinnan" Kamar taji me yace kuwa ta kai masa duka a fuska harda yakushi. Zafin da yaji a gefen idonsa na hagu yasa shi sakinta tim a kasa ta fasa wata gigitacciyar kara. Zainab da Mami ke rige rigen shiga dakin ya dafe gefen idonsa da yake jini ko ta kanta bai bi ba a kasan. Zainab tayi saurin daukarta yayin da Mami babu tambayar ba'asi ta dauke Awwab da mari. "Me kayi mata take wannan kukan?" Shima kukan yake sosai Mairama ta taho ta rike shi murya na rawa ya nuna mata wurin "yakushi na tayi fa" "Sai kayi mata me?" Mami ta kuma tahowa kamar za ta doke shi. Da karamar murya ya amsa "Faduwa tayi daga hannuna" Takaici ne ya kamata kuma wai Mairama tana kare masa. "Bari Daddynku ya dawo sai na fada masa" ta koma ga Mairama rai a bace "ke kuma kin karbi yarinyar nan kin rarrasheta ko kuwa" Mairama tace to yau abin harda ita. Karbarta tayi ba shiri an tabo Mami yau ta fara shayar da ita amai ya taso mata da gudu tayi bandaki. Abu kamar wasa sai gata ko tashi da kafafunta ta kasa. Mazajen nasu ba ma sa cikin barrack din an turasu wani training cikin jeji sai sunyi kwanaki. Dalilin ma da suke tarewa gidan Mamin kenan. Abu na taron mata tare su ukun da yaransu suka tafi asibiti. Ciki aka gano a jikin Mairama har wata uku. Kuka ta saka ganin Radhiya duka duka nawa take. Kuma ga kunyar ace yarinya bata shekara ba ta sake ciki. Su Zainab kuwa sai murna. Mami tace mata ya kamata kafin su Zayyan su dawo ta yaye Radhiya saboda cikin yana wahalar da ita ga tsotso. Da yake akwai kawaici a daren ta tafi ta barwa Mami ita sai kayanta da ta turo Awwab dasu. Yadda Mami ke bawa Radhiya kulawa ya kara tabbatar musu da cewa zaman mutumci da amana ba sai da jini ba. Da ita da yaranta duk sun tare a jikin Radhiya an bar Mairama da uban laulayi sai Zainab dake sintirin zuwa wurinta. A kwana na biyar su Zayyan su ka dawo. Sun sha wahala sosai sai dai kuma aiki ne na sabo. Da murnarsa ya shigo yana kiran 'yar soja Mairama tace masa tana gidan Major ta tafi yaye. "Yaye Mairam? Ko shekara bata yi ba" Hannunsa ta kama suka zauna ta dora kanta a kafadarsa "Sojana bani da lafiya ne" Ya dago kan ta "na sani kuma asibiti zan kaiki, amma meyasa baki bari na dawo ba sai yaye?" Baki ta tura masa "to ba..." "Me?" "Ciki" tace tana rufe fuska da tafukan hannayenta Sungumarta Zayyan yayi yana murna "Mairam kice Tureta ya tureki a karo na biyu" Salati ta hau yi tana mai jin kunyarsa shi kuwa ko a jikinsa. Dama ta samu sai sabon amarci don ma laulayin yana hana sakewa. Sai da Radhiya ta cika kwana goma sannan Mami ta dawo da ita da kaya da tarkacen wasa. ****** Bayan wata guda da yaye Radhiya wata litinin Mairama tana gyaran wake za ta yi alala da rana Zayyan ya shigo ba lokacin dawowarsa ba. Hannunta ta dauraye ta fito wurinsa. "Sojana ya dai yau ka dawo da wuri" Mikewa yayi akan doguwar kujera yana riko hannunta ta zauna a wurin da ya matsa mata. "Me kike dafa mana ne?" "Alala zanyi" Hanci ya dage "Uhmm kayan bata ciki" Hancin nasa ta riko tana dariya "nasan ba ka ci, banyi tsammanin dawowarka yanzu ba ne. Sai na canja abincin, waken...." Kofar falon da taji ana bugawa da karfi kuma kamar muryar Zainab yasa bata gama fadin me tayi niyar fada ba. Da sauri ta bude kofar tayi baya a tsorace ganin Zainab tana rusa kuka kamar ranta zai fita ga Hadir a bayanta dauke da Ibrahim. Hanya ta basu su ka wuce cikin falon Zayyan ya hada ido da Hadir yayi murmushin dole jikinsa a sanyaye yace "ka fada mata ne?" Zainab kuka take har lokacin Mairama ta rude sai tambayarta take me ya faru. Hadir take kallo tana jiran bayani daga baya tace "ko dai aure za ka kara?" "Wallahi dama auren ne Ummin Awwab da ya fiye min da wannan tashin hankalin" Kanta ya sake shiga duhu "ba dai saki bane ko?" "Liberia zai tafi" Dif Mairama tayi sakon yana sauka a kwakwalwarta. Liberian da babu wanda yake cikin barikin da bai san tashin hankalin da suke ciki ba. Nigeria ta shiga cikin lamarin tana basu gudunmawar sojoji domin a kwantar da tarzoma. Dibansu akeyi lokaci lokaci ana turawa. Rawa taji jikinta yana yi ta kasa tsayuwa da kyau sai da Zayyan ya riketa ya zaunar da ita a kusa dashi. Cikin tsantsar tashin hankali tace "da kai za'ayi tafiyar?" Abinda ya dawo dashi gida da wuri kenan ya kasa fada mata. Kai ya gyada kawai ta kalli yadda Zainab ke kuka itama ta soma hawaye. Duk wata kalmar rarrashi da ban baki abokan sun lalubo domin kwantarwa matansu da hankali. Zainab ta fi gigicewa itama tana son Hadir fiye da zato da tsammani. Da kyar ya samu ta tashi su ka koma gidansu aka bar Zayyan da Mairama. Ranar bata iya yin girkin ba jikinta yayi mugun sanyi. Abincin Radhiya ma sai shi yake bata. Ita kwanciya tayi a daki kawai tana zubar da hawaye. Bai ce mata komai ba sai cikin dare ya kwantar da ita a jikinsa yana rarrashi "Mairam nayi zaton zaki bani goyon baya sosai har naje na dawo mu koma Kano" "Yaushe zaku dawo?" Ta tambaye shi murya a dashe. Tsokanarta ya fara yi don ta sake "tafiyar wata uku ce fa, zan dawo kafin ki haihu in Allah Ya yarda" Sake shigewa jikinsa tayi yana jin cikinta da ya fara tasawa ya dora hannu a kai "Ashe haka ki ke so na ban sani ba?" Shiru tayi ya cigaba da maganarsa shi kadai "a iya zamana dake Mairam bani da wani abu da zan fada akanki sai alkhairi. Duk abubuwan da na rasa a baya zuwanki ya wanke min kuncinsu. Shiyasa nake matukar son ki. Wannan tafiya da ina da yadda zanyi ko dai na tafi daku ko kuma na hakura ne. Ina rokonki da ki karfafa min gwiwa naji dadin bautawa kasata." Wani irin abu take ji yana mata yawo a jikinta. Idan a da tana tunanin tana son mijinta to a yau sonsa yana neman ranta ne. Gani take kamar bazata iya jurar rashinsa a tare da ita ko da na kwana daya bane. Ashe baka sanin mahimmancin abun da ka ke dashi sai yayi nisa da kai. Bata san lokacin da bacci ya dauketa ba sai ajiyar zuciya da take ta saukewa. Sai da ya tabbatar tayi bacci ya tashi ya dauro alwala. Yasan yaudarar kansa zaiyi idan yace zaiyi bacci a wannan daren. Nan da kwana biyar zasu bar kasar, zai bar iyalinsa wanda basu dogara da kowa ba sai Allah sai kuma shi da nauyinsu yake wuyansa. Yayi nafila raka'a goma tare da witri sannan ya zauna yana jero addu'o'i. Motsin Radhiya yaji yayi saurin fita da ita daga dakin don kada ta tashi Mairam yaje ya hada mata tea a feeder ta shanye. Yana jiran ta koma bacci yarinya ido ya soye ta fara kiriniya. Bata tafiya sai rarrafe da mikewa. Biye mata yayi suna wasan. Sai gabanin asuba ta bingire a jikinsa tayi bacci. Kan ta ya rinka shafawa baiyi zato ba sai hawaye ya ziraro masa ya goge da sauri yana baiwa zuciyarsa hakurin cewa wata uku a wurin Allah kamar kiftawar ido zasu zo su wuce. ********** Gidan Hadir ma basuyi bacci ba don Zainab kwana tayi kuka. Mami da sauki tunda ba zuwan Major na farko wurin rikici ko yaki kenan ba. Sai dai itanma kukan tayi don ba'a sabo da rabuwa. Washegari harabar gidajen nasu kaf babu wata hayaniyar kirki. Sojoji ashirin ne zasu tafi a cikin magidantan da suke wurin. Kowa yana gida tare da iyalinsa. Bayan la'asar Zayyan ya dauki Mairam su ka je gidansu da gidan kawunansa da Mal Aminu ya fada musu zaiyi tafiya. Kowa yayi masa addua da fatan alkhairi ban da Jume da bata dena jin zafin rashin basu kudi ba. Duk da haka ya yi musu kyauta ita da su Maikudi tunda sunyi aure. Matan ma a ranar sai da ya kai musu ziyara. Sukuku su Mairam su ka koma babu walwala a tare dasu ita da Zainab. Mami ce tayi musu fada akan idan sun cigaba da haka a wane yanayi suke so mazajensu su tafi. Sun ji maganarta don kowacce sai da tayi kokarin gyarawa. Mairam dambun nama ta yiwa Zayyan gari guda sai da ya dibarwa Hadir da Major. Ta kuma saki jiki tana bashi kulawa fiye da yadda ta saba. Sauran kwana biyu su tafi tana goge masa khakinsa Radhiya ta fito daga daki da kafafunta a hankali saboda rashin kwarin tafiyar. Murna ta kama Zayyan ya sunkuceta yana sumbatar kumatunta. " 'Yar soja ta girma, yau yawo zamu je tunda anyi kafa" Kamar taji me yace ta rinka bangala dariya. Ajiyeta yayi zai chanja kaya su fita tasa masa kuka "Daaadaa" yaji tace tana dago masa hannuwa. A nutse ya juyo ya tabbatar shi take kira. Har yanzu hannuwanta take miko masa "Daaadaa". Ya kalli Mairam ita ma mamakin yarinyar ya kamata. Awwab bashi da aiki sai koya mata Ummi da Daddy wai dole sai tayi magana. Yau gashi ta kira mahaifinta dadi yasa yaji idonsa na alamun zafin kwalla. Daukanta yayi ya shiga dakin su ka bar Mairam tana guga tana diga masa hawaye a kayansa. Ranar ashirin da daya ga watan Mayu na 1993 ne Giginya Barrack dake cikin garin Sakkwato ta kwashi sojojinta za'a kaisu Lagos washegari su tashi zuwa Liberia ta ruwa. Daren ranar ya kasance dare na soyayya, jaddada alkawura da kuma sabunta matsayi a zukatan su Zayyan da iyalansu. Daga shi har Mairam babu wanda ya runtsa kuma hakan take a wurin Hadir da Zainab da Major kansa da Mami. Komai Mairam ce ta yiwa Zayyan hatta abinci a baki take bashi. Tayi ta daurewa kada tayi kuka zuciyarta ta kasa daukan wannan lamari. Ko kadan baya son nuna mata damuwar da yake ciki shiyasa ya fake da yiwa Radhiya wasa. Jiniya mai sanar da su fito ce tayi kara sai da cikin Mairama ya murda kawai ta fashe da kuka iya karfinta. "Zayyan" Tashi yayi ya rungumeta tsam a jikinsa "ashe kin iya fadin suna na" "Ka ajiye aikin nan mu koma Nijar ko kiwo ka rinka yi" Fuskarta ya zagaye a tsakiyar tafukan hannunsa. "I love you Maryam Ali Gidado. Ki rike wannan a zuciyarki har na dawo. Nayi miki ajiya a kan mudubi idan na tafi ki duba" Hade bakinsu yayi tamkar ranar su ka fara haduwa yana jin karar jiniyar a karo na biyu ya saketa ya dauki Radhiya. "Ki tayani kula da Umminki da baby kinji mamana." "Daaadaa" tace tana washe hakoranta biyu dimple dinta ya lotsa ciki sosai. Ita ma ya sumbaci kuncinta hagu da dama kafin Mairam ta farga ya fice daga gidan.....ALLAH NA NASA "Ummin Awwab me yake damunki ne kwanakin nan sai wata rama kike yi kamar wadda za'a yiwa kishiya" Dago kai Mairama tayi jiki a sanyaye "Mami ni kaina na rasa gane dalilin wannan rama. Kuma ke shaida ce ina cin abinci sosai" "Kinbi kin dashe kinyi fayau. Jiya ina ji baban Radhiya yana fadawa Hadir wai kinki bari ku je asibiti. Baki ga yadda ya damu ba fa" Mairama tayi shiru ita kanta ramar da take yi tana damunta. Dadinta ma dai Radhiya kullum kara habbaka take. Suna wannan hirar Fauziyya ta shigo da Radhiya tana nishi anyi daukan rungumarni mu fadi. Kafin su shigo kukan Radhiyan ne ya isar da zuwansu. Mairama ta girgiza kai tana takaicin wannan kukan banza na Radhiya. Tana jaririya babu ruwanta amma yanzu rigima da kuka ga fada duk ta iya. Idan ta raina girman mutum ya dauketa sai yakushi tana doke doke duka wataninta tara a lokacin. Zayyan dariya yake yace 'yar Soja bata daukar raini. Wasu lokutan kuma sunanta na gaskiya yake kira idan yana jin nishadi. Har ta gane indai taji Alheran tasan babanta ne. A cinyar Mairama ta ajiyeta ta kalli uwar tasa dariya. Zainab tace "kunji min mara kunya ko? Mu da take gani kullum yanzu dariyar ma sai mun roka. Dadinta dai har Awwab bata yiwa" Homework yake yi a gefe yana jin tsokanar da ake masa ya taso ya kinkimeta yana cewa "Ummi wallahi tayi nauyi da yawa ki dena bata abinci" Me zasu yi banda dariya kuwa. " to sarkin wauta, an taba hana mutum abinci saboda kiba ne?" Cewar Mami Shi dai bai ga aibun maganarsa ba ya dauketa gashi siriri sai tsayi da yake faman yi ya tafi dakinsu Zahra. Kayan wasa ya baje mata yana cewa sai tace Ummi da Daddy. Gajiya tayi da wasan ta soma rigima sai ya dauketa. Duk da haka kukan take masa ya sabata yana haki "gaskiya kin fiye kuka Alheran dinnan" Kamar taji me yace kuwa ta kai masa duka a fuska harda yakushi. Zafin da yaji a gefen idonsa na hagu yasa shi sakinta tim a kasa ta fasa wata gigitacciyar kara. Zainab da Mami ke rige rigen shiga dakin ya dafe gefen idonsa da yake jini ko ta kanta bai bi ba a kasan. Zainab tayi saurin daukarta yayin da Mami babu tambayar ba'asi ta dauke Awwab da mari. "Me kayi mata take wannan kukan?" Shima kukan yake sosai Mairama ta taho ta rike shi murya na rawa ya nuna mata wurin "yakushi na tayi fa" "Sai kayi mata me?" Mami ta kuma tahowa kamar za ta doke shi. Da karamar murya ya amsa "Faduwa tayi daga hannuna" Takaici ne ya kamata kuma wai Mairama tana kare masa. "Bari Daddynku ya dawo sai na fada masa" ta koma ga Mairama rai a bace "ke kuma kin karbi yarinyar nan kin rarrasheta ko kuwa" Mairama tace to yau abin harda ita. Karbarta tayi ba shiri an tabo Mami yau ta fara shayar da ita amai ya taso mata da gudu tayi bandaki. Abu kamar wasa sai gata ko tashi da kafafunta ta kasa. Mazajen nasu ba ma sa cikin barrack din an turasu wani training cikin jeji sai sunyi kwanaki. Dalilin ma da suke tarewa gidan Mamin kenan. Abu na taron mata tare su ukun da yaransu suka tafi asibiti. Ciki aka gano a jikin Mairama har wata uku. Kuka ta saka ganin Radhiya duka duka nawa take. Kuma ga kunyar ace yarinya bata shekara ba ta sake ciki. Su Zainab kuwa sai murna. Mami tace mata ya kamata kafin su Zayyan su dawo ta yaye Radhiya saboda cikin yana wahalar da ita ga tsotso. Da yake akwai kawaici a daren ta tafi ta barwa Mami ita sai kayanta da ta turo Awwab dasu. Yadda Mami ke bawa Radhiya kulawa ya kara tabbatar musu da cewa zaman mutumci da amana ba sai da jini ba. Da ita da yaranta duk sun tare a jikin Radhiya an bar Mairama da uban laulayi sai Zainab dake sintirin zuwa wurinta. A kwana na biyar su Zayyan su ka dawo. Sun sha wahala sosai sai dai kuma aiki ne na sabo. Da murnarsa ya shigo yana kiran 'yar soja Mairama tace masa tana gidan Major ta tafi yaye. "Yaye Mairam? Ko shekara bata yi ba" Hannunsa ta kama suka zauna ta dora kanta a kafadarsa "Sojana bani da lafiya ne" Ya dago kan ta "na sani kuma asibiti zan kaiki, amma meyasa baki bari na dawo ba sai yaye?" Baki ta tura masa "to ba..." "Me?" "Ciki" tace tana rufe fuska da tafukan hannayenta Sungumarta Zayyan yayi yana murna "Mairam kice Tureta ya tureki a karo na biyu" Salati ta hau yi tana mai jin kunyarsa shi kuwa ko a jikinsa. Dama ta samu sai sabon amarci don ma laulayin yana hana sakewa. Sai da Radhiya ta cika kwana goma sannan Mami ta dawo da ita da kaya da tarkacen wasa. ****** Bayan wata guda da yaye Radhiya wata litinin Mairama tana gyaran wake za ta yi alala da rana Zayyan ya shigo ba lokacin dawowarsa ba. Hannunta ta dauraye ta fito wurinsa. "Sojana ya dai yau ka dawo da wuri" Mikewa yayi akan doguwar kujera yana riko hannunta ta zauna a wurin da ya matsa mata. "Me kike dafa mana ne?" "Alala zanyi" Hanci ya dage "Uhmm kayan bata ciki" Hancin nasa ta riko tana dariya "nasan ba ka ci, banyi tsammanin dawowarka yanzu ba ne. Sai na canja abincin, waken...." Kofar falon da taji ana bugawa da karfi kuma kamar muryar Zainab yasa bata gama fadin me tayi niyar fada ba. Da sauri ta bude kofar tayi baya a tsorace ganin Zainab tana rusa kuka kamar ranta zai fita ga Hadir a bayanta dauke da Ibrahim. Hanya ta basu su ka wuce cikin falon Zayyan ya hada ido da Hadir yayi murmushin dole jikinsa a sanyaye yace "ka fada mata ne?" Zainab kuka take har lokacin Mairama ta rude sai tambayarta take me ya faru. Hadir take kallo tana jiran bayani daga baya tace "ko dai aure za ka kara?" "Wallahi dama auren ne Ummin Awwab da ya fiye min da wannan tashin hankalin" Kanta ya sake shiga duhu "ba dai saki bane ko?" "Liberia zai tafi" Dif Mairama tayi sakon yana sauka a kwakwalwarta. Liberian da babu wanda yake cikin barikin da bai san tashin hankalin da suke ciki ba. Nigeria ta shiga cikin lamarin tana basu gudunmawar sojoji domin a kwantar da tarzoma. Dibansu akeyi lokaci lokaci ana turawa. Rawa taji jikinta yana yi ta kasa tsayuwa da kyau sai da Zayyan ya riketa ya zaunar da ita a kusa dashi. Cikin tsantsar tashin hankali tace "da kai za'ayi tafiyar?" Abinda ya dawo dashi gida da wuri kenan ya kasa fada mata. Kai ya gyada kawai ta kalli yadda Zainab ke kuka itama ta soma hawaye. Duk wata kalmar rarrashi da ban baki abokan sun lalubo domin kwantarwa matansu da hankali. Zainab ta fi gigicewa itama tana son Hadir fiye da zato da tsammani. Da kyar ya samu ta tashi su ka koma gidansu aka bar Zayyan da Mairama. Ranar bata iya yin girkin ba jikinta yayi mugun sanyi. Abincin Radhiya ma sai shi yake bata. Ita kwanciya tayi a daki kawai tana zubar da hawaye. Bai ce mata komai ba sai cikin dare ya kwantar da ita a jikinsa yana rarrashi "Mairam nayi zaton zaki bani goyon baya sosai har naje na dawo mu koma Kano" "Yaushe zaku dawo?" Ta tambaye shi murya a dashe. Tsokanarta ya fara yi don ta sake "tafiyar wata uku ce fa, zan dawo kafin ki haihu in Allah Ya yarda" Sake shigewa jikinsa tayi yana jin cikinta da ya fara tasawa ya dora hannu a kai "Ashe haka ki ke so na ban sani ba?" Shiru tayi ya cigaba da maganarsa shi kadai "a iya zamana dake Mairam bani da wani abu da zan fada akanki sai alkhairi. Duk abubuwan da na rasa a baya zuwanki ya wanke min kuncinsu. Shiyasa nake matukar son ki. Wannan tafiya da ina da yadda zanyi ko dai na tafi daku ko kuma na hakura ne. Ina rokonki da ki karfafa min gwiwa naji dadin bautawa kasata." Wani irin abu take ji yana mata yawo a jikinta. Idan a da tana tunanin tana son mijinta to a yau sonsa yana neman ranta ne. Gani take kamar bazata iya jurar rashinsa a tare da ita ko da na kwana daya bane. Ashe baka sanin mahimmancin abun da ka ke dashi sai yayi nisa da kai. Bata san lokacin da bacci ya dauketa ba sai ajiyar zuciya da take ta saukewa. Sai da ya tabbatar tayi bacci ya tashi ya dauro alwala. Yasan yaudarar kansa zaiyi idan yace zaiyi bacci a wannan daren. Nan da kwana biyar zasu bar kasar, zai bar iyalinsa wanda basu dogara da kowa ba sai Allah sai kuma shi da nauyinsu yake wuyansa. Yayi nafila raka'a goma tare da witri sannan ya zauna yana jero addu'o'i. Motsin Radhiya yaji yayi saurin fita da ita daga dakin don kada ta tashi Mairam yaje ya hada mata tea a feeder ta shanye. Yana jiran ta koma bacci yarinya ido ya soye ta fara kiriniya. Bata tafiya sai rarrafe da mikewa. Biye mata yayi suna wasan. Sai gabanin asuba ta bingire a jikinsa tayi bacci. Kan ta ya rinka shafawa baiyi zato ba sai hawaye ya ziraro masa ya goge da sauri yana baiwa zuciyarsa hakurin cewa wata uku a wurin Allah kamar kiftawar ido zasu zo su wuce. ********** Gidan Hadir ma basuyi bacci ba don Zainab kwana tayi kuka. Mami da sauki tunda ba zuwan Major na farko wurin rikici ko yaki kenan ba. Sai dai itanma kukan tayi don ba'a sabo da rabuwa. Washegari harabar gidajen nasu kaf babu wata hayaniyar kirki. Sojoji ashirin ne zasu tafi a cikin magidantan da suke wurin. Kowa yana gida tare da iyalinsa. Bayan la'asar Zayyan ya dauki Mairam su ka je gidansu da gidan kawunansa da Mal Aminu ya fada musu zaiyi tafiya. Kowa yayi masa addua da fatan alkhairi ban da Jume da bata dena jin zafin rashin basu kudi ba. Duk da haka ya yi musu kyauta ita da su Maikudi tunda sunyi aure. Matan ma a ranar sai da ya kai musu ziyara. Sukuku su Mairam su ka koma babu walwala a tare dasu ita da Zainab. Mami ce tayi musu fada akan idan sun cigaba da haka a wane yanayi suke so mazajensu su tafi. Sun ji maganarta don kowacce sai da tayi kokarin gyarawa. Mairam dambun nama ta yiwa Zayyan gari guda sai da ya dibarwa Hadir da Major. Ta kuma saki jiki tana bashi kulawa fiye da yadda ta saba. Sauran kwana biyu su tafi tana goge masa khakinsa Radhiya ta fito daga daki da kafafunta a hankali saboda rashin kwarin tafiyar. Murna ta kama Zayyan ya sunkuceta yana sumbatar kumatunta. " 'Yar soja ta girma, yau yawo zamu je tunda anyi kafa" Kamar taji me yace ta rinka bangala dariya. Ajiyeta yayi zai chanja kaya su fita tasa masa kuka "Daaadaa" yaji tace tana dago masa hannuwa. A nutse ya juyo ya tabbatar shi take kira. Har yanzu hannuwanta take miko masa "Daaadaa". Ya kalli Mairam ita ma mamakin yarinyar ya kamata. Awwab bashi da aiki sai koya mata Ummi da Daddy wai dole sai tayi magana. Yau gashi ta kira mahaifinta dadi yasa yaji idonsa na alamun zafin kwalla. Daukanta yayi ya shiga dakin su ka bar Mairam tana guga tana diga masa hawaye a kayansa. Ranar ashirin da daya ga watan Mayu na 1993 ne Giginya Barrack dake cikin garin Sakkwato ta kwashi sojojinta za'a kaisu Lagos washegari su tashi zuwa Liberia ta ruwa. Daren ranar ya kasance dare na soyayya, jaddada alkawura da kuma sabunta matsayi a zukatan su Zayyan da iyalansu. Daga shi har Mairam babu wanda ya runtsa kuma hakan take a wurin Hadir da Zainab da Major kansa da Mami. Komai Mairam ce ta yiwa Zayyan hatta abinci a baki take bashi. Tayi ta daurewa kada tayi kuka zuciyarta ta kasa daukan wannan lamari. Ko kadan baya son nuna mata damuwar da yake ciki shiyasa ya fake da yiwa Radhiya wasa. Jiniya mai sanar da su fito ce tayi kara sai da cikin Mairama ya murda kawai ta fashe da kuka iya karfinta. "Zayyan" Tashi yayi ya rungumeta tsam a jikinsa "ashe kin iya fadin suna na" "Ka ajiye aikin nan mu koma Nijar ko kiwo ka rinka yi" Fuskarta ya zagaye a tsakiyar tafukan hannunsa. "I love you Maryam Ali Gidado. Ki rike wannan a zuciyarki har na dawo. Nayi miki ajiya a kan mudubi idan na tafi ki duba" Hade bakinsu yayi tamkar ranar su ka fara haduwa yana jin karar jiniyar a karo na biyu ya saketa ya dauki Radhiya. "Ki tayani kula da Umminki da baby kinji mamana." "Daaadaa" tace tana washe hakoranta biyu dimple dinta ya lotsa ciki sosai. Ita ma ya sumbaci kuncinta hagu da dama kafin Mairam ta farga ya fice daga gidan. [02/11 7:29 AM] My 2nd Mtn: 12. Daga tashar jirgin ruwa ta Apapa da ke dake Lagos su Zayyan zasu tashi a jirgin ruwa zuwa babban birnin Liberia wato Monrovia. Akan tekun Atlantika jirgin nasu ya dau hanya sai da suka wuce Benin republic wadda mu ka fi sani da Cotounou, sai Togo, Ghana, Cote d'voire sannan Allah Ya saukesu a kasar da rikici na cikin gida ya kaurewa tun shekarar 1989. Motocin yaki aka turo domin daukarsu. Zayyan da Hadir zuwansu sansanin yaki irin wannan na farko kenan. Major Mustapha yazo ne a matsayin babban soja don ba wuri daya zasu zauna ba. Shi Computer Engineer ne saboda haka aikinsa yafi karfi ne daga bayan fage musamman da a wannan lokacin babu masu karatu irin nasa da yawa saboda karancin kayan aiki. Cikin garuruwa ko kauyuka da rikicin yafi shafa ake watsa sojojin. Sune suke kwantar da tarzoma da fitina idan ta taso a tsakanin mazauna garin da kuma 'yan tawaye. Ranar farko su Zayyan da sauran da su ka zo tare da yawansu basu iya rintsawa ba. Daki ne kato kowa da yalolowar katifarsa akan gadon karfe mai hawa biyu. Wasu kuma a kasa katifunsu suke saboda rashin wadatar gadajen. Zayyan da Hadir a kusa da juna suka shimfida katifun da aka basu. Shi dai tunanin Mairama da Radhiya yake yi. Ko me sukeyi a wannan lokaci? Tafiyar Radhiya ta kara kwari a kwanakin da suka shafe a kan ruwa? Idan ya koma zata yi masa kyuya? Gajeren tsaki yayi da wannan tunanin. Burinsa ace kowane mataki na rayuwar 'yarsa ya faru a kan idanunsa. Hadir yace "kaima ka kasa bacci ko?" "Yadda ka san nayi tsuntsuwa naje na gansu na dawo" yayi maganar cike da kewa. Muskutawa Hadir yayi ya gyara kwanciyarsa. Shi kuma Zayyan yayi rub da ciki ya rike fuskarsa a tafukan hannunsa da ya tokare kansa dasu. "Bansan yaya Zainab take yi da Ibrahim ba yanzu. Kusan wata guda yaron nan ba ya iya bacci sai akan kirjina" Dariya Zayyan yayi "kace akwai daru, don ma bai kai Alheran rigima ba abin zai zo da sauki." Wani cikin wadanda suka tarar a sansanin yana daga gefe yana jin hirarsu ya soma dariya "kusan kowa ranar farko sai yayi hirar gida" Gwangwani ya dauka a kusa da shi ya bubbuga da hancin katuwar bindigarsa. Sai ga sojoji suna tashi zaune wasu akan gado wasu a katifa. Kalilan ne masu bacci. Mutumin yace "kunga yau anyi baki ku tashi mu san juna." Ya kalli bangaren da yawancin bakin nasu suke "babu wani abin debe kewa a wurin nan sai hira da muke samun yi da juna cikin dare" Na kan gado na dirowa na kasa na matsawa sai gasu sunyi da'ira sun zagaye katifar wanda yayi maganar. Da gani zai girmi da yawansu. Kallonsa ya ga suna yi ya kada kafada. "Ok, ok ni zan fara" Ihu wasu suka fara su Zayyan dai abin duka sabo ya zame musu. Duk wata hayaniya sun saba da ita a irin training da suke zuwa. Amma wannan karon fa a filin yaki suke tare da sojojin wasu barracks din da basu taba haduwa ba. Muryar mutumin yaji ya soma magana. "Nine shugabanku a harkar abinci" sai sowa da tafi yayi murmushi "Chief cook kuke gani. Suna na Captain Ogbonna Odili. Ina da mata Mabel da yara hudu a Enugu. Ogechi, Uloma, Nneka da Kachiku muna kiransa Kachi. Kamar kowa a nan ina matukar son family dina. Musamman ma Uloma saboda tana da kokari sosai a school. Yanzu zaka rubuta mata abu indai ta karance shi daga farko zuwa karshe to ya gama zama. Da kuke ganina kudi nake nema domin na kaita wata babbar makaranta a garinmu ta gifted children. Uloma is born to be a great doctor" "So shall it beeeee" wasu suka amsa da ihunsu na sojoji. Capt. Ogbonna yana ta dariya ya cigaba da hirar iyalinsa ana tayashi murna. Bayan shi sai aka ce mutum daya cikin newcomers ya gabatar da kansa. Papa Dolapo ne ya fara shima yana bayani ana dariya da kuma nuna tausayi musamman da yace ya baro matarsa da tsohon ciki suna jinjina masa. Zayyan sai ya tuna cikin jikin tasa matar ya daga hannu "I am next please, please" Dariya suka sa ana tsokanarsa ya dake yana basu labarin Mairama da Radhiya "babban farincikina kafin na taho Alheran ta iya kiran suna na" "Fada mana ya take cewa" wani yace sauran na goya masa baya. "Daaadaa" Ihunsu ya karade dakin masu baccin ma sun tashi anayi dasu. "Kuma nima matata tana da ciki amma sai mun koma zata haihu In sha Allah. Sorry Papa Dolapo kaine za'ayi ba kai" Hadir yayi dariya yana cewa Zayyan yayi masa wayo "muna komawa da wata tara zaka ji Zainab ta haihu" Tafawa suka yi wani mutumin Adamawa Austin Bakari dan kabilar Chamba ya fara bada labarin iyayensa tsofaffi wanda sun dora duk wani buri nasu akan cigabansa. Labarin iyayen nasa akwai ban tausayi domin dukkansu guragu ne da basu da mataimaki sai shi kadai. Dan albashin nasa shine cinsu shine shansu. Ya sanya sauran cikin yanayi na jimami kowa na fadin albarkacin bakinsa sai su ka ji wata muguwar kara mai razanarwa. Basu gama da wannan firgicin da ya sanyasu daukan bindigoginsu cikin sauri ba kuma sai ga daya daga cikin masu patrol na wannan daren ya shigo bindigarsa tana kan saiti ya fada musu 'yan tawayen da su ka addabi wannan sansanin nasu sun kawo musu hari. Idan da suna jin wai-wai, yau ga su zahiri a filin daga. Harbi ne yake tashi ko ta ina suka firfito kan kace meye wannan wurin ya kaure. Anyi musayar harsashi sosai duk da duhun dare sun sami damar fatattakar mutanen har da nasarar cafke mutum daya. Wani bacci dama babu shi a lissafi maza suna filin daga. Kwana ukun farko sunyi su ne cikin rudani da tashin hankali. Da gasken gaske 'yan tawayen suke son korar sojojin Nigeria daga wurin. Akwai wuraren da suke tsammanin samun nasara su janyo mutanen garin domin a hadu a ture gwamnatin shugaba mai ci a lokacin. Rigima ta cikin gida a ganinsu mai zai kawo wasu baki da abin bai shafa ba a matsayin peacekeepers. Kafin wani lokaci su Zayyan sun kara gogewa da halin da suka tsinci kansu yanzu. Shine ya koma yi musu limanci bayan tafiyar Abdulwahid Gbenga wanda ya kasance da shine limamin. Duk daren da babu gajiya sosai a tare dasu suna zaman hira a daki ko a waje. Su kunna wuta su zagaye wurin suna jin dumi saboda shigowar sanyi gadan gadan. Da safe kuma masu manyan mukami su ke jagorantar training dinsu don ba zama. Watansu daya da kwanaki annobar cholera ta shigo kauyen da yafi kusa da inda suke. Garin kai taimako wurin fitar da marasa lafiyan zuwa asibiti a cikin gari wasunsu suka dauko ciwon suka kawo musu. Cikin kwanaki bakwai mutum tara sun kamu. Amai suke yi sosai da gudawa. Suna ta kokarin neman agajin babban sansanin domin a kawo musu magunguna sannan a dauke marasa lafiyan cikinsu zuwa asibiti amma abu yaci tura. Ba wai sakon bai isa garesu bane, yaje amma su ma suna jiran command daga babbar headquarter saboda komai na soja bisa doka da oda ake yi. Major Mustapha da ya ankara cewa sansanin su Zayyan ne ya matsa lamba sosai ranar da za'a kai musu maganin bayan kwanaki shadaya da fara cutar yabi bayan ma'aikatan lafiyan cikinsu. Su ma din sojoji ne amma hannuwan rigarsu daga dantse akwai wani farin abu da yake nuni da alamun cewa su likitoci ne. Major Mustapha har yanzu bashi da magana sosai amma ya damu kwarai da kannen nasa Zayyan da Hadir. Motarsu ta iso sansanin a daidai lokacin da Zayyan yake limancin sallatar gawar Papa Dolapo wanda yayi ta fama da cutar ta amai da gudawa na kwana uku kafin rai yayi halinsa. Jikin Major yayi sanyi haka na likiticin da suke tare dasu. Zagaye sansanin nasu akayi da wasu irin wayoyi masu kaifi aka rubuta musu QUARANTINE da manyan harufa. Ma'ana an kebesu daga shiga ko fita har sai an sami kyakkyawan tabbacin cutar babu sauranta a tare dasu. Ana gudun su sanyawa wasu sojijin ko kuma su sakawa mutanen wani kauyen garin kai taimako. Likitocin kadai aka bari suka shiga suma sun rufe jiki sosai da wasu kaya hatta fuskokinsu ba'a gani. Sunyiwa kowa allura sannan aka shiga bawa marasa lafiyan taimakon da ya dace. Ta bayan wayar suke magana da Major yana tambayarsu halin da suke ciki. Nuna masa suke yi babu wani abu lafiya kalau suke. Ta'aziyar Papa Dolapo yayi musu wanda aka saka gawarsa a cikin motar da zasu koma da ita nasu sansanin. Idan sunyi sa'a za'a bari gawar ta koma Nigeria. Idan basuyi ba kuma to a nan za'a binne shi iyalinsa su dau hakuri. "Shekaranjiya da aka toro wani troop din wannan wasikar tazo. Ta Lt Badmus ce" Wasikar ya dago musu kowa jiki a sanyaye domin Papa Dolapo ne Lt Badmus. Major Mustapha ya kara da cewa "duk da ban bude ba amma an fada min matarsa ce ta haihu. Zayyan makotanku ne ko?" Kai ya gyada ya kasa cewa komai ya juya ya bar wurin zuciya tayi nauyi. "Follow him Lieutenant" ya umarci Hadir. Sai da ya ga sun shiga cikin wurin da yake mazaunin dakinsu ya koma motar da ta kawusu suka bar wurin. ********** Rayuwar matan da mazajensu basa nan a barikin babu dadi. Ci da sha bai yanke ba tunda ana basu albashinsu to amma fa kowacce kullum kwanan duniya da fargaba take kwana matsawar ba mijinta ta gani ya dawo ba. Mairama, Mami da Zainab dauriya suke yi kowacce tana son nuna ita ma jarumar kanta ce mai hakuri da juriya. A gefe daya basu fasa yiwa mazajensu addu'a da fatan alkhairi ba. Awwab kusan ya dawo gidan Mairama da zama. A nan yake kwana idan ya dawo daga makaranta ya lalace wurin wasa da Radhiya. Sunyi shakuwar da har Mairama tana tabawa kyuya musamman idan zai fita. Kyalesu take yi tana fama da cikinta don ma laulayin yayi sauki yanzu. Awwab ya fita da Radhiya sun tafi wurin Mami sai Mairama ita kadai a cikin gida. Hayaniya ta soma ji daga waje ta yafa mayafi ta leka. Can ta hango Zainab da wasu matan da suke tare sun zagaye wata. Fitowa tayi cikin sauri jin kamar ana kuka. "Innolillahi wa inno ilaihi raji'oon....Oko mi tikú" kuka Maman Dolapo take tana tumani a kasa ga danyen jego. Mairama ta tsorata da yanayin da ta ganta, ta taba wadda ta fi kusa da ita "what is wrong with her" "Ahhh Mama Radhiya...Papa Dolapo don die oooo" Ita ce amsar da ta doki kunnenta taji gabanta ya yanke ya fadi. Zainab ta matso kusa da ita tana fada mata wai yanzu aka sanar dasu rasuwar tasa. Cholera ce ta kashe shi Zayyan ne ma ya sallace shi, sannan anyi masa sutura a can kasar. Kuka su ka taya Mama Dolapo aka kaita cikin gidanta. Bayan kwana biyu sai ga 'yan uwanta da yayan mijin suka zo daukansu ita da yaranta guda hudu zasu koma Akure. Ranar ma wani sabon kukan ne ya barke a tsakaninsu domin da yawa sun sani da wahala su sake sanya juna a ido har abada. Maman Dolapo ta tafi ta barsu da kewa da kuma fargabar labarin wa zasu sake samu kuma. ********** Jaruman kasarmu suna can suna aiki tukuru bisa umarnin da kasa ta basu na wanzar da zaman lafiya a daya daga cikin kasashen gamayyar ECOWAS. A yayin da magidanta suke tashi da safe su je ofishoshinsu yamma na yi su koma gida ga iyalansu, su ci, su sha mai kyau, su kalli matansu da 'ya'yansu su ji dadi wadannan sojoji suna cikin dokar daji suna fama da cizon sauro da wasu nau'in kwarin, rashin abinci mai gina jiki, karancin tsaftataccen ruwa balle ayi maganar wanka kullum da sauransu. Masu aure a cikinsu suna kewar matansu amma babu halin kasancewa dasu. Yau da gobe kunnuwa sun saba da jin harbi da karar tashin bomb. Da idanunsu suke ganin 'yan uwansu, abokansu harsashi ya huda wani sassa na jikinsu sun mutu a take. Ko kuma bomb ya tashi dasu kana kallon mutumin da kuke tafiya kuna hira dashi ya tarwatse gabobin jikinsa sun watsu ko ta ina. Jaruman nan sun yarda sun aminci su sadaukar da rayukansu a duk lokacin da kasa ta bukata domin zaman lafiya da kwanciyar hankanlin al'ummar kasarsu. Babu ruwansu da addini, kabila ko wata al'ada. Sun hadu akan abu daya ne wato TSARO na rayuka da dukiya. A yayin da wahala tayi wahala, anga jiya anga yau a fanin rashin makusanta ko a kama mutum a sansanin abokan gaba a gana masa azaba domin ya fadi wani sirri da za'a iya cutar da nasa 'yan uwan sai ka ga zukatansu sun bushe ana yi musu kallon mutane marasa tausayi da imani. Sai dai abubuwan da idanunsu suka gani da wanda kunne yaji wani fa har ya bar duniya bazai taba kusantar abu makamancin wannan ba. Jarumanmu ababen alfaharinmu, sadaukanmu da babu albashin da kasa zata basu da zai wanke ciwuka na zahiri da badini da suke dawowa dasu daga filin daga. Ga kuma iyalansu a yashe madogaran nasu, bangon jinginar nasu basa nan. Wata hudu da tafiyarsu Zayyan sun fara jiyo kamshin komawa gida wata rana da yamma gari ya hade yayi bakikkirin ruwa zai iya saukowa a kowane lokaci wani mutum yazo wurin gaje gaje dashi da shiga irin ta mutanen wani kauye a kusa dasu. Jikinsa duk raunuka yace 'yan tawaye sun yiwa garinsu kawanya suna harbi kan mai uwa da wabi. Sun riga sun san mutanen suna yin haka shiyasa su ka shiga motarsu ta yaki su ka durfafi kauyen da hanzari. A bakin wurin da yake kamar gate dinsu ne su ka hadu da motar su Major Mustapha. Ya fake da aiki ya taho ganin kannensa. Duk da bambancin matsayi bai hana Zayyan zuwa ya rungume shi ba. Major yayi turus yana cewa. "Stand at attention Lady" Zayyan ya dago yana gyara rigarsa ya dan basar "Sorry Sir" Major Mustapha sai yayi murmushi yana mikawa Hadir hannu. "My Ladies are all grown up, sun dena dariya" Zayyan ya kara gyara fuska sai dai dole dariya ta kwace masa. Karar bomb suka ji mutumin da ya kawo rahoton yace ‘yan tawayen sun kai mota shida. Su Major Mustapha sai kawai su ka bisu. Sai da suka yi rabin tafiya kawai babu zato babu tsammani sai tashin bomb suka ji a gabansu ga ruwa ya fara sauka. Mutane ne suka fara bullowa ta tsakanin bishiyu da yawa ba na wasa ba sun zagayesu. Babu wata mafita sai fitowa suka yi suna musayar harsashi ga wuta motarsu ta kama saboda tankin mai da aka harba. Bayan wani lokaci a cikin wannan yanayi ruwa mai karfi ya soma sauka kamar da bakin kwarya a cikin jejin gari yayi duhu baka ganin komai sai tashin kura, hayaki da wutar da ruwan bai gama kashewa ba. A gefe guda kuma Zayyan da Hadir ne suke gudun ceton rayukansu sakamakon bomaboman da suka tashi a wurin har uku ga harbin bindiga da bazasu iya tantance takamaimai daga ina yake fitowa ba. A motocin yaki uku suka fito banda babbar range rover da suka ciko ta su Major Mustapha. A lissafe sun kai mutum ashirin da takwas amma su biyun suka rage wanda kusan da taimakon Zayyan ne Hadir bai mutu ba. Duk inda ka juya gawarwaki ne kwance cikin ruwa da jini. Kallo daya zaka yiwa wurin zuciya ta tsinke kaji inama dai mafarki ne. Duk mai imani bazai so koda makiyinsa ya tsinci kansa a wurin ba. Suna cikin wannan jeji dumu-dumu a tsakanin abokan gaba. Hankulansu a tashe kunnuwansu basa jin komai sun dode saboda karar bomb ya yi musu karfi. Zayyan ne ya hango Major Mustapha wanda a bisa la'akari da matsayi shine shugabansu a wannan fitar. Mutumin da yake tsananin mutuntawa kwance yana daga hannu. Baya yayi da sauri Hadir yayi masa kallon mamaki don bai iya ganin komai shi saboda karfin ruwan "kada kace min komawa zakayi? Kazo mu bar wurin nan don Allah" Kallon Hadir yayi ya sake kallon Major din ya koma gareshi a guje. Dago shi yayi da zafin nama sautin harsashi yasa shi komawa ya kifa a kansa suka fadi tare. Wata siririyar kara Major Mustapha ya saki mai cike da tsananin azaba wadda ta saka shi kai duba gareshi. Wani mummunan firgici ne ya saukar masa ganin kafar Major din ta dama a gutsire bomb ya tarwatsata. Zuciyarsa ce tayi nauyi ya soma kokarin daga shi domin su gudu. Wata damka yaji ya kai masa ruwa yana wanke musu fuskoki "Lieutenant get out of here" Bai saurare shi ba ya ciccibe shi duk da cewa ya fishi girma sosai ya saba shi a baya. Ture shi yaji yana yi yana dan dake muryarsa "this is my final command to you Tureta. Go!" Sojoji sun horo da tsananin biyayya ga na gaba amma wannan karon bazai bi ba. Gudu ya soma yi dashi suka nufi inda Hadir yake tsaye hannunsa na zubar jini sakamakon harbinsa da akayi suka soma yankar daji. Cak ya tsaya ya dena tafiya har Hadir yana cewa "muje mana" Gabansa ke lugude ya kalli kafarsa ya dago a razane "Karbe shi ku bar wurin nan" Major ya dan leko da kansa ta saman kafadar Zayyan "Lieutenant?" Wata ajiyar zuciya ya sauke kafin Hadir ya karbi goyon duk da shima yana da raunuka. Matsawa yace suyi nesa dashi sannan ya dago idanunsa da suka jike da hawaye sosai. Kamar mai rada yake musu bayani. "Bomb ne" Su biyun duka suka kalle shi a gigice. Bai nuna damuwa ba ya cigaba da magana hawayensa suna tona asirin firgicinsa. Motsi kadan zaiyi bomb din wanda aka binne cikin kasa ya tarwatsa shi. Daya bayan daya yake kallonsu "My friend..." yace da Hadir "....Major am afraid this is the end" Abinda Major ya dade baiyi ba ya soma shima sai kuka duka su ukun babu mai rarrashin dan uwansa. Kafarsa ce ta danyi rawa cikin karaji yace su bar wurin. Ba yadda suka iya dole suka bar wurin a guje zukatansu suna kuka idanu na hawaye. Basuyi nisa sosai ba suka jiyo muryarsa mai dadin sauraro idan yana yi musu limanci. "Mairama, Alheran waye zai dubi iyalina?" Kuka ya fashe dashi sosai a hankali ya soma karanto kalmar shahada yana ji a ransa wannan ma dama ce da Allah Ya bashi. Sunyi gudun rabin kilometer suka ji wata gigitacciyar kara wadda tasa su biyun faduwa su ka gangara kasan wani katon rami. Kafin su kai kasansa daga Major Mustapha har Hadir tunaninsu yana ga Zayyan Muhammad Tureta. Zayyan sarkin barkwanci, mutum mai tsananin so da kaunar iyalinsa da basu da wani wanda zasu jingina dashi suji dadi idan ba shi ba ya mutu a bakin aiki bayan yayi matukar kokari wurin tseratar da rayukansu. [02/11 7:29 AM] My 2nd Mtn: 13. BAYAN AWA TALATIN DA BIYU Mutumin da ya kai rahoton karya ga rundunar su Zayyan shine durkushe a babban sansanin da su Major Mustapha suke. Kuka yake kamar karamin yaro ga sojoji sun tsare shi babu wasa a idanunsu. "Ka tabbatar ba yaudararmu kazo sake yi ba?" Cewar Captain Jonah. Mutumin ya daga idanunsa jajir ya sake maimaita musu cewa yan tawaye ne suka kamashi. Sunyi masa mugun duka sannan aka umarce shi da yaje ya san yadda yayi ya kawo sojojin Nigeria wannan wurin. Idan baiyi ba garinsu gabadaya zasu tasa. Tsoro ya sanya shi cika umarni. Amma suna zuwa da ya ga me ake yi ya gudu. Shine yazo nema musu agaji duk da yasan da wahala a samu mai rai cikinsu. Yana rufe baki wani zuciya ta debe shi ya buga masa kasan bindiga a keya ya fadi sannan ya bishi ya rinka duka da kafcecen takalminsa. Da kyar aka rike shi kowa ya sani akwai kaninsa uwa daya uba daya a cikin wannan sansanin. Motocinsu suka cika da makamai suka tafi tare da wannan mutumin. Daga nesa suke hango sauran hayaki ga kauri ya karade wurin. Dirgowa suka shiga yi daga motocin suna gudu har suka je wurin. Su din sojoji ne fa jaruman maza amma hankulansu sunyi mumminan tashi da ganin wannan kisan gilla da aka yiwa mutanensu. Binsu suka rinka yi daya bayan daya wadanda jikinsu yayi alamun harbi ne kawai likitocin cikinsu suna dubawa ko akwai masu rai. Basu yi dacen samun ko daya ba. Duk da haka shugaban tawagar yace su bazu cikin dajin babu mai tafiya sai sun tabbatar ba'a bar kowa ba. Mutum biyu ne suka bi hanyar da su Zayyan suka wuce cikin sa'a sai gasu a bakin kwazazzabon da Major Mustapha da Lieutenant Hadir suka fada. Suna hangosu daya ya dira ciki dayan kuma yana daga waje ya fara kiran ga wasu gawarwarkin a nan. Sai dai me, yana juya Major Mustapha yaji yayi wani irin gurnani na azabar ciwo. Ya zubar da jini ba kadan ba wurin da kafar ta cire ya kumbura suntum ta soma yin kore. Ihu yasa yana kiran suyi sauri wannan yana da rai don bai ma gane shi ba. Ya koma ya juya Hadir. Mamaki karo na biyu, shima da ransa saboda bugun zuciyarsa da yake a raunane amma baya motsa komai na jikinsa. Sauran sun zo an taru an fitar dasu cikin sauri suka isa sansanin inda aka wuce dasu bangaren kula da lafiya. Daki ne madaidaici da 'yan kayayyakin taimakon gaggawa da abinda ba'a rasa ba. Komai cikin sauri ake gabatar dashi domin alamu sun nuna su biyun sun galabaita fiye da zato da tsammani. Anyi nasarar cirewa Hadir bullet a hannunsa sai dai buguwar da yayi wanda suke tsammani a kansa ne har yanzu bai motsa ko da yatsa ba. Babu kayan gwaje-gwaje sosai da zasu iya gano ainihin matsalarsa. Major Mustapha shima an gyara wurin da kafarsa ta cire. Bayan allurai da ruwa da ake kara masa babban likitan Major Dalhatu ya tafi ofishin ogansu gaba daya a wurin. Izinin shiga ya nema ya tsaya a kame a gaban Colonel Fredrick Madueke. "Sir they need medical attention more than we can provide" Lt Col Madueke ya dago idanunsa sunyi ja kamar gauta. A yini daya sun rasa sojoji da dama wanda duka a karkashinsa suke a wannan tafiyar. "I am trying to reach the HQ at Monrovia Captain . We need to fly them back to Lagos" Captain Dalhatu ya juya ya fita bayan ya sara masa. Yasan Lt Col Madueke akwai tsantseni. Bazaiyi saken da rayuwar wadanda suka tsira zata salwanta ba a nashi bangaren. Kwana daya, biyu, uku, hudu....shiru headquarter bata turo helicopter da suka roka domin a kai su Major airport din Monrovia ba. Lt Col Madueke kullum yana magana da headquarter sun ce suna jiran feedback daga Nigeria. Abu yaci tura suka debesu da kansu a motoci ga gargada da komai zuwa Monrovia din. Nan ma a basu dama ko izinin fitar dasu ya zama aiki. A haka sai da suka kwashe sati uku ana abu daya. Hadir yana nan jiya-e-yau. Major Mustapha kuwa ya farka amma azabar ciwon kafarsa tasa ya koma yana sumbatu. Dole yayi sambatu wurin ciwon nasa ya soma fitar da ruwa mai wari saboda kwayoyin cuta da suka shiga ga rashin kayan aiki. Anyi rigima harda nunawa juna bindiga tsakanin Capt Dalhatu da wani soja a headquarter din saboda rashin daukar patients dinsa da akayi. A haka sai manya masu mukami ko wanda yasan wani shine abin dubawa. Mu kasarmu har kullum wa ka sani wa ya sanka ce. A rana ta ashirin da bakwai Allah Yayi aka dauki Major Mustapha da Lt Hadir zuwa Lagos. Yanayin da suke ciki suna bukatar taimako na gaggawa sosai. Kai tsaye aka wuce dasu 68 Nigerian Army Reference Hospital dake Yaba a Lagos. An yiwa Hadir gwaje gwaje karshe dai likitoci sunce kawai a jira ko dai ya tashi ko kuma rai yayi halinsa. Idan da hali ana bukatar 'yan uwansa domin jinya da kuma fara biyan kudaden asibiti idan ana son su cigaba da aiki a kansa. Buguwar da yayi a kansa sai ya farfado zasu san ainihin iya damejin da tayi masa. Major Mustapha kuwa aiki gagarumi yake bukata a rubabbiyar kafarsa. Ciwo wata guda ya ga izaya ra'ayil aini har yanzu bai san waye a kansa ba duk da ya farka. Dungulmin kafar ke fitar da tsutsa saboda rashin gatance musu da kasa tayi a lokacin da suke da bukata. Gasu da rauni ga rashin kayan aiki a inda suke. Anzo kasar tasu kuma asibiti na bukatar makudan kudade domin su yi masa aiki a yanke abinda yayi saura na kafar. Sojoji da basu kirguwa sun tafi da lafiya sun dawo gidajensu da nakasa ta har abada. Shima dai an bukaci a nemo nasa iyalin domin kulawa dashi da kuma kudin asibiti wanda gwamnati bazata iya daukar nauyi ba duk kuwa da cewa a kokarin bin umarninta suka riski kawunansu a wannan hali. BOYAYYUN JARUMAI (NA SARAWA MATAN SOJOJI) Jiniya ce irin wadda aka kunna ranar tafiyarsu yau ma aka saki. Motoci manya na sojoji suka rinka shigowa barrack din a guje zuwa bangaren ofisoshin manyansu. A can aka bada cikakken rahoto game da mutuwar gabadaya sojoji da aka dauka a ranar tafiyarsu Zayyan daga Giginya Barrack da kuma halin da Hadir da Major suke ciki. Wuri ba sai ya kaure da hayaniya ba, manyan sojoji ana ta shige da fice suna samun cikakkun bayanai. Tattaunawa ce tsakaninsu akan yadda ya kamata su bullowa lamarin. Masu aure cikin wadanda suka tafin wurin tara ne sauran duk samari. Wasu ma basu dade da zuwa barikin ba. Matan wadanda suke asibiti dai babu yadda za'ayi a boye musu. Bisa wannan dalilin aka buga takarda mai dauke da bayanin halin da kowanne yake ciki za'a bawa matarsa. *********** Mairama tana gidan Zainab taje kitso suna zaune daga bayan gidan wanda katanga ta karesu babu mai ganinsu. Sannan an dan zarta bangon gidajen ta barin hagu da dama domin ya zama kariya tsakaninsu da gidajen kusa dasu. Sai dai ba'a hade ginin ba zasu iya wucewa. Yawanci matan ke amfani da wannan wurin domin ayyukan da suka fi karfin cikin gidan kamar suya da babbar sallah. Zainab tana yi mata kitson gefe Radhiya ce da Ibrahim an baza musu tarkacen wasa suna ta ihunsu irin na yara da duniya ta yiwa dadi. "Ke yaushe zaki yi kitson ne?" Mairama ta tambayi Zainab "Ai kallonki nake duk sati kitso, ni nan ina jiran muji kishin kishin din zasu dawo ne naje ayi min famin (perming ko saka relaxer). Ya tafi ya barni da kitson ya dawo ya tarar dashi. Hum'uhm" Dariya Mairama tayi "nima da kika ga na nacewa kitson bana son haihuwa da kai a tsefe ne. Lokacin wannan yarinyar kan na kusa cizgewa don azaba" Tafawa suka yi suna kyakyata dariya kowacce tana tuna nakuda da haihuwarta. "Kin gansu tafiya daga wata uku an shiga na biyar ga ki haihuwa ko yau ko gobe" cewar Zainab da 'yar damuwa a fuskarta. Wannan dadewar tasu ta dami matansu sosai. Kowacce dai tana kokarin daurewa ne don kada su rinka tadawa juna hankali. Amma a zahiri babu wadda bata kukan dare idan kewar mijinta da rashin sanin halin da suke ciki ya dameta. Radhiya baki ya bude ba laifi don akwai surutu. Zaman da take yi dasu Zahra shi yake kara bude bakin. Ta dai fi likewa Awwab saboda yawo. Sai ya dauketa suyi ta karade barikin nan. Yanzu ma 'yan takalmanta masu madauri aka sanya mata bayan an gama kitson tasa kuka ganin sun doshi gida "Ummi, Amma wawo" nufinta a kaita wurin Hamma su tafi yawo. "Hajiyar gantali ni dai na gaji. Kiyi fatan daga islamiyya ya biyo sai ya kaiki wurin Mami" Tana jin sunan Mami kuma kukan ya karkata tana kiranta. Tana ta bata baki yarinya taki shiru. Ba yadda ta iya dole ta kaita gidan. Mami tana cewa ta zauna tace gida zata tafi jikinta babu dadi. Radhiya harda yi mata bye bye tace idan Awwab ya dawo yazo ya karbar mata kaya don tasan yau ma ita kadai zata kwana Mami bazata bari a dawo da Radhiya ba. Cikin dare bacci ya gagareta kamar yadda take ta fama 'yan kwanakin nan. Kullum cikin mafarkin Zayyan take, watarana ta tashi da kuka wani lokacin kuma idan mafarkin yayi dadi ta tashi da farinciki. Sai dai a can kasan zuciyarta tana fama da wani irin firgici wanda ta kasa gane dalilinsa. Envelop din da ya bar mata ranar tafiyarsa ta dauko ta shafa amma har yau taki budewa. Tsoron me ya rubuta take yi, karshe ma dai ta fadawa kanta idan ya dawo ya karanta mata da kansa. Haka ta cinye daren a tunani baccin da kyar ya dauketa. Bayan tayi asuba ma komawa tayi abinta ta kwanta. Wurin tara na safe ta ji bugu kamar za'a balle mata kofa. Haka ta taso da hijab a baibai saboda sauri ta bude tayi karo da Christie. Itama makociyarsu ce tare da mijinta akayi tafiyar. "Mama Radhiya e bi like say your sister don die ooo. She just knack her head for ground after one officer wey I no know come give her letter" Cikinta ne ya murde da tsoro ta bi bayan Christie da gidanta yake kallon na Zainab. Mata ta ga sun zagaye Zainab ga Ibrahim yana ta tsala ihu. Ashe a kansa ma ta fada bayan ta karanta takardar Allah Yasa akwai mata a wajen suka dauke shi. Da kyar Mairama ta durkusa a gabanta tana rike mata hannu "Zainab menene?" Takardar ta iya mika mata kawai. Mairama tana karantawa itan ma sai kuka da tausayin Hadir. Christie ta cewa ta shiga da Zainab gida tana zuwa. Hankali a tashe tana baza sauri ta tafi gidan Mami don ta fada mata. A can ta tarar da wani mummunan tashin hankalin. Mami ke kuka sosai tana ta hada kaya ta jibge akwatuna biyu a falon tana ta watsa kayanta da na su Fauziyya a ciki. Gabadaya yaran suna gefe kowa yayi tsit harda Radhiya da ta ga babu mai kula ta. Awwab bai san me ya faru ba amma ganin mahaifiyarsa na hawaye shima yake tayata. Mami na ganin Mairama taje ta rungumeta ta sake fashewa da kuka "Ummin Awwab na shiga uku, ina zan sanya kaina" Duk ta gama tsorata ta daure tace "addu'a zakiyi Mami ba kuka ba, komai yayi zafi maganinsa Allah. Me ya faru?" "Daddy ne..." sai ta mika mata takardar ta karanta da kanta. Hawaye ne ya cigaba da zuba a fuskokinsu Mami tace "Katsina zan tafi yanzu. Sai naje na ajiye yaran in sanar dasu sai mu wuce Legas din" Suna haka Zainab ta shigo ta goya Ibrahim da har yanzu yake kukan faduwarsu ta dazu tana jijjiga goyon tana kuka. Mairama ce tayi mata bayanin me ya sami Major kuma. Su uku suka hada kai suna ta kuka abin tausayi. Kusan a tare Mami da Zainab su ka fuskanci Mairama "Zayyan fa?" Dammm taji gabanta ya yanke ya fadi ta juya a guje ga nauyin ciki ga kafarta da take yawan rikewa ta nufi gidanta. Tsoronta daya kada itama anzo sanar da ita halin da Zayyan yake ciki ba'a sameta ba. Bata tarar da kowa ba ta tsaya tana ta haki tana jin kamar za ta amayar da abinda yake cikinta a lokacin. Da jan kafa ta koma gidan Mami sun gama shiri ita da yaran. "Zainab, Mairama...Allah kadai yasan ranar sake haduwarmu. Komai nawa ya danganta da samun saukin Daddy" "Babu komai, Allah Ya basu lafiya baki daya." "Amin" suka amsa sannan Zainab ta kara da cewa itama zata je ta sanar da nata iyayen ne domin a aika Kano gidansu Hadir. Sannan a san yadda za'ayi a dawo dashi gida. Ji suke kamar daga ranar sun rabu kenan suka yi ta kuka sosai. Radhiya da kyar aka rabata da Awwab ta makale masa wuya tana ta ihun Amma. *********** Gidan iyayenta Zainab ta wuce cikin kasa da awa guda ta isa. Bayan ta yiwa mahafinta bayani a take ya taso babban wan ta ya bashi kudin mota yace ya wuce Kano gidansu Hadir ya sanar dasu. Zainab na kuka tace masa su yaushe zasu tafi Lagos din. "Zainab kinfi kowa sanin halin da nake ciki. Kudin da na bawa yayanki wallahi harda na cefanmu na yau da gobe ne. Kasuwar babu kudi yanzu sai nayi huluna biyar ba'a sayi ko daya ba" Shiru tayi wani hawayen yana sauko mata. Ita ta sani kuma bata boyewa iyayenta talakawa ne fitik. A Kano ma iyayen Hadir ba wasu masu karfi bane. Sai dai sun fi nata sosai. Albashin Hadir shine yake turawa gida kuma a haka yake yiwa iyayenta ihsani lokaci zuwa lokaci. Zuciyarta ta gama tsinkewa da wannan bakon lamari a gefe guda kukan Ibrahim yaki tsagaitawa. Mahaifiyarta ta karbe shi tana ta juya shi da shafa jikinsa ashe ya sami gocewar kashi ne a hannu sakamakon faduwar da Zainab tayi a kansa. Babanta ya karbe shi ya tabbatar hakan ne yace ta tashi su tafi gidan dori. "Wayyo Allahna Baba. Da me zanji?" Ta kara rushewa da kuka. "Zainab kamar baki da ilimin Tauhidi? Ki fawwalawa Allah ki yawaita addu'a. Daga gidan dorin zan wuce wurin kawunki ko Allah zai sa yana da abinda zai ranta min ko ni kadai ne sai na wuce Ikkon. Kinsan babu yadda za'ayi na barki kije ke kadai baki san ko ina ba ga yaro babu lafiya" Kai ta gyada kawai suka tafi gidan dorin aka gyara masa hannun. Ibrahim ya zama abin tausayi don ya jigata ba kadan ba. Suna dawowa sai zazzabi da amai ya sarke shi ko hannu baya iya motsawa da kyau. Zainab tayi kuka har taji babu dadi.A rana daya rayuwar wannan baiwar Allah ta juye gabadaya. Miji yana asibiti a wata uwa duniya, amma babu kudin zuwa gareshi. Babanta yace su jira yayanta da yaje Kano ya dawo. Idan iyayensa sun dauko shi sai ta tafi can ko da yaya zai samu ya biya mata kudin mota. Yini kuka, kwana kuka haka ranar ta kasance mata. *********** Gidansu Mami unguwa daya ne da na su Major Mustapha. Iyayensu maza su biyar ne a gidansu. Baban Major ne na biyu nata kuma auta. Da suka tashi aure sai suka zauna a gidajen da katanga kadai ke raba su. Daga tasha bus ta hau zuwa unguwar tasu. Tana shiga layin ta hango babban wan iyayen nasu da suke kira Alh Baba. Yayi shigar mutumci da babbar riga da farin rawaninsa irin na malamai. Motarsa kirar Pigeout (pijo) zai shiga daya daga cikin yaransa zai kaishi unguwa ya hangota. Dakatawa yayi don ya tabbatar da wace ce saboda ita da Usainarta sai kayi musu farin sani kake iya tantance su. Tana matsowa ya saki murmushi saboda daga yaranta ya ganeta masu kama da mahaifinsu "Mutanen Shehu saukar kenan?" Daga ita har yaran sun durkusa da niyar gaishe shi kawai ta fashe da kuka. Yaran ya kalla yasan duk yadda akayi wani abu ya faru "Kai Muhammadu wuce ciki da kannenka" ya fadawa Awwab. "Ke kuma muje" ya nuna mata hanyar gidansu Major. Awwab kamar ya bita ganin tun a gida suke ta kuka amma tarbiyarsu tasa ya bi umarnin kakan nasu. Ciki suka shiga matan gidan suna ta murna ana tambayarsu mamansu suka ce tana wurin Alh Baba. Basu sami baban Major ba sai Iya mahaifiyarsa. Alh Baba ya tura aka kira ragowar kannensa sannan suka bukaci jin dalilin zuwanta tana kuka. Duk sun sani cewa ya tafi Liberia tunda yazo yayi musu sallama. Tana kuka ta sanar dasu abinda takardar da aka bata ta kunsa. Gidan sai kuka tamkar ance ya riga ya rasu. Bayan dawowar mahaifin Major iyayen su kayi zaman shawara. An daidaita magana akan cewa Alh Karami baban Mami da kuma yayan Major Mustapha da suke uwa daya uwa daya su ne zasu tafi. Mami ta kasa daurewa tana kuka, Alh Baba ya dubeta "kiyi hakuri Hassana. Su dinmu dauko shi zasuyi a dawo dashi gida yayi jinyar a kusa. Legas tayi mana nisa. Idan munje da yawa bamu san ina zamu kwana ba" Ba haka taso ba ko kadan amma bata da yadda zata yi. Tana ji tana gani asubar fari suka kama hanya a motar Alh Baba. ********** Kwanaki biyar kenan da samun sakon da ya tada hankula a Giginya army barrack. Mairama ta rame sosai a 'yan kwanakin. Radhiya ma bata samun kulawa yadda ya kamata saboda tun ranar da suka tafi fargaba tasa ta fara nakuda a tsattsaye tana daurewa. Rayuwa take yi mara dadi. Babu miji kuma babu wadanda suka zame mata tamkar 'yan uwa na jini. Tarin fargaba ne ya cika zuciyarta da kokonto. Ta damu tasan halin da su Hadir suke ciki ga kuma rashin sanin komai game da Zayyan ya sanya take jin kamar zata yi hauka. A kwana na shida ciwo yaci karfinta ta daure taje ta buga kofar gidan Christie. Ita dinma duk zulumi da fargaba sun cinyeta tana ta ramewa. Tana ganin Mairama a haka tasan nakuda ce. Gida ta koma ta dauko zani ta saba Radhiya a baya sannan ta taimaka mata suka tafi asibitin sojojin inda take awo. Ta kwashe kusan awa shida tana fama banda wanda tayi a cikin gidanta kafin Allah Yasa ta sauka lafiya ta haifi danta tamkar Zayyan yayi khaki don yafi Radhiya kama dashi sosai. Likitocin sun bata kulawa yadda ya dace sannan aka kaita dakin da zata huta saboda wahalar da tasha. Christie tace mata zata je gida tayi girki ta kawo mata don taji kwari. Matar akwai kirki sosai ita ma. Radhiya ta sake dauka dama da tana ciki wurin haihuwa ta siyo mata fanke a 'yar kasuwar gefen asibitin taci ta koshi ta debo ruwa a famfon waje ta bata. Suna fita ta sake daukan jaririn sai kawai tasa kuka. Yaron da tayi fatan zuwansa duniya mahaifinsa ya karbeshi yayi masa addu'a. Sai gashi ta haihu din a lokacin da bata da masaniyar halin da yake ciki. Karin kukanta yau ta haihu babu kowa nata sai Christie da ta tsaya mata tamkar 'yar uwa. Mami da Zainab suna can lalurar mazajensu ta saka su a gaba. Yanzu ita wa take dashi da zata tura a sanar da gidansu da gidan iyayen Zayyan. Tun tafiyarsa babu wanda ya tako ganinta cikin 'yan uwansa ko da wasa. Me ya ja mata nesanta da 'yan uwanta da na mijinta da rashin zama cikin mutanen da tasan sunyi tarayya a yare, addini da al'ada? Auren Soja ta bawa kanta amsa. Sojan ma Zayyan wanda idan za'a sake bata zabi tayi rantsuwa har ranta shi din a sojansa zata sake aure. Tana sonsa kuma tana alfahari da aikinsa kamar yadda yake yi shima. Tunani ta zurfafa tana yi akan rashin sanin yaya zata yi labarin haihuwarta ya iske danginsu. Lokacin Radhiya shi yayi komai abinsa. Yanzu kuwa komai ya dawo gareta. Kan jaririn ta shafa tana hawaye "Daadaa yaci burin ganin zuwanka duniya ko suna bai yarda mun zaba ba saboda yace yana son yayi yiwa jaririnsa huduba da kansa" Yaro yana baccinsa cikin kwanciyar hankali ta kwantar dashi a gefenta daga jikin bango tana shafa shi a hankali. "Sojana ka bar min amana mai nauyi. Baka fada min yaya zanyi ba idan baka dawo da wuri ba" Kuka ta shiga rerawa a hankali tana jin wani matsanancin ciwon kai. Kwanciya ta gyara a gefen dan ta lumshe idanunta ta baiwa kofa baya. Tana ji likitoci biyu suka shigo dukkansu sojoji da nos guda daya. Wanda ya karbi haihuwarta ya yiwa dayan bayanin cewa ta zubar da jini kuma jininta ya hau kada a sallameta sai gobe. "Na fahimta Dr. Ina file din nata?" Ya tambayi Nos ta mika masa. Zaro idanu yayi ya dago yana kallon wancan likitan. "Matar Lt. Zayyan Tureta ce? Sune last week akace gabadaya unit dinsu...." Wanda ya karbi haihuwar yayi saurin sa hannu akan lebensa yana magana a hankali harda juya harshe zuwa turanci a zatonsu bacci take, kuma kana yi mata kallo daya ka ga bafillatana wadda ake musu kallon basu da wani ilimin boko sai kiwon shanu. "Shhh I don't think they know what has happened" Mairama taji gabanta ya fadi wani abu yana mata yawo a jiki tun daga kai har tafin kafa, sai ta daure ko motsi bata yi ba. Nos din ta kalli bayanta da tausayawa a hankali tace. "I pity their wives" Basu san daga ina ba sai ganin Mairama suka yi rike da kafadun Nos din idanunta a rufe cikin karaji take tambayarta "what happened to my husband?" Kallon kallo suke yi sai taji gabadaya duniyar tana son kife mata. Durkushewa tayi gwiwoyi a kasa tana kallonsu tamkar wadda ta sami tabin kwakwalwa. "Don Allah don Annabi ku fada min gaskiya" Tashinta yazo musu a bazata haka fahimtar turancinta shiyasa suka kasa bata amsa kai tsaye. Shirunsu kadai ya isheta amsar da take nema da yanayin da taga sun shiga na tausayinta da tsoron fada mata gaskiya. "Kinga ki kwantar da hankalinki idan kinji sauki za'a fada miki komai" Murmushi tayi mai sauti tana ja da baya da baya har ta kai jikin bango ga hawaye tana zubarwa kamar ruwan famfo "da hankalina fa, nasan abinda nake tunani hakane. Innalillahi wa inna ilaihi raji'un. Ya Allah....ahhhh. ....kirjina..wayyo Allah.. Ka jikanka Sojana" Likitan da yazo zai canji wancan aiki ya dan matso kadan "kizo ki zauna...uhmm" Nos tace "Mairama" "Ok Mairama ki zauna muyi magana kinji" Jaririnta kawai ta dauka ta saka shi a kafada tana cigaba da kukanta tana cewa "tun yaushe ya rasu?" Basu iya cewa komai ba tayi hanyar kofa suna kiranta taki tsayawa. Sai dai kafin ta fita jikinta ya soma rawa likitan da yafi kusa da ita yayi saurin karbe jaririn ta fara neman faduwa tana wata irin jijjiga ga jini ya balle mata. Nos da daya likitan ne suka kamata aka dora akan gado suna neman ceto rayuwarta. [02/11 7:29 AM] My 2nd Mtn: 14. Kwana biyu da rabin wuni Mairama tayi kafin ta gane inda take da babbar jarabawar da ta tunkaro rayuwarta. Ta farfado da misalin uku na rana washegarin ranar da ta haihu. Idanunta a rufe suke amma tana iya jiyo maganganu kamar ana fada. A hankali ta fara fuskantar me ake cewa wanda yayi sanadin fitowar hawaye daga idanunta, kuma har lokacin a rufe suke. "Ni dai na fada miki gobe zan tura Rayyanu yaje garinsu ya sanar da iyayenta su zo su dauketa don bazan iya jigila ba." "Haba Maikudi kai kuwa baka ganin ga danyen jego ga rashin lafiya. A barta ta huta mana" Gwaggo Ladi da tayi maganar ya kalla darajar mijinta Mal Aminu ya kasa bata amsar da yayi niyya. Wani dan tunani yayi ya kara tabbatarwa gara yabi komai a hankali don samun biyan bukata. "To naji sai ta zauna har sai ta gama takaba an raba gado. Ince ko hakan yayi" ya mayar da kallonsa ga Mal.Aminu da ya dauke kansa saboda takaicin halin Maikudi. Yaron ya fita zakka tamkar ba jinin Mal Muhammadu ba. Mal Aminu da ya gama tofe jariri da addu'a ya dago kansa "bana son hauka Maikudi. Takaba dai tana haihuwa ta fita. Sannan tun muna shaida juna kada inji kada in gani, kaf abinda Zayyanu ya bari na matarsa ne da 'ya'yansa tunda yana da da namiji." A fusace ya juyo "inji uban wa?" "Inji ubanka" Mamaki kamar ya kashe shi saboda Jume ce ta bashi wannan amsar. Akan tabarma take tana bawa Radhiya abinci. Daga jiya zuwa yau tayi wuri-wuri da ita. Rasuwar Zayyan ta tabata fiye da zato da tsammaninta. Duk wata mugunta da ta taba yiwa mahaifiyarsa dashi kansa sune suka yi mata dabaibayi. Cikinsu babu wanda ya taba nufinta da sharri gashi sun bar mata duniyar tayi yadda take so. Nadama ce ta gaske take nukurkusar zuciyarta. Ga Maikudu don abin kunya daga jiya zuwa yau banda rashin mutumci babu abinda yake zubawa a dakin. Daure fuska ta sake yi "Saboda baka san me kake yi ba ace kaninka ya rasu amma ko a jikinka?" "Kina ji fa aka ce yayi wata guda harda dorin kwanaki, duk dacin mutuwa ai yaci ace tayi sauki an fara fuskantar gaba" Mairamu ta kasa boye kukan zucin ta koma yi a fili. Ashe har yafi wata da rasuwa bata da masaniya. Shine take ci tasha har tayi wasa da dariya? Ashe Sojanta ya koma ga Allah take ta tunanin dawowarsa. Yanzu shikenan nata mijin saboda soja ne ko kabarinsa babu wani danginsa da zai sani? Anyi masa wankan gawa? An sallace shi? Wace irin mutuwa yayi duk basu sani ba. Kukanta ya tsananta Gwaggo Ladi ta tashi ta matsa kusa da ita ta tsaya a gefen gadon. "Mairama hakuri zakiyi da yawaita yi masa addu'a" Rarrashinta suke ta yi ita da Jume sannan Mal Aminu ya fita saboda ance ta shayar da jaririn. Maikudi yayi qiqam kamar sanda sai da Jume tace ya fita, yayi waje yana surutai. Yaron ta karba wanda rabonta dashi tun jiya. Yaji yunwa kuwa sai ruwa aka rinka bashi da tana kwance. Gwaggo Ladi tace Malam yayi masa huduba da Muhammad Zayyan. Ina fata hakan yayi miki" Hawayen Mairama har fuskar jaririn tayi murmushi "Sojana Allah Ya raya min kai." ********** "Wai Zayyanu dai Zayyanu soja mijin 'yata Mairama kake nufi?" Malamijo yayi maganar kamar zaiyi kuka. "Shi nake nufi. Allah Yayi masa rasuwa a kasar da suka je" Rayyanu ya bashi amsa. Shi da Badaru da 'yan uwansu mata kaf mutuwar Zayyan ta shigesu sosai. Mutum mai barkwanci da saurin manta bacin rai. Duk yadda su ke bata masa bai hana shi kyakyawan zumunci dasu ba ko da su bazasu yi masa kallon arziki ba. Malamijo ya daga hannu ya dora a ka "Laaaaahhhh ha'ila ha ilallahu, kaico Mairama, 'yar marainiyata ta rasa miji kuma" Lokaci kankani a tsakani zance ya bazu ko ina mijin Mairama ya rasu a filin daga. Mutane suka fara zuwa yiwa Malamiji ta'aziyya yana cewa nan da kwana biyu zai wuce Sakkwato. A cikin gidan ma jikinsu duk yayi sanyi. Ba wani haduwa suke yi sosai ba saboda nisan garuruwansu amma duk da haka a iya lokutan da su ka ganshi anyi masa shaidar arziki. Malamijo yasa a dafa abincin sadaka ya saki bakin aljihu abinda basu saba gani ba. Cikin yaransa maza ya tura babban mai bin Mairama a shekaru yaje Balan ya sanar da Nene Marka. Idan zata bisu ta'aziyya ta taho washegari su wuce jibi. Sannan ya tura mai bi masa Kano gidan Salame. Suna zaune shi da 'yan gaisuwa wani yake tambayar yaya Zayyan din ya rasu don shi ma akwai dan uwansa soja a kudu, yana tsoron a tura shi yaki. Malamijo bai tashi bada amsa ba sai da yaga Rayyanu ya tashi zai zaga ya soma jawabi. "Hmm ai ba'a cewa komai Haladu. Yaron nan harbi, harbi dai da kake ji da gani a finafinan su Amita Bachan sai da aka sakar masa harsashi kusan goma amma a haka ya rinka kutsa kai cikin abokan gaba yana gamawa dasu. Bawan Allah ya tafi ya barwa Mairama da yaranta komai nasa. Ko sati batayi da haihuwa ba. Shine ma zanje domin na tattaro dukiyar na kawo nan sai na juya mata da kaina saboda duk yadda ka kai da yarda da wani ba kamar naka ba. Nakan ma mahaifi" [02/11 7:29 AM] My 2nd Mtn: 14. Dattijuwa ce goye da yaro tana gurfane a gaban gadon Salame wadda take hakimce tana bata umarnin ayyukan da zata yi a cikin gidan. Banda kudi sune masu gida rana yaushe wannan mata da a shekaru zata girmi Ta Madina ace ita ce Salame 'yar cikin cikinta take yiwa rashin kunya son rai tana kada kafafu tayi daurin Mayam Babangida. "Kada ki sake na fito baki gama aikin nan ba Kande" ta kare cikin fada. "Sha Allahu ma zan gama da wuri." Sai ta dan kwantar da kai "nace ko na kwantar miki da Halifa tunda ya riga yayi bacci? Aikin nawa zai fi sauri" Wata uwar harara da Salame ta galla mata ya sanya ta tashi da sauri ta fita daga dakin. Tana fitowa ta sami wani matashi yana sallama. Kallo daya tayi masa ta gane ya hada jini da matar gidan shiyasa tace ya zauna. Ruwa ta kawo masa sannan ta sanar da Salame tayi bako. Sai da ta gama bata lokaci sannan ta fito tana takaicin hanata hutu da akayi. Tun aurenta da Salisu bazata ce ga wata rana da take cikin farinciki sosai ba. Haka dai take rayuwa daga fada sai masifa sai kuma muguwar hassadar Mairama da tayi sake ta kama zuciyarta sosai. Dago labulen dakinta tayi ta fito. A wulakance take kallon kanin nata "ah'a Bature kai ne dama" Zamowa yayi daga kan kujerar ya gaisheta. Bai manta zuwansu da sallah ba inda ta karesu musu tas wai sun haye kujeru abinda ba'a saba ba. Da suka koma gida kowa yana korafi suna cewa da Adda Mairama ce bazata musu haka ba banda shi don ransa ya baci. Ya dai ci alwashin idan ba aike ba babu abinda zai sake kaishi gidanta. Gaisuwar kuwa albarkacin mai aikinta da ya gani ne kada ace basu da hadin kai. Kusan halinsu daya da Mairama shiyasa Malamijo ya aiko shi don sauran babu mai yarda yazo. "Wani abin ne ya faru kazo ko kuwa?" Shigowar Salisu kenan yaji yadda take yiwa kaninta magana. Shi ya rasa dalilinta na kin 'yan uwanta yanzu kaf bata son mu'amala ta hadasu. Nashi dangin ma bata raga musu amma yana daf da magance matsalar nan. Bature ya gaishe shi ya amsa a mutumce sannan yace ta biyo shi daki. Bakin nan a gaba ta bi bayansa. "Me yake damunki ne? Yaro ya taho tun daga Sumaila babu wata tarba me kyau sai me ya faru? Yanzu ke da 'yan uwanki babu wanda zai zo don sada zumunci wurinki sai da wani dalili?" Ya jero mata tambayoyin cikin bacin rai. Juya idanu tayi "ai dai 'yan uwana ne ba na mutum ba" "Ni kike yiwa magana haka ko Salame?" Bata saurare shi ba ta fice don sallamar Bature ya koma inda ya fito. Salisu ashe yana bayanta sai ganinsa tayi ya zauna yana tambayarsa mutanen gida. "Kawo masa abinci mana Salame" ya umarceta. Cire baki tayi ta kwalawa Kande kira. "Ki kyale Kande aiki na ga tana yi. Kuma shi Halifa ba'a kwantar dashi ne? Kusan a bayan matar nan yake wuni ita bata huta ba shi ba'a barshi ya sake yayi wasa ba" "Idan ta sauke shi damuna zaiyi. Kuma dai tunda biyanta akeyi meye a ciki?" "Babu komai kuwa tunda kudinki ne Hajiya" Magana suke yiwa juna a hasale kowa rai a bace. Bature da bashi da sha'awar kwanar musu a gida ya katse rigimar ta hanyar fada musu abinda aka turo shi ya fada. A tare suka juyo kansa. Salisu hankali a tashe Salame kuwa numfashinta taji ya tsaya na wucin gadi. "Wane Zayyan din?" Salisu ya tattaro karfin halin tambaya. "Mijin Adda Mairama." "Salame kin..." kasa karasa magana yayi ganin ta tafi luuu kamar zata fadi ta saki kara iya karfinta. Maimakon Salisu ya tarota sai mamaki ya kama shi har ya kasa motsi. Salame ce fa da yasan bata kaunar kanwarta. Me zai sa ta shiga wannan yanayi kamar ance mata shi da kansa ne ya mutu ko mahaifinta. Bature ma abin ya daure masa kai "Adda cewa nayi mijin Adda Mairama fa ba Malamijo ba" Zama kawai tayi dabas akan kujera tana kuka sosai. Shikenan Zayyan ashe bata da rabon zama dashi. Salisu ya kawar da kai daga gareta. "Bature yau zaka koma ne?" "Yanzu ma kuwa in sha Allahu. Gobe za'a tafi gaisuwa" Zumbur ta mike "ku biyo min, ko kuma dai ka jirani na shirya" Tsawa Salisu ya daka mata "koma ki zauna. Bature muje" Bakin gate ya raka Bature ta bashi kudin mota sannan ya koma ciki. Tana nan tana rusa kuka Kande na bata hakuri. Yana zuwa ya finciko hannunta sai da Kande ta tsorata. Dakinsa ya kaita ya jefata kan gado iya karfinsa. Fuskarsa a daure babu wasa ko kadan ya jefa mata tambayar da ta kada mata hanji. "Tun farkon haduwarmu dama Zayyan kike so?" Shiru tayi sai faduwar gabanta da ta tsananta. "Ki bani amsa mana!" Ya sake yi mata tsawa sai da ta firgice. Wasu sababbin hawayen ta soma yi yaji kamar ya rufeta da duka. "Kin cuceni, ban dade da aurenki ba zuciyata ta bani cewa ban yiwa kaina adalci wurin zabar matar aure ba. A tunanina na auro mace mara son zumunci ne kawai da raina na kasa da ita. Ashe kin wuce haka. Salame mijin kanwarki kike so kuma har kike kishi da ita alhalin kina gidan naki mijin" Har yanzu ta kasa magana sai kuka. Shi din ma nasa idon da hawaye saboda bai taba kawo hakan a matsayin dalilin da yasa take yiwa Mairama haka ba. "Bazaki je Sakkwato gaisuwa ba" kallonsa tayi da sauri ya sake hade rai "ke daga yau sai abu yayi tsanani sosai zanyi miki izinin fita kina ji na. Idan kika karya min doka wallahi, wallahi sai na shayar dake mamaki" ********** Ranar da aka sallami Mairama a ranar Mal Aminu da Jume su ka amince da a kwashe kayanta ta koma gidansu Zayyan. Idan iyayenta sun zo sai su tafi da ita gida. "Ku wuce da ita su Mubaraka sai su zo a kwashe kayan gobe tunda zaman barikin babu amfani" Mairama tana jin haka ta ajiye kunyarta a gefe "Kawu ina son zuwa don akwai abubuwan da nake son hadawa da kaina" Caraf a kunnen Maikudi "ko ma meye muma din jinin Zayyanu ne. Kije ki huta ni da kaina zan jagoranci zuwa a debo kayan saboda kada wani abu ya salwanta" Soye idanu tayi don bazata yarda a hanata zuwa ba. Ta nuna musu akwai makota da take son yiwa sallama irinsu Christie wadda bata kara gani ba tun lokacin da tace zata je yi mata girki. Mal Aminu yace "Ka barta taje Maikudi. Daga nan ma sai mu bincika muji ko akwai wani abu da zasu bawa iyalin mamatan. Mu bari jikinta ya kara kwari ko nan da kwana biyu ne" Ransa baya so saboda ya kula tunda ta dage sai taje akwai dukiya dankare a gidan da bai taba zuwa ko kofarsa ba. "Ina mukullin a bani na rike saboda 'yan barka da gaisuwa kada wata ta dafe" "Maikudi kenan, ko ma wacece ba sai dai muce Allah Ya bada sa'a ba. Sata a gidan soja, gidan sojan ma a cikin bariki kamar mutum ya tashi da burin karar kwana" Gwaggo Ladi ta gwaba masa magana. Bai sake magana ba su ka tafi gida. Jume tasa matan su Badaru gyarawa Mairama dakin Innar Zayyan. Tana shiga ta tuna ranar sunan Radhiya da hotunan da suka yi da Zayyan da Awwab a ciki. Idanunta da basa rabo da hawaye suka fara abinda ya zame musu jiki yanzu. Jume da kanta tazo tace mata ta shirya ta fito zata yi mata wankan jego. Jariri kuma Gwaggo Ladi ta dauka tayi masa wanka irin wanda bai samu ba tun ranar haihuwarsa saboda kasancewarsu a asibiti. ********** "Ya muke ta bin lungu ne yaro? Nayi zaton a irin unguwannin nan da suke malale da titi gidan yake" Rayyanu ya kalli Malamijo ya sake daure zuciyarsa a karo na barkatai ya bashi amsa akan irin wadannan tambayoyin da yake ta yi masa. "Gidan iyayenmu ne a nan unguwar. Zayyanu a cikin bariki ya zauna da iyalinsa" Malamijo sai murmushi "Auhooo ko da naji. Ca nake a nan Mairaman tawa ta zauna ne" Su hudu ne a ayarin tafiyar banda Rayyanu suka biyo motar haya. Nene Marka, Malamijo, Hajjo da kuma Salisu. Gidan yanzu Yadikko da Hajjo ne kawai a gidan, ya saki Dije da Inno yana shirin karo wata. Tun a tashar Kano ana cewa a kawo kudin mota Malamijo ya shiga tarin karya, daga baya ma sai yayi gaba yana dukan kirji sai da ya hango Salisu ya biya musu kudin motar su duka sannan ya dawo yana cewa kwarewa yayi. "Sai ji nayi wani abu siririt ya wuce min ta makoshi. Kwarewa babu dadi, ammm nawa ne kudin motar ne?" Nene tasan dalilin tafiyar tasa sai kawai ta dauke kai. Hajjo ce ta fada an biya yayi wata barazanar zura hannu a aljihu zai dauko kudin ya bawa shi. Sal da Salisu yace ya bari duk daga ne. Iyaye da dangi duk lalacewarsu sunfi ace baka da kowa. Sallamar Malamijo kawai Mairama taji ta sa kuka sosai. Kuka ne na ganin babban gatan da ya rage mata duk fadin duniyar nan. Shine bango abin jingina a gareta wanda take sa ran idan tayi kukan rashin miji zai rarrasheta yace ta barwa Allah komai. Idan tayi kukan rayuwar marayunta zai yi mata alkawarin matsawar yana numfashi 'ya'yanta bazasu tagayyara ba. Jikin Nene Marka ta zube suna kuka tare. Malamijo ya tausayawa Mairama sosai ya mika hannu ya dauki Radhiya. Zayyan wanda duka gidan an rasa mai kiran sunansa har Maikudi kuwa saboda tuna musu da marigayi da yake yi matar Badaru ta kwanto daga bayanta ta mikawa Hajjo. "Iko sai mai shi, Malamijo dubi yaron nan don Ma'aiki." Radhiya tana gefensa ya karbi jaririn yana kare masa kallo. Salisu yazo ya karbe shi shima ya ga kama sosai da mahaifinsa. "Allah Ya raya mana kai karamin soja " Mazan sun koma waje inda ake zuwa yi musu ta'aziyya matan kuma suna daga ciki. Sai dare ne Mal Aminu ya sanar da Malamijo za'a kwaso kayan Mairama sai su tafi da ita. "A'a a bar yarinya a gidan mijinta. Idan akwai wata dukiya da bazata iya juyawa ba ni sai na tafi da ita ba wani abu." Maikudi yayi saurin cewa "dukiyar marayu zata fi dadi a hannun dangin uba. Saboda haka gobe zamuje ayi duk yadda za'ayi ne. Gida kuma ba nasu bane na bariki ne. Tunda ya rasu dole ne su tashi komai dadewa" A hankali zantukan nasu suka fara neman komawa rigima. Maikudi da Malamijo kowa ya nuna zalamarsa a fili. Shiyasa kowa cikinsu yake ganin dole ya tsaya akan dukiyar da basu da tabbacin akwaita. Shabiyun rana kuwa washegari suka isa kofar gidan da ya kasance na Mairama da Zayyan kwanaki kadan da suka wuce. Ta kalli gidan Zainab a rufe har yanzu. Tana son sanin halin da suke ciki da mazansu amma yanzu babu hali sai komai ya daidaita a nata bangaren. Gidan Christie ma a rufe yake. Bayan ta bude nata gidan sun shiga da yayyen Zayyan mata da kuma Hajjo sai ga wasu cikin abokan zamansu na kusa. Gaisuwar mijinta suka yi mata da barkar Zayyan karami. Ta tambayi ina Christie wata ta bata amsa da cewa ranar da ta haihu Christie tazo tayi mata girki kuma ta farfadawa makota haihuwar. Ta koma daidai lokacin da Mairama ta suma. A nan take jin duka sojojin sun rasu ciki kuwa harda mijinta. Bata iya shiga ba ta koma gida bayan ta sauke musu Radhiya. Shine aka sami wani da ya san gidansu Zayyan aka fada musu. Ita kuma Christie ta tafi garinsu ta fadi mutuwar har yanzu bata dawo ba. Duka matan abin tausayi musamman wadanda mazansu suka tafi a bayan su Zayyan. Suna cike da tsoro da fargabar me zai je ya dawo. Wasunsu sun saka hannu wurin tattare kayan kitchen da na falon Mairama ana hade komai wuri guda ana fitarwa. Cikin dakin ta shiga zuciyarta tayi matukar rauni. Shikenan daga yau duk wasu memories da suka gina da Zayyan a gidan nan cikin wannan dakin sai dai zu dawo mata a tunani. Kukanta Hajjo ta jiyo ta shiga dakin da sauri. "Haba Mairama ashe bazaki sakawa zuciyarki salama ba? Ni ko kadan ban so aka ce wai azo kwasar kaya da wuri kamar ana korarki ba. Su dakata ki sami nutsuwar zuciya sun ki" Mairama ta bude wani akwai ta dauko envelop din da Zayyan ya bata hannu na rawa ta saka a jakar hannunta sannan aka fara hada kayan gidan. Malamijo yana waje yaki shiga ba don kunya ba sai don bakinciki. Shi kadai a ransa yake nanata an yaudareshi aka ce masa Zayyan soja ne. To yaji sojan ne amma ba wani mai mukami bane ashe. Ji dai wannan akurki da ya ajiye masa 'yarsa ya raya a zuciyarsa. Kuma ashe ma ba nasa bane. To duka kudaden da yake masa alheri dasu a ina yake samowa? Faduwar gaba yaji da ya tuna indai fa babu wani abin kirki da ya bari komai na Mairama da 'ya'yan wuyansa zai dawo. Hodijan inji mutanensa, aradun Allah bazai iya karawa kansa nauyi ba. Yanzu fa yara goma sha bakwai gareshi. Salame ce kadai a gidan miji tunda dai Zayyan ya rasu. Gata ta tunda tayi aure ta ari rigar rashin mutumci ta saka.Tsaki yaja sai hankalinsa ya koma ciki inda yake jiyo muryar Maikudi. "Kai wannan takadirin yaro da gani zaiyi mugunta. Me kuma yake nema a cikin mata?" Shiga yayi da Salisu ya sami Maikudi yana fada "ki fito min da duk wani kudi ko takardun abubuwa masu mahimmanci na Zayyan. Dukiyar magada sai da saka ido. Ba wai da ka zaki dauke komai ki rike ba" Salisu ya riko hannunsa "kaga Mal Maikudi duk abin nan ba na rigima bane. Mairama ba jahila bace da zata ci dukiyar mamaci. Sai dai fa ina so ka sani duk danginku babu mai gadon Zayyan sai Mairama da 'ya'yanta" Kamar zai kaiwa Salisu duka ya soma fada "ni nasan ba banza ba kuka taho kwanku da kwarkwata. Ashe da manufarku. To babu wanda ya isa yayi sama da fadi da dukiyar magada muddin ina raye" Mairama dai sai kuka. Malamijo ya zakalkale yana ta zubar musu da daraja a gaban 'yan uwan Zayyan. Idan Maikudi yayi shi za'a ce da sauran kuruciya. Shi kuwa yana mahaifinta ga jikoki har uku amma har yau bai fasa halinsa ba. Mal Aminu da kawunsu Zayyan sun shigo sun same su ana ta mayar da magana. Sam Mal Aminu baiji dadi ba. Ga Mairama sai ajiyar zuciya kawai take yi. "Daga can ofishin nasu nake an kaini har wurin wani babba cikinsu a nan munyi magana. A takaice dai muna da yawa da muka rasa 'yan uwa a wurin nan. Amma yace muyi hakuri ba'a turo komai daga gwamnatin tarayya ba da zasu sallami iyalan sojojin ko kuma masu rauni" "Ikon Allah, yanzu ace mutum ya rasa rayuwarsa a bakin aikinku amma babu sallama ga iyalansa da maraici ya kama su?" Cewar Salisu "Don ma baka je wurin bane. Mutanen da yawa wallahi. Sun ce kuma sojojin da aka rasa suna da yawa ba wai na nan bane kadai. Kuma wai gwamnati bata da kudi amma zasu neme mu idan an sami wani abin" "Wannan ai zancen banza ne, bata da kudin take kashe mana 'yan uwa? Ni bazan hakura ba. Wannan magana kuma bazan bari ta mutu a nan ba." Maikudi yace yana tashi tsaye "idan ma an fada ne don a sa jikina yayi sanyi kada na tsayawa marayun nan wallahi sai naje" ya zubawa Mal Aminu idanu. Murmushi yayi kawai yace motar daukan kayan tazo. Kawunsu ne ma ya rinka yi masa fadan baya son rashin kunya. To amma da yake duka talakawa ne maganarsu bata wani tasiri a wurinsa. Abu kamar wasa Mairama da tazo barikin nan a matsayin amarya kasa da shekara biyu wai har anyi zaman an gama. Mijinta abin kaunarta ya tafi ya barta a hannun wadanda basu damu da halin da take ciki ba, kawunansu kawai suka sani. A daren Malamijo yace su shirya da wuri zasu wuce gobe. Mairama ta roke shi alfarmar zata je gidansu Zainab kafin su tafi. Jume tana zaune tare da Mairama bayan ta yiwa Zayyan karami wankan yamma tace mata "yanzu Mairama daga yau shikenan ko? Nasan da wuya ku rinka zuwa tunda kin san ba ni bace na haifi Zayyanu. Ga bakin kishi yasa ni ban san ta yadda za'ayi na sami dangin mahaifiyarsa ba balle su san halin da ake ciki ma " "In sha Allahu zan rinka zuwa Jume. Idan basu zo ba wa zasu nuna a matsayin dangin uba?" "To nagode Mairama. Sai kin daura dammarar hakuri da juriya. Yanzu sabuwar rayuwa ce zata bijiro miki da baki taba zato da tsammani ba." Hawaye ya zubo mata da ta tuna rasuwar Mal Muhammadu. Washegari da wuri Mairama ta tafi gidansu Zainab. Allah Ya taimaketa bata mance hanyar ba. Mahaifiyar Zainab din ta samu wadda ta fada mata kwana hudu da suka wuce babanta ya kaita Kano gidansu Hadir. Duk da bata san kan garin Kanon sosai ta nemi tayi mata kwatance amma anyi rashin sa'a ko sunan unguwar bazata iya tunawa ba don wahala yake mata. Mairama tana kuka tace ta fada mata tazo itama zata koma garinsu. "Kema mijin naki yaji rauni ne?" "Rasuwa yayi." Idanu ta zaro "idan Hadir yaji ban yaya zai ji ba. Allah Ya zama gatanku Mairama" Sallama tayi mata ta koma gidan domin su karasa shirin tafiya. A daren jiya ta bude envelop din da Zayyan ya bar mata. Ashe gabadaya sauran kudin gadonsa ne ya bar mata da takardun gidansa na Kano. Dasu ta fita a jakarta idan ta koma zata fito dasu ta nunawa iyayen. Dama suna rayuwa ne bayan tafiyar mazan akan albashinsu da ake bawa matan. Kudi ne da bai wani taka kara ya karya ba. Wasikarta kuwa zuciyarta ta kasa bata kwarin gwiwar karantawa har lokacin. **********Dattijuwa ce goye da yaro tana gurfane a gaban gadon Salame wadda take hakimce tana bata umarnin ayyukan da zata yi a cikin gidan. Banda kudi sune masu gida rana yaushe wannan mata da a shekaru zata girmi Ta Madina ace ita ce Salame 'yar cikin cikinta take yiwa rashin kunya son rai tana kada kafafu tayi daurin Mayam Babangida. "Kada ki sake na fito baki gama aikin nan ba Kande" ta kare cikin fada. "Sha Allahu ma zan gama da wuri." Sai ta dan kwantar da kai "nace ko na kwantar miki da Halifa tunda ya riga yayi bacci? Aikin nawa zai fi sauri" Wata uwar harara da Salame ta galla mata ya sanya ta tashi da sauri ta fita daga dakin. Tana fitowa ta sami wani matashi yana sallama. Kallo daya tayi masa ta gane ya hada jini da matar gidan shiyasa tace ya zauna. Ruwa ta kawo masa sannan ta sanar da Salame tayi bako. Sai da ta gama bata lokaci sannan ta fito tana takaicin hanata hutu da akayi. Tun aurenta da Salisu bazata ce ga wata rana da take cikin farinciki sosai ba. Haka dai take rayuwa daga fada sai masifa sai kuma muguwar hassadar Mairama da tayi sake ta kama zuciyarta sosai. Dago labulen dakinta tayi ta fito. A wulakance take kallon kanin nata "ah'a Bature kai ne dama" Zamowa yayi daga kan kujerar ya gaisheta. Bai manta zuwansu da sallah ba inda ta karesu musu tas wai sun haye kujeru abinda ba'a saba ba. Da suka koma gida kowa yana korafi suna cewa da Adda Mairama ce bazata musu haka ba banda shi don ransa ya baci. Ya dai ci alwashin idan ba aike ba babu abinda zai sake kaishi gidanta. Gaisuwar kuwa albarkacin mai aikinta da ya gani ne kada ace basu da hadin kai. Kusan halinsu daya da Mairama shiyasa Malamijo ya aiko shi don sauran babu mai yarda yazo. "Wani abin ne ya faru kazo ko kuwa?" Shigowar Salisu kenan yaji yadda take yiwa kaninta magana. Shi ya rasa dalilinta na kin 'yan uwanta yanzu kaf bata son mu'amala ta hadasu. Nashi dangin ma bata raga musu amma yana daf da magance matsalar nan. Bature ya gaishe shi ya amsa a mutumce sannan yace ta biyo shi daki. Bakin nan a gaba ta bi bayansa. "Me yake damunki ne? Yaro ya taho tun daga Sumaila babu wata tarba me kyau sai me ya faru? Yanzu ke da 'yan uwanki babu wanda zai zo don sada zumunci wurinki sai da wani dalili?" Ya jero mata tambayoyin cikin bacin rai. Juya idanu tayi "ai dai 'yan uwana ne ba na mutum ba" "Ni kike yiwa magana haka ko Salame?" Bata saurare shi ba ta fice don sallamar Bature ya koma inda ya fito. Salisu ashe yana bayanta sai ganinsa tayi ya zauna yana tambayarsa mutanen gida. "Kawo masa abinci mana Salame" ya umarceta. Cire baki tayi ta kwalawa Kande kira. "Ki kyale Kande aiki na ga tana yi. Kuma shi Halifa ba'a kwantar dashi ne? Kusan a bayan matar nan yake wuni ita bata huta ba shi ba'a barshi ya sake yayi wasa ba" "Idan ta sauke shi damuna zaiyi. Kuma dai tunda biyanta akeyi meye a ciki?" "Babu komai kuwa tunda kudinki ne Hajiya" Magana suke yiwa juna a hasale kowa rai a bace. Bature da bashi da sha'awar kwanar musu a gida ya katse rigimar ta hanyar fada musu abinda aka turo shi ya fada. A tare suka juyo kansa. Salisu hankali a tashe Salame kuwa numfashinta taji ya tsaya na wucin gadi. "Wane Zayyan din?" Salisu ya tattaro karfin halin tambaya. "Mijin Adda Mairama." "Salame kin..." kasa karasa magana yayi ganin ta tafi luuu kamar zata fadi ta saki kara iya karfinta. Maimakon Salisu ya tarota sai mamaki ya kama shi har ya kasa motsi. Salame ce fa da yasan bata kaunar kanwarta. Me zai sa ta shiga wannan yanayi kamar ance mata shi da kansa ne ya mutu ko mahaifinta. Bature ma abin ya daure masa kai "Adda cewa nayi mijin Adda Mairama fa ba Malamijo ba" Zama kawai tayi dabas akan kujera tana kuka sosai. Shikenan Zayyan ashe bata da rabon zama dashi. Salisu ya kawar da kai daga gareta. "Bature yau zaka koma ne?" "Yanzu ma kuwa in sha Allahu. Gobe za'a tafi gaisuwa" Zumbur ta mike "ku biyo min, ko kuma dai ka jirani na shirya" Tsawa Salisu ya daka mata "koma ki zauna. Bature muje" Bakin gate ya raka Bature ta bashi kudin mota sannan ya koma ciki. Tana nan tana rusa kuka Kande na bata hakuri. Yana zuwa ya finciko hannunta sai da Kande ta tsorata. Dakinsa ya kaita ya jefata kan gado iya karfinsa. Fuskarsa a daure babu wasa ko kadan ya jefa mata tambayar da ta kada mata hanji. "Tun farkon haduwarmu dama Zayyan kike so?" Shiru tayi sai faduwar gabanta da ta tsananta. "Ki bani amsa mana!" Ya sake yi mata tsawa sai da ta firgice. Wasu sababbin hawayen ta soma yi yaji kamar ya rufeta da duka. "Kin cuceni, ban dade da aurenki ba zuciyata ta bani cewa ban yiwa kaina adalci wurin zabar matar aure ba. A tunanina na auro mace mara son zumunci ne kawai da raina na kasa da ita. Ashe kin wuce haka. Salame mijin kanwarki kike so kuma har kike kishi da ita alhalin kina gidan naki mijin" Har yanzu ta kasa magana sai kuka. Shi din ma nasa idon da hawaye saboda bai taba kawo hakan a matsayin dalilin da yasa take yiwa Mairama haka ba. "Bazaki je Sakkwato gaisuwa ba" kallonsa tayi da sauri ya sake hade rai "ke daga yau sai abu yayi tsanani sosai zanyi miki izinin fita kina ji na. Idan kika karya min doka wallahi, wallahi sai na shayar dake mamaki" ********** Ranar da aka sallami Mairama a ranar Mal Aminu da Jume su ka amince da a kwashe kayanta ta koma gidansu Zayyan. Idan iyayenta sun zo sai su tafi da ita gida. "Ku wuce da ita su Mubaraka sai su zo a kwashe kayan gobe tunda zaman barikin babu amfani" Mairama tana jin haka ta ajiye kunyarta a gefe "Kawu ina son zuwa don akwai abubuwan da nake son hadawa da kaina" Caraf a kunnen Maikudi "ko ma meye muma din jinin Zayyanu ne. Kije ki huta ni da kaina zan jagoranci zuwa a debo kayan saboda kada wani abu ya salwanta" Soye idanu tayi don bazata yarda a hanata zuwa ba. Ta nuna musu akwai makota da take son yiwa sallama irinsu Christie wadda bata kara gani ba tun lokacin da tace zata je yi mata girki. Mal Aminu yace "Ka barta taje Maikudi. Daga nan ma sai mu bincika muji ko akwai wani abu da zasu bawa iyalin mamatan. Mu bari jikinta ya kara kwari ko nan da kwana biyu ne" Ransa baya so saboda ya kula tunda ta dage sai taje akwai dukiya dankare a gidan da bai taba zuwa ko kofarsa ba. "Ina mukullin a bani na rike saboda 'yan barka da gaisuwa kada wata ta dafe" "Maikudi kenan, ko ma wacece ba sai dai muce Allah Ya bada sa'a ba. Sata a gidan soja, gidan sojan ma a cikin bariki kamar mutum ya tashi da burin karar kwana" Gwaggo Ladi ta gwaba masa magana. Bai sake magana ba su ka tafi gida. Jume tasa matan su Badaru gyarawa Mairama dakin Innar Zayyan. Tana shiga ta tuna ranar sunan Radhiya da hotunan da suka yi da Zayyan da Awwab a ciki. Idanunta da basa rabo da hawaye suka fara abinda ya zame musu jiki yanzu. Jume da kanta tazo tace mata ta shirya ta fito zata yi mata wankan jego. Jariri kuma Gwaggo Ladi ta dauka tayi masa wanka irin wanda bai samu ba tun ranar haihuwarsa saboda kasancewarsu a asibiti. ********** "Ya muke ta bin lungu ne yaro? Nayi zaton a irin unguwannin nan da suke malale da titi gidan yake" Rayyanu ya kalli Malamijo ya sake daure zuciyarsa a karo na barkatai ya bashi amsa akan irin wadannan tambayoyin da yake ta yi masa. "Gidan iyayenmu ne a nan unguwar. Zayyanu a cikin bariki ya zauna da iyalinsa" Malamijo sai murmushi "Auhooo ko da naji. Ca nake a nan Mairaman tawa ta zauna ne" Su hudu ne a ayarin tafiyar banda Rayyanu suka biyo motar haya. Nene Marka, Malamijo, Hajjo da kuma Salisu. Gidan yanzu Yadikko da Hajjo ne kawai a gidan, ya saki Dije da Inno yana shirin karo wata. Tun a tashar Kano ana cewa a kawo kudin mota Malamijo ya shiga tarin karya, daga baya ma sai yayi gaba yana dukan kirji sai da ya hango Salisu ya biya musu kudin motar su duka sannan ya dawo yana cewa kwarewa yayi. "Sai ji nayi wani abu siririt ya wuce min ta makoshi. Kwarewa babu dadi, ammm nawa ne kudin motar ne?" Nene tasan dalilin tafiyar tasa sai kawai ta dauke kai. Hajjo ce ta fada an biya yayi wata barazanar zura hannu a aljihu zai dauko kudin ya bawa shi. Sal da Salisu yace ya bari duk daga ne. Iyaye da dangi duk lalacewarsu sunfi ace baka da kowa. Sallamar Malamijo kawai Mairama taji ta sa kuka sosai. Kuka ne na ganin babban gatan da ya rage mata duk fadin duniyar nan. Shine bango abin jingina a gareta wanda take sa ran idan tayi kukan rashin miji zai rarrasheta yace ta barwa Allah komai. Idan tayi kukan rayuwar marayunta zai yi mata alkawarin matsawar yana numfashi 'ya'yanta bazasu tagayyara ba. Jikin Nene Marka ta zube suna kuka tare. Malamijo ya tausayawa Mairama sosai ya mika hannu ya dauki Radhiya. Zayyan wanda duka gidan an rasa mai kiran sunansa har Maikudi kuwa saboda tuna musu da marigayi da yake yi matar Badaru ta kwanto daga bayanta ta mikawa Hajjo. "Iko sai mai shi, Malamijo dubi yaron nan don Ma'aiki." Radhiya tana gefensa ya karbi jaririn yana kare masa kallo. Salisu yazo ya karbe shi shima ya ga kama sosai da mahaifinsa. "Allah Ya raya mana kai karamin soja " Mazan sun koma waje inda ake zuwa yi musu ta'aziyya matan kuma suna daga ciki. Sai dare ne Mal Aminu ya sanar da Malamijo za'a kwaso kayan Mairama sai su tafi da ita. "A'a a bar yarinya a gidan mijinta. Idan akwai wata dukiya da bazata iya juyawa ba ni sai na tafi da ita ba wani abu." Maikudi yayi saurin cewa "dukiyar marayu zata fi dadi a hannun dangin uba. Saboda haka gobe zamuje ayi duk yadda za'ayi ne. Gida kuma ba nasu bane na bariki ne. Tunda ya rasu dole ne su tashi komai dadewa" A hankali zantukan nasu suka fara neman komawa rigima. Maikudi da Malamijo kowa ya nuna zalamarsa a fili. Shiyasa kowa cikinsu yake ganin dole ya tsaya akan dukiyar da basu da tabbacin akwaita. Shabiyun rana kuwa washegari suka isa kofar gidan da ya kasance na Mairama da Zayyan kwanaki kadan da suka wuce. Ta kalli gidan Zainab a rufe har yanzu. Tana son sanin halin da suke ciki da mazansu amma yanzu babu hali sai komai ya daidaita a nata bangaren. Gidan Christie ma a rufe yake. Bayan ta bude nata gidan sun shiga da yayyen Zayyan mata da kuma Hajjo sai ga wasu cikin abokan zamansu na kusa. Gaisuwar mijinta suka yi mata da barkar Zayyan karami. Ta tambayi ina Christie wata ta bata amsa da cewa ranar da ta haihu Christie tazo tayi mata girki kuma ta farfadawa makota haihuwar. Ta koma daidai lokacin da Mairama ta suma. A nan take jin duka sojojin sun rasu ciki kuwa harda mijinta. Bata iya shiga ba ta koma gida bayan ta sauke musu Radhiya. Shine aka sami wani da ya san gidansu Zayyan aka fada musu. Ita kuma Christie ta tafi garinsu ta fadi mutuwar har yanzu bata dawo ba. Duka matan abin tausayi musamman wadanda mazansu suka tafi a bayan su Zayyan. Suna cike da tsoro da fargabar me zai je ya dawo. Wasunsu sun saka hannu wurin tattare kayan kitchen da na falon Mairama ana hade komai wuri guda ana fitarwa. Cikin dakin ta shiga zuciyarta tayi matukar rauni. Shikenan daga yau duk wasu memories da suka gina da Zayyan a gidan nan cikin wannan dakin sai dai zu dawo mata a tunani. Kukanta Hajjo ta jiyo ta shiga dakin da sauri. "Haba Mairama ashe bazaki sakawa zuciyarki salama ba? Ni ko kadan ban so aka ce wai azo kwasar kaya da wuri kamar ana korarki ba. Su dakata ki sami nutsuwar zuciya sun ki" Mairama ta bude wani akwai ta dauko envelop din da Zayyan ya bata hannu na rawa ta saka a jakar hannunta sannan aka fara hada kayan gidan. Malamijo yana waje yaki shiga ba don kunya ba sai don bakinciki. Shi kadai a ransa yake nanata an yaudareshi aka ce masa Zayyan soja ne. To yaji sojan ne amma ba wani mai mukami bane ashe. Ji dai wannan akurki da ya ajiye masa 'yarsa ya raya a zuciyarsa. Kuma ashe ma ba nasa bane. To duka kudaden da yake masa alheri dasu a ina yake samowa? Faduwar gaba yaji da ya tuna indai fa babu wani abin kirki da ya bari komai na Mairama da 'ya'yan wuyansa zai dawo. Hodijan inji mutanensa, aradun Allah bazai iya karawa kansa nauyi ba. Yanzu fa yara goma sha bakwai gareshi. Salame ce kadai a gidan miji tunda dai Zayyan ya rasu. Gata ta tunda tayi aure ta ari rigar rashin mutumci ta saka.Tsaki yaja sai hankalinsa ya koma ciki inda yake jiyo muryar Maikudi. "Kai wannan takadirin yaro da gani zaiyi mugunta. Me kuma yake nema a cikin mata?" Shiga yayi da Salisu ya sami Maikudi yana fada "ki fito min da duk wani kudi ko takardun abubuwa masu mahimmanci na Zayyan. Dukiyar magada sai da saka ido. Ba wai da ka zaki dauke komai ki rike ba" Salisu ya riko hannunsa "kaga Mal Maikudi duk abin nan ba na rigima bane. Mairama ba jahila bace da zata ci dukiyar mamaci. Sai dai fa ina so ka sani duk danginku babu mai gadon Zayyan sai Mairama da 'ya'yanta" Kamar zai kaiwa Salisu duka ya soma fada "ni nasan ba banza ba kuka taho kwanku da kwarkwata. Ashe da manufarku. To babu wanda ya isa yayi sama da fadi da dukiyar magada muddin ina raye" Mairama dai sai kuka. Malamijo ya zakalkale yana ta zubar musu da daraja a gaban 'yan uwan Zayyan. Idan Maikudi yayi shi za'a ce da sauran kuruciya. Shi kuwa yana mahaifinta ga jikoki har uku amma har yau bai fasa halinsa ba. Mal Aminu da kawunsu Zayyan sun shigo sun same su ana ta mayar da magana. Sam Mal Aminu baiji dadi ba. Ga Mairama sai ajiyar zuciya kawai take yi. "Daga can ofishin nasu nake an kaini har wurin wani babba cikinsu a nan munyi magana. A takaice dai muna da yawa da muka rasa 'yan uwa a wurin nan. Amma yace muyi hakuri ba'a turo komai daga gwamnatin tarayya ba da zasu sallami iyalan sojojin ko kuma masu rauni" "Ikon Allah, yanzu ace mutum ya rasa rayuwarsa a bakin aikinku amma babu sallama ga iyalansa da maraici ya kama su?" Cewar Salisu "Don ma baka je wurin bane. Mutanen da yawa wallahi. Sun ce kuma sojojin da aka rasa suna da yawa ba wai na nan bane kadai. Kuma wai gwamnati bata da kudi amma zasu neme mu idan an sami wani abin" "Wannan ai zancen banza ne, bata da kudin take kashe mana 'yan uwa? Ni bazan hakura ba. Wannan magana kuma bazan bari ta mutu a nan ba." Maikudi yace yana tashi tsaye "idan ma an fada ne don a sa jikina yayi sanyi kada na tsayawa marayun nan wallahi sai naje" ya zubawa Mal Aminu idanu. Murmushi yayi kawai yace motar daukan kayan tazo. Kawunsu ne ma ya rinka yi masa fadan baya son rashin kunya. To amma da yake duka talakawa ne maganarsu bata wani tasiri a wurinsa. Abu kamar wasa Mairama da tazo barikin nan a matsayin amarya kasa da shekara biyu wai har anyi zaman an gama. Mijinta abin kaunarta ya tafi ya barta a hannun wadanda basu damu da halin da take ciki ba, kawunansu kawai suka sani. A daren Malamijo yace su shirya da wuri zasu wuce gobe. Mairama ta roke shi alfarmar zata je gidansu Zainab kafin su tafi. Jume tana zaune tare da Mairama bayan ta yiwa Zayyan karami wankan yamma tace mata "yanzu Mairama daga yau shikenan ko? Nasan da wuya ku rinka zuwa tunda kin san ba ni bace na haifi Zayyanu. Ga bakin kishi yasa ni ban san ta yadda za'ayi na sami dangin mahaifiyarsa ba balle su san halin da ake ciki ma " "In sha Allahu zan rinka zuwa Jume. Idan basu zo ba wa zasu nuna a matsayin dangin uba?" "To nagode Mairama. Sai kin daura dammarar hakuri da juriya. Yanzu sabuwar rayuwa ce zata bijiro miki da baki taba zato da tsammani ba." Hawaye ya zubo mata da ta tuna rasuwar Mal Muhammadu. Washegari da wuri Mairama ta tafi gidansu Zainab. Allah Ya taimaketa bata mance hanyar ba. Mahaifiyar Zainab din ta samu wadda ta fada mata kwana hudu da suka wuce babanta ya kaita Kano gidansu Hadir. Duk da bata san kan garin Kanon sosai ta nemi tayi mata kwatance amma anyi rashin sa'a ko sunan unguwar bazata iya tunawa ba don wahala yake mata. Mairama tana kuka tace ta fada mata tazo itama zata koma garinsu. "Kema mijin naki yaji rauni ne?" "Rasuwa yayi." Idanu ta zaro "idan Hadir yaji ban yaya zai ji ba. Allah Ya zama gatanku Mairama" Sallama tayi mata ta koma gidan domin su karasa shirin tafiya. A daren jiya ta bude envelop din da Zayyan ya bar mata. Ashe gabadaya sauran kudin gadonsa ne ya bar mata da takardun gidansa na Kano. Dasu ta fita a jakarta idan ta koma zata fito dasu ta nunawa iyayen. Dama suna rayuwa ne bayan tafiyar mazan akan albashinsu da ake bawa matan. Kudi ne da bai wani taka kara ya karya ba. Wasikarta kuwa zuciyarta ta kasa bata kwarin gwiwar karantawa har lokacin. ********** [02/11 7:29 AM] My 2nd Mtn: 15. Maikudi ne tsaye a ofishin da aka tura shi cikin barikin su Zayyan akan maganar kudi ne dai. "Jiya Babanku yazo akan zancen nan mun fada masa bamu da komai. Ya bada adireshinsa duk lokacin da kudi yazo zamu nemeku" officer din ya bashi amsa bayan ya gama jero tambayoyi. Yana hargaginsa na rashin mutumci yace "Ashe cewa yayi shine babanmu don ya ci kudin gado. To wallahi karya yake. Babu wata alaka ta jini tsakaninmu" Wani sojan ne ya shigo yana tambayar wancan me yake faruwa cikin harshen turanci. Sai da ya sara masa ya bashi amsa da gani ya fishi mukami. Maikudi yana jin ana bayani duk da bai iya gane duka maganar amma ya dan fahimci me akeyi ya katse wancan "You understant Zayyan Muhammad Tureta is die? Me. Biggggggggg broza. Is me faza dinmu daya ai" ya nuna kansa yana murmushi yana so su fahimci shine babban wan Zayyan. Mutumin ya hade rai yace a kore shi kuma idan ya kuskura ya sake zuwa ba'a neme shi ba a kulle shi saboda yana mudu hayaniya. Dayan yana soma fassara masa bai tsaya jin karshen ba ya fice yana ta Allah Ya isa an kashe masa kani. A hanyarsa ta komawa ne ya rinka tunanin dole fa akwai abinda Zayyan ya barwa matarsa. Idan ba haka ba da me suke rayuwa duk tsahon lokacin nan? Yafi karfin ita da kwadayayyen babanta suyi masa wayau akan hakkinsa. Yana zuwa dakin da Malamijo yayi masauki ya shiga. A shirye suke suna jiran dawowar Mairama. "Dama nazo akan yaran nan ne Radhiya da Zayyan. Nace ko zaka yiwa Mairama magana idan ta yaye shi zan zo na dawo dasu gabanmu saboda gatansu dai bai wuce wurin dangin mahaifinsu. Idan kun tafi yanzu kai ma nauyi ne kawai zai kara hawa kanka. Sannan bazan zuba ido bane tayi aure 'ya'yana su koma agolanci a gidan wani" Malamijo an tabo inda yake masa kaikayi kuwa. Ina zai kai karin bakuna uku a gidansa. Gara Mairama yana son abarsa, amma yaran nan da aka ha'ince shi yayi ta yiwa babansu kallon kitse ashe rogo ne "indai wannan ne babu damuwa. Zanyi magana da ita kuma dole ta amince don nima bazan so suyi rayuwar agolanci ba azo ana wulakantasu" Maikudi ya fita da wani mugun murmushi. Soro ya koma ya zauna jiranta. Ilai kuwa babu jimawa sai gata tana ta sauri kada a gaji da jiranta. Dukawa ta danyi ta gaishe shi ya yafito ta da hannu. "Yaki zo Mairama. Magana nake son yi da ke" Kanta a kasa ya fada mata yadda ya fadawa Malamijo. Ai tuni ta saka kuka iya karfinta tana rokansa ya rufa mata asiri ita bata da niyar sake aure. "Kinga da har mun gama magana da babanki" Gabanta ne ya fadi. Ta san halin Malamijo kuma tas zai bada yaran nata. "Don Allah kayi hakuri" "Naji, amma bazaki bar garin nan ba sai kin fito da dukiyar kanina. Dole ne a raba gadonsa saboda a sauke masa nauyi" Hannunta yana rawa ta zaro envelop dinnan daga jakarta ya warce gabadaya. Sakar masa tayi kafin ya hada da hannunta. "Daren jiya na gansu shine nace dama yanzu zan fito dasu ayi abinda ya kamata" Kankance idanu yayi yana kallonta bayan ya zaro takardun gidan da kuma damin kudi da aka nannade da kyauro "ashe ke mutuniyar banza ce ban sani ba? Wato da guduwa zakiyi da komai saboda tsabar mugunta da bakin hali kamar na tsohonki" Ta shiga girgiza kai tana hawaye "a'a wallahi" Wasikarta ta hango ta fadi ta mika hannu ya taketa da sauri da kafa "meye a ciki?" Hankalinta yayi matukar tashi "wallahi Allah wasika ce ya bar min. Ba takardar komai bace" Sai ta ga yayi murmushi saboda ya fuskanci yadda ta rude "soyayya manya" yatsansa ya kada mata "kalli nan, zan cire takardun gidan saboda dama ina binsa bashi da bai biya ba. Ina jin gidan ma bazai isa ya biyani ba amma dai su kadai zan dauka. Muje ciki idan munafukan dattijan nan sun zo ki basu kudin a rabawa wanda aka ga damar bawa. Ni kuma nayi miki alkawarin babu wanda ya isa ya rabaki da 'ya'yanki kuma zaki koma Kano da wasikar masoyinki" Mairama kallon mugunta irin ta Maikudi ta tsaya yi ta rasa shawarar yankewa. A zatonta zaa raba gado a barwa yaranta gidan sai su zauna a ciki. Ita kuma a cikin kudin ta nemi abinyi domin kula dasu. Wani hawaye ke bin kuncinta tana jin zafinsu har zuciyarta "hakan yayi maka?" Ya dage gira "yayi...ki sani idan kina tunanin juya magana ko Jume tayi kadan tasa na bar miki yaran nan balle kuma wancan tsohon Mal. Aminu. Mahaifinki kuma a yadda na fahimta ko sadakarki na nema zai iya hada min" Share idanunta tayi tabi bayansa. Kowa yayi zaton kukan tafiya ne take yi da mutuwar mijinta. Su Mal.Aminu sun zo ta dauko kudi ta mika masa. A take aka kira wani malami ya kasafta da aukinsu kuwa aka bata nata aka ware na yaran yace batun bashi fa Mairama tace ya tabbatar mata babu msi binsa komai kafin ya tafi. Maikudi ko tari baiyi ba ganin babu mai gadon nashi sai su kadai. Jume har dadi taji yayi hankali. Nasiha da ban hakuri aka sake yiwa juna sannan Mal.Aminu ya roki alfarmar kada ta tafi ta yanke zumunci dasu albarkarcin 'ya'ya "mu kuma nan babban kalubale ne a garemu mu da gwamnati. Mu dubi marayun yaran nan da mahaifiyarsu kafin mu ga me Allah Ya tsara musu. Haka ma gwamnatin ta dubi rayuwar sojojin da take takama da sadaukarwarsu. A dubi masu ran wanda suke a bakin aiki, a dubi masu rauni da nakasa sannan a dubi iyalan mamatan domin a gaskiya akwai nakasu mai girma a rayuwar iyalan bayin Allahn nan" Sun fara fitowa mata ana ta kuka Maikudi ya samu ya tarar da Malamijo shi kadai iska tana ta kada yalolon yadin jikinsa yana manne masa ramar tana kara nunawa. Takardun gidan ya nuna masa yana murmushin samun nasara. "Naga ka kawo idanu ka dora akan dukiyar da baka da alaka da taruwarta shine nace bari dai na nuna maka waye Maikudi." Ware ido Malamijo yayi ya karewa takardun kallo "na meye?" "Na gidan Zayyan ne wanda yanzu ya zama nawa. Kana iya kaini kotu don a kwatarwa 'yarka da jikoki hakkinsu amma ka sani kana yin hakan zan rabata da yaran nan ni kuma. Ta fada min akan ta baka dukiyarta gara kowa ya rasa don baka ragawa kowa akan kudi" Kallon Mairama yayi zuciyarsa tana tafarfasa. Wato Zayyan yana da gida shine ta dauka ta bawa wan mijinta tana tunanin zata dawo masa gida ta jabe ya ciyar dasu. Lallai Mairama bata gama saninsa bane shiyasa har taje tana tona masa asiri. Har shi zata ha'inta yana mahaifinta. Kwafa yayi yana jiran su kebe don bashi da bukatar magana a gaban mutanen da ya kula bakinsu duka daya. Maikudi kuwa dariya yayi bayan ya tafi. Alamun Malamijo da ya gani ne yasa shi wannan magana sai gashi tazo daidai da halin nasa. Mairama da Zayyan ma ta kasa tonawa mahaifinta asiri a gabansa me zai kaita fada a gaban Maikudi? Radhiya ta dauka Hajjo ta goya Zayyan suka tafi tashar da zasu sami motar Kano. Sai da suka dau hanya don Salisu ya biya su kadai ne a ciki Mairama tana hawayenta Nene Marka na bata baki kawai Malamijo ya soma fada akan bayar da takardun gida da tayi. Kai, ita kam da me zata ji ne a rayuwarta. Tana kuka tayi musu bayanin yadda abin ya kasance. "Ko dai mu koma ne a karbo takardun? Duk tsiyarsa baifi karfin hukuma ba fa Mairama" Salisu yace nasa ran a bace. Tsorata tayi "don Allah ku kyale shi. Yaran nan zai karbe, babansu ma baiji dadin zama dashi ba" Nene tace "Duk da haka Mairama mu zamu tsaya miki. Gidan a ina yake?" "A Kano ne" Salisu ya tabo dreban "Malam don Allah kayi hakuri ko zamu koma" "Babu inda zamu je. Idan kuma sai kun koma to ni a ajiyeni a nan." Nene Marka tace "haba Malamijo meye hakan?" Rufe idanu yayi yana ta fada don sosai yaji haushin maganar Maikudi da rasa gidan da yayi. Ace 'yarsa da yafi so da tausayi a cikin 'ya'yansa ita ce tayi masa haka. "Ina nan kan baka na bazan koma ba sannan kuma ki shirya tunda dangin miji sunfi uba ni bazan dauki nauyin kowa ba. Gida dai gaki gashi kuje a baku daki. Sai yanzu na raina waye Zayyanun ma. Har me yayi miki wanda ni ban miki dubunsa ba. Ji gidan da ya ajiyeki...." Ta daure matuka amma bata jin zata taba jurewa wani ko da kuwa Malamijo ne ya zagi Zayyan. Ko bata aure shi ba yanzu ta san daraja da kimar soja....wallahi yafi karfin raini. "Yayi min komai Malamijo" tace cikin kuka tana rungume Nene iya karfinta har Radhiya sai da ta tsorata "ko a kango muka zauna dashi har abada bani da tamkarsa. Wayyo ni ashe haka mutuwa take da daci da tona asiri? Lokacin da nayi maraicin uwa bansan ciwon rashi ba saboda bamu saba ba. Allah Ka jikan Zayyan ko Ka dauki raina nima na huta" Zubar hawayenta ya taba Malamijo bare da ya ga ta rike kirjinta da yake mata mugun zafi. Dreban yace wa su juya ta dago rinannun jajayen idanunta. "Allah Ya kaimu masu gidan su girma zasu karbi abinsu da izinin Allah. Amma a yanzu tunda yace yaji ya gani zai ci haram bazan shiga tsakaninsu ba" Duk rashin halin Hajjo sai da tayi kukan tausayin Mairama. A haka suka tafi Kano Salisu yana ta mamakin halin Malamijo. Ashe Salame gado tayi na munin hali ba taka haye ba. Tare suka sauka a tasha ya ja Mairama gefe ya fito da kudi masu tsoka ya damka mata sannan suka nemi motar Sumaila shi kuma ya shiga hayis zuwa gidansa. Dama ya riga ya gama shawararsa tun a hanya shiyasa yana ganin yadda Salame ta fito muzumuzu ita a dole tana cikin alhinin mutuwar masoyi ko sannu bata yi masa ba ya dakatar da ita zata tashi ta bar falon saboda ta ganshi. "Salame ki hada kayanki ki tafi gida na sakeki saki daya" Kiris...sauran kiris irin mai riss dinnan zawo ya tsinke mata. Tunda take bata taba jin fargaba da tsoro kamar wannan lokacin ba. Ya saketa ta tafi ina? Sumaila? Allah Ya kiyaye. A iya zurfin tunaninta Salisu yana mata son da zai iya hadiye kowane abu tazo dashi. Shiyasa take yadda taga dama iyaka yayi fada anjima ya dawo yana bibiyarta. To ko dai kunnenta baiji da kyau bane. "Ni ka saka?" "Halifa da muka haifa da ana komawa baya Salame bazan so hada jini dake da mahaifinki ba. 'Yar cikinsa tana cikin magagin rashin miji amma dukiya yake nema duk arzikinsa. Wallahi bazan iya ba. Kije Allah Ya baki daidai dake." Kande ya kwalawa kira tazo ya cire naira goma yace ta wuce ta kaiwa mamansa Halifa yana tafe. Dayake daga can gidansu aka kawota ta riga tasan gidan. Salame tana kame ta kasa motsawa ya wuceta ya shiga daki. Sai da abin ya sami wurin zama a kwanyarta ta shiga ta fara masa ihun masifa. "Wato akan Mairama ka sakeni saboda Malamijo ya bata mata rai. Bazaka burgeni ba sai naga ta tare a gidan nan ranar asabar" "Ki fita sawunki a likkafa kafin na tashi" yace daga kwance Tafa hannuwa tayi " nima na huta da auren kaddara zama da mijin da baka so" Duk inda zata cusa masa haushi ta rinka nema ko a jikinsa tunda ya rabu da kwallon mangwaro ya huta da kuda. Gidansu ta koma ko ta kan Halifa bata bi ba. Awa uku tsakanin saukar su Malamijo da dawowarta gidan. Yadikko ta tareta ganinta da akwati niki niki "ke kuma daga ina?" "Sakoni yayi" ta fada cikin yanayin ko in kula. Ashar Malamijo ya lailayo ya saki yana kara tunzura da yadda take magana ko a jikinta "wai nufinku duk kun dawo min gida kenan?" "Ya son ranka? Ca nake mata biyu ka saki a dan tsukin lokaci guda, ai gara ka dana" Hajjo ta fada masa sannan ta saki labulen dakinta. "To Al-Qur'an daga ke har Mairaman kowa taji da kanta bazan iya ba. Yara masu bakin hali kun fita a talauce kun dawo a tsiyace" Dakinsu na da ta shige abinta ta barshi tsaye. Nan taci karo da Mairama da kyawawan 'ya'yanta. Kamar ta shareta sai ta fasa tace mata ya hakuri. "Mungode Allah" "Allah Ya jikan shi" "Amin" Daga haka babu wadda ta sake kula 'yar uwarta har suka yi shirin kwanciya. Ganin Mairama da yaranta ya tuna mata da Halifa sai taji wani iri gashi bata yaye shi ba dama. Kyandir Mairama ta kunna a gefen katifar da suke kwance ta kwanto wasikar Zayyan ta soma karantawa. _(Na rubuta wannan takardar tun ranar da sunana ya fito a cikin masu tafiya Liberia. Sai nake ganin kamar jiya muka yi aure har zan tafi na barki. Mairam ban sani ba ko zan dawo ko shikenan tafiyar. Don Allah alfarma daya nake roko kada bakinki ya taba gajiyawa da sanyani a addu'a. Idan kewa ta isheki kinyi kukan rashina ki sani cewa nima ko a ina nake idan na tunoki sai na zubar da hawaye. Ina sonki Fillo Allah Ya sani amma ina son ki saka a ranki mijinki yayi alkawarin bautawa kasarsa ne. Zanfi kowa son son ace ina tare da iyalina kamar kowane magidanci. Sai gashi aikina yayi min tsakani da hakan. Lokaci zuwa lokaci zan rinka tafiyar da babu lallai na dawo. Duk da haka ina alfahari da aikina kema ki tayani kinji. Idan kin haihu kafin na dawo ki zabawa abinda muka samu suna. Ki kular min da 'Yar Soja Alheran innar Daadaa. Sauran kalaman da suka rage a kirjina sai na dawo gareki zaki ji su. Idan ban dawo ba na baki amanar kanki da ta 'ya'yana. Allah Yayi muku albarka. Lt Zayyan Muhammad Tureta)_ TAKWAS [02/11 7:29 AM] My 2nd Mtn: 16.*********** "Ke Radhiya, zo kije kantin sauki ki siyo min yis" Shanyar kayansu da ta wanke take yi nata da na Emzee da Mairama. Kallon Binta tayi tace "ki aiki Emzee ko wani don Allah kinga ni bana fita saboda Ummi" "Inda na aike kin har wani nisa ne dashi da zaki fara yi min felekenki na tsiya. Ko kuwa nace kije ki zauna ne?" Zumburo baki tayi "Ummi wanka zata yi idan na gama shanya. Zaki kai mata ruwan ki ajiye mata soso da komai a kusa da ita inji miki aiken?" Mairama tana daki ta jiyo su ta rinka shafa bango har ta fito. "Ke!" Tace da tsawa Radhiya ta juyo tana jira taji Mairama ta umarceta da zuwa kantin ta fada mata kai tsaye ba zuwa zata yi ba. Tunda mahaifiyarta ta makance ta kara hankali da bambance su waye masu kaunarsu da gaskiya. Malamijo ya gina gidansa da turbar nafsi nafsi kowa ta kansa yake yi. Babu wani jinkai na azo a gani saboda rashin wadata su da abubuwan da ya dace. Idan ka cire Yadikko babu wadda take leka Mairama balle ace mata yaya jiki. Dukkansu take kallo tana jin kanta daidai dasu. A duniya bata da sama da Umminta sai Emzee. Shi kuma haushinsa take ji saboda rashin magana. Gabadayansa bashi da walwala sosai yaron saboda tsangwama musamman daga Salame kafin ta bar gidan. "Ki karba kije ki siyo mata ko ma meye idan kin dawo sai nayi wankan" Radhiya yarinya 'yar kimanin shekara goma sha daya wadda ta gado zuciya ta mahaifiyarta, barkwanci da jarumtar mahaifinta da kuma jinkai da tausayi nasu su biyu ta kekashe idanu "Ummi ni bazani ba idan na tafi ma zubar da kudin zanyi a kwata ko na sayi danmalelen gidan Fadi. Haka kawai yau babu makaranta kowa yana nan taki aikensu sai ni saboda bata damu dake ba" ta kare maganar muryarta da alamun zata yi kuka. Mairama ta daga hannu daga inda take tsaye kamar za ta dake ta "kizo ki karba kafin ranki ya baci" Juya keya tayi ta mika hannu ta baya tana jira Binta ta ajiye mata kudin harda wani kada jiki. Emzee ne yazo ya karbe "ni zanje me za'a siyo miki?" Binta ta warce kudin "bazaka je ba din, wannan fitsararriyar nake so inga uban da ya tsaya mata a cikin gidan nan. Har ni kike juyawa keya saboda baki da kunya" Mairama daurewa kawai take yi saboda rashin ido. Itama ta sani an tsangwami 'ya'yanta an hanasu rawar gaban hantsi saboda an ga tana zaune. Amaren Malamijo Hanne da Binta sunfi kowa kaudi da takura musu. Kuncin zuciyarta ne ya taso ta tuna mijinta. Da yana raye waye duk gidan nan ya isa ya taka su? Yadda kowane uba ke kaunar 'ya'yan shima tasan zai so nasa kuma ya kyautata musu rayuwa. "Karami janyo min hannun yayarka" Da kanta ta karaso gaban Mairama ta kama hannunta don ta nuna mata ta iso. Hannunta ta shimfide mata a gadon baya, dukan ya shigeta amma ta dake. Mairama kanta ciwo take ji yana addabar zuciyarta "in ce kije aiken ki ce bazaki ba saboda ban isa ba? Ko saboda bani da ido sai yadda..." Zubewa tayi a kasa tasa kuka "Ummi kiyi hakuri don Allah zanje." Kudin ta karba daga hannun Emzee tana cewa ya mayar da Ummi daki kafin ta dawo. Rai a bace taje ta siyo yeast din naira hamsin maimakon na ashirin da aka aiketa. Da ta dawo daga bakin kofa ta tsaya ta zura hannu "Gashi" "Shigo ki bani" Binta tace da gadara tana fadawa yayarta "kinga fa irin jarabar da muke fama da ita. Uwa makauniya 'ya'ya marasa da'a" "Mu ba jaraba bane" Radhiya ta maida mata da tsiwa. Bintu bata bata lokaci ba ta kai mata lafiyayyen mari. "Uwarki makauniyar nan ma bata isa ba wallahi" Tana kuka baki bai mutu ba "ba dai uwata ba" Ran Binta ya kara baci "sai ta wa?" "Wanda ya tsargu dashi nake" Radhiya ta amsa kai tsaye. Kafin Binta ta ankara ta fice daga dakin. Da sauri ta kamo Radhiya a tsakar gidan tana shirin shiga dakinsu. Mairama tana jinsu ta yi salati ta sake tashi "me kika sake yi kuma?" Binta ke dukan Radhiya da zagi amma a hakan cewa take ba dai tata uwar ba. Hajjo ta taho kwatar Radhiya Binta ta sake tunzura ta daga hannu zata sake kai mata duka ga Mairama har ta soma hawaye suka ji sallama. Amsa sallamar bakuwar suka yi Binta bata kula ba ta kuma daga hannu taji matar da ta shigo tace tayi hakuri kada ta sake dukanta yara sai da rarrashi. Idanu a soye don itama Binta ba kunyar gareta ba tace "yau ko uban da ya haifi uwarta ne wallahi bai isa ya hanani dukanta ba" Malamijo wanda motocin da ya gani a kofar gidansa suka saka shi tasowa daga majalisar da yake ko kallon mutanen wajen baiyi ba tunda ya ga daya ta shiga gidansa. Ya shigo kenan ya ji me Binta tace ya kuwa murtuke fuska. "Ahhh lallai yarinya kwananki a gidana ne ya kare shiyasa kike zagina. To shiga ki kwaso tsiyarki kizo ki wuce na sakeki saki biyu" Innawuro ta kalli Ali tana jin wani bacin rai. Wato duk tsayin shekarun nan yana nan da bakin halinsa na sakin mata. Ta sani wadda ya saka din tayi laifi amma a bainar jama'a haka ya dankara mata saki. Shi kuwa ko a jikinsa sai ma binta da yayi da kallo yana son tuna a ina ya santa. Matan gidan da yara hankali ya koma wurin Binta da tayi dakinta tana kuka basu kula da Radhiya da take zaune a kasa ba ko bakuwar da take tsaye. Yadikko har kullum ita ce mai hankalin kuma bata gida a lokacin. Mairama ta duka tana mika hannu neman Radhiya da ta tabbatar tana wurin tana kuka. Cikin kuka da ta gaji da laluben tace "ina kike ne?" Muryarta kawai Innawuro taji ta saki baki tana kallonta. Babu tantama wannan ce Mairama diyar Mairo don banda kama ta fuska hatta muryarsu tayi shige sosai. Kafadar Radhiyan tayi sa'ar dafawa ita kuma haushin aiken tun farko ta janye jikinta tana saka kuka mai sautin da bata yi ba a gaban wadda ta daketa. "Ba ke kika ce sai naje mata aike ba" "Allah Ya baki hakuri to tashi muje daki" Mairama ta mikar da Radhiya a daidai lokacin da Innawuro tace "Mairama?" Malamijo kuma yace "Innawuro?" Mairama ta juya duk da bata ganinta ita kuma ta juya tana kallon Malamijo ashe tun dazu yana tsaye. Hankalinta duk yayi kan Mairama tace "muna da yawa sauran suna waje. Na shigo ne sanar da zuwan namu" Yawun bakinsa ne ya kafe, lebbansa suka bushe sai harshe yake ta fitarwa yana lashesu. Duka motocin nan bus uku da canta daya 'yan uwan Mairo ne? Ya sani da kansa ya taba nemansu saboda tausayin Mairama. Amma tuni ya watsar musamman yanzu da rayuwarta take cikin garari. Innawuro ta dawo dashi cikin hayyacinsa da yaji tana cewa Emzee ya fita ya cewa bakin waje su shigo. Yaron ya tafi yin abinda ta saka shi ta dawo da kallonta ga Radhiya da Mairama da suke tsaye kawai a wurin. Gani tayi har yanzu Malamijo yaki magana ta cewa Mairama "muje dakinki kinji 'yata" Mamaki ne fal cikinta bata san ko su waye ba. "Ke muje daki" ta ce da Radhiya Hannunta cikin na Radhiya suka shiga dakin da komai ya kare masa yanzu sai katifa da shirgin kayansu. Rage tsayi Mairama tayi daidai kunnen Radhiya "ina bakuwar take? Kin taba ganinta?" Innawuro tana kusa dasu kuma taji tambayoyin da tayi mata. Radhiya sai ta dago kai tayi mata murmushi tana dan jin kunya. Mairama ta matsa mata hannu "Ki bani amsa mana, idan rigima kika sake kwaso min zaneki zanyi wannan karon" Hayaniya ce ta cika tsakar gidan. Maza ne matasa da magidanta harda dattijai haka ma mata suka rinka tururuwar shigowa. Malamijo yayi tsamo dashi yana kallonsu zuciyarsa ta cika da firgici da ya ga cikin matasan harda masu sanduna. Sandarsu ce ta fulani da ado baya cika sai da ita, amma da yake ba gaskiya gareshi ba sai ya manta da wannan al'adar ya luluka tunanin ko dai duka zasu yi masa. Fulatanci suke ziryan baka jin komai sai sunan Mairama. To shima dai yaren gidansa kenan sai dai suna taba Hausa sosai. Gaban Radhiya sai da ya fadi da ta hangosu q ta tabota "Ummi sun kara yawa wallahi harda sanduna." A kidime tace "dan gidan wa kika tabo kuma?" Harda dan guntun hawayenta na tsoro tace "ni da bana fita wa zan taba?" "Mairama kwantar da hankalinki muje wajen don nan bazai daukemu ba. Ni da su duka dangin Mairo ne mahaifiyarki" "Me? Da gaske?" Matsawa tayi daga jikin Radhiya hannuwanta suna neman kofa da sauri zata fita. Innawuro jiki ya kama rawa ganin da yadda Mairama ta fita. Radhiya ta kalla hawaye suna wanke fuskarta. "Bata gani ne?" Radhiya tabi bayan Mairama don ta karasa da ita gabansu tana cewa "eh" "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" ta iya fada tana kuka har wajen suna jin sautinta. Duka idanunsu sun koma kan Mairama tana kuka take tambayar Radhiya da ta rike mata hannu su nawa ne? Baffa Gide kamar yadda 'ya'yan 'yan uwa suke kiransa ji yayi kamar iska zata daga shi don tashin hankali da yaji me takw cewa kuma tamkar ya ga Mairo haka kamanin Mairama suke da na 'yar uwarta. Kyaunta ne yasa Malamijo zabarta da biyan bashi duk da a lokacin Innawuro ta girme mata kuma itama bata yi aure ba. Tsakar gidan kamar gidan kallo ya koma. Ga dangin mahaifiyar Mairama ga ahalin gidan Malamijo kacokan. Shi Baffa Habubakari kuka yake ma saboda rauninsa yafi na dan uwansa. 'Ya'yansu jiki yayi sanyi. Basu san Mairo ba don manyan ma suna kanana komai ya faru amma sun san wannan makauniyar da ta nufosu jininsu ce. Ga dai idanu a bude amma basa ganin komai. Sai da suka zo tsakiya Radhiya taja hannunta don su gaishesu tunda ta ga akwai manya "ummi mu gaishesu" Emzee sai ya baro gefe shima ya dawo ya durkusa tare da Umminsa da Addarsa. "Ina wuninku, yaya hanya....Allah sarki ashe baku manta dani ba" shine abinda Mairama take cewa tana ta waige hagu da dama saboda rashin sanin a ina suke. Su Radhiya ma gaishe su suka yi bakin Mairama kamar gonar auduga duk da bata san mutum nawa bane. Ganinsu su ukun nan ya ishi bawa tausayi. Ga uwa mai cike da kuruciya amma makauniya mai marayu biyu a gabanta. Ga kuma 'ya'yanta tamkar zakuna suna gadin farincikinsu, jigon rayuwarsu. Sautin kuka Mairama ta fara ji daga yawancin matan da suke wurin ta rinka murmushi tana jiran taji wani cikinsu ya tabata taji dumin uwa. Kamar Innawuro ta sani ta durkusa a gabanta ta rungumeta suna sakin kuka a tare. Ardo Barkindo ya kalli Malamijo ya fito a tsolon rakensa yace "a bamu wuri mu zauna ko" Sai kuma ya farga ya dawo daga duniyar tunani "kai, kai ina kuke ne, ga baki a shimfada musu tabarmi daga jikin bangon can yafi inuwa." Tabarmin aka kawo suka zazzauna ya sake dubansu "wace mai girki ne a kawo musu abinci" Hajjo sarkin bakar magana ta tabe baki "Binta ce kuma yanzu ka dankara mata saki ko a kirawo ta ne?" Kunya tamkar wanda aka watsawa ruwan kankara haka Malamijo yaji ya muzanta a gaban mutanen da ya taba wulakantawa yau suka taru suka yi masa kwarjini. Allah Ya taimake shi Yadikko ta dawo yace "Uhmm, uhmmm....Yadikko fito da kwanuka aje gidan Tsahare ayi musu hadin wake da shinkafa amma da miya za'a siyo da salak. Idan akwai taliya 'yar gwamnati duka ta bada saboda ya ishesu. Sannan tasa nama a wadace do Allah" Yau wace rana Malamijo zaiyi abin kai. Ya zura hannu zai zaro kudi yaji hankalinsa ya tashi...mutanen nan fa da yawa, anya ba duka rugarsu Gide ya kwaso ba? Ardo ya dakatar dashi don bai manta bayanan da yaji game da Malamijo ba. "Kaga Malam Ali ba zama zamuyi ba a kan hanya muke. Ka zauna muyi magana" A tsorace ya zauna daga gefen Baffa Gide don kallon da yake masa kamar zai wafto shi ya shiga dukansa ne. Bangaren matan kuwa Mairama sai dai taji wannan ta rike mata hannu ko an shafa bayanta suna fadin sunayensu. Da addua ga marigayiya Mairo Ardo ya fara bude zaman nasu sannan ya ari bakin duka dangin nasu ya baiwa Mairama hakuri akan zumunci da suka yi sakaci dashi. Daga karshe ya gabatar da bukatarsu da cewa a yau dinnan ba gobe ba suke son daukarta da 'ya'yanta zasu koma da ita wurinsu. "Don Allah da gaske?" Mairama ta sami kanta da fada cike da farinciki. Bata sansu ba kuma bata san halayensu ba amma ko don samun nutsuwarta tana so ace gata da dangin mahaifiyarta. Matar Baffa Habubakari tace mata "Allah Yasa ki yarda ki bimu" Ita kuwa me zai hanata yarda idan ba rashin sanin ciwon kai ba. Ardo ya umarci yaran nasu maza da su je su shigo da kayan da suka zo dasu. Malamijo ya baza ido ya ga wane shirgin suka kawo sai kukan tumaki ya ratsa kunnensa. Raguna hudu ne da katoto kuma kosasshen sa guda daya. Kwanduna manya manya guda biyu cike da kwan zabi, buhun shinkafa daya 'yar gwamnati mai doki sai 'yar hausa daya da kuma buhun gero shima biyu. "Tun daga haihuwar Mairama har aurenta, haihuwar jikokinmu da rasuwar mijinta da muka sami labari babu wani abu daya da muka halarta balle mu bada gudunmawa a matsayin iyayenta. Mal Ali ga wannan kayan, ba wai sakayya bace sai dai ihsani ne daga garemu kuma muna godiya a madadin marigayiya Mairo na kula da marainiyar Allah da kayi" Baffa Gide ya ce sauran suna gyada kai. Innawuro ta riko hannun Emzee ya zauna a gefenta "ba rabaka zamuyi da ita ba. Mairama har abada 'yarka ce. Muna so ne dai ta bimu ta sanmu muma mu santa" Yake Malamijo yake ya rasa dalilin da yasa suka yi masa kwarjini "bama zan hanaku tafiya da ita ba" Kasa magana Malamijo yayi sai tarin kunya kamar ya tona rami ya binne kansa. Ba Mairama ba kadai kaf 'yayansa me zai bugi kirji yace yayi musu. Hajjo sai da ta magantu taji dadi ta fake da yi musu godiya "Allah Ya saka da alkhairi mungode. Ohh Malamijo baki sun zo gari -e- gari ko ruwa ba'a basu ba sai karbar kyauta daga hannunsu. Ke Radhiya tashi muje na tayaku hada kaya yau kakarku ta yanke saka" Cike da zumudi Radhiya ta mike tana kallon yadda Mairama take ta fara'a a tsakanin mutane. Idan ma kuruciya tasa bata gane mahimmancin zumunci ba a iya hankalinta ta sani cewa Umminta tana cikin farinciki. Wannan kuma ya isheta komai. Yadikko bata hakura ba sai da ta dafa musu dafadukan shinkafa da wake. Babu bama dai bare kifi amma tayi nata kokarin. Abin kunya ne ace wannan bakin sun zo sun tafi basu ci komai ba ga nisan hanya. Tasan tsiyar da suka tarar a gidan ita ta kara tunzura komawarsu a ranar. Batare da bata lokaci ba suka fito an gama shiri. Wani dan akwati da take ajiyar mahimman abubuwa kamar khakin Zayyan, wasikarsa da kuma hotuna tace Radhiya ta tabbata ta dauko. Dariya tayi don ta gama haddace komai na ciki. Hotunan yawanci na bikin iyayenta ne da na sunanta. Karfe biyar da kwata sun gama shiga mota. Baffa Gide yana tsaye a gefen mota kusa da Malamijo suka sake yin musabaha "yanzu da muka dena yawo idan kana nemanmu mun koma Giade can asalin garinmu amma rugarmu tana daga ciki da dan tafiya daga garin. Wannan da kake gani mijin Innawuro shine Ardo na biyu bayan kafuwar rugar" Sallama Mairama tayi da kowa daga ita har su Radhiya ko digon hawaye irin na kewa dinnan. Rabuwa da Yadikko da Hajjo da kuma sauran 'yan uwa ya dan sa sunji wani iri to amma fa ko kadan bikin Magaji bazai hana na Magajiya ba. ********** WAIWAYE.... [02/11 7:29 AM] My 2nd Mtn: 17. "Ahayye nanaye, wallahi mutum ya yi min ba kyalewa zanyi ba don kaji in gaya maka yaro" tafa hannuwa tayi sannan ta rike kugu tana girgiza jiki a dole ranta ne a bace. Abokin fadan nata wani sangamemen yaro ne don shima akwai kuruciya sai girman jiki. "An fada din" yace sannan ya cigaba da wakar da ta hadasu fada "Malamijo Malamijo tsolon rake. Ga kwadayi ga rowa yaki yin gaba" Wani kukan kura Radhiya tayi ta dire a gabansa ta nuna kasa "in ba tsoro ba dangwali" ta nuna masa kasar wurin. Dabi'arsu kenan 'yan makarantar wadda ta kasance firamare ta gwamnati idan ka yarda zaku dambace to kowa ya dangwali kasa. Daga nan sai a kaure karfinka ya kwace ka. Dukawa yayi zai dangwala ga tsirarun abokansu da basu bar makarantar da wuri ba sun tsaya kallo. Sai da ta daidaici yayi kasa da fuskar nan kawai ta dauke shi da mari ta ranta a na kare. Kai tsaye staffroom ta wuce inda malamai suke wurin Umminta. Tana shiga ta cukwikuye jikin Mairama tana kuka wai su Danmama ne suka dake ta. Tahowa suka yi Danmama ne a gaba kayansa duk kura saboda faduwar da yayi garin bin Radhiya. Kofar staffroom din taje ta saka su kneeldown har Radhiya sannan ta nemi jin ba'asi. Sai aka rasa me fada mata. Duk fitsarar Danmama yasan da kunya dai ya maimaita wakar a gabanta. Radhiya dama ko me zata yi mata bazata fada ba don kada ranta ya baci. Daga bayanta taji wani malami yace "Anti barni dasu kiyi tafiyarki gida. Idan na gama zanesu zan taho da wannan mai kunnen kashin" Mairama ta gyara zaman farin gilashinta tayi dan murmushinta da ta saba yanzu da wuya kake ganin bacin ranta ta koma ta dauko 'yan tarkacenta tayi hanyar fita daga makarantar don dama an riga an tashi. Daga karkashin wata katuwar bishiyar marke take hango yara suna 'yan wasanninsu. Idanunta suka sauka akan Emzee yana zaune yayi shiru yadda ya saba yana jiranta. "Karami zo mu tafi" tace da dan karfi don ta kula bai ganta ba sai gashi ya taso da saurinsa. Kayan hannunta zai karba tace ya barsu su tafi "Ummi ina Adda?" "Kyale wannan yau ma fada tayi" Sunyi gaba wasu 'yan ajinsu suka rinka kwalo masa kira suna Emzee sai an dawo hutu. Wannan suna da Mairama ta hakura da yakar sa dole shine sunan da yabi Muhammad Zayyan har gida. Mutane kalilan ke kiransa Zayyan ko Karami kamar yadda take fada. Yace wani malami da suka yi a firamare two ne yake kiransa MZ Tureta. Shikenan abu na yara ya koma Emzee. A makaranta kuma gurfane gaban Uncle Idris su Radhiya ne da Danmama. Sai da Mairama ta tafi Radhiya ta fada masa sunan da suke kiran kakanta dashi. Uncle Idris ya tabbatar zasu aikata yayi musu bulala biyar biyar mai zafi da dorinarsa ita kuma biyu ladan biye musu. A waje ta jira shi shima ya dauko kayansa tunda yau take ranar hutu suka tafi yana mata nasihar fada da maza. A cikin shekarun da suka gabata rayuwar Mairama sai dai godiyar Allah. Zamanta a gidan Malamijo tamkar zaman gidan haya ne. Iyakar gaskiyarsa shi nauyi ya masa yawa fitar da kudi kamar ana mintsininsa ne. Ya kara kudin cefane da kyar da sudin goshi amma daga nan fa ko me mutum ke bukata mace ko namiji cikin iyalinsa sai dai su nemawa kansu. Abu na farko da Mairama ta fara yi shine adana kudaden gadonsu a ranta tana tanadinsu ne domin karatun yaran a gaba. Sai da ta fuskanci sabulun wanka wannan idan bazata saya ba sai dai su watsa ruwa kawai ta fara taba kudin. A hankali kudi suka fara samun gibi dole ta fara neman sana'a. Tashin farko ta saro zobo tunda ta tsira da firig dinta ta soma yin zobo da lamurje na saidawa. TV da bidiyo da duka kayan gadonta banda katifar da ta ajiye kusu suke kwana da yaran duka suma saidawa tayi don ta kara jari. Allah Ya dubi halin da suke ciki ya buda mata kasuwa tana ciniki sosai. Salame tana gefe kullum tana yawo tsakanin nan gidan nasu da wurin Ta Madina wadda da fari ta dauki fushi mai tsanani da ita sakamakon mutuwar aurenta. Har gida suka tura aka nemo Salisu ko zai maidata yace idan ta sami miji tayi aure shima auren zaiyi. Zaman gaba, bakinciki da hassada ta dauka tana yi da Mairama. Kayan dakinta Ta Madina ta sayar ne ana bin malamai domin karkato hankalin Salisu. Shiya janyo ita bata da komai gashi jiki ya saba da jindadi an manta wanki, shara da wanke-wanke. Wahalar gidansu a yanzu har tafi ta da tsanani ko don zawarci suke oho. Hankalin Mairama yana kan inganta rayuwar 'ya'yanta, na Salame yana kan me zata yi ta kere Mairama ko ta hanata cigaba. 'Ya'yanta musamman Radhiya sun tsole mata ido. Abu kadan ne zata yi ta kai mata hannu da duka amma Mairama bata taba tankawa ba. Lokuta da dama wurin Yadikko suke zama ko Hajjo idan 'yan mutumcin suna kusa. Wata rana ta gama zobonta da lamurje ta kukkulle a leda santana suna cikin wani katon baho a nan bakin famfon tsakar gidan inda take aikinta ta tashi ta tafi jawo ruwa a rijiya zata wanke wurin. Salame tana ta fakonta don dama ta gane yanayin aikin nata. Idan ta gama kullewa sai ta janyo ruwa ta wanke wurin sannan ta dauka ta kai firig dinta ta jera. Su kan wuni da wuta amma da wuya ta kwana. Tafasasshen ruwan zafi Salame ta taho dashi a bokiti tayi daurin kirji kamar mai niyar shiga wanka sai da tazo daidai bakin bahon da kayan Mairama suke ta sheka musu ruwan nan. Ledojin dole suka yi laushi sunyi tsamo tsamo babu dadin tabawa. Salati ta soma yi wai wucewa zata yi ta sirka ruwan wankanta don ta ga kamar famfon wurin yana diga an kawo ruwa. Mairama ci gaba tayi da diban ruwanta sai da ta ciko bokiti tana zuwa ta ajiye shi sannan ta cira hannu ta kwashe Salame da mari mai gigitarwa don tana kallon yadda komai ya faru. Ihu ta kurma gidan da suke neman abin gani kuwa aka fara fitowa bawa ido abinci. "Ni kika mara Mairama?" Rai a bace Mairama tace "ko zaki rama ne?" "Kan bala'i, billahillazi baki mari banza ba sai na rama" "Gaki ga kumatun Adda Salame. Na gaji da wannan abubuwan da kika tsira tun kafin muyi aure har yanzu ana abu daya. Kece dukan min yara, yada min habaici da bakaken maganganu duk akan me? Me na tsare miki?" "Dole kice haka mana tunda kin rabani da wanda nake so" Yadikko na jin haka ta kora yaran gabadaya tace su shiga dakinta. Hajjo ba kunya ta bisu don jin ba'asi. Salame kasa karasa bayanin tayi don tasan ita ce da jin kunya. Tabarmar kunya ta nade da hauka wai Mairama tana yi mata gani gani saboda ta fara rike kudi. Da daddare da Malamijo ya dawo Yadikko ta bashi shawarar ya raba musu daki mana. "Babu wadda ta bani ko asi domin ginin gidan saboda haka idan zasu cinye kawunansu ne ma su cinye bai dameni ba. Wadda taji haushi ta kawo miji tayi aure" "Idan bazaka rabasu ba ka taimaka ka zame musu uba na kwarai ka kawo karshen wannan rashin jituwa da yake tsakaninsu. Kafi kowa sanin cewa da ba haka suke ba" Shu'umar dariya yayi kafin ya turo hularsa gaba ya bata amsa "ki kan bani mamaki wani lokacin kamar baki san zafin zawarci ba. Kodayake baki taba danawa bane amma cuta ce mai zaman kanta. Shiyasa kika ga suna harin junansu. Babu mai tayar min hankali ni dai" Babu yadda ta iya haka ta tashi ta bar dakin nasa tana kara godewa Allah da bai bata haihuwa da Malamijo ba. Mairama ta gama yiwa Karami shirin bacci ta goya shi tana jiran kanwarta ta kawo Radhiya da take wasa a wurinsu Salame ta shigo ta dawo daga zance da dan gayun saurayinta. Matashi ne ko auren fari baiyi ba. Baje ledar da ya bata ta tsire tayi a gefen katifarta da burin cusawa Mairama haushi. Abin dariya yadda take ci tana shuu da baki. Tana ganin Radhiya ta sake bude ledar da kyau. Yarinya tace "Ummi nama" Mairama ta dauko wata leda babba ta mikawa Na'ima kanwarta tace suje su raba sannan ta dauko wata 'yar madaidaiciya ta bude ta janyo hannun Radhiya ta bata cinyar gasasshiyar kaza. Sai yanzu take gode Allah da haka nan ta bawa Bature kudi ya siyo kajin nan guda uku. Ta dauki daya ta basu biyu su raba. Ai kuwa Salame ta shaka har wuya ta shiga fadin maganganu wai gara su suna kwance ake basu. Wahalallu kuwa sai sunyi da karfin jikinsu kafin su dandani zakin nama. Shiru ma magana ce. Mairama bata ce mata komai ba haushi ya kamata tsiren ya fice mata a rai. "Dazu nace kin rabani da masoyina baki tambayi ko waye ba bare ki bani hakuri" "Indai Salisu ne nayi imanin bazai sakeki saboda ni ba. Allah kadai Yasan dalilin mutuwar aurenki sai kuma ku kanku" Kallon cikin ido ta yiwa kanwar tata "Mairama, na rigaki ganin Zayyan kuma na rigaki fara...." A harzuke Mairama ta tashi duk wani kulli na kanta yana kwancewa. Yanzun ta gama gano duk abubuwan da Salame tayi mata sunfi kama da kishi. Duk da mijin nata baya raye amma tana tsananin kishinsa itama. "Ya isheni ba sai kin karasa ba, na fahimci da aurenki kike son nawa mijin. Idan abinda Salisu ya gano ya sakeki kenan sai ince Allah Ya dada karawa." Daga haka bata koma cewa komai ba sai da ta tabbatar Salame tayi bacci ta sha kuka ta godewa Allah. Ta tabbatar Zayyan ya sani shiyasa shima baya son Salame saboda kada yaci amanarta. Sabuwar kewarsa ke ratsa duk wani sassa na jikinta tana inama yana nan tare da ita. *********** Shekararsu biyu a gida Salame tayi aure. Kafin auren Mairama ta tuna cewa Salisu abokin Hadir ne a lokacin ta kwantar da kai wurin sau uku tana tambayar Salame kwatancen gidansu Salisu. Ita kuma ganin ta matsu tasan ko meye yana da mahimmanci shiyasa taki fada. Gashi baya zuwa garin don idan za'a kawo mata Halifa aiko drebansa yake likkafa ta kara ci gaba. Bayan auren Salame ne Idris dan gidan Mal Kallamu abokin Malamijo ya sami aikin koyarwa a makarantar firamare ta gwamnati ta cikin Sumaila. Da yake suna shiri da Mairama kamar wasa ya gabatarwa Headmaster da ita akan ko 'yan aji daya ne ta samu ta rinka koyarwa. Shine ya amince aka yi mata cuku cuku sai gashi ta sami aikin a karkashin L.E.A. Kwalin karatun nata iyakarsa sakandire shiyasa bata wuce aji daya ba a koyarwar. Ita dai ko yaya ne hakan yayi mata don albashinta yana mata rana ga cinikin zobo da lamurje. Haihuwar Salame daya aurenta ya sake mutuwa. Wannan karon lalaci da rainawa miji ya janyo mijin ya saketa. Duk abinda zai kawo mata sai ta karba a wulakance tace ba haka baban Halifa yake yi ba. Sai da ta kaishi makurar da yayi mata duka ya sakota. To yanzu ma an sake dawowa gidan jiya. Dan da ta sake haifa shima babansa ya kaiwa yarsa. Ta dawo gida an sake komawa zaman zawarci ga rashin abinyi. Bakincikinta ya karu da yadda Mairama da yaranta suke rayuwa ta rufin asiri. Duka suna karatu a inda take koyarwa. Ta soma saka gilashi ne a lokacin da ta fara fama da matsanancin kaikayin ido da gani dishi-dishi. Ta sha wahalar idon sosai ta kuma kashe kudi. ********** Sun dawo gida da Emzee ya shiga dakunan duka matan gidan su hudu don tuni Malamijo ya sake cike gurbi. Yadikko tana nan a matsayin uwargida Hajjo kuma ta biyu sai amare Hanne da Binta. A gajiye take ta kwanta tana murna anyi hutu. Sallama taji anayi ana kwala mata kira ta tashi a zabure Salame tana kwalliya zata je wurin mamanta. "Uwar yarinyar nan Alhihi take ko me kace Danmama?" Danmama ya zumburo baki "Alheran amma Radhiya naji ana cewa. Ita ce ta mareni kuma Anti batayi komai ba saboda 'yarta ce" "Allah gamu gareka" Mairama tace a ranta kafin ta fita tsakar gidan zuwa wurin matar. "Hajiya kiyi hakuri rigima ce irin ta yara kuma tun a wurin an hukunta su" Rai a bace tana nuna bayan Danmama ta ce "a hukuncin ne aka yi masa bulala biyar ita kuma biyu saboda son kai. Dama wane adalci kuke yi idan kuna koyarwa a makarantun da 'ya'yanku suke. Daga yau sai yau ki jawa 'yarki kunne. Idan ta sake taba min yaro bazan yarda ba" Hakuri Mairama ta bata duk kunya ta isheta. Radhiya ba dai dauko magana ba. Idan anyi magana tace ita 'yar soja ce. Yadda take alfahari da aikin babanta sai ka rantse ta tashi tare dashi. Ko ina ta tsaya ma yanzu bata sani ba. Bari dai ta dawo yau mai rabasu sai Allah. Ashe gidan Mal Kallamu ta bi Uncle Idris. Can taci abincinta a bangaren amaryar Idris din sannan ta fito suka hadu da Malamijo a kofar shiga. Harararta yayi kamar ya kwadeta jiya taje gonarsa ta sami wani sabon maikaci da yayi ta nuna masa wata tinkiya wai Malamijo ne ya aiko ta fada masa a yanka ya dau kai da kafa. Ana cikin fida yazo ya gani jikinsa na tsuma yayo kanta tace gani tayi ta kasa. Kunnenta ya damko tana ihu " 'Yar kundun uba ta ina kika ga ta kasa din?" Ba yadda ya iya a dole jiya gidansa aka ci dafge kowa ya warwasa. Dakinsa ta bishi yana gwawiyar kashi tace "Malamijo ashe kaima kana son naman dai. Allah Yasa in ga wata ta kuma kasawa" da mafici ya biyota har yana tuntube. Ita ce a gaba ta hango Umminta da Danmama da mamansa. A guje tayi niyar komawa Malamijo ya riko wuyan rigarta ya kaita gabansu. "Mairama ki jawa 'yarki kunne idan ba haka ba wannan karon idan kunje hutun Sakkwato ki barta a can. Yarinya ce kamar aljana. Dubi kaninki nasa salihancin har haushi yake bani. Ke kadai kina mace kin tattaro duk halayen kiriniyar kin dorawa kanki" Kallon da ta ga Mairama na yi mata tasan yau jiki zai fada shiyasa tana tura baki da magana ciki-ciki tace "to ba shine yake wakar wai Malamijo tsolon rake ba, rama maka fa nayi" Jikin Malamijo da na uwar Danmama sai yayi sanyi. Danmama yayi wiki-wiki da idanu hakan ya tabbatar ba karya take ba. Babarsa kuwa ta talle masa keya tana cewa ya bashi hakuri. Yara kuwa sai dariya suke a hankali Malamijo yaji kunya ya shige daki. Kunnen Radhiya Mairama ta kama tace ta wuce daki. Da yamma ranar sai ga Alh Ado Indararo da kansa yazo bayan matarsa ta fada masa abinda Danmama yayi. Sun saba ciniki da Malamijo baya son kasuwar ta watse don yana dukan hancin Malamijo akan dabbobinsa sosai batare da shi ya sani ba. Ya bashi hakuri ya nemi Mairama itama ta fito da babban mayafi ta gaishe shi. Kallon farko Alh Indararo ya fada kogin kauna baya ji baya gani. Tana komawa ciki baiyi kasa a gwiwa ba ya fadawa Malamijo bukatarsa. Zani ce ta tadda muje mu. Shima kwadayin kudin Alhajin yake yace ya bar masa wuka da nama. A daren ya sanar da ita tayi tsalle ta dire tace bata da sauran aure a duniya. Sun fara rigimarsu bayan kwana biyu ta tattara ta tafi Sakkwato kamar yadda ta saba duk hutu suna zuwa suyi sati daya ko kwana goma. Duk gidajen 'yan uwan Zayyan na jini da makusanta irin su Mal Aminu sai taje. Kuma bata fasa zuwa barikinsu ba ko zata sami labarin Zainab da Mami. Gidan iyayen Zainab yanzu wasu ne a ciki. Ta matsu tasan halin da suke ciki amma babu dama. Haka kuma har yau babu wanda ya kirasu akan wani kudi na ihsani ga jaruman da suka rasu. Suna hira da matar Maikudi da Jume Maikudin ya shigo yana hade rai. Shi yafi kowa sanin babban dalilinsa na kin zuwansu garin amma bazai iya fadawa kowa ba. Yaran dama baya sakar musu fuska. Sai dai suna da kyakkyawar mu'amala da 'yan uwansu wato jikokin gidan. Satinsu daya suka juya Jume kamar a bar mata su. Babbar damuwarta shine rashin kowa daga bangaren Innar Zayyan wanda Jume tace har yau itama tana zuba idanu ne. Maikudi bai sami sukuni ba sai da suka bar garin. Sirrika biyu yake boyewa Mairama saboda mugunta da kuma son kai irin na dan Adam. Na farko dai wata shida da rasuwar Zayyan kawunsa Sidi yazo bisa shawarar 'yan uwa. Ashe ya tura musu wasika da zai tafi ta tasha. Sidi yazo gari Jume da matan gidan sun tafi Tureta biki. Maikudi kawai ya samu su Badaru basa gida. Lokacin yana tsaka da jin haushin rashin mutumcin Malamijo kuma yasan idan mutanen nan suka san da zamansu ba karamin alheri zasu rinka musu ba. Wanda zai koma jikin Malamijo a karshe. Saboda haka ya matso hawaye ya sanar dashi mutuwar Zayyan da kuma hatsarin da su Mairama suka yi ita da 'yarta suka rasu gabadaya. Wannan shine dalilin da yasa aka dena ji daga garesu. Abu na biyu kuma shine aike duk karshen wata daga kasar Germany wanda Retired Major Mustapha bai taba dena yi ba tun bayan samun lafiyarsa da aiki a can din kusan shekaru hudu. Kudi ne yake turowa ta hanyar wani soja da yake karkashinsa a da kuma ya yarda dashi. Wannan mutumi duk wata Maikudi yasan ranar da yake zuwa har barikinsu ya karbi kudin da suke mazaunin kudin makarantar Radhiya da kuma tallafi ga Mairama. Soke abinsa yake ga gidan Kano ya saka 'yan haya. A takaice dai yana ta gina kansa don ya sayi fili a cikin Sakkwato yana ta makara gini da kudin marayu. ********** Mairama ta koma ta tarar da babbar kura. Malamijo ya karbi sadakinta daga hannun Alh Indararo an saka biki wata uku kafin ya gama yi mata gyaran gida. Ta shiga matsanancin tashin hankali har Nene Marka tazo amma kowa cewa yake tayi auren ko zata sami hutu itama. Tayi kukan, tayi haukan duk a banza bata da mai tsaya mata. A bangare daya kuma duniyar Salame ta juye. Mutum kamar Alh Indararo ace yana son mace kakarta ta yanke saka. Shine wannan karon ma irin abinda take muradi ya tafi ga Mairama. Rantsuwa tayi cewa hakan bazata sake sabuwa ba. Gidan Malaminta da suka saba kashewa kudi domin a dawo mata da Salisu taje. Bayan dogon bugun kasa yace ta saka ranta a inuwa akwai rabo yana iya gani tsakaninta da Alh Indararo amma sai an kawar da Mairama. "Malam rufa min asiri kanwata ce fa. Ni dai bazan iya kasheta ba" Gemunsa na munafurci da suke cutar jama'a dashi ya ja yana murmushi "waye yace sai kin kasheta. Idan kina so nakasa kawai zamu dora mata wadda zata saka ya fasa." Kwana biyu tana tunani kafin ta hasko me take son ayiwa Mairama. Magani ya bata ta wuce gida ta saka a inda ya umarceta. Kwana uku a tsakani kuwa wata safiyar lahadi Mairama ta tashi bata gani sai dususu komai yayi hazo. Cikin maganin digawarta na ido Salame ta zuba mata maganin. Cikin wata guda idanun Mairama sai suna. Duk abinda ya rage mata ya kare a neman maganin ciwon idon amma asibiti basa ganin komai. Kuka ashe bai kare mata ba. Bata gane kowa sai duhun inuwa. Tashi guda Radhiya ta koma idanunta madogararta. Alh Indararo ya canja sheka bazai iya auran musaka ba Salame har ta tare abinta. Karatun yaran ya tsaya yau da gobe Malamijo ya gaji da dan mikawar da yake yi. A bisa dole ta hakura da karatun Radhiya da Emzee. Tana kuka kan kuka amma mahaifinta bazai iya kulawa da ita ba bare 'ya'ya, iyakarsa dasu shine za'a dafa abincin gidan dasu. Radhiya ta fara hankali tasan cewa mahaifiyarta tana bukatarta shiyasa bata fita idan ba aike ba. Emzee kuwa dama daddawar daka ne shiyasa bata hadu da matsalar ace suna yawace-yawace ba. Rayuwar Mairama matar soja ta cika da wahalhalun da suka sa take bukatar a dube ta. *********** Maza ne uku a karkashin bishiyar darbejiya wadda ta yiwa wurin yalwatacciyar inuwa. Daya yana zaune akan kujera sauran biyun kuma suna gabansa ne kana gani kasan mai mulki ne da wadanda yake mulka. Gyaran murya na kan kujerar yayi suka dawo da hankula gareshi "Mal Gide" "Ranka ya dade" wanda yafi manyanta cikinsu ya amsa. "Habubakari" "Allah Yaja zamaninka" na biyun ya amsa. Dan murmushi yayi domin kuwa su biyun yayun matarsa ne Innawuro. "Mal Gide kaine babba saboda haka ta kanka zan fara. Ba tare da jan zance ba magana ce akan sakacinku da zumunci saboda wani abu can da ya faru shekarun baya" Mal Gide ya hadiyi yawu yana kallon Habubakari shima kuma yayan nasa yake kallo. Ardo Barkindo ya dan duku da kansa kadan daga kan kujerar "wannan zumuncin da kuka banzatar ina mai tabbatar muku sai Allah Ya tambayeku akansa. Kune kuka ci bashi kamar yadda naji a bisa dole. Dole tasa kuka biya bashin da kanwarku sai gashi daga karshe ya sakota ya bukaci kudinsa ko. 'Yar uwarku ta sadaukar da farincikinta saboda ku amma shekaru sun tasanmu talatin marainiyar da ta bari baku san cinta ba baku san shanta ba" Habubakar wanda abin shima ya dame shi amma tsoron Gide ya hana shi furtawa ya sharce kwalla "Ardo zamu gyara, wallahi nima abin ya dameni. Ali bashi da kirki ko kadan. Allah ma yasa tana da rai yarinyar nan" "Yarinya da ranta amma tana cikin mawuyacin hali. Yanzu da na kiraku dama sanar daku zanyi cewa zan daukota ko dan kwanciyar hankalin Innawuro" Nan ya sanar dasu komai game da Mairama kamar yadda yaji daga bakin mijin Nene Marka bayan ya soma binciken nemota. Mal Gide sai hawaye. Bakar zuciya tasa ya umarci 'yan uwansa da babu su babu zuri'ar Malamijo, ciki kuwa harda 'ya daya tilo ga kanwarsa Mairo wadda ya yiwa auren dole da Malamijo. "Da kaina zanje in daukota da yaran su zauna a gidana Zan gyara wannan abu duka laifina ne" Ardo Barkindo ya kada kai yana murmushi "haba dai Gide ai bazamu yi haka da kai ba. Yarinya a wurin babarta zata zauna. Duk na gama wahalar neman sannan kace zaka daukota ka kwashe ladan" Murmushi ya maida masa "duk yadda kace ranka ya dade, kamar yaushe zamu tafi?" "Jibi in sha Allahu. Ina so ku tattaro kan 'ya'yanku har na gidan aure da suke rugar nan da kewaye maza da mata. So nake muje mu cika musu ido mu wanke gorin dangin uwa da na tabbatar ansha yi mata." Sun tashi da fara'a kowa yana jin kamar an sauke masa nauyi daga zuciya. Ardo Barkindo ya nisa yana tunanin ya boye musu makantar Mairama saboda yasan duka hankulansu zasu tashi. Idan sun je zasu ganewa idanunsu. Ko matarsa ya kasa fadawa ita da ta uzzura masa akan neman 'yar yayarta da take bi. Mal Gide kuwa har ya isa gida yana tunanin da yardar Allah zasu kula da ita bakin iyawarsu su daidaita tsohuwar baraka. Tunawa yayi da umarnin Ardo ya tura guda cikin 'ya'yansa da yaje ya fara sanar da yayyensa cewa suna da zuwa Kano jibi daga rugarsu wadda take cikin karamar hukumar Giade a jihar Bauchin Yakubu."Ahayye nanaye, wallahi mutum ya yi min ba kyalewa zanyi ba don kaji in gaya maka yaro" tafa hannuwa tayi sannan ta rike kugu tana girgiza jiki a dole ranta ne a bace. Abokin fadan nata wani sangamemen yaro ne don shima akwai kuruciya sai girman jiki. "An fada din" yace sannan ya cigaba da wakar da ta hadasu fada "Malamijo Malamijo tsolon rake. Ga kwadayi ga rowa yaki yin gaba" Wani kukan kura Radhiya tayi ta dire a gabansa ta nuna kasa "in ba tsoro ba dangwali" ta nuna masa kasar wurin. Dabi'arsu kenan 'yan makarantar wadda ta kasance firamare ta gwamnati idan ka yarda zaku dambace to kowa ya dangwali kasa. Daga nan sai a kaure karfinka ya kwace ka. Dukawa yayi zai dangwala ga tsirarun abokansu da basu bar makarantar da wuri ba sun tsaya kallo. Sai da ta daidaici yayi kasa da fuskar nan kawai ta dauke shi da mari ta ranta a na kare. Kai tsaye staffroom ta wuce inda malamai suke wurin Umminta. Tana shiga ta cukwikuye jikin Mairama tana kuka wai su Danmama ne suka dake ta. Tahowa suka yi Danmama ne a gaba kayansa duk kura saboda faduwar da yayi garin bin Radhiya. Kofar staffroom din taje ta saka su kneeldown har Radhiya sannan ta nemi jin ba'asi. Sai aka rasa me fada mata. Duk fitsarar Danmama yasan da kunya dai ya maimaita wakar a gabanta. Radhiya dama ko me zata yi mata bazata fada ba don kada ranta ya baci. Daga bayanta taji wani malami yace "Anti barni dasu kiyi tafiyarki gida. Idan na gama zanesu zan taho da wannan mai kunnen kashin" Mairama ta gyara zaman farin gilashinta tayi dan murmushinta da ta saba yanzu da wuya kake ganin bacin ranta ta koma ta dauko 'yan tarkacenta tayi hanyar fita daga makarantar don dama an riga an tashi. Daga karkashin wata katuwar bishiyar marke take hango yara suna 'yan wasanninsu. Idanunta suka sauka akan Emzee yana zaune yayi shiru yadda ya saba yana jiranta. "Karami zo mu tafi" tace da dan karfi don ta kula bai ganta ba sai gashi ya taso da saurinsa. Kayan hannunta zai karba tace ya barsu su tafi "Ummi ina Adda?" "Kyale wannan yau ma fada tayi" Sunyi gaba wasu 'yan ajinsu suka rinka kwalo masa kira suna Emzee sai an dawo hutu. Wannan suna da Mairama ta hakura da yakar sa dole shine sunan da yabi Muhammad Zayyan har gida. Mutane kalilan ke kiransa Zayyan ko Karami kamar yadda take fada. Yace wani malami da suka yi a firamare two ne yake kiransa MZ Tureta. Shikenan abu na yara ya koma Emzee. A makaranta kuma gurfane gaban Uncle Idris su Radhiya ne da Danmama. Sai da Mairama ta tafi Radhiya ta fada masa sunan da suke kiran kakanta dashi. Uncle Idris ya tabbatar zasu aikata yayi musu bulala biyar biyar mai zafi da dorinarsa ita kuma biyu ladan biye musu. A waje ta jira shi shima ya dauko kayansa tunda yau take ranar hutu suka tafi yana mata nasihar fada da maza. A cikin shekarun da suka gabata rayuwar Mairama sai dai godiyar Allah. Zamanta a gidan Malamijo tamkar zaman gidan haya ne. Iyakar gaskiyarsa shi nauyi ya masa yawa fitar da kudi kamar ana mintsininsa ne. Ya kara kudin cefane da kyar da sudin goshi amma daga nan fa ko me mutum ke bukata mace ko namiji cikin iyalinsa sai dai su nemawa kansu. Abu na farko da Mairama ta fara yi shine adana kudaden gadonsu a ranta tana tanadinsu ne domin karatun yaran a gaba. Sai da ta fuskanci sabulun wanka wannan idan bazata saya ba sai dai su watsa ruwa kawai ta fara taba kudin. A hankali kudi suka fara samun gibi dole ta fara neman sana'a. Tashin farko ta saro zobo tunda ta tsira da firig dinta ta soma yin zobo da lamurje na saidawa. TV da bidiyo da duka kayan gadonta banda katifar da ta ajiye kusu suke kwana da yaran duka suma saidawa tayi don ta kara jari. Allah Ya dubi halin da suke ciki ya buda mata kasuwa tana ciniki sosai. Salame tana gefe kullum tana yawo tsakanin nan gidan nasu da wurin Ta Madina wadda da fari ta dauki fushi mai tsanani da ita sakamakon mutuwar aurenta. Har gida suka tura aka nemo Salisu ko zai maidata yace idan ta sami miji tayi aure shima auren zaiyi. Zaman gaba, bakinciki da hassada ta dauka tana yi da Mairama. Kayan dakinta Ta Madina ta sayar ne ana bin malamai domin karkato hankalin Salisu. Shiya janyo ita bata da komai gashi jiki ya saba da jindadi an manta wanki, shara da wanke-wanke. Wahalar gidansu a yanzu har tafi ta da tsanani ko don zawarci suke oho. Hankalin Mairama yana kan inganta rayuwar 'ya'yanta, na Salame yana kan me zata yi ta kere Mairama ko ta hanata cigaba. 'Ya'yanta musamman Radhiya sun tsole mata ido. Abu kadan ne zata yi ta kai mata hannu da duka amma Mairama bata taba tankawa ba. Lokuta da dama wurin Yadikko suke zama ko Hajjo idan 'yan mutumcin suna kusa. Wata rana ta gama zobonta da lamurje ta kukkulle a leda santana suna cikin wani katon baho a nan bakin famfon tsakar gidan inda take aikinta ta tashi ta tafi jawo ruwa a rijiya zata wanke wurin. Salame tana ta fakonta don dama ta gane yanayin aikin nata. Idan ta gama kullewa sai ta janyo ruwa ta wanke wurin sannan ta dauka ta kai firig dinta ta jera. Su kan wuni da wuta amma da wuya ta kwana. Tafasasshen ruwan zafi Salame ta taho dashi a bokiti tayi daurin kirji kamar mai niyar shiga wanka sai da tazo daidai bakin bahon da kayan Mairama suke ta sheka musu ruwan nan. Ledojin dole suka yi laushi sunyi tsamo tsamo babu dadin tabawa. Salati ta soma yi wai wucewa zata yi ta sirka ruwan wankanta don ta ga kamar famfon wurin yana diga an kawo ruwa. Mairama ci gaba tayi da diban ruwanta sai da ta ciko bokiti tana zuwa ta ajiye shi sannan ta cira hannu ta kwashe Salame da mari mai gigitarwa don tana kallon yadda komai ya faru. Ihu ta kurma gidan da suke neman abin gani kuwa aka fara fitowa bawa ido abinci. "Ni kika mara Mairama?" Rai a bace Mairama tace "ko zaki rama ne?" "Kan bala'i, billahillazi baki mari banza ba sai na rama" "Gaki ga kumatun Adda Salame. Na gaji da wannan abubuwan da kika tsira tun kafin muyi aure har yanzu ana abu daya. Kece dukan min yara, yada min habaici da bakaken maganganu duk akan me? Me na tsare miki?" "Dole kice haka mana tunda kin rabani da wanda nake so" Yadikko na jin haka ta kora yaran gabadaya tace su shiga dakinta. Hajjo ba kunya ta bisu don jin ba'asi. Salame kasa karasa bayanin tayi don tasan ita ce da jin kunya. Tabarmar kunya ta nade da hauka wai Mairama tana yi mata gani gani saboda ta fara rike kudi. Da daddare da Malamijo ya dawo Yadikko ta bashi shawarar ya raba musu daki mana. "Babu wadda ta bani ko asi domin ginin gidan saboda haka idan zasu cinye kawunansu ne ma su cinye bai dameni ba. Wadda taji haushi ta kawo miji tayi aure" "Idan bazaka rabasu ba ka taimaka ka zame musu uba na kwarai ka kawo karshen wannan rashin jituwa da yake tsakaninsu. Kafi kowa sanin cewa da ba haka suke ba" Shu'umar dariya yayi kafin ya turo hularsa gaba ya bata amsa "ki kan bani mamaki wani lokacin kamar baki san zafin zawarci ba. Kodayake baki taba danawa bane amma cuta ce mai zaman kanta. Shiyasa kika ga suna harin junansu. Babu mai tayar min hankali ni dai" Babu yadda ta iya haka ta tashi ta bar dakin nasa tana kara godewa Allah da bai bata haihuwa da Malamijo ba. Mairama ta gama yiwa Karami shirin bacci ta goya shi tana jiran kanwarta ta kawo Radhiya da take wasa a wurinsu Salame ta shigo ta dawo daga zance da dan gayun saurayinta. Matashi ne ko auren fari baiyi ba. Baje ledar da ya bata ta tsire tayi a gefen katifarta da burin cusawa Mairama haushi. Abin dariya yadda take ci tana shuu da baki. Tana ganin Radhiya ta sake bude ledar da kyau. Yarinya tace "Ummi nama" Mairama ta dauko wata leda babba ta mikawa Na'ima kanwarta tace suje su raba sannan ta dauko wata 'yar madaidaiciya ta bude ta janyo hannun Radhiya ta bata cinyar gasasshiyar kaza. Sai yanzu take gode Allah da haka nan ta bawa Bature kudi ya siyo kajin nan guda uku. Ta dauki daya ta basu biyu su raba. Ai kuwa Salame ta shaka har wuya ta shiga fadin maganganu wai gara su suna kwance ake basu. Wahalallu kuwa sai sunyi da karfin jikinsu kafin su dandani zakin nama. Shiru ma magana ce. Mairama bata ce mata komai ba haushi ya kamata tsiren ya fice mata a rai. "Dazu nace kin rabani da masoyina baki tambayi ko waye ba bare ki bani hakuri" "Indai Salisu ne nayi imanin bazai sakeki saboda ni ba. Allah kadai Yasan dalilin mutuwar aurenki sai kuma ku kanku" Kallon cikin ido ta yiwa kanwar tata "Mairama, na rigaki ganin Zayyan kuma na rigaki fara...." A harzuke Mairama ta tashi duk wani kulli na kanta yana kwancewa. Yanzun ta gama gano duk abubuwan da Salame tayi mata sunfi kama da kishi. Duk da mijin nata baya raye amma tana tsananin kishinsa itama. "Ya isheni ba sai kin karasa ba, na fahimci da aurenki kike son nawa mijin. Idan abinda Salisu ya gano ya sakeki kenan sai ince Allah Ya dada karawa." Daga haka bata koma cewa komai ba sai da ta tabbatar Salame tayi bacci ta sha kuka ta godewa Allah. Ta tabbatar Zayyan ya sani shiyasa shima baya son Salame saboda kada yaci amanarta. Sabuwar kewarsa ke ratsa duk wani sassa na jikinta tana inama yana nan tare da ita. *********** Shekararsu biyu a gida Salame tayi aure. Kafin auren Mairama ta tuna cewa Salisu abokin Hadir ne a lokacin ta kwantar da kai wurin sau uku tana tambayar Salame kwatancen gidansu Salisu. Ita kuma ganin ta matsu tasan ko meye yana da mahimmanci shiyasa taki fada. Gashi baya zuwa garin don idan za'a kawo mata Halifa aiko drebansa yake likkafa ta kara ci gaba. Bayan auren Salame ne Idris dan gidan Mal Kallamu abokin Malamijo ya sami aikin koyarwa a makarantar firamare ta gwamnati ta cikin Sumaila. Da yake suna shiri da Mairama kamar wasa ya gabatarwa Headmaster da ita akan ko 'yan aji daya ne ta samu ta rinka koyarwa. Shine ya amince aka yi mata cuku cuku sai gashi ta sami aikin a karkashin L.E.A. Kwalin karatun nata iyakarsa sakandire shiyasa bata wuce aji daya ba a koyarwar. Ita dai ko yaya ne hakan yayi mata don albashinta yana mata rana ga cinikin zobo da lamurje. Haihuwar Salame daya aurenta ya sake mutuwa. Wannan karon lalaci da rainawa miji ya janyo mijin ya saketa. Duk abinda zai kawo mata sai ta karba a wulakance tace ba haka baban Halifa yake yi ba. Sai da ta kaishi makurar da yayi mata duka ya sakota. To yanzu ma an sake dawowa gidan jiya. Dan da ta sake haifa shima babansa ya kaiwa yarsa. Ta dawo gida an sake komawa zaman zawarci ga rashin abinyi. Bakincikinta ya karu da yadda Mairama da yaranta suke rayuwa ta rufin asiri. Duka suna karatu a inda take koyarwa. Ta soma saka gilashi ne a lokacin da ta fara fama da matsanancin kaikayin ido da gani dishi-dishi. Ta sha wahalar idon sosai ta kuma kashe kudi. ********** Sun dawo gida da Emzee ya shiga dakunan duka matan gidan su hudu don tuni Malamijo ya sake cike gurbi. Yadikko tana nan a matsayin uwargida Hajjo kuma ta biyu sai amare Hanne da Binta. A gajiye take ta kwanta tana murna anyi hutu. Sallama taji anayi ana kwala mata kira ta tashi a zabure Salame tana kwalliya zata je wurin mamanta. "Uwar yarinyar nan Alhihi take ko me kace Danmama?" Danmama ya zumburo baki "Alheran amma Radhiya naji ana cewa. Ita ce ta mareni kuma Anti batayi komai ba saboda 'yarta ce" "Allah gamu gareka" Mairama tace a ranta kafin ta fita tsakar gidan zuwa wurin matar. "Hajiya kiyi hakuri rigima ce irin ta yara kuma tun a wurin an hukunta su" Rai a bace tana nuna bayan Danmama ta ce "a hukuncin ne aka yi masa bulala biyar ita kuma biyu saboda son kai. Dama wane adalci kuke yi idan kuna koyarwa a makarantun da 'ya'yanku suke. Daga yau sai yau ki jawa 'yarki kunne. Idan ta sake taba min yaro bazan yarda ba" Hakuri Mairama ta bata duk kunya ta isheta. Radhiya ba dai dauko magana ba. Idan anyi magana tace ita 'yar soja ce. Yadda take alfahari da aikin babanta sai ka rantse ta tashi tare dashi. Ko ina ta tsaya ma yanzu bata sani ba. Bari dai ta dawo yau mai rabasu sai Allah. Ashe gidan Mal Kallamu ta bi Uncle Idris. Can taci abincinta a bangaren amaryar Idris din sannan ta fito suka hadu da Malamijo a kofar shiga. Harararta yayi kamar ya kwadeta jiya taje gonarsa ta sami wani sabon maikaci da yayi ta nuna masa wata tinkiya wai Malamijo ne ya aiko ta fada masa a yanka ya dau kai da kafa. Ana cikin fida yazo ya gani jikinsa na tsuma yayo kanta tace gani tayi ta kasa. Kunnenta ya damko tana ihu " 'Yar kundun uba ta ina kika ga ta kasa din?" Ba yadda ya iya a dole jiya gidansa aka ci dafge kowa ya warwasa. Dakinsa ta bishi yana gwawiyar kashi tace "Malamijo ashe kaima kana son naman dai. Allah Yasa in ga wata ta kuma kasawa" da mafici ya biyota har yana tuntube. Ita ce a gaba ta hango Umminta da Danmama da mamansa. A guje tayi niyar komawa Malamijo ya riko wuyan rigarta ya kaita gabansu. "Mairama ki jawa 'yarki kunne idan ba haka ba wannan karon idan kunje hutun Sakkwato ki barta a can. Yarinya ce kamar aljana. Dubi kaninki nasa salihancin har haushi yake bani. Ke kadai kina mace kin tattaro duk halayen kiriniyar kin dorawa kanki" Kallon da ta ga Mairama na yi mata tasan yau jiki zai fada shiyasa tana tura baki da magana ciki-ciki tace "to ba shine yake wakar wai Malamijo tsolon rake ba, rama maka fa nayi" Jikin Malamijo da na uwar Danmama sai yayi sanyi. Danmama yayi wiki-wiki da idanu hakan ya tabbatar ba karya take ba. Babarsa kuwa ta talle masa keya tana cewa ya bashi hakuri. Yara kuwa sai dariya suke a hankali Malamijo yaji kunya ya shige daki. Kunnen Radhiya Mairama ta kama tace ta wuce daki. Da yamma ranar sai ga Alh Ado Indararo da kansa yazo bayan matarsa ta fada masa abinda Danmama yayi. Sun saba ciniki da Malamijo baya son kasuwar ta watse don yana dukan hancin Malamijo akan dabbobinsa sosai batare da shi ya sani ba. Ya bashi hakuri ya nemi Mairama itama ta fito da babban mayafi ta gaishe shi. Kallon farko Alh Indararo ya fada kogin kauna baya ji baya gani. Tana komawa ciki baiyi kasa a gwiwa ba ya fadawa Malamijo bukatarsa. Zani ce ta tadda muje mu. Shima kwadayin kudin Alhajin yake yace ya bar masa wuka da nama. A daren ya sanar da ita tayi tsalle ta dire tace bata da sauran aure a duniya. Sun fara rigimarsu bayan kwana biyu ta tattara ta tafi Sakkwato kamar yadda ta saba duk hutu suna zuwa suyi sati daya ko kwana goma. Duk gidajen 'yan uwan Zayyan na jini da makusanta irin su Mal Aminu sai taje. Kuma bata fasa zuwa barikinsu ba ko zata sami labarin Zainab da Mami. Gidan iyayen Zainab yanzu wasu ne a ciki. Ta matsu tasan halin da suke ciki amma babu dama. Haka kuma har yau babu wanda ya kirasu akan wani kudi na ihsani ga jaruman da suka rasu. Suna hira da matar Maikudi da Jume Maikudin ya shigo yana hade rai. Shi yafi kowa sanin babban dalilinsa na kin zuwansu garin amma bazai iya fadawa kowa ba. Yaran dama baya sakar musu fuska. Sai dai suna da kyakkyawar mu'amala da 'yan uwansu wato jikokin gidan. Satinsu daya suka juya Jume kamar a bar mata su. Babbar damuwarta shine rashin kowa daga bangaren Innar Zayyan wanda Jume tace har yau itama tana zuba idanu ne. Maikudi bai sami sukuni ba sai da suka bar garin. Sirrika biyu yake boyewa Mairama saboda mugunta da kuma son kai irin na dan Adam. Na farko dai wata shida da rasuwar Zayyan kawunsa Sidi yazo bisa shawarar 'yan uwa. Ashe ya tura musu wasika da zai tafi ta tasha. Sidi yazo gari Jume da matan gidan sun tafi Tureta biki. Maikudi kawai ya samu su Badaru basa gida. Lokacin yana tsaka da jin haushin rashin mutumcin Malamijo kuma yasan idan mutanen nan suka san da zamansu ba karamin alheri zasu rinka musu ba. Wanda zai koma jikin Malamijo a karshe. Saboda haka ya matso hawaye ya sanar dashi mutuwar Zayyan da kuma hatsarin da su Mairama suka yi ita da 'yarta suka rasu gabadaya. Wannan shine dalilin da yasa aka dena ji daga garesu. Abu na biyu kuma shine aike duk karshen wata daga kasar Germany wanda Retired Major Mustapha bai taba dena yi ba tun bayan samun lafiyarsa da aiki a can din kusan shekaru hudu. Kudi ne yake turowa ta hanyar wani soja da yake karkashinsa a da kuma ya yarda dashi. Wannan mutumi duk wata Maikudi yasan ranar da yake zuwa har barikinsu ya karbi kudin da suke mazaunin kudin makarantar Radhiya da kuma tallafi ga Mairama. Soke abinsa yake ga gidan Kano ya saka 'yan haya. A takaice dai yana ta gina kansa don ya sayi fili a cikin Sakkwato yana ta makara gini da kudin marayu. ********** Mairama ta koma ta tarar da babbar kura. Malamijo ya karbi sadakinta daga hannun Alh Indararo an saka biki wata uku kafin ya gama yi mata gyaran gida. Ta shiga matsanancin tashin hankali har Nene Marka tazo amma kowa cewa yake tayi auren ko zata sami hutu itama. Tayi kukan, tayi haukan duk a banza bata da mai tsaya mata. A bangare daya kuma duniyar Salame ta juye. Mutum kamar Alh Indararo ace yana son mace kakarta ta yanke saka. Shine wannan karon ma irin abinda take muradi ya tafi ga Mairama. Rantsuwa tayi cewa hakan bazata sake sabuwa ba. Gidan Malaminta da suka saba kashewa kudi domin a dawo mata da Salisu taje. Bayan dogon bugun kasa yace ta saka ranta a inuwa akwai rabo yana iya gani tsakaninta da Alh Indararo amma sai an kawar da Mairama. "Malam rufa min asiri kanwata ce fa. Ni dai bazan iya kasheta ba" Gemunsa na munafurci da suke cutar jama'a dashi ya ja yana murmushi "waye yace sai kin kasheta. Idan kina so nakasa kawai zamu dora mata wadda zata saka ya fasa." Kwana biyu tana tunani kafin ta hasko me take son ayiwa Mairama. Magani ya bata ta wuce gida ta saka a inda ya umarceta. Kwana uku a tsakani kuwa wata safiyar lahadi Mairama ta tashi bata gani sai dususu komai yayi hazo. Cikin maganin digawarta na ido Salame ta zuba mata maganin. Cikin wata guda idanun Mairama sai suna. Duk abinda ya rage mata ya kare a neman maganin ciwon idon amma asibiti basa ganin komai. Kuka ashe bai kare mata ba. Bata gane kowa sai duhun inuwa. Tashi guda Radhiya ta koma idanunta madogararta. Alh Indararo ya canja sheka bazai iya auran musaka ba Salame har ta tare abinta. Karatun yaran ya tsaya yau da gobe Malamijo ya gaji da dan mikawar da yake yi. A bisa dole ta hakura da karatun Radhiya da Emzee. Tana kuka kan kuka amma mahaifinta bazai iya kulawa da ita ba bare 'ya'ya, iyakarsa dasu shine za'a dafa abincin gidan dasu. Radhiya ta fara hankali tasan cewa mahaifiyarta tana bukatarta shiyasa bata fita idan ba aike ba. Emzee kuwa dama daddawar daka ne shiyasa bata hadu da matsalar ace suna yawace-yawace ba. Rayuwar Mairama matar soja ta cika da wahalhalun da suka sa take bukatar a dube ta. *********** Maza ne uku a karkashin bishiyar darbejiya wadda ta yiwa wurin yalwatacciyar inuwa. Daya yana zaune akan kujera sauran biyun kuma suna gabansa ne kana gani kasan mai mulki ne da wadanda yake mulka. Gyaran murya na kan kujerar yayi suka dawo da hankula gareshi "Mal Gide" "Ranka ya dade" wanda yafi manyanta cikinsu ya amsa. "Habubakari" "Allah Yaja zamaninka" na biyun ya amsa. Dan murmushi yayi domin kuwa su biyun yayun matarsa ne Innawuro. "Mal Gide kaine babba saboda haka ta kanka zan fara. Ba tare da jan zance ba magana ce akan sakacinku da zumunci saboda wani abu can da ya faru shekarun baya" Mal Gide ya hadiyi yawu yana kallon Habubakari shima kuma yayan nasa yake kallo. Ardo Barkindo ya dan duku da kansa kadan daga kan kujerar "wannan zumuncin da kuka banzatar ina mai tabbatar muku sai Allah Ya tambayeku akansa. Kune kuka ci bashi kamar yadda naji a bisa dole. Dole tasa kuka biya bashin da kanwarku sai gashi daga karshe ya sakota ya bukaci kudinsa ko. 'Yar uwarku ta sadaukar da farincikinta saboda ku amma shekaru sun tasanmu talatin marainiyar da ta bari baku san cinta ba baku san shanta ba" Habubakar wanda abin shima ya dame shi amma tsoron Gide ya hana shi furtawa ya sharce kwalla "Ardo zamu gyara, wallahi nima abin ya dameni. Ali bashi da kirki ko kadan. Allah ma yasa tana da rai yarinyar nan" "Yarinya da ranta amma tana cikin mawuyacin hali. Yanzu da na kiraku dama sanar daku zanyi cewa zan daukota ko dan kwanciyar hankalin Innawuro" Nan ya sanar dasu komai game da Mairama kamar yadda yaji daga bakin mijin Nene Marka bayan ya soma binciken nemota. Mal Gide sai hawaye. Bakar zuciya tasa ya umarci 'yan uwansa da babu su babu zuri'ar Malamijo, ciki kuwa harda 'ya daya tilo ga kanwarsa Mairo wadda ya yiwa auren dole da Malamijo. "Da kaina zanje in daukota da yaran su zauna a gidana Zan gyara wannan abu duka laifina ne" Ardo Barkindo ya kada kai yana murmushi "haba dai Gide ai bazamu yi haka da kai ba. Yarinya a wurin babarta zata zauna. Duk na gama wahalar neman sannan kace zaka daukota ka kwashe ladan" Murmushi ya maida masa "duk yadda kace ranka ya dade, kamar yaushe zamu tafi?" "Jibi in sha Allahu. Ina so ku tattaro kan 'ya'yanku har na gidan aure da suke rugar nan da kewaye maza da mata. So nake muje mu cika musu ido mu wanke gorin dangin uwa da na tabbatar ansha yi mata." Sun tashi da fara'a kowa yana jin kamar an sauke masa nauyi daga zuciya. Ardo Barkindo ya nisa yana tunanin ya boye musu makantar Mairama saboda yasan duka hankulansu zasu tashi. Idan sun je zasu ganewa idanunsu. Ko matarsa ya kasa fadawa ita da ta uzzura masa akan neman 'yar yayarta da take bi. Mal Gide kuwa har ya isa gida yana tunanin da yardar Allah zasu kula da ita bakin iyawarsu su daidaita tsohuwar baraka. Tunawa yayi da umarnin Ardo ya tura guda cikin 'ya'yansa da yaje ya fara sanar da yayyensa cewa suna da zuwa Kano jibi daga rugarsu wadda take cikin karamar hukumar Giade a jihar Bauchin Yakubu. [02/11 7:29 AM] My 2nd Mtn: 18. WAIWAYE.... Zainab tayi kuka har ta gode Allah. Hadir dinta ne kwance baya iya motsa kowace gaba a jikinsa sannan baya iya magana. Idanunsa kadai ke aiki idan anyi magana kuma yana ji amma babu damar amsawa. Tun iyaye na rarrashinta har suka kyaleta ta koka ko zata ji sa'ida. Zuwansu Kano kenan aka kaisu tsohon dakinsa inda yake zaman jinya. A hankali ya bude idanunsa ya saukesu a kanta. Murmushi yayi wanda ya hado da zubar hawayensa. Sunanta yake kira amma babu mai jin sautin saboda baya iya motsa harshensa. A guje ta fita da ta ga ya tashi ta dauko Ibrahim yana wasansa a dakin kakarsa. Dakin ta koma dashi ta kama hannun Hadir ta hada da nasa. "Idan ni bazaka tabani ba ka tashi ka dauki danka. Don Allah...don Allah Hadir ko Ibrahim ne ka rike da kanka" Runtse idanunsa kawai yayi. Yaya zaiyi da iyalinsa? Allah ne gatan gidansu sai shi da guntun albashinsa. Shikenan rayuwarsa da tasu ta tsaya saboda lalurar da ta same shi? Ina Major Mustapha? Yayi rai ko shima ya rasu? Ina Mairama da Radhiya? Akwai amanar takardun kwafin gidansa a wurinsa. Ta yaya zai isa ga wannan mutane da yake tausayawa duk da halin da yake ciki. Kanwar Hadir ce ta jiyo Zainab tana surutai ita kadai tazo ta fitar da Ibrahim sannan ta fadawa mamansu halin da take ciki. Tun zuwansu ko ruwa bata sha ba sai kuka. Umman tasu taje har dakin tace mata ta taso ta ci abinci shima ta barshi ya huta. Kamar ba da ita take ba tana ta magana taki tashi sai cewa take ta koshi. Babansu Hadir aka kira shima yazo yace indai kuka zata rinka yi to ta fita daga dakin. Hannu ta dora a baki da sauri "na dena, wallahi na dena" tana magana hawayenta da na Hadir yana karuwa. Baban ya fita yana cewa Umma ta kyaleta dama sun sani dole tayi kuka. Bayan fitarsu hannunsa ta kama tana shafa kumatunta "Hadir kana ji na?" Jikakkun idanunsa ya kifta mata yana son yin murmushi "kin fiye rigima" yace a ransa. Shagwabar da ta saba yi masa take kokarin yi kuka yana cin karfinta "ka taimakeni ka tashi, kaga Ibrahim ya kara nauyi yanzu. Ni kadai kake so na rinka daukarsa? So kake ya buda min kirji irin naka?" Lumshe idanu yayi yana sauraronta tana ta yi masa magana. Can ya soma jin fitsari, ya rasa yadda zaiyi tun yana kokarin rikewa har ya saki a kan katifar kamar kodayaushe yanzu ya zamewa kannensa wani karin nauyi. Lura da danshin Zainab tayi ta mayar masa da hannunsa inda yake ta fita wurin Ummansa tana neman tsumma da ruwa. "Fitsari yayi ko?" Umman tace tana jin babu dadi. Murmushi Zainab tayi "eh Umma, yanzu zan gyara wurin" "Barshi Zainab ki huta kinji. Idan kannensa sun shigo sai su gyara. Yanzu zaki ga daya daga cikinsu. Sun san yanayin nasa shiyasa basa yin nisa ake barin guda a kusa" Kai ta dukar "danshi zai dame shi. Zan iya gyarawa" Bata jira cewarta ba ta koma dakin. Yana nan inda ta barshi sai kansa da ya juya yana kallon sama sabanin dazu da yake kallonta. Wani kululun bakinciki yaji ya rufe shi a lokacin. Ya gama wahala ya dawo da ransa amma ya zama kaya irin haka. Zainab dinsa abar tattalinsa ita ce haduwarsu ta farko bayan watanni zata kare a gyaran fitsari. Kuka zuci ya rinka yi har ta gama mirgina shi ta sauya masa kaya sannan ta cire zanin gadon ta shimfida zanin goyon Ibrahim a gefe inda ta ja shi ya kwanta. Zama ta kuma yi ta dora kansa a cinyarta "Hadir" Bude idanu ya sake yi sai ya ga ta duku da kanta ta sumbaci lebensa. Zuciyarsa tayi nauyi matuka. Ga matar da yake so take son shi amma ko yatsanta bazai iya rikewa ba. "Ka ga alamomi zamu fara koya yadda zan rinka ganewa idan kana bukatar wani abu" Ido ya kifta don ya nuna mata ya fahimceta. Ta gyara zama tana yawo da yatsunta a kansa "idan kana son abinci ko ruwa sai ka juya kanka barin dama. Idan kuma bandaki kake son zuwa sai ka juya hagu. Ni kuma sai ince abinci ko ruwa idan dama ne. Sai ka kifta ido sau data shine eh, sau biyu kuma a'a" Ta jima ko lokaci bata tunawa tace sai sun kwatanta. Ummansa da kanta ta dawo tace lallai tazo taci abinci. Ko da ta diba dakin nasa ta sulale ta koma taci. Shi sai su kunu ko koko ake bashi da ruwa. Asibitin da aka kaishi a Kano ne suka ce kada a bashi mai nauyi har sai ya soma sabawa da sabon yanayin jikinsa. Kudin da aka nema na gwaji da aikin da ake tunanin yi masa kuwa ko yana daukar albashi kila sai ya shekara biyar zai tara su. Aiki a lakarsa ta kashin baya ba karamin tsada bane dashi. Da daddare ko keyarta basu gani ba a ciki. Hadir ya sake matsuwa cikin daren tana rungume dashi tana bacci haka ya saki fitsarin nan ya bata musu jiki saboda bashi da damar tashinta. Tana tashi da asuba gyaran wurin ta soma yi sannan ta goge masa nasa jikin tayi masa alwala. Satinsu daya babanta ya koma. Zainab ita take yiwa Hadir komai banda zuwa bandaki saboda yayi mata nauyi. Wannan tana ganin yayi alamar take sanar da kaninsa. Wata guda suka yi a haka babu wani cigaba kullum yana nan a yadda yake sai ma hawan jini da ya kama shi saboda yawan tunani. A wata na uku mahaifanta suka dawo dubiya. A lokacin ne kuma baban Hadir a gabansa da Ummansa da iyayen Zainab ya bijiro da maganar kashe aure. Kofin kunun hannunta ne ya subuce bata sani ba kuma bata damu ba. "Kashe auren wa kenan?" Babanta ya tambaye shi. "Zainab da Hadir" Zubewa tayi a kasa ta fashe da kuka "Umma kuyi hakuri idan wani abu nayi zan gyara." "Ko daya Zainab. Wannan shawarar da wahala muka iya yanke ta. Zamanki da Hadir babu alfanu sai tarin wahala. Nasan kunyi mana halacci da kawaici amma in sha Allahu bazamu bari naku hakurin ya kare ba" Kuka sosai Zainab ta saka tana ji suna cigaba da maganar tana ta magiya. Shi kansa Hadir din hawaye yake fitarwa. Babansa ya sake bata hakuri "kina da kuruciyarki ta yaya zamu barki da mutumin da bazai iya yi miki komai ba sai zame miki nauyi. Abu na biyu Hadir ne karfinmu mu kanmu. Yana kwance yanzu mu ma rayuwar wahala take mana ta ina zamu ajiyeki? Yau da gobe sai Allah 'yata Zainab, watarana zaki bukaci fiye da Hadir amma aure yayi miki dabaibayi. Zaki so kulawa da kowacce mace take muradi a gidan aurenta. Sannan ko mu iyayensa zamu iya gajiyawa balle mata. Komai fa sai anyi masa hatta gyara kwanciya. Kudin aikinsa kuma bamu da yadda zamuyi mu taba hada rabinsa ma. Zuwana Sakkwato uku akan maganarsa sun ce babu kudi a barikin" Zainab daga gaban wannan take zuwa gaban wancan tana kuka tana roko akan su barta da mijinta. Kwarai ta basu tausayi amma basa son nuna son kansu da rashin dattako. Hadir sai rufe ido kawai yayi zuciyarsa tana kuna sai da yaji mahaifinsa ya kira sunansa. "Hadir, ina mai umartarka da ka sauwakewa Zainab kada mu zama masu daukan alhaki, ka amince" "Kada ka sakeni, don Allah ku barni da aurena" Zainab ta fada cikin tashin hankali. Kifta ido Hadir yayi babansa ya sake cewa " ka amince cewa kai Hadir ka yiwa Zainab matarka saki daya?" Wannan karon ma ido ya sake kiftawa yana zubar da hawaye. Zainab yaji ta fado a jikinsa ta kankame shi tana kuka bata san ma me take yi ba "Wallahi ban saku ba, babu inda zani" Mamanta da Umman Hadir kukan suke tayata saboda tausayi. "Zainab kiyi hakuri" "Ba fa zan je ko ina ba ai ba da bakinsa yayi sakin ba" Babanta gani yayi abin yana daukan lokaci an kasa rarrashinta ya tashi ya mareta. Ta rike kunci baban Hadir yana cewa don me zai mareta "yaya take so muyi mata ne? Duk wani bayani anyi amma da gangan taki ganewa. Ki tashi maza ki hada kayanki yau dinnan ma zamu koma" Karamin hauka Zainab tayi ranar har suka bar garin gashi ance ta bar Ibrahim saboda Hadir yaji saukin rabuwa da ita shima. Sau biyu tana guduwa Kano bayan sun koma sai da babanta yayi mata kaca kaca karshe ya yi mata aure. Lokacin Hadir ya kusa shekara biyu a kwance. Ranar da aka kaita a ranar ta nuna mijin da wuka tace ko ya saketa ko ta kashe shi ta kashe kanta. Bai tsaya bata lokaci ba yayi mata saki ukun da ta bukata. Iyayenta sunyi fushi sosai da ita ta koma wata iri ita kanta saboda tashin hankali. Sai da kyar ta samu suka hakura bayan an sake saka mata rana da wani ma'aikacin kamfanin man fetur a Port Harcourt. Wannan karon babanta yace idan ta sake kashe aurenta ko taje Kano bazai yafe mata ba. Mijin nata mutumin Sakkwato ne amma a can Port Harcourt din zasu zauna. Ba don taso ba akayi auren. Mutumin mai suna Musa Waziri yana matukar son Zainab shiyasa baya fushi da ita. Yana da kudi shi ya canjawa iyayenta gida ya samarwa yayyenta maza biyu aiki a branch din gidan mansu suka samu rangwame daga kangin talaucin da suke ciki. Ranar da ta tare tayi kuka kamar ranta zai fita. Gani take taci amanar Hadir shiyasa har shekaru suke tafiya tsakaninta da mijinta bata taba wata doguwar walwala ba. 'Ya'yansa 'yan mata biyu da ya rabu da mahaifiyarsu su kadai ne suke samun kulawarta. Wannan dalilin shi ya karawa Musa hakuri da ita da halinta na rashin son sa. Duka wani hakkinsa tana saukewa amma soyayya da fara'arta sai yayi watanni bai gani ba. Hadir yana nan kwance sai gashi da suka samu kaninsa yake kaishi idan yayi ciniki a kasuwa kudi sun samu. Gashin yana taimaka masa wurin jin dadin jikinsa saboda yawan kwanciya. Magana ce dai da wuya yake iya hada kalma daya kwakkwara. Ibrahim yana girma ya gane waye Hadir a wurinsa a hankali ya gudu daga cikin gidan ya koma dakin mahaifinsa. Sannu a hankali indai ba yana makaranta ba komai na Hadir ya dawo gareshi. Idan aka kaishi hutu wurin Zainab baya iya sati biyu ya rinka cewa Abbansa kenan dole a mayar dashi da wuri. A haka shekaru ke tafiya a haka rayuwar wannan iyalin ta wargaje gabadaya daga aikin soja. Miji ya koma kan wheelchair ga ciwon zuciya ya kama shi da gaske saboda yawan tunani. Uwa ta sake aure bisa dole amma zuciyarta tana ga tsohon mijinta sannan dansu ya taso a wata bahaguwar rayuwa bai san komai ba tunda ya fara wayo sai jinyar mahaifinsa. A bangaren Hadir rashin iya magana ya nemi iyalin Zayyan yana damunsa sai ya kwana yana kuka idan ya tuna rasuwar aminin da ya dauka tamkar dan uwa. A irin lokutan ciwonsa ke tashi a kasa gane kansa. Zainab ma bata taba mantawa dasu ba amma kunyar nemansu take yi a yanzu bayan shekaru sun ja ta dan dawo cikin nutsuwarta. Bata san Zayyan ya rasu ba haka nan bata sani ba ko shima ya dawo kamar Hadir. Mami kuwa sunan garinsu kadai ta sani ta ina zata fara nemanta. Babban abin dubawa shine komai na rayuwa duk yadda ka kai da matsuwa dashi sai Allah Ya nufeka da yinsa. Mukan kwadaitu da gabatar da wani abu mai girma a garemu amma sau tari sai wasu abubuwa suyi mana shamaki dasu. Yanayin rayuwa bai mantar da Zainab mutanen da suka yi zaman amana ba amma halin da ta tsinci kanta yasa damuwarta ta danne hangenta. Burinta daya ne a rayuwa...ta komawa Hadir! ********** "Ni na kashe shi...ni nayi ajalin Zayyan..ina zan saka kaina? Hassana na kashewa Alheran mahaifi. Meyasa nima ban mutu ba?" Kuka ne irin na mazan da suka ga tashin hankali muraran ba labari ba. Babban soja mai ji da jarumta shine yake zubar da hawaye kamar yaron goye. Farfadowarsa kenan daga allurar anasiziya da aka yi masa kafin a shiga dashi theatre. Tsahon sati biyu da kwanaki da yayi a asibitin Katsina kafin likitan da zaiyi masa aikin kafar yazo daga asibitin koyarwa na Zaria yayi su ne a cikin halin rashin sanin inda yake. Irin kukan da Mami tayi na fili da na zuci bazai fadu ba. Major Mustapha soja yayanta kuma uban 'ya'yanta shine wasu cikin masu zuwa dubiya suke kirawa hauka. Dole ace yana hauka don idan har zaka zauna dashi na minti biyar ido biyu surutan da zaka ji yana yi kwatakwata babu ma'ana ga wanda baya tare dasu a ranar da abin nan ya faru a dajin Liberia. Labari ne na yaki, tashin hankali da zubar jini. Tsananin ciwon da kafarsa take yi shine musabbabin fitarsa daga hayyacinsa har yake wadannan surutai. An tabbatar musu da cewa zafin ciwo ne kawai. Asibitin suna kokarin dressing din ciwon amma yadda tsutsa ke fita suna cin namansa daga ciki shi kadai yasan azabar da yake ciki. Dakin kansa wani irin wari yake yi don kannensu maza ke kwana dashi ma. An hana Mami kwana sai dai tazo ta wuni ta koma gida. Kudi sosai suka kashe akan ciwon nasa. To yau dai Allah Yayi likita yazo an yanke kafa dan abinda aka bari iya rabin cinyarsa ne. Sauran naman duk ya zagwanye saboda infection. Abinda yake fada ya tadawa Mami hankali. Cikin nutsuwa ta matsa kusa dashi tana tambayarsa me ya sami Zayyan din. "Ni ne dai nayi ajalinsa. Ashe duk mutuncin da yaron nan yake nuna min a dalilina zai rasa ransa. Ya ceci rayuwata ya rasa tasa. Me yasa nima ban mutu ba?" Mami ta shiga rudani aka sake kiran likita yace su kwantar da hankulansu allura bata gama sakinsa ba. Da kadan da kadan sai da suka kwashe wata uku cur a asibitin nan. Kafarsa ta hade wurin sai dungulmi amma ya gamu da wata sabuwar lalurar da basu ankara da ita da wuri ba wato septicemia. Infection ne na jini da yake samuwa daga infection a wani bangaren jiki sai kwayoyin cutar su gangara cikin jini. Da zazzafan zazzabi abin ya fara sai kuma yawan jin sanyi. Da fari magunguna da alluran malaria aka bashi. Yayi sati ana wannan babu wani chanji sai ma gaba da abin ya kara. Bugun zuciyarsa sai ya kara gudu har ana gani dagowar kirjinsa, dama ga muguwar rama da ya hada. Da likitocin suka ga babu sauki akace typoid ce. Nan ma duk wasu allurai da magunguna sai da ya karar dasu. Hankula sun kara tashi ne ranar da zuciyarsa ta nemi bugawa shine fa aka rinka gwaje gwaje baji ba gani. Jininsa har asibitocin koyarwa na Zaria, Kano da Ibadan an tura domin gano abinda yake damunsa. Rashin wadatar kayan aiki a asibitocin kasarmu ya janyo Major Mustapha ya kusa rasa rayuwarsa. Da kyar aka gano a asibitin Ibadan aka turo musu sakamakon. Sai a lokacin aka fara treatment bayan infection din yaci jininsa sosai har ya fara harin kayan cikinsa. Da aka sallamo shi haka ya dawo gida kamar mutum mutumi. Yau da lafiya gobe babu. Ya rage surutai sai ma rashin son magana da kebewa daga mutane. Idan ya kalli kafarsa sai yaji ya tsani rayuwa gabadaya. Da bai rasata ba Zayyan bazai dawo daukarsa ba. Da sai su gudu tare su tsira tare. Yayi shekara a kwance. An sayar da motarsa da filinsa na nan Katsina duk a siyan magunguna masu tsada domin samun lafiyarsa. Wata rana Mami tayi masa zancen su Mairama sai kawai ya saka mata kuka. Taya shi tayi don gabadaya mijin nata yanzu tamkar bashi ba. "Da wane ido zan kalleta Hassana? Ko kinsan cewa da don ta ni ne wallahi na gwammace na kare rayuwa a Liberia da na dawo gida na fuskanci matar Zayyan. Na zama silar da bomb ya tarwatsa mata miji shine abinda kike so kiji na fada mata idan ta tambayeni ta yaya mijinta ya rasa ransa?" "Kayi hakuri Daddy ba manufata ba kenan. Kasan ya barta da ciki ga Radhiya" Kai ya girgiza "baki san nauyin da zuciyata take ciki bane da kin kyaleni. I feel guilty and I hate myself and.... my life. Idan zaki je nayi miki izini" Tasowa tayi ta rungume shi tana hawaye "nima me zance mata?" "Ban sani ba..." yace da raunin zuciya yana kara kankameta. Kwanaki kadan da yin wannan magana wata rana da daddare suna kwance ta tuna Fauziyya ta kwanta bata yi fitsari ba. A gidansu Major din aka basu wani bangare dakuna biyu masu fuskantar juna. Awwab a wurin samari yake kwana har an mayar dasu makaranta. Ta je ta kai Fauziyya tayi fitsari ta dawo da sanda saboda kada ta tashe shi. Amma duk da haka sai da ya farka. Inuwarta ya gani ta tuna masa da lokacin da 'yan tawayen nan suka rinka fitowa ta baya da saman bishiyoyi suna harbinsu. Baiyi wata wata ba ya mirgina jikinsa ya damkota. A daidai wannan lokacin jinsa yake kamar a wancan lokacin. Kunnuwansa suna jiyo masa sautin harbi da hayaniya tartar. Wata muguwar shaka ya kaiwa Mami ya sakar mata karfi. "Captain na kama daya kuzo ku daure shi mu tafi dashi base dinmu" yace da dan karfi. Mami sai kokawa take tana son yi masa magana ta kasa saboda wuyanta da ya shake tana numfashi sama sama. A daidai kunnenta yace "Who sent you?" Wahala ta fara yawa Mami duhu duhu take gani. Da kyar ta samu ta juya ta saka duka karfinta ta galla masa cizo a kirji. Gashin kanta ya damko da karfi ta saki kara. Daga hannu yayi ya kwada mata mari ta sake yin wata karar. Zai kuma marinta haske ya mamaye dakin. Mahaifiyarsa ce ta shigo tare da kaninsa da suka ji ihun Mami. Tana zuwa itama hannu ta cire ta mare shi. "Kasheta kake son yi ne Mustapha? Sakar mata gashi" Tamkar wanda ya tashi daga bacci sai lokacin ya kula da hannunsa da inda hannunsa yake yayi saurin sakinta. A guje ta tashi ta fada jikin Innarsa tana kuka. Wuyanta Innar ta lura dashi saboda farar fata yayi jawur. "Na shiga uku ni Fatima me zan gani? Ba dai shaketa kayi ba?" Kansa yaji ya daure wai me yake yi a dakin nan shi da suke tare da su Zayyan a daji. Firgici da tsoro ya kama shi ya soma yunkurin sauka daga kan gadon. Innarsa ta dakatar dashi. "Kada ka soma matsowa inda muke wallahi." Ta kalli kaninsa "rufe min shi da safe sai a fadawa Alh Baba kafin babanku ya dawo" Washegari zama na musamman akayi akan abinda ya faru a daren. Mahaifiyar Mami ta shafawa idonta toka tace 'yarta ko dai ta koma gida ko kuma a raba musu daki bazata yarda a kasheta ba. Ko wace ma hakan zata yi shiyasa aka tattara Mami da yaranta ta kuma gidan iyayenta. Major Mustapha kuma ya shiga wani sabon mawuyacin mataki a rayuwarsa. Iyaye duka sun hadu akan cewa gamo yayi a dajin nan aka shiga banka masa magungunan gargajiya, hayaki da rubutu. Kowa yaji labarin maganin aljanu cikinsu zai bada kudi domin a kawo su gwada. Idan ka ganshi dole ka koka in kasan waye Major Mustapha. Ya rame ya kare sai kashi da tashin hankali. Kuma abu kadan yake tayar masa da wannan abu ya fada cikin dogon tunani yana ganin kamar yanzu abin yake faruwa. Awwab shine mai zama dashi sosai kafin watarana shima ya shigo daki ya nemi Daddyn nasu ya rasa. Ya zauna jiran ko yana bandaki amma shiru. Haka akayi ta neman Major hankalin kowa a tashe. Mami taci kuka ta more. Sai can kamar ance Awwab ya duka ya ganshi a karkashin gado yana ta rarraba idanu. "Mami gashi nan" "Shhhh zasu ganmu." Mami ta dake ta duka itama "su waye zasu ganmu Daddy?" " 'Yan tawayen mana" Kasa magana tayi ta tashi ta koma dakin Innarsa tana kuka. Har yaushe zasu kare rayuwarsu a wannan yanayi? Dama haka ake auren sojan ko kuwa kaddararsu ce haka? Sauki babu sai daga Allah. A wannan yanayin Gambonsu Mami da mijinta Harun da a wurin Alh Baba suka zo daga Germany inda yake aiki a gidan rediyo a matsayin mai labarai. Sunyi bakincikin yadda rayuwa ta mayar da 'yan uwansu shine Harun ya shiga newarwa Major da Mami visar tafiya. A cewarsa zai kai dan uwansa asibiti ne tunda babu wani cigaba a gida. Iyayensu dai sun kyaleshi ne amma a iya tunaninsu asarar kudi zaiyi. Abu na Allah sun tafi Germany a shekara ta uku bayan rasuwar Zayyan. A can ne bincike ya nuna Major yana fama da Post Traumatic Stress Disorder (PTSD). Lalura ce ta kwakwalwa da a lokacin ba'a waye da ita sosai a bangarenmu na Africa ba. PTSD tana samuwa ne ga mutanen da suka yi gamo da mummunan yanayi ko al'amari kuma tana tashi ne idan suka samu kansu a yanayin da zai iya tuna musu da wannan abu. Yawan mafarkin da yake yi da kuma ji ko ganin kamar yanzu abin yake faruwa duka alamominta ne. Mami tambaya take ba haukacewa yayi ba aka ce mata ba hauka bane sai dai masu ita suna bukatar tsantsar kulawa daga makusantansu don idan abu yayi yawa wasu har kashe kansu suke yi. A gidan Gambo suka zauna har zuwa lokacin da ya fara jin sauki. Mami ta jajirce sosai wurin kula dashi. Daga baya ta fara tunanin kada su zame musu nauyi tace Harun ya nema mata aiki. To aiki a wata kasar ba'a samunsa kai tsaye. Ta bukaci ko yaya tana son neman kudi kafin su koma saboda kusan karkaf sunyi. Komai nashi ya kare an fara shiga aljihun dangi. Aikin nanny ya samar mata har yana tsoron fada mata sai ta basu mamaki wurin karbar aikin hannu bibbiyu. Gidan wasu 'yan kasa take zuwa daga bakwai na safe zuwa bakwai na yamma. Tayi su shara, wankin toilet da sauran ayyukan gida hade da raino. Mutane da dama suna zaton da ance ka fita waje watayawa kake. Aikatuwa take bilhakki mijinta yana kukan nakasa a gefe. A hankali masu gidan suka yaba da kwazonta sai aka basu wani dan bangare karami a gidan. Cikin shekarsu ta biyu Harun yaje gida abinda ta hada ta bayar aka dauko musu 'ya'yansu sauran kuma ta aika Sakkwato wurin sojan da Major ya rubutawa sako cewa a bawa su Mairama. Shekara guda cif cikin kudin aikin Mami ake dibarwa Mairama. Sako ya riskesu daga karyar Maikudi cewa tayi aure sannan dan cikinta baizo da rai ba. Hoton Alheran Radhiya kuwa da suka bukata cikin dakin Jume ya dauko wani da aka yi musu da yaransu gidan wani zuwansu da sallah. Murna sosai ranar da suka amshi hoton. Cikin ikon Allah sai ga Mami da ciki. Allah Ya bata 'ya mace Major ya saka mata suna Zayyanatu. Dariya tayi da taji sunan yace idan haihuwa goma zata sake Zayyan da Zayyanatu zaiyi ta saka musu. A yanzu Major ya sami aiki a wani kamfani shima sannan Awwab ya sami scholarship saboda kwazonsa a makaranta. Harun da Gambo sun koma Nigeria da 'ya'yansu uku Ghazalatu, Hafsa da Imam. Su Mami kuwa zaman jiran kammaluwar karatun Awwab suke su koma su ma. Sun sami rufin asiri daidai gwargwado kuma sai Major yayi watanni lalurarsa bata tashi ba sai anyi zancen Nigeria ranar zai kwana hankali a tashe yana tuna aikin da ya yiwa kasarsa ya kaishi ga wannan rayuwa ********** HADUWAR ALKHAIRI [02/11 7:30 AM] My 2nd Mtn: 19. Max, Anna da Liam sune 'ya'yan da suka tashi a hannun Mami. Suna ganin shigowarsu lawn din suka taho suna murna. Idanun Anna jazur taci kuka tun safe take abu daya. Rungume Mami tayi "bana so ki tafi Naanaa" tace cikin yaren jamusanci. Da yaren Mami ta maida mata "kiyi hakuri Anna, watarana zan zo ziyara ko ke kizo mana Nigeria ko" "Zaki zo aurena next year?" "In sha Allah" Hawaye Anna take ta rinka sumbatar kumatun Mami ita kuwa sai dariya. Liam da Max hannuwanta suka rike suka kaita tsakiyar wurin suna nunawa jama'a Naanaa dinsu. Mai aiki ce amma wadda take a inda aka san darajar masu aiki har masu gida suke karrama su. Ta sami kyaututtuka da yawa daga abokan aikinta da abokan arziki. Frau Marie Schmidt ta kawo envelop da kudi a ciki ta bata sannan ta bawa Fauziyya da Zahra wasu setin dankunne da sarka 'yan ubansu wai su saka da bikinsu. Zayyana ma an bata katon teddy kusan kansu daya. Tana ta murna Mami a ranta tayi dariya kawai. 'Yan kasarmu ina muka wani san darajar teddy. Hotunan tarihi suke dauka Major ya daga waya yana fadin inda suke. Ko minti biyu ba'ayi ba sai ga matashin saurayi kyakkyawa wankan tarwada mai cike da kwarjini da haiba ya shigo wurin sanye da uniform dinsa na matukin jirgin KLM mallakar kasar Germany. Jacket da wando ne navy blue sai farar shirt a ciki kansa sanye da hula irin ta Captain din jirgi. Mata hudu ne a gefensa hagu da dama air hostess kowacce da uniform riga da skirt sky blue suna rike da flowers masu kyau. Shigowar tasu ta kayatar da mutanen wurin bare iyayensa. Yana shigowa kai tsaye wurin Major ya nufa ya rungume shi. Mami ta saki baki sai kuma ta daure fuska cikin wasa. "Awwab, yau din ma?" Sai da yayi mata dariya sannan ya rungume Maminsa a kunnenta yana cewa "sorry Mamina" 'Yan matan da suke abokan aikinsa kowacce ta mika mata flower da dan gift suna mata fatan alkhairi. Awwab ya fiddo tickets biyar daga aljihun sa ya mikawa Major. "Daddy ga nawa gift din...Captain M.A Mustapha shine zai ja jirginku zuwa birnin Abuja. Sai da na duba schedule dina na sayi ticket. Tafiya ta dawo nan da sati biyu. I hope it is okay" Zayyana tayi tsalle ta dane shi tana ihun murna. Mami sai murmushi kawai na jindadi. Major kuwa tsokanarsa yake yi wai bazai shiga ba kada ya zubar dasu a teku. An gama party lafiya suka koma gida tare dashi. Shirye shirye ya kankama inda suka hada ya nasu ya nasu sai gida Nigeria. *********** Iyayen Zainab sun sakata a gaba kowa da abinda yake cewa tun da ta sanar musu cewa a yiwa iyayen Hadir magana akan aurensu. "Wai shin idan kin koma soyayya zaki rinka zuba muku a kwano kuna ci? Ke ba aiki shi a zaune. Ni har yau ban gamsu da ba ke kika kashewa kanki aure ba" mamanta tace a hasale. Babanta ne ma mai dan sauki a gareta "Zainab nasan kila ko a wurin Ibrahim kina ji cewa jikin Hadir babu wani sauki sai na musulunci. Kinje kin shafe shekaru tare da Musa kin saba da jindadi. Ta ina zaki koma gidansu?" "Baba na fada muku ya bani gida a Kano sannan ya kara min jari akan wanda ya bani tun da nake zuwa Dubai saro kaya dashi. Alhamdulillah Allah Ya wadatani Abbansu Aisha ne sila. Ni zan cigaba da tafiya kasuwancina ne Ibrahim ya rinka kula dashi idan bana nan" Mamanta ta kara kulewa "sannu uwar tsari, waro har kin gama tsara yadda komai zai kasance" Allah Ya sani tana son iyayenta kuma tana girmama su. Amma wannan karon tana jin tayi girman da ya kamata a karbi uzurinta idan tazo dashi. "Idan ba kwa so na komawa Hadir bazan koma ba. Amma wallahi bazan kara aure ba har na mutu" Tsam ta tashi daga dakin Baban nata. Sun san Zainab da taurin kai. Anyi sa'a ma zamanta da Musa Allah Yayi da tsayin kwana. Tufka suke da warwara suna guje mata matsala a gaba. Karshe mahaifinta yace su barta Allah kadai Yasan dalilin wannan soyayya da take yi masa. Bayan kwanaki ana muhawara da 'yan uwa babanta da kansa yaje Kano da dan uwansa ya gabatarwa Baban Hadir bukatarsu. Sunyi matukar mamaki ace har yanzu Zainab tana son dansu. Matar da sun sani yanzu ita dashi kamar wutsiyar rakumi ne da kasa. Daga irin suturun da take yiwa Ibrahim da abubuwan zamani da take wadata shi dasu zaka san Haj Zainab take don tayi Hajji da Umara albarkacin Musa. "Idan na fadawa Hadir bazai yarda ya aureta ba saboda lalurarsa" Babansa ya amsa musu a sanyaye. Hadir ya riga ya karbi kaddarar rayuwarsa. "Sai kayi shiru mu kulla abinmu a tsakaninmu ba shikenan ba" Kawun Zainab ya bashi amsa. Da izinin Allah a ranar basu tashi ba sai da aka mayar da auren Zainab jaruma mai sadaukarwa da Hadir jarumin kasata da kasar ta dade da mantawa dashi. Da aka kirata da wannan kyakkyawan labari tayi kukan farinciki sosai. Sati daya aka diba tariya inda Baba ya sa Ibrahim ya kwashe kayan sawarsu ya rinka maidawa gidanta da yake Janbulo. Hadir yana kallo bai iya tambaya sai ya sawa ransa ko gyara za'ayi a dakin. ********** "Wayyo Innawuro, kiyi min rai....Ummiiiii ki ceceni" Ihun Radhiya kenan da ya karade gidan tana zaune Emzee ya danneta Innawuro zata yi mata aski. Mairama hakuri take bata akan ta bari ayi "idan ba'a magance kwarkwatar nan ba wallahi duka sai kin shafa mana. Har na gama makarantar kwana ni banyi ba. Ku baku iya kula da kanku sai kazanta da gayun banza" Kyabe fuska ta sake yi hankalinta yana kara tashi "zan wanke Ummi harda karkashi in gumbuda musu gishiri Yasin duk su mutu" "Innawuro ko za'a bari ta gwada saka karkashin?" Mairama tace a hankali tana jin kunyar shigarwa 'yarta. "Kyaleta Mairama don baki ga kan bane. Makero ya cinye keyar sai gashi kadan, gaban kuma amosani da kwarkwata. Yarinya mai cikar gashi da laushi duk ya lalace saboda rashin kula. Na fada miki Mairo ta biyo a cikar nan zai tofo da wuri" "Ayya Ummi ki tausaya min mana" tace a wahale. Emzee ya sake sakar mata nauyinsa akan cinyarta da ya dora kafafunsa yana dariya. "Mugu daga ni" Sake danneta yayi tayi kara Mairama ta kasa hakuri "Karami ka kiyayeni fa, me kake mata ne?" Innawuro ya kalla suka sa dariya wai ta tarewa abokiyar fadanta sai ta kama bakinta ta kunshe. Radhiya na ganin gashinta ya soma zuba ta soma wani sabon kukan "kiyiwa Allah da ManzonSa Innawuro ki bar min na zaman falo. Kina ji fa Baffa Gide yace duk aurar damu zaiyi" Wannan karon dariya harda Mairama "wanne ne na zaman falo kuma?" "Wanda zan rinka daurewa da ribbon inyi kwalliya" Innawuro da Emzee suka cigaba da tunzurata tana ta zuba ana kwashe gashin "ance miki aure za'ayi miki ne kike neman gashin zaman falo?" "Aure kuma Innawuro ai kamar habo ne. Yanzu idan kika kwashe gashin nan miji yazo yay...." shiru tayi da ta ji ana kankarar kan nata da reza. Wani uban ihu ta saka an gama askin Innawuro tana mata kwaryar molo na gasken da reza ana kwashe sauran gashin da fatar da makero ya gama cinyewa tayi wani fari da tudu-tudu. "Wayyo Allahna na shiga uku na lalace, wayyo, wayyo, wayyo" Mairamu maficin hannunta ta daga zata kwada mata "wane irin sakarci ne wannan kike mana ihu kamar wata mara hankali" Sai da ta tashi ta makawa Emzee harara da daradaran idanunta sannan tayi gaba tana cewa "dama Ummi wane hankali ne zaiyi saura akan budurwar da bata da gashi ai sai gyaran Allah" Baki ta rike tana kada kai "anya yarinyar nan ba dabanci ta koyo a bodin din ba?" "Ummi gang garesu fa na fitinannu inji wata kanwar abokina" Daga cikin daki tana kuka ta leko "almunafunfun me ya kaika makarantar mata har ka jiyo gulma. Ummi ta sani dai SS ne ba wata kungiya ba" Tsawa Mairama tayi mata akan ta dena amfani da kalmomi irin wadannan ga kaninta. Innawuro tace "kema kinsan yau tunda da amincewarki akayi askin nan to dukkanmu sai ta nuna mana fushi take yi. Kai Karami zuba gashin nan a leda kaje ka kona. Kwarkwata harda ta sayarwa." Hannuwansa yayi saurin nadewa a kirji cike da kyama "kwarkwatar zan taba? Ashe kowa zaiyi susa a gidan nan" Dama Umminsa yake son tsokana ta fara fada yana dariya ya kwashe yaje bakin murhu ya zazzage. Waje yayi bayan ya wanke hannunsa aka bar su Mairama su kadai a tsakar gidan. Tayi zurfi a tunani da kwadayin ina ma ace zata iya ganin kamanin yaran a yanzu da suka kara girma. Alheran da Zayyan dinta suna da shekaru sha takwas da sha bakwai. "Radhiya kyakkywa ce kamar wata dan daren goma sha hudu, Karami kuwa yadda kika san sojan maigidanki ba maraba sai haskenki da ya dauko" Murmushi Mairama tayi kunya na kamata "Innawuro me ya kawo wannan bayanin kuma?" "Daga yin abin arziki, godiya kawai zaki yi tunda na faranta miki" Karamar dariya tayi ta lalubi sandarta ta tashi. Yanzu ta gane hanyar dakunan gidan ko babu dan jagora. Nasu ta karasa tana mitar wane irin jan kunne zata yiwa Alheran mai tambotsai. Kwanansu hudu tun washegarin dawowarta daga makaranta wai a saya mata form din makarantar sojoji. Tun Mairama na daukar abin wasa sai ga zance har kunnen su Ardo. Shine aka fara zancen aurar dasu. Ita kuma tana da burin Radhiya tayi ilimi mai zurfi amma bazata iya watsa musu kasa a ido ba. Tunawa da tayi anyi aski yau gidan kowa mai laifi ne a wurin 'Yar soja ya saka ta dariya ba shiri. ********** Hadir sai tunani yake yi ina zasu je bayan masallaci maimakon su wuce gida. A motar kaninsa da yake kaisu sallar juma'a suke tare da Ibrahim. Yau sababbin kaya Ibrahim din ya saka masa iri daya da nasa, yadi ne mai kyau da laushi ruwan kwanduwar kwai anyi musu dinki iri daya wanda akayi da zare coffee color. Hatta hulunansu iri daya ne masu kalar zaren dinkin. Sai kamshi suke bazawa sunyi wani irin kyau. Tarin tambayoyi fal a zuciyar Hadir tun da aka fara komai. Mai aski har gida Ibrahim ya kawo yasa yayi masa gyaran fuska sabanin da da yake masa a gida da clipper da Zainab ta siyo masa. Sun taimaka sun dora shi akan kujerarsa wheelchair bayan sun shiga gidan. Daga gefen matattakalar shiga anyi shafen sumunti alamun hanya ta hawa da wheelchair din. Gangara babansa yayi cikin ni'imtaccen falon da ya wadatu da sanyin AC da kamshi. Daga nan kanin Hadir yayi musu sallama ya juya abinsa. Idanunsa na nuni da tashin hankali sai waige yake yi Ibrahim ya barshi ya nufi bakin wasu steps hudu da za'a taka abi hanyar dakuna. Su ma a gefe akwai wurin tura kujerar. Wai kunya ce ta hana Zainab fitowa tana jinsu ta makale a daki. Ibrahim na taba kofar ta taso da wayoyinta a hannu kamar fitowa dama zata yi. Wani kayataccen murmushi yayi mata na jindadi "Mama kinyi kyau wallahi" Irin yadin jikinsu ta saka. Hatta zaren dinkin iri daya ne nata doguwar riga anyi mata surfani siriri mai kyau adon. Daurinta shima yayi kyau ga sarkar gwal dasu awarwaro. Haj Zainab kenan mata a gidan Hadir. Murmushi tayi sai kuma tace "Wuce muje ni" "Fara zuwa Mama naji cikina yana juya min" Bai jira ta amsa ba ya fita da sauri ya shige sabon dakinsa ya dire akan gado yana murna. Abokinsa ne ya bashi shawarar kada ya tsaya musu a ka ya barsu su kadai. Hadadden kamshinta ne ya fara zuwa hancin Hadir kafin yayi tozali da Zainabu Abunsa. Rufe ido yayi ya sake budesu a kanta. Wai da gaske Zainab ce kuwa? A nutse ta iso har gaban kujerar tasa sai ta durkuso ta daidaita fuskarta da tasa. Hawayen farinciki ne ya sauko mata shi kuma idanunsa sunyi ja ya kasa dauke ido daga kanta. Hannu tasa a kasan habarsa ta dago kansa tana masa kallon ido da ido ta sumbaci bakinsa sannan ta rungumo shi a jikinta tana mai kankame shi sosai ta saki kuka. Hamdala Hadir ya rinka yi a jejjere a zuciyarsa don ya tabbata abu daya ne ma'anar kawo shi nan gidan da kuma kasancewarta a cikinsa. ********** Danginsu Major na kusa da na nesa sai tururuwa suke domin ganinsu da yi musu barka da dawowa. Shekaru a kalla sha hudu ba wasa ba. Anyi haihuwa anyi rashi duk basa nan. Gidan kullum a cike da baki. Satinsu biyu kafin suka samu damar kai kayansu sabon gidan da suka rinka turo kudi domin ginawa a GRA. Sun sayi filin tun farkon fara aikin Mami kafin abubuwa su kara tsada. Kwanansu biyu suna aikin son ganin gidan ya dau saiti abu yaci tura suka hakura sai sun dawo daga wurin su Hadir da Mairama. Wannan Sojan mai alkawari da suke turawa kudin Mairama shine ya binciko musu Hadir yana Kano gidan iyayensa. Major yayi ta mamakin to me ya same shi yake gida. Mairama kuma wan Zayyan wato Maikudi tun a baya yace masa tayi aure amma Alheran tana Sakkwato wurinsa. Da wannan suka yi amfani akayi shawarar Kano zasu fara zuwa sannan su wuce Sakkwaton. Basu riga sun sayi mota ba Daddy Harun da yake Abuja yanzu shine ya basu wata bus fara mai kyau da iyalinsa ke amfani da ita wurin tafiye tafiye tare da dreba. Doki da fargabar yaya rayuwa ta kasancewa bayin Allahn nan sun cika zukatan su Mami da Major. Zahra da Fauziyya suna ta kokarin tuna Antinsu Zainab da Ibrahim da suke fada akan daukarsa. Babu wadda tayi shekara goma cikinsu lokacin. Labaran duka wanda Mami ke basu ne don babu abinda suke tunawa. Awwab kuma tuni 'yan kwanakin hutun nasa ya cinyesu a Katsina gashi tsarin aikinsu ba na zama wuri daya bane. Da tambaya Allah Ya kaisu gidansu Hadir can cikin lungu. Bayan gaishe gaishe da iyayensa Major ya gabatar dasu. Sai da ta share hawaye tace yau kwanansa ashirin da shida da barin gidan an mayar da aurensa da Zainab tsohuwar matarsa. "Bangane ba, da auren nasu ya mutu ne?" Yayi mata tambayar don neman karin bayani. Murmushi tayi masa ganin hankalinsa ya tashi "Bari dai nasa a kaiku can gidan nasu sai kuji daga bakinta" Wayar Zainab tasa aka kira mata bata shiga saboda suna asibiti. Kwanansu biyu da aure ta mayar dashi asibitin koyarwa na Kano wato Aminu Kano Teaching Hospital. Gwaji da bincike tasa ayi masa sosai inda aka gano matsalar da ya samu a kashin bayansa yayin fadawa wannan kwazazzabon a Liberia ita ce silar mutuwar jikinsa kashi ya danne wane bangaren na lakar bayansa. Rashin magana kuwa Likita ya tabbatar mata da cewa shock wato firgici ne ya haifar dashi. Da ace tun a baya sun tsananta dabarun dauke masa damuwa kila da tuni an manta da ya taba dena magana.. "Duk da haka Hajiya mijinki zai iya samun lafiya amma shawara mafi a'ala gaskiya ki fitar dashi ko da Egypt ne idan da hali. Lalurar ta dade a jikinsa yana bukatar kwararru a kansa da ingantattun kayan aiki" Kallon Hadir tayi ta saki murmushi "Doctor ka taimaka ka tayani duba asibiti da kuma rough estimate na abinda zan bukata" Bata ankara ba ta bayan kujerar taji an rungumo wuyanta sosai ta sa hannu tana dukan hannayen Ibrahim "dan gidanku shakeni zaka yi?" Hadir yayi murmushi suna bashi sha'awa zamansu tamkar kaka da jikanta. Ibrahim dinsu matashi ne wanda kana kallonsa sai ka sake bare yanzu da mamansa ke kara wadata shi da kaya sa suka dace da zamani. Kin sakinta yayi yana kara manna kansa a wuyanta "Mama mungode injini da Babana" Kwalla taji a idonta da ta kalli Hadir ta ga ya gyada kai "ni ku tashi mu tafi kuna neman saka mutane kuka." Ibrahim ke tura kujerar babansa bayan ta yiwa likitan godiya suka kama hanyar wurin ajiye motoci. Gasu dai suna tafiya miji na zaune amma dole su baka sha'awa yadda duk suka yi kyau ga kuma alamu sun nuna iyali ne da ke matukar kaunar juna. "Mama ki koya min tuki don Allah" "Da wannan rawar kan" "Baba ai bani da rawar kai ko?" Ya dukar da kansa yana tambayar Hadir shi kuwa ya gyada kai yana supporting dansa. "Kuma sunana zaka fara fada idan ka warke ko" Hararar da Zainab tayi masa ce ta saka shi wata dariyar shakiyanci "baka isa ba yaro" Dariya suka rinka yiwa juna kowa ba cewa dashi za'a fara ba kace uwa da danta bane. Tana tuki Ibrahim ke nuna mata hanya don bata waye da garin Kano ba wayar autansu Hadir ta shigo yace yana tare da baki a kofar gidansu. Ya sanar dashi suna hanya sun kusa karasowa. Da ya fadawa Zainab tace su waye. "Bari na kira na tambayeshi" "A'a barshi kawai" Bus ta gani a kofar gidanta da mutane a ciki. Mami tun da Zainab ta karyo kwana ta ganeta. Jikinta na rawa tana sauri ta bude kofar motar ta fito. Major ma haka ya fito yana hango Hadir a daga bayan motar. Hannunta taji yana rawa da ta tabbatar da su waye a kofar gidan. Ta juya a hankali za ta cewa Hadir ya gane su sai ta ga yana hawaye. Bata iya gyara packing ba ta kashe motar ta fito da sauri ko takalmanta bata saka ba. Hannu ta dora akan bakinta ta toshe kukan da yake barazanar yin sautin da kila sai makota sun leko ta suka tako gaban juna sunyi sharkaf da hawaye. "Mami?" "Antin su Zahra" A wajen nan suka rungume juna suna kuka, kuka na gaske. Major ya karasa ya budewa Hadir kofar bayan fuskarsa cike da annuri. "Lieutenant fito mu gaisa" Hadir ko motsi baiyi ba sai rufe ido da yayi hawaye mai dumi na sauko masa. Da yana da lafiya wallahi zai sarawa Major Mustapha ne domin soja ne a gaban ubangidansa. Ibrahim ya fuskaci bai san yaya baban nasa yake ba ya cire kai ya kira mamansa. "Mama zo mu fito da Baba daga motar" A kidime Major yace "me ya same shi?" Zainab ta dawo tana kuka tana dariya tace Ibrahim ya bude gate su shiga ciki. Kallonsa su Mami suke yi ya budw gate din ta shigar da motar sannan duka suka shigo. Wheelchair Major ya ga Ibrahim ya dauko a boot yaji zuciyarsa ta karye Zainab tazo zata taimaka su dora shi yace bari yasa hannu. Hadir ba kiba gareshi ba shiyasa ma suke jin saukin daga shi din. Sai da ya zauna Major ya dube shi da tausayawa "kai kuma taka lalurar kenan Hadir?" "Baba baya magana" Zainab ta share hawaye ta bude musu kofar gidan. Mami da Major mamaki ya kara kama su da jin wai baya magana kuma. Sai da suka zazzauna yaran suka sake gaishe su Zainab ta rike baki "yanzu Zahra da Fauziyya ne haka? Ikon Allah, Inna Awwab din Mairama. Ita kuma wannan 'yan matan kamar a tafi a barmin ita wace" "Zayyanatu sunana" ta amsa da kanta. Mami tana murmushi tace "Daddy yaso yiwa Zayyan takwara sai tazo a namiji" "Allah sarki Mairamu da Zayyan ban san yaya suke ba" Hadir sai runtse idanu yayi Mami da Major na kallonsa da ita. Mami ta daure tace "ashe baki san Allah Ya karbi ran Zayyan tun a Liberia wurin ceton rayukan mazajenmu ba" A gigice tace "ME??? Baban Radhiya ya rasu? Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Kuka suke yi sosai mazan na hawaye harda Major duk dakiya irin tasa. Zainab ta tsahirta tace su Zahra da taga suna tayasu kukan su shiga dakinta bari ta aika a siyo abinci don bata yi girki ba. "Turasu kitchen kawai su dafo mana" "Ayi haka ko ware gajiya basuyi ba. Naga alamun daga nesa kuke" "Babu komai ku shige kitchen ku duka kowa tasa hannu" "Ibrahim jeka sai ka nuna musu. Su dafa mana abin da suke so, ko motsi bana son yi daga wurin nan" Sun san dai wai wayo ake son yi musu. Suna yin hanyar kitchen din Ibrahim ya dawo da baya ya labe sai ga Zayyana ita ma ta dawo kusa dashi tana kara kunnenta a jikin kofa. "Meye haka" ya dan sha kunu. A shagwabe tace "Your mummy and daddy are making mine to cry" Wane kallon sama da kasa yayi mata "sannu baturiya ai ni ya kamata nace haka" Kunnuwansu Zahra ta rike su biyun Fauziyya kuma tace "ku rufe mana baki dalla can muji me ake cewa sosai" Duka su hudun suka sami wurin tsayawa suna jiyo labaran ban tausayi daga iyayensu. Yadda su Mami ke kuka a falon haka suma suke yi. Sun tausayawa juna sosai kowa da irin tasa kaddarar. Damuwarsu sai kuma ta karkata kan Mairama da Radhiya. Sun share kusan awa suna jajantawa juna sannan Mami ta dan bude murya "yaya ne shiru babu ku babu abinci" Zahra ce ta fara fitowa taje ta fada jikinta tana kuka. "Kuji min yaran nan, labe kuka yi kenan?" Zayyana ta gyada kai tana sababbin hawaye. Zainab tayi dariya "to yau kunji rayuwar iyayenku ko" Ibrahim ba kunya ya koma gefen Zainab kamar zai shige mata ciki yana kara son mahaifiyarsa. "Anya wannan zaiyi soja kuwa?" Inji Major "A'a wallahi ni malamin makaranta zan zama." yace da dukkan gaskiyarsa. Suna ta dariya Zainab ta dauko kudi ta bashi "kayi sauri ka siyo mana abinci tunda labe ya hana ku girki" Kwanan Radhiya biyu da yiwa gidan Ardo yaji tunda aka yi mata aski. Yaran dangi sa'aninta duk Emzee ya fesa musu sai ta wuni suna zuwa gidan tsokanarta. Na yau yafi bata haushi harda cire mata dankwali gashi Zakari dan gidan Baffa Habubakari da take hasashen yana son ta yana gidan. 'Yar yayarsa ce ta cire mata kullin maganin da take yi a kanta yanzu kunya ta isheta. Zakari sai ya rufe yarinyar da fada ya fita. Zaune take a daki tana kwafa don idan ta kamata sai jikinta ya fada mata, dazu ma albarkacin kawunta taci kada abin kunyar yayi yawa. Muryar Baffa Gide taji yana fada yana sanar da matarsa ya rasa taurin kan da yake damun Mairama. Maza sun fi biyar masu neman aurenta amma kowa yazo sai tace wai ita makauniya ce. Yayi iya kokarinsa ya samu makaho dan wani attajiri a cikin Giade mai mata biyu shine yaje ya sanar da ita ta watsa masa kasa a ido. "Na fuskanci yarinyar nan dama can fakewa take da makanta amma bata son yin aure" "To banda abinka Malam ku kyaleta mana." "Sai ta rayu babu aure? Yaran nan suna nasu auren fa zata soma jin shiru da kadaici. Ni gata nake son yi mata amma taki gani. Fitowa nayi na barta tana ta kuka" Hijabinta ta figo bayan ta gama jin bayanin Baffa Gide tace zata tafi gida. "Dena hararata ba kinji nace na barta tana kuka ba ni ban taba miki uwa ba" Iyalle matarsa ta soma dariya don fuskar Radhiya a hade take. " 'Yar soja a gaida gida" Tana zuwa gidan ko dakin Innawuro bata je ba ta tafi wurin Umminta. Hotuna ne a hannunta tana shafawa tana kuka. Babu mai sanin yanayin da zuciyarta take ciki sai wadda ta tsinci kanta a irin yanayin. Zayyan ya tafi ya barta kuma babu wani kwakkwaran bayani da zata kama taji salama a ranta game da mutuwarsa. Ko ranar da ya rasu bata sani ba sai kiyasin lokaci da aka bata. Saurin daga pillow tayi zata boye su da taji motsin mutum. Radhiya ta rigata ta hanyar karba tana kallon iyayenta a ranar bikinsu. "Ummi" Share hawayen take da sauri kafin ta fara tsareta da tambayoyi. "Meye, ba yaji kika yi mana ba mai kwal kwabo" Radhiya tayi dariya duk da ta tsani askin. Tana son farantawa mahaifiyarta. "Kaina yanzu fa yafi dadin wanka. Insa sabulu harda soso in dirje shi. Idan na shirya na mulke abina da man kwakwar da Yadikko ta bani wancan zuwan da mukayi Sumaila" "Da kike ishi mutane da kuka harda yaji" "Ba'a kyauta min bane...da kinga kan nan bazaki so ace nawa bane" A hankali sai ga Mairama tana dariyar shiriritar Radhiya. ********** Bayan kwana biyu da zuwan su Major Kano suka shirya harda su Zainab sai birnin Shehu. Da yake Zainab 'yar gari ce dadewa bata sa ta manta hanyar gidan ba. Sun so bata saboda gyare gyaren da aka samu kadan. Sojan da ake turowa kudi ya riga ya bar garin ma ta banki yake turawa MaiKudi kudin. Alhamdulillah gida ya cika da yara ko ta ina. Ibrahim yana tura Hadir gefensa Major ne yana fada masa dawowar Awwab nan da kwana goma. Matan ne suka fara shiga aka amsa musu. Sun gaisa Mami ta tambayi Jume wata yarinya ta nuna musu dakinta. "Fada mata abokan aikin marigayi ne da iyalansu suka zo" Yarinya ta ruga sai gasu sun fito tare Jume tana musu marhabin da lale. Tabarmi uku aka shimfida musu suka zauna aka gaisa. "Jama'a ina kuka shige duk shekarun nan ba'a jin duriyarku?" Kunya ta kamasu duk da kowa dai da nasa uzurin. Sun dan yiwa Jume bayanin da zata iya fahimta Major yana dariya yace "ina Alheran ne?" "Wai, 'Yar soja ai tana rugar Barkindo, da yake dai akwai bikin yayarta 'yar wajen Mubaraka nasan suna tafe in Allah Ya so" Kallon juna suka shiga yi sai Mami ta gyara tambayar "aka ce mana bayan Mairama tayi aure ita ta dawo nan wurinku" Itama nema suke su juya mata kai ta kwalawa Matar Badaru kira "kinji wai 'Yar soja suke cigiya ni duk ban fahimci zancen ba, nasan Badaru yana ciki turo min shi ya musu bayani." Tsayawa tayi suka gaisa sannan taje ta dawo tare da maigidanta. Shima ya gaisa dasu a mutumce Major yayi masa bayanin yadda suka yi da sojan da yake turo musu kudi akan cewa Mairama tana gidan miji, Radhiya kuma tana nan. Badaru ya rike baki abin da daure kai "Yallabai gaskiya ka binciki mutumin da yayi maka karairayin nan tun wuri" "Ban fahimceka ba" Mami da Zainab har sun fara damuwa ganin yadda iyalan gidan su ka canja fuska su ma. Badaru ya gyara zama ya soma yi musu bayani "zancen da nake muku Mairama tayi akalla shekara shida ko ma fi da makancewa, Radhiya da Zayyan kuma suna tare da ita a can wurin dangin babarta. Sai dai mutumci irin nata wallahi har ila yau tana turo mana yaran idan sun sami hutu" Kuka wiwi Zainab da Mami suke yi. Zuwa yanzu sai dai su ce sun ga jiya sun ga yau a auren soja. Makanta, yanzu ace Mairama ta makance babu ido. A sanyaye Major yace "ban tari numfashinka ba, wane Zayyan kake magana a kai?" Jume tace "Zayyanu karami kanin Radhiya" Mami ta zaro idanu "aka ce mana ta haihu jariri babu rai" A fusace Jume tace "wai uban waye ne da wadannan karairayin? Yarinya tana fama da lalura da rashin miji anbi an dabaibayeta da karya. Rashin waiwayarta da kuka yi yafi komai damunta, bata da masaniyar inda kowa yake cikinku gashi dangin ita mahaifiyar Zayyanu suma shiru rabonmu dasu tun sunan 'Yar soja" Zuciyar Major tuni ta kawo wuya ya daga waya zai kira dan sakon nasa sai ga Maikudi ikon Allah. Su Maikudi an karo wulakanci yana shiga yana fita duk wata yana jin 'yan chanjinsa a aljihu. Saboda son zuciya ma sai ya dena 'yar fafutukar da yake tunda dai albashin nan yana shigowa babu fashi. "Yauwa Maikudi gara da Allah Ya dawo da kai da yanzu." Idanunsa akan bakin ya kula akwai maiko a tare dasu "hee...hee baki muka yi a gidan ne. Sannunku da zuwa." Matarsa ya shiga kwalawa kira "ya naga babu ko 'yar mantina dinnan a gabansu? Wannan ai halin karanta ne. Waye nan a cikin yaran azo a nemo musu abin sha mai sanyi" Ran Jume ya fara baci tace "to dan ayi jikan na'isa, mu duk bamu iya ba sai kai. Ni zo ka jiye min baki ke neman Radhiya wai an fada musu a gidan nan take" A take kuzarinsa ya fara raguwa "ki fada musu inda take su je mana" "Mutanen nan fa abokan Marigayi ne, shi wannan yace ya dauki lokaci yana aiko da kudi kuma ance a gidannan ake karba" Badaru ya kara masa haske Abinka da munafuki gumi ya soma yi kamar an kwara masa ruwa "indai don Allah suke yi sai abar tone tone su sake mata kyautar tunda sun dawo. Ni bari na shiga ciki na gaji" Wani irin kallo Major da Hadir ke yi masa. Ashe Jume ma tasha jinin jizkinta. Ai kuwa bazata barshi ba indai haka ne. Kankace ido tayi ta kaurara murya "Maikudi kada kace min kana da masaniya akan maganar da mutanen nan suke yi" Ja da baya ya soma yi a tsorace "Ni kuma? Daga shigowata? Uhmm nayi nan akwai mai son ganina a waje" kafin su farga ya fice da sauri. Yau da ace Hadir na da lafiya Maikudi sai ya yabawa aya zakinta. Major ma tashi ne dai baiyi ba amma ko ciki daya suka fito da Zayyan sai ya nuna masa yayi kuskure. "Ku tashi mu tafi" yace dasu gabadaya. Jume tana kuka matan gida da Badaru suna salati suke basu hakuri. Babu alamun wasa a fuskarsa yace "Ku bani nambar waya da zamu nemi kwatancen inda Ummin Awwab take. Shi kuma wancan kafin na turo masu kama shi a fada masa nasan iya abinda na turo saboda haka ina bukatar kudin nan...da gaggawa" Ransa yayi matukar baci ne yaki amincewa da masaukin da Jume tace ayi musu a gidan. Giginya hotel suka yi masauki washegari sai ga Badaru da sassafe ya kira yace zaiyi musu rakiya har Rugar Barkindo. ********** Saboda yanayin matsanancin zafi da ake fama dashi yau gidan har Ardo suna zazzaune a karkashin katuwar darbejiyar da ta yiwa tsakar gidan inuwa suna taba hira. Yammaci ne na asabar Radhiya tasan cewa Zakari zai zo kawo wani sabon maganin ciwon ido da aka rubutawa Mairama a asibitin Bauchi inda yake aikin lab wato dakin gwaji. Gyaran nono ta gama wanda ta cire man shanu sannan ta je tayi wanka. Shiryawa tayi cikin riga da skirt ta saka hijabinta iya gwiwa don zuciyarta tana raya mata yau kawun nata zai fada mata abinda idanunta suke ganin yana boyewa...soyayyarta. Har kofar gidan Ardo aka rako su Major suka firfito kowa da nasa tunanin. A yayin da rayuwa tayi ta garasu ita Mairama kauye ta fado. Kauyen ma ruga da abubuwan cigaba suka yi mata karanci fiye da ko ina. Fitowarsu ke da wuya sai ga Emzee nan da wani abokinsa sun dawo daga kiwon shanun Ardo. Sanda ce a wuyansa amma shirt da dogon wando ya saka suna ta hirarsu ta samari. Ba Major da Hadir ba, hatta Mami da Zainab sai da gabansu ya fadi da ganinsa. Wannan banda haske babu ta inda zaka ce ya baro mahaifinsa. Kawunsa ya hango ya yi saurin barin abokinsa ya taho "Kawu Badaru yaushe ka iso" "Tare da bakin Umminku nake. Yi maza ka shiga kayi mana iso" Gaishe su yayi cikin gurbatacciyar hausarsu ta tsantsar fulani ya shiga ya fada musu. Mairama ta auna ta auno ta kasa gane su waye zasu zo nemanta tare da Badaru. Radhiya da ta tabbatar zuwan bakin zai hanata sakewa da Zakari ta shiga tura baki. Innawuro tace tayi shimfida sannan aka ce su shigo. Zainab da Mairama kowacce wai dakewa take yi kada suyi abin kunya a gaban 'ya'yansu amma da sauri suka shiga gidan. Mairama tana zaune akan tabarma ga sandarta a gefe ta yafa mayafi kalar kayanta. Daga bayanta kuwa babu tantama Alheran Radhiya ce wadda ganin 'yan gayu suna shigowa yasa ta manta da batun Zakari ta shiga washe baki. Mairama tana ji Innawuro tana yi musu barka da zuwa amma yaran kadai ke amsawa. Manyan kuwa Mairama suke kallo da take ta murmushi a hankali a zatonta babu mai ji tace "Ke su waye ne sai kamshi nake ji" Mami a gabanta ta zauna tana kuka ta kama hannunta da makanta bata hanata ayyuka irinsu yin fura ba da nata lallausan hannun. Zainab kuwa a gefenta ta zauna ta rungumo Mairama a jikinta. Rasa gane me yake faruwa ita da kowa na gidan suka yi. Radhiya da ta kurawa Major da Hadir idanu ta saki ihu kamar an tsunguleta. "Yasin Ummi na ganesu na hoton nan ne" Mami tasa hannu ta shafa fuskar Mairama tace "Ummin Awwab" Duk da bata gani sai da idanunta suka kara girma gabanta ya tsananta faduwa, baki na rawa tace "Mami??? Ke duba hotunan akwai wannan a ciki?" Ta fada tana kankame hannun Mami kamar zata kuma tafiya. "Ai shikenan tunda baki ce a duba dani ba" Zainab tayi maganar da wasa cikin kukan da yaci karfinta. Mairama fashewa kawai tayi da kuka su ukun suka rungume juna suna hawaye sauran jama'ar wurin suna tayasu mazansu da matansu. [02/11 7:30 AM] My 2nd Mtn: 20.Mairama ta ga gata da ya amsa sunan gata a Rugar Barkindo. 'Yan uwa ke tururuwar ganinta har ana fadan gidan wa zata zauna. Ardo yayi tsalle ya dire yace matarsa ce zata dauka ai ita ce mace. Dole sauran suka amince aka barwa Innawuro. Idan manya ko dattijai cikin danginsu sunzo sai ayi ta kallonta ana cewa kaza dinta irin na Mairo ne. Murmushi kawai take yi don ko hoton mahaifiyarta bata taba gani ba. Sun tausaya mata da jin labarin rasuwar mijinta ga makanta. Radhiya da Emzee sai gasu cikin 'yan uwa sa'anninsu ana ta nishadi. Abinci da nama anci an ture. Kafin sati ya zagayo jikinsu ya fara nuna kwanciyar hankali da koshi. Mairama kullum cikin godiya take ga Allah da Ya dawo mata da dangin mahaifiyarta. Ba jimawa sabo ya kullu sosai a tsakaninsu baki daya. So da tausayawa suke nuna mata da 'ya 'yanta. Ardo ke cewa su duka marayu ne ababen dubawa. Bata cuci kanta ba ta roki alfarmar su Radhiya su koma makaranta. Tare aka nema musu JSS 1 ita da Emzee da ya gama aji biyar. Ita a makarantar kwana ta gwamnatin jaha ta mata shi kuma jeka ka dawo ta maza. Ranar da dan gidan Baffa Habubakari ya kawo takardun tubure musu Radhiya tayi da kuka wai bata so. "Karatun kike yiwa haka Radhiya?" Innawuro tace tana kokarin bata baki. "Dama saboda bama cin abinci mu koshi ne fa Ummi ta kaini makaranta inyi kudi" Mairama kunya ta isheta tasa hannu tana nemanta "haka muka yi dake? Kuji min yarinya" "Da naga ko nama bama ci irin na gidan Baba Kallamu shine nayi zaton haka ne" ta mayar mata da amsa tana shure-shure. "Idan bata yi ba ai ba'a kirata jikar Ali ba" Innawuro tace tana dariya. Radhiya ta turo baki "Malamijo muke kiransa mu dai" "Ina yaga malanta sai bakar rowa da mammakon tsiya" "La la lahhhh baban Ummi ne fa" Ardo yana jinsu yana rubutu a jikin allo yace "da kyau 'yar albarka ki kare masa kinji ko. Duk tsiyar naka ai naka ne Innawuro" Dariya rigimar Radhiyan ke bata tace "kasan ni ba bakuwar zafi bace Allah Ya baki hakuri. Nima kizo na baki labarin 'yar uwata Mairo. Ga kyau ga kirki kamar wata dan daren goma sha hudu" Idanu Radhiya ta bude sosai da mamaki "wata dai irin na sama Innawuro?" "Akwai wata a kasa ne?" Mairama ta fada tana jin kamar ta mangareta. "Tabdi, Ummi kenan Innar taki a mulmule take kamar wata. Ga Malamijo kamar tsolon rake. Mu dai Allah Ya taimakemu ke daidai kike." Mairama ta fusata ta fara wawurarta "Karami dauko min yayarka ko ka janyo min ita. Yau tambotsan nata harda iyayena kuma" A guje ta tashi "Ardo don Allah ba Innawuro ce ta fada ba." Innawuro ta dauko muciya "bari na mulmule ki kema sai aji dadin kiranki jikarta" Hanyar waje tayi tana gudu wai ita gidan Malamijo zata koma. Mairama ta daure fuska "da ya fi miki mu ma mu huta. Kuma karatu ki ma fara shiri sai kinyi" Dawowa tayi da baya tana murza yatsan kafarta a cikin kasa tana tura baki "to don Allah ki kaini soja irin na babana indai kina so nayi karatu" Gaban Mairama ne ya fadi ba shiri sai ga hawaye. Innawuro da ta dauki abin wasa tana biyewa Radhiya ta shiga bata hakuri tasan bazai wuce mijinta ta tuna ba. Radhiya ma sai ta soma kuka tana cewa tayi hakuri zata yi karatun ko wanne ne. ********** Alheran Radhiya Zayyan Tureta irin fitinanun daliban nan ne marasa tsoro ga kin ji. Duk inda akace 'yan aji daya sunyi laifi to in sha Allahu Radhiya tana cikinsu. Kan kace kwabo tayi kaurin suna tsakanin dalibai da malamai. Kirikiri tace sunanta 'Yar soja haka babanta yake kiranta daga Mairama ta bata labari. Shikenan makaranta suka santa da wannan sunan. Anyi sa'a tana dan taba karatun babu laifi. Wata rana suna layin dibar ruwa suna ta hayaniya irin ta 'yan makaranta ta dage tana ta zuba. "Allah Ya kaimu siniya wallahi zan warwasa a makarantar nan. Duk wasu jiniya a lokacin sun shiga talatin a hannuna" Kawarta Ruqayya tace "ke 'Yar soja so kike yadda muke tsinewa su senior Jummai kema a tsine miki?" "Ke baki gane ba. Lokacin kannen su senior Jummai mai tafiyar agwagwa ne a makarantar. Ramuwa zan zauna yi" Wata tace "ai kuwa nima zan so, rannan fa kwai tace nayi mata a karkashin gadonta" Radhiya ta daka tsalle "inama nice wallahi, na samu na sassaka mata kashi mai waaaaaari" Dariya suke duniya sweet kampo sai ga senior Jummai ta taho da tafiyar catwalk dinta da su Radhiya suke yiwa lakabi da tafiyar agwagwa. Ta gama jinsu tsaf suna bayan ginin da famfon yake. Idonta ya kyallo mata ita sai kawai ta canja hirar amma saboda tsoro muryarta har rawa take yi. "Allah Yasa senior Jummai tace in zama daughter dinta a makarantar nan. Daga ranar wanki da debo ruwanta duka zan rinka yi" Sauran sai suka fara mamakin me take nufi tunda dai haduwa suka yi ana zaginta. Yadda tayi maganar ne idanu har sun ciko da hawaye yasa Jummai da sauran seniors din dariya. Kawayen Radhiya ciki ya duri ruwa. Ita kanta a tsorace take. Jummai ta dafa kafadarta kamar ta saki fitsari don tsoro sai ji tayi tace daga yau kada wani ya sake ko da aiken daughter dinta ne. Kowa yayi mamaki harda kawayenta tace Radhiya tana burgeta saboda ko me za'ayi mata sai ta aikata abinda tayi niya. Idanunta kawai zaka kalla kasan fitina da rigima suna dawainiya da ita. Wata kungiya da aka bude a makarantarsu SS wato School Soldiers a nan aka samu kanta. Da jikinta da zuciyarta take wannan aikin na kare hakkin dalibai. Gashi da kayan makarantarsu riga da zani ne amma an basu hula irin ta sojoji mai lankwashewar nan suna sakawa akan hijabansu. Radhiya jin kanta take kamar sojar gaske. An kamanta gaskiya da amana sannan an gurji seniors masu hana sababbin dalibai sakat. Idan kaji ana Officer 'Yar soja a makarantar zaka rantse wani babban soja ne saboda yadda ake shayin shiga tarkonta. Zaman SS shine babban jindadinta a makarantar. A haka aka yi karatun cikin ikon Allah tayi nasarar fita da credit bakwai. Emzee kuma duka taran ya haye. Sai dai ko kadan a yadda ilimin ya tabarbare bazaka hada makarantar gwamnati dake kauye da wadda take birni ba. *** Tana jin shigowarsa dakin nata tayi saurin rufe ido kamar mai bacci. Murmushi kawai yayi yana kada kai. Zainab bazata taba canjawa ba indai tare dashi ne. Shekarun da suka yi a matsayin ma'aurata bai sa ta canja komai daga yadda ta faro ba. Akan doguwar kujera irin ta hutawar nan ta dakin ya zauna sannan ya soma yi mata magana. "Tashi magana zamuyi" Kin motsawa tayi sai da taji yace bari ya hawo gadon ya tabbatar ko idonta biyu. Juyowa tayi a hankali tana jin kunyar ya gano karyarta. Bata son yadda take yiwa Musa amma zuciyarta ta kasa rissina. "Shawara nazo nema" "A wurina?" Ta tambaya mamaki yana bayyana a fuskarta. "Eh, aure nake son karawa sai dai na kasa tsayar da shawara akan na dawo da mamansu Aisha ko na auro wata daban" "To ni me kake so nace? Ka auri wadda tafi kwanta maka" Fuskarsa ta nuna ba haka yaso ba kuma shima bai boye ba yace "zan so kiyi min rigima irin wadda kowace mace take yiwa mijinta a lokacin da ya tashi yi mata kishiya" Cikin yanayin rashin damuwa don har ranta ita bata ga abin rigima ba tace "saboda me?" "Saboda nasan cewa ko yaya Zainab ta damu dani kamar yadda na damu da ita. Sai dai nafi kowa sanin zaman hakuri kike yi a gidan nan. Na tauyeki na hanaki walwala da jindadin zama da wanda kike so" An tabo inda yake mata kaikayi sai hawaye sharrr tana gogewa da bayan hannunta. Musa yana jin kukan har ransa amma yasan ba nasa bane na wani ne "kinyi hakuri sosai Zainab, naso ace mun haihu don in samu abinda zan cigaba da garkuwa dashi in ki rabuwa dake amma Allah bai kawo ba. Sai nace zan barki ko don su Aisha. Yanzu kuma gashi suna shirin aure nan da watanni kadan. Ina ganin kamar bani da sauran dalilin cigaba da zama sanadin kuncinki" Kukan Zainab sai ya koma mai sauti. Tana tausayin Musa bisa soyayyar da yake mata. Tayi iya yinta amma zuciyarta taki amsarsa a matsayin masoyi. "Kayi hakuri da dukkan bata maka da nake yi, zanyi kokarin gyarawa" Murmushi yayi mata yana mika mata takardar hannunsa "ni na gyara mana matsalar ina fata Allah Yasa nayi abinda ya dace. Zainab na sakeki saki daya" A gigice ta kalle shi hawayenta yana karuwa. Idan ya saketa fa kenan babu sauran shamaki tsakaninta da Hadir. A gaggauce ta bude takardar sai ta kula guda uku ne a hade da stapler. Daya takardar saki, daya check na miliyan biyu, dayar kuma takardar mallakar wani gida ne a Kano da ya saya mata dan madaidaici. Dago kai tayi sharbe da hawaye harda majina. Cikin nutsuwarsa yake magana daki-daki "tukwicin kulawar da Aisha da Anisa suka samu daga gareki ne. Bana son fada amma yabon gwani ya zama dole. A kanki na yarda ba sojoji bane kadai jaruman kasata harda matansu. Soyayyarki ga baban Ibrahim ita tafi komai kara miki kima a idanu na. Nayi zaton kudina zai sa ki manta da wanda yake talaka mai nakasa amma bakiyi ba. Kin so zama da mutumin da bautar kasa ta nakasa farincikinku domin cikar soyayya. Nagode da lokacinki da kika ara min muka zauna tare" Maganganun sunyi mata tsauri sun taba mata zuciya. Tashi yayi zai fita Zainab ta taho da sauri ta rungume shi tana kuka. Bata taba yi masa haka ba idan ba shi ya nema ba sai yau. "Allah Ya faranta maka fiye da yadda kayi min Abban Aisha. Ka yafe min duk laifukan da nayi maka a zamanmu tare" Dago kanta yayi kana ganin damuwa a cikin idanunsa "yanzu dai ki soma hada kayanki kafin na chanja shawara" Da hawayen take murmushi "nagode" "Nima nagode" yace ya sa kai ya fita yana jin a ransa kamar an sauke masa wani kaya mai nauyi. Ya dade yana tsoron hakkinta kada ya kama shi saboda son zuciyarsa yau Allah Ya bashi iko ya rabu da ita ba don yana so ba. Ajiyar zuciya ta saki bayan fitarsa ta mika godiyarta ga Allah sannan cike doki ta kira Ibrahim. Labaran tara na NTA ya kunnawa Hadir yana gefe game ya dauke masa hankali a wayar kiranta ya shigo. Murmushi yayi ya dauka. "Hello Mama" Hadir ya juyo ya kalle shi sai kuma ya dauke kai. Ina ma zai iya tambayar lafiyarta da yayi. Daga daya bangaren tace "Ibrahim yaya su Umma?" "Lafiya kalau, ya su Anti Anisa da Baba?" "Su ma lafiya kalau. Ibrahim nace me kake so gift din graduation ka ki fada min kamar wata surukar ka ko, na kula ko hira baka son yi dani" tayi karamar dariya. "Ina naga fuskar" yace a zuci. Ita da bata sakin jiki da kowa bare ayi batun hira. Daga gaisuwa sai ta fada kogin tunane tunanenta ta bar mutum zuru. Yana mamakin yadda idan yaje hutu take hira da su Anisa duk da ba wata hirar kirki suke yi ba. "Ya kayi shiru ne?" "To kiyi hakuri zan gyara" "Shikenan, ina babanka?" Hadir ya kalla suka hada ido. Anya Mama ce kuwa yace a ransa. Bata taba tambayarsa babansa ba sai su Umma kawai. Kara kashe shi tayi da wani mamakin ta hanyar cewa ya dora masa wayar a kunne "saura ka sani a speaker" Bai san lokacin da ya kwashe da dariya ba. Wai dama Mama ta iya wasa haka? Hankalin Hadir gabadaya yana gare shi sai kawai ya dora masa. Wani irin sanyi taji ya ratsa zuciyarta da taji sautin numfashinsa. Soyayyar da ta dade tana dannewa ce ta taso mata. Da suna tare yanzu shekararsu goma sha tara da aure. Cikin wani yanayi na shauki da begen da yake nuna soyayya bata tsufa tace "Hadir" Allah Sarki rayuwa, yaji sunan har tsakiyar kansa amma bazai iya amsa mata ba. "ASTAGFIRULLAH" tace da sauri ta katse wayar. Shaf ta manta cewa har yanzu tana karkashin Musa har sai ta gama iddah. Tashi tayi ta bude wardrobe ta dauko akwatunanta. Da safe Musa da kansa ya sanar da su Aisha cewa mamansu zata dawo sannan Antinsu Zainab zata tafi. Sun saba da ita sosai a hannunta suka girma. Tana kuka suna kuka har airport suka rakata. Motarta Musa yace zai bayar a kawo mata har gida. Tayi ta masa godiya da kyakkyawar addu'a ta shige jirgi zuwa garinsu tana mai fatan samun sauyin rayuwa mai dadi. ********** A firgice Rtd Major Mustapha ya tashi jike da gumi daga mafarkin da yake yawan yi wanda yake daga masa hankali ya shiga laluben kafar katakonsa. Mafarkin ya tsananta a gareshi tun bayan da suka sanya ranar komawa kasar haihuwarsu. Korido din da zai sada shi da kitchen ya nufa don ya sha ruwa ya hango Mami ta barbaza kaya a gabanta na tsaraba da take ta warewa tana saka sunaye. Kasa tafiya yayi duk motsinta yake bi da kallo. Wannan kyakkyawar matar kanwarsa ce, matarsa kuma uwar 'ya'yansa. Hakika a kullum baya gajiya da sanya Hassana cikin addu'o'insa domin ta cancanci fiye da haka. Tayi hakuri dashi iyakar hakuri musamman a lokutan da yake ganiyar ciwo har yakan nemi rayuwarta ba a cikin hayyacinsa ba. Tunanin kawai kan sa tsigar jikinsa tashi. Tabo uku ne a jikin Mami wanda suka samu a dalilin PTSD dinsa. Jikinta ya bata yana kallonta haka kawai, ta daga kai suka hada ido. Murmushi suka yiwa juna ya dawo falon ya zauna. "Me ya hanaki bacci shabiyu har ta wuce?" "Aikin nan yaki karewa Daddy. List din mutanen ma kamar bamu yi rabi ba" ta dan bata rai. "Ku kuma mata da baku da nutsuwa indai akan tsaraba ne ko" Tattara kayan ta soma yi gefe sannan ta dube shi "me ya tasheka ne?" Shirunsa ya fahimtar da ita komai. Kusa dashi taje ta zauna "nan da kwanaki goma in sha Allah muna gida. Muna kwana biyu an gama gaisawa da 'yan uwa babu inda zamu je sai wurin Ummin Awwab da Hadir. Lokaci yayi da zaka kore komai daga ranka ka rungumi kaddara." "Yes Ma" yace yana murmushi. Maida masa martanin murmushin tayi ita ma "Tashi muje mu kwanta kasan gobe is a big day" Suna kwance tuni Mami tayi bacci amma shi ya kasa sai rarraba dayan biyu yake. Ko yaya iyalin Zayyan? Allah Yasa suna cikin mafi kyaun yanayi. Sai kuma ya koma tunanin auren Zahra da Fauziyya da za'ayi nan da wata biyu. Kowaccensu tuni ta hada degree dinta. Hadi ne na gida zasu auri 'ya'yan 'yan uwa kamar yadda ya kusan zamewa danginsu al'ada. Har nan aka turo mazan suka daidaita kawunansu. Bai san lokacin da bacci yayi awon gaba dashi ba. Washegari kuwa banda shirin tafiyarsu da yaki karewa karfe bakwai na dare suka tasarma gidan da Mami take aiki. Major sanye yake sa suit sky blue da light grey din shirt a ciki. Yayi gyaran fuska yayi kyau yana rike da sandarsa da take taimakawa wurin rage masa rashin jindadin tafiya da kafar katako duk da ya saba yanzu. Mami, Zahra, Fauziyya da Zayyana duka abaya ne a jikinsu masu kyau kowacce tayi nadi da mayafin da ya dace. Party ne na bankwana iyalin Herr(Mr) da Frau(Mrs) Schmidt suka shiryawa Mami a matsayinta na shugabar ma'aikatan katon gidan. Sun matukar jindadin zama da ita tun lokacin da suka basu wuri a gidansu kafin daga baya su kama wani mai dan girma a waje. Iyalin babu abinda yasa suka likewa Mami kamar tsantsar tarbiyar da yaransu suke koyi da ita har a makarantunsu. Tarbiya ce irin ta musulunci batare da ta fito zahiri ta tallata musu addinin ba. A fakaice ta rinka kwadaita musu tana fatan wataran idan da rabo su karba. Farkon zuwanta sun so hanata zuwa da lullubi ko karamin hijab. A take tace ta bar aikin. To amma amanar da suke gani daga gareta yasa da kansu suka sake nemota. Aikin Mami a gidan yana daga cikin abinda Major bazai taba mantawa a rayuwarsa ba. Wai shi Mustapha da ya kai matakin Major a soja shine matarsa take aikatau. Abinda yafi karfi a kasarsu yazo lalura ta cinye komai nasa yafi karfinsa. Bashi da tamkarta a duk duniya. Ya amince samun kamarta sai wata matar sojan. Jarumar mace matar jarumin namiji. Katuwar harabar gidan tasha gyara da fitilu da flowers ko ina yana kyalli ga kayan abinci a gefe debi wanda kake so. [02/11 7:30 AM] My 2nd Mtn: 21. Duk dauriya irin ta Ardo sai da ya matse kwalla ganin yadda hatta mazan kowanne ido yayi jajir. Mairama ce ta fara magana cikinsu "ina Awwab dan Ummi? Nasan ya girma yanzu? Anyi masa aure ne?" Zahra tace "Mami ashe da gaske dai Ummin Hamma Awwab mu bata sonmu" Mairama sai dariya ta kufce mata ta daga hannuwa ta tashi tsaye tana cewa "Zahra, kece ko? Ina Fauziyya da Ibrahim abokin fadan wannan yarinyar?" Fauziyya da Zahra suka matso suna rike hannuwanta tace "kuji min yara yaushe zan ganeku da hannu kawai, haka ake yi" ta fada tana rungumesu. Muryar wata shagwababbiya da hausarta ke fita kamar mai waka saboda yadda yaren Germany da turanci ya kama mata baki taji tana cewa "Daddy ni kowa baya sona, she even asked for Hamma that is not here" Ibrahim kallonta yayi ya tabe baki, yarinya yar shekara sha hudu kamar yadda yaji Mami ta fada sai ta dage tana zuba tabara Daddynta yana biye mata. Emzee kuwa murmushi yayi bai ce mata komai ba. A gidan Ardo shine karami bai saba ganin haka ba shiyasa yadda tayi ya burge shi. Mairama sai ta sake dariya ta rasa ina zata kai farincikin da yake cikin zuciyarta. "Such a sweet voice, wace ce wannan?" Zayyana dadi ya mamayeta ance muryarta da dadi ta tafi da sauri ta ture Fauziyya da Zahra ta shige jikin Mairama tana cewa cikin tsantsar mamakin wannan 'yar kauyen "Daddy she speaks English too" Ibrahim ya kwalo idanu a hankali yace "ji min rainin wayo." Sai kuma suka tsinkayi Radhiya muryar tayi kicin-kicin da fuska tana kallon Zayyana "ke yarinya iya bakinki wallahi, Ummina ma 'yar boko ce har secondary ta gama ehe" "Zaki fara ko?" Mairama tace tana zaunawa har lokacin Zayyana na jikinta ba ta fahimci dogon zancen Radhiyan ba. "Ai gara na fada mata gaskiya tun wuri kada ganinki a kauye yasa ayi miki kallon wata local" Haba wuri sai ya kaure da dariya harda Major. Sai lokacin Mairama ta gama gane su waye a wurin kunya ta kamata. Halin Radhiya sai ita. Zainab tana cewa ta zo Mami ma tana kiranta sai ta rasa wurin wa zata je. Zainab tace "jeki dai dama ita ce mamanki, ni Zayyan zan dauka nafi kama da maman maza" Rufe fuska tayi da hannuwanta tana kallonsu a fakaice sai wani blushing take "wallahi kun sani jin kunya...duk sona kuke yi" Wata dariyar ta basu Mami ta janyo hannunta ta zauna a kusa da ita "haka kika koma Alheran din Awwab? Wannan idan na wuni dake cikina sai ya kulle" "Indai wannan ce baki ga komai ba" cewar Innawuro. Kowa a cikinsu yana cike da tsananin farinciki. 'Ya'yansu ma ko da basu gama sanin mahimmancin iyayen nasu a wurin juna ba sun amince wannan haduwa ta faranta ran iyayensu su ma dole su ji dadi. "Idan kun gama kukan da dariyar ya kamata a gaisa kuma haka" Ardo yace dasu don ya dakatar da zubar hawayen matan. Sai kuma aka soma gaisawa ana tambayar yaya bayan saduwa. Mairama ta fuskanci bangaren da take jin a nan su Major suke ta saki fuska. "Daddy ina fata duka kuna lafiya" "Lafiya kalau Ummin Awwab" yace a sanyaye. Dan bata rai tayi cikin wasa "abokinmu tun shigowarku banji ko tarinka ba, ai shikenan." Dif taji shiru ya rasa wurin babu mai cewa komai cikinsu. Hantar cikinta ta kada a sanyaye ta rike Zainab "ba dai....Subhanallahi, ba dai shima" Wani irin kuka Zainab ta saka tana jin ciwon lalurar Hadir har kokon ranta. Jikin Mairama ya gama saki ta sadakar kila shima babu rai. Radhiya da Emzee sun gane shine akan kujerar amma su din ma basu iya bata amsa ba. Major ne ya danyi gyaran murya ya soma maganar da kafin ya kai karshe wurin ya sake rikicewa. "Hadir gashi nan muna tare sai dai tsahon shekarun nan da bamu tare ya yi su ne da paralysis sannan baya iya magana." Sai da ta dan sami nutsuwa daga wannan tashin hankalin abinda yake ci mata rai shekara da shekaru ta kasa daurewa cikin karyewa da dashewar murya tace "uhmmm...uhmm nace babansu Karami. Kuna tare ya rasu ko?" Major da Hadir da dukkansu da suka san labarin abinda ya sami Zayyan daga bakin shi kowa gabansa ya fadi. Mairama da ba ganin fuskokinsu take yi ba ta cigaba da magana. "Ko baku san ya rasu ba ma?" "Mun sani Ummin Awwab, muna tare" Major ya amsa da sauri. Ajiyar zuciya tayi harda guntun murmushi "Alhamdulillahi, da hankalina ba karamin tashi yake ba da tunanin kila ba'ayi masa sutura kamar kowane Musulmi ba. Nace ko irin mutuwar nan ce ta su da yawa. Ance ramin kawai ake guda daya. " Major Mustapha shiru yayi ya rasa me zai fadawa wannan baiwar Allah. Allah ne ya cece shi a lokacin aka fara kiran sallar Magariba Ardo yace kowa ya tashi. Mazan waje suka tafi wurin masallacin da yake gefen gidan akwai butoci cike da ruwa. Ibrahim ya dauko daya ya duka a gaban Hadir zaiyi masa. Emzee yana tsaye a gefe yana ta kallonsa. "Za kayi masa?" Ibrahim ya tambaye shi yana murmushi. Murmushi Emzee yayi ya gyada kai. "Gashi" Ibrahim ya bashi butar. Emzee ya karba "ka tsaya ka rinka gani kada nayi ba daidai ba" Da taimakon Ibrahim din Emzee ya yiwa Hadir alwala. Kukan zuci yake yana murmushin zahiri. Yau dan Zayyan dinsa ne yake masa alwala. Bayan sun gama ya kuma cewa shi zai tura shi cikin masallacin. Dadi ya kama Ibrahim don ba karamin ji da babansa yake ba. Da suka idar da sallah ma Emzee din ne ya sake turo shi zuwa bakin kofar, Ibrahim sai ya tsaya daga waje ya kama kujerar suka daga shi sannan aka sauketa a kasa saboda tudun da yake wurin shigar. "Sunana Ibrahim Hadir" Takalminsa yake lalube wannan ya bawa Hadir damar ganin fuskarsa sosai yana murmushi tamkar an ajiye mahaifinsa a wurin. "Muhammad Zayyan Tureta" Wani dagen gira Ibrahim yayi "amma Zeezee naji ana ce maka ko?" Emzee mai wuyar sabo ya sami kansa da kwashewa da dariya "Zeezee kuma kamar wani mace, Emzee ne." Ibrahim sai yaji yana son zolayarsa "ni dai kafi min kama da Zeezee haka zan rinka kiranka" "To Surbajo babu damuwa" Hadir yana jinsu yana dariya a hankali musamman da ya ga Ibrahim yaji dadi yana cewa zai fadawa Umma kakarsa cewa yazo garin Fulani an saka masa suna irin nasu. Emzee ya gimtse dariyarsa suka koma gidan. Major ne karshen komawa ya tsaya amsa wayar Awwab da yake ta mita an tafi ba'a jira dawowarsa ba. "Idan kaso ranar da ka dawo a tare dasu zaka kwana babu mai hanaka" Daga daya bangaren Awwab yana kwance a dakinsa na hotel a Austria washegari goman dare zai sake wani trip din zuwa Germany ya shafi habarsa. "Duk dadin ya wuce yanzu. Kun hadu da Ummin?" "Muna rugarsu a Bauchi" Tashi yayi zaune da murnarsa "ta tuna ni Daddy?" "Kai ta fara tambaya" Wani sanyi yaji a ransa don Allah ne shaida bai taba mantawa dasu ba musamman ita Mairama mamansa ta biyu. Karshen haduwarsu ranar da duka su ukun suke ta kuka daga karshe ya gane halin da nasa mahaifin yake ciki. A wurinsa yaji rasuwar babansa Zayyan mutumin da yake matukar so. "Daddy Alheran fa?" "Ita ma baka manta da ita ba?" Dariya yayi, a shekara goma watanni ne babu tsakaninsu. Babban abinda yafi tunawa da ita shine fada da kuka. Sauran kuwa sai abinda Ummi ta bashi labari. Da kuma hotuna da ta nuna masa nasu lokacin suna tare. Tabon inda ta taba yakushinsa yayi dan siririn layi mai dan duhu daga gefen girarsa ya taba. "Ban manta ta ba Daddy. Ko za ka bawa Ummin waya?" "Ka kira ta Mami sai ta hadaku" ********** Duhun dare ya soma kawo rashin wuta ya sa aka kunna fitilun kwai guda uku aka ajiye a tsakar gidan. Bishiyar tana kada musu iska daidai gwargwado aka zauna mayar da zancen yadda kowa yayi rayuwarsa bayan rabuwa. Wannan karon Innawuro ce ta cewa yaran su tafi gidan Baffa Gide saboda kula da tayi hirar tasu mai taba zuciya ce. Radhiya tace su taho kowa ya tashi kamar gaske. Suna fita bakin kofar Zayyana tace da Fauziyya "nan gidan basu da wurin da zamu buya" "A buya kuma, kunyi gamo ne a hanya?" Radhiya ta tambaya tana waige. Murmushi Zahra tayi yanzu an girma suna jin kunya. Ibrahim kuwa sai yace "kinga magana zasuyi mai mahimmanci idan bamu tsaya munji ba wallahi za'ayi ba mu" Haba Radhiya ta rike tana jinjina kai "Allah ko? To amma zunubin laben wa za'a rubutawa a cikinmu? Ni dai shekarata goma sha tara da sauran kuruciyata." Fauziya da Zahra har Ibrahim sai dariya. Emzee da ya saba shi kam bai ga komai ba. Salati suka ji Inmawuro tayi da karfi tana kuka gabadayansu babu babba babu yaro suka dawo suka tsaya a siririyar hanyar karasa shiga cikin gidan. Duhu da girman maganganun suka hana a gano su. Duk da sun ji yadda iyalin Major da na Hadir suka kare a Kano bai hanasu sake kokawa iyayensu ba. Jin labarin da Mairama ta bayar a karon farko a rayuwarta ta fadi yanayin zaman gidan mahaifinta. Tayi haka ba don ta tona masa asiri ba sai don su Mami su fahimci ainihin yadda al'amura suka kasance mata. Ga wanda bai san Malamijo ba sai a suna bazaka taba hangowa jikokinsa ma talauci da kuncin rayuwa ba. Dabbobinsa tarin arziki ne da shi kansa bai san dashi ba. Ko shanu ashirin ya sayar a yadda suke da girma kosassu zai iya ajiye abincin shekara a gidansa kuma su wadata da abubuwa da dama da bai taba tunanin ya basu ba. "Abinda ban fahimta ba Ummin Awwab shin gidan da Zayyan ya gina a Kano me ya faru dashi?" Major ya tambayeta Jan numfashi Hadir yayi da karfi sai da suka kalle shi. Rashin damar bawa Mairama takardun nan kusan shine ya haddasa masa hawan jini. Bai ma san ko Zayyan ya bata na wurinsa ba. Shi dai burinsa wadda aka bashi ajiya ya sadar da ita ga masu hakkinta. Takardun suna cikin wani akwatinsa da yake tunanin babu wanda ya taba bude shi tunda ya koma gida. A nutse ta warware musu komai da ya wakana tsakaninta da Maikudi. Kunya kuwa ta kama Badaru kamar ya bace daga wurin saboda abinda yayansa ya aikawa matar kaninsu. Major rai ya kara baci ba don duhu ba sai an ga jijiyoyin kansa da suka dago. Mami tace "Wallahi mutumin nan sai munyi da gaske. Ta kowace fuska da zai toshe miki jindadi sai da yabi. Mu fa aure yace kinyi kuma baki haifi dan cikinki da rai ba sannan Radhiya tana hannunsa shine muke aikata mata kudin makaranta ta hannunsa" "Banten uba" Radhiya tace a harzuke tana kumfar baka daga inda suke tsaye. Hanyar shiga ciki tayi Emzee da Zahra suka rikota. Idanu sun rufe ta shiga kokawar fuzgewa "ku cikani" Zainab suka gani a gabansu suna sunkuyar da kai kasa tace duk su dawo su zauna tunda annobar labe ta kamasu. "Ban hanaki wannan zagin ba" Mairama tace da Radhiya cikin fada. "Ai wallahi Ummi sai dai fa kiyi hakuri yau daya dai. Hmmm gaya miki ne banyi ba da idan munje hutu fa duk inda ya ganni sai ya rankwasheni ko ya makeni. Inata hakuri, inata hakuri. Wata rana yana rankwashina na tafi a gabansa na dauki Bushira lokacin tana karama na maka ta da kasa. Shine fa ya dena dukana. Yo ashe harda ke bai kyale ba" "Ya isa haka Radhiya kiyi hakuri tunda magana ta fito ba zamu bar masa hakkin marayu ba" Mami tace da sigar lallashi. "Uhmhum" kawai ta amsa ba don ta hakura ba. Badaru ya ari baki ya basu hakuri sannan ya kara da cewa "dole ne na sake neman su mutanen Nijar din. Bana yi musu zaton wadanda rasuwar Zayyan zata sanya su watsar da iyalinsa. Allah Yasa su din ma ba wani abin yaje ya fada musu ba. Don ni yanzu lamarin nasa ya fara bani tsoro kuma." Sunje sunyi sallar isha sun dawo sai ga yara biyar suka shigo gidan a tare rike da kwanukan abinci. Biyu yaran babban dan Innawuro ne sauran ukun kuma na mai binsa mace. Tun a masallaci lokacin Magariba Ardo ya sanar da dan nasa da kuma mijin 'yar suna da baki ayi abinci na gani na fada. Farantai da cokula Radhiya ta dauko sai ruwan sanyi da aka aiki Emzee ya siyo a wani shago daga bakin titi Ibrahim ya bishi. Anci an sha hira taki karewa Innawuro ta sa Radhiya da Emzee tayata gyaran dakunan saukar baki. Su Mami da ko baa fada ba da Mairama zasu kwana. Badaru, Major da Hadir Baffa Gide yazo ya tafi dasu gidansa. Ibrahim da Emzee a dakin Emzee din da yake daga hanyar waje. Sai 'yan matan su hudu a dakin Innawuro. Dreban da ya kawo su shima an sama masa masauki. Da asuba kaji goma aka yanka domin yi musu abincin safe. A gaban Hadir Major ya fadawa su Baffa da Ardo cewar auren su Zahra ya matsu suna neman izini su tafi da su Mairama zuwa bayan biki. Radhiya da Zayyan kuma a bar masa su zai nema musu makaranta su fara jami'a a. "A yi haka kuwa?" Baffa Gide yace yana kallon Ardo "a son ranmu dai suyi zamansu da yaran a tare damu har Allah Yasa duka suyi aure." "Abinda baffanta Gide ya fada gaskiya ne. Ita ga matsalar idanu ga marayunta gara suna tare damu. Lokaci lokaci idan kun bukaci su zo su kwanan muku biyu sai a turo su" Ransa dama ya bashi da wahala kai tsaye su bari ya daukesu. Sai dai kam yaci alwashin bazai yarda alkawarin da ya daukarwa kansa na cigaba da kula da bayan Zayyan ya tashi ba. Sauran labarin da ya kasa bayyanawa jiya na ainihin yadda Zayyan ya rasu ya fada musu. Baffa Habubakari sai da yayi kuka don tausayi. Cikin damuwa da fami ga gyambon zuciyarsa yace "Bazan taba iya kallon idanun matarsa in bata wannan mummunan labari ba. Tana da hakuri amma ina ganin sai ta tsaneni da iyalina. Yau da nake raye ku ke ganina Allah ne Yayi da sauran kwana na amma Zayyan shine sila." Ya nuna Hadir "wannan bawan Allah da lafiya kalau yake wallahi kunji na rantse zaiyi komai don ganin 'ya'yan Zayyan sun koma karkashin kulawarsa. Sai dai shima lalura ta same shi ne da ya cigaba da kokarin kare rayuwata kamar yadda dan uwansa ya fara. Ku taimaka ku barni na kyautatawa bayan Zayyan sannan kuma na saukewa Hadir nauyin da nasan da yana da lafiya bazai taba bari na dauka ba" Jikkunansu sunyi sanyi da maganganun Major. Ardo ya kira Innawuro yace "kece uwar Mairama kakar 'ya'yanta me zaki ce game da batun da bawan Allahn nan yazo dashi?" Nazari Innawuro ta soma don abun da yake nema ba karami bane. Mairaman da mahaifinta ya gagara rikewa, dan uwan tsohon mijinta ya tozarta ta yaya zasuyi saurin amincewa bare. Idan a gaba gori ya taso ko wani abu makamancinsa fa. Bafillatani duk talaucinsa akwai pride. Basa son zubar da mutumcinsu gaban kowa saboda babu azo aji dadin takasu. "To na amince amma Zayyanu kadai zaku dauka. Dalili kuwa kun dai ga irin halin 'Yar Soja wallahi zama da ita akwai dadi akwai wuya. Mairama kuwa bana son nisa da 'yata ko kadan." Hadir ya kafe Major da ido har ya fahimci so yake ya cigaba da rokonsu. Ai kuwa bai fasa ba yana ta kawo hujjoji. "Kayi hakuri amma indai ka ga 'Yar soja ta bar garin nan to aure ne ya dauketa" Innawuro tace don ta kawo karshen muhawarar. "Na ji na amince" Major ya amsa batare da dogon nazari ba. Baffa Gide ya kalle shi da mamaki "kada kace min aurenta zakayi." Mafita daya ya hango ya kuwa yi amfani da ita "a'a , akwai babban dana Awwab shine nake son aurawa. Dreban jirgin sama ne yana bakin aiki shiyasa bamu zo tare ba." "Lallai da gaske kake, amma bana so ka cuci yaronka da auren dole don a baka yarinya. Kasan yanayin zamani" "Na sani amma ina da yakinin bazai bani kunya ba. Don Allah ku amince. Yanzu ku bari mu tafi dasu har Sakkwato saboda wancan wan Zayyan din. Sai kuma danginsu na uwa dake Nijar su ma ina so na hadasu kafin nan da lokacin bikin" Tsakaninsu da Allah basu da niyar hana shi yaran ko kadan sai dai magana ta gaskiya sunyi masa haka ne domin kada nan gaba a raina musu. Da mutumcinsu da rufin asirinsu ya nemi daukar yaran ba wai talauci ko maula ya kaisu ba. Sun kara jinjinawa Marigayi Zayyan domin wannan abu halinsa na kwarai ne ya kawo haka. Idan akwai wani abu na bajinta a rayuwar Mairama da Malamijo ya taba yi bai wuce aura mata dan kwarai irin albarka Zayyan Muhammad Tureta ba. Innawuro da kanta ta fada musu su hada kaya zasu tafi tare suyi musu kwanaki don kowa ya sani hirar jiya da wadda aka sake dorawa yau tayi kadan ta cike gurbin shekarun da suka yi basa tare. Radhiya sai murna nan da nan ta shiga jibgar kaya. Zainab ta ja ta gefe tace mata ta debi kamar biyar biyar nata da na Mairama. "Ni fa na zaci kuna sonmu ne sosai baza ku so muyi kwana kadan ba mu dawo" Tunda suka farka suke cin dariyar Radhiya ashe abin bai kare ba. "Mu kuwa muke son ku Radhiya, ko nima 'Yar sojan zan fara fada ne"z Turo baki tayi "to meyasa kika ce na debi kayan 'yan kadan?" "Kinga muna zuwa zan sa a kaiku wurin tela ayi muku dinkuna masu kyau. Ko da wadannan kayan zaki je bikin Zahra da Fauziyya da za'ayi karshen wata mai zuwa?" Dariya Radhiya tayi kumatunta na dama ya lotsa. "To gidan wa zamu fara zuwa?" "Gidana mana" Mami da take tahowa daga bayansu ta rike baki "sannu maman yara, ashe wayo kike shirin yi min. To ban yarda ba Katsina zamu wuce" Zainab ta mairaice "habaaa Mami, mu da zamu zo biki muyi kwanaki. Ki bari a ya da zango a Kano don Allah" Mairama suka tambaya ina take son fara zuwa tayi murmushi "duk inda mota ta fara tsayawa zan sauka ne." Ta kashe bakin nasu ta barsu da muhawararsu. Wayar Mami aka kira tana dubawa ta ga Awwab ne. Dariya tayi don jiya yayi ta kira bata sani ba. Tana dagawa a kunnen Mairama ta manna wayar. Ko gaisuwa baiyi ba ya fara mita "Kai Mami tun jiya nake kira ki bani Ummi mu gaisa kinki dauka." "To Allah Ya huci zuciyarka dan Ummi" "La ila ha illallahu Ummi kece?" yace yana mai farincikin sake jin muryarta. "Nice Awwab, yaya aiki?" "Lafiya kalau, kinga sun taho sun barni ko" "Kayi hakuri, kana dawowa zaka ganmu in sha Allah" "Ummi ina Alheran?" "Tana can wurinsu Zahra tana damunsu da surutu" Dariya yayi yana imagining yaya ta koma yanzu "ta dena fada ko?" "Awwab kenan baka manta halin nata ba ashe. Sai kazo zaka ganewa kanka." "To Ummi don Allah kice Mami ta turo min numbar da zan rinka samunki. Ki gaishe min da Alheran" Mami ta bawa wayar ya shiga tambayarta wai yaya girman Alheran yake yanzu don tsaraba yake son yi musu ita da Umminsa, Anti Zainab da Ibrahim. "Kai kana fa da wani kanin Zayyan sunansa. Dama mun rabu Ummin taka ta kusa haihuwa" Mamaki da jindadi suka baibaye shi nan yayi musu sallama zai fita. Suma aka gama shiri suka rankaya sai Katsinan Dikko. ********** Mairama ta rasa wa zata goyi baya tsakanin Mami da Zainab. Gobe su Zainab zasu koma Kano bayan sun zo sunyi kwanaki uku a Katsina. Gidan kullum cikin hayaniya yake sun taru sun gama gyara shi an saka komai a muhallinsa. "Gaskiya Mami wannan fa amfani da girmanki kike yi kina yi min wayo. Ki bar min 'yan matan nan muje suyi sati. Aure fa zasu yi ina ni ina sake cewa su zo su kwanar min" "Ai ban hanaki ba, Radhiya ce na hana" "Ummin Awwab kice wani abu mana" "Ni ban san yaushe kuka koma haka ba. Ina nan bacci zanyi wadda tayi nasara ta tasheni. Idan zama ne na zauna. Idan kuma Kano ce tayi kira a hada min kaya" Dariya ta basu daga baya dai an yanke Zainab zata tafi da 'yan mata kuma mazan ma ko don Hadir dole su bita. Mairama ce zata rage tare da Mami. Taron mata ne a kitchen su Zahra na girki Radhiya na koyo. "Kunsan nima mai aikacin asibiti zan aura a Bauchi zan zauna. Gara na koya kada aji kunya wata rana" Emzee da yake shan ruwa sai da ya kware da yaji me take cewa "Adda saurayi gareki bamu sani ba?" Daure fuska tayi zai bata kunya a gaban mutane "fata nagari lamiri yaro...meye aibu don nayi fatan auren likita?" Ibrahim ya rinka mata wani kallo kafin yasa dariya "na gama harbo jirgin naki. Wato dai wani ma aikacin asibiti kike so" "Hhhhhh Adda Kawu Zakari kike so hala? Shi kadai na sani a asibiti" Yadda tayi da fuska ya karasa fallasata. Suka taru ana tsokanarta, Emzee yace wannan labari duk rugar Barkindo sai ya tona. Tun tana da bakin ramawa ta gaji ta watsar ta fita ta koma daki. Zayyana ta samu tana busar da gashinta da ta wanke da hand dryer. Sai ta dena fushin hankalinta yayi gaba. "Shi kuma wannan ya sunansa Zayyana?" "Hand dryer, kema ki wanke kanki sai na busar miki. Mai kitso zata zo an turota daga gidan Alh Baba" Tsit Radhiya tayi kamar ruwa ya cinyeta. Zayyana tayi tayi tace bazata wanke ba kanta babu datti. Da su Fauziyya suka shigo Zayyana ta fada musu. Radhiya ta galla mata harara "kinga ki fita idona, ina ruwanki don naki wankewa ba kaina bane?" Zayyana ta mike a fusace ta fita "kuma sai na fadaki da Daddy" "Sannu shasshaka uwar narkewa, shagwabar nan nima na iya. Kuma bazan wanke kan ba" "Dama masu gashi bakwa son bude kai fa. Shiyasa kullum kina cikin hijabi" inji Fauziyya. Zayyana kuwa tana kai karar Radhiya wurin Daddy ashe Mairama ta jiyo yana cewa a fada mata yace ta wanke shi zai bada kudin kitson. Idan kuma taki wankewa a gida zai bada kudin salon. "Daddy fada fa zaka yi mata, kara na kawo" "Yi hakuri Zayyana ai ko ni bazan taba Alheran ba." Harda guntun hawayenta tace "kafi sonta akaina" Ibrahim yana gefensu yace "Daddy ka barni na dan saita yarinyar nan mana." "Taron dangi zaku yiwa auta. To a kira min Alheran yau sai an wanke kan nan" Mairama tana ji ta tabo Mami "taimaka ki hana wankin kan nan wallahi idan suka bude mata kai gidan nan yau ba lafiya" Mami ta tashi da sauri duk da bata san ko meye matsalar ba. Tana zuwa Zayyana ta kai rahoton Daddy. Dama su Zahra sun matsu su ga gashinta saboda na Mairama da suke gani mai tsaho sosai. Duk sun dauki abin nata wasa suka danneta aka cire dankwalin suna cewa yau sai sun ga gashin da take boyewa. ********** Shiri Awwab yake da sauri sauri yau kadai yake da damar fita yayi sayayyar da zaiyi gobe ya taho Nigeria. Tun dare yake tunanin me zai saya ya kai musu ya rasa. Ba sabawa yayi da irin wannan abubuwan na mata yayi ba. Dan tunani yayi ya dauki waya ya kira wadda yasan za ta bashi shawara mai kyau. Ringing biyu ta dauka kamar jira take dama. A shagwabe ta soma magana tana korafin rashin kiranta da yayi har na kwana biyu. "Sorry my G aiki ne" "Lokacin aiki daban nawa ma daban" Ghazalatu ta sake narke masa. "Naji nayi laifi shiyasa ma ticket din Abuja na saya don na fara ganinki kafin na wuce gida" Ihun da tayi sai da ya cire wayar daga kunnensa yana dariya. Yana matukar son Ghazalatu. Ita ta nemi su boye soyayyarsu ma sai ta gama degree dinta idan ba haka ba aure za'ayi mata a gida ta sani. Yanzu wata biyu da yin final exam bautar kasa take jira. Sun gama tsarinsu idan Awwab ya dawo zasu gabatarwa da iyayensu da abinda ke tsakaninsu. Sun taba hira don ta dena fushin tunda taji zai taho washegari. "G albishirinki" "Goro kyakkyawa kamar Yayana" "Su Mami sun je gidan Ummin nan nawa da nake baki labari" Yadda taji yana murna dole ta taya shi ba don ta damu ba. Yayi ta fada mata ashe harda kani an yiwa Alheran. "Na tayaka murna, zan so ganinta gaskiya" "Ki bini Katsina mana idan na zo" Dadi taji tayi saurin amincewa. Awwab bai kyaleta ba yace "kune sarakan tsaraba, me kike ganin zai dace da yarinya about 18 to 19 years" "Friend kayi mace har kake fada min za kayi mata siyayya?" Tace cikin fushi da kishi. "Nope, Alheran nake son sayawa wani abu" Duk da haka ranta baiyi mata dadi ba amma bata son bata masa rai yanzu sai yace ya fasa tsayawa a Abujan. "Ka saya mata takalmi, jaka, turare, kayan kwalliya da jewelleries" Yaji kayan da yawa to amma so yake ya yi musu abin bajinta "thanks dear" yace da Ghazalatu kafin ya ajiye wayar. [02/11 7:30 AM] My 2nd Mtn: 22. Iyakar karfinta tasa suna jan hijabin nata su ma suna ja. Mami na isowa tace su dagata amma an makara don Zahra tayi nasarar cire dankwalin. Emzee da Ibrahim suna bakin kofa don sun jiyo hayaniya daga dakin. Rasa me bakin magana akayi harda Mami kuwa. Zainab ce ta kawo Mairama dakin, tunda taji shiru tasan aikin gama ya gama. Zayyana ce ta fara dariya gashi ya soma lekowa amma saboda makero baifi a kirga ba sai wani uban fari fari kamar amosani kamar kora. Kullum tana shafa mai idan tayi wanka amma yau saboda da mutane a dakin ta hakura ta daure kayanta. Kowa ta kalla gimtse dariya yake ta harzuka sosai tayi kan Zahra tana ihu "wallahi sai na rama" "KE! Samu wuri ki zauna kada naji kinyi fada da kowa." Kuka ta fashe dashi da karfi "wallahi Ummi kada ki cuceni ki barni na rama." "Zahra bata dankwalinta kafin na saba muku. Wane irin abu ne haka da girmanku saboda Allah." Mami ta soma fada. Jefa mata dankwalin Zahra tayi don yadda take kallonta kamar kura ta ga nama bazata so hannunsu ya gogi na juna ba. Jikinsu sai yayi sanyi saboda kukan da take yi ta dauki dankwalinta ta kulle kan sannan ta mayar da hijabinta. Zainab da Mami na bata hakuri taki kula kowa sai sautin kuka da take karawa. Mairama tace su kyaleta ba shiru zata yi ba. Kowa ya fita daga dakin tana zaune tana kukanta dole Mami taje ta fadawa Major. "A kirawo min ita" Zahra ta kalli Fauziyya, a, tsorace tace "ba dai ni ba, kece babba kuma ke kika bude mata kan" "Zayyana...." Zahra ta soma kira ta bari saboda kyabe fuskar da ta ga tayi ta koma gefen Major tana cewa "Daddy kace bazani ba" "Mazaje waye zai kira min 'yata?" Yace da Ibrahim da Emzee kamar yana rokonsu. Ibrahim ne ya tashi, Emzee kamar ruwa ya cinye shi. Yana zuwa ya sameta ta gama hada kayanta a cikin jakar da tazo da ita tana bakin kofa zata fito. "Dariya ka dawo yi?" "Daddy ne yake kiranki" Gani tayi ya tsaya kallonta yaki tafiya ta zaro masa idanu "in sake bude maka ka gani da kyau ne?" Murmushi yayi mata kawai don idan ya sake ya bude baki sai ta saka shi dariyar da baiyi niyya ba. Sai yanzu ya gane meyasa kan nata yake kullum a daure kamar mai tallan magani. Da jakarta a hannu ta shiga su Zahra suka fara kuskus. Daddy ya gani sai ya shareta "waye ya saka ki kuka?" Rage tsayi tayi bakin nan a gaba kowa ya ganta yasan an tabota karshe "Daddy na san komai fa, kaine da kanka ka turo Zayyana su gane min aski na" Kafin su shigo sai da Mami ta roke shi akan ya taimaka kada yayi dariya. An san soja da dakiya, amma a cikin iyalansu, iyalan ma na Zayyanunsa mantawa yake ya taba zama soja. Ya fi fahimtar ya sake tare dasu ya nuna musu shi uba ne a garesu domin kada a sami wani shamaki tsakaninsu. "Cewa nayi ace ki wanke kanki fa 'Yar soja uwar sojoji" Sai da tayi murmushin jindadin kirarin ta sake daurewa "a bani kudin mota in tafi gida ko kuma a barni na rama" "Radhiya kiyi hakuri da kaina zanyi punishing dinsu. Amma ki bar zancen ramuwa ko tafiya gida" Mami tace tana hararar bangaren da su Zahra suke. Kumbura baki tayi "ni dai wallahi sai dai a zabi daya" Mairama taji kunyar kada a fara ganin ko harda sakacin tarbiya a halayen Radhiya. Fada ta soma yi mata tace ta tashi ta koma ciki ta zauna. "Allah Yasa naji kinyi fada da wani, zaki ga yadda zanyi dake. Ana lallabaki kina wani botsarewa mutane" "Laifinsu ne fa ki kyaleta, zo nan kinji Radhiya" Kin tashi tayi tana kallon Zainab din tace "kema Mama na ga kamar kin danyi dariya da aka bude kan" Mairama ta sake fusata Daddy yace duk suyi hakuri laifinsa ne amma tayi hakuri. "Ku kuma manyan ku daku kuna tsokanarta na kusa bata kambun girma a gidan nan. Kwanannan zata zama yayar kowa da kowa a cikinku sai na ga wanda zai sake gane mata askinta" murmushi yayi amma bata ji haushi ba tunda ya yi mata alkawarin zata zama yayar kowa. Da yake ba riko gareta ba sai ta saki fuska ta harari wannan ta harari wancan "kun dai ji me Daddy yace, kuma daga nan ma soja zai kaini abuna. Hahaha idan na dawo gidan nan za'a ga kawuna" Zayyana sai tasa hannu ta rike nata kan tana kallonta a tsorace "yanke mana kai zaki yi?" "Inaaa yarinya kan Balotelli zanyi muku in huce haushin yau" Ibrahim ya tuntsire da dariya harda fadowa daga kan kujera. Zainab ta daka masa duka a baya ko a jikinsa sai dariya yake "zan rike miki su 'yar uwa, ai dai baki ganni ina dariya ba" Major ma dariyar yake yadda ta hakikance abinta. Sauran matan babu wadda ta damu da ball ko 'yan ball balle su fahimci me take nufi da Balotelli din. Hakuri dai yayi ta bata tana kara jaddada masa burinta na zama soja tunda ta ga yana lallabata. "Soja mai babban mukami zanyi miki amma ta cikin gida, yanzu dai ku tashi amma idan kun shiga ciki kada ki kula kowa" "Daddy gaba fa kenan?" Tace tana ware idanunta ta rike haba. Su Zainab sai dariya, Major ya dage yana ta bayanin cewa ba gaba yake nufi ba. Kada ta kula su dai azo ana rigima. "Au ho...ai na hakura tunda idan na dawo daga soja zan dauki mataki. Baba zanyi kyau da soja ko?" Tace tana kallon Hadir. Kai ya gyada mata yana murmushi. Hannunsa taje ta rike tana durkushe a gabansa ita dai tana son sa sosai, sai da Daddy yace ta bi bayan 'yan uwanta zaiyi magana da iyayenta ta fita. Da taje dakin daga bakin kofa ta wulla jakarta ciki sai gasu suna darewa da sauri don ba karamin tsoro ta basu ba. Wata shu'umar dariya tayi wani abu ma sai an dawo daga makarantar sojoji. Babu wadda ta tanka mata ta shigo ta haye gado ta kwanta. Wayar Zahra aka kira ashe Awwab ne ya ya tambayeta size din takalmin Radhiya saboda yasan suna gidan. Kintata kawai tayi ta fada masa saboda ita dai bazata tambayeta ba a yau dai sannan a gabanta bazata taba mata takalmi ba don tsoron me zai faru take ji. A falon Daddy kuwa bayan fitarsu Mairama ta shiga basu hakurin halayyar Radhiya. Gani take kamar laifinta ne ko sakacin tarbiya ne ya kawo hakan. "Kowane da da irin halayensa da dabi'u da ake haihuwarsa dashi. Kuma yadda take dinnan Allah kadai Yasan wace irin tarin baiwa Yayi mata. Ki dena damun kaki watarana zaki ga kamar ba'ayi ba" Mami ce da wannan dogon jawabi sauran suna gyada kai. Daddy ya bijoro musu da zancen da sukayi da su Ardo. "Hada Awwab da kanwarsa abu ne da na kudurta tun ranar da na dora ido a kanta. Hadir ya amince ina fata Allah Yasa ku ma ku bani goyon baya" Gabadaya matan nan uku bakunansu murmushin jindadi suke nunawa. Mami tana maraba da wannan hadin domin bazata taba kyamar tsatson Mairama da Zayyan ba. Tafi kowa sanin mahimmancin yin hakan a wurin mijinta. Zai kara sakawa yaji a ransa cewa bai ya da iyalan Zayyan din ba. Ya so Zayyan tun basu saba ba duk ranar da suka je training zata kwana yana bata labarin fitinannen basakkwacen nan. Lokaci kalilan ne Radhiya zata waye tayi zarra cikin sa'anni. Zainab ma taji dadi don burinta su hadu su baiwa Mairama da 'ya'yanta dukkan farincikin da suka rasa. Allah Ya sani ba don sa'anni suke da Ibrahim har ta bashi watanni ba itama da zata so hadasu ne. Farincikin Mairama yafi na kowa. Wadannan mutane masu dimbin karamci a gareta ace babu kyamar yadda su suka kara wayewa ita da 'ya'yanta suka sake ci baya ta fannin wayewa da sanin ababen rayuwa amma su nemi hada Radhiya da Awwab, Awwab dinta dai wanda ya mayar da ita da mijinta iyaye tun farkon haduwarsu. Hawaye ta shiga yi tana mika godiya garesu. "Bani da bakin godiya, Zainab kunji wani karamcin kuma?" "Idan kina haka sai mu ga kamar a wurinka Radhiya da Zayyan ba namu bane Ummin Awwab" "Haba Mami kada kice haka mana, farinciki ne kawai yayi min yawa" Mami ta tambayi Major "yaushe kake tunanin auren?" "Kuna ganin zamu iya hadawa da na su Zahra? Idan hakan yayi in sha Allahu karshen sati Alh Baba zai dawo daga Umara sai na fada masa" To waye ma zaice baiyi na'am da wannan hadi ba. Bakinsu duk yazo daya, abu guda ya rage a sanar da Alh Baba sai ayi shiri aje a nemi aurenta wurin wadanda ya dace wato dangin mahaifinta na Sakkwato da kuma marikanta ta bangaren uwa su Ardo Barkindo. ********** "Banza jaka bace min da gani ko inyi kwallo dake. Har yau ina tsananin mamakin yadda akayi na kwaso ki Salame" Janye tsumman jikinta tayi da ya gama karewa ya tsotse babu wani tudu a jikinta bayan cikin jikinta na wata shida. Gabadaya ta mokade baka ce Salame bace da tauraruwarta ta taba haskawa a gidan Salisu. Aure dududu bai wuce shekara takwas ba amma haihuwarta biyar ga cikin na shida. Da kyar take tafiya yunwa ta yiwa hanjinta mugun lahani ga yara tun asuba suke kira mata yunwa suna kuka. Ba ta daddara ba ta sake hada hannuwa a gaban Alh Indararo "Alhaji ko naira hamsin ce ka bani don Allah, bani da karfin karbo wankau da bazan tambayeka ba" Kallon kin ma rainani ya jefa mata "sai ki tafi inda kika saba zuwa gidan tsoho aje a ci abinda ya sauwaka" Duk magiya da rokonta ta bayan kunnensa tabi sai da ranta ya baci sosai ta tsaya masa kerere a gaba. Tulun cikinsa kadai ya isa ya tureta dashi ta fadi. "Ka sakeni in koma gidan ubana ai ba a titi aka daura mana aure ba. Wannan wace irin rayuwa ce ace matanka tsakaninka dasu bai wuce ka dirka mana ciki ba. Ci da sha da sutura sai dai mu yiwa kanmu. Ko kunya baka ji duk kudinka. Mune wankau, surfe da duk wani aikin kaskanci don mu ciyar da kanmu da 'ya 'yanmu" Marin da ya zabga mata ne yana faman nade hannun malum malum ya gigita ta ta kasa cigaba da maida martani. "Ki fita idona Salame, wannan jarababben auren naki kuma yanzu muka fara babu inda zaki je" Fuuuu ya fice daga gidan sai dariyar Maman Danmama da ta cika mata kunne. Bata saurara ba sai da ta fito daga dakinta tazo gaban Salame tana mata dariyar mugunta. "Mu dai sai dai muce Allah Ya kara karawa. Ki koma wurin bokanki kice masa kwabarki tayi ruwa. Irin wadannan ranakun tsakaninki da Alhaji su kan sani nishadi da wanke min zuciya. Anyi walkiya Salame mun ganki tsamo tsamo" Dan sauran kuzarin nata na fada marin da ta sha ya tafi dashi, shiyasa ta kasa maidawa Maman Danmama. Ita kuwa batayi shiru ba. "Ohhh ni 'yasu. Kamar ba'ayi zamanin da kike sa Alhaji ya zage ya zanemu a cikin gidan nan ba. Kika dawo kika saka shi sakin kowa banda ni wai na zauna nayi raino kema a gidanku uwargidan babanku aikinta kenan. Ai ance tsafi gaskiyar mai shi. Kinyi kin gama surkullen tazo ta kare miki" Wani dukunkunannen hijabi Salame ta saka taki kula Mama ta fita tare da yaranta ta nufi gida. A soro suka yi kicibus da Malamijo zai fita. Girma ya kara kama shi sai dai akwai kyan jiki tunda babu kiba kuma yanzu ya yarda da ci da sha wa kansa mai kyau a waje. 'Yar fara'ar da ya taho da ita sakamakon faranta masa da amarya tayi kafin ya fito ce ta bace yana ganinta. "Allah Yayi dare gari ya waye an kwaso jiki an taho cin banza. To baki isa ba Salame. Tunda na aurar dake ko dan ihsanin nan na tsakanin da da mahaifi bai taba giftawa tsakaninmu ba sai ma dai ki karkace ki fada min magana idan kinso. Amma 'yan kwanakin nan kullum ana fada min sai kinzo, kuma ba kya tashi zuwa sai kin daidaici an gama abinci. Ki kwaso yara rabe-rabe azo aci bati. To na gaji, ki juya sawunki a likkafa ki koma inda kika fito" Jikinta har bari yake saboda yunwar dake sasakarta fushi da maidawa mahaifinta martani ba nata bane yau dinnan idan ba so take daga ita har yaran yunwa ta kar su ba. "Ku shige gani nan zuwa" tace tana kadasu ciki. "Ya ina cewa ku koma kina turasu? Salame, Salame ki kiyayeni." Yace yana nunata da yatsa. "Gaisawa kawai zanyi dasu mu tafi" Tausayinta ya dan ji saboda ya tabbatar yadda ta fige dinnan tabbas kila mijin da har shi take iya yiwa rashin kunya a kansa ya juya mata baya ne. "Jeki amma daga yau na sake ganinki zanje na sami Alh Indararon inji ko har ya cinye sadakinsa ne shiyasa zamu fara raba nauyin. Mairama ma da take ruga ta fiki abin arziki. Makanta, rashin miji da nisa basu hanata yi min alheri ba." Kunci taji ya ziyarci zuciyarta saboda ya ambaci kamwarta da ta mayar kishiyarta ta karfin tsiya. Duk ita ce silar komai tunda dalilinta taje wurin boka aka rabata da Alh Indararo saboda kawai bata son ta ga tayi gaba ta barta ba wai don ita din sonsa take yi ba. Da asiri ta rinka cin galaba akansa da matansa komai na tafiya daidai ta kuma saki jiki tana ta haihuwa don ta tara magada sosai. Cikin jikinta na da wata biyu bokan nata yace ga garinku. Shikenan duniya tayi mata atishawar 'yan tsaki. Komai ya lalace wai ita da take mulkin gidan a tsakar gida Alh Indararo ya kalleta yace yaushe ya aurota. Da bakinsa yake cewa ina Mairama kanwarta. Rai a bace ta shige ta ce da yaranta su taso su tafi. "Ki barsu yanzu zan zuba musu abinci Salame" Yadikko tace mata tana kallonta da tausayawa. Ko bata ce komai ba kana kallonta kasan akwai yunwa daga ita har yaran. "Tafiya zamuyi, kai ku tashi mana" "Umma ki bari muci abinci" babbar 'yarta tace idonta cike da kwalla. "Ko ku tashi ko jikinku ya gaya muku ku duka. Aikin banza kai." Duk yadda Yadikko taso kin zama tayi saboda kawai an yabi Mairama ta gwammace su sake kwana da yunwa. ********** Karfe biyar da rabi Awwab ya sauka a Nnamdi Azikiwe International Airport da yake birnin tarayya. Ya saba tafiye tafiyensa babu wasu kaya sai 'yar jaka karama da yake saka kayan sakawa biyu ko uku ya danganta da kwana nawa zaiyi a garin. Wannan karon kuwa sai da ya hado da akwati mai kyau na turawa dan madaidaici. Jin kansa yake wasai babu tarin gajiyar nan saboda a fasinja ya taho ba pilot ba, tun daga tasowarsu sai minti goma kafin saukar jirgin ya farka. [02/11 7:30 AM] My 2nd Mtn: 23. Ruwa yaje ya watsawa fuskarsa yayi brush sannan ya dauko wani karamin hankici kamar tawul iya tafin hannunsa ya goge fuskar. Komawa yayi ya zauna yana jin kansa yayi wani fresh balle da ya tuna mutanen da zai gani. Kayataccen murmushi yayi shi kadai wata matashiya da suke zaune tare ta maida masa saboda ya dan fuskanceta ne yana laluben seat belt dinsa. "Hi handsome" tace dashi da ingantaccen turancinta. Sai da ya waiga bayansa ya tabbatar babu kowa sannan ya nuna kansa sai ta gyada kai. "Hello" ya maida mata da kyar don baya son mace mara kamun kai. Da ace magana tayi masa kawai bazai damu ba. Amma idan kaji ana handsome ko beautiful ai kasan kwanan zancen. "Kaima bahaushe ne ko?" Baiyi mamakin da ta gane ba tunda suna zama ya soma waya bai dena ba sai da yaga jirgin ya fara tafiya. "Kema haka ko?" Murmushi tayi, a rayuwarta tana son namiji mai kaurin murya. Ba da karfi ya amsa mata ba amma amon muryar ya isa ya sanya mata da yawa muradin son kasancewa da mai ita musamman idan suka hado dashi. Wankan tarwada, dogo, hanci madaidaici da ya dace da kyakkyawar fuskarsa. "Na kula baka ci komai ba tun tasowarmu." Bai wani kare mata kallo ba yace "bana jin yunwa ne" So take hirar ta tsawaita don tunda ta dora idanu a kansa zuciyarta bata kara samun sauki ba. Ta kula mutumin kamar yana da ji da kai sai dai kuma bazata bari shan kamshinsa ya hanata samun abinda take so ba. Dawowarta kenan daga Germany inda taje hutu wurin yayarta. Mahaifinta tsohon soja ne da ya tsunduma siyasa tun lokacin mulkin farar hula. Yanzu haka sanata ne da yake wakiltar mazabarsu a jihar Plateau. "Suna na Arifah" "Awwab" Daga haka ya kafa waya a kunne don tuni sun sauka an bada damar kowa ya tashi. Cikin cabin crew din wata 'yar Nigeria da tasan Awwab tazo suna gaisawa da ya tashi zai dauki jakarsa. "Captain yau fa ka yi mana wayo. Kasha bacci ka barmu da aiki" Sai yanzu Arifah ta ga ya sake sakin fuska harda dariya "ki dauki hutu kema sai mu koma tare. Yanzu ina da wata guda na mantawa da kowa sai family dina" 'Yar hira suka taba sannan suka yi sallama. Awwab na fita Arifah ta bi bayan matar da suka gaisa mai suna Chisom ta roketa numbar wayarsa. "Ki bishi ya baki da kansa, Captain Awwab baya son irin haka don an taba yi masa na gani" Marairaicewa tayi tana fada mata yadda take son shi tare da rokon ta taimaka mata. Kudi ta dauko daga jakarta za ta mika mata Chisom ta bata rai "ba sai kin sayeni ba, Awwab is a nice man ga number dinsa ki gwada sa'arki" Arifah kamar ta zuba ruwa a kasa tasha ta rubuce number din da ta karanto mata daga wayarta ta fita da sauri ko zata sake samunsa sai dai yayi mata nisa bata ma san ina yayi ba. Bata da damuwa tunda akwai numbar da zata same shi. Yana fitowa waje hasken rana ya kwale a sama kamar ba shida ke neman yi ba. Jacket dinsa ya cire ya sakale a hannunsa ya jana jan akwatinsa. Kamar ance ya kalli hagunsa suka hada ido da Ghazalatu. Taci kwalliya sosai don ta burge shi ta kuwa yi nasarar sanya shi murmushi. Daga ita sai dreba suka zo daukarsa kannenta suna makaranta. "Yayana" tace da ya zagayo wurin motar tana murmushi. "My G kinyi kyau fa" "Ba wani nan, kai dai kawai ka dade baka ganni bane" Gaisawa yayi da dreban ya shiga gaba ita kadai a baya suna ta hira. Ji take kamar ya dawo bayan motar su zauna tare. Ta rasa gane masa ne ana soyayya amma shi tamkar wanda ya taso a kauye. Baya irin yadda wayayyu suke yi. Ko gidansu taje hutu haka zata karaci zamanta hannu wannan bai san ya rike mata ba ko da su kadai suka fita. Yanzu wata hudu rabon da ya ganta amma simple hug ma su ji dumin juna ya gagara. Waya ya rinka yi a rabin tafiyar saboda tazarar airport din da cikin gari. Mami ta fada masa su Alheran suna Kano amma Ummi tana tare dasu. "In sha Allahu gobe asubanci zanyi zuwa Katsina. Sai na ga Ummi zanje wurinsu. Uhmm Mami tare zamu taho da Ghazalatu fa" "Jiya Gambo ta fada min, sai kun iso. Jirgi zaku biyo?" "Gamu nan dai sai abinda Mummy tace" Sunyi sallama Ghazalatu ta rankwafa daidai kansa yana jin numfashinta a kunnuwansa da wuya. "Daga kanki G" yace yana yin gaba da kansa saboda yadda yake ji. Komawa tayi ta gyara zamanta "na daga shikenan, dama tambayarka zanyi ko kayi min tsaraba nima kamar kowa" "Su waye kowa?" "Yarinyar da ka tambayeni jiya me zaka saya mata" "Allah Yasa ba kishi kike yi da yarinyar da ni dake duk bamu gani ba" yace yana dariya. "Akwai dalilin da zanyi kishinta ne?" "Ko kadan, please kada muyi abinda muka saba daga zuwana. A bar maganar haka ko." Bata sake cewa komai ba har suka isa gida. Mummy Gambo tasa an hada masa kayan tarbar babban bako. Ranar da daddare da kansa ya sanar da ita abinda ke tsakaninsa da Ghazalatu. Gambo tayi murna sosai tana ta dokin maganar ta kai kunnen Hassana wato Mami. Abu ne da ya shafi dangi gabadaya ta bangarensu da bangaren mazajensu. Ga Awwab din da shiga rai dole taji dadin wannan hadi. ********** Harun mahaifin Ghazalatu da ne ga Alh Baba. Babansu Mami kaninsa ne na uku yayin da baban Major ya kasance autansu. Harun ne ya biyawa Alhajinsu umara suka tafi tare. Mutumci, shakuwa da kyakkyawar alakar dake tsakaninsa da Major tasa ya kaishi Germany gashi yanzu shi ma ya tsaya da kafarsa. Major bashi da wani abokin shawara a dangi kamar Harun shiyasa a daren ranar da ya sanar dasu Mami game da hadin Awwab da Alheran ya kira shi ya fada masa. "Gaskiya kayi tunani mai kyau ko babu komai yanzu zaka fi ji a ranka cewa ka rike iyalin bawan Allahn nan. Allah Ya gafarta masa Ya nuna mana lokacin" "Amin Harun" "Zan fara yiwa Alh Baba maganar yadda muna dawowa za'a je neman aure. Bikin su Zahra duka duka baifi wata daya ba kuma gashi kace gara a hada" "Gara a hada din muma sai mu sami sauki" "Hakane, ga 'yarka can Ghazalatu ta tsaya ruwan ido da ta fitar itama ba sai muyi komai mu gama lokaci guda ba" "Barni da ita, gobe suna hanya ita da Awwab zan binciketa ko akwai wani" Hirarsu suka yi irin na 'yan uwantaka suna kulla shawarwari game da yadda bikin zai kasance. Washegari Awwab ya sauka a garin nasu cike da tsantsar farinciki ya rinka sallama a kofar dakin Mami. Tana sane wai sai ta ja masa rai taki amsawa. "Mami manaaaa" Dariya tayi "shigo dai ba don halinka ba" Da saurinsa ya bude kofar idanunsa suka sauka akan Umminsa Mairama maman Alheran. Murmushi take ta yi masa daga inda take zaune wai wannan muryar Awwab ce. Shi kuwa wani dumi yaji a idonsa da sauri ya karasa gabanta ya riko duka hannayenta biyu ya dago kai yana kallon fuskarta. "Ummi" Da hannunta daya take bin fuskarsa tana shafawa "Awwab kaine ka zama babban mutum haka" Mami tana gefe tana murmushin jindadi Ghazalatu kuma ta coge a bakin kofa. "Ummina kina lafiya? Kin rinka tunawa dani kuwa" yace yana matse hannuwanta cikin nasa. Yau gashi da Umminsa abinda ya dade da cire rai saboda yadda shekaru suke ta yawaita. Hawaye ta soma yi "ban taba mantawa daku ba Awwab. Ina ma zan iya ganinka da kyau in gani ko wannan tsayin kamar bulala ka dan cike shi da tsoka" A razane ya kalli Mami sai ya ga tana hawaye. Hannunsa yasa yana yawo dashi a gaban idanunta ya ga ko gezau. Awwab kasa mallakar kansa yayi ya kifa kansa a cinyarta yana kuka. "Kaji mutum kamar ba namiji ba, meye na kukan? Ai komai ya wuce da yardar Allah" Hawaye yake da gaske yaji bazai iya zama ba ya tashi ya nufi inda yasan nan ne dakinsa. Mami tace da Mairama ta dena damuwa zai hakura kamar kowa. Ghazalatu ko shiga dakin bata yi ba ranta ya baci da kukan da wannan makauniyar ta saka mata shi. A take taji wani haushin Mairama ya kamata. Dama akan wannan da kallo daya zai sanar da mutum daga kauye take yake ta damuwa harda kuka. "Ghazalatu shigo mana, kinga yayanki na kuka ko? Kada ki damu zanyi masa magana" Ba yadda ta iya dole ta shiga tana nadamar tahowa don gidan har ya fice mata daga rai. Akwatinta ta tura gefe sai da Mami tace "ga Ummin Awwab ki gaisheta mana" "Sannu" "Yauwa sannu 'yata. Yaya gajiyar hanya?" Mugun kallon da Mami ta watsa mata ya sa ta chanja salon gaisuwar tace "ina wuni" a dakile. Ba jimawa Mairama ta shiga bandaki ai kuwa Mami rai a bace ta soma yiwa Ghazalatu fada. "Kar ki yarda na sake ganin irin haka kina jina? Wannan matar da kike gani ba karamar daraja da kima gareta a wurinmu ba. Dangi kowa kokari yake ya tayamu karramata. Bazan lamuncewa dabi'ar banza ba kinzo kina wani cin magan" Abinka da makaho kunne ya kara fikewa. Mairama tana jinsu tayi murmushi kawai. To dama yaushe zata yi tunanin kowa nasu zai sota. Ita ce fa wadda mahaifinta har yau bai taba bin sawunta ba sai dai ita har sau uku taje kuma tana aika masa da 'yan abinda ba'a rasawa. "Kiyi hakuru gajiyar hanya ce" Ghazalatu tace da ta tuna Mami ce fa mahaifiyar Awwab. "A dai gyara" ********** Fauziyya da Zahra suna kallo a falo Zainab tana duba takardun asibitoci uku da likitann nan ya aiko mata. Ibrahim baya gidan yaje gaishe da kakaninsa Hadir kuwa bacci yake a daki. Radhiya ce ta fito yau babu hijabi tana dan murmushi fuskarta tasha kwalliua harda janbaki. Fauziyya da Zahra suka shiga gyara dankwalayensu. Zayyana daga shiga deban abinci a kitchen ta kasa fitowa tunda taji muryar Radhiya tana cewa. "Ha mutum ya fito yasha iskar Allah." Tana zama su Zahra suka mike, Zainab ta kwashe da dariya. Radhiya ta zama horror tunda tace zata yi musu balotelli. Jiya a gabanta Ibrahim ya nuna musu hoton Mario Balotelli wani dan ball baki na kasar Italy wanda yake kwashe kansa hagu da dama ya bar tsoro guda a tsakiya tun daga gaba har keya. A karkace ta kallesu "tashi kuma zaku yi daga zamana?" "Ni bacci nake ji" cewar Fauziyya "Fitsari zanyi ni kuma" Zahra tace tana matsawa gefe. "To sai kun dawo, gumi ne ya dameni yau na saka lasi" kawai sai ta tuge dankwalinta rantal ya bayyana. Wata irin dariya suka kwashe da ita har Zayyana dake kofar kitchen. Zainab na dago kai ta mayar dashi kan takardu kafin ta soma dariya itama. Radhiya ta bata rai "ayi dariya da kyau naje soja na dawo. Kuma na dena daura dankwali iska zan rinka sha" "Ki rufa mana asiri don Allah ki rufe" Zahra tace idonta harda hawayen ganin wannan gashi na Radhiya tsilli tsilli. "Allah bazan rufe ba iska nazo sha." Kyalesu tayi suka sha dariyarsu tana cewa su kiyaye kada tayi sanadin da zaa kai amare da kwalkwal. Daga nan hira ta kaure don daga Zahran har Fauziyya basu da girman kai duk da ba sa'arsu bace. Suna cikin hira ta soma gyangyadi Zainab tace ta koma daki ta soma musu irin na masu magagi wai ba bacci take ba. Kafin la'asar ta bingire akan doguwar kujera abinta. Ana kiran sallah duka suka watse sai Zayyana. Ta wayar Fauziyya Awwab ya kira yace yana kofar gida don dreban Harun ne ya kawo shi. Zayyana da ta amsa wayar taje ta bude masa gate tana murnar ganinsa. Suna shigowa falo idanunsa suka gane masa Radhiya. Kanta yake iya gani sai rabin jikinta ta rufa dankwalinta daga kasa kuma fuskarta jikin kujera take kallo. Ya dai tabbatar kayan mata ne a jikin mai wannan kan a sanyaye ya karasa shigowa Zainab tana turo Hadir ya kallesu da tausayawa. Da guda daya tilo da suka haifa ashe dan daudu ne jiya da Mami da Ummi suna bashi labarin komai yana kwalla basu hada masa da wannan ba. [02/11 7:30 AM] My 2nd Mtn: 24. Zainab baki yaki rufuwa "Awwab, Masha Allah sannu da zuwa...zauna, zauna kasha hanya" Shi dai murmushi yake yi amma hankalinsa gabadaya yana wurin wannan kan dake kwance akan kujera. Allah ne Ya taimaka Zainab ta kula da me yake kallo tayi saurin dora yatsanta a baki wai yayi shiru. Dankwalin da Radhiya ta rufe kafa dashi shi ta dauka a hankali ta mayar mata dashi kanta. Sai lokacin ya iya dauke ido daga kanta ya mayar garesu. Gaban Hadir yaje ya durkusa ya rike masa hannu yana jin kwalla ta taho masa. "Nasan ka gama jin duk wani labari a wurinsu Mami kuma ka gama kukanka. Kayi hakuri ka saki zuciyarka muyi murnar sake haduwa" Zainab tace tana kallon yadda Awwab din ya koma ingarman matashi. Motsi Radhiya ta soma yi dankwalin yana neman faduwa aka yi sa'a ya zauna. Ita dai Zainab a tsorace take kada ta tashi a hagu su rasa inda zasuyi da ita. "Ina Ibrahim da Zayyan karami?" Yayi tambayar har ransa yana fatan Allah Yasa ba wannan na kwancen da ya kasa tantance waye ba za'a kira da daya daga cikinsu. "Sun fita cikin gari amma nasan suna hanya" Iska ya furzar yana fadada murmushinsa "da gaske? Huhhh Alhamdulillah" Zainab sai tayi tunanin yana murna ne don tace suna hanya. Sake kallon Radhiya yayi shi dai hankalinsa gaskiya bai kwanta da ita ba. Kamar ta san tunanin da yake a kanta kuwa tayi mika ta tashi zaune. Dankwalin ya zamo daidai lokacin da ta sauke idanu akan fuskarshi. Shi ma ita din yake kallo daga sama har kasa don ya tabbatar da jinsinta sai dai fuskarta ta tsaya masa har ya kasa magana. Kai a lailaye ga fuskarta harda janbaki. A hankali idanunsa suka fara saukowa daga fuskar a kokarin kure mata kallo sai ya tsaya cak a wuyanta ya kasa karasawa yana jin wani yanayi da bai saba ba a jikinsa. A hankali ya furtawa kansa "mace ce". Tsuke baki Radhiya tayi tana jin ba don Innawuro ce tayi mata askin nan ba wallahi da abinda zata fara yi idan ta koma rugar Barkindo shine ta sauke mata nata gashin. Waye wannan da ya cika mata ido ta kasa sakin baki a gabansa ya gane mata sirrinta. Motsa bakin ta sake yi ko ihu ne ta kwarma musu amma ta kasa. Kumatunta na dama da yake lotsawa idan tayi yunkurin magana shine ya sake daukar hankalin Awwab ya kuma kallonta da kyau. "Kaddai? Nooo it can't be." Ya nanatawa kansa da sauri. Girgiza kai yayi shi kadai gamo da Radhiya yana nema tafiya da nutsuwa da tunaninsa. Su Fauziyya da suka taho yi masa barka da zuwa kowacce tayi shiru kamar ta hadiyi kota suna jiran su ga me Radhiya za tayi. Dankwali dai gashi nan amma rabin kai a bude yake. Hannunta ta dora a ka taji iya ina ne a bude. Tana ji ta janyo dankwalin a hankali ta tashi bata ce komai ba ta bar falon. Karar kofa suka ji da karfi wadda ta gwara saboda bacin rai. Zainab ta girgiza kai su Zayyana jiki yayi lakwas. Awwab yana lura da yadda suka sauya su duka ya daure yace "Alheran?" Da sigar tambaya yana tsananta addu'a kada ace wannan ce da ta tashi yanzu. Kamar jiransa suke suka bushe da dariya gabadayansu. Alheran din da yaci burin gani har ya kasa zaman Katsina ce. Babu wanda ya tsammaci zuwansa Kano a yau ana tunanin zai zauna ya huta amma doki ya hana. Ghazalatu har fushi tayi ya bata hakuri da alkawarin zai dawo washegari. Kin zama tayi a gidan yayi mata shiru da yawa ta tafi gidan Alh Baba wurin kakarta. "Ita ce ta shige ciki yanzu" Zainab ta bashi amsa da dan murmushinta. Da ba don da kanta ta amsa masa ba zai ce ko wani salon tsokana ne kuma suke yi masa don ansan yadda ya damu da ita kuma ya matsu ya sake haduwa da ita. Da hannu ya nuna hanyar da ta bi ya marairaice fuska "wannan din?" Basu dena dariyar ba kuwa Zainab tace "yau idan kuka shiga hannunta ko kafata bazaku gani ba" Rige rigen bashi labarin Radhiya suka shiga yi kowa tana fadin nata. Awwab bai san lokacin da ya saki murmushi ba wato bata chanja ba kenan daga sanin da yayi mata. Shiru kusan minti ashirin bata dawo ba abinda bata saba ba. Hadir yana ta kallon kofa Zainab ta fahimce shi tace su dubo mata ita. "Mama gaskiya ki tura Zayyana ita ce karama" "Wani sabon abu ne kuka koya a aikeku ku tsaya zaben mai zuwa?" Awwab yace yana dan bata rai. "Radhiyan ce ai Hamma" "Come on tashi ki karawo min ita Zayyana" Tana zumbura baki ta shiga kofar hanyar dakunan. Tun kafin ta karasa take jin shesshekar kuka. Da dan gudu tayi sauri ta bude kofar dakin. Radhiya ta gani kwance akan abin sallah tana kuka fuskarta har tayi ja. "Uhmm Adda Radhiya kizo inji Hamma Awwab" Zumbur ta tashi zaune Zayyana ta dan ja baya kadan ta share kamar bata gani ba, cikin yanayin damuwa tace "shi wannan na falon shine Hamma Awwab din?" "Eh" "Kunci amanata! babu wanda yace min zai zo kuma aka ki tashina daga falo da zai shigo" Radhiya tace tana sake fashewa da kuka. Yanzu da wane ido zata kalli mutumin da taci burin haduwa dashi saboda irin labaran da ake bata. Ance mata sun shaku da tana karama kuma yana sonta sosai. Ashe ma ya zama dan gayu irin haka kamar likita amma aka bari ya ga askinta. Zayyana komawa tayi tana jin tausayin Radhiya. Ko ita ce da kwalkwal bazata so ace kowa ya gani ba. "Ina take?" "Kuka take yi Mama" Da 'yar damuwa a fuskarta tace "Yanzu dai Awwab duk kaine ka janyo wannan rigima da ka ga kanta, yau ban san yadda zamuyi ba" "Ni kuma me nayi daga zuwana" Su Zahra ya tsare da idanuwa "me yasa baku tasheta ta rufe kan ba?" Kusa dashi Zayyana ta zauna "haka tace wai munci amanarta da bamu tasheta ba ma" Samun kansa yayi da rashin jindadi, ba haka ya tsara haduwarsu ba. Garin yaya ma aka yi mata aski irin haka don Allah? Sallamar Ibrahim da Zayyan ita ta katse tunaninsa. Zaratan samari ne dake ganiyar tashinsu. "Kunga Hammana" suka ji Zayyana ta fada tana murmushi ta nuna shi. "Naki ko namu?" Ibrahim yace yana mika masa hannu. "Da gani kaine Ibrahim, sau biyu Zayyana tana kawo min kararka. Baka san ba'a tsokanar autar Daddy ba?" Awwab yace cikin sakin fuska. "To kace ta dena shagwaba ko muma mu fara ko Emzee, mu dinma duka autoci ne" Kalmar tasa ta karshe ta sanyasu dariya. Awwab ya kalli Emzee yaron is very calm sai murmushi da yake yi kawai. Ji yayi ya burge shi, a fuska ya tuna masa da babansa Zayyan sosai amma wannan Zayyan din da gani ba mai hayaniya bane. Hannu ya mika masa suka gaisa Emzee yana dari-dari ba kamar Ibrahim mai saurin sakewa da sabo ba. "Dama kai nake jira taimaka ka fito min da yayarka wadannan duk matsorata ne" ya nuna su Fauziyya. "Kin fitowa tayi?" Ibrahim yace da mamaki "kullum fa zancenta idan ka dawo zata dena kula kowa a gidannan" " 'Yan cin amana sun saka mana ido ya muka iya yau sunci amanarmu" Awwab yace yana aron kalmar da Zayyana tace tayi amfani da ita. Ibrahim yace "Mama me suka yi mata?" Zayyana ce ta bashi labari kafin Zainab ta soma magana. "Anci amana gaskiya, bari na koma cikin gari na kwana don ga dukkan alamu yau mutanen gidan nan zasu kwana da balotelli" Emzee ya daki kafadar Ibrahim suna dariya kafin ya nufi dakin. Tana nan zaune hanci ya kumbura, idanu sun kankance sunyi ja saboda kukan da tasha. An cuceta da aka aske mata kai. Da an bar mata na zaman falon da ta roka ko babu komai zai rufa mata asiri yau. "Adda kizo inji Hamma Awwab" "Ni fa gida zan tafi" Daure fuska ta ga yayi "ke babu dama ranki ya baci sai kice zaki je gida? Idan Ummi taji abinda kike yi a gidannan zata ji dadi ne? Kowa na tsoron bata miki rai kina jin dadi kamar abin kirki" Mamakinsa ta soma yi. Emzee din da babu ruwansa ko me tace ta zauna shine yake mata fada. Jan hanci tayi "to ba kaina suka bari ya gani ba" "Ance iska kika je sha, kina da wannan kan da kike boyewa ki rasa wurin shan iska sai falo. Yanzu da Kawu Zakari ne ya zo fa?" "Bakinka ya sari danyen kashi, wannan ai mugun fata ne." tace tana harararsa ta tuna wanda ya dan gani a gidan Baffa Gide. "Tunda Allah Ya rufa miki asiri ba shi din bane ba sai kawai ki basar ba irin a zuwan baki ma san me ya faru ba. Da nine ke fa wallahi da magagin baccin karya zan bar falon" Sauran hawayen ta goge da bayan hannunta tana dariya harda kyakyatawa "shege Emzee ka iya bada shawara Yasin" "Shine zaki zageni to" ya harareta yadda take masa. Dan ture shi tayi bayan ta daure kanta da dankwali ta saka hijab "wasa ne dalla" ita ce a gaba yana bayanta. Sai da suka zo bakin kofar ta kasa fita tana jin kunya. Emzee na zuwa ya turata ta soma turjewa amma da ta ga kowa ita yake kallo sai ta dake yadda yace mata ta basar. Duk da kumburin fuskarta bai hana Awwab sake gano kamannin wannan Alheran din mai askakken kai da 'yar karamar kanwarsa mai rigima ba. Ta girma amma tana nan da dan jikinta don tafi karfin a kirata ramammiya sannan baza'a ce ta shiga sahun lukutaye kai tsaye ba. Radhiya a dire take ta ciko ta ko ina. Da kadan ta dara Zayyana a tsayi ita da ake yiwa kallon doguwa saboda tsayin kafa. Yayin da Awwab ke kokarin hada ido da ita, ita kuma su Zahra ta kalla tana ta kokarin kada ta kalle shi. Tunda Emzee yace ta basar to fa basarwar zata yi. "Shine baku tasheni nayi sallah da wuri ba Adda Zahra" "Naga baccin naki yayi dadi ne" Sai ta maida hankalinta ga Ibrahim "ka fadawa Umma ina gaisheta?" "Tace kafin ku koma kije kiyi mata kwana biyu" "Mama gobe zaki sa ya rakani?" "Sai dai jibi Radhiya. Gobe asibiti zan kaiki ko har kin manta?" Asibiti za ta kaita saboda makeron da yaki barin gashinta yayi abin kirki. Awwab sai binta yake da ido tana ta jan mutane da hira banda shi kamar ma baya wurin. Sai da Zainab tace "wai baki ga Awwab bane?" Radhiya ta wani bude baki da idanu irin mamakin nan "laahhhh Mama yaushe yazo? Hamma, oyoyo" Emzee tashi yayi ya sulale daga falon saboda tsabar kunya. Radhiya halinta sai ita. Yace ta basar kamar ba'ayi ba shine zata nuna bata ganshi ba gabadaya. Ji yayi kamar ya saka kuka da ma bai bata wannan shawarar ba. "Baki ma ganni ba sai yanzu?" Yace yana kallon fuskarta. Dimple dinnan da yake saka yatsansa a ciki idan tana dariya yake kallo yana tuna masa rayuwar da. Dakewa tayi abinta "ina na ganka na fito ina ta hira da 'yan uwa, yaya hanya? Ka ga Ummi?" "Baki ganni ba da kika tashi daga bacci dazun nan?" Radhiya an koyi basarwa da gaske ta wani langabe kai "yaushe? Ka dade da zuwa ne?" Wai raina masa wayo zata yi ne? Kowa kallonsu yake yi ana dariya kasa-kasa. Hadir kansa murmushinsa ya kusa zama dariya da ya gane so take ta nuna bata ganshi ba. Awwab da bai fahimta ba dama shima anyi masa tambarin wauta idan abin dan farin nasa ya tashi yace "dazu fa kin farka har muka hada ido." Tsuke baki ta soma yi. Ya kamata idan ta basar sau daya kawai a wuce wurin amma sai neman jan zance yake yi. "Ni din? Bacci fa nayi a kan kujerar nan sai farkawa nayi na ganni a daki su Adda Zahra sun rikeni sun kaini saboda nauyin baccina, ban san lokacin da ka shigo ba" Zahra ta soma kifta masa ido akan ya bar zancen haka shi kuma ya dage sai ya ga abinda ya turewa buzu nadi. "Lokacin da abin kanki ya zame haka " ya kwatanta da dan jan dankwalin Fauziyya " har na ga kan...." Ihu ta saka ta tashi da sauri tana jin kamar taje ta toshe masa baki kada ya karasa fadin ya ga kanta. Kamar zata yi kuka take kallonsa "idan nace ban ganka ba sai kawai ka yarda haka ake yi ko Em..." shiru tayi ta shiga waige da ta ga baya wurin "ina Emzee?" Tayi tambayar tana kallon Ibrahim da dariya tasa ko magana ya kasa. "Ya fice" "Ku ga min shegen yaro, shi yace idan na basar kamar ba'ayi ba komai zai wuce." Gabadaya falon ya sake kaurewa da dariya. Zainab ta tashi ta kama kujerar Hadir "bari naje na bawa babanku magani, Fauziyya ku kawowa Awwab abinci ko ruwa bai sha ba tunda ya shigo kun saka min 'ya a gaba" Gani tayi ya dace su baiwa yaran wuri don ba ta biye musu ana tunzura Radhiya ba. So take Awwab ya so kanwar tasa da wuri, gara su fara sabawa da juna. Taimakawa Hadir tayi ya kwanta ta dauko takardun asibitin ta koma kusa dashi tana yi masa bayanin kowanne don neman shawararsa. Da ido da yanayin chanjin fuska take fahimtar abubuwa da dama da yake nufi idan tayi masa tambaya. Sakale tayi tana kallon Awwab yana murmushi "ban san haka kike so ba, to koma ki sake fitowa. I promise zan tayaki basarwa" Ita ma sai da abin ya bata dariya ta koma ta zauna tana jiran fitowar Emzee ko ma ina yaje ya buya. Dama idan ba ganganci ba me zaisa ta karbi shawararsa. Wautar kanta take gani na biye masa. Yana jiyo me suke yi a inda ya tsaya ya girgiza kai. Bawa Radhiya shawara wataran kamar zuba gari ne a rariya. Kana fada yana zuba. Ibrahim da Zayyana suka tashi suka bi bayan shi zuwa waje. Ibrahim na cewa ta dena binsa ta murguda masa baki tace ita wurin Emzee zata je ba shi take bi ba. Ya rage su hudu a falon Awwab ya watsawa su Zahra idanunsa "bazaku bani abincin bane?" Da sauri Radhiya ta tashi don yau dai taji kunya fiye da yadda ta saba "bari na kawo maka" "No, dawo ki zauna" Inkiya yake musu su basu wuri sumsum suka tashi suna dariyar dramar Radhiya. Kai ta sunkuyar karon farko da zata iya tunawa a rayuwarta ta rasa bakin magana saboda kunyar da ta bawa kanta. Dan gayu kamar wannan kyakkyawa daga ita sai shi a falo ai dole harshe yayi nauyi tace a zuciyarta. Nazarinta Awwab yake yi ya dago kansa daga jinginar da yayi da kujera yana mamakin wannan yarinyar ta gabansa ita ce Alheran dinnan da yake dauka suyi ta yawo a barrack shekarun baya. "Alheran" ya ambaci sunanta a hankali taji wani yarr a jikinta saboda yadda muryar ta ratsata. "Uhmm" "Kin dena magana ne kuma?" Ya tsokaneta da ya ga kamar ma a takure take. Girgiza kai tayi sannan tayi kwafa da guntun tsaki "Wallahi kunya naji, ashe ba haka ake basarwa ba. Bari Emzee ya dawo zai gamu dani" "Balotelli zaki yi masa?" Dago kai tayi da sauri ya dage mata gira yana jin komai nata na burge shi. Ba haka yayi zaton ganinta ba. Yana ta kissima wata budurwa mai ji da kai da gayu sai ya hadu da Radhiya wadda kwatancenta sai wanda ya santa. Amma duk da haka yaji tayi masa a yadda ya sameta cikin kankanin lokaci. [02/11 7:30 AM] My 2nd Mtn: 25. Bata tsaya ko ina ba sai daki ta cire hijabin da dankwali ta fada kan gado. Wani tunani ne ya shigeta haka kawai kada a sake tsautsayi ta dauki dankwalinta ta daura. Awwab kamar bai san me yayi ba ya shiga cin abinci hankali kwance yana jin matan suna kuskus a junansu. To meye ma a ciki daga bata abinci. Da ace sun tashi tare baya jin akwai abinda zai kasa yi mata sai dai a taka masa birki tunda mace ce. Allah ne Ya hada jininsa da na iyayenta sai Ya sanya masa matukar kaunarta tun tana tsumman goyo. Emzee yaso dauke kai amma ya kasa. Karshe ya dauko wani littafi a kusa dashi ya bude shi ya kifa akan fuskarsa yana dariyar da ba sauti. Gaskiya yaji kunya kamar shi aka bawa abincin. Ibrahim ne ya fara tsokanarsa sai kawai ya tashi da plate dinsa a hannu zai koma daki. "Dawo ka zauna ka gama cin abincin nan" Awwab yace ko kallonsa baiyi ba. "Na koshi" "Kira min Alheran" Ba musu yaje ya fadi sakon, maimakon amsa sai ta kara dukunkune kanta ta tura a karkashin filo. Murmushi yayi kawai ya fita ya dawo ya fadawa Awwab taki tashi. Sai da yaci rabin abincin ya mika masa plate din "ka kai mata nata, sai da safen ku" Tashi yayi zai tafi dakin Ibrahim inda aka yi masa masauki Zayyana da ta kasa hakuri ta fara shagwabe fuska "Hamma ni baka taba yi min irin haka ba, harda bata a baki" "Ba kiji ta fada muku cewa a rashinta nake kulaki ba" ya fada da wasa. Kukan shagwabar da ta saba ta fara "kuma sai na...." "....fadawa Daddy" Ibrahim ya karashe mata yana kyabe fuska yadda take yi. Awwab ya kusa kofa don idan ya biye mata karshenta a daren sai ya ga wayar Daddy. Juye juye ta soma yi Emzee ya dawo daga ajiyewa Radhiya abinci ya ganta. "Wa kike nema?" "Kai mana" "Inyi miki me?" "Ba Hamma Ibrahim bane yake tsokanata" "In fada miki sunan Fulatancinsa ki rama?" Cikin sauri Ibrahim yazo ya tura shi daki yana magiya da yayi shiru. Tun da Radhiya ta fassara masa ma'anar Surbajo yake gudun sunan kuma dashi Emzee yake samu ya dan kashe bakin idan ya dame su. Da yake Mami ta fada musu cewa sammako zasuyi su baro Katsina su ma basu yi sanya ba wurin tashi da wuri. Zuwan 'yan matan ba karamin dadi ya yiwa Zainab ba. Su tayata hira ayi ta barkwanci sannan basa bari tayi komai. Zahra da Fauziyya sun jima da gogewa wurin aikin gida da girki. Saboda Mami taran safe zuwa taran dare tana gidan aikinta. Su ne suke komai. Shiyasa Zayyana ta shaku dasu sosai wani zubin bazaka ce yayyenta bane da suka girme mata da yawa. Kowa ya shirya cikin kayan kirki Radhiya ta bude jakarta kenan bayan ta gama shafa mai Zainab ta leko tayi kiranta. Dakinta ta bar musu dama. Yanzu kuwa da ta kai Hadir falo bayan ya gama breakfast sai ta kirata dakinsa. Ledoji uku ne a gabanta manya ta tura mata daya. "Ga naki kafin ku tashi daga bacci telan ya kawo" Radhiya ta bude baki tana kallon kayan da Zainab din take zarowa. Atampa guda uku, material daya, shadda daya da wasu yadika combination biyu. Kwalkwal tayi ta idanu zata yi kuka. Duk wannan ita kadai. "Bana son kuka fa kin sani ko yanzu naje na fada a hanaki yin sojan." "Mama nagode" tace hawayen yana fitowa. Yarinya ce mai rike abu a rai shiyasa bata manta alkhairi ko sharri. Da yake dai wasa da shirme sunyi mata yawa a ka shiyasa sai ka ga kamar bata da damuwar komai. Banda kaddara da Zayyan yana raye Zainab ta sani da yanzu sun kai wani mataki a aikinsu. Yadda yake da kwazo da himma tasan 'ya'yansa sai dai wani yaci arzikinsu. Babban dalilin kiran dama so take ta shirya Radhiya da kanta. Mama Zainab 'yar kwalliya ce ajin karshe. Idan ka ganta a yanzu da take cikin farincikin kasancewa da Hadir duk da a zahiri za'a iya cewa nauyi ne shi a gareta amma fes take kullum. Gogewarta a soyayya duba da tarihin rayuwarta yasa tun jiya ta daukarwa kanta nauyin sake hada Awwab da Alheran domin su cimma burinsu cikin sauki akan yaran. Kallo daya zaka yi musu kasan sun dace da juna amma idan ka san kowannensu ta fannin zamantakewar rayuwa dole ka chanja shawara. Awwab dan boko ne tashin turai. Yana da ilimi, wayewa da kudi domin kuwa pilots masu aiki da kamfanin KLM suna cikin mafiya samun kudi cikin tsararrakinsu. Alheran Radhiya kuwa yarinya ce da ta tashi a rugar fulani a cikin wata karamar hukuma. Wannan kadai ya isa zama wawakeken bambamci tsakaninsu indai zaman aure zasuyi wanda babu soyayya. Abubuwan da ya sani ko yake so bata sansu ba bare ta so su. Wayewarsu ba iri daya bace. Tayi nata karatun daidai gwargwado amma baza'a taba hada shi da nasa ba tunda iyakarta secondary. Shiyasa indai ana so zaman aurensu yayi karko to a samu soyayya mai karfi da za ta zama igiyar dauresu. Wani kaya Zainab ta ciro daga ledar ta mika mata "jeki ki saka wadannan gani nan zuwa. Ko hoda kada ki shafa sai nazo" "To Mama" tace ta fita da murnarta taje ta nunawa su Zahra su ka tayata murna. Yadi ne mai kala biyu. Mara adon light purple ne anyi mata skirt dogo da dankwali. Rigar kuwa yadinta duka zanen filawoyi ne manya pink da light light purple kamar skirt din. Tsayinta ya wuce gwiwa da kadan anyi mata dogon hannu mai dan fadi daga kasansa. Kadan akayi mata shape don kada ta kama jiki ba wani ado a jikinta sai maballai guda hudu na wuya amma tayi kyau musamman a jikin Radhiya. Wani juyi ta rinka yi tana jindadi su Zahra na zuga ta har Zainab ta shigo tace suyi sauri wanda basu ci abinci ba su je su ci nan da awa daya ko kasa da haka su Mami zasu iso. Duka su ukun su ka fita aka barsu su kadai. Hoda, kwalli da janbaki pink mara duhu ta shafawa Radhiya a fuska bayan tayi mata lining da jagira pink mai duhu a leben. Simple make up ne amma fuskarta tayi kyau. Cikas din kawai kanta ne. Zainab ta daura mata dankwalin da kanta ya danyi tudu daga keya sannan ta mika mata hijab mai kyau da kananun duwatsu a kasansa pink irin kayan. Iyakarsa ya sauko kirjinta da kadan. Radhiya harda hajijiya a gaban mudubi. "Mama nayi kyau ko?" Murmushi tayi ta yaba sosai da 'yar tasu "kinyi kyau amma don Allah bana son baragada kinji ko. Wannan hayaniyar da saurin fushi ko fada ki ajiyesu. So nake naga kina taku daidai yadda babu wanda zai raina min ke" "Idan nayi sanyi da yawa bazan kai labari ba a makarantar sojoji Mama. Anfi son mu da dakiya da fada saboda gudun raini" "Allah nagode Maka. Har yanzu kina jiran zuwa sojan ne bayan miji zan samo miki" Da murnarta tace "Likita?" "Idan ba likita bane ba fa?" "Gaskiya Mama ki barshi kawai. Idan ba likita ba sai dai ko soja irina. Sauran duk na rainasu, kada ayi auren su rinka kawo karata kullum" Hannuwa Zainab ta tafa tana dariya, yanzu ta gama cewa ta dena shirme gashi ta hade fuska tana buga kayanta a ganinta kuma ba laifi bane. "Jeki kici abinci kada azo ana jiranki" Kallon kanta ta sake yi yadda tayi kyau abinci zai iya goge mats jambakin ta dawo tayi zamanta akan gado "bana jin yunwa" "Ashe kuwa za'a tafi a barki" Zainab tace tana yin gaba. Ba don taso ba ta tashi itama. Tana saka kafa a falon ta tuna abinda Awwab yayi mata sai ta juya suka kusa karo da Zainab. "Wuce muje kici abinci" ta umarceta. Gani tayi babu alamun Awwab din sai ta saki ranta ta fara gaishe da Hadir da yake kallon labarai sannan ta tafi gaban dinning table inda kayan tea suke za ta hada taji Zainab tana tambayar ko Awwab ya shirya. "Da kyar idan ma ya tashi Mama, shi fa idan yana gida yafi zaman daki yayi bacci saboda yanayin aikinsa" Zahra ta bata amsa. Radhiya ta saki murmushi "kice kamar dai mu sojoji ashe nasa aikin shima baya samun isasshen hutu". Suna mata dariya za ta fara abin nata ta mayar da hankali ga abinda take yi. Madara da milo ta zuba a cup din nata ta mika hannu za ta dauki sugar Awwab ya bude kofar dakin ya fito. Wani hadadden kamshi ke tasowa tun kafin ya iso tsakiyar falon. Yayi kyau cikin wani lallausan yadi ruwan madara. Rabonsa da manyan kaya ya kwana biyu sai jiya da Daddy ya bashi su guda biyu dinkakku da zai taho. Su Zainab ya fara gaisarwa sannan ya amsa gaisuwar kannensa da Radhiya da jikinta yayi sanyi saboda kada a sake irin ta jiya. Tana tsaye ta kasa karasa abinda take yi balle ta ja kujera ta zauna. Jiya ke mata yawo a ka yadda ya bata abinci a baki kamar wata baby. Runtse idanu tayi tana son kawar da tunanin daga zuciyarta taji ya janye kofin daga hannunta. "Kawo na karasa hadawa naga ba kya sauri" Sakar masa tayi da sauri ya ture robar sugar din ya kara mata madara da milo ya fara zuba ruwan zafi. "Hamma ya isa haka" tace da ta ga ya wuce rabi. Bai saurareta ba sai da ya cika kofin ya ja kujerar gefenta ya zauna. Kujerar kusa dashi ya tura mata baya da kafarsa ta zauna tana waigen baya. Babu mai kallonsu Zainab da Hadir labarai suke gani a tashar Channels. Zahra da Fauziyya suna hirar angwayensu dake korafin sun makale a Kano. Zayyana kuwa ta tafi dafa indomie. Wani irin kallo yayi mata sau daya ya dauke kansa, tayi masa kyau sosai har yana tsoron kada kallon da yake mata ya wuce gona da iri "namu ne mu biyu" Turo baki tayi "Habaaa Hamma don Allah yunwa nake ji" "Okay fara sha ki bani" yace yana tura mata kofin. "Ni a'a, ka shanye na hada wani" Lumshe idanu yayi yana mata murmushi "wannan zamu sha, jiya dama ance abincin da na rage miki dawo dashi kikayi. Ko muyi kama-kama da shima baki bari munyi ba" "Na shiga uku" ta furta a hankali tana cike da kunya ta tura kujerarta baya za ta tashi ya bata rai. "Ki dena tashi idan muna magana bana so" Zama tayi tana ta zumbura masa baki ya sha rabin tea din ya mika mata ta karba ta bishi da harara. "Baka saka suga ba ni kuma dashi nake sha" ta mika hannu zata dauko robar ya riga ta daukewa. "Da zaki a haka, try it." Samun kanta tayi da bin umarninsa ta sha tea din shi kuma ya tashi ya koma daki bai taba doyar da aka soya da kwai ba. Tana nan zaune ya dawo da ledoji masu kyau a hannunsa da tambarin wani babban kamfani a kasar Germany. Su Zainab ya fara mikawa ta karba da murmushi ta bude. Turaruka ne na alfarma na mace da na namiji ita da Babansu Hadir da agogo set shima na mace da namiji. "Harda dorawa kanka wahala Awwab?" "Ku sa mana albarka kawai Mama" "To Allah Ya saka da alkhairi Yasa kafi haka. Allah Ya baku masu yi muku a nan gaba" "Amin" kowa ya amsa harda Radhiya. Leda ta biyu ya mika mata "na Ibrahim da Emzee, suna ina ne ma?" "Leka ta window wankin mota ake mana" Komawa yayi dinning table din ya zauna a inda ya tashi Radhiya ta kafe shi da ido. "Ya?" Yace yana gimtse dariya don ya kula ta fara cika tana jiran nata. "Ina nawa?" "Me din?" Kai tsaye tace "Abin cikin ledar" "Kina harar tawa zan baki abin cikin leda? Wanda na siyo da sunanki ma zan je in kaiwa Ummi tayi sadaka dasu" Kallon shirts da agoguna da Zainab ke fitarwa da sunan Emzee da Ibrahim yasa ta sake hade rai harda kwalla. Ita da tafi kowa cika baki akan Hamma Awwab amma ita ce ko tsinke bai bata ba. Abincin ma fushi tayi dashi ta ture. Sai yaji ta dan bashi tausayi ya gama dariyar abinda yake shirin kulla mata kawai don ya tsokaneta ya matso da kansa yana mata magana a hankali. "Kin yarda daga yanzu ko me zamu ci zamu ragewa juna har na koma?" yayi dan murmushin rigimarsa da Mami a baya "da ko me naci sai na rage miki Mami tayi ta fada wai ba komai zaki iya ci ba. Ni kuma tana barin wurin sai na tura miki a baki ko yaya ne ki cinye" Murmushin da tayi masa jinsa yayi har ransa saboda yadda take lumshe idanu batare da tayi la'akari da tasirin hakan gareshi ba "to ai kaine baka yi min bayani ba kawai kasa ni jin kunya jiya." "Silly girl me akayi na jin kunyar? Kinsan me kike yi min kuwa da?" Radhiya ta girgiza kai. Yafito ta yayi da hannu ta sake duku kanta tana shakar daddadan kamshinsa "abin bakina kike cirewa ki saka a naki idan na hanaki" Hannuwanta ta saka a gefe da gefen kumatunta ta bude baki da idanu duka a lokaci daya. Tana ta jiran Hamma Awwab ya dawo gashi ya dawo ya hadata da jin kunyar da bata taba sanin tana da ita ba. Abin bakinsa fa yace! Yanzu tana tashi kuma zai ce ta zauna ko yayi maganar yadda kowa sai yaji. Gara kawai tayi kamar bata ji komai ba ta bawa kanta shawara. Daurewa tayi kamar bata ji nauyin maganar ba tace "Yanzu dai kasan bazan ci abin baki ba" "Sure?" Yace yana mata kallon gefen ido. "Na fa girma" "If you say so" ya rausaya kansa sai kuma ya tashi tsaye "kinsan me? sai na sa kin karbi abin bakina kafin na koma Katsina" "Idan naki fa?" "Ki tambayeni duk abinda kike so. Amma nima idan nayi winning zan tambayeki" "Ka shirya bani tsarabata kawai" tace tana dariya ta tashi tayi waje da sauri. Sai da ta rufe kofar falon ta dafe kirjinta da yake bugu kamar zai ballo. Kofar ta kalla ta jingina da bango tana girgiza kai "Abin baki? Hmmuhmm, kai lallai ma Hamma Awwab dinnan idan ba bazan karba ba" kunya ta ji kamar me amma ta daure sosai tana bashi amsa saboda kada ya gane zancen na shigarta tana bashi wata ma'anar daban. Emzee yana kallonta shi ya gama wanke motar Mamansu Zainab har ya fara taya Ibrahim da yake wankin bus din da zasu tafi Sumaila a ciki. Dauraye hannuwansa yayi Ibrahim ya bata baya bai hangota ba ya karasa gabanta. "Ke da wa Adda?" Dantsen hannunsa ta riko tana dariyar jindadi "Emzee yau na koyi basarwa" Yasan Addarsa da shirirta "na tayaki murna, wa kika basar?" "Hamma Awwab mana, wai kasan me yace min kuwa?" Yatsunsa na nuni ya sanya a kunnuwansa ya toshesu "bana son ji don Allah" Shan kunu tayi tana harararsa "me yasa?" "Rike kayanki, hirarku ce" ya bata amsa yana komawa wurin Ibrahim. Haka kawai jikinsa ya bashi wani abin jin kunyar Awwab yayi don abinda zai korota waje ita kadai ba karami bane. Shi kuwa bai tashi jin ko ma meye ba a saka shi jin kunyar da za ta jima bata barshi ba su kuma su cigaba da harkokinsu. ********** [02/11 7:30 AM] My 2nd Mtn: 26. "Gulmata suka rinya yi maka?" Tayi maganar a cikin shagwabar da batayi niyya ba. Hakan yasa Awwab sake yin murmushi. Daga shigowarsa gidan zuwa yanzu idan ma yana da damuwa to tabi ruwa tabi iska Radhiya ta dauke masa ita. "Kinki zuwa na ganki ba sai na nemi labarinki ba" "Ba ga su Mama ka gani ba maimakon kayi hira dasu shine zasu kawo maka zancena?" Ta sake marairaice masa. "Kinsan me yasa na kasa zama na huta duk da tarin gajiyar da nayi?" "A'a" tace tana girgiza kai. "Because I missed you Alheran" yace suna hada idanu tayi saurin lumshe nata. Tayi karatu bare ace bata jin turanci bata fahimce shi ba. I miss you ai sai masoya a iya saninta. Shiyasa taji wata irin kunya ta saukar mata. Ko a jikinsa don iyakar gaskiyarsa kenan. Murna da sanin cewa ga inda take ya wadatar dashi ya hana shi sukunin duk wani hutu idan ba haduwa suka yi ba "sai da nazo na ga ashe ni kadai na damu dake, kina kallona kina basarwa" Maganarsa ta bata dariya kamar yadda ya fadeta yana yamutsa fuska shi ba'a kyauta masa ba "wasa ne wannan amma ni fa ban iya tuna ka ba ne sai labarin da Ummi ta bani" Hannu yasa ya karbi lemon da Fauziyya ta tsiyaya masa. Sai da ya kurba sau biyu ya sake kallonta "ko kadan?" "Me?" "Rashin tunawa dani din" "Ka ga fa nayi kankanta lokacin" Gefen girarsa ya shafa "kinga wannan tabon?" Daga inda take tana ganin duhun layin "bille ne ya karkace? Ko ka hadu da wanzamin da bai san aikinsa ba. Me ya hada tsakiyar goshi da gefen gira? Ko irin na gefen nan mai uku-uku aka so yi maka?" Ta rinka jero masa tambayoyi. "Na hadu da wanzamiya dai" Fauziya za ta fara dariya don gidansu kowa yasan tabon aikin Radhiya ne ya kalleta sai ta sake tashi. Wai meye ne Hamma yake korarsu...kodai, kodai...dan murmushi ta saki amma kuwa da tayi farinciki idan haka ne. Abincin da Zahra ta gama hadawa ta karbo don so take ta sake ganin gulma. "Ana wanzamai mata dama?" "Alheran sunanta ma" "Da gaske?" "Yakushina fa kika yi" yace yana kallon yadda ta ware idano ta saman kofin hannunsa. Tasowa tayi ta dawo kujerar gefensa yadda zata gani sosai tana ta karkata kai hagu da dama "Allah Hamma, ko dai don nace ban tunaka bane zaka dora min" ta rinka dage girarta duka biyu a tare tana cewa "eyye, eyye?" "Cute" ya furta a sanyaye ya rasa me yake damunsa tun da ta fito daga dakin. Wasu abubuwa take yi da suke tado masa da memories din kuruciyarsu. Ta bude ido ta lumshe, ta turo baki ta sha kunu ko murmushi. "Da kina yarinya kin fiye rigima da fada...uhmm harda kuka. Gashi naga alama babu wanda kika dena cikinsu." "Tsokanata akayi ne, amma yanzu na dena fada" Fauziyya da ta duka za ta zuba masa abincin a plate tace "A yaushe kika dena fadan?" "Babu ruwanki da hirarmu bar abincin ma zata zuba min idan na tashi ci. Tafi kawai ki barmu kinsan ba wurinku nazo ba" Dadi kamar ta zuba ruwa a kasa ta sha yace ba wurinsu yazo ba. Kai na rawa tana jujjuya idanu tace mata " yehhh sai a tafi kinji me Hamma Awwab dina yace. Dama na fada muku idan ya zo zai dena kula kowa sai ni, nima kuma in dena kula ku ehe" "Shikenan ka bata damar cigaba da raina mu ni da Zahra" Kallon tuhuma yayi mata "wai haka?" "Fada kawai take yi don ta hadamu, kowa ya shaideni a gidan nan wurin girmama manya ba daga nan ba" yanayin maganar kadai zai gane karya taje yi. Bata da innocent face, kana ganinta kasan akwai jini a jika. "Allah Ya shiryeki Radhiya" Fauziyya tace tana tafiya za ta je kaiwa Zahra tsirku. Abincin ya nuna mata ta soma zuba masa "ba kya son na kula kowa?" Ta dago kai "eh wallahi, ko na yau kawai kada kayi musu magana su gani duk kafi sona. Ni kadai ce kanwarka banda su" "Gobe zan koma Kt ba kya so nayi hira dasu Ibrahim?" Dena zuba abincin tayi tana jin babu dadi a ranta "gobe kuma Hamma ko sabawa bamuyi ba zaka koma?" Wannan karon shi ya fara janye idanunsa daga gareta. Ya rasa gane me yasa suna kallon juna sai yaji abu ya taba zuciyarsa. Ya dai alakanta hakan da dawo masa da tunanin baya da take yi ne. "Akwai wani sabon da ya rage msna bayan wanda muka yi in less than an hour?" Wuya ta shiga sosawa irin na marasa gaskiya tana sunkuyar da kai da murmushi. Dimple dinnan ya sake kallo ya miko hannu kamar zai saka yatsansa yadda ya saba yi mata a baya ya tallabo habarta da ragowar yatsunsa sai kuma yayi saurin janyewa. Alheran is not a child anymore ya yiwa kansa fada. "Na yarda kayi hirar minti goma goma da kowa su Baba kuma awa daya, sauran kuma duka nawa ne." "Bazaki gaji dani ba?" Bai san me ya kaishi yin tambayar ba. Yayi saurin datse bakinsa bayan ta fito. Da ido daya ta karkace kai tana kallonsa "hmmm na gane wato ka gaji dani ko? Nasan komai idan ana yi min irin haka saurin fahimta nake yi. Kora da hali kake min irin na Ummi idan ta gani da hirata" Hannu ya daga yana bata hakuri "ba haka nake nufi ba, yadda kike so haka za'ayi. A lokacin kowa ma sai a cire minti daya da rabi in kara miki" Murmushi ta saki tayi masa gwalo "na maka wayau" Girgiza kai kawai yayi yana jin nishadi da farinciki suna ratsa shi. ********** Malamijo ke zaune a tsakar dakinsa akan filo yana sharba gumi. Zafi ya ishe shi daga shi sai dogon wando Hajjo da tayi karkon zama kamar Yadikko saboda bakinta dake kwatarta a wurinsa tana masa firfita. "Ya kamata kaje asibiti fa, ka kwana ka tashi da abu daya ba'a zauna a gida ba" Daure fuska yayi ga azaba ta ishe shi da kyar yake magana "zaki biya min kudin asibitin ne?" "Lallai ma Malamijo, to don Allah zauna kada kaje ka gani idan zan damu. Ka bar kudin kar ka tabasu idan ciwo ya karasa ka a raba mana gado. Nasan a lalace idan ban saka dogon buri ba zan tashi da a kalla shanu uku manya." Ido ya ware yana jin kamar ya shakota amma jikinsa babu kwari. Ta turo dankwali gaba tana lissafi da yatsunta "kaga mafi girma a ciki in sa a danne a yanka min. In soya, in gasa, inyi miya. Kai har tafasasshe sai naci. Sauran biyun kuma in sayar nayi sababbin dinkuna kafin Allah Ya kawo bazawari" "Mmmugguwa, saaai kin riga..rigani mutuwa" "A hakan, karmai-kamai da kai kamar kazar mayu?" "Akwai mayyyyyyar da ta wuccceki ne?" Yace yana cije lebe. Yadikko ta dago labule ta shigo fuskarta da damuwa "Malamijo anya zaku cigaba da zaman nan kuwa haka? Use da Asabe fa suma irin lalurarka ta same su. Asabe sai kuka take da kyar na bata hakuri na fito" Hajjo na jin haka ta tashi da sauri "Yadikko kice ciwon na ango ne da amarensa. Wannan abu shi ake kira guzurin masoya. To ni nayi nan. Kayan lefen can da aka gama gani zan je in killace kada ayi sibare inzo banci nanin ba nanin ta cinyeni ace don ba ni na haifesu ba ina musu bakinciki na bari an kwashe musu kaya" Fita tayi tana rangaji da dariyar mugunta. Malamijo da amarensa duka sun kasa fitsari. Duka duka Asabe watanta uku a gidan ya cike gurbi da Use. Auren sati uku an wayi gari sun kasa fitsari. Shi tun jiya ya fara gashi yace a matse yake amma ko digo ya kasa yi. Bata gama gyara kayan ba Yadikko ta shigo babu walwala a fuskarta saboda yadda ta kula yana jin jiki. "Hajjo me ya kamata ayi ne, rashin fitsarin nan fa ba karamin abu bane. Malamijo sai zufa yaje yi yana numfarfashi" "Sai kiyi ta damun kanki Yadikko. Akan me? Nan yayi auren nan fa ya soma mana wulakancin da ya saba. Saboda alhaki kwikuyo ne da yace mu dena girki wai ya bamu hutu kannenmu suyi ai ga sakamako nan ya samo. Banda kwadayi irin na namiji yaran da basu fi yayi jikoki dasu ba wai sune kannenmu" "To dai a bar tone-tone mu kira su Habu yazo ko da motar da yake haya ne a kaisu asibiti. Zan tura a fadawa Salame ke kuma ki kira Innawuro ta fadawa Mairama itama su zo babansu ba lafiya sannan ga karbar lefe ma da basu san anyi ba" Ido Hajjo ta zaro "Ni shegiya inji dan daudu, da wane bakin zan fada musu mahaifinsu ya kamu da tagomashin soyayya? Kyaleni naji da aike gidan waccan mara mutumcin Salame. Amma Mairama ai akwai kunya taakaninmu, yarinyar mutumcinta yasa yanzu kunyarta ma nake ji" "Meye kuma tagomashin soyayya ni Yadikko?" "Sunan da ya dace da ciwon nasu kenan ai" Yadikko ma dariya ce ta kama ta. Sai yamma aka samu biyu cikin mazan gidan suka dawo. Dama daga Mairama sai taron maza. Matan da suka taso kuma halin Malamijo ke korar musu manema. To yanzu anyi sa'a mutum hudu cikinsu abin yazo tare. An aikawa Salame dan aiken ko kallo bai isheta ba kamar ba kaninta ba. Mairama kuma Bature ne ya kira lambar Baffa Habubakari ya fada masa. A daren ya nemi layin Major ya sanar dashi cewa a fada mata. ********** Hankalin Mairama ya tashi duk da bata san me ya sami Malamijo ba amma tunda aka fada mata tana ganin ba karamin abu bane. Major ya tsara musu tafiya washegari ganin duk ta tashi hankalinta. Dama motocin da yayi order biyu an riga an kawo su. Daya domin bukatarsa dayar kuma saboda Mami da kuma kai Zayyana makaranta da suke jiran a koma hutu ta fara SS1 sabon zangon karatu mai kamawa. Jibi zai tafi Sakkwato kaninsa zaiyi masa rakiya su kuma yace washegari su tafi sai su tsaya a Kano su dauki yaran. "Amma ina ganin motar zata yi muku kadan. Bus din da aka kai Awwab Kano kuma yace gobe zasu dawo. Dreban ya kamata ya huta haka shiyasa ba zan ce ya kwashe su ba" "Awwab ya tuka ba sai ya bimu a baya ba" Mami tace su kuma dan gidan Hussainarta Abdallah ne zai tuka su. "Bana son tukin Awwab a babbar hanya gudun nan nasa kamar yana iska". Mairama ta fara musu godiya sannan tace "da kun barshi Daddy a hakan ma nagode sosai wallahi. Ba sai an sake wata wahalar daukarsu ba. Shima Awwab din yana bukatar hutu" Mami ce mai kwantar mata da hankali tace "haba Ummin Awwab ki bar wannan godiyar mu dake duka daya ne. Babu matsala in sha Allah" Babban abinda zai kai Major wanda zasu hadu da Baffa Gide a Sakkwaton shine binciken dangin Zayyan na Nijar. Idan da gaske rashin idonsa a duniya yasa suka zare hannunsu daga kan iyalinsa ko kuma su ma karya Maikudi ya shara musu duk zai jiyo. Shi kanshi sojan da yake tura kudin zai baro bakin aikinsa ya taho don ransa ya baci fiye da ba Major akan rainin hankalin da Maikudi yayi masa. Idonsa idon Maikudi kawai yake jira. ********** Tun dare anyiwa Zainab waya game da zuwa Sumaila duba Malamijo. Ita bazata sami zuwa ba saboda Hadir gashi asibiti zasu koma. Tunda ba kwana zasuyi ba Mairama da su Radhiya ne kadai zasu kwana sai ta yiwa Ibrahim izinin fita duk da shine karfin taimaka mata akan babansa sai Emzee da yake taya shi sosai. "Yaya zakiyi da Baba" ya fara cewa da tace yaje. "Gara na fara sabawa, daga kai har Karami WEAC dinku ake jira a nema muku admission. In kana makaranta zanyi ta jiranka ne?" Godiya yayi mata don yana son bin 'yan uwansa amma baya son kwana saboda kada aikin yayi mata yawa. Dakin da aka sauki dreban gidansu Ghazalatu yaje ya tarar da Awwab ya karbi mukullin motar. Kudin mota da Zainab ta bayar a kai masa da zai koma Katsina yaje kai masa. Iyalan gidan su ma duka sati mai zuwa zasu taho Katsinan saboda bikin da yake na gida duka a garesu. Shi kadai ya koma ciki Awwab ya zauna akan dan ginin da ya zagaye flowers din da aka shuka daga jikin bangon gidan. Waya yake son yi da Ghazalatu yau tun da ya taho tana fushi basu sake magana ba. Da sauri ta dauka da ya kira sai kuma tayi shiru don ta nuna masa fushinta na kin kiranta da wuri. "My G fushin ne ya tashi?" Nishadi yake ji sosai yadda suka rinka hira da Alheran kamar basu rabu ba. Kusan komai na rayuwarta da zata iya tunawa ta fada masa sai yake ga kamar a gabansa ta tashi. "Idan nayi magana kace na fiye kishi ko korafi. Tun yaushe ka isa amma ko text ban samu ba talkless of waya." Sai yaji babu dadi don ya sani bai kyauta mata ba. Hakuri ya bata don bashi da girman kai ko kadan. Yayi mata laifi dole ya kwantar da kai ya rarrasheta. Kusan wayar minti talatin suka yi sai da yaji ana masa warning na karewar credit. "Zan kiraki gobe in sha Allah, zamu je duba baban Ummi a garinsu. Dawowarmu sai wurin jibi kenan dasu Mami" "Mami ba tana gida ba?" "Zasu taho da Ummina gobe sai mu wuce tare" "Yayana kace mata zani please. Da saasafe sai na koma gidan mu taho tare" Yaji dadi sosai saboda shima ya soma kewarta. Suna gama wayar yace ta kira Mami din credit dinsa ya kare. Ta kirata ta wayance da cewa wurinsu Zahra take son zuwa. Mami tace to ta zauna su zasu biyo su dauketa. Falon ya koma ya same su kowa na cin abincin dare banda Radhiya da tasa plate a gaba tana kallonsu. Akan doguwar kujera ya zauna ya kwantar da kansa baya. Alamun idanu yaji a kansa ya dago. Ai kuwa duka shi suke kallo har Radhiya "What?" Yace yana kallon kansa. Fauziyya ta nuna masa plate din gaban Radhiya. Taliya ce fara da sauce din ganyen alayyahu da ugu sai balangu mai dan karen dadi da Ibrahim da Emzee suka siyo. Dama yanzu sune 'yan zuwa aike. "Me ya sami abincin Alheran?" Kunya taji ta kasa fada masa bayan cika bakin da ta gama. Zayyana kuwa tace "kowa shaida ne Adda Radhiya zaki min gyaran akwatina tunda kin kasa" "Dama akwai abinda zaki kasa?" Yayi tambayar yana kallonta. Ta dai yi saranda inji bature kaudin nata bai kai nan ba ashe ta gama cika baki. Tana ganinsa taji ko da wasa bazata iya fada masa zaman me take yi ba. "Emzee me ya kama bakin yayarka ne ta kasa magana?" "Babu ruwana ni dai" ya cigaba da cin abincinsa yana murmushi. "Ni bari na fada maka Hamma" Ibrahim yace yana kallo Radhiya ta daure fuska "Zayyana tace kafi sonta shine Radhiya tace don bata nan ne dama. To shine Zayyana tace mata ita fa ko me take so kana yi mata. Idan kana gida hatta abinci tare kuke ci. Shine Radhiya tace wai wannan na gaban nata kaine kace ta zuba muku tare kafin ka shigo. Betting su ka yi" Zamowa yayi daga kan kujerar yana janyo plate din gabansa bayan ya tankwashe kafafunsa. "Babu ruwana da wasanninku, Alheran matso mu ci yunwa nake ji" Bude baki su kayi cike da mamaki harda ita Radhiyan. Kifta mata ido Awwab yayi a kunyace ta matso ya dauki fork a kan tray din da aka kawo kwanukan abincin. "Muyi kama-kama irin na yara?" Yayi magana yana kallon idanunta. Tsabar kunya tashi tayi zata gudu. "Ba fa ki isa ba, wannan abincin na mutum biyu ne so just sit mu cinye" "Kaci ka rage min Hamma Awwab" tace tana kallon su Zahra tana neman taimako. "Tare zamu ci kada a barki da gyaran akwati" "Babu komai zan iya" Hade rai yayi "ina wasa dake ne?" Ba shiri ta zauna tana bashi hakuri sai kuma ta waiga tana kallon kowa an zuba musu ido "don Allah ka bari su gama duka su tafi kunyarsu nake ji" "Kin tabbata zaki zauna muci idan sun tafi?" "Eh mana" "Kamar gaske" Bude baki tayi za ta sake magana kawai ya tura mata fork din da ya ciko da abinci tun dazu. Ibrahim ya dora hannu ya rufewa Emzee idanun da ya zaro sun ga abinda basu saba ba. Zahra ma sai ta rufe nata ta sakalo hannuwanta akan idanun Fauziyya da Zayyana suna faman dariya. Radhiya kasa motsi tayi sai idanu da take ta kiftawa ba kakkautawa. Awwab yayi murmushi duk da yayi ne kawai saboda kannensa amma abin ya tsaya masa a rai dakewa kawai yayi ya dauko kofin da aka cika da juice ya miko saitin bakinta. "Sorry na cika miki baki, hadiye ki sha wannan" A guje Radhiya ta bar falon kafin ta kasa numfashi. Yau ta gamu da gamonta. Ita bata taba kunyar wani mahaluki ba kamar yadda taji Awwab ya gama da ita ba yau. [02/11 7:31 AM] My 2nd Mtn: 27. Shadaya da rabi mutanen Katsina suka iso. Radhiya sai murna ta ga Umminta ta kara kyau. Mairama hadaddiyar mace ce da rayuwa ta yiwa cikas. Kwanakin da tayi a Katsina da kulawar Mami yasa jikinta ya kara kyau kamar ba ita ba. Zahra da Fauziyya na ganin Ghazalatu suka sa ihun murna don basu san da ita za'a zo ba. Mami tace bata san lokacin da zasu girma ba irin wannan tsalle da suke yi. Ita Ghazalatu hankalinta yana kan Radhiya dake zaune a gefen Umminta ana mata tsiyar Ummin na tureta bata ma san tana yi ba. Gaisawa suka yi aka dan taba hira Mami tace gara su zo su dau hanya saboda a ranar suke son dawowa. "Ku tsaya kuci abinci an gama tun dazu" Mami tace "muci abinci muji bacci kenan, ni kin sanni da na koshi sai na fara neman wurin kwanciya" "Shiyasa nake jin alamun kinyi ukun yadda na sanki ashe" Mairama tace tana murmushi. Yaran dariya suke yi Zainab tace lokaci ne ai, shekarunsu na soma ja zasu fara ajiye kiba ko da ta girma ce. "Mama banda ni a kibar, mu sojoji ina muka ga lokacin yin kiba muna faman guje-guje a daji" Sai da kowa ya dara Fauziyya ta tabo Ghazalatu "kinga kanwar Hamma ko, Radhiya ake ce mata. Yini daya kika yi da ita sai cikinki ya kusa ciwo don dariya" "Na ganta". Gabadaya ranta babu dadi tun da ta ga wacece Alheran din da Awwab yake ta rawar kafa a kai. Tayi zaton wata 'yar yarinya zata gani da bata fi Zayyana ko kasa da haka ba. Dama jiya saboda wannan budurwar mai idanu a tsatstsaye ya taho Kano ya barta. Shigowar Awwab da Abdallah wanda ya kawo su Mami dan Hussainarta daga waje kenan daidai lokacin da Mamin take ce mata. "Idan ke soja ce bakiyi kibar ba mijinki da ba soja ba zaiyi ne" Tsuke baki tayi tana kada yatsa "No, no, no, no , no Mami. Ni likita zan aura fa. Kinsan shima aikinsu babu zama bazaiyi kibar ba" "Mara kunya" Mairama tace tana daka mata duka a baya. Su Ibrahim an sami abinda ake so suna ta dariya. Zainab ta maimaita musu abinda Radhiyan tace dazu wai ta raina kowa idan ba soja da likita ba. "Mama mu dasu aikin ceton rai muke yi shiyasa kowa bai kai mu ba" Mairama sarkin kunya sai ta soma tsoron kada Radhiyan ta fadi wani abin da yafi wannan. Ta tuna ranar da tace mata tana abu kamar ba bafillatana ba. Ita kuwa ta ce dama ba ita bace, su Sakkwatawa ne. "Ku barni da ita kwanannan zanyi mata miji a aurar da ita mu huta" inji Zainab. Tun shigowarsu Awwab yake kallon yadda take ta zuba surutu. Dauke kansa yayi ya kalli Ghazalatu ya sakar mata murmushi ta maida masa. Ibrahim ne yace "Mama ki samo mata malamin makaranta kawai" "Tabdi, yo ni malamin makaranta ba sai dai na zane shi da dorinarsa ba. Tsorona zai rinka ji" Fauziyya da ta saka musu ido ita da Awwab tun jiya kuma take fatan hakan tace "ina jin zaki fi dacewa da dreban jirgin sama" Mami da Zainab har Mairama sai su ka yi murmushi. Ko dai Fauziyyan ta ga wata alama ne take hasashen abinda suke shiryawa. Awwab da yake shan ruwa cire kofin yayi yana son jin amsarta. Abinka da 'Yar soja ta hade rai "ke kadai ce bakya sona Adda Fauziyya. Me zanyi da dreba sai kace ta kare min?" Kowa yayi shiru yana kallon Awwab da ya zuba mata idanu harda Ghazalatu da misalin na Fauziyya ya kona mata rai. Bata san suna yi ba bare ta gyara zancen. Zahra ce ta tace "mun ganku a rana ke da Hamma Awwab tunda shima dreban jirgin ne" Ba arziki Radhiya ta tashi yana tsaye ya harde hannuwansa a kirji. Tayi zaton zaiyi fushi sai ta ga shi ya fara dariya kafin sauran "wato mu sai ta karewa mace za ta auremu ko" "Wayo Adda Fauziyya tayi min ba haka nake nufi ba. Maimakon tace pilot yadda zan fahimta" "Sannu Queen Elizabeth wato sai anyi turanci zaki fahimta" Ibrahim yace. "Ka kiyayeni Surbajo" A dolensa yayi shiru da yaji abin zai dawo kansa. Tsokanarta suka cigaba da yi tana karewa kanta. Awwab yana kallon Ghazalatu yace da Radhiya "ki shirya zata kare miki kwanannan kuwa don sai kin auri pilot. Kafin nan kuma ki zamarwa matata 'yar aiki" Mama da Zainab suka kalli juna suna gyada kai da murmushi. Bakin mota suka firfito Mami da Ummi zasu bi karamar motar sauran kowa yace bus din da Awwab zai tuka zasu shiga. Radhiya da jikinta yayi sanyi tana jin babu dadi akan maganar da tayi tace ita ma motarsu zata shiga sai ta zauna a gaba. "Koma cikin 'yan uwanki Radhiya" Zainab tace tana turata bakin daya motar. Awwab ta kalla ko zaiyi magana sai ta kula hirarsa kawai yake yi da Ghazalatu. Juyowa yayi ya kalli Radhiya duk ta zama wata salihar karfi da yaji "ina zuwa" ya cewa Ghazalatu ya taho inda take tsaye a jikin motar. "Zo in nuna miki wani abu" "Wai ba fushi kayi da abinda nace ba kake yi min magana" Murmushi yayi "Silly girl, kawai sai nayi fushi bayan nasan ta kusa kare miki kwanannan...auren dreba ba fashi" "Shine ka barni inata damuwa, kuma a gaba zan zauna inyi ta ganinka tunda yau zaku dawo" Wurin wata katuwar fulawa inda Ghazalatu ke tsaye suka nufa. Suna jiran iyayensu su gama maganar da suke yi su dau hanya ne shiyasa basu tafi ba. "Dama babu mai zama wurinki ne nima inyi ta kallonki" Dariya tayi fuskar Ghazalatu ta hade tsaf da kishi. Awwab yasan me yake bata mata rai don yanzu ta gama fada masa ita bata son yadda yake yiwa Alheran dinnan bayan ba karamar yarinya bace. Domin ya kwantar mata da hankali yaje ya kira ta. "My G, ga Alheran kanwata. Alheran ga Ghazalatu kanwata kuma matar da zan aura" Sai yanzu hankalin Ghazalatu ya kwanta sosai. Ta kurawa Radhiya ido sai ta ga yarinyar ko a jikinta sai ma dariyar ta take yi fuskarta ta tana wani annuri. Dage girrarta duka biyun ta rinka yi yadda ta saba idan zata yi tsokana " Eyye eyye Hamma shine kace zanyi aiki a gidanka? Naji zan rinka tayata indai itace matar" "Bana bukatar house girl so kiyi zamanki" Ghazalatu tace tana shan kamshi. Fuskar Awwab kadai zaka kalla kasan kalaman basuyi masa ba. "House girl?" Yace yana kankance idanu. Ta fuskanci ransa ne ya baci sai ta wayance "naji kace za tayi min aiki ne dazu" "Lallai wannan 'yar wulakanci ce" Radhiya tace a ranta. Ita bata san maganar wasa bane da zata yi tunanin da gaske aiki zata je yi mata. Hamma Awwab yafi karfin komai a wurinta tunda yake son Umminta da babanta da ita kanta. Kuma ba wani abu bane a wurinta ta taya matarsa aiki amma wallahi ba dai taje a house girl ba. Idan bata gwaba mata magana ko yaya bane tasan bazata ji dadi ba shiyasa ta ajiye katon murmushi a fuskarta tace "ko babu albashi zanyi miki aikin ma, kinsan mu 'yan kauye bamu san komai ba sai bautawa 'yan birni" "No ki barshi fa bana bukata, idan ina so Yayana zai nemo min" " Yes dai inzo inyi ko babu komai zan hutar da Hammana barnar kudi" Hannuwansa ya zuba a aljihu yana kallon ikon Allah. Rigima ke neman tashi tsakaninsu daga su gaisa. Daure fuska yayi yace "ku wuce ku shiga mu tafi" Suna zuwa bakin motar Ibrahim zai bude gaba ya shiga saboda yana son Awwab ya koya masa tuki Ghazalatu ta riga shi budewa itama tana son zama kusa da masoyinta. Radhiya da ta fisu iyawa tayi sauri ta shige ta kofar bayan ta haura gaba. Awwab kansa sai ganinta yayi ta kusa fado masa garin sauri. Gyara zamanta tayi ta ballawa Ghazalatu da Ibrahim harara suna tsaye suna kallon abinda tayi. "Ni dama ga wurina can kusa da Zeezee" Ibrahim yace yana shiga bayan inda Emzee ke yi masa dariya. Ghazalatu ta kalli Awwab tana jira yayi magana "kace ta koma baya ina son muyi magana" "Idan muna dawowa sai ki zauna a nan din kinji." Tsabar bakinciki ji tayi kamar tasa ihu. Mami daga cikin tasu motar tace ta shiga su tafi rana tana kara yi. Hararar Radhiya tayi ita kuma tayi mata gwalo. "Bansan mutum nayi ba sai naji a jikina" "Alheran" taji yace muryarsa a dake sannan ya kalli Ghazalatu da take ta cika tana batsewa "ki shiga ki zauna mu tafi" Daurewar da yayi yasa ta shige ba don ta hakura ba. Radhiya da take kusa dashi kuwa ji tayi kamar ta koma baya ita ma. Tukinsa kawai yake yi wanda baya masa dadi saboda bin bayan Abdallah da dole sai yayi tunda bai san hanya ba. Motar duk sai tayi musu shiru mai bakin tsoro ya hanata magana Zayyana har ta soma gyangyadi a jikin Zahra. Su basu ma san me yake faruwa ba sai Ibrahim da yake tunanin saboda zaman gaba ne kawai. Can dai taji shirun ya isheta ta dago a hankali ta saci kallonsa. Titi dai yake kallo har yanzu babu wannan sakin fuskar. "Hamma" Radhiya ta kira sunansa a tausashe. "Kar ki dameni please" Shiru tayi ran sojoji ya baci. Ita kadai zaiyi fushi da ita bai ji masoyiyar tasa tana kiranta housegirl ba. Tura baki tayi ta juya duk jikinta tana kallon waje. Shima satar kallonta yayi yayi gajeren murmushi. Da gaske dai Alheran dinsa bata chanja ba sai ma abinda yayi gaba. Su mata abin rigima baya yi musu kadan ya kula. Su biyun kowa matsayinta daban to me ya kawo rigimar. Ko don Ghazalatu tace mata house girl? Shima kalmar bata yi masa dadi ba. Duka su biyun sai yayi aikin basu hakuri kenan. Haka kawai zasu tayar masa da hankali kamar wasu kishiyoyi. Ta mudubi ya hango Ghazalatu ita ma fuska babu wakwala kamar ma kuka take shirin yi. A take ya jinjinawa masu mata biyu. [02/11 7:31 AM] My 2nd Mtn: 27. Sun isa Sumaila karfe biyu na rana a gajiye saboda tashin wuri da suka yi. Emzee ne ya koma jagora da suka shigo garin shiyasa tasu motar take gaba. Awwab ba tsayawa Emzee din ya fita da sauri saboda magana da yake son yi wa Ummin tasu. Gefe ya ja ta ana kokarin fitowa da kayan da ita kanta bata san da zamansu ba a boot. "Ummi wai kuwa sun san zamu zo da baki?" Yace yana rage murya. "Na fadawa Innawuro da ta kira nace ta sanar dasu tunda kaga ba waya gareni ba. Menene?" Da damuwa a fuskarsa yace "kada muje a rasa abinda za'a basu nasan bazaki ji dadi ba" Murmushi Mairama tayi. Zayyan dinta akwai hankali da nutsuwa ga zurfin tunani. Rashin abin tarbar baki tabbas zai iya faruwa don tasan halin gidan nasu "to yanzu me ya kamata ayi?" "Idan kina da kudi kawo naje na siyo gurasa da tsire kawai" Karamar jakarta ta mika masa. Dubu uku ya cire cikin kudin da Ardo ya bata ne da zasu taho. Ya tafi tana ta masa addu'a a zuciyarta. Radhiya kuma ta kama kofa za ta bude Awwab ya danna central lock. A zuciye ta juyo "bude min" "Ko nima balotellin zaki yi min ne? Zai fi miki sauki akan wannan juya idanun" bayansa ya juya "Ghazalatu zauna magana zamuyi" Murtuke fuska tayi itama ya kallesu ya tabe baki. Mata, mata halinku sai ku. Su Zayyana duk sun fita sun bi bayan iyayensu cikin gidan. Basu san me yasa ya tsayar da su Radhiya ba amma ko ma meye tabbas basu ga alamun wasa a tare da yayan nasu ba. "Kun gama fushin ko har yanzu da saura?" Ghazalatu dama jira take yi "don na biyoka shine zaka wulakantani akan wannan yarinyar kamar wata kishiyata? Tunda muka zo sai kayi mata magana sau uku baka yi min daya ba. Sannan nazo shiga gaba ta shige duka ka kyaleta. Idan wani abu ne tsakaninku gara ka fada min da wuri na san matsayina. Amma bazai yiwu ta rinka jin kanta kamar wata a wurinka ba tana neman shiga tsakaninmu" "Kin gama? To bari kiji in fada miki. Alheran wata ce a wurina Ghazalatu kuma bazan yarda kici mata mutumci ba. She is my sister kamar yadda na dauki su Zahra haka ita ma na dauketa. Idan ma kishi zakiyi ba da ita zakiyi ba. Ki bari sai kin hadu da wadda take da matsayi irin naki a wurina" Dazu gani take wannan Ghazalatun take ko wa tayi mata rashin mutumci amma maganar Awwab ta yanzu tafi kona mata rai akan komai duk da cewa gaskiya ce ya fada. Ita din kanwa take a wurinsa amma meyasa kalaman nasa suka yi mata zafi haka. Daga haduwa dashi kwana daya kawai take neman matsayi fiye da abinda zai iya bata. To me ma take nema ta tambayi zuciyarta. Ranta taji ya cunkushe gabadaya taji ta tsani zaman da take yi tare dasu a motar. Dago kai tayi kamar ba ita bace zuciyarta take kai kawo a abinda ta kasa gane zahirinsa ta kalli Ghazalatu. "Matar Hamma kiyi hakuri don Allah. Haushi naji da kika kirani house girl. Ke da kishiya sai dai mota in sha Allahu" Awwab kallonta yayi yadda ta nutsu tana magana kamar ba ita ba. Suka hada ido tayi masa wani murmushi da ya tsaya masa a rai yaji kamar ya dora hannunsa a kumatunta da ya lotsa. "Kaima kayi hakuri bazan kara ba" Tana kaiwa nan ta kama kofar zata bude sai ya cire lock din ta fita tare da duka tunaninsa kamar ta zare masa duk wani kuzari da yake jikinsa. A katon soron gidan ta ya da zango jikin wani dan tudun siminti da akayi domin zama. Abinda ya bata mamaki bai wuce kukan da ta fashe dashi sosai ba. Ji take idan bata yi ba ma zuciyarta zata iya bugawa. Kukan na meye? Oho, itama bata sani ba. Abu daya ne kawai ya tsaya mata a rai kalmomin Hammanta na karshe wai Ghazalatu ta jira sai ta hadu da mai matsayi irin nata a wurinsa sannan tayi kishi. Tsaki taja tana jan hanci "Mtswwww in kun ga dama ku cinye juna karewarta, aikin banza. Dadinta dai nima Kawu Zakari ina komawa zai ce yana sona. Mu za'a yiwa burga da wata soyayya? Maza na fita filin yaki ko su je ceton rai a asibiti kai ka makale a jirgin sama kamar tsuntsu wa zai so ka idan ba wannan mai kwalakwalan idanun ba dama" Hannu tasa ta share hawayenta bayan ta gama rarrashin kanta ta shiga gidan da sallama. A can mota kuwa Awwab da Ghazalatu an bude sabon shafi sai dai a wurinsa babu wannan dokin jikinsa kamar wanda aka yiwa duka haka yake ji. Su ma tana shiga suna shigowa. Tabarmi ne aka shimfida daga can gefe inda inuwa take don dakunan gidan babu mai girman da zasu zauna a wadace da su da kuma tawagar Malamijo da suka zo kallon 'yan gayu. Akan abin sallah yake zaune ya mike kafafu dawowarsu kenan daga asibiti an zuke fitsarin an hadosu da tulin magunguna. Sallamar baki yasa aka kawo masa babbar riga ya saka ya rufe kasusuwan kirjinsa. Radhiya ya hango zai fara tsokanarta sai da ta matso ya kula idanunta sunyi ja sosai. "Kukan me kika yi ke kuma?" Kamshin turaren Awwab kawai ta ji a bayanta ta gane ya shigo shima. Gashi ana ta kallonta idanunta sunyi ja haka saman hancinta. "Ji nayi kamar ana kuka ance ka tafi shine na fara nawa nima. Ashe ashe kana nan." "Kaniyarki" Malamijo yace ya yi mata dakuwa "Mairama ki rasa da wa zaki zo gidan nan sai da wannan aljanar 'yar taki, ko wancan hutun da kika turo su ni banji dadin zama da ita ba. Sau biyu tana yi min barna a gona" Awwab sam hankalinsa kasa kwanciya yayi da aka ce tayi kuka. Bayan ya gaisa da mutanen gidan da suke wurin fuskarta ya rinka lalube yana son hada ido da ita amma fafur taki. Baya so ya zama sanadin kukanta ko kadan. Muryarta ya tsinkaya tana cewa "wai me ya sameka ne Malamijo, ciwon me kake?" Hajjo ta soma dariya za ta tona masa asiri a gaban 'yan gayu yayi saurin cewa "zazzabi ne mai zafi ya damkeni kamar bazan kai labari ba. Ai naci wahala ba kadan ba. Yanzu ma daga asibiti nake" Sannu da adduar samun sauki suka yi masa. Yadikko ta soma cigiyar Emzee shine Mairama tace ya tafi sayen gurasa da tsire wai yana sha'awa. Hakanan Malamijo ya tsargu ya daure ya cije yace a kira guda cikin samarin gidan ya yanka kaji uku ayi musu farfesu. Mami ce tace " Kada ka damu Baba muna sallah zamu juya akwai tafiya a gabanmu. Ibrahim idan Karami ya dawo ku shigo da kayan nan ciki" Nan fa hankalinsa ya tattara yayi waje. Ba dadewa Emzee ya dawo da ledoji a hannu. Ya sayo gurasar da nama a wadace harda lemuka irin su cway, lacasera da maltina masu sanyi. Ashe 'yan matan yunwa suke ji. Kafin Hajjo ta gama dafa shinkafar da Malamijo ya aunar mata bayan ya koma daki daga buhu daya cikin wanda su Mami suka kawo don kwarewa a tsiya har sun koshi. Sallah kasaru suka gabatar azahar da la'asar sannan suka ce zasu koma. Idan sun isa da wuri ma Katsina zasu wuce kawai saboda kada su yiwa Zainab yawa a gida. Da sauri Radhiya ta dago kai rike da gurasa a hannu sai lokacin take ci ta kalli Awwab. Hada ido su ka yi shima tun dazu ita yake kallo. Kin kula shi da take yi shine yake damunsa. Kwana biyar Mairama tace zasuyi a nan sannan su wuce Rugar Barkindo. Sai bikin su Zahra ya rage sati daya zasu koma Katsina. "Wannan dan samarin baici komai ba zaku tafi. Radhiya ko saurayinki ne kika kawo baki gabatar min dashi ba?" Malamijo yace yana kallon Awwab. Yaron da gani akwai maiko maiko zai so ya auri jikar tasa. Murguda baki tayi da ta ga Ghazalatu ta sha kunu "idan ma kishi kake yi to ka dena Malamijo, ka jira sai na sami mai matsayi daidai da naka amma ba wannan ba." Yanzu ya gano bakin zaren. Da gaske maganarsa ce ta bata mata rai harda kuka don sai da ya gano ja da kankancewar da idanun nata suka yi. Da ya juya kalaman a bakinsu sai ya ga rashin dacewarsu a dazun. Mami haka nan ta fara zargin ko Awwab din ya yiwa Radhiya wani abin ne ya bata mata rai. Bazasu so ayi aure basa son juna ba. 'Yar dabarar manya ta kirkiro wadda bata baude da yanayin Awwab din ba a yadda ta san shi "haka yake baya son cin abinci, ga tuki a gabansa mai nisa" "Ke zuba masa abinci ki kai masa wajen soro tunda babu kowa a wurin. Kila kunya yake ji ko dan Ummi" Mairama tace tana murmushi. Hakan yayi masa daidai har ransa. Abincin da Hajjo ta dafa da wanda Emzee ya siyo ta zuba masa a plates biyu ta dora akan tray tayi gaba batare da tayi masa magana ba. Ghazalatu kamar ta bisu sai ta tuna bayan fitarta dazu daga motar yadda ya jaddada mata son da yake mata. Tayi ta gama iyayinta ta koma kauyensu kowa ma ya huta. Wurin yana da fadi daga kan tudun dazu ta ajiye abincin ta koma daukar tabarma suka yi kicibus. Wai sai tayi masa murmushi a zuwan komai lafiya shima ya maida mata. Da ta kawo tabarmar yana zaune a gefen abincin ta shimfida ta sauke masa a kasa. "Hamma sauko kaci kada kuyi dare" Kura mata idanu yayi sai da taji kallon ya hanata motsi sannan ya sauko ya zauna a kan tabarmar ya tankwashe kafafunsa. "Zauna mu ci" "Na koshi" "Ban isa da ke ba ko?" Taji yace a hankali yana daukar cokali. Bata so yana magana irin haka sai ta taji zuciyarta tayi wani iri. Zama tayi a daya bangaren tray din ta tankwashe kafa yadda yayi. Cokali daya ne a ciki ya debi abincin yaci ya mika mata. Satar kallonsa tayi ya dage mata gira da ido yayi mata nuni da taci. Sai da ta sauke numfashi tana kunyar wannan abu ta rufe ido taci da cokalin da ya fito daga bakin Hamma Awwab. Karba yayi ya sake ci ya kuma mika mata. Za tayi magana yasa hannunsa a kan lebensa sai ta hakura. Duk loma daya sai ya mika mata har suka cinye abincin gabadaya. "Wannan gurasar dai bani da inda zan cusa ta ki mayar ciki" Dama ta kagu ta tashi ta kinkimi tray din za ta gudu ya danne gefensa. "Ban gama magana ba" Komawa tayi ta zauna ba don taso ba taji yace "I am sorry Alheran. Nazo ina ta yi miki laifi ba da niyya ba" Sake karyar mata da zuciya maganarsa tayi. Shi kam bashi da girman kai. Wai ita dinnan kanwar bayansa 'yar kauye yake bawa hakuri. "An daure harshen ne? Talk" Rufe ido tayi sai hawaye sharrr kamar famfo. Ta rasa gane irin emotions din da suke yawo a zuciyarta yau dinnan. Hankali a tashe yace "Ya Allah, me nayi miki kuma?" "Nima ban sani ba Hamma" tace tana kara fashewa da wani kukan. Me ya sami zuciyarta ne a cikin kankanin lokaci? Rabonta da kuka tun farkon zuwan su Mami rugarsu da ana bada labarin abinda kawunsu Maikudi yayi. Kuka tayi harda shessheka Awwab bai hanata ba har ta gama don kanta ya bata tissue irin ya ledar nan karama ta goge idanunta. "Feeling better?" Ta gyada kai tana kallon kwanukan gabanta. "Good, yanzu ki fada min tsakani da Allah me ya same ki? Nine ko?" Rasa me za ta ce masa tayi ta kare da cewa "ba kaine kake murna zaka tafi ba" "Ke kuma ba kya so na tafi?" Kada fa ya fassarata ta soma tunani "dena fada kada budurwarka taji. Duk baka tambayeni labarin komai nawa ba zaka koma kila bazan kuma ganinka ba sai an dade. Shine naji raina ya baci" "Sai nake ji kamar dai maganata ta dazu ce ta baki haushi. Amma nima bana son tafiyar ko sabawa bamu gama yi ba ko" yayi yar dariya. "Eh, ko askina ban fada maka me yasa akayi min ba" Sai da yayi dariya sosai yace "an gaya miki ni bana tsoron kiyi min balotellin ne? Ina sane naki tambaya kada na janyowa kaina" "Ashe kai matsoraci ne" ta kyalkyale da dariya kamar ba ita ta gama kuka ba. Sweet ya dauko daga aljihunsa irin mai mint dinnan ya bare ya jefa a baki yana dariyar matsoracin da ta kira shi. "Dazu ka raba abin leda baka bani ba yanzu ma a gabana ka shanye alawar? Kuma nice karama ni ya kamata ka bawa" "Sorry gashi in kina so" ya cirota daga bakinsa dama niyyarsa kenan. Wata zuciyar tana kwabarta wata tana ingizata har ta mika hannu tayi saurin janyewa "wayo zaka yi min, na tuna me kace dazu" "Ke dai kina kyankyamin abin bakina kawai" "Haba dai..." bata rufe bakin ba ya saka mata sauran da ya rage har hannunsa yana taba lebenta. Saurin tashi tsaye yayi ita kuwa ta rasa me zata yi ma. "Ki rage min kinga kadan na sha" Lumshe ido tayi tana tsotsar alawar yana kallon yadda bakinta yake motsawa yana jin kamar ya taya shi. Girgiza kai yayi da sauri. Lafiyata kalau kuwa ya tambayi kansa. "Ahhhh" Radhiya tace ta bude bakin ta mike tsaye yadda zai gano cikin bakin nata sosai. Ta shanye alawar saura yar kadan. "Cewa nayi ki rage min fa" "Nima bata isheni ba. Babu kari?" "Zan gamu dake ne, muje ciki su fito bana jin zamu iya wucewa a yau sai dai mu kwana a Kano" tafiya ciki ya soma yi. "Hamma gashi" ya juyo ta miko masa yar karamar sweet din ya karba yana kallon cikin kwayar idonunta ya saka a bakinsa. Bata sani ba ko shima yaji amma ita dai wani abu ne ya zarga mata har kasan zuciyarta. [02/11 7:29 AM] My 2nd Mtn: 15. Maikudi ne tsaye a ofishin da aka tura shi cikin barikin su Zayyan akan maganar kudi ne dai. "Jiya Babanku yazo akan zancen nan mun fada masa bamu da komai. Ya bada adireshinsa duk lokacin da kudi yazo zamu nemeku" officer din ya bashi amsa bayan ya gama jero tambayoyi. Yana hargaginsa na rashin mutumci yace "Ashe cewa yayi shine babanmu don ya ci kudin gado. To wallahi karya yake. Babu wata alaka ta jini tsakaninmu" Wani sojan ne ya shigo yana tambayar wancan me yake faruwa cikin harshen turanci. Sai da ya sara masa ya bashi amsa da gani ya fishi mukami. Maikudi yana jin ana bayani duk da bai iya gane duka maganar amma ya dan fahimci me akeyi ya katse wancan "You understant Zayyan Muhammad Tureta is die? Me. Biggggggggg broza. Is me faza dinmu daya ai" ya nuna kansa yana murmushi yana so su fahimci shine babban wan Zayyan. Mutumin ya hade rai yace a kore shi kuma idan ya kuskura ya sake zuwa ba'a neme shi ba a kulle shi saboda yana mudu hayaniya. Dayan yana soma fassara masa bai tsaya jin karshen ba ya fice yana ta Allah Ya isa an kashe masa kani. A hanyarsa ta komawa ne ya rinka tunanin dole fa akwai abinda Zayyan ya barwa matarsa. Idan ba haka ba da me suke rayuwa duk tsahon lokacin nan? Yafi karfin ita da kwadayayyen babanta suyi masa wayau akan hakkinsa. Yana zuwa dakin da Malamijo yayi masauki ya shiga. A shirye suke suna jiran dawowar Mairama. "Dama nazo akan yaran nan ne Radhiya da Zayyan. Nace ko zaka yiwa Mairama magana idan ta yaye shi zan zo na dawo dasu gabanmu saboda gatansu dai bai wuce wurin dangin mahaifinsu. Idan kun tafi yanzu kai ma nauyi ne kawai zai kara hawa kanka. Sannan bazan zuba ido bane tayi aure 'ya'yana su koma agolanci a gidan wani" Malamijo an tabo inda yake masa kaikayi kuwa. Ina zai kai karin bakuna uku a gidansa. Gara Mairama yana son abarsa, amma yaran nan da aka ha'ince shi yayi ta yiwa babansu kallon kitse ashe rogo ne "indai wannan ne babu damuwa. Zanyi magana da ita kuma dole ta amince don nima bazan so suyi rayuwar agolanci ba azo ana wulakantasu" Maikudi ya fita da wani mugun murmushi. Soro ya koma ya zauna jiranta. Ilai kuwa babu jimawa sai gata tana ta sauri kada a gaji da jiranta. Dukawa ta danyi ta gaishe shi ya yafito ta da hannu. "Yaki zo Mairama. Magana nake son yi da ke" Kanta a kasa ya fada mata yadda ya fadawa Malamijo. Ai tuni ta saka kuka iya karfinta tana rokansa ya rufa mata asiri ita bata da niyar sake aure. "Kinga da har mun gama magana da babanki" Gabanta ne ya fadi. Ta san halin Malamijo kuma tas zai bada yaran nata. "Don Allah kayi hakuri" "Naji, amma bazaki bar garin nan ba sai kin fito da dukiyar kanina. Dole ne a raba gadonsa saboda a sauke masa nauyi" Hannunta yana rawa ta zaro envelop dinnan daga jakarta ya warce gabadaya. Sakar masa tayi kafin ya hada da hannunta. "Daren jiya na gansu shine nace dama yanzu zan fito dasu ayi abinda ya kamata" Kankance idanu yayi yana kallonta bayan ya zaro takardun gidan da kuma damin kudi da aka nannade da kyauro "ashe ke mutuniyar banza ce ban sani ba? Wato da guduwa zakiyi da komai saboda tsabar mugunta da bakin hali kamar na tsohonki" Ta shiga girgiza kai tana hawaye "a'a wallahi" Wasikarta ta hango ta fadi ta mika hannu ya taketa da sauri da kafa "meye a ciki?" Hankalinta yayi matukar tashi "wallahi Allah wasika ce ya bar min. Ba takardar komai bace" Sai ta ga yayi murmushi saboda ya fuskanci yadda ta rude "soyayya manya" yatsansa ya kada mata "kalli nan, zan cire takardun gidan saboda dama ina binsa bashi da bai biya ba. Ina jin gidan ma bazai isa ya biyani ba amma dai su kadai zan dauka. Muje ciki idan munafukan dattijan nan sun zo ki basu kudin a rabawa wanda aka ga damar bawa. Ni kuma nayi miki alkawarin babu wanda ya isa ya rabaki da 'ya'yanki kuma zaki koma Kano da wasikar masoyinki" Mairama kallon mugunta irin ta Maikudi ta tsaya yi ta rasa shawarar yankewa. A zatonta zaa raba gado a barwa yaranta gidan sai su zauna a ciki. Ita kuma a cikin kudin ta nemi abinyi domin kula dasu. Wani hawaye ke bin kuncinta tana jin zafinsu har zuciyarta "hakan yayi maka?" Ya dage gira "yayi...ki sani idan kina tunanin juya magana ko Jume tayi kadan tasa na bar miki yaran nan balle kuma wancan tsohon Mal. Aminu. Mahaifinki kuma a yadda na fahimta ko sadakarki na nema zai iya hada min" Share idanunta tayi tabi bayansa. Kowa yayi zaton kukan tafiya ne take yi da mutuwar mijinta. Su Mal.Aminu sun zo ta dauko kudi ta mika masa. A take aka kira wani malami ya kasafta da aukinsu kuwa aka bata nata aka ware na yaran yace batun bashi fa Mairama tace ya tabbatar mata babu msi binsa komai kafin ya tafi. Maikudi ko tari baiyi ba ganin babu mai gadon nashi sai su kadai. Jume har dadi taji yayi hankali. Nasiha da ban hakuri aka sake yiwa juna sannan Mal.Aminu ya roki alfarmar kada ta tafi ta yanke zumunci dasu albarkarcin 'ya'ya "mu kuma nan babban kalubale ne a garemu mu da gwamnati. Mu dubi marayun yaran nan da mahaifiyarsu kafin mu ga me Allah Ya tsara musu. Haka ma gwamnatin ta dubi rayuwar sojojin da take takama da sadaukarwarsu. A dubi masu ran wanda suke a bakin aiki, a dubi masu rauni da nakasa sannan a dubi iyalan mamatan domin a gaskiya akwai nakasu mai girma a rayuwar iyalan bayin Allahn nan" Sun fara fitowa mata ana ta kuka Maikudi ya samu ya tarar da Malamijo shi kadai iska tana ta kada yalolon yadin jikinsa yana manne masa ramar tana kara nunawa. Takardun gidan ya nuna masa yana murmushin samun nasara. "Naga ka kawo idanu ka dora akan dukiyar da baka da alaka da taruwarta shine nace bari dai na nuna maka waye Maikudi." Ware ido Malamijo yayi ya karewa takardun kallo "na meye?" "Na gidan Zayyan ne wanda yanzu ya zama nawa. Kana iya kaini kotu don a kwatarwa 'yarka da jikoki hakkinsu amma ka sani kana yin hakan zan rabata da yaran nan ni kuma. Ta fada min akan ta baka dukiyarta gara kowa ya rasa don baka ragawa kowa akan kudi" Kallon Mairama yayi zuciyarsa tana tafarfasa. Wato Zayyan yana da gida shine ta dauka ta bawa wan mijinta tana tunanin zata dawo masa gida ta jabe ya ciyar dasu. Lallai Mairama bata gama saninsa bane shiyasa har taje tana tona masa asiri. Har shi zata ha'inta yana mahaifinta. Kwafa yayi yana jiran su kebe don bashi da bukatar magana a gaban mutanen da ya kula bakinsu duka daya. Maikudi kuwa dariya yayi bayan ya tafi. Alamun Malamijo da ya gani ne yasa shi wannan magana sai gashi tazo daidai da halin nasa. Mairama da Zayyan ma ta kasa tonawa mahaifinta asiri a gabansa me zai kaita fada a gaban Maikudi? Radhiya ta dauka Hajjo ta goya Zayyan suka tafi tashar da zasu sami motar Kano. Sai da suka dau hanya don Salisu ya biya su kadai ne a ciki Mairama tana hawayenta Nene Marka na bata baki kawai Malamijo ya soma fada akan bayar da takardun gida da tayi. Kai, ita kam da me zata ji ne a rayuwarta. Tana kuka tayi musu bayanin yadda abin ya kasance. "Ko dai mu koma ne a karbo takardun? Duk tsiyarsa baifi karfin hukuma ba fa Mairama" Salisu yace nasa ran a bace. Tsorata tayi "don Allah ku kyale shi. Yaran nan zai karbe, babansu ma baiji dadin zama dashi ba" Nene tace "Duk da haka Mairama mu zamu tsaya miki. Gidan a ina yake?" "A Kano ne" Salisu ya tabo dreban "Malam don Allah kayi hakuri ko zamu koma" "Babu inda zamu je. Idan kuma sai kun koma to ni a ajiyeni a nan." Nene Marka tace "haba Malamijo meye hakan?" Rufe idanu yayi yana ta fada don sosai yaji haushin maganar Maikudi da rasa gidan da yayi. Ace 'yarsa da yafi so da tausayi a cikin 'ya'yansa ita ce tayi masa haka. "Ina nan kan baka na bazan koma ba sannan kuma ki shirya tunda dangin miji sunfi uba ni bazan dauki nauyin kowa ba. Gida dai gaki gashi kuje a baku daki. Sai yanzu na raina waye Zayyanun ma. Har me yayi miki wanda ni ban miki dubunsa ba. Ji gidan da ya ajiyeki...." Ta daure matuka amma bata jin zata taba jurewa wani ko da kuwa Malamijo ne ya zagi Zayyan. Ko bata aure shi ba yanzu ta san daraja da kimar soja....wallahi yafi karfin raini. "Yayi min komai Malamijo" tace cikin kuka tana rungume Nene iya karfinta har Radhiya sai da ta tsorata "ko a kango muka zauna dashi har abada bani da tamkarsa. Wayyo ni ashe haka mutuwa take da daci da tona asiri? Lokacin da nayi maraicin uwa bansan ciwon rashi ba saboda bamu saba ba. Allah Ka jikan Zayyan ko Ka dauki raina nima na huta" Zubar hawayenta ya taba Malamijo bare da ya ga ta rike kirjinta da yake mata mugun zafi. Dreban yace wa su juya ta dago rinannun jajayen idanunta. "Allah Ya kaimu masu gidan su girma zasu karbi abinsu da izinin Allah. Amma a yanzu tunda yace yaji ya gani zai ci haram bazan shiga tsakaninsu ba" Duk rashin halin Hajjo sai da tayi kukan tausayin Mairama. A haka suka tafi Kano Salisu yana ta mamakin halin Malamijo. Ashe Salame gado tayi na munin hali ba taka haye ba. Tare suka sauka a tasha ya ja Mairama gefe ya fito da kudi masu tsoka ya damka mata sannan suka nemi motar Sumaila shi kuma ya shiga hayis zuwa gidansa. Dama ya riga ya gama shawararsa tun a hanya shiyasa yana ganin yadda Salame ta fito muzumuzu ita a dole tana cikin alhinin mutuwar masoyi ko sannu bata yi masa ba ya dakatar da ita zata tashi ta bar falon saboda ta ganshi. "Salame ki hada kayanki ki tafi gida na sakeki saki daya" Kiris...sauran kiris irin mai riss dinnan zawo ya tsinke mata. Tunda take bata taba jin fargaba da tsoro kamar wannan lokacin ba. Ya saketa ta tafi ina? Sumaila? Allah Ya kiyaye. A iya zurfin tunaninta Salisu yana mata son da zai iya hadiye kowane abu tazo dashi. Shiyasa take yadda taga dama iyaka yayi fada anjima ya dawo yana bibiyarta. To ko dai kunnenta baiji da kyau bane. "Ni ka saka?" "Halifa da muka haifa da ana komawa baya Salame bazan so hada jini dake da mahaifinki ba. 'Yar cikinsa tana cikin magagin rashin miji amma dukiya yake nema duk arzikinsa. Wallahi bazan iya ba. Kije Allah Ya baki daidai dake." Kande ya kwalawa kira tazo ya cire naira goma yace ta wuce ta kaiwa mamansa Halifa yana tafe. Dayake daga can gidansu aka kawota ta riga tasan gidan. Salame tana kame ta kasa motsawa ya wuceta ya shiga daki. Sai da abin ya sami wurin zama a kwanyarta ta shiga ta fara masa ihun masifa. "Wato akan Mairama ka sakeni saboda Malamijo ya bata mata rai. Bazaka burgeni ba sai naga ta tare a gidan nan ranar asabar" "Ki fita sawunki a likkafa kafin na tashi" yace daga kwance Tafa hannuwa tayi " nima na huta da auren kaddara zama da mijin da baka so" Duk inda zata cusa masa haushi ta rinka nema ko a jikinsa tunda ya rabu da kwallon mangwaro ya huta da kuda. Gidansu ta koma ko ta kan Halifa bata bi ba. Awa uku tsakanin saukar su Malamijo da dawowarta gidan. Yadikko ta tareta ganinta da akwati niki niki "ke kuma daga ina?" "Sakoni yayi" ta fada cikin yanayin ko in kula. Ashar Malamijo ya lailayo ya saki yana kara tunzura da yadda take magana ko a jikinta "wai nufinku duk kun dawo min gida kenan?" "Ya son ranka? Ca nake mata biyu ka saki a dan tsukin lokaci guda, ai gara ka dana" Hajjo ta fada masa sannan ta saki labulen dakinta. "To Al-Qur'an daga ke har Mairaman kowa taji da kanta bazan iya ba. Yara masu bakin hali kun fita a talauce kun dawo a tsiyace" Dakinsu na da ta shige abinta ta barshi tsaye. Nan taci karo da Mairama da kyawawan 'ya'yanta. Kamar ta shareta sai ta fasa tace mata ya hakuri. "Mungode Allah" "Allah Ya jikan shi" "Amin" Daga haka babu wadda ta sake kula 'yar uwarta har suka yi shirin kwanciya. Ganin Mairama da yaranta ya tuna mata da Halifa sai taji wani iri gashi bata yaye shi ba dama. Kyandir Mairama ta kunna a gefen katifar da suke kwance ta kwanto wasikar Zayyan ta soma karantawa. _(Na rubuta wannan takardar tun ranar da sunana ya fito a cikin masu tafiya Liberia. Sai nake ganin kamar jiya muka yi aure har zan tafi na barki. Mairam ban sani ba ko zan dawo ko shikenan tafiyar. Don Allah alfarma daya nake roko kada bakinki ya taba gajiyawa da sanyani a addu'a. Idan kewa ta isheki kinyi kukan rashina ki sani cewa nima ko a ina nake idan na tunoki sai na zubar da hawaye. Ina sonki Fillo Allah Ya sani amma ina son ki saka a ranki mijinki yayi alkawarin bautawa kasarsa ne. Zanfi kowa son son ace ina tare da iyalina kamar kowane magidanci. Sai gashi aikina yayi min tsakani da hakan. Lokaci zuwa lokaci zan rinka tafiyar da babu lallai na dawo. Duk da haka ina alfahari da aikina kema ki tayani kinji. Idan kin haihu kafin na dawo ki zabawa abinda muka samu suna. Ki kular min da 'Yar Soja Alheran innar Daadaa. Sauran kalaman da suka rage a kirjina sai na dawo gareki zaki ji su. Idan ban dawo ba na baki amanar kanki da ta 'ya'yana. Allah Yayi muku albarka. Lt Zayyan Muhammad Tureta)_ TAKWAS [02/11 7:29 AM] My 2nd Mtn: 16.*********** "Ke Radhiya, zo kije kantin sauki ki siyo min yis" Shanyar kayansu da ta wanke take yi nata da na Emzee da Mairama. Kallon Binta tayi tace "ki aiki Emzee ko wani don Allah kinga ni bana fita saboda Ummi" "Inda na aike kin har wani nisa ne dashi da zaki fara yi min felekenki na tsiya. Ko kuwa nace kije ki zauna ne?" Zumburo baki tayi "Ummi wanka zata yi idan na gama shanya. Zaki kai mata ruwan ki ajiye mata soso da komai a kusa da ita inji miki aiken?" Mairama tana daki ta jiyo su ta rinka shafa bango har ta fito. "Ke!" Tace da tsawa Radhiya ta juyo tana jira taji Mairama ta umarceta da zuwa kantin ta fada mata kai tsaye ba zuwa zata yi ba. Tunda mahaifiyarta ta makance ta kara hankali da bambance su waye masu kaunarsu da gaskiya. Malamijo ya gina gidansa da turbar nafsi nafsi kowa ta kansa yake yi. Babu wani jinkai na azo a gani saboda rashin wadata su da abubuwan da ya dace. Idan ka cire Yadikko babu wadda take leka Mairama balle ace mata yaya jiki. Dukkansu take kallo tana jin kanta daidai dasu. A duniya bata da sama da Umminta sai Emzee. Shi kuma haushinsa take ji saboda rashin magana. Gabadayansa bashi da walwala sosai yaron saboda tsangwama musamman daga Salame kafin ta bar gidan. "Ki karba kije ki siyo mata ko ma meye idan kin dawo sai nayi wankan" Radhiya yarinya 'yar kimanin shekara goma sha daya wadda ta gado zuciya ta mahaifiyarta, barkwanci da jarumtar mahaifinta da kuma jinkai da tausayi nasu su biyu ta kekashe idanu "Ummi ni bazani ba idan na tafi ma zubar da kudin zanyi a kwata ko na sayi danmalelen gidan Fadi. Haka kawai yau babu makaranta kowa yana nan taki aikensu sai ni saboda bata damu dake ba" ta kare maganar muryarta da alamun zata yi kuka. Mairama ta daga hannu daga inda take tsaye kamar za ta dake ta "kizo ki karba kafin ranki ya baci" Juya keya tayi ta mika hannu ta baya tana jira Binta ta ajiye mata kudin harda wani kada jiki. Emzee ne yazo ya karbe "ni zanje me za'a siyo miki?" Binta ta warce kudin "bazaka je ba din, wannan fitsararriyar nake so inga uban da ya tsaya mata a cikin gidan nan. Har ni kike juyawa keya saboda baki da kunya" Mairama daurewa kawai take yi saboda rashin ido. Itama ta sani an tsangwami 'ya'yanta an hanasu rawar gaban hantsi saboda an ga tana zaune. Amaren Malamijo Hanne da Binta sunfi kowa kaudi da takura musu. Kuncin zuciyarta ne ya taso ta tuna mijinta. Da yana raye waye duk gidan nan ya isa ya taka su? Yadda kowane uba ke kaunar 'ya'yan shima tasan zai so nasa kuma ya kyautata musu rayuwa. "Karami janyo min hannun yayarka" Da kanta ta karaso gaban Mairama ta kama hannunta don ta nuna mata ta iso. Hannunta ta shimfide mata a gadon baya, dukan ya shigeta amma ta dake. Mairama kanta ciwo take ji yana addabar zuciyarta "in ce kije aiken ki ce bazaki ba saboda ban isa ba? Ko saboda bani da ido sai yadda..." Zubewa tayi a kasa tasa kuka "Ummi kiyi hakuri don Allah zanje." Kudin ta karba daga hannun Emzee tana cewa ya mayar da Ummi daki kafin ta dawo. Rai a bace taje ta siyo yeast din naira hamsin maimakon na ashirin da aka aiketa. Da ta dawo daga bakin kofa ta tsaya ta zura hannu "Gashi" "Shigo ki bani" Binta tace da gadara tana fadawa yayarta "kinga fa irin jarabar da muke fama da ita. Uwa makauniya 'ya'ya marasa da'a" "Mu ba jaraba bane" Radhiya ta maida mata da tsiwa. Bintu bata bata lokaci ba ta kai mata lafiyayyen mari. "Uwarki makauniyar nan ma bata isa ba wallahi" Tana kuka baki bai mutu ba "ba dai uwata ba" Ran Binta ya kara baci "sai ta wa?" "Wanda ya tsargu dashi nake" Radhiya ta amsa kai tsaye. Kafin Binta ta ankara ta fice daga dakin. Da sauri ta kamo Radhiya a tsakar gidan tana shirin shiga dakinsu. Mairama tana jinsu ta yi salati ta sake tashi "me kika sake yi kuma?" Binta ke dukan Radhiya da zagi amma a hakan cewa take ba dai tata uwar ba. Hajjo ta taho kwatar Radhiya Binta ta sake tunzura ta daga hannu zata sake kai mata duka ga Mairama har ta soma hawaye suka ji sallama. Amsa sallamar bakuwar suka yi Binta bata kula ba ta kuma daga hannu taji matar da ta shigo tace tayi hakuri kada ta sake dukanta yara sai da rarrashi. Idanu a soye don itama Binta ba kunyar gareta ba tace "yau ko uban da ya haifi uwarta ne wallahi bai isa ya hanani dukanta ba" Malamijo wanda motocin da ya gani a kofar gidansa suka saka shi tasowa daga majalisar da yake ko kallon mutanen wajen baiyi ba tunda ya ga daya ta shiga gidansa. Ya shigo kenan ya ji me Binta tace ya kuwa murtuke fuska. "Ahhh lallai yarinya kwananki a gidana ne ya kare shiyasa kike zagina. To shiga ki kwaso tsiyarki kizo ki wuce na sakeki saki biyu" Innawuro ta kalli Ali tana jin wani bacin rai. Wato duk tsayin shekarun nan yana nan da bakin halinsa na sakin mata. Ta sani wadda ya saka din tayi laifi amma a bainar jama'a haka ya dankara mata saki. Shi kuwa ko a jikinsa sai ma binta da yayi da kallo yana son tuna a ina ya santa. Matan gidan da yara hankali ya koma wurin Binta da tayi dakinta tana kuka basu kula da Radhiya da take zaune a kasa ba ko bakuwar da take tsaye. Yadikko har kullum ita ce mai hankalin kuma bata gida a lokacin. Mairama ta duka tana mika hannu neman Radhiya da ta tabbatar tana wurin tana kuka. Cikin kuka da ta gaji da laluben tace "ina kike ne?" Muryarta kawai Innawuro taji ta saki baki tana kallonta. Babu tantama wannan ce Mairama diyar Mairo don banda kama ta fuska hatta muryarsu tayi shige sosai. Kafadar Radhiyan tayi sa'ar dafawa ita kuma haushin aiken tun farko ta janye jikinta tana saka kuka mai sautin da bata yi ba a gaban wadda ta daketa. "Ba ke kika ce sai naje mata aike ba" "Allah Ya baki hakuri to tashi muje daki" Mairama ta mikar da Radhiya a daidai lokacin da Innawuro tace "Mairama?" Malamijo kuma yace "Innawuro?" Mairama ta juya duk da bata ganinta ita kuma ta juya tana kallon Malamijo ashe tun dazu yana tsaye. Hankalinta duk yayi kan Mairama tace "muna da yawa sauran suna waje. Na shigo ne sanar da zuwan namu" Yawun bakinsa ne ya kafe, lebbansa suka bushe sai harshe yake ta fitarwa yana lashesu. Duka motocin nan bus uku da canta daya 'yan uwan Mairo ne? Ya sani da kansa ya taba nemansu saboda tausayin Mairama. Amma tuni ya watsar musamman yanzu da rayuwarta take cikin garari. Innawuro ta dawo dashi cikin hayyacinsa da yaji tana cewa Emzee ya fita ya cewa bakin waje su shigo. Yaron ya tafi yin abinda ta saka shi ta dawo da kallonta ga Radhiya da Mairama da suke tsaye kawai a wurin. Gani tayi har yanzu Malamijo yaki magana ta cewa Mairama "muje dakinki kinji 'yata" Mamaki ne fal cikinta bata san ko su waye ba. "Ke muje daki" ta ce da Radhiya Hannunta cikin na Radhiya suka shiga dakin da komai ya kare masa yanzu sai katifa da shirgin kayansu. Rage tsayi Mairama tayi daidai kunnen Radhiya "ina bakuwar take? Kin taba ganinta?" Innawuro tana kusa dasu kuma taji tambayoyin da tayi mata. Radhiya sai ta dago kai tayi mata murmushi tana dan jin kunya. Mairama ta matsa mata hannu "Ki bani amsa mana, idan rigima kika sake kwaso min zaneki zanyi wannan karon" Hayaniya ce ta cika tsakar gidan. Maza ne matasa da magidanta harda dattijai haka ma mata suka rinka tururuwar shigowa. Malamijo yayi tsamo dashi yana kallonsu zuciyarsa ta cika da firgici da ya ga cikin matasan harda masu sanduna. Sandarsu ce ta fulani da ado baya cika sai da ita, amma da yake ba gaskiya gareshi ba sai ya manta da wannan al'adar ya luluka tunanin ko dai duka zasu yi masa. Fulatanci suke ziryan baka jin komai sai sunan Mairama. To shima dai yaren gidansa kenan sai dai suna taba Hausa sosai. Gaban Radhiya sai da ya fadi da ta hangosu q ta tabota "Ummi sun kara yawa wallahi harda sanduna." A kidime tace "dan gidan wa kika tabo kuma?" Harda dan guntun hawayenta na tsoro tace "ni da bana fita wa zan taba?" "Mairama kwantar da hankalinki muje wajen don nan bazai daukemu ba. Ni da su duka dangin Mairo ne mahaifiyarki" "Me? Da gaske?" Matsawa tayi daga jikin Radhiya hannuwanta suna neman kofa da sauri zata fita. Innawuro jiki ya kama rawa ganin da yadda Mairama ta fita. Radhiya ta kalla hawaye suna wanke fuskarta. "Bata gani ne?" Radhiya tabi bayan Mairama don ta karasa da ita gabansu tana cewa "eh" "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" ta iya fada tana kuka har wajen suna jin sautinta. Duka idanunsu sun koma kan Mairama tana kuka take tambayar Radhiya da ta rike mata hannu su nawa ne? Baffa Gide kamar yadda 'ya'yan 'yan uwa suke kiransa ji yayi kamar iska zata daga shi don tashin hankali da yaji me takw cewa kuma tamkar ya ga Mairo haka kamanin Mairama suke da na 'yar uwarta. Kyaunta ne yasa Malamijo zabarta da biyan bashi duk da a lokacin Innawuro ta girme mata kuma itama bata yi aure ba. Tsakar gidan kamar gidan kallo ya koma. Ga dangin mahaifiyar Mairama ga ahalin gidan Malamijo kacokan. Shi Baffa Habubakari kuka yake ma saboda rauninsa yafi na dan uwansa. 'Ya'yansu jiki yayi sanyi. Basu san Mairo ba don manyan ma suna kanana komai ya faru amma sun san wannan makauniyar da ta nufosu jininsu ce. Ga dai idanu a bude amma basa ganin komai. Sai da suka zo tsakiya Radhiya taja hannunta don su gaishesu tunda ta ga akwai manya "ummi mu gaishesu" Emzee sai ya baro gefe shima ya dawo ya durkusa tare da Umminsa da Addarsa. "Ina wuninku, yaya hanya....Allah sarki ashe baku manta dani ba" shine abinda Mairama take cewa tana ta waige hagu da dama saboda rashin sanin a ina suke. Su Radhiya ma gaishe su suka yi bakin Mairama kamar gonar auduga duk da bata san mutum nawa bane. Ganinsu su ukun nan ya ishi bawa tausayi. Ga uwa mai cike da kuruciya amma makauniya mai marayu biyu a gabanta. Ga kuma 'ya'yanta tamkar zakuna suna gadin farincikinsu, jigon rayuwarsu. Sautin kuka Mairama ta fara ji daga yawancin matan da suke wurin ta rinka murmushi tana jiran taji wani cikinsu ya tabata taji dumin uwa. Kamar Innawuro ta sani ta durkusa a gabanta ta rungumeta suna sakin kuka a tare. Ardo Barkindo ya kalli Malamijo ya fito a tsolon rakensa yace "a bamu wuri mu zauna ko" Sai kuma ya farga ya dawo daga duniyar tunani "kai, kai ina kuke ne, ga baki a shimfada musu tabarmi daga jikin bangon can yafi inuwa." Tabarmin aka kawo suka zazzauna ya sake dubansu "wace mai girki ne a kawo musu abinci" Hajjo sarkin bakar magana ta tabe baki "Binta ce kuma yanzu ka dankara mata saki ko a kirawo ta ne?" Kunya tamkar wanda aka watsawa ruwan kankara haka Malamijo yaji ya muzanta a gaban mutanen da ya taba wulakantawa yau suka taru suka yi masa kwarjini. Allah Ya taimake shi Yadikko ta dawo yace "Uhmm, uhmmm....Yadikko fito da kwanuka aje gidan Tsahare ayi musu hadin wake da shinkafa amma da miya za'a siyo da salak. Idan akwai taliya 'yar gwamnati duka ta bada saboda ya ishesu. Sannan tasa nama a wadace do Allah" Yau wace rana Malamijo zaiyi abin kai. Ya zura hannu zai zaro kudi yaji hankalinsa ya tashi...mutanen nan fa da yawa, anya ba duka rugarsu Gide ya kwaso ba? Ardo ya dakatar dashi don bai manta bayanan da yaji game da Malamijo ba. "Kaga Malam Ali ba zama zamuyi ba a kan hanya muke. Ka zauna muyi magana" A tsorace ya zauna daga gefen Baffa Gide don kallon da yake masa kamar zai wafto shi ya shiga dukansa ne. Bangaren matan kuwa Mairama sai dai taji wannan ta rike mata hannu ko an shafa bayanta suna fadin sunayensu. Da addua ga marigayiya Mairo Ardo ya fara bude zaman nasu sannan ya ari bakin duka dangin nasu ya baiwa Mairama hakuri akan zumunci da suka yi sakaci dashi. Daga karshe ya gabatar da bukatarsu da cewa a yau dinnan ba gobe ba suke son daukarta da 'ya'yanta zasu koma da ita wurinsu. "Don Allah da gaske?" Mairama ta sami kanta da fada cike da farinciki. Bata sansu ba kuma bata san halayensu ba amma ko don samun nutsuwarta tana so ace gata da dangin mahaifiyarta. Matar Baffa Habubakari tace mata "Allah Yasa ki yarda ki bimu" Ita kuwa me zai hanata yarda idan ba rashin sanin ciwon kai ba. Ardo ya umarci yaran nasu maza da su je su shigo da kayan da suka zo dasu. Malamijo ya baza ido ya ga wane shirgin suka kawo sai kukan tumaki ya ratsa kunnensa. Raguna hudu ne da katoto kuma kosasshen sa guda daya. Kwanduna manya manya guda biyu cike da kwan zabi, buhun shinkafa daya 'yar gwamnati mai doki sai 'yar hausa daya da kuma buhun gero shima biyu. "Tun daga haihuwar Mairama har aurenta, haihuwar jikokinmu da rasuwar mijinta da muka sami labari babu wani abu daya da muka halarta balle mu bada gudunmawa a matsayin iyayenta. Mal Ali ga wannan kayan, ba wai sakayya bace sai dai ihsani ne daga garemu kuma muna godiya a madadin marigayiya Mairo na kula da marainiyar Allah da kayi" Baffa Gide ya ce sauran suna gyada kai. Innawuro ta riko hannun Emzee ya zauna a gefenta "ba rabaka zamuyi da ita ba. Mairama har abada 'yarka ce. Muna so ne dai ta bimu ta sanmu muma mu santa" Yake Malamijo yake ya rasa dalilin da yasa suka yi masa kwarjini "bama zan hanaku tafiya da ita ba" Kasa magana Malamijo yayi sai tarin kunya kamar ya tona rami ya binne kansa. Ba Mairama ba kadai kaf 'yayansa me zai bugi kirji yace yayi musu. Hajjo sai da ta magantu taji dadi ta fake da yi musu godiya "Allah Ya saka da alkhairi mungode. Ohh Malamijo baki sun zo gari -e- gari ko ruwa ba'a basu ba sai karbar kyauta daga hannunsu. Ke Radhiya tashi muje na tayaku hada kaya yau kakarku ta yanke saka" Cike da zumudi Radhiya ta mike tana kallon yadda Mairama take ta fara'a a tsakanin mutane. Idan ma kuruciya tasa bata gane mahimmancin zumunci ba a iya hankalinta ta sani cewa Umminta tana cikin farinciki. Wannan kuma ya isheta komai. Yadikko bata hakura ba sai da ta dafa musu dafadukan shinkafa da wake. Babu bama dai bare kifi amma tayi nata kokarin. Abin kunya ne ace wannan bakin sun zo sun tafi basu ci komai ba ga nisan hanya. Tasan tsiyar da suka tarar a gidan ita ta kara tunzura komawarsu a ranar. Batare da bata lokaci ba suka fito an gama shiri. Wani dan akwati da take ajiyar mahimman abubuwa kamar khakin Zayyan, wasikarsa da kuma hotuna tace Radhiya ta tabbata ta dauko. Dariya tayi don ta gama haddace komai na ciki. Hotunan yawanci na bikin iyayenta ne da na sunanta. Karfe biyar da kwata sun gama shiga mota. Baffa Gide yana tsaye a gefen mota kusa da Malamijo suka sake yin musabaha "yanzu da muka dena yawo idan kana nemanmu mun koma Giade can asalin garinmu amma rugarmu tana daga ciki da dan tafiya daga garin. Wannan da kake gani mijin Innawuro shine Ardo na biyu bayan kafuwar rugar" Sallama Mairama tayi da kowa daga ita har su Radhiya ko digon hawaye irin na kewa dinnan. Rabuwa da Yadikko da Hajjo da kuma sauran 'yan uwa ya dan sa sunji wani iri to amma fa ko kadan bikin Magaji bazai hana na Magajiya ba. ********** WAIWAYE.... [02/11 7:29 AM] My 2nd Mtn: 17. "Ahayye nanaye, wallahi mutum ya yi min ba kyalewa zanyi ba don kaji in gaya maka yaro" tafa hannuwa tayi sannan ta rike kugu tana girgiza jiki a dole ranta ne a bace. Abokin fadan nata wani sangamemen yaro ne don shima akwai kuruciya sai girman jiki. "An fada din" yace sannan ya cigaba da wakar da ta hadasu fada "Malamijo Malamijo tsolon rake. Ga kwadayi ga rowa yaki yin gaba" Wani kukan kura Radhiya tayi ta dire a gabansa ta nuna kasa "in ba tsoro ba dangwali" ta nuna masa kasar wurin. Dabi'arsu kenan 'yan makarantar wadda ta kasance firamare ta gwamnati idan ka yarda zaku dambace to kowa ya dangwali kasa. Daga nan sai a kaure karfinka ya kwace ka. Dukawa yayi zai dangwala ga tsirarun abokansu da basu bar makarantar da wuri ba sun tsaya kallo. Sai da ta daidaici yayi kasa da fuskar nan kawai ta dauke shi da mari ta ranta a na kare. Kai tsaye staffroom ta wuce inda malamai suke wurin Umminta. Tana shiga ta cukwikuye jikin Mairama tana kuka wai su Danmama ne suka dake ta. Tahowa suka yi Danmama ne a gaba kayansa duk kura saboda faduwar da yayi garin bin Radhiya. Kofar staffroom din taje ta saka su kneeldown har Radhiya sannan ta nemi jin ba'asi. Sai aka rasa me fada mata. Duk fitsarar Danmama yasan da kunya dai ya maimaita wakar a gabanta. Radhiya dama ko me zata yi mata bazata fada ba don kada ranta ya baci. Daga bayanta taji wani malami yace "Anti barni dasu kiyi tafiyarki gida. Idan na gama zanesu zan taho da wannan mai kunnen kashin" Mairama ta gyara zaman farin gilashinta tayi dan murmushinta da ta saba yanzu da wuya kake ganin bacin ranta ta koma ta dauko 'yan tarkacenta tayi hanyar fita daga makarantar don dama an riga an tashi. Daga karkashin wata katuwar bishiyar marke take hango yara suna 'yan wasanninsu. Idanunta suka sauka akan Emzee yana zaune yayi shiru yadda ya saba yana jiranta. "Karami zo mu tafi" tace da dan karfi don ta kula bai ganta ba sai gashi ya taso da saurinsa. Kayan hannunta zai karba tace ya barsu su tafi "Ummi ina Adda?" "Kyale wannan yau ma fada tayi" Sunyi gaba wasu 'yan ajinsu suka rinka kwalo masa kira suna Emzee sai an dawo hutu. Wannan suna da Mairama ta hakura da yakar sa dole shine sunan da yabi Muhammad Zayyan har gida. Mutane kalilan ke kiransa Zayyan ko Karami kamar yadda take fada. Yace wani malami da suka yi a firamare two ne yake kiransa MZ Tureta. Shikenan abu na yara ya koma Emzee. A makaranta kuma gurfane gaban Uncle Idris su Radhiya ne da Danmama. Sai da Mairama ta tafi Radhiya ta fada masa sunan da suke kiran kakanta dashi. Uncle Idris ya tabbatar zasu aikata yayi musu bulala biyar biyar mai zafi da dorinarsa ita kuma biyu ladan biye musu. A waje ta jira shi shima ya dauko kayansa tunda yau take ranar hutu suka tafi yana mata nasihar fada da maza. A cikin shekarun da suka gabata rayuwar Mairama sai dai godiyar Allah. Zamanta a gidan Malamijo tamkar zaman gidan haya ne. Iyakar gaskiyarsa shi nauyi ya masa yawa fitar da kudi kamar ana mintsininsa ne. Ya kara kudin cefane da kyar da sudin goshi amma daga nan fa ko me mutum ke bukata mace ko namiji cikin iyalinsa sai dai su nemawa kansu. Abu na farko da Mairama ta fara yi shine adana kudaden gadonsu a ranta tana tanadinsu ne domin karatun yaran a gaba. Sai da ta fuskanci sabulun wanka wannan idan bazata saya ba sai dai su watsa ruwa kawai ta fara taba kudin. A hankali kudi suka fara samun gibi dole ta fara neman sana'a. Tashin farko ta saro zobo tunda ta tsira da firig dinta ta soma yin zobo da lamurje na saidawa. TV da bidiyo da duka kayan gadonta banda katifar da ta ajiye kusu suke kwana da yaran duka suma saidawa tayi don ta kara jari. Allah Ya dubi halin da suke ciki ya buda mata kasuwa tana ciniki sosai. Salame tana gefe kullum tana yawo tsakanin nan gidan nasu da wurin Ta Madina wadda da fari ta dauki fushi mai tsanani da ita sakamakon mutuwar aurenta. Har gida suka tura aka nemo Salisu ko zai maidata yace idan ta sami miji tayi aure shima auren zaiyi. Zaman gaba, bakinciki da hassada ta dauka tana yi da Mairama. Kayan dakinta Ta Madina ta sayar ne ana bin malamai domin karkato hankalin Salisu. Shiya janyo ita bata da komai gashi jiki ya saba da jindadi an manta wanki, shara da wanke-wanke. Wahalar gidansu a yanzu har tafi ta da tsanani ko don zawarci suke oho. Hankalin Mairama yana kan inganta rayuwar 'ya'yanta, na Salame yana kan me zata yi ta kere Mairama ko ta hanata cigaba. 'Ya'yanta musamman Radhiya sun tsole mata ido. Abu kadan ne zata yi ta kai mata hannu da duka amma Mairama bata taba tankawa ba. Lokuta da dama wurin Yadikko suke zama ko Hajjo idan 'yan mutumcin suna kusa. Wata rana ta gama zobonta da lamurje ta kukkulle a leda santana suna cikin wani katon baho a nan bakin famfon tsakar gidan inda take aikinta ta tashi ta tafi jawo ruwa a rijiya zata wanke wurin. Salame tana ta fakonta don dama ta gane yanayin aikin nata. Idan ta gama kullewa sai ta janyo ruwa ta wanke wurin sannan ta dauka ta kai firig dinta ta jera. Su kan wuni da wuta amma da wuya ta kwana. Tafasasshen ruwan zafi Salame ta taho dashi a bokiti tayi daurin kirji kamar mai niyar shiga wanka sai da tazo daidai bakin bahon da kayan Mairama suke ta sheka musu ruwan nan. Ledojin dole suka yi laushi sunyi tsamo tsamo babu dadin tabawa. Salati ta soma yi wai wucewa zata yi ta sirka ruwan wankanta don ta ga kamar famfon wurin yana diga an kawo ruwa. Mairama ci gaba tayi da diban ruwanta sai da ta ciko bokiti tana zuwa ta ajiye shi sannan ta cira hannu ta kwashe Salame da mari mai gigitarwa don tana kallon yadda komai ya faru. Ihu ta kurma gidan da suke neman abin gani kuwa aka fara fitowa bawa ido abinci. "Ni kika mara Mairama?" Rai a bace Mairama tace "ko zaki rama ne?" "Kan bala'i, billahillazi baki mari banza ba sai na rama" "Gaki ga kumatun Adda Salame. Na gaji da wannan abubuwan da kika tsira tun kafin muyi aure har yanzu ana abu daya. Kece dukan min yara, yada min habaici da bakaken maganganu duk akan me? Me na tsare miki?" "Dole kice haka mana tunda kin rabani da wanda nake so" Yadikko na jin haka ta kora yaran gabadaya tace su shiga dakinta. Hajjo ba kunya ta bisu don jin ba'asi. Salame kasa karasa bayanin tayi don tasan ita ce da jin kunya. Tabarmar kunya ta nade da hauka wai Mairama tana yi mata gani gani saboda ta fara rike kudi. Da daddare da Malamijo ya dawo Yadikko ta bashi shawarar ya raba musu daki mana. "Babu wadda ta bani ko asi domin ginin gidan saboda haka idan zasu cinye kawunansu ne ma su cinye bai dameni ba. Wadda taji haushi ta kawo miji tayi aure" "Idan bazaka rabasu ba ka taimaka ka zame musu uba na kwarai ka kawo karshen wannan rashin jituwa da yake tsakaninsu. Kafi kowa sanin cewa da ba haka suke ba" Shu'umar dariya yayi kafin ya turo hularsa gaba ya bata amsa "ki kan bani mamaki wani lokacin kamar baki san zafin zawarci ba. Kodayake baki taba danawa bane amma cuta ce mai zaman kanta. Shiyasa kika ga suna harin junansu. Babu mai tayar min hankali ni dai" Babu yadda ta iya haka ta tashi ta bar dakin nasa tana kara godewa Allah da bai bata haihuwa da Malamijo ba. Mairama ta gama yiwa Karami shirin bacci ta goya shi tana jiran kanwarta ta kawo Radhiya da take wasa a wurinsu Salame ta shigo ta dawo daga zance da dan gayun saurayinta. Matashi ne ko auren fari baiyi ba. Baje ledar da ya bata ta tsire tayi a gefen katifarta da burin cusawa Mairama haushi. Abin dariya yadda take ci tana shuu da baki. Tana ganin Radhiya ta sake bude ledar da kyau. Yarinya tace "Ummi nama" Mairama ta dauko wata leda babba ta mikawa Na'ima kanwarta tace suje su raba sannan ta dauko wata 'yar madaidaiciya ta bude ta janyo hannun Radhiya ta bata cinyar gasasshiyar kaza. Sai yanzu take gode Allah da haka nan ta bawa Bature kudi ya siyo kajin nan guda uku. Ta dauki daya ta basu biyu su raba. Ai kuwa Salame ta shaka har wuya ta shiga fadin maganganu wai gara su suna kwance ake basu. Wahalallu kuwa sai sunyi da karfin jikinsu kafin su dandani zakin nama. Shiru ma magana ce. Mairama bata ce mata komai ba haushi ya kamata tsiren ya fice mata a rai. "Dazu nace kin rabani da masoyina baki tambayi ko waye ba bare ki bani hakuri" "Indai Salisu ne nayi imanin bazai sakeki saboda ni ba. Allah kadai Yasan dalilin mutuwar aurenki sai kuma ku kanku" Kallon cikin ido ta yiwa kanwar tata "Mairama, na rigaki ganin Zayyan kuma na rigaki fara...." A harzuke Mairama ta tashi duk wani kulli na kanta yana kwancewa. Yanzun ta gama gano duk abubuwan da Salame tayi mata sunfi kama da kishi. Duk da mijin nata baya raye amma tana tsananin kishinsa itama. "Ya isheni ba sai kin karasa ba, na fahimci da aurenki kike son nawa mijin. Idan abinda Salisu ya gano ya sakeki kenan sai ince Allah Ya dada karawa." Daga haka bata koma cewa komai ba sai da ta tabbatar Salame tayi bacci ta sha kuka ta godewa Allah. Ta tabbatar Zayyan ya sani shiyasa shima baya son Salame saboda kada yaci amanarta. Sabuwar kewarsa ke ratsa duk wani sassa na jikinta tana inama yana nan tare da ita. *********** Shekararsu biyu a gida Salame tayi aure. Kafin auren Mairama ta tuna cewa Salisu abokin Hadir ne a lokacin ta kwantar da kai wurin sau uku tana tambayar Salame kwatancen gidansu Salisu. Ita kuma ganin ta matsu tasan ko meye yana da mahimmanci shiyasa taki fada. Gashi baya zuwa garin don idan za'a kawo mata Halifa aiko drebansa yake likkafa ta kara ci gaba. Bayan auren Salame ne Idris dan gidan Mal Kallamu abokin Malamijo ya sami aikin koyarwa a makarantar firamare ta gwamnati ta cikin Sumaila. Da yake suna shiri da Mairama kamar wasa ya gabatarwa Headmaster da ita akan ko 'yan aji daya ne ta samu ta rinka koyarwa. Shine ya amince aka yi mata cuku cuku sai gashi ta sami aikin a karkashin L.E.A. Kwalin karatun nata iyakarsa sakandire shiyasa bata wuce aji daya ba a koyarwar. Ita dai ko yaya ne hakan yayi mata don albashinta yana mata rana ga cinikin zobo da lamurje. Haihuwar Salame daya aurenta ya sake mutuwa. Wannan karon lalaci da rainawa miji ya janyo mijin ya saketa. Duk abinda zai kawo mata sai ta karba a wulakance tace ba haka baban Halifa yake yi ba. Sai da ta kaishi makurar da yayi mata duka ya sakota. To yanzu ma an sake dawowa gidan jiya. Dan da ta sake haifa shima babansa ya kaiwa yarsa. Ta dawo gida an sake komawa zaman zawarci ga rashin abinyi. Bakincikinta ya karu da yadda Mairama da yaranta suke rayuwa ta rufin asiri. Duka suna karatu a inda take koyarwa. Ta soma saka gilashi ne a lokacin da ta fara fama da matsanancin kaikayin ido da gani dishi-dishi. Ta sha wahalar idon sosai ta kuma kashe kudi. ********** Sun dawo gida da Emzee ya shiga dakunan duka matan gidan su hudu don tuni Malamijo ya sake cike gurbi. Yadikko tana nan a matsayin uwargida Hajjo kuma ta biyu sai amare Hanne da Binta. A gajiye take ta kwanta tana murna anyi hutu. Sallama taji anayi ana kwala mata kira ta tashi a zabure Salame tana kwalliya zata je wurin mamanta. "Uwar yarinyar nan Alhihi take ko me kace Danmama?" Danmama ya zumburo baki "Alheran amma Radhiya naji ana cewa. Ita ce ta mareni kuma Anti batayi komai ba saboda 'yarta ce" "Allah gamu gareka" Mairama tace a ranta kafin ta fita tsakar gidan zuwa wurin matar. "Hajiya kiyi hakuri rigima ce irin ta yara kuma tun a wurin an hukunta su" Rai a bace tana nuna bayan Danmama ta ce "a hukuncin ne aka yi masa bulala biyar ita kuma biyu saboda son kai. Dama wane adalci kuke yi idan kuna koyarwa a makarantun da 'ya'yanku suke. Daga yau sai yau ki jawa 'yarki kunne. Idan ta sake taba min yaro bazan yarda ba" Hakuri Mairama ta bata duk kunya ta isheta. Radhiya ba dai dauko magana ba. Idan anyi magana tace ita 'yar soja ce. Yadda take alfahari da aikin babanta sai ka rantse ta tashi tare dashi. Ko ina ta tsaya ma yanzu bata sani ba. Bari dai ta dawo yau mai rabasu sai Allah. Ashe gidan Mal Kallamu ta bi Uncle Idris. Can taci abincinta a bangaren amaryar Idris din sannan ta fito suka hadu da Malamijo a kofar shiga. Harararta yayi kamar ya kwadeta jiya taje gonarsa ta sami wani sabon maikaci da yayi ta nuna masa wata tinkiya wai Malamijo ne ya aiko ta fada masa a yanka ya dau kai da kafa. Ana cikin fida yazo ya gani jikinsa na tsuma yayo kanta tace gani tayi ta kasa. Kunnenta ya damko tana ihu " 'Yar kundun uba ta ina kika ga ta kasa din?" Ba yadda ya iya a dole jiya gidansa aka ci dafge kowa ya warwasa. Dakinsa ta bishi yana gwawiyar kashi tace "Malamijo ashe kaima kana son naman dai. Allah Yasa in ga wata ta kuma kasawa" da mafici ya biyota har yana tuntube. Ita ce a gaba ta hango Umminta da Danmama da mamansa. A guje tayi niyar komawa Malamijo ya riko wuyan rigarta ya kaita gabansu. "Mairama ki jawa 'yarki kunne idan ba haka ba wannan karon idan kunje hutun Sakkwato ki barta a can. Yarinya ce kamar aljana. Dubi kaninki nasa salihancin har haushi yake bani. Ke kadai kina mace kin tattaro duk halayen kiriniyar kin dorawa kanki" Kallon da ta ga Mairama na yi mata tasan yau jiki zai fada shiyasa tana tura baki da magana ciki-ciki tace "to ba shine yake wakar wai Malamijo tsolon rake ba, rama maka fa nayi" Jikin Malamijo da na uwar Danmama sai yayi sanyi. Danmama yayi wiki-wiki da idanu hakan ya tabbatar ba karya take ba. Babarsa kuwa ta talle masa keya tana cewa ya bashi hakuri. Yara kuwa sai dariya suke a hankali Malamijo yaji kunya ya shige daki. Kunnen Radhiya Mairama ta kama tace ta wuce daki. Da yamma ranar sai ga Alh Ado Indararo da kansa yazo bayan matarsa ta fada masa abinda Danmama yayi. Sun saba ciniki da Malamijo baya son kasuwar ta watse don yana dukan hancin Malamijo akan dabbobinsa sosai batare da shi ya sani ba. Ya bashi hakuri ya nemi Mairama itama ta fito da babban mayafi ta gaishe shi. Kallon farko Alh Indararo ya fada kogin kauna baya ji baya gani. Tana komawa ciki baiyi kasa a gwiwa ba ya fadawa Malamijo bukatarsa. Zani ce ta tadda muje mu. Shima kwadayin kudin Alhajin yake yace ya bar masa wuka da nama. A daren ya sanar da ita tayi tsalle ta dire tace bata da sauran aure a duniya. Sun fara rigimarsu bayan kwana biyu ta tattara ta tafi Sakkwato kamar yadda ta saba duk hutu suna zuwa suyi sati daya ko kwana goma. Duk gidajen 'yan uwan Zayyan na jini da makusanta irin su Mal Aminu sai taje. Kuma bata fasa zuwa barikinsu ba ko zata sami labarin Zainab da Mami. Gidan iyayen Zainab yanzu wasu ne a ciki. Ta matsu tasan halin da suke ciki amma babu dama. Haka kuma har yau babu wanda ya kirasu akan wani kudi na ihsani ga jaruman da suka rasu. Suna hira da matar Maikudi da Jume Maikudin ya shigo yana hade rai. Shi yafi kowa sanin babban dalilinsa na kin zuwansu garin amma bazai iya fadawa kowa ba. Yaran dama baya sakar musu fuska. Sai dai suna da kyakkyawar mu'amala da 'yan uwansu wato jikokin gidan. Satinsu daya suka juya Jume kamar a bar mata su. Babbar damuwarta shine rashin kowa daga bangaren Innar Zayyan wanda Jume tace har yau itama tana zuba idanu ne. Maikudi bai sami sukuni ba sai da suka bar garin. Sirrika biyu yake boyewa Mairama saboda mugunta da kuma son kai irin na dan Adam. Na farko dai wata shida da rasuwar Zayyan kawunsa Sidi yazo bisa shawarar 'yan uwa. Ashe ya tura musu wasika da zai tafi ta tasha. Sidi yazo gari Jume da matan gidan sun tafi Tureta biki. Maikudi kawai ya samu su Badaru basa gida. Lokacin yana tsaka da jin haushin rashin mutumcin Malamijo kuma yasan idan mutanen nan suka san da zamansu ba karamin alheri zasu rinka musu ba. Wanda zai koma jikin Malamijo a karshe. Saboda haka ya matso hawaye ya sanar dashi mutuwar Zayyan da kuma hatsarin da su Mairama suka yi ita da 'yarta suka rasu gabadaya. Wannan shine dalilin da yasa aka dena ji daga garesu. Abu na biyu kuma shine aike duk karshen wata daga kasar Germany wanda Retired Major Mustapha bai taba dena yi ba tun bayan samun lafiyarsa da aiki a can din kusan shekaru hudu. Kudi ne yake turowa ta hanyar wani soja da yake karkashinsa a da kuma ya yarda dashi. Wannan mutumi duk wata Maikudi yasan ranar da yake zuwa har barikinsu ya karbi kudin da suke mazaunin kudin makarantar Radhiya da kuma tallafi ga Mairama. Soke abinsa yake ga gidan Kano ya saka 'yan haya. A takaice dai yana ta gina kansa don ya sayi fili a cikin Sakkwato yana ta makara gini da kudin marayu. ********** Mairama ta koma ta tarar da babbar kura. Malamijo ya karbi sadakinta daga hannun Alh Indararo an saka biki wata uku kafin ya gama yi mata gyaran gida. Ta shiga matsanancin tashin hankali har Nene Marka tazo amma kowa cewa yake tayi auren ko zata sami hutu itama. Tayi kukan, tayi haukan duk a banza bata da mai tsaya mata. A bangare daya kuma duniyar Salame ta juye. Mutum kamar Alh Indararo ace yana son mace kakarta ta yanke saka. Shine wannan karon ma irin abinda take muradi ya tafi ga Mairama. Rantsuwa tayi cewa hakan bazata sake sabuwa ba. Gidan Malaminta da suka saba kashewa kudi domin a dawo mata da Salisu taje. Bayan dogon bugun kasa yace ta saka ranta a inuwa akwai rabo yana iya gani tsakaninta da Alh Indararo amma sai an kawar da Mairama. "Malam rufa min asiri kanwata ce fa. Ni dai bazan iya kasheta ba" Gemunsa na munafurci da suke cutar jama'a dashi ya ja yana murmushi "waye yace sai kin kasheta. Idan kina so nakasa kawai zamu dora mata wadda zata saka ya fasa." Kwana biyu tana tunani kafin ta hasko me take son ayiwa Mairama. Magani ya bata ta wuce gida ta saka a inda ya umarceta. Kwana uku a tsakani kuwa wata safiyar lahadi Mairama ta tashi bata gani sai dususu komai yayi hazo. Cikin maganin digawarta na ido Salame ta zuba mata maganin. Cikin wata guda idanun Mairama sai suna. Duk abinda ya rage mata ya kare a neman maganin ciwon idon amma asibiti basa ganin komai. Kuka ashe bai kare mata ba. Bata gane kowa sai duhun inuwa. Tashi guda Radhiya ta koma idanunta madogararta. Alh Indararo ya canja sheka bazai iya auran musaka ba Salame har ta tare abinta. Karatun yaran ya tsaya yau da gobe Malamijo ya gaji da dan mikawar da yake yi. A bisa dole ta hakura da karatun Radhiya da Emzee. Tana kuka kan kuka amma mahaifinta bazai iya kulawa da ita ba bare 'ya'ya, iyakarsa dasu shine za'a dafa abincin gidan dasu. Radhiya ta fara hankali tasan cewa mahaifiyarta tana bukatarta shiyasa bata fita idan ba aike ba. Emzee kuwa dama daddawar daka ne shiyasa bata hadu da matsalar ace suna yawace-yawace ba. Rayuwar Mairama matar soja ta cika da wahalhalun da suka sa take bukatar a dube ta. *********** Maza ne uku a karkashin bishiyar darbejiya wadda ta yiwa wurin yalwatacciyar inuwa. Daya yana zaune akan kujera sauran biyun kuma suna gabansa ne kana gani kasan mai mulki ne da wadanda yake mulka. Gyaran murya na kan kujerar yayi suka dawo da hankula gareshi "Mal Gide" "Ranka ya dade" wanda yafi manyanta cikinsu ya amsa. "Habubakari" "Allah Yaja zamaninka" na biyun ya amsa. Dan murmushi yayi domin kuwa su biyun yayun matarsa ne Innawuro. "Mal Gide kaine babba saboda haka ta kanka zan fara. Ba tare da jan zance ba magana ce akan sakacinku da zumunci saboda wani abu can da ya faru shekarun baya" Mal Gide ya hadiyi yawu yana kallon Habubakari shima kuma yayan nasa yake kallo. Ardo Barkindo ya dan duku da kansa kadan daga kan kujerar "wannan zumuncin da kuka banzatar ina mai tabbatar muku sai Allah Ya tambayeku akansa. Kune kuka ci bashi kamar yadda naji a bisa dole. Dole tasa kuka biya bashin da kanwarku sai gashi daga karshe ya sakota ya bukaci kudinsa ko. 'Yar uwarku ta sadaukar da farincikinta saboda ku amma shekaru sun tasanmu talatin marainiyar da ta bari baku san cinta ba baku san shanta ba" Habubakar wanda abin shima ya dame shi amma tsoron Gide ya hana shi furtawa ya sharce kwalla "Ardo zamu gyara, wallahi nima abin ya dameni. Ali bashi da kirki ko kadan. Allah ma yasa tana da rai yarinyar nan" "Yarinya da ranta amma tana cikin mawuyacin hali. Yanzu da na kiraku dama sanar daku zanyi cewa zan daukota ko dan kwanciyar hankalin Innawuro" Nan ya sanar dasu komai game da Mairama kamar yadda yaji daga bakin mijin Nene Marka bayan ya soma binciken nemota. Mal Gide sai hawaye. Bakar zuciya tasa ya umarci 'yan uwansa da babu su babu zuri'ar Malamijo, ciki kuwa harda 'ya daya tilo ga kanwarsa Mairo wadda ya yiwa auren dole da Malamijo. "Da kaina zanje in daukota da yaran su zauna a gidana Zan gyara wannan abu duka laifina ne" Ardo Barkindo ya kada kai yana murmushi "haba dai Gide ai bazamu yi haka da kai ba. Yarinya a wurin babarta zata zauna. Duk na gama wahalar neman sannan kace zaka daukota ka kwashe ladan" Murmushi ya maida masa "duk yadda kace ranka ya dade, kamar yaushe zamu tafi?" "Jibi in sha Allahu. Ina so ku tattaro kan 'ya'yanku har na gidan aure da suke rugar nan da kewaye maza da mata. So nake muje mu cika musu ido mu wanke gorin dangin uwa da na tabbatar ansha yi mata." Sun tashi da fara'a kowa yana jin kamar an sauke masa nauyi daga zuciya. Ardo Barkindo ya nisa yana tunanin ya boye musu makantar Mairama saboda yasan duka hankulansu zasu tashi. Idan sun je zasu ganewa idanunsu. Ko matarsa ya kasa fadawa ita da ta uzzura masa akan neman 'yar yayarta da take bi. Mal Gide kuwa har ya isa gida yana tunanin da yardar Allah zasu kula da ita bakin iyawarsu su daidaita tsohuwar baraka. Tunawa yayi da umarnin Ardo ya tura guda cikin 'ya'yansa da yaje ya fara sanar da yayyensa cewa suna da zuwa Kano jibi daga rugarsu wadda take cikin karamar hukumar Giade a jihar Bauchin Yakubu."Ahayye nanaye, wallahi mutum ya yi min ba kyalewa zanyi ba don kaji in gaya maka yaro" tafa hannuwa tayi sannan ta rike kugu tana girgiza jiki a dole ranta ne a bace. Abokin fadan nata wani sangamemen yaro ne don shima akwai kuruciya sai girman jiki. "An fada din" yace sannan ya cigaba da wakar da ta hadasu fada "Malamijo Malamijo tsolon rake. Ga kwadayi ga rowa yaki yin gaba" Wani kukan kura Radhiya tayi ta dire a gabansa ta nuna kasa "in ba tsoro ba dangwali" ta nuna masa kasar wurin. Dabi'arsu kenan 'yan makarantar wadda ta kasance firamare ta gwamnati idan ka yarda zaku dambace to kowa ya dangwali kasa. Daga nan sai a kaure karfinka ya kwace ka. Dukawa yayi zai dangwala ga tsirarun abokansu da basu bar makarantar da wuri ba sun tsaya kallo. Sai da ta daidaici yayi kasa da fuskar nan kawai ta dauke shi da mari ta ranta a na kare. Kai tsaye staffroom ta wuce inda malamai suke wurin Umminta. Tana shiga ta cukwikuye jikin Mairama tana kuka wai su Danmama ne suka dake ta. Tahowa suka yi Danmama ne a gaba kayansa duk kura saboda faduwar da yayi garin bin Radhiya. Kofar staffroom din taje ta saka su kneeldown har Radhiya sannan ta nemi jin ba'asi. Sai aka rasa me fada mata. Duk fitsarar Danmama yasan da kunya dai ya maimaita wakar a gabanta. Radhiya dama ko me zata yi mata bazata fada ba don kada ranta ya baci. Daga bayanta taji wani malami yace "Anti barni dasu kiyi tafiyarki gida. Idan na gama zanesu zan taho da wannan mai kunnen kashin" Mairama ta gyara zaman farin gilashinta tayi dan murmushinta da ta saba yanzu da wuya kake ganin bacin ranta ta koma ta dauko 'yan tarkacenta tayi hanyar fita daga makarantar don dama an riga an tashi. Daga karkashin wata katuwar bishiyar marke take hango yara suna 'yan wasanninsu. Idanunta suka sauka akan Emzee yana zaune yayi shiru yadda ya saba yana jiranta. "Karami zo mu tafi" tace da dan karfi don ta kula bai ganta ba sai gashi ya taso da saurinsa. Kayan hannunta zai karba tace ya barsu su tafi "Ummi ina Adda?" "Kyale wannan yau ma fada tayi" Sunyi gaba wasu 'yan ajinsu suka rinka kwalo masa kira suna Emzee sai an dawo hutu. Wannan suna da Mairama ta hakura da yakar sa dole shine sunan da yabi Muhammad Zayyan har gida. Mutane kalilan ke kiransa Zayyan ko Karami kamar yadda take fada. Yace wani malami da suka yi a firamare two ne yake kiransa MZ Tureta. Shikenan abu na yara ya koma Emzee. A makaranta kuma gurfane gaban Uncle Idris su Radhiya ne da Danmama. Sai da Mairama ta tafi Radhiya ta fada masa sunan da suke kiran kakanta dashi. Uncle Idris ya tabbatar zasu aikata yayi musu bulala biyar biyar mai zafi da dorinarsa ita kuma biyu ladan biye musu. A waje ta jira shi shima ya dauko kayansa tunda yau take ranar hutu suka tafi yana mata nasihar fada da maza. A cikin shekarun da suka gabata rayuwar Mairama sai dai godiyar Allah. Zamanta a gidan Malamijo tamkar zaman gidan haya ne. Iyakar gaskiyarsa shi nauyi ya masa yawa fitar da kudi kamar ana mintsininsa ne. Ya kara kudin cefane da kyar da sudin goshi amma daga nan fa ko me mutum ke bukata mace ko namiji cikin iyalinsa sai dai su nemawa kansu. Abu na farko da Mairama ta fara yi shine adana kudaden gadonsu a ranta tana tanadinsu ne domin karatun yaran a gaba. Sai da ta fuskanci sabulun wanka wannan idan bazata saya ba sai dai su watsa ruwa kawai ta fara taba kudin. A hankali kudi suka fara samun gibi dole ta fara neman sana'a. Tashin farko ta saro zobo tunda ta tsira da firig dinta ta soma yin zobo da lamurje na saidawa. TV da bidiyo da duka kayan gadonta banda katifar da ta ajiye kusu suke kwana da yaran duka suma saidawa tayi don ta kara jari. Allah Ya dubi halin da suke ciki ya buda mata kasuwa tana ciniki sosai. Salame tana gefe kullum tana yawo tsakanin nan gidan nasu da wurin Ta Madina wadda da fari ta dauki fushi mai tsanani da ita sakamakon mutuwar aurenta. Har gida suka tura aka nemo Salisu ko zai maidata yace idan ta sami miji tayi aure shima auren zaiyi. Zaman gaba, bakinciki da hassada ta dauka tana yi da Mairama. Kayan dakinta Ta Madina ta sayar ne ana bin malamai domin karkato hankalin Salisu. Shiya janyo ita bata da komai gashi jiki ya saba da jindadi an manta wanki, shara da wanke-wanke. Wahalar gidansu a yanzu har tafi ta da tsanani ko don zawarci suke oho. Hankalin Mairama yana kan inganta rayuwar 'ya'yanta, na Salame yana kan me zata yi ta kere Mairama ko ta hanata cigaba. 'Ya'yanta musamman Radhiya sun tsole mata ido. Abu kadan ne zata yi ta kai mata hannu da duka amma Mairama bata taba tankawa ba. Lokuta da dama wurin Yadikko suke zama ko Hajjo idan 'yan mutumcin suna kusa. Wata rana ta gama zobonta da lamurje ta kukkulle a leda santana suna cikin wani katon baho a nan bakin famfon tsakar gidan inda take aikinta ta tashi ta tafi jawo ruwa a rijiya zata wanke wurin. Salame tana ta fakonta don dama ta gane yanayin aikin nata. Idan ta gama kullewa sai ta janyo ruwa ta wanke wurin sannan ta dauka ta kai firig dinta ta jera. Su kan wuni da wuta amma da wuya ta kwana. Tafasasshen ruwan zafi Salame ta taho dashi a bokiti tayi daurin kirji kamar mai niyar shiga wanka sai da tazo daidai bakin bahon da kayan Mairama suke ta sheka musu ruwan nan. Ledojin dole suka yi laushi sunyi tsamo tsamo babu dadin tabawa. Salati ta soma yi wai wucewa zata yi ta sirka ruwan wankanta don ta ga kamar famfon wurin yana diga an kawo ruwa. Mairama ci gaba tayi da diban ruwanta sai da ta ciko bokiti tana zuwa ta ajiye shi sannan ta cira hannu ta kwashe Salame da mari mai gigitarwa don tana kallon yadda komai ya faru. Ihu ta kurma gidan da suke neman abin gani kuwa aka fara fitowa bawa ido abinci. "Ni kika mara Mairama?" Rai a bace Mairama tace "ko zaki rama ne?" "Kan bala'i, billahillazi baki mari banza ba sai na rama" "Gaki ga kumatun Adda Salame. Na gaji da wannan abubuwan da kika tsira tun kafin muyi aure har yanzu ana abu daya. Kece dukan min yara, yada min habaici da bakaken maganganu duk akan me? Me na tsare miki?" "Dole kice haka mana tunda kin rabani da wanda nake so" Yadikko na jin haka ta kora yaran gabadaya tace su shiga dakinta. Hajjo ba kunya ta bisu don jin ba'asi. Salame kasa karasa bayanin tayi don tasan ita ce da jin kunya. Tabarmar kunya ta nade da hauka wai Mairama tana yi mata gani gani saboda ta fara rike kudi. Da daddare da Malamijo ya dawo Yadikko ta bashi shawarar ya raba musu daki mana. "Babu wadda ta bani ko asi domin ginin gidan saboda haka idan zasu cinye kawunansu ne ma su cinye bai dameni ba. Wadda taji haushi ta kawo miji tayi aure" "Idan bazaka rabasu ba ka taimaka ka zame musu uba na kwarai ka kawo karshen wannan rashin jituwa da yake tsakaninsu. Kafi kowa sanin cewa da ba haka suke ba" Shu'umar dariya yayi kafin ya turo hularsa gaba ya bata amsa "ki kan bani mamaki wani lokacin kamar baki san zafin zawarci ba. Kodayake baki taba danawa bane amma cuta ce mai zaman kanta. Shiyasa kika ga suna harin junansu. Babu mai tayar min hankali ni dai" Babu yadda ta iya haka ta tashi ta bar dakin nasa tana kara godewa Allah da bai bata haihuwa da Malamijo ba. Mairama ta gama yiwa Karami shirin bacci ta goya shi tana jiran kanwarta ta kawo Radhiya da take wasa a wurinsu Salame ta shigo ta dawo daga zance da dan gayun saurayinta. Matashi ne ko auren fari baiyi ba. Baje ledar da ya bata ta tsire tayi a gefen katifarta da burin cusawa Mairama haushi. Abin dariya yadda take ci tana shuu da baki. Tana ganin Radhiya ta sake bude ledar da kyau. Yarinya tace "Ummi nama" Mairama ta dauko wata leda babba ta mikawa Na'ima kanwarta tace suje su raba sannan ta dauko wata 'yar madaidaiciya ta bude ta janyo hannun Radhiya ta bata cinyar gasasshiyar kaza. Sai yanzu take gode Allah da haka nan ta bawa Bature kudi ya siyo kajin nan guda uku. Ta dauki daya ta basu biyu su raba. Ai kuwa Salame ta shaka har wuya ta shiga fadin maganganu wai gara su suna kwance ake basu. Wahalallu kuwa sai sunyi da karfin jikinsu kafin su dandani zakin nama. Shiru ma magana ce. Mairama bata ce mata komai ba haushi ya kamata tsiren ya fice mata a rai. "Dazu nace kin rabani da masoyina baki tambayi ko waye ba bare ki bani hakuri" "Indai Salisu ne nayi imanin bazai sakeki saboda ni ba. Allah kadai Yasan dalilin mutuwar aurenki sai kuma ku kanku" Kallon cikin ido ta yiwa kanwar tata "Mairama, na rigaki ganin Zayyan kuma na rigaki fara...." A harzuke Mairama ta tashi duk wani kulli na kanta yana kwancewa. Yanzun ta gama gano duk abubuwan da Salame tayi mata sunfi kama da kishi. Duk da mijin nata baya raye amma tana tsananin kishinsa itama. "Ya isheni ba sai kin karasa ba, na fahimci da aurenki kike son nawa mijin. Idan abinda Salisu ya gano ya sakeki kenan sai ince Allah Ya dada karawa." Daga haka bata koma cewa komai ba sai da ta tabbatar Salame tayi bacci ta sha kuka ta godewa Allah. Ta tabbatar Zayyan ya sani shiyasa shima baya son Salame saboda kada yaci amanarta. Sabuwar kewarsa ke ratsa duk wani sassa na jikinta tana inama yana nan tare da ita. *********** Shekararsu biyu a gida Salame tayi aure. Kafin auren Mairama ta tuna cewa Salisu abokin Hadir ne a lokacin ta kwantar da kai wurin sau uku tana tambayar Salame kwatancen gidansu Salisu. Ita kuma ganin ta matsu tasan ko meye yana da mahimmanci shiyasa taki fada. Gashi baya zuwa garin don idan za'a kawo mata Halifa aiko drebansa yake likkafa ta kara ci gaba. Bayan auren Salame ne Idris dan gidan Mal Kallamu abokin Malamijo ya sami aikin koyarwa a makarantar firamare ta gwamnati ta cikin Sumaila. Da yake suna shiri da Mairama kamar wasa ya gabatarwa Headmaster da ita akan ko 'yan aji daya ne ta samu ta rinka koyarwa. Shine ya amince aka yi mata cuku cuku sai gashi ta sami aikin a karkashin L.E.A. Kwalin karatun nata iyakarsa sakandire shiyasa bata wuce aji daya ba a koyarwar. Ita dai ko yaya ne hakan yayi mata don albashinta yana mata rana ga cinikin zobo da lamurje. Haihuwar Salame daya aurenta ya sake mutuwa. Wannan karon lalaci da rainawa miji ya janyo mijin ya saketa. Duk abinda zai kawo mata sai ta karba a wulakance tace ba haka baban Halifa yake yi ba. Sai da ta kaishi makurar da yayi mata duka ya sakota. To yanzu ma an sake dawowa gidan jiya. Dan da ta sake haifa shima babansa ya kaiwa yarsa. Ta dawo gida an sake komawa zaman zawarci ga rashin abinyi. Bakincikinta ya karu da yadda Mairama da yaranta suke rayuwa ta rufin asiri. Duka suna karatu a inda take koyarwa. Ta soma saka gilashi ne a lokacin da ta fara fama da matsanancin kaikayin ido da gani dishi-dishi. Ta sha wahalar idon sosai ta kuma kashe kudi. ********** Sun dawo gida da Emzee ya shiga dakunan duka matan gidan su hudu don tuni Malamijo ya sake cike gurbi. Yadikko tana nan a matsayin uwargida Hajjo kuma ta biyu sai amare Hanne da Binta. A gajiye take ta kwanta tana murna anyi hutu. Sallama taji anayi ana kwala mata kira ta tashi a zabure Salame tana kwalliya zata je wurin mamanta. "Uwar yarinyar nan Alhihi take ko me kace Danmama?" Danmama ya zumburo baki "Alheran amma Radhiya naji ana cewa. Ita ce ta mareni kuma Anti batayi komai ba saboda 'yarta ce" "Allah gamu gareka" Mairama tace a ranta kafin ta fita tsakar gidan zuwa wurin matar. "Hajiya kiyi hakuri rigima ce irin ta yara kuma tun a wurin an hukunta su" Rai a bace tana nuna bayan Danmama ta ce "a hukuncin ne aka yi masa bulala biyar ita kuma biyu saboda son kai. Dama wane adalci kuke yi idan kuna koyarwa a makarantun da 'ya'yanku suke. Daga yau sai yau ki jawa 'yarki kunne. Idan ta sake taba min yaro bazan yarda ba" Hakuri Mairama ta bata duk kunya ta isheta. Radhiya ba dai dauko magana ba. Idan anyi magana tace ita 'yar soja ce. Yadda take alfahari da aikin babanta sai ka rantse ta tashi tare dashi. Ko ina ta tsaya ma yanzu bata sani ba. Bari dai ta dawo yau mai rabasu sai Allah. Ashe gidan Mal Kallamu ta bi Uncle Idris. Can taci abincinta a bangaren amaryar Idris din sannan ta fito suka hadu da Malamijo a kofar shiga. Harararta yayi kamar ya kwadeta jiya taje gonarsa ta sami wani sabon maikaci da yayi ta nuna masa wata tinkiya wai Malamijo ne ya aiko ta fada masa a yanka ya dau kai da kafa. Ana cikin fida yazo ya gani jikinsa na tsuma yayo kanta tace gani tayi ta kasa. Kunnenta ya damko tana ihu " 'Yar kundun uba ta ina kika ga ta kasa din?" Ba yadda ya iya a dole jiya gidansa aka ci dafge kowa ya warwasa. Dakinsa ta bishi yana gwawiyar kashi tace "Malamijo ashe kaima kana son naman dai. Allah Yasa in ga wata ta kuma kasawa" da mafici ya biyota har yana tuntube. Ita ce a gaba ta hango Umminta da Danmama da mamansa. A guje tayi niyar komawa Malamijo ya riko wuyan rigarta ya kaita gabansu. "Mairama ki jawa 'yarki kunne idan ba haka ba wannan karon idan kunje hutun Sakkwato ki barta a can. Yarinya ce kamar aljana. Dubi kaninki nasa salihancin har haushi yake bani. Ke kadai kina mace kin tattaro duk halayen kiriniyar kin dorawa kanki" Kallon da ta ga Mairama na yi mata tasan yau jiki zai fada shiyasa tana tura baki da magana ciki-ciki tace "to ba shine yake wakar wai Malamijo tsolon rake ba, rama maka fa nayi" Jikin Malamijo da na uwar Danmama sai yayi sanyi. Danmama yayi wiki-wiki da idanu hakan ya tabbatar ba karya take ba. Babarsa kuwa ta talle masa keya tana cewa ya bashi hakuri. Yara kuwa sai dariya suke a hankali Malamijo yaji kunya ya shige daki. Kunnen Radhiya Mairama ta kama tace ta wuce daki. Da yamma ranar sai ga Alh Ado Indararo da kansa yazo bayan matarsa ta fada masa abinda Danmama yayi. Sun saba ciniki da Malamijo baya son kasuwar ta watse don yana dukan hancin Malamijo akan dabbobinsa sosai batare da shi ya sani ba. Ya bashi hakuri ya nemi Mairama itama ta fito da babban mayafi ta gaishe shi. Kallon farko Alh Indararo ya fada kogin kauna baya ji baya gani. Tana komawa ciki baiyi kasa a gwiwa ba ya fadawa Malamijo bukatarsa. Zani ce ta tadda muje mu. Shima kwadayin kudin Alhajin yake yace ya bar masa wuka da nama. A daren ya sanar da ita tayi tsalle ta dire tace bata da sauran aure a duniya. Sun fara rigimarsu bayan kwana biyu ta tattara ta tafi Sakkwato kamar yadda ta saba duk hutu suna zuwa suyi sati daya ko kwana goma. Duk gidajen 'yan uwan Zayyan na jini da makusanta irin su Mal Aminu sai taje. Kuma bata fasa zuwa barikinsu ba ko zata sami labarin Zainab da Mami. Gidan iyayen Zainab yanzu wasu ne a ciki. Ta matsu tasan halin da suke ciki amma babu dama. Haka kuma har yau babu wanda ya kirasu akan wani kudi na ihsani ga jaruman da suka rasu. Suna hira da matar Maikudi da Jume Maikudin ya shigo yana hade rai. Shi yafi kowa sanin babban dalilinsa na kin zuwansu garin amma bazai iya fadawa kowa ba. Yaran dama baya sakar musu fuska. Sai dai suna da kyakkyawar mu'amala da 'yan uwansu wato jikokin gidan. Satinsu daya suka juya Jume kamar a bar mata su. Babbar damuwarta shine rashin kowa daga bangaren Innar Zayyan wanda Jume tace har yau itama tana zuba idanu ne. Maikudi bai sami sukuni ba sai da suka bar garin. Sirrika biyu yake boyewa Mairama saboda mugunta da kuma son kai irin na dan Adam. Na farko dai wata shida da rasuwar Zayyan kawunsa Sidi yazo bisa shawarar 'yan uwa. Ashe ya tura musu wasika da zai tafi ta tasha. Sidi yazo gari Jume da matan gidan sun tafi Tureta biki. Maikudi kawai ya samu su Badaru basa gida. Lokacin yana tsaka da jin haushin rashin mutumcin Malamijo kuma yasan idan mutanen nan suka san da zamansu ba karamin alheri zasu rinka musu ba. Wanda zai koma jikin Malamijo a karshe. Saboda haka ya matso hawaye ya sanar dashi mutuwar Zayyan da kuma hatsarin da su Mairama suka yi ita da 'yarta suka rasu gabadaya. Wannan shine dalilin da yasa aka dena ji daga garesu. Abu na biyu kuma shine aike duk karshen wata daga kasar Germany wanda Retired Major Mustapha bai taba dena yi ba tun bayan samun lafiyarsa da aiki a can din kusan shekaru hudu. Kudi ne yake turowa ta hanyar wani soja da yake karkashinsa a da kuma ya yarda dashi. Wannan mutumi duk wata Maikudi yasan ranar da yake zuwa har barikinsu ya karbi kudin da suke mazaunin kudin makarantar Radhiya da kuma tallafi ga Mairama. Soke abinsa yake ga gidan Kano ya saka 'yan haya. A takaice dai yana ta gina kansa don ya sayi fili a cikin Sakkwato yana ta makara gini da kudin marayu. ********** Mairama ta koma ta tarar da babbar kura. Malamijo ya karbi sadakinta daga hannun Alh Indararo an saka biki wata uku kafin ya gama yi mata gyaran gida. Ta shiga matsanancin tashin hankali har Nene Marka tazo amma kowa cewa yake tayi auren ko zata sami hutu itama. Tayi kukan, tayi haukan duk a banza bata da mai tsaya mata. A bangare daya kuma duniyar Salame ta juye. Mutum kamar Alh Indararo ace yana son mace kakarta ta yanke saka. Shine wannan karon ma irin abinda take muradi ya tafi ga Mairama. Rantsuwa tayi cewa hakan bazata sake sabuwa ba. Gidan Malaminta da suka saba kashewa kudi domin a dawo mata da Salisu taje. Bayan dogon bugun kasa yace ta saka ranta a inuwa akwai rabo yana iya gani tsakaninta da Alh Indararo amma sai an kawar da Mairama. "Malam rufa min asiri kanwata ce fa. Ni dai bazan iya kasheta ba" Gemunsa na munafurci da suke cutar jama'a dashi ya ja yana murmushi "waye yace sai kin kasheta. Idan kina so nakasa kawai zamu dora mata wadda zata saka ya fasa." Kwana biyu tana tunani kafin ta hasko me take son ayiwa Mairama. Magani ya bata ta wuce gida ta saka a inda ya umarceta. Kwana uku a tsakani kuwa wata safiyar lahadi Mairama ta tashi bata gani sai dususu komai yayi hazo. Cikin maganin digawarta na ido Salame ta zuba mata maganin. Cikin wata guda idanun Mairama sai suna. Duk abinda ya rage mata ya kare a neman maganin ciwon idon amma asibiti basa ganin komai. Kuka ashe bai kare mata ba. Bata gane kowa sai duhun inuwa. Tashi guda Radhiya ta koma idanunta madogararta. Alh Indararo ya canja sheka bazai iya auran musaka ba Salame har ta tare abinta. Karatun yaran ya tsaya yau da gobe Malamijo ya gaji da dan mikawar da yake yi. A bisa dole ta hakura da karatun Radhiya da Emzee. Tana kuka kan kuka amma mahaifinta bazai iya kulawa da ita ba bare 'ya'ya, iyakarsa dasu shine za'a dafa abincin gidan dasu. Radhiya ta fara hankali tasan cewa mahaifiyarta tana bukatarta shiyasa bata fita idan ba aike ba. Emzee kuwa dama daddawar daka ne shiyasa bata hadu da matsalar ace suna yawace-yawace ba. Rayuwar Mairama matar soja ta cika da wahalhalun da suka sa take bukatar a dube ta. *********** Maza ne uku a karkashin bishiyar darbejiya wadda ta yiwa wurin yalwatacciyar inuwa. Daya yana zaune akan kujera sauran biyun kuma suna gabansa ne kana gani kasan mai mulki ne da wadanda yake mulka. Gyaran murya na kan kujerar yayi suka dawo da hankula gareshi "Mal Gide" "Ranka ya dade" wanda yafi manyanta cikinsu ya amsa. "Habubakari" "Allah Yaja zamaninka" na biyun ya amsa. Dan murmushi yayi domin kuwa su biyun yayun matarsa ne Innawuro. "Mal Gide kaine babba saboda haka ta kanka zan fara. Ba tare da jan zance ba magana ce akan sakacinku da zumunci saboda wani abu can da ya faru shekarun baya" Mal Gide ya hadiyi yawu yana kallon Habubakari shima kuma yayan nasa yake kallo. Ardo Barkindo ya dan duku da kansa kadan daga kan kujerar "wannan zumuncin da kuka banzatar ina mai tabbatar muku sai Allah Ya tambayeku akansa. Kune kuka ci bashi kamar yadda naji a bisa dole. Dole tasa kuka biya bashin da kanwarku sai gashi daga karshe ya sakota ya bukaci kudinsa ko. 'Yar uwarku ta sadaukar da farincikinta saboda ku amma shekaru sun tasanmu talatin marainiyar da ta bari baku san cinta ba baku san shanta ba" Habubakar wanda abin shima ya dame shi amma tsoron Gide ya hana shi furtawa ya sharce kwalla "Ardo zamu gyara, wallahi nima abin ya dameni. Ali bashi da kirki ko kadan. Allah ma yasa tana da rai yarinyar nan" "Yarinya da ranta amma tana cikin mawuyacin hali. Yanzu da na kiraku dama sanar daku zanyi cewa zan daukota ko dan kwanciyar hankalin Innawuro" Nan ya sanar dasu komai game da Mairama kamar yadda yaji daga bakin mijin Nene Marka bayan ya soma binciken nemota. Mal Gide sai hawaye. Bakar zuciya tasa ya umarci 'yan uwansa da babu su babu zuri'ar Malamijo, ciki kuwa harda 'ya daya tilo ga kanwarsa Mairo wadda ya yiwa auren dole da Malamijo. "Da kaina zanje in daukota da yaran su zauna a gidana Zan gyara wannan abu duka laifina ne" Ardo Barkindo ya kada kai yana murmushi "haba dai Gide ai bazamu yi haka da kai ba. Yarinya a wurin babarta zata zauna. Duk na gama wahalar neman sannan kace zaka daukota ka kwashe ladan" Murmushi ya maida masa "duk yadda kace ranka ya dade, kamar yaushe zamu tafi?" "Jibi in sha Allahu. Ina so ku tattaro kan 'ya'yanku har na gidan aure da suke rugar nan da kewaye maza da mata. So nake muje mu cika musu ido mu wanke gorin dangin uwa da na tabbatar ansha yi mata." Sun tashi da fara'a kowa yana jin kamar an sauke masa nauyi daga zuciya. Ardo Barkindo ya nisa yana tunanin ya boye musu makantar Mairama saboda yasan duka hankulansu zasu tashi. Idan sun je zasu ganewa idanunsu. Ko matarsa ya kasa fadawa ita da ta uzzura masa akan neman 'yar yayarta da take bi. Mal Gide kuwa har ya isa gida yana tunanin da yardar Allah zasu kula da ita bakin iyawarsu su daidaita tsohuwar baraka. Tunawa yayi da umarnin Ardo ya tura guda cikin 'ya'yansa da yaje ya fara sanar da yayyensa cewa suna da zuwa Kano jibi daga rugarsu wadda take cikin karamar hukumar Giade a jihar Bauchin Yakubu. [02/11 7:29 AM] My 2nd Mtn: 18. WAIWAYE.... Zainab tayi kuka har ta gode Allah. Hadir dinta ne kwance baya iya motsa kowace gaba a jikinsa sannan baya iya magana. Idanunsa kadai ke aiki idan anyi magana kuma yana ji amma babu damar amsawa. Tun iyaye na rarrashinta har suka kyaleta ta koka ko zata ji sa'ida. Zuwansu Kano kenan aka kaisu tsohon dakinsa inda yake zaman jinya. A hankali ya bude idanunsa ya saukesu a kanta. Murmushi yayi wanda ya hado da zubar hawayensa. Sunanta yake kira amma babu mai jin sautin saboda baya iya motsa harshensa. A guje ta fita da ta ga ya tashi ta dauko Ibrahim yana wasansa a dakin kakarsa. Dakin ta koma dashi ta kama hannun Hadir ta hada da nasa. "Idan ni bazaka tabani ba ka tashi ka dauki danka. Don Allah...don Allah Hadir ko Ibrahim ne ka rike da kanka" Runtse idanunsa kawai yayi. Yaya zaiyi da iyalinsa? Allah ne gatan gidansu sai shi da guntun albashinsa. Shikenan rayuwarsa da tasu ta tsaya saboda lalurar da ta same shi? Ina Major Mustapha? Yayi rai ko shima ya rasu? Ina Mairama da Radhiya? Akwai amanar takardun kwafin gidansa a wurinsa. Ta yaya zai isa ga wannan mutane da yake tausayawa duk da halin da yake ciki. Kanwar Hadir ce ta jiyo Zainab tana surutai ita kadai tazo ta fitar da Ibrahim sannan ta fadawa mamansu halin da take ciki. Tun zuwansu ko ruwa bata sha ba sai kuka. Umman tasu taje har dakin tace mata ta taso ta ci abinci shima ta barshi ya huta. Kamar ba da ita take ba tana ta magana taki tashi sai cewa take ta koshi. Babansu Hadir aka kira shima yazo yace indai kuka zata rinka yi to ta fita daga dakin. Hannu ta dora a baki da sauri "na dena, wallahi na dena" tana magana hawayenta da na Hadir yana karuwa. Baban ya fita yana cewa Umma ta kyaleta dama sun sani dole tayi kuka. Bayan fitarsu hannunsa ta kama tana shafa kumatunta "Hadir kana ji na?" Jikakkun idanunsa ya kifta mata yana son yin murmushi "kin fiye rigima" yace a ransa. Shagwabar da ta saba yi masa take kokarin yi kuka yana cin karfinta "ka taimakeni ka tashi, kaga Ibrahim ya kara nauyi yanzu. Ni kadai kake so na rinka daukarsa? So kake ya buda min kirji irin naka?" Lumshe idanu yayi yana sauraronta tana ta yi masa magana. Can ya soma jin fitsari, ya rasa yadda zaiyi tun yana kokarin rikewa har ya saki a kan katifar kamar kodayaushe yanzu ya zamewa kannensa wani karin nauyi. Lura da danshin Zainab tayi ta mayar masa da hannunsa inda yake ta fita wurin Ummansa tana neman tsumma da ruwa. "Fitsari yayi ko?" Umman tace tana jin babu dadi. Murmushi Zainab tayi "eh Umma, yanzu zan gyara wurin" "Barshi Zainab ki huta kinji. Idan kannensa sun shigo sai su gyara. Yanzu zaki ga daya daga cikinsu. Sun san yanayin nasa shiyasa basa yin nisa ake barin guda a kusa" Kai ta dukar "danshi zai dame shi. Zan iya gyarawa" Bata jira cewarta ba ta koma dakin. Yana nan inda ta barshi sai kansa da ya juya yana kallon sama sabanin dazu da yake kallonta. Wani kululun bakinciki yaji ya rufe shi a lokacin. Ya gama wahala ya dawo da ransa amma ya zama kaya irin haka. Zainab dinsa abar tattalinsa ita ce haduwarsu ta farko bayan watanni zata kare a gyaran fitsari. Kuka zuci ya rinka yi har ta gama mirgina shi ta sauya masa kaya sannan ta cire zanin gadon ta shimfida zanin goyon Ibrahim a gefe inda ta ja shi ya kwanta. Zama ta kuma yi ta dora kansa a cinyarta "Hadir" Bude idanu ya sake yi sai ya ga ta duku da kanta ta sumbaci lebensa. Zuciyarsa tayi nauyi matuka. Ga matar da yake so take son shi amma ko yatsanta bazai iya rikewa ba. "Ka ga alamomi zamu fara koya yadda zan rinka ganewa idan kana bukatar wani abu" Ido ya kifta don ya nuna mata ya fahimceta. Ta gyara zama tana yawo da yatsunta a kansa "idan kana son abinci ko ruwa sai ka juya kanka barin dama. Idan kuma bandaki kake son zuwa sai ka juya hagu. Ni kuma sai ince abinci ko ruwa idan dama ne. Sai ka kifta ido sau data shine eh, sau biyu kuma a'a" Ta jima ko lokaci bata tunawa tace sai sun kwatanta. Ummansa da kanta ta dawo tace lallai tazo taci abinci. Ko da ta diba dakin nasa ta sulale ta koma taci. Shi sai su kunu ko koko ake bashi da ruwa. Asibitin da aka kaishi a Kano ne suka ce kada a bashi mai nauyi har sai ya soma sabawa da sabon yanayin jikinsa. Kudin da aka nema na gwaji da aikin da ake tunanin yi masa kuwa ko yana daukar albashi kila sai ya shekara biyar zai tara su. Aiki a lakarsa ta kashin baya ba karamin tsada bane dashi. Da daddare ko keyarta basu gani ba a ciki. Hadir ya sake matsuwa cikin daren tana rungume dashi tana bacci haka ya saki fitsarin nan ya bata musu jiki saboda bashi da damar tashinta. Tana tashi da asuba gyaran wurin ta soma yi sannan ta goge masa nasa jikin tayi masa alwala. Satinsu daya babanta ya koma. Zainab ita take yiwa Hadir komai banda zuwa bandaki saboda yayi mata nauyi. Wannan tana ganin yayi alamar take sanar da kaninsa. Wata guda suka yi a haka babu wani cigaba kullum yana nan a yadda yake sai ma hawan jini da ya kama shi saboda yawan tunani. A wata na uku mahaifanta suka dawo dubiya. A lokacin ne kuma baban Hadir a gabansa da Ummansa da iyayen Zainab ya bijiro da maganar kashe aure. Kofin kunun hannunta ne ya subuce bata sani ba kuma bata damu ba. "Kashe auren wa kenan?" Babanta ya tambaye shi. "Zainab da Hadir" Zubewa tayi a kasa ta fashe da kuka "Umma kuyi hakuri idan wani abu nayi zan gyara." "Ko daya Zainab. Wannan shawarar da wahala muka iya yanke ta. Zamanki da Hadir babu alfanu sai tarin wahala. Nasan kunyi mana halacci da kawaici amma in sha Allahu bazamu bari naku hakurin ya kare ba" Kuka sosai Zainab ta saka tana ji suna cigaba da maganar tana ta magiya. Shi kansa Hadir din hawaye yake fitarwa. Babansa ya sake bata hakuri "kina da kuruciyarki ta yaya zamu barki da mutumin da bazai iya yi miki komai ba sai zame miki nauyi. Abu na biyu Hadir ne karfinmu mu kanmu. Yana kwance yanzu mu ma rayuwar wahala take mana ta ina zamu ajiyeki? Yau da gobe sai Allah 'yata Zainab, watarana zaki bukaci fiye da Hadir amma aure yayi miki dabaibayi. Zaki so kulawa da kowacce mace take muradi a gidan aurenta. Sannan ko mu iyayensa zamu iya gajiyawa balle mata. Komai fa sai anyi masa hatta gyara kwanciya. Kudin aikinsa kuma bamu da yadda zamuyi mu taba hada rabinsa ma. Zuwana Sakkwato uku akan maganarsa sun ce babu kudi a barikin" Zainab daga gaban wannan take zuwa gaban wancan tana kuka tana roko akan su barta da mijinta. Kwarai ta basu tausayi amma basa son nuna son kansu da rashin dattako. Hadir sai rufe ido kawai yayi zuciyarsa tana kuna sai da yaji mahaifinsa ya kira sunansa. "Hadir, ina mai umartarka da ka sauwakewa Zainab kada mu zama masu daukan alhaki, ka amince" "Kada ka sakeni, don Allah ku barni da aurena" Zainab ta fada cikin tashin hankali. Kifta ido Hadir yayi babansa ya sake cewa " ka amince cewa kai Hadir ka yiwa Zainab matarka saki daya?" Wannan karon ma ido ya sake kiftawa yana zubar da hawaye. Zainab yaji ta fado a jikinsa ta kankame shi tana kuka bata san ma me take yi ba "Wallahi ban saku ba, babu inda zani" Mamanta da Umman Hadir kukan suke tayata saboda tausayi. "Zainab kiyi hakuri" "Ba fa zan je ko ina ba ai ba da bakinsa yayi sakin ba" Babanta gani yayi abin yana daukan lokaci an kasa rarrashinta ya tashi ya mareta. Ta rike kunci baban Hadir yana cewa don me zai mareta "yaya take so muyi mata ne? Duk wani bayani anyi amma da gangan taki ganewa. Ki tashi maza ki hada kayanki yau dinnan ma zamu koma" Karamin hauka Zainab tayi ranar har suka bar garin gashi ance ta bar Ibrahim saboda Hadir yaji saukin rabuwa da ita shima. Sau biyu tana guduwa Kano bayan sun koma sai da babanta yayi mata kaca kaca karshe ya yi mata aure. Lokacin Hadir ya kusa shekara biyu a kwance. Ranar da aka kaita a ranar ta nuna mijin da wuka tace ko ya saketa ko ta kashe shi ta kashe kanta. Bai tsaya bata lokaci ba yayi mata saki ukun da ta bukata. Iyayenta sunyi fushi sosai da ita ta koma wata iri ita kanta saboda tashin hankali. Sai da kyar ta samu suka hakura bayan an sake saka mata rana da wani ma'aikacin kamfanin man fetur a Port Harcourt. Wannan karon babanta yace idan ta sake kashe aurenta ko taje Kano bazai yafe mata ba. Mijin nata mutumin Sakkwato ne amma a can Port Harcourt din zasu zauna. Ba don taso ba akayi auren. Mutumin mai suna Musa Waziri yana matukar son Zainab shiyasa baya fushi da ita. Yana da kudi shi ya canjawa iyayenta gida ya samarwa yayyenta maza biyu aiki a branch din gidan mansu suka samu rangwame daga kangin talaucin da suke ciki. Ranar da ta tare tayi kuka kamar ranta zai fita. Gani take taci amanar Hadir shiyasa har shekaru suke tafiya tsakaninta da mijinta bata taba wata doguwar walwala ba. 'Ya'yansa 'yan mata biyu da ya rabu da mahaifiyarsu su kadai ne suke samun kulawarta. Wannan dalilin shi ya karawa Musa hakuri da ita da halinta na rashin son sa. Duka wani hakkinsa tana saukewa amma soyayya da fara'arta sai yayi watanni bai gani ba. Hadir yana nan kwance sai gashi da suka samu kaninsa yake kaishi idan yayi ciniki a kasuwa kudi sun samu. Gashin yana taimaka masa wurin jin dadin jikinsa saboda yawan kwanciya. Magana ce dai da wuya yake iya hada kalma daya kwakkwara. Ibrahim yana girma ya gane waye Hadir a wurinsa a hankali ya gudu daga cikin gidan ya koma dakin mahaifinsa. Sannu a hankali indai ba yana makaranta ba komai na Hadir ya dawo gareshi. Idan aka kaishi hutu wurin Zainab baya iya sati biyu ya rinka cewa Abbansa kenan dole a mayar dashi da wuri. A haka shekaru ke tafiya a haka rayuwar wannan iyalin ta wargaje gabadaya daga aikin soja. Miji ya koma kan wheelchair ga ciwon zuciya ya kama shi da gaske saboda yawan tunani. Uwa ta sake aure bisa dole amma zuciyarta tana ga tsohon mijinta sannan dansu ya taso a wata bahaguwar rayuwa bai san komai ba tunda ya fara wayo sai jinyar mahaifinsa. A bangaren Hadir rashin iya magana ya nemi iyalin Zayyan yana damunsa sai ya kwana yana kuka idan ya tuna rasuwar aminin da ya dauka tamkar dan uwa. A irin lokutan ciwonsa ke tashi a kasa gane kansa. Zainab ma bata taba mantawa dasu ba amma kunyar nemansu take yi a yanzu bayan shekaru sun ja ta dan dawo cikin nutsuwarta. Bata san Zayyan ya rasu ba haka nan bata sani ba ko shima ya dawo kamar Hadir. Mami kuwa sunan garinsu kadai ta sani ta ina zata fara nemanta. Babban abin dubawa shine komai na rayuwa duk yadda ka kai da matsuwa dashi sai Allah Ya nufeka da yinsa. Mukan kwadaitu da gabatar da wani abu mai girma a garemu amma sau tari sai wasu abubuwa suyi mana shamaki dasu. Yanayin rayuwa bai mantar da Zainab mutanen da suka yi zaman amana ba amma halin da ta tsinci kanta yasa damuwarta ta danne hangenta. Burinta daya ne a rayuwa...ta komawa Hadir! ********** "Ni na kashe shi...ni nayi ajalin Zayyan..ina zan saka kaina? Hassana na kashewa Alheran mahaifi. Meyasa nima ban mutu ba?" Kuka ne irin na mazan da suka ga tashin hankali muraran ba labari ba. Babban soja mai ji da jarumta shine yake zubar da hawaye kamar yaron goye. Farfadowarsa kenan daga allurar anasiziya da aka yi masa kafin a shiga dashi theatre. Tsahon sati biyu da kwanaki da yayi a asibitin Katsina kafin likitan da zaiyi masa aikin kafar yazo daga asibitin koyarwa na Zaria yayi su ne a cikin halin rashin sanin inda yake. Irin kukan da Mami tayi na fili da na zuci bazai fadu ba. Major Mustapha soja yayanta kuma uban 'ya'yanta shine wasu cikin masu zuwa dubiya suke kirawa hauka. Dole ace yana hauka don idan har zaka zauna dashi na minti biyar ido biyu surutan da zaka ji yana yi kwatakwata babu ma'ana ga wanda baya tare dasu a ranar da abin nan ya faru a dajin Liberia. Labari ne na yaki, tashin hankali da zubar jini. Tsananin ciwon da kafarsa take yi shine musabbabin fitarsa daga hayyacinsa har yake wadannan surutai. An tabbatar musu da cewa zafin ciwo ne kawai. Asibitin suna kokarin dressing din ciwon amma yadda tsutsa ke fita suna cin namansa daga ciki shi kadai yasan azabar da yake ciki. Dakin kansa wani irin wari yake yi don kannensu maza ke kwana dashi ma. An hana Mami kwana sai dai tazo ta wuni ta koma gida. Kudi sosai suka kashe akan ciwon nasa. To yau dai Allah Yayi likita yazo an yanke kafa dan abinda aka bari iya rabin cinyarsa ne. Sauran naman duk ya zagwanye saboda infection. Abinda yake fada ya tadawa Mami hankali. Cikin nutsuwa ta matsa kusa dashi tana tambayarsa me ya sami Zayyan din. "Ni ne dai nayi ajalinsa. Ashe duk mutuncin da yaron nan yake nuna min a dalilina zai rasa ransa. Ya ceci rayuwata ya rasa tasa. Me yasa nima ban mutu ba?" Mami ta shiga rudani aka sake kiran likita yace su kwantar da hankulansu allura bata gama sakinsa ba. Da kadan da kadan sai da suka kwashe wata uku cur a asibitin nan. Kafarsa ta hade wurin sai dungulmi amma ya gamu da wata sabuwar lalurar da basu ankara da ita da wuri ba wato septicemia. Infection ne na jini da yake samuwa daga infection a wani bangaren jiki sai kwayoyin cutar su gangara cikin jini. Da zazzafan zazzabi abin ya fara sai kuma yawan jin sanyi. Da fari magunguna da alluran malaria aka bashi. Yayi sati ana wannan babu wani chanji sai ma gaba da abin ya kara. Bugun zuciyarsa sai ya kara gudu har ana gani dagowar kirjinsa, dama ga muguwar rama da ya hada. Da likitocin suka ga babu sauki akace typoid ce. Nan ma duk wasu allurai da magunguna sai da ya karar dasu. Hankula sun kara tashi ne ranar da zuciyarsa ta nemi bugawa shine fa aka rinka gwaje gwaje baji ba gani. Jininsa har asibitocin koyarwa na Zaria, Kano da Ibadan an tura domin gano abinda yake damunsa. Rashin wadatar kayan aiki a asibitocin kasarmu ya janyo Major Mustapha ya kusa rasa rayuwarsa. Da kyar aka gano a asibitin Ibadan aka turo musu sakamakon. Sai a lokacin aka fara treatment bayan infection din yaci jininsa sosai har ya fara harin kayan cikinsa. Da aka sallamo shi haka ya dawo gida kamar mutum mutumi. Yau da lafiya gobe babu. Ya rage surutai sai ma rashin son magana da kebewa daga mutane. Idan ya kalli kafarsa sai yaji ya tsani rayuwa gabadaya. Da bai rasata ba Zayyan bazai dawo daukarsa ba. Da sai su gudu tare su tsira tare. Yayi shekara a kwance. An sayar da motarsa da filinsa na nan Katsina duk a siyan magunguna masu tsada domin samun lafiyarsa. Wata rana Mami tayi masa zancen su Mairama sai kawai ya saka mata kuka. Taya shi tayi don gabadaya mijin nata yanzu tamkar bashi ba. "Da wane ido zan kalleta Hassana? Ko kinsan cewa da don ta ni ne wallahi na gwammace na kare rayuwa a Liberia da na dawo gida na fuskanci matar Zayyan. Na zama silar da bomb ya tarwatsa mata miji shine abinda kike so kiji na fada mata idan ta tambayeni ta yaya mijinta ya rasa ransa?" "Kayi hakuri Daddy ba manufata ba kenan. Kasan ya barta da ciki ga Radhiya" Kai ya girgiza "baki san nauyin da zuciyata take ciki bane da kin kyaleni. I feel guilty and I hate myself and.... my life. Idan zaki je nayi miki izini" Tasowa tayi ta rungume shi tana hawaye "nima me zance mata?" "Ban sani ba..." yace da raunin zuciya yana kara kankameta. Kwanaki kadan da yin wannan magana wata rana da daddare suna kwance ta tuna Fauziyya ta kwanta bata yi fitsari ba. A gidansu Major din aka basu wani bangare dakuna biyu masu fuskantar juna. Awwab a wurin samari yake kwana har an mayar dasu makaranta. Ta je ta kai Fauziyya tayi fitsari ta dawo da sanda saboda kada ta tashe shi. Amma duk da haka sai da ya farka. Inuwarta ya gani ta tuna masa da lokacin da 'yan tawayen nan suka rinka fitowa ta baya da saman bishiyoyi suna harbinsu. Baiyi wata wata ba ya mirgina jikinsa ya damkota. A daidai wannan lokacin jinsa yake kamar a wancan lokacin. Kunnuwansa suna jiyo masa sautin harbi da hayaniya tartar. Wata muguwar shaka ya kaiwa Mami ya sakar mata karfi. "Captain na kama daya kuzo ku daure shi mu tafi dashi base dinmu" yace da dan karfi. Mami sai kokawa take tana son yi masa magana ta kasa saboda wuyanta da ya shake tana numfashi sama sama. A daidai kunnenta yace "Who sent you?" Wahala ta fara yawa Mami duhu duhu take gani. Da kyar ta samu ta juya ta saka duka karfinta ta galla masa cizo a kirji. Gashin kanta ya damko da karfi ta saki kara. Daga hannu yayi ya kwada mata mari ta sake yin wata karar. Zai kuma marinta haske ya mamaye dakin. Mahaifiyarsa ce ta shigo tare da kaninsa da suka ji ihun Mami. Tana zuwa itama hannu ta cire ta mare shi. "Kasheta kake son yi ne Mustapha? Sakar mata gashi" Tamkar wanda ya tashi daga bacci sai lokacin ya kula da hannunsa da inda hannunsa yake yayi saurin sakinta. A guje ta tashi ta fada jikin Innarsa tana kuka. Wuyanta Innar ta lura dashi saboda farar fata yayi jawur. "Na shiga uku ni Fatima me zan gani? Ba dai shaketa kayi ba?" Kansa yaji ya daure wai me yake yi a dakin nan shi da suke tare da su Zayyan a daji. Firgici da tsoro ya kama shi ya soma yunkurin sauka daga kan gadon. Innarsa ta dakatar dashi. "Kada ka soma matsowa inda muke wallahi." Ta kalli kaninsa "rufe min shi da safe sai a fadawa Alh Baba kafin babanku ya dawo" Washegari zama na musamman akayi akan abinda ya faru a daren. Mahaifiyar Mami ta shafawa idonta toka tace 'yarta ko dai ta koma gida ko kuma a raba musu daki bazata yarda a kasheta ba. Ko wace ma hakan zata yi shiyasa aka tattara Mami da yaranta ta kuma gidan iyayenta. Major Mustapha kuma ya shiga wani sabon mawuyacin mataki a rayuwarsa. Iyaye duka sun hadu akan cewa gamo yayi a dajin nan aka shiga banka masa magungunan gargajiya, hayaki da rubutu. Kowa yaji labarin maganin aljanu cikinsu zai bada kudi domin a kawo su gwada. Idan ka ganshi dole ka koka in kasan waye Major Mustapha. Ya rame ya kare sai kashi da tashin hankali. Kuma abu kadan yake tayar masa da wannan abu ya fada cikin dogon tunani yana ganin kamar yanzu abin yake faruwa. Awwab shine mai zama dashi sosai kafin watarana shima ya shigo daki ya nemi Daddyn nasu ya rasa. Ya zauna jiran ko yana bandaki amma shiru. Haka akayi ta neman Major hankalin kowa a tashe. Mami taci kuka ta more. Sai can kamar ance Awwab ya duka ya ganshi a karkashin gado yana ta rarraba idanu. "Mami gashi nan" "Shhhh zasu ganmu." Mami ta dake ta duka itama "su waye zasu ganmu Daddy?" " 'Yan tawayen mana" Kasa magana tayi ta tashi ta koma dakin Innarsa tana kuka. Har yaushe zasu kare rayuwarsu a wannan yanayi? Dama haka ake auren sojan ko kuwa kaddararsu ce haka? Sauki babu sai daga Allah. A wannan yanayin Gambonsu Mami da mijinta Harun da a wurin Alh Baba suka zo daga Germany inda yake aiki a gidan rediyo a matsayin mai labarai. Sunyi bakincikin yadda rayuwa ta mayar da 'yan uwansu shine Harun ya shiga newarwa Major da Mami visar tafiya. A cewarsa zai kai dan uwansa asibiti ne tunda babu wani cigaba a gida. Iyayensu dai sun kyaleshi ne amma a iya tunaninsu asarar kudi zaiyi. Abu na Allah sun tafi Germany a shekara ta uku bayan rasuwar Zayyan. A can ne bincike ya nuna Major yana fama da Post Traumatic Stress Disorder (PTSD). Lalura ce ta kwakwalwa da a lokacin ba'a waye da ita sosai a bangarenmu na Africa ba. PTSD tana samuwa ne ga mutanen da suka yi gamo da mummunan yanayi ko al'amari kuma tana tashi ne idan suka samu kansu a yanayin da zai iya tuna musu da wannan abu. Yawan mafarkin da yake yi da kuma ji ko ganin kamar yanzu abin yake faruwa duka alamominta ne. Mami tambaya take ba haukacewa yayi ba aka ce mata ba hauka bane sai dai masu ita suna bukatar tsantsar kulawa daga makusantansu don idan abu yayi yawa wasu har kashe kansu suke yi. A gidan Gambo suka zauna har zuwa lokacin da ya fara jin sauki. Mami ta jajirce sosai wurin kula dashi. Daga baya ta fara tunanin kada su zame musu nauyi tace Harun ya nema mata aiki. To aiki a wata kasar ba'a samunsa kai tsaye. Ta bukaci ko yaya tana son neman kudi kafin su koma saboda kusan karkaf sunyi. Komai nashi ya kare an fara shiga aljihun dangi. Aikin nanny ya samar mata har yana tsoron fada mata sai ta basu mamaki wurin karbar aikin hannu bibbiyu. Gidan wasu 'yan kasa take zuwa daga bakwai na safe zuwa bakwai na yamma. Tayi su shara, wankin toilet da sauran ayyukan gida hade da raino. Mutane da dama suna zaton da ance ka fita waje watayawa kake. Aikatuwa take bilhakki mijinta yana kukan nakasa a gefe. A hankali masu gidan suka yaba da kwazonta sai aka basu wani dan bangare karami a gidan. Cikin shekarsu ta biyu Harun yaje gida abinda ta hada ta bayar aka dauko musu 'ya'yansu sauran kuma ta aika Sakkwato wurin sojan da Major ya rubutawa sako cewa a bawa su Mairama. Shekara guda cif cikin kudin aikin Mami ake dibarwa Mairama. Sako ya riskesu daga karyar Maikudi cewa tayi aure sannan dan cikinta baizo da rai ba. Hoton Alheran Radhiya kuwa da suka bukata cikin dakin Jume ya dauko wani da aka yi musu da yaransu gidan wani zuwansu da sallah. Murna sosai ranar da suka amshi hoton. Cikin ikon Allah sai ga Mami da ciki. Allah Ya bata 'ya mace Major ya saka mata suna Zayyanatu. Dariya tayi da taji sunan yace idan haihuwa goma zata sake Zayyan da Zayyanatu zaiyi ta saka musu. A yanzu Major ya sami aiki a wani kamfani shima sannan Awwab ya sami scholarship saboda kwazonsa a makaranta. Harun da Gambo sun koma Nigeria da 'ya'yansu uku Ghazalatu, Hafsa da Imam. Su Mami kuwa zaman jiran kammaluwar karatun Awwab suke su koma su ma. Sun sami rufin asiri daidai gwargwado kuma sai Major yayi watanni lalurarsa bata tashi ba sai anyi zancen Nigeria ranar zai kwana hankali a tashe yana tuna aikin da ya yiwa kasarsa ya kaishi ga wannan rayuwa ********** HADUWAR ALKHAIRI [02/11 7:30 AM] My 2nd Mtn: 19. Max, Anna da Liam sune 'ya'yan da suka tashi a hannun Mami. Suna ganin shigowarsu lawn din suka taho suna murna. Idanun Anna jazur taci kuka tun safe take abu daya. Rungume Mami tayi "bana so ki tafi Naanaa" tace cikin yaren jamusanci. Da yaren Mami ta maida mata "kiyi hakuri Anna, watarana zan zo ziyara ko ke kizo mana Nigeria ko" "Zaki zo aurena next year?" "In sha Allah" Hawaye Anna take ta rinka sumbatar kumatun Mami ita kuwa sai dariya. Liam da Max hannuwanta suka rike suka kaita tsakiyar wurin suna nunawa jama'a Naanaa dinsu. Mai aiki ce amma wadda take a inda aka san darajar masu aiki har masu gida suke karrama su. Ta sami kyaututtuka da yawa daga abokan aikinta da abokan arziki. Frau Marie Schmidt ta kawo envelop da kudi a ciki ta bata sannan ta bawa Fauziyya da Zahra wasu setin dankunne da sarka 'yan ubansu wai su saka da bikinsu. Zayyana ma an bata katon teddy kusan kansu daya. Tana ta murna Mami a ranta tayi dariya kawai. 'Yan kasarmu ina muka wani san darajar teddy. Hotunan tarihi suke dauka Major ya daga waya yana fadin inda suke. Ko minti biyu ba'ayi ba sai ga matashin saurayi kyakkyawa wankan tarwada mai cike da kwarjini da haiba ya shigo wurin sanye da uniform dinsa na matukin jirgin KLM mallakar kasar Germany. Jacket da wando ne navy blue sai farar shirt a ciki kansa sanye da hula irin ta Captain din jirgi. Mata hudu ne a gefensa hagu da dama air hostess kowacce da uniform riga da skirt sky blue suna rike da flowers masu kyau. Shigowar tasu ta kayatar da mutanen wurin bare iyayensa. Yana shigowa kai tsaye wurin Major ya nufa ya rungume shi. Mami ta saki baki sai kuma ta daure fuska cikin wasa. "Awwab, yau din ma?" Sai da yayi mata dariya sannan ya rungume Maminsa a kunnenta yana cewa "sorry Mamina" 'Yan matan da suke abokan aikinsa kowacce ta mika mata flower da dan gift suna mata fatan alkhairi. Awwab ya fiddo tickets biyar daga aljihun sa ya mikawa Major. "Daddy ga nawa gift din...Captain M.A Mustapha shine zai ja jirginku zuwa birnin Abuja. Sai da na duba schedule dina na sayi ticket. Tafiya ta dawo nan da sati biyu. I hope it is okay" Zayyana tayi tsalle ta dane shi tana ihun murna. Mami sai murmushi kawai na jindadi. Major kuwa tsokanarsa yake yi wai bazai shiga ba kada ya zubar dasu a teku. An gama party lafiya suka koma gida tare dashi. Shirye shirye ya kankama inda suka hada ya nasu ya nasu sai gida Nigeria. *********** Iyayen Zainab sun sakata a gaba kowa da abinda yake cewa tun da ta sanar musu cewa a yiwa iyayen Hadir magana akan aurensu. "Wai shin idan kin koma soyayya zaki rinka zuba muku a kwano kuna ci? Ke ba aiki shi a zaune. Ni har yau ban gamsu da ba ke kika kashewa kanki aure ba" mamanta tace a hasale. Babanta ne ma mai dan sauki a gareta "Zainab nasan kila ko a wurin Ibrahim kina ji cewa jikin Hadir babu wani sauki sai na musulunci. Kinje kin shafe shekaru tare da Musa kin saba da jindadi. Ta ina zaki koma gidansu?" "Baba na fada muku ya bani gida a Kano sannan ya kara min jari akan wanda ya bani tun da nake zuwa Dubai saro kaya dashi. Alhamdulillah Allah Ya wadatani Abbansu Aisha ne sila. Ni zan cigaba da tafiya kasuwancina ne Ibrahim ya rinka kula dashi idan bana nan" Mamanta ta kara kulewa "sannu uwar tsari, waro har kin gama tsara yadda komai zai kasance" Allah Ya sani tana son iyayenta kuma tana girmama su. Amma wannan karon tana jin tayi girman da ya kamata a karbi uzurinta idan tazo dashi. "Idan ba kwa so na komawa Hadir bazan koma ba. Amma wallahi bazan kara aure ba har na mutu" Tsam ta tashi daga dakin Baban nata. Sun san Zainab da taurin kai. Anyi sa'a ma zamanta da Musa Allah Yayi da tsayin kwana. Tufka suke da warwara suna guje mata matsala a gaba. Karshe mahaifinta yace su barta Allah kadai Yasan dalilin wannan soyayya da take yi masa. Bayan kwanaki ana muhawara da 'yan uwa babanta da kansa yaje Kano da dan uwansa ya gabatarwa Baban Hadir bukatarsu. Sunyi matukar mamaki ace har yanzu Zainab tana son dansu. Matar da sun sani yanzu ita dashi kamar wutsiyar rakumi ne da kasa. Daga irin suturun da take yiwa Ibrahim da abubuwan zamani da take wadata shi dasu zaka san Haj Zainab take don tayi Hajji da Umara albarkacin Musa. "Idan na fadawa Hadir bazai yarda ya aureta ba saboda lalurarsa" Babansa ya amsa musu a sanyaye. Hadir ya riga ya karbi kaddarar rayuwarsa. "Sai kayi shiru mu kulla abinmu a tsakaninmu ba shikenan ba" Kawun Zainab ya bashi amsa. Da izinin Allah a ranar basu tashi ba sai da aka mayar da auren Zainab jaruma mai sadaukarwa da Hadir jarumin kasata da kasar ta dade da mantawa dashi. Da aka kirata da wannan kyakkyawan labari tayi kukan farinciki sosai. Sati daya aka diba tariya inda Baba ya sa Ibrahim ya kwashe kayan sawarsu ya rinka maidawa gidanta da yake Janbulo. Hadir yana kallo bai iya tambaya sai ya sawa ransa ko gyara za'ayi a dakin. ********** "Wayyo Innawuro, kiyi min rai....Ummiiiii ki ceceni" Ihun Radhiya kenan da ya karade gidan tana zaune Emzee ya danneta Innawuro zata yi mata aski. Mairama hakuri take bata akan ta bari ayi "idan ba'a magance kwarkwatar nan ba wallahi duka sai kin shafa mana. Har na gama makarantar kwana ni banyi ba. Ku baku iya kula da kanku sai kazanta da gayun banza" Kyabe fuska ta sake yi hankalinta yana kara tashi "zan wanke Ummi harda karkashi in gumbuda musu gishiri Yasin duk su mutu" "Innawuro ko za'a bari ta gwada saka karkashin?" Mairama tace a hankali tana jin kunyar shigarwa 'yarta. "Kyaleta Mairama don baki ga kan bane. Makero ya cinye keyar sai gashi kadan, gaban kuma amosani da kwarkwata. Yarinya mai cikar gashi da laushi duk ya lalace saboda rashin kula. Na fada miki Mairo ta biyo a cikar nan zai tofo da wuri" "Ayya Ummi ki tausaya min mana" tace a wahale. Emzee ya sake sakar mata nauyinsa akan cinyarta da ya dora kafafunsa yana dariya. "Mugu daga ni" Sake danneta yayi tayi kara Mairama ta kasa hakuri "Karami ka kiyayeni fa, me kake mata ne?" Innawuro ya kalla suka sa dariya wai ta tarewa abokiyar fadanta sai ta kama bakinta ta kunshe. Radhiya na ganin gashinta ya soma zuba ta soma wani sabon kukan "kiyiwa Allah da ManzonSa Innawuro ki bar min na zaman falo. Kina ji fa Baffa Gide yace duk aurar damu zaiyi" Wannan karon dariya harda Mairama "wanne ne na zaman falo kuma?" "Wanda zan rinka daurewa da ribbon inyi kwalliya" Innawuro da Emzee suka cigaba da tunzurata tana ta zuba ana kwashe gashin "ance miki aure za'ayi miki ne kike neman gashin zaman falo?" "Aure kuma Innawuro ai kamar habo ne. Yanzu idan kika kwashe gashin nan miji yazo yay...." shiru tayi da ta ji ana kankarar kan nata da reza. Wani uban ihu ta saka an gama askin Innawuro tana mata kwaryar molo na gasken da reza ana kwashe sauran gashin da fatar da makero ya gama cinyewa tayi wani fari da tudu-tudu. "Wayyo Allahna na shiga uku na lalace, wayyo, wayyo, wayyo" Mairamu maficin hannunta ta daga zata kwada mata "wane irin sakarci ne wannan kike mana ihu kamar wata mara hankali" Sai da ta tashi ta makawa Emzee harara da daradaran idanunta sannan tayi gaba tana cewa "dama Ummi wane hankali ne zaiyi saura akan budurwar da bata da gashi ai sai gyaran Allah" Baki ta rike tana kada kai "anya yarinyar nan ba dabanci ta koyo a bodin din ba?" "Ummi gang garesu fa na fitinannu inji wata kanwar abokina" Daga cikin daki tana kuka ta leko "almunafunfun me ya kaika makarantar mata har ka jiyo gulma. Ummi ta sani dai SS ne ba wata kungiya ba" Tsawa Mairama tayi mata akan ta dena amfani da kalmomi irin wadannan ga kaninta. Innawuro tace "kema kinsan yau tunda da amincewarki akayi askin nan to dukkanmu sai ta nuna mana fushi take yi. Kai Karami zuba gashin nan a leda kaje ka kona. Kwarkwata harda ta sayarwa." Hannuwansa yayi saurin nadewa a kirji cike da kyama "kwarkwatar zan taba? Ashe kowa zaiyi susa a gidan nan" Dama Umminsa yake son tsokana ta fara fada yana dariya ya kwashe yaje bakin murhu ya zazzage. Waje yayi bayan ya wanke hannunsa aka bar su Mairama su kadai a tsakar gidan. Tayi zurfi a tunani da kwadayin ina ma ace zata iya ganin kamanin yaran a yanzu da suka kara girma. Alheran da Zayyan dinta suna da shekaru sha takwas da sha bakwai. "Radhiya kyakkywa ce kamar wata dan daren goma sha hudu, Karami kuwa yadda kika san sojan maigidanki ba maraba sai haskenki da ya dauko" Murmushi Mairama tayi kunya na kamata "Innawuro me ya kawo wannan bayanin kuma?" "Daga yin abin arziki, godiya kawai zaki yi tunda na faranta miki" Karamar dariya tayi ta lalubi sandarta ta tashi. Yanzu ta gane hanyar dakunan gidan ko babu dan jagora. Nasu ta karasa tana mitar wane irin jan kunne zata yiwa Alheran mai tambotsai. Kwanansu hudu tun washegarin dawowarta daga makaranta wai a saya mata form din makarantar sojoji. Tun Mairama na daukar abin wasa sai ga zance har kunnen su Ardo. Shine aka fara zancen aurar dasu. Ita kuma tana da burin Radhiya tayi ilimi mai zurfi amma bazata iya watsa musu kasa a ido ba. Tunawa da tayi anyi aski yau gidan kowa mai laifi ne a wurin 'Yar soja ya saka ta dariya ba shiri. ********** Hadir sai tunani yake yi ina zasu je bayan masallaci maimakon su wuce gida. A motar kaninsa da yake kaisu sallar juma'a suke tare da Ibrahim. Yau sababbin kaya Ibrahim din ya saka masa iri daya da nasa, yadi ne mai kyau da laushi ruwan kwanduwar kwai anyi musu dinki iri daya wanda akayi da zare coffee color. Hatta hulunansu iri daya ne masu kalar zaren dinkin. Sai kamshi suke bazawa sunyi wani irin kyau. Tarin tambayoyi fal a zuciyar Hadir tun da aka fara komai. Mai aski har gida Ibrahim ya kawo yasa yayi masa gyaran fuska sabanin da da yake masa a gida da clipper da Zainab ta siyo masa. Sun taimaka sun dora shi akan kujerarsa wheelchair bayan sun shiga gidan. Daga gefen matattakalar shiga anyi shafen sumunti alamun hanya ta hawa da wheelchair din. Gangara babansa yayi cikin ni'imtaccen falon da ya wadatu da sanyin AC da kamshi. Daga nan kanin Hadir yayi musu sallama ya juya abinsa. Idanunsa na nuni da tashin hankali sai waige yake yi Ibrahim ya barshi ya nufi bakin wasu steps hudu da za'a taka abi hanyar dakuna. Su ma a gefe akwai wurin tura kujerar. Wai kunya ce ta hana Zainab fitowa tana jinsu ta makale a daki. Ibrahim na taba kofar ta taso da wayoyinta a hannu kamar fitowa dama zata yi. Wani kayataccen murmushi yayi mata na jindadi "Mama kinyi kyau wallahi" Irin yadin jikinsu ta saka. Hatta zaren dinkin iri daya ne nata doguwar riga anyi mata surfani siriri mai kyau adon. Daurinta shima yayi kyau ga sarkar gwal dasu awarwaro. Haj Zainab kenan mata a gidan Hadir. Murmushi tayi sai kuma tace "Wuce muje ni" "Fara zuwa Mama naji cikina yana juya min" Bai jira ta amsa ba ya fita da sauri ya shige sabon dakinsa ya dire akan gado yana murna. Abokinsa ne ya bashi shawarar kada ya tsaya musu a ka ya barsu su kadai. Hadadden kamshinta ne ya fara zuwa hancin Hadir kafin yayi tozali da Zainabu Abunsa. Rufe ido yayi ya sake budesu a kanta. Wai da gaske Zainab ce kuwa? A nutse ta iso har gaban kujerar tasa sai ta durkuso ta daidaita fuskarta da tasa. Hawayen farinciki ne ya sauko mata shi kuma idanunsa sunyi ja ya kasa dauke ido daga kanta. Hannu tasa a kasan habarsa ta dago kansa tana masa kallon ido da ido ta sumbaci bakinsa sannan ta rungumo shi a jikinta tana mai kankame shi sosai ta saki kuka. Hamdala Hadir ya rinka yi a jejjere a zuciyarsa don ya tabbata abu daya ne ma'anar kawo shi nan gidan da kuma kasancewarta a cikinsa. ********** Danginsu Major na kusa da na nesa sai tururuwa suke domin ganinsu da yi musu barka da dawowa. Shekaru a kalla sha hudu ba wasa ba. Anyi haihuwa anyi rashi duk basa nan. Gidan kullum a cike da baki. Satinsu biyu kafin suka samu damar kai kayansu sabon gidan da suka rinka turo kudi domin ginawa a GRA. Sun sayi filin tun farkon fara aikin Mami kafin abubuwa su kara tsada. Kwanansu biyu suna aikin son ganin gidan ya dau saiti abu yaci tura suka hakura sai sun dawo daga wurin su Hadir da Mairama. Wannan Sojan mai alkawari da suke turawa kudin Mairama shine ya binciko musu Hadir yana Kano gidan iyayensa. Major yayi ta mamakin to me ya same shi yake gida. Mairama kuma wan Zayyan wato Maikudi tun a baya yace masa tayi aure amma Alheran tana Sakkwato wurinsa. Da wannan suka yi amfani akayi shawarar Kano zasu fara zuwa sannan su wuce Sakkwaton. Basu riga sun sayi mota ba Daddy Harun da yake Abuja yanzu shine ya basu wata bus fara mai kyau da iyalinsa ke amfani da ita wurin tafiye tafiye tare da dreba. Doki da fargabar yaya rayuwa ta kasancewa bayin Allahn nan sun cika zukatan su Mami da Major. Zahra da Fauziyya suna ta kokarin tuna Antinsu Zainab da Ibrahim da suke fada akan daukarsa. Babu wadda tayi shekara goma cikinsu lokacin. Labaran duka wanda Mami ke basu ne don babu abinda suke tunawa. Awwab kuma tuni 'yan kwanakin hutun nasa ya cinyesu a Katsina gashi tsarin aikinsu ba na zama wuri daya bane. Da tambaya Allah Ya kaisu gidansu Hadir can cikin lungu. Bayan gaishe gaishe da iyayensa Major ya gabatar dasu. Sai da ta share hawaye tace yau kwanansa ashirin da shida da barin gidan an mayar da aurensa da Zainab tsohuwar matarsa. "Bangane ba, da auren nasu ya mutu ne?" Yayi mata tambayar don neman karin bayani. Murmushi tayi masa ganin hankalinsa ya tashi "Bari dai nasa a kaiku can gidan nasu sai kuji daga bakinta" Wayar Zainab tasa aka kira mata bata shiga saboda suna asibiti. Kwanansu biyu da aure ta mayar dashi asibitin koyarwa na Kano wato Aminu Kano Teaching Hospital. Gwaji da bincike tasa ayi masa sosai inda aka gano matsalar da ya samu a kashin bayansa yayin fadawa wannan kwazazzabon a Liberia ita ce silar mutuwar jikinsa kashi ya danne wane bangaren na lakar bayansa. Rashin magana kuwa Likita ya tabbatar mata da cewa shock wato firgici ne ya haifar dashi. Da ace tun a baya sun tsananta dabarun dauke masa damuwa kila da tuni an manta da ya taba dena magana.. "Duk da haka Hajiya mijinki zai iya samun lafiya amma shawara mafi a'ala gaskiya ki fitar dashi ko da Egypt ne idan da hali. Lalurar ta dade a jikinsa yana bukatar kwararru a kansa da ingantattun kayan aiki" Kallon Hadir tayi ta saki murmushi "Doctor ka taimaka ka tayani duba asibiti da kuma rough estimate na abinda zan bukata" Bata ankara ba ta bayan kujerar taji an rungumo wuyanta sosai ta sa hannu tana dukan hannayen Ibrahim "dan gidanku shakeni zaka yi?" Hadir yayi murmushi suna bashi sha'awa zamansu tamkar kaka da jikanta. Ibrahim dinsu matashi ne wanda kana kallonsa sai ka sake bare yanzu da mamansa ke kara wadata shi da kaya sa suka dace da zamani. Kin sakinta yayi yana kara manna kansa a wuyanta "Mama mungode injini da Babana" Kwalla taji a idonta da ta kalli Hadir ta ga ya gyada kai "ni ku tashi mu tafi kuna neman saka mutane kuka." Ibrahim ke tura kujerar babansa bayan ta yiwa likitan godiya suka kama hanyar wurin ajiye motoci. Gasu dai suna tafiya miji na zaune amma dole su baka sha'awa yadda duk suka yi kyau ga kuma alamu sun nuna iyali ne da ke matukar kaunar juna. "Mama ki koya min tuki don Allah" "Da wannan rawar kan" "Baba ai bani da rawar kai ko?" Ya dukar da kansa yana tambayar Hadir shi kuwa ya gyada kai yana supporting dansa. "Kuma sunana zaka fara fada idan ka warke ko" Hararar da Zainab tayi masa ce ta saka shi wata dariyar shakiyanci "baka isa ba yaro" Dariya suka rinka yiwa juna kowa ba cewa dashi za'a fara ba kace uwa da danta bane. Tana tuki Ibrahim ke nuna mata hanya don bata waye da garin Kano ba wayar autansu Hadir ta shigo yace yana tare da baki a kofar gidansu. Ya sanar dashi suna hanya sun kusa karasowa. Da ya fadawa Zainab tace su waye. "Bari na kira na tambayeshi" "A'a barshi kawai" Bus ta gani a kofar gidanta da mutane a ciki. Mami tun da Zainab ta karyo kwana ta ganeta. Jikinta na rawa tana sauri ta bude kofar motar ta fito. Major ma haka ya fito yana hango Hadir a daga bayan motar. Hannunta taji yana rawa da ta tabbatar da su waye a kofar gidan. Ta juya a hankali za ta cewa Hadir ya gane su sai ta ga yana hawaye. Bata iya gyara packing ba ta kashe motar ta fito da sauri ko takalmanta bata saka ba. Hannu ta dora akan bakinta ta toshe kukan da yake barazanar yin sautin da kila sai makota sun leko ta suka tako gaban juna sunyi sharkaf da hawaye. "Mami?" "Antin su Zahra" A wajen nan suka rungume juna suna kuka, kuka na gaske. Major ya karasa ya budewa Hadir kofar bayan fuskarsa cike da annuri. "Lieutenant fito mu gaisa" Hadir ko motsi baiyi ba sai rufe ido da yayi hawaye mai dumi na sauko masa. Da yana da lafiya wallahi zai sarawa Major Mustapha ne domin soja ne a gaban ubangidansa. Ibrahim ya fuskaci bai san yaya baban nasa yake ba ya cire kai ya kira mamansa. "Mama zo mu fito da Baba daga motar" A kidime Major yace "me ya same shi?" Zainab ta dawo tana kuka tana dariya tace Ibrahim ya bude gate su shiga ciki. Kallonsa su Mami suke yi ya budw gate din ta shigar da motar sannan duka suka shigo. Wheelchair Major ya ga Ibrahim ya dauko a boot yaji zuciyarsa ta karye Zainab tazo zata taimaka su dora shi yace bari yasa hannu. Hadir ba kiba gareshi ba shiyasa ma suke jin saukin daga shi din. Sai da ya zauna Major ya dube shi da tausayawa "kai kuma taka lalurar kenan Hadir?" "Baba baya magana" Zainab ta share hawaye ta bude musu kofar gidan. Mami da Major mamaki ya kara kama su da jin wai baya magana kuma. Sai da suka zazzauna yaran suka sake gaishe su Zainab ta rike baki "yanzu Zahra da Fauziyya ne haka? Ikon Allah, Inna Awwab din Mairama. Ita kuma wannan 'yan matan kamar a tafi a barmin ita wace" "Zayyanatu sunana" ta amsa da kanta. Mami tana murmushi tace "Daddy yaso yiwa Zayyan takwara sai tazo a namiji" "Allah sarki Mairamu da Zayyan ban san yaya suke ba" Hadir sai runtse idanu yayi Mami da Major na kallonsa da ita. Mami ta daure tace "ashe baki san Allah Ya karbi ran Zayyan tun a Liberia wurin ceton rayukan mazajenmu ba" A gigice tace "ME??? Baban Radhiya ya rasu? Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Kuka suke yi sosai mazan na hawaye harda Major duk dakiya irin tasa. Zainab ta tsahirta tace su Zahra da taga suna tayasu kukan su shiga dakinta bari ta aika a siyo abinci don bata yi girki ba. "Turasu kitchen kawai su dafo mana" "Ayi haka ko ware gajiya basuyi ba. Naga alamun daga nesa kuke" "Babu komai ku shige kitchen ku duka kowa tasa hannu" "Ibrahim jeka sai ka nuna musu. Su dafa mana abin da suke so, ko motsi bana son yi daga wurin nan" Sun san dai wai wayo ake son yi musu. Suna yin hanyar kitchen din Ibrahim ya dawo da baya ya labe sai ga Zayyana ita ma ta dawo kusa dashi tana kara kunnenta a jikin kofa. "Meye haka" ya dan sha kunu. A shagwabe tace "Your mummy and daddy are making mine to cry" Wane kallon sama da kasa yayi mata "sannu baturiya ai ni ya kamata nace haka" Kunnuwansu Zahra ta rike su biyun Fauziyya kuma tace "ku rufe mana baki dalla can muji me ake cewa sosai" Duka su hudun suka sami wurin tsayawa suna jiyo labaran ban tausayi daga iyayensu. Yadda su Mami ke kuka a falon haka suma suke yi. Sun tausayawa juna sosai kowa da irin tasa kaddarar. Damuwarsu sai kuma ta karkata kan Mairama da Radhiya. Sun share kusan awa suna jajantawa juna sannan Mami ta dan bude murya "yaya ne shiru babu ku babu abinci" Zahra ce ta fara fitowa taje ta fada jikinta tana kuka. "Kuji min yaran nan, labe kuka yi kenan?" Zayyana ta gyada kai tana sababbin hawaye. Zainab tayi dariya "to yau kunji rayuwar iyayenku ko" Ibrahim ba kunya ya koma gefen Zainab kamar zai shige mata ciki yana kara son mahaifiyarsa. "Anya wannan zaiyi soja kuwa?" Inji Major "A'a wallahi ni malamin makaranta zan zama." yace da dukkan gaskiyarsa. Suna ta dariya Zainab ta dauko kudi ta bashi "kayi sauri ka siyo mana abinci tunda labe ya hana ku girki" Kwanan Radhiya biyu da yiwa gidan Ardo yaji tunda aka yi mata aski. Yaran dangi sa'aninta duk Emzee ya fesa musu sai ta wuni suna zuwa gidan tsokanarta. Na yau yafi bata haushi harda cire mata dankwali gashi Zakari dan gidan Baffa Habubakari da take hasashen yana son ta yana gidan. 'Yar yayarsa ce ta cire mata kullin maganin da take yi a kanta yanzu kunya ta isheta. Zakari sai ya rufe yarinyar da fada ya fita. Zaune take a daki tana kwafa don idan ta kamata sai jikinta ya fada mata, dazu ma albarkacin kawunta taci kada abin kunyar yayi yawa. Muryar Baffa Gide taji yana fada yana sanar da matarsa ya rasa taurin kan da yake damun Mairama. Maza sun fi biyar masu neman aurenta amma kowa yazo sai tace wai ita makauniya ce. Yayi iya kokarinsa ya samu makaho dan wani attajiri a cikin Giade mai mata biyu shine yaje ya sanar da ita ta watsa masa kasa a ido. "Na fuskanci yarinyar nan dama can fakewa take da makanta amma bata son yin aure" "To banda abinka Malam ku kyaleta mana." "Sai ta rayu babu aure? Yaran nan suna nasu auren fa zata soma jin shiru da kadaici. Ni gata nake son yi mata amma taki gani. Fitowa nayi na barta tana ta kuka" Hijabinta ta figo bayan ta gama jin bayanin Baffa Gide tace zata tafi gida. "Dena hararata ba kinji nace na barta tana kuka ba ni ban taba miki uwa ba" Iyalle matarsa ta soma dariya don fuskar Radhiya a hade take. " 'Yar soja a gaida gida" Tana zuwa gidan ko dakin Innawuro bata je ba ta tafi wurin Umminta. Hotuna ne a hannunta tana shafawa tana kuka. Babu mai sanin yanayin da zuciyarta take ciki sai wadda ta tsinci kanta a irin yanayin. Zayyan ya tafi ya barta kuma babu wani kwakkwaran bayani da zata kama taji salama a ranta game da mutuwarsa. Ko ranar da ya rasu bata sani ba sai kiyasin lokaci da aka bata. Saurin daga pillow tayi zata boye su da taji motsin mutum. Radhiya ta rigata ta hanyar karba tana kallon iyayenta a ranar bikinsu. "Ummi" Share hawayen take da sauri kafin ta fara tsareta da tambayoyi. "Meye, ba yaji kika yi mana ba mai kwal kwabo" Radhiya tayi dariya duk da ta tsani askin. Tana son farantawa mahaifiyarta. "Kaina yanzu fa yafi dadin wanka. Insa sabulu harda soso in dirje shi. Idan na shirya na mulke abina da man kwakwar da Yadikko ta bani wancan zuwan da mukayi Sumaila" "Da kike ishi mutane da kuka harda yaji" "Ba'a kyauta min bane...da kinga kan nan bazaki so ace nawa bane" A hankali sai ga Mairama tana dariyar shiriritar Radhiya. ********** Bayan kwana biyu da zuwan su Major Kano suka shirya harda su Zainab sai birnin Shehu. Da yake Zainab 'yar gari ce dadewa bata sa ta manta hanyar gidan ba. Sun so bata saboda gyare gyaren da aka samu kadan. Sojan da ake turowa kudi ya riga ya bar garin ma ta banki yake turawa MaiKudi kudin. Alhamdulillah gida ya cika da yara ko ta ina. Ibrahim yana tura Hadir gefensa Major ne yana fada masa dawowar Awwab nan da kwana goma. Matan ne suka fara shiga aka amsa musu. Sun gaisa Mami ta tambayi Jume wata yarinya ta nuna musu dakinta. "Fada mata abokan aikin marigayi ne da iyalansu suka zo" Yarinya ta ruga sai gasu sun fito tare Jume tana musu marhabin da lale. Tabarmi uku aka shimfida musu suka zauna aka gaisa. "Jama'a ina kuka shige duk shekarun nan ba'a jin duriyarku?" Kunya ta kamasu duk da kowa dai da nasa uzurin. Sun dan yiwa Jume bayanin da zata iya fahimta Major yana dariya yace "ina Alheran ne?" "Wai, 'Yar soja ai tana rugar Barkindo, da yake dai akwai bikin yayarta 'yar wajen Mubaraka nasan suna tafe in Allah Ya so" Kallon juna suka shiga yi sai Mami ta gyara tambayar "aka ce mana bayan Mairama tayi aure ita ta dawo nan wurinku" Itama nema suke su juya mata kai ta kwalawa Matar Badaru kira "kinji wai 'Yar soja suke cigiya ni duk ban fahimci zancen ba, nasan Badaru yana ciki turo min shi ya musu bayani." Tsayawa tayi suka gaisa sannan taje ta dawo tare da maigidanta. Shima ya gaisa dasu a mutumce Major yayi masa bayanin yadda suka yi da sojan da yake turo musu kudi akan cewa Mairama tana gidan miji, Radhiya kuma tana nan. Badaru ya rike baki abin da daure kai "Yallabai gaskiya ka binciki mutumin da yayi maka karairayin nan tun wuri" "Ban fahimceka ba" Mami da Zainab har sun fara damuwa ganin yadda iyalan gidan su ka canja fuska su ma. Badaru ya gyara zama ya soma yi musu bayani "zancen da nake muku Mairama tayi akalla shekara shida ko ma fi da makancewa, Radhiya da Zayyan kuma suna tare da ita a can wurin dangin babarta. Sai dai mutumci irin nata wallahi har ila yau tana turo mana yaran idan sun sami hutu" Kuka wiwi Zainab da Mami suke yi. Zuwa yanzu sai dai su ce sun ga jiya sun ga yau a auren soja. Makanta, yanzu ace Mairama ta makance babu ido. A sanyaye Major yace "ban tari numfashinka ba, wane Zayyan kake magana a kai?" Jume tace "Zayyanu karami kanin Radhiya" Mami ta zaro idanu "aka ce mana ta haihu jariri babu rai" A fusace Jume tace "wai uban waye ne da wadannan karairayin? Yarinya tana fama da lalura da rashin miji anbi an dabaibayeta da karya. Rashin waiwayarta da kuka yi yafi komai damunta, bata da masaniyar inda kowa yake cikinku gashi dangin ita mahaifiyar Zayyanu suma shiru rabonmu dasu tun sunan 'Yar soja" Zuciyar Major tuni ta kawo wuya ya daga waya zai kira dan sakon nasa sai ga Maikudi ikon Allah. Su Maikudi an karo wulakanci yana shiga yana fita duk wata yana jin 'yan chanjinsa a aljihu. Saboda son zuciya ma sai ya dena 'yar fafutukar da yake tunda dai albashin nan yana shigowa babu fashi. "Yauwa Maikudi gara da Allah Ya dawo da kai da yanzu." Idanunsa akan bakin ya kula akwai maiko a tare dasu "hee...hee baki muka yi a gidan ne. Sannunku da zuwa." Matarsa ya shiga kwalawa kira "ya naga babu ko 'yar mantina dinnan a gabansu? Wannan ai halin karanta ne. Waye nan a cikin yaran azo a nemo musu abin sha mai sanyi" Ran Jume ya fara baci tace "to dan ayi jikan na'isa, mu duk bamu iya ba sai kai. Ni zo ka jiye min baki ke neman Radhiya wai an fada musu a gidan nan take" A take kuzarinsa ya fara raguwa "ki fada musu inda take su je mana" "Mutanen nan fa abokan Marigayi ne, shi wannan yace ya dauki lokaci yana aiko da kudi kuma ance a gidannan ake karba" Badaru ya kara masa haske Abinka da munafuki gumi ya soma yi kamar an kwara masa ruwa "indai don Allah suke yi sai abar tone tone su sake mata kyautar tunda sun dawo. Ni bari na shiga ciki na gaji" Wani irin kallo Major da Hadir ke yi masa. Ashe Jume ma tasha jinin jizkinta. Ai kuwa bazata barshi ba indai haka ne. Kankace ido tayi ta kaurara murya "Maikudi kada kace min kana da masaniya akan maganar da mutanen nan suke yi" Ja da baya ya soma yi a tsorace "Ni kuma? Daga shigowata? Uhmm nayi nan akwai mai son ganina a waje" kafin su farga ya fice da sauri. Yau da ace Hadir na da lafiya Maikudi sai ya yabawa aya zakinta. Major ma tashi ne dai baiyi ba amma ko ciki daya suka fito da Zayyan sai ya nuna masa yayi kuskure. "Ku tashi mu tafi" yace dasu gabadaya. Jume tana kuka matan gida da Badaru suna salati suke basu hakuri. Babu alamun wasa a fuskarsa yace "Ku bani nambar waya da zamu nemi kwatancen inda Ummin Awwab take. Shi kuma wancan kafin na turo masu kama shi a fada masa nasan iya abinda na turo saboda haka ina bukatar kudin nan...da gaggawa" Ransa yayi matukar baci ne yaki amincewa da masaukin da Jume tace ayi musu a gidan. Giginya hotel suka yi masauki washegari sai ga Badaru da sassafe ya kira yace zaiyi musu rakiya har Rugar Barkindo. ********** Saboda yanayin matsanancin zafi da ake fama dashi yau gidan har Ardo suna zazzaune a karkashin katuwar darbejiyar da ta yiwa tsakar gidan inuwa suna taba hira. Yammaci ne na asabar Radhiya tasan cewa Zakari zai zo kawo wani sabon maganin ciwon ido da aka rubutawa Mairama a asibitin Bauchi inda yake aikin lab wato dakin gwaji. Gyaran nono ta gama wanda ta cire man shanu sannan ta je tayi wanka. Shiryawa tayi cikin riga da skirt ta saka hijabinta iya gwiwa don zuciyarta tana raya mata yau kawun nata zai fada mata abinda idanunta suke ganin yana boyewa...soyayyarta. Har kofar gidan Ardo aka rako su Major suka firfito kowa da nasa tunanin. A yayin da rayuwa tayi ta garasu ita Mairama kauye ta fado. Kauyen ma ruga da abubuwan cigaba suka yi mata karanci fiye da ko ina. Fitowarsu ke da wuya sai ga Emzee nan da wani abokinsa sun dawo daga kiwon shanun Ardo. Sanda ce a wuyansa amma shirt da dogon wando ya saka suna ta hirarsu ta samari. Ba Major da Hadir ba, hatta Mami da Zainab sai da gabansu ya fadi da ganinsa. Wannan banda haske babu ta inda zaka ce ya baro mahaifinsa. Kawunsa ya hango ya yi saurin barin abokinsa ya taho "Kawu Badaru yaushe ka iso" "Tare da bakin Umminku nake. Yi maza ka shiga kayi mana iso" Gaishe su yayi cikin gurbatacciyar hausarsu ta tsantsar fulani ya shiga ya fada musu. Mairama ta auna ta auno ta kasa gane su waye zasu zo nemanta tare da Badaru. Radhiya da ta tabbatar zuwan bakin zai hanata sakewa da Zakari ta shiga tura baki. Innawuro tace tayi shimfida sannan aka ce su shigo. Zainab da Mairama kowacce wai dakewa take yi kada suyi abin kunya a gaban 'ya'yansu amma da sauri suka shiga gidan. Mairama tana zaune akan tabarma ga sandarta a gefe ta yafa mayafi kalar kayanta. Daga bayanta kuwa babu tantama Alheran Radhiya ce wadda ganin 'yan gayu suna shigowa yasa ta manta da batun Zakari ta shiga washe baki. Mairama tana ji Innawuro tana yi musu barka da zuwa amma yaran kadai ke amsawa. Manyan kuwa Mairama suke kallo da take ta murmushi a hankali a zatonta babu mai ji tace "Ke su waye ne sai kamshi nake ji" Mami a gabanta ta zauna tana kuka ta kama hannunta da makanta bata hanata ayyuka irinsu yin fura ba da nata lallausan hannun. Zainab kuwa a gefenta ta zauna ta rungumo Mairama a jikinta. Rasa gane me yake faruwa ita da kowa na gidan suka yi. Radhiya da ta kurawa Major da Hadir idanu ta saki ihu kamar an tsunguleta. "Yasin Ummi na ganesu na hoton nan ne" Mami tasa hannu ta shafa fuskar Mairama tace "Ummin Awwab" Duk da bata gani sai da idanunta suka kara girma gabanta ya tsananta faduwa, baki na rawa tace "Mami??? Ke duba hotunan akwai wannan a ciki?" Ta fada tana kankame hannun Mami kamar zata kuma tafiya. "Ai shikenan tunda baki ce a duba dani ba" Zainab tayi maganar da wasa cikin kukan da yaci karfinta. Mairama fashewa kawai tayi da kuka su ukun suka rungume juna suna hawaye sauran jama'ar wurin suna tayasu mazansu da matansu. 💕[02/11 7:30 AM] 20💕 .Mairama ta ga gata da ya amsa sunan gata a Rugar Barkindo. 'Yan uwa ke tururuwar ganinta har ana fadan gidan wa zata zauna. Ardo yayi tsalle ya dire yace matarsa ce zata dauka ai ita ce mace. Dole sauran suka amince aka barwa Innawuro. Idan manya ko dattijai cikin danginsu sunzo sai ayi ta kallonta ana cewa kaza dinta irin na Mairo ne. Murmushi kawai take yi don ko hoton mahaifiyarta bata taba gani ba. Sun tausaya mata da jin labarin rasuwar mijinta ga makanta. Radhiya da Emzee sai gasu cikin 'yan uwa sa'anninsu ana ta nishadi. Abinci da nama anci an ture. Kafin sati ya zagayo jikinsu ya fara nuna kwanciyar hankali da koshi. Mairama kullum cikin godiya take ga Allah da Ya dawo mata da dangin mahaifiyarta. Ba jimawa sabo ya kullu sosai a tsakaninsu baki daya. So da tausayawa suke nuna mata da 'ya 'yanta. Ardo ke cewa su duka marayu ne ababen dubawa. Bata cuci kanta ba ta roki alfarmar su Radhiya su koma makaranta. Tare aka nema musu JSS 1 ita da Emzee da ya gama aji biyar. Ita a makarantar kwana ta gwamnatin jaha ta mata shi kuma jeka ka dawo ta maza. Ranar da dan gidan Baffa Habubakari ya kawo takardun tubure musu Radhiya tayi da kuka wai bata so. "Karatun kike yiwa haka Radhiya?" Innawuro tace tana kokarin bata baki. "Dama saboda bama cin abinci mu koshi ne fa Ummi ta kaini makaranta inyi kudi" Mairama kunya ta isheta tasa hannu tana nemanta "haka muka yi dake? Kuji min yarinya" "Da naga ko nama bama ci irin na gidan Baba Kallamu shine nayi zaton haka ne" ta mayar mata da amsa tana shure-shure. "Idan bata yi ba ai ba'a kirata jikar Ali ba" Innawuro tace tana dariya. Radhiya ta turo baki "Malamijo muke kiransa mu dai" "Ina yaga malanta sai bakar rowa da mammakon tsiya" "La la lahhhh baban Ummi ne fa" Ardo yana jinsu yana rubutu a jikin allo yace "da kyau 'yar albarka ki kare masa kinji ko. Duk tsiyar naka ai naka ne Innawuro" Dariya rigimar Radhiyan ke bata tace "kasan ni ba bakuwar zafi bace Allah Ya baki hakuri. Nima kizo na baki labarin 'yar uwata Mairo. Ga kyau ga kirki kamar wata dan daren goma sha hudu" Idanu Radhiya ta bude sosai da mamaki "wata dai irin na sama Innawuro?" "Akwai wata a kasa ne?" Mairama ta fada tana jin kamar ta mangareta. "Tabdi, Ummi kenan Innar taki a mulmule take kamar wata. Ga Malamijo kamar tsolon rake. Mu dai Allah Ya taimakemu ke daidai kike." Mairama ta fusata ta fara wawurarta "Karami dauko min yayarka ko ka janyo min ita. Yau tambotsan nata harda iyayena kuma" A guje ta tashi "Ardo don Allah ba Innawuro ce ta fada ba." Innawuro ta dauko muciya "bari na mulmule ki kema sai aji dadin kiranki jikarta" Hanyar waje tayi tana gudu wai ita gidan Malamijo zata koma. Mairama ta daure fuska "da ya fi miki mu ma mu huta. Kuma karatu ki ma fara shiri sai kinyi" Dawowa tayi da baya tana murza yatsan kafarta a cikin kasa tana tura baki "to don Allah ki kaini soja irin na babana indai kina so nayi karatu" Gaban Mairama ne ya fadi ba shiri sai ga hawaye. Innawuro da ta dauki abin wasa tana biyewa Radhiya ta shiga bata hakuri tasan bazai wuce mijinta ta tuna ba. Radhiya ma sai ta soma kuka tana cewa tayi hakuri zata yi karatun ko wanne ne. ********** Alheran Radhiya Zayyan Tureta irin fitinanun daliban nan ne marasa tsoro ga kin ji. Duk inda akace 'yan aji daya sunyi laifi to in sha Allahu Radhiya tana cikinsu. Kan kace kwabo tayi kaurin suna tsakanin dalibai da malamai. Kirikiri tace sunanta 'Yar soja haka babanta yake kiranta daga Mairama ta bata labari. Shikenan makaranta suka santa da wannan sunan. Anyi sa'a tana dan taba karatun babu laifi. Wata rana suna layin dibar ruwa suna ta hayaniya irin ta 'yan makaranta ta dage tana ta zuba. "Allah Ya kaimu siniya wallahi zan warwasa a makarantar nan. Duk wasu jiniya a lokacin sun shiga talatin a hannuna" Kawarta Ruqayya tace "ke 'Yar soja so kike yadda muke tsinewa su senior Jummai kema a tsine miki?" "Ke baki gane ba. Lokacin kannen su senior Jummai mai tafiyar agwagwa ne a makarantar. Ramuwa zan zauna yi" Wata tace "ai kuwa nima zan so, rannan fa kwai tace nayi mata a karkashin gadonta" Radhiya ta daka tsalle "inama nice wallahi, na samu na sassaka mata kashi mai waaaaaari" Dariya suke duniya sweet kampo sai ga senior Jummai ta taho da tafiyar catwalk dinta da su Radhiya suke yiwa lakabi da tafiyar agwagwa. Ta gama jinsu tsaf suna bayan ginin da famfon yake. Idonta ya kyallo mata ita sai kawai ta canja hirar amma saboda tsoro muryarta har rawa take yi. "Allah Yasa senior Jummai tace in zama daughter dinta a makarantar nan. Daga ranar wanki da debo ruwanta duka zan rinka yi" Sauran sai suka fara mamakin me take nufi tunda dai haduwa suka yi ana zaginta. Yadda tayi maganar ne idanu har sun ciko da hawaye yasa Jummai da sauran seniors din dariya. Kawayen Radhiya ciki ya duri ruwa. Ita kanta a tsorace take. Jummai ta dafa kafadarta kamar ta saki fitsari don tsoro sai ji tayi tace daga yau kada wani ya sake ko da aiken daughter dinta ne. Kowa yayi mamaki harda kawayenta tace Radhiya tana burgeta saboda ko me za'ayi mata sai ta aikata abinda tayi niya. Idanunta kawai zaka kalla kasan fitina da rigima suna dawainiya da ita. Wata kungiya da aka bude a makarantarsu SS wato School Soldiers a nan aka samu kanta. Da jikinta da zuciyarta take wannan aikin na kare hakkin dalibai. Gashi da kayan makarantarsu riga da zani ne amma an basu hula irin ta sojoji mai lankwashewar nan suna sakawa akan hijabansu. Radhiya jin kanta take kamar sojar gaske. An kamanta gaskiya da amana sannan an gurji seniors masu hana sababbin dalibai sakat. Idan kaji ana Officer 'Yar soja a makarantar zaka rantse wani babban soja ne saboda yadda ake shayin shiga tarkonta. Zaman SS shine babban jindadinta a makarantar. A haka aka yi karatun cikin ikon Allah tayi nasarar fita da credit bakwai. Emzee kuma duka taran ya haye. Sai dai ko kadan a yadda ilimin ya tabarbare bazaka hada makarantar gwamnati dake kauye da wadda take birni ba. *** Tana jin shigowarsa dakin nata tayi saurin rufe ido kamar mai bacci. Murmushi kawai yayi yana kada kai. Zainab bazata taba canjawa ba indai tare dashi ne. Shekarun da suka yi a matsayin ma'aurata bai sa ta canja komai daga yadda ta faro ba. Akan doguwar kujera irin ta hutawar nan ta dakin ya zauna sannan ya soma yi mata magana. "Tashi magana zamuyi" Kin motsawa tayi sai da taji yace bari ya hawo gadon ya tabbatar ko idonta biyu. Juyowa tayi a hankali tana jin kunyar ya gano karyarta. Bata son yadda take yiwa Musa amma zuciyarta ta kasa rissina. "Shawara nazo nema" "A wurina?" Ta tambaya mamaki yana bayyana a fuskarta. "Eh, aure nake son karawa sai dai na kasa tsayar da shawara akan na dawo da mamansu Aisha ko na auro wata daban" "To ni me kake so nace? Ka auri wadda tafi kwanta maka" Fuskarsa ta nuna ba haka yaso ba kuma shima bai boye ba yace "zan so kiyi min rigima irin wadda kowace mace take yiwa mijinta a lokacin da ya tashi yi mata kishiya" Cikin yanayin rashin damuwa don har ranta ita bata ga abin rigima ba tace "saboda me?" "Saboda nasan cewa ko yaya Zainab ta damu dani kamar yadda na damu da ita. Sai dai nafi kowa sanin zaman hakuri kike yi a gidan nan. Na tauyeki na hanaki walwala da jindadin zama da wanda kike so" An tabo inda yake mata kaikayi sai hawaye sharrr tana gogewa da bayan hannunta. Musa yana jin kukan har ransa amma yasan ba nasa bane na wani ne "kinyi hakuri sosai Zainab, naso ace mun haihu don in samu abinda zan cigaba da garkuwa dashi in ki rabuwa dake amma Allah bai kawo ba. Sai nace zan barki ko don su Aisha. Yanzu kuma gashi suna shirin aure nan da watanni kadan. Ina ganin kamar bani da sauran dalilin cigaba da zama sanadin kuncinki" Kukan Zainab sai ya koma mai sauti. Tana tausayin Musa bisa soyayyar da yake mata. Tayi iya yinta amma zuciyarta taki amsarsa a matsayin masoyi. "Kayi hakuri da dukkan bata maka da nake yi, zanyi kokarin gyarawa" Murmushi yayi mata yana mika mata takardar hannunsa "ni na gyara mana matsalar ina fata Allah Yasa nayi abinda ya dace. Zainab na sakeki saki daya" A gigice ta kalle shi hawayenta yana karuwa. Idan ya saketa fa kenan babu sauran shamaki tsakaninta da Hadir. A gaggauce ta bude takardar sai ta kula guda uku ne a hade da stapler. Daya takardar saki, daya check na miliyan biyu, dayar kuma takardar mallakar wani gida ne a Kano da ya saya mata dan madaidaici. Dago kai tayi sharbe da hawaye harda majina. Cikin nutsuwarsa yake magana daki-daki "tukwicin kulawar da Aisha da Anisa suka samu daga gareki ne. Bana son fada amma yabon gwani ya zama dole. A kanki na yarda ba sojoji bane kadai jaruman kasata harda matansu. Soyayyarki ga baban Ibrahim ita tafi komai kara miki kima a idanu na. Nayi zaton kudina zai sa ki manta da wanda yake talaka mai nakasa amma bakiyi ba. Kin so zama da mutumin da bautar kasa ta nakasa farincikinku domin cikar soyayya. Nagode da lokacinki da kika ara min muka zauna tare" Maganganun sunyi mata tsauri sun taba mata zuciya. Tashi yayi zai fita Zainab ta taho da sauri ta rungume shi tana kuka. Bata taba yi masa haka ba idan ba shi ya nema ba sai yau. "Allah Ya faranta maka fiye da yadda kayi min Abban Aisha. Ka yafe min duk laifukan da nayi maka a zamanmu tare" Dago kanta yayi kana ganin damuwa a cikin idanunsa "yanzu dai ki soma hada kayanki kafin na chanja shawara" Da hawayen take murmushi "nagode" "Nima nagode" yace ya sa kai ya fita yana jin a ransa kamar an sauke masa wani kaya mai nauyi. Ya dade yana tsoron hakkinta kada ya kama shi saboda son zuciyarsa yau Allah Ya bashi iko ya rabu da ita ba don yana so ba. Ajiyar zuciya ta saki bayan fitarsa ta mika godiyarta ga Allah sannan cike doki ta kira Ibrahim. Labaran tara na NTA ya kunnawa Hadir yana gefe game ya dauke masa hankali a wayar kiranta ya shigo. Murmushi yayi ya dauka. "Hello Mama" Hadir ya juyo ya kalle shi sai kuma ya dauke kai. Ina ma zai iya tambayar lafiyarta da yayi. Daga daya bangaren tace "Ibrahim yaya su Umma?" "Lafiya kalau, ya su Anti Anisa da Baba?" "Su ma lafiya kalau. Ibrahim nace me kake so gift din graduation ka ki fada min kamar wata surukar ka ko, na kula ko hira baka son yi dani" tayi karamar dariya. "Ina naga fuskar" yace a zuci. Ita da bata sakin jiki da kowa bare ayi batun hira. Daga gaisuwa sai ta fada kogin tunane tunanenta ta bar mutum zuru. Yana mamakin yadda idan yaje hutu take hira da su Anisa duk da ba wata hirar kirki suke yi ba. "Ya kayi shiru ne?" "To kiyi hakuri zan gyara" "Shikenan, ina babanka?" Hadir ya kalla suka hada ido. Anya Mama ce kuwa yace a ransa. Bata taba tambayarsa babansa ba sai su Umma kawai. Kara kashe shi tayi da wani mamakin ta hanyar cewa ya dora masa wayar a kunne "saura ka sani a speaker" Bai san lokacin da ya kwashe da dariya ba. Wai dama Mama ta iya wasa haka? Hankalin Hadir gabadaya yana gare shi sai kawai ya dora masa. Wani irin sanyi taji ya ratsa zuciyarta da taji sautin numfashinsa. Soyayyar da ta dade tana dannewa ce ta taso mata. Da suna tare yanzu shekararsu goma sha tara da aure. Cikin wani yanayi na shauki da begen da yake nuna soyayya bata tsufa tace "Hadir" Allah Sarki rayuwa, yaji sunan har tsakiyar kansa amma bazai iya amsa mata ba. "ASTAGFIRULLAH" tace da sauri ta katse wayar. Shaf ta manta cewa har yanzu tana karkashin Musa har sai ta gama iddah. Tashi tayi ta bude wardrobe ta dauko akwatunanta. Da safe Musa da kansa ya sanar da su Aisha cewa mamansu zata dawo sannan Antinsu Zainab zata tafi. Sun saba da ita sosai a hannunta suka girma. Tana kuka suna kuka har airport suka rakata. Motarta Musa yace zai bayar a kawo mata har gida. Tayi ta masa godiya da kyakkyawar addu'a ta shige jirgi zuwa garinsu tana mai fatan samun sauyin rayuwa mai dadi. ********** A firgice Rtd Major Mustapha ya tashi jike da gumi daga mafarkin da yake yawan yi wanda yake daga masa hankali ya shiga laluben kafar katakonsa. Mafarkin ya tsananta a gareshi tun bayan da suka sanya ranar komawa kasar haihuwarsu. Korido din da zai sada shi da kitchen ya nufa don ya sha ruwa ya hango Mami ta barbaza kaya a gabanta na tsaraba da take ta warewa tana saka sunaye. Kasa tafiya yayi duk motsinta yake bi da kallo. Wannan kyakkyawar matar kanwarsa ce, matarsa kuma uwar 'ya'yansa. Hakika a kullum baya gajiya da sanya Hassana cikin addu'o'insa domin ta cancanci fiye da haka. Tayi hakuri dashi iyakar hakuri musamman a lokutan da yake ganiyar ciwo har yakan nemi rayuwarta ba a cikin hayyacinsa ba. Tunanin kawai kan sa tsigar jikinsa tashi. Tabo uku ne a jikin Mami wanda suka samu a dalilin PTSD dinsa. Jikinta ya bata yana kallonta haka kawai, ta daga kai suka hada ido. Murmushi suka yiwa juna ya dawo falon ya zauna. "Me ya hanaki bacci shabiyu har ta wuce?" "Aikin nan yaki karewa Daddy. List din mutanen ma kamar bamu yi rabi ba" ta dan bata rai. "Ku kuma mata da baku da nutsuwa indai akan tsaraba ne ko" Tattara kayan ta soma yi gefe sannan ta dube shi "me ya tasheka ne?" Shirunsa ya fahimtar da ita komai. Kusa dashi taje ta zauna "nan da kwanaki goma in sha Allah muna gida. Muna kwana biyu an gama gaisawa da 'yan uwa babu inda zamu je sai wurin Ummin Awwab da Hadir. Lokaci yayi da zaka kore komai daga ranka ka rungumi kaddara." "Yes Ma" yace yana murmushi. Maida masa martanin murmushin tayi ita ma "Tashi muje mu kwanta kasan gobe is a big day" Suna kwance tuni Mami tayi bacci amma shi ya kasa sai rarraba dayan biyu yake. Ko yaya iyalin Zayyan? Allah Yasa suna cikin mafi kyaun yanayi. Sai kuma ya koma tunanin auren Zahra da Fauziyya da za'ayi nan da wata biyu. Kowaccensu tuni ta hada degree dinta. Hadi ne na gida zasu auri 'ya'yan 'yan uwa kamar yadda ya kusan zamewa danginsu al'ada. Har nan aka turo mazan suka daidaita kawunansu. Bai san lokacin da bacci yayi awon gaba dashi ba. Washegari kuwa banda shirin tafiyarsu da yaki karewa karfe bakwai na dare suka tasarma gidan da Mami take aiki. Major sanye yake sa suit sky blue da light grey din shirt a ciki. Yayi gyaran fuska yayi kyau yana rike da sandarsa da take taimakawa wurin rage masa rashin jindadin tafiya da kafar katako duk da ya saba yanzu. Mami, Zahra, Fauziyya da Zayyana duka abaya ne a jikinsu masu kyau kowacce tayi nadi da mayafin da ya dace. Party ne na bankwana iyalin Herr(Mr) da Frau(Mrs) Schmidt suka shiryawa Mami a matsayinta na shugabar ma'aikatan katon gidan. Sun matukar jindadin zama da ita tun lokacin da suka basu wuri a gidansu kafin daga baya su kama wani mai dan girma a waje. Iyalin babu abinda yasa suka likewa Mami kamar tsantsar tarbiyar da yaransu suke koyi da ita har a makarantunsu. Tarbiya ce irin ta musulunci batare da ta fito zahiri ta tallata musu addinin ba. A fakaice ta rinka kwadaita musu tana fatan wataran idan da rabo su karba. Farkon zuwanta sun so hanata zuwa da lullubi ko karamin hijab. A take tace ta bar aikin. To amma amanar da suke gani daga gareta yasa da kansu suka sake nemota. Aikin Mami a gidan yana daga cikin abinda Major bazai taba mantawa a rayuwarsa ba. Wai shi Mustapha da ya kai matakin Major a soja shine matarsa take aikatau. Abinda yafi karfi a kasarsu yazo lalura ta cinye komai nasa yafi karfinsa. Bashi da tamkarta a duk duniya. Ya amince samun kamarta sai wata matar sojan. Jarumar mace matar jarumin namiji. Katuwar harabar gidan tasha gyara da fitilu da flowers ko ina yana kyalli ga kayan abinci a gefe debi wanda kake so. 💕02/11 7:30 AM] 21💕 Duk dauriya irin ta Ardo sai da ya matse kwalla ganin yadda hatta mazan kowanne ido yayi jajir. Mairama ce ta fara magana cikinsu "ina Awwab dan Ummi? Nasan ya girma yanzu? Anyi masa aure ne?" Zahra tace "Mami ashe da gaske dai Ummin Hamma Awwab mu bata sonmu" Mairama sai dariya ta kufce mata ta daga hannuwa ta tashi tsaye tana cewa "Zahra, kece ko? Ina Fauziyya da Ibrahim abokin fadan wannan yarinyar?" Fauziyya da Zahra suka matso suna rike hannuwanta tace "kuji min yara yaushe zan ganeku da hannu kawai, haka ake yi" ta fada tana rungumesu. Muryar wata shagwababbiya da hausarta ke fita kamar mai waka saboda yadda yaren Germany da turanci ya kama mata baki taji tana cewa "Daddy ni kowa baya sona, she even asked for Hamma that is not here" Ibrahim kallonta yayi ya tabe baki, yarinya yar shekara sha hudu kamar yadda yaji Mami ta fada sai ta dage tana zuba tabara Daddynta yana biye mata. Emzee kuwa murmushi yayi bai ce mata komai ba. A gidan Ardo shine karami bai saba ganin haka ba shiyasa yadda tayi ya burge shi. Mairama sai ta sake dariya ta rasa ina zata kai farincikin da yake cikin zuciyarta. "Such a sweet voice, wace ce wannan?" Zayyana dadi ya mamayeta ance muryarta da dadi ta tafi da sauri ta ture Fauziyya da Zahra ta shige jikin Mairama tana cewa cikin tsantsar mamakin wannan 'yar kauyen "Daddy she speaks English too" Ibrahim ya kwalo idanu a hankali yace "ji min rainin wayo." Sai kuma suka tsinkayi Radhiya muryar tayi kicin-kicin da fuska tana kallon Zayyana "ke yarinya iya bakinki wallahi, Ummina ma 'yar boko ce har secondary ta gama ehe" "Zaki fara ko?" Mairama tace tana zaunawa har lokacin Zayyana na jikinta ba ta fahimci dogon zancen Radhiyan ba. "Ai gara na fada mata gaskiya tun wuri kada ganinki a kauye yasa ayi miki kallon wata local" Haba wuri sai ya kaure da dariya harda Major. Sai lokacin Mairama ta gama gane su waye a wurin kunya ta kamata. Halin Radhiya sai ita. Zainab tana cewa ta zo Mami ma tana kiranta sai ta rasa wurin wa zata je. Zainab tace "jeki dai dama ita ce mamanki, ni Zayyan zan dauka nafi kama da maman maza" Rufe fuska tayi da hannuwanta tana kallonsu a fakaice sai wani blushing take "wallahi kun sani jin kunya...duk sona kuke yi" Wata dariyar ta basu Mami ta janyo hannunta ta zauna a kusa da ita "haka kika koma Alheran din Awwab? Wannan idan na wuni dake cikina sai ya kulle" "Indai wannan ce baki ga komai ba" cewar Innawuro. Kowa a cikinsu yana cike da tsananin farinciki. 'Ya'yansu ma ko da basu gama sanin mahimmancin iyayen nasu a wurin juna ba sun amince wannan haduwa ta faranta ran iyayensu su ma dole su ji dadi. "Idan kun gama kukan da dariyar ya kamata a gaisa kuma haka" Ardo yace dasu don ya dakatar da zubar hawayen matan. Sai kuma aka soma gaisawa ana tambayar yaya bayan saduwa. Mairama ta fuskanci bangaren da take jin a nan su Major suke ta saki fuska. "Daddy ina fata duka kuna lafiya" "Lafiya kalau Ummin Awwab" yace a sanyaye. Dan bata rai tayi cikin wasa "abokinmu tun shigowarku banji ko tarinka ba, ai shikenan." Dif taji shiru ya rasa wurin babu mai cewa komai cikinsu. Hantar cikinta ta kada a sanyaye ta rike Zainab "ba dai....Subhanallahi, ba dai shima" Wani irin kuka Zainab ta saka tana jin ciwon lalurar Hadir har kokon ranta. Jikin Mairama ya gama saki ta sadakar kila shima babu rai. Radhiya da Emzee sun gane shine akan kujerar amma su din ma basu iya bata amsa ba. Major ne ya danyi gyaran murya ya soma maganar da kafin ya kai karshe wurin ya sake rikicewa. "Hadir gashi nan muna tare sai dai tsahon shekarun nan da bamu tare ya yi su ne da paralysis sannan baya iya magana." Sai da ta dan sami nutsuwa daga wannan tashin hankalin abinda yake ci mata rai shekara da shekaru ta kasa daurewa cikin karyewa da dashewar murya tace "uhmmm...uhmm nace babansu Karami. Kuna tare ya rasu ko?" Major da Hadir da dukkansu da suka san labarin abinda ya sami Zayyan daga bakin shi kowa gabansa ya fadi. Mairama da ba ganin fuskokinsu take yi ba ta cigaba da magana. "Ko baku san ya rasu ba ma?" "Mun sani Ummin Awwab, muna tare" Major ya amsa da sauri. Ajiyar zuciya tayi harda guntun murmushi "Alhamdulillahi, da hankalina ba karamin tashi yake ba da tunanin kila ba'ayi masa sutura kamar kowane Musulmi ba. Nace ko irin mutuwar nan ce ta su da yawa. Ance ramin kawai ake guda daya. " Major Mustapha shiru yayi ya rasa me zai fadawa wannan baiwar Allah. Allah ne ya cece shi a lokacin aka fara kiran sallar Magariba Ardo yace kowa ya tashi. Mazan waje suka tafi wurin masallacin da yake gefen gidan akwai butoci cike da ruwa. Ibrahim ya dauko daya ya duka a gaban Hadir zaiyi masa. Emzee yana tsaye a gefe yana ta kallonsa. "Za kayi masa?" Ibrahim ya tambaye shi yana murmushi. Murmushi Emzee yayi ya gyada kai. "Gashi" Ibrahim ya bashi butar. Emzee ya karba "ka tsaya ka rinka gani kada nayi ba daidai ba" Da taimakon Ibrahim din Emzee ya yiwa Hadir alwala. Kukan zuci yake yana murmushin zahiri. Yau dan Zayyan dinsa ne yake masa alwala. Bayan sun gama ya kuma cewa shi zai tura shi cikin masallacin. Dadi ya kama Ibrahim don ba karamin ji da babansa yake ba. Da suka idar da sallah ma Emzee din ne ya sake turo shi zuwa bakin kofar, Ibrahim sai ya tsaya daga waje ya kama kujerar suka daga shi sannan aka sauketa a kasa saboda tudun da yake wurin shigar. "Sunana Ibrahim Hadir" Takalminsa yake lalube wannan ya bawa Hadir damar ganin fuskarsa sosai yana murmushi tamkar an ajiye mahaifinsa a wurin. "Muhammad Zayyan Tureta" Wani dagen gira Ibrahim yayi "amma Zeezee naji ana ce maka ko?" Emzee mai wuyar sabo ya sami kansa da kwashewa da dariya "Zeezee kuma kamar wani mace, Emzee ne." Ibrahim sai yaji yana son zolayarsa "ni dai kafi min kama da Zeezee haka zan rinka kiranka" "To Surbajo babu damuwa" Hadir yana jinsu yana dariya a hankali musamman da ya ga Ibrahim yaji dadi yana cewa zai fadawa Umma kakarsa cewa yazo garin Fulani an saka masa suna irin nasu. Emzee ya gimtse dariyarsa suka koma gidan. Major ne karshen komawa ya tsaya amsa wayar Awwab da yake ta mita an tafi ba'a jira dawowarsa ba. "Idan kaso ranar da ka dawo a tare dasu zaka kwana babu mai hanaka" Daga daya bangaren Awwab yana kwance a dakinsa na hotel a Austria washegari goman dare zai sake wani trip din zuwa Germany ya shafi habarsa. "Duk dadin ya wuce yanzu. Kun hadu da Ummin?" "Muna rugarsu a Bauchi" Tashi yayi zaune da murnarsa "ta tuna ni Daddy?" "Kai ta fara tambaya" Wani sanyi yaji a ransa don Allah ne shaida bai taba mantawa dasu ba musamman ita Mairama mamansa ta biyu. Karshen haduwarsu ranar da duka su ukun suke ta kuka daga karshe ya gane halin da nasa mahaifin yake ciki. A wurinsa yaji rasuwar babansa Zayyan mutumin da yake matukar so. "Daddy Alheran fa?" "Ita ma baka manta da ita ba?" Dariya yayi, a shekara goma watanni ne babu tsakaninsu. Babban abinda yafi tunawa da ita shine fada da kuka. Sauran kuwa sai abinda Ummi ta bashi labari. Da kuma hotuna da ta nuna masa nasu lokacin suna tare. Tabon inda ta taba yakushinsa yayi dan siririn layi mai dan duhu daga gefen girarsa ya taba. "Ban manta ta ba Daddy. Ko za ka bawa Ummin waya?" "Ka kira ta Mami sai ta hadaku" ********** Duhun dare ya soma kawo rashin wuta ya sa aka kunna fitilun kwai guda uku aka ajiye a tsakar gidan. Bishiyar tana kada musu iska daidai gwargwado aka zauna mayar da zancen yadda kowa yayi rayuwarsa bayan rabuwa. Wannan karon Innawuro ce ta cewa yaran su tafi gidan Baffa Gide saboda kula da tayi hirar tasu mai taba zuciya ce. Radhiya tace su taho kowa ya tashi kamar gaske. Suna fita bakin kofar Zayyana tace da Fauziyya "nan gidan basu da wurin da zamu buya" "A buya kuma, kunyi gamo ne a hanya?" Radhiya ta tambaya tana waige. Murmushi Zahra tayi yanzu an girma suna jin kunya. Ibrahim kuwa sai yace "kinga magana zasuyi mai mahimmanci idan bamu tsaya munji ba wallahi za'ayi ba mu" Haba Radhiya ta rike tana jinjina kai "Allah ko? To amma zunubin laben wa za'a rubutawa a cikinmu? Ni dai shekarata goma sha tara da sauran kuruciyata." Fauziya da Zahra har Ibrahim sai dariya. Emzee da ya saba shi kam bai ga komai ba. Salati suka ji Inmawuro tayi da karfi tana kuka gabadayansu babu babba babu yaro suka dawo suka tsaya a siririyar hanyar karasa shiga cikin gidan. Duhu da girman maganganun suka hana a gano su. Duk da sun ji yadda iyalin Major da na Hadir suka kare a Kano bai hanasu sake kokawa iyayensu ba. Jin labarin da Mairama ta bayar a karon farko a rayuwarta ta fadi yanayin zaman gidan mahaifinta. Tayi haka ba don ta tona masa asiri ba sai don su Mami su fahimci ainihin yadda al'amura suka kasance mata. Ga wanda bai san Malamijo ba sai a suna bazaka taba hangowa jikokinsa ma talauci da kuncin rayuwa ba. Dabbobinsa tarin arziki ne da shi kansa bai san dashi ba. Ko shanu ashirin ya sayar a yadda suke da girma kosassu zai iya ajiye abincin shekara a gidansa kuma su wadata da abubuwa da dama da bai taba tunanin ya basu ba. "Abinda ban fahimta ba Ummin Awwab shin gidan da Zayyan ya gina a Kano me ya faru dashi?" Major ya tambayeta Jan numfashi Hadir yayi da karfi sai da suka kalle shi. Rashin damar bawa Mairama takardun nan kusan shine ya haddasa masa hawan jini. Bai ma san ko Zayyan ya bata na wurinsa ba. Shi dai burinsa wadda aka bashi ajiya ya sadar da ita ga masu hakkinta. Takardun suna cikin wani akwatinsa da yake tunanin babu wanda ya taba bude shi tunda ya koma gida. A nutse ta warware musu komai da ya wakana tsakaninta da Maikudi. Kunya kuwa ta kama Badaru kamar ya bace daga wurin saboda abinda yayansa ya aikawa matar kaninsu. Major rai ya kara baci ba don duhu ba sai an ga jijiyoyin kansa da suka dago. Mami tace "Wallahi mutumin nan sai munyi da gaske. Ta kowace fuska da zai toshe miki jindadi sai da yabi. Mu fa aure yace kinyi kuma baki haifi dan cikinki da rai ba sannan Radhiya tana hannunsa shine muke aikata mata kudin makaranta ta hannunsa" "Banten uba" Radhiya tace a harzuke tana kumfar baka daga inda suke tsaye. Hanyar shiga ciki tayi Emzee da Zahra suka rikota. Idanu sun rufe ta shiga kokawar fuzgewa "ku cikani" Zainab suka gani a gabansu suna sunkuyar da kai kasa tace duk su dawo su zauna tunda annobar labe ta kamasu. "Ban hanaki wannan zagin ba" Mairama tace da Radhiya cikin fada. "Ai wallahi Ummi sai dai fa kiyi hakuri yau daya dai. Hmmm gaya miki ne banyi ba da idan munje hutu fa duk inda ya ganni sai ya rankwasheni ko ya makeni. Inata hakuri, inata hakuri. Wata rana yana rankwashina na tafi a gabansa na dauki Bushira lokacin tana karama na maka ta da kasa. Shine fa ya dena dukana. Yo ashe harda ke bai kyale ba" "Ya isa haka Radhiya kiyi hakuri tunda magana ta fito ba zamu bar masa hakkin marayu ba" Mami tace da sigar lallashi. "Uhmhum" kawai ta amsa ba don ta hakura ba. Badaru ya ari baki ya basu hakuri sannan ya kara da cewa "dole ne na sake neman su mutanen Nijar din. Bana yi musu zaton wadanda rasuwar Zayyan zata sanya su watsar da iyalinsa. Allah Yasa su din ma ba wani abin yaje ya fada musu ba. Don ni yanzu lamarin nasa ya fara bani tsoro kuma." Sunje sunyi sallar isha sun dawo sai ga yara biyar suka shigo gidan a tare rike da kwanukan abinci. Biyu yaran babban dan Innawuro ne sauran ukun kuma na mai binsa mace. Tun a masallaci lokacin Magariba Ardo ya sanar da dan nasa da kuma mijin 'yar suna da baki ayi abinci na gani na fada. Farantai da cokula Radhiya ta dauko sai ruwan sanyi da aka aiki Emzee ya siyo a wani shago daga bakin titi Ibrahim ya bishi. Anci an sha hira taki karewa Innawuro ta sa Radhiya da Emzee tayata gyaran dakunan saukar baki. Su Mami da ko baa fada ba da Mairama zasu kwana. Badaru, Major da Hadir Baffa Gide yazo ya tafi dasu gidansa. Ibrahim da Emzee a dakin Emzee din da yake daga hanyar waje. Sai 'yan matan su hudu a dakin Innawuro. Dreban da ya kawo su shima an sama masa masauki. Da asuba kaji goma aka yanka domin yi musu abincin safe. A gaban Hadir Major ya fadawa su Baffa da Ardo cewar auren su Zahra ya matsu suna neman izini su tafi da su Mairama zuwa bayan biki. Radhiya da Zayyan kuma a bar masa su zai nema musu makaranta su fara jami'a a. "A yi haka kuwa?" Baffa Gide yace yana kallon Ardo "a son ranmu dai suyi zamansu da yaran a tare damu har Allah Yasa duka suyi aure." "Abinda baffanta Gide ya fada gaskiya ne. Ita ga matsalar idanu ga marayunta gara suna tare damu. Lokaci lokaci idan kun bukaci su zo su kwanan muku biyu sai a turo su" Ransa dama ya bashi da wahala kai tsaye su bari ya daukesu. Sai dai kam yaci alwashin bazai yarda alkawarin da ya daukarwa kansa na cigaba da kula da bayan Zayyan ya tashi ba. Sauran labarin da ya kasa bayyanawa jiya na ainihin yadda Zayyan ya rasu ya fada musu. Baffa Habubakari sai da yayi kuka don tausayi. Cikin damuwa da fami ga gyambon zuciyarsa yace "Bazan taba iya kallon idanun matarsa in bata wannan mummunan labari ba. Tana da hakuri amma ina ganin sai ta tsaneni da iyalina. Yau da nake raye ku ke ganina Allah ne Yayi da sauran kwana na amma Zayyan shine sila." Ya nuna Hadir "wannan bawan Allah da lafiya kalau yake wallahi kunji na rantse zaiyi komai don ganin 'ya'yan Zayyan sun koma karkashin kulawarsa. Sai dai shima lalura ta same shi ne da ya cigaba da kokarin kare rayuwata kamar yadda dan uwansa ya fara. Ku taimaka ku barni na kyautatawa bayan Zayyan sannan kuma na saukewa Hadir nauyin da nasan da yana da lafiya bazai taba bari na dauka ba" Jikkunansu sunyi sanyi da maganganun Major. Ardo ya kira Innawuro yace "kece uwar Mairama kakar 'ya'yanta me zaki ce game da batun da bawan Allahn nan yazo dashi?" Nazari Innawuro ta soma don abun da yake nema ba karami bane. Mairaman da mahaifinta ya gagara rikewa, dan uwan tsohon mijinta ya tozarta ta yaya zasuyi saurin amincewa bare. Idan a gaba gori ya taso ko wani abu makamancinsa fa. Bafillatani duk talaucinsa akwai pride. Basa son zubar da mutumcinsu gaban kowa saboda babu azo aji dadin takasu. "To na amince amma Zayyanu kadai zaku dauka. Dalili kuwa kun dai ga irin halin 'Yar Soja wallahi zama da ita akwai dadi akwai wuya. Mairama kuwa bana son nisa da 'yata ko kadan." Hadir ya kafe Major da ido har ya fahimci so yake ya cigaba da rokonsu. Ai kuwa bai fasa ba yana ta kawo hujjoji. "Kayi hakuri amma indai ka ga 'Yar soja ta bar garin nan to aure ne ya dauketa" Innawuro tace don ta kawo karshen muhawarar. "Na ji na amince" Major ya amsa batare da dogon nazari ba. Baffa Gide ya kalle shi da mamaki "kada kace min aurenta zakayi." Mafita daya ya hango ya kuwa yi amfani da ita "a'a , akwai babban dana Awwab shine nake son aurawa. Dreban jirgin sama ne yana bakin aiki shiyasa bamu zo tare ba." "Lallai da gaske kake, amma bana so ka cuci yaronka da auren dole don a baka yarinya. Kasan yanayin zamani" "Na sani amma ina da yakinin bazai bani kunya ba. Don Allah ku amince. Yanzu ku bari mu tafi dasu har Sakkwato saboda wancan wan Zayyan din. Sai kuma danginsu na uwa dake Nijar su ma ina so na hadasu kafin nan da lokacin bikin" Tsakaninsu da Allah basu da niyar hana shi yaran ko kadan sai dai magana ta gaskiya sunyi masa haka ne domin kada nan gaba a raina musu. Da mutumcinsu da rufin asirinsu ya nemi daukar yaran ba wai talauci ko maula ya kaisu ba. Sun kara jinjinawa Marigayi Zayyan domin wannan abu halinsa na kwarai ne ya kawo haka. Idan akwai wani abu na bajinta a rayuwar Mairama da Malamijo ya taba yi bai wuce aura mata dan kwarai irin albarka Zayyan Muhammad Tureta ba. Innawuro da kanta ta fada musu su hada kaya zasu tafi tare suyi musu kwanaki don kowa ya sani hirar jiya da wadda aka sake dorawa yau tayi kadan ta cike gurbin shekarun da suka yi basa tare. Radhiya sai murna nan da nan ta shiga jibgar kaya. Zainab ta ja ta gefe tace mata ta debi kamar biyar biyar nata da na Mairama. "Ni fa na zaci kuna sonmu ne sosai baza ku so muyi kwana kadan ba mu dawo" Tunda suka farka suke cin dariyar Radhiya ashe abin bai kare ba. "Mu kuwa muke son ku Radhiya, ko nima 'Yar sojan zan fara fada ne"z Turo baki tayi "to meyasa kika ce na debi kayan 'yan kadan?" "Kinga muna zuwa zan sa a kaiku wurin tela ayi muku dinkuna masu kyau. Ko da wadannan kayan zaki je bikin Zahra da Fauziyya da za'ayi karshen wata mai zuwa?" Dariya Radhiya tayi kumatunta na dama ya lotsa. "To gidan wa zamu fara zuwa?" "Gidana mana" Mami da take tahowa daga bayansu ta rike baki "sannu maman yara, ashe wayo kike shirin yi min. To ban yarda ba Katsina zamu wuce" Zainab ta mairaice "habaaa Mami, mu da zamu zo biki muyi kwanaki. Ki bari a ya da zango a Kano don Allah" Mairama suka tambaya ina take son fara zuwa tayi murmushi "duk inda mota ta fara tsayawa zan sauka ne." Ta kashe bakin nasu ta barsu da muhawararsu. Wayar Mami aka kira tana dubawa ta ga Awwab ne. Dariya tayi don jiya yayi ta kira bata sani ba. Tana dagawa a kunnen Mairama ta manna wayar. Ko gaisuwa baiyi ba ya fara mita "Kai Mami tun jiya nake kira ki bani Ummi mu gaisa kinki dauka." "To Allah Ya huci zuciyarka dan Ummi" "La ila ha illallahu Ummi kece?" yace yana mai farincikin sake jin muryarta. "Nice Awwab, yaya aiki?" "Lafiya kalau, kinga sun taho sun barni ko" "Kayi hakuri, kana dawowa zaka ganmu in sha Allah" "Ummi ina Alheran?" "Tana can wurinsu Zahra tana damunsu da surutu" Dariya yayi yana imagining yaya ta koma yanzu "ta dena fada ko?" "Awwab kenan baka manta halin nata ba ashe. Sai kazo zaka ganewa kanka." "To Ummi don Allah kice Mami ta turo min numbar da zan rinka samunki. Ki gaishe min da Alheran" Mami ta bawa wayar ya shiga tambayarta wai yaya girman Alheran yake yanzu don tsaraba yake son yi musu ita da Umminsa, Anti Zainab da Ibrahim. "Kai kana fa da wani kanin Zayyan sunansa. Dama mun rabu Ummin taka ta kusa haihuwa" Mamaki da jindadi suka baibaye shi nan yayi musu sallama zai fita. Suma aka gama shiri suka rankaya sai Katsinan Dikko. ********** Mairama ta rasa wa zata goyi baya tsakanin Mami da Zainab. Gobe su Zainab zasu koma Kano bayan sun zo sunyi kwanaki uku a Katsina. Gidan kullum cikin hayaniya yake sun taru sun gama gyara shi an saka komai a muhallinsa. "Gaskiya Mami wannan fa amfani da girmanki kike yi kina yi min wayo. Ki bar min 'yan matan nan muje suyi sati. Aure fa zasu yi ina ni ina sake cewa su zo su kwanar min" "Ai ban hanaki ba, Radhiya ce na hana" "Ummin Awwab kice wani abu mana" "Ni ban san yaushe kuka koma haka ba. Ina nan bacci zanyi wadda tayi nasara ta tasheni. Idan zama ne na zauna. Idan kuma Kano ce tayi kira a hada min kaya" Dariya ta basu daga baya dai an yanke Zainab zata tafi da 'yan mata kuma mazan ma ko don Hadir dole su bita. Mairama ce zata rage tare da Mami. Taron mata ne a kitchen su Zahra na girki Radhiya na koyo. "Kunsan nima mai aikacin asibiti zan aura a Bauchi zan zauna. Gara na koya kada aji kunya wata rana" Emzee da yake shan ruwa sai da ya kware da yaji me take cewa "Adda saurayi gareki bamu sani ba?" Daure fuska tayi zai bata kunya a gaban mutane "fata nagari lamiri yaro...meye aibu don nayi fatan auren likita?" Ibrahim ya rinka mata wani kallo kafin yasa dariya "na gama harbo jirgin naki. Wato dai wani ma aikacin asibiti kike so" "Hhhhhh Adda Kawu Zakari kike so hala? Shi kadai na sani a asibiti" Yadda tayi da fuska ya karasa fallasata. Suka taru ana tsokanarta, Emzee yace wannan labari duk rugar Barkindo sai ya tona. Tun tana da bakin ramawa ta gaji ta watsar ta fita ta koma daki. Zayyana ta samu tana busar da gashinta da ta wanke da hand dryer. Sai ta dena fushin hankalinta yayi gaba. "Shi kuma wannan ya sunansa Zayyana?" "Hand dryer, kema ki wanke kanki sai na busar miki. Mai kitso zata zo an turota daga gidan Alh Baba" Tsit Radhiya tayi kamar ruwa ya cinyeta. Zayyana tayi tayi tace bazata wanke ba kanta babu datti. Da su Fauziyya suka shigo Zayyana ta fada musu. Radhiya ta galla mata harara "kinga ki fita idona, ina ruwanki don naki wankewa ba kaina bane?" Zayyana ta mike a fusace ta fita "kuma sai na fadaki da Daddy" "Sannu shasshaka uwar narkewa, shagwabar nan nima na iya. Kuma bazan wanke kan ba" "Dama masu gashi bakwa son bude kai fa. Shiyasa kullum kina cikin hijabi" inji Fauziyya. Zayyana kuwa tana kai karar Radhiya wurin Daddy ashe Mairama ta jiyo yana cewa a fada mata yace ta wanke shi zai bada kudin kitson. Idan kuma taki wankewa a gida zai bada kudin salon. "Daddy fada fa zaka yi mata, kara na kawo" "Yi hakuri Zayyana ai ko ni bazan taba Alheran ba." Harda guntun hawayenta tace "kafi sonta akaina" Ibrahim yana gefensu yace "Daddy ka barni na dan saita yarinyar nan mana." "Taron dangi zaku yiwa auta. To a kira min Alheran yau sai an wanke kan nan" Mairama tana ji ta tabo Mami "taimaka ki hana wankin kan nan wallahi idan suka bude mata kai gidan nan yau ba lafiya" Mami ta tashi da sauri duk da bata san ko meye matsalar ba. Tana zuwa Zayyana ta kai rahoton Daddy. Dama su Zahra sun matsu su ga gashinta saboda na Mairama da suke gani mai tsaho sosai. Duk sun dauki abin nata wasa suka danneta aka cire dankwalin suna cewa yau sai sun ga gashin da take boyewa. ********** Shiri Awwab yake da sauri sauri yau kadai yake da damar fita yayi sayayyar da zaiyi gobe ya taho Nigeria. Tun dare yake tunanin me zai saya ya kai musu ya rasa. Ba sabawa yayi da irin wannan abubuwan na mata yayi ba. Dan tunani yayi ya dauki waya ya kira wadda yasan za ta bashi shawara mai kyau. Ringing biyu ta dauka kamar jira take dama. A shagwabe ta soma magana tana korafin rashin kiranta da yayi har na kwana biyu. "Sorry my G aiki ne" "Lokacin aiki daban nawa ma daban" Ghazalatu ta sake narke masa. "Naji nayi laifi shiyasa ma ticket din Abuja na saya don na fara ganinki kafin na wuce gida" Ihun da tayi sai da ya cire wayar daga kunnensa yana dariya. Yana matukar son Ghazalatu. Ita ta nemi su boye soyayyarsu ma sai ta gama degree dinta idan ba haka ba aure za'ayi mata a gida ta sani. Yanzu wata biyu da yin final exam bautar kasa take jira. Sun gama tsarinsu idan Awwab ya dawo zasu gabatarwa da iyayensu da abinda ke tsakaninsu. Sun taba hira don ta dena fushin tunda taji zai taho washegari. "G albishirinki" "Goro kyakkyawa kamar Yayana" "Su Mami sun je gidan Ummin nan nawa da nake baki labari" Yadda taji yana murna dole ta taya shi ba don ta damu ba. Yayi ta fada mata ashe harda kani an yiwa Alheran. "Na tayaka murna, zan so ganinta gaskiya" "Ki bini Katsina mana idan na zo" Dadi taji tayi saurin amincewa. Awwab bai kyaleta ba yace "kune sarakan tsaraba, me kike ganin zai dace da yarinya about 18 to 19 years" "Friend kayi mace har kake fada min za kayi mata siyayya?" Tace cikin fushi da kishi. "Nope, Alheran nake son sayawa wani abu" Duk da haka ranta baiyi mata dadi ba amma bata son bata masa rai yanzu sai yace ya fasa tsayawa a Abujan. "Ka saya mata takalmi, jaka, turare, kayan kwalliya da jewelleries" Yaji kayan da yawa to amma so yake ya yi musu abin bajinta "thanks dear" yace da Ghazalatu kafin ya ajiye wayar. 💕[02/11 7:30 : 22. 💕 Iyakar karfinta tasa suna jan hijabin nata su ma suna ja. Mami na isowa tace su dagata amma an makara don Zahra tayi nasarar cire dankwalin. Emzee da Ibrahim suna bakin kofa don sun jiyo hayaniya daga dakin. Rasa me bakin magana akayi harda Mami kuwa. Zainab ce ta kawo Mairama dakin, tunda taji shiru tasan aikin gama ya gama. Zayyana ce ta fara dariya gashi ya soma lekowa amma saboda makero baifi a kirga ba sai wani uban fari fari kamar amosani kamar kora. Kullum tana shafa mai idan tayi wanka amma yau saboda da mutane a dakin ta hakura ta daure kayanta. Kowa ta kalla gimtse dariya yake ta harzuka sosai tayi kan Zahra tana ihu "wallahi sai na rama" "KE! Samu wuri ki zauna kada naji kinyi fada da kowa." Kuka ta fashe dashi da karfi "wallahi Ummi kada ki cuceni ki barni na rama." "Zahra bata dankwalinta kafin na saba muku. Wane irin abu ne haka da girmanku saboda Allah." Mami ta soma fada. Jefa mata dankwalin Zahra tayi don yadda take kallonta kamar kura ta ga nama bazata so hannunsu ya gogi na juna ba. Jikinsu sai yayi sanyi saboda kukan da take yi ta dauki dankwalinta ta kulle kan sannan ta mayar da hijabinta. Zainab da Mami na bata hakuri taki kula kowa sai sautin kuka da take karawa. Mairama tace su kyaleta ba shiru zata yi ba. Kowa ya fita daga dakin tana zaune tana kukanta dole Mami taje ta fadawa Major. "A kirawo min ita" Zahra ta kalli Fauziyya, a, tsorace tace "ba dai ni ba, kece babba kuma ke kika bude mata kan" "Zayyana...." Zahra ta soma kira ta bari saboda kyabe fuskar da ta ga tayi ta koma gefen Major tana cewa "Daddy kace bazani ba" "Mazaje waye zai kira min 'yata?" Yace da Ibrahim da Emzee kamar yana rokonsu. Ibrahim ne ya tashi, Emzee kamar ruwa ya cinye shi. Yana zuwa ya sameta ta gama hada kayanta a cikin jakar da tazo da ita tana bakin kofa zata fito. "Dariya ka dawo yi?" "Daddy ne yake kiranki" Gani tayi ya tsaya kallonta yaki tafiya ta zaro masa idanu "in sake bude maka ka gani da kyau ne?" Murmushi yayi mata kawai don idan ya sake ya bude baki sai ta saka shi dariyar da baiyi niyya ba. Sai yanzu ya gane meyasa kan nata yake kullum a daure kamar mai tallan magani. Da jakarta a hannu ta shiga su Zahra suka fara kuskus. Daddy ya gani sai ya shareta "waye ya saka ki kuka?" Rage tsayi tayi bakin nan a gaba kowa ya ganta yasan an tabota karshe "Daddy na san komai fa, kaine da kanka ka turo Zayyana su gane min aski na" Kafin su shigo sai da Mami ta roke shi akan ya taimaka kada yayi dariya. An san soja da dakiya, amma a cikin iyalansu, iyalan ma na Zayyanunsa mantawa yake ya taba zama soja. Ya fi fahimtar ya sake tare dasu ya nuna musu shi uba ne a garesu domin kada a sami wani shamaki tsakaninsu. "Cewa nayi ace ki wanke kanki fa 'Yar soja uwar sojoji" Sai da tayi murmushin jindadin kirarin ta sake daurewa "a bani kudin mota in tafi gida ko kuma a barni na rama" "Radhiya kiyi hakuri da kaina zanyi punishing dinsu. Amma ki bar zancen ramuwa ko tafiya gida" Mami tace tana hararar bangaren da su Zahra suke. Kumbura baki tayi "ni dai wallahi sai dai a zabi daya" Mairama taji kunyar kada a fara ganin ko harda sakacin tarbiya a halayen Radhiya. Fada ta soma yi mata tace ta tashi ta koma ciki ta zauna. "Allah Yasa naji kinyi fada da wani, zaki ga yadda zanyi dake. Ana lallabaki kina wani botsarewa mutane" "Laifinsu ne fa ki kyaleta, zo nan kinji Radhiya" Kin tashi tayi tana kallon Zainab din tace "kema Mama na ga kamar kin danyi dariya da aka bude kan" Mairama ta sake fusata Daddy yace duk suyi hakuri laifinsa ne amma tayi hakuri. "Ku kuma manyan ku daku kuna tsokanarta na kusa bata kambun girma a gidan nan. Kwanannan zata zama yayar kowa da kowa a cikinku sai na ga wanda zai sake gane mata askinta" murmushi yayi amma bata ji haushi ba tunda ya yi mata alkawarin zata zama yayar kowa. Da yake ba riko gareta ba sai ta saki fuska ta harari wannan ta harari wancan "kun dai ji me Daddy yace, kuma daga nan ma soja zai kaini abuna. Hahaha idan na dawo gidan nan za'a ga kawuna" Zayyana sai tasa hannu ta rike nata kan tana kallonta a tsorace "yanke mana kai zaki yi?" "Inaaa yarinya kan Balotelli zanyi muku in huce haushin yau" Ibrahim ya tuntsire da dariya harda fadowa daga kan kujera. Zainab ta daka masa duka a baya ko a jikinsa sai dariya yake "zan rike miki su 'yar uwa, ai dai baki ganni ina dariya ba" Major ma dariyar yake yadda ta hakikance abinta. Sauran matan babu wadda ta damu da ball ko 'yan ball balle su fahimci me take nufi da Balotelli din. Hakuri dai yayi ta bata tana kara jaddada masa burinta na zama soja tunda ta ga yana lallabata. "Soja mai babban mukami zanyi miki amma ta cikin gida, yanzu dai ku tashi amma idan kun shiga ciki kada ki kula kowa" "Daddy gaba fa kenan?" Tace tana ware idanunta ta rike haba. Su Zainab sai dariya, Major ya dage yana ta bayanin cewa ba gaba yake nufi ba. Kada ta kula su dai azo ana rigima. "Au ho...ai na hakura tunda idan na dawo daga soja zan dauki mataki. Baba zanyi kyau da soja ko?" Tace tana kallon Hadir. Kai ya gyada mata yana murmushi. Hannunsa taje ta rike tana durkushe a gabansa ita dai tana son sa sosai, sai da Daddy yace ta bi bayan 'yan uwanta zaiyi magana da iyayenta ta fita. Da taje dakin daga bakin kofa ta wulla jakarta ciki sai gasu suna darewa da sauri don ba karamin tsoro ta basu ba. Wata shu'umar dariya tayi wani abu ma sai an dawo daga makarantar sojoji. Babu wadda ta tanka mata ta shigo ta haye gado ta kwanta. Wayar Zahra aka kira ashe Awwab ne ya ya tambayeta size din takalmin Radhiya saboda yasan suna gidan. Kintata kawai tayi ta fada masa saboda ita dai bazata tambayeta ba a yau dai sannan a gabanta bazata taba mata takalmi ba don tsoron me zai faru take ji. A falon Daddy kuwa bayan fitarsu Mairama ta shiga basu hakurin halayyar Radhiya. Gani take kamar laifinta ne ko sakacin tarbiya ne ya kawo hakan. "Kowane da da irin halayensa da dabi'u da ake haihuwarsa dashi. Kuma yadda take dinnan Allah kadai Yasan wace irin tarin baiwa Yayi mata. Ki dena damun kaki watarana zaki ga kamar ba'ayi ba" Mami ce da wannan dogon jawabi sauran suna gyada kai. Daddy ya bijoro musu da zancen da sukayi da su Ardo. "Hada Awwab da kanwarsa abu ne da na kudurta tun ranar da na dora ido a kanta. Hadir ya amince ina fata Allah Yasa ku ma ku bani goyon baya" Gabadaya matan nan uku bakunansu murmushin jindadi suke nunawa. Mami tana maraba da wannan hadin domin bazata taba kyamar tsatson Mairama da Zayyan ba. Tafi kowa sanin mahimmancin yin hakan a wurin mijinta. Zai kara sakawa yaji a ransa cewa bai ya da iyalan Zayyan din ba. Ya so Zayyan tun basu saba ba duk ranar da suka je training zata kwana yana bata labarin fitinannen basakkwacen nan. Lokaci kalilan ne Radhiya zata waye tayi zarra cikin sa'anni. Zainab ma taji dadi don burinta su hadu su baiwa Mairama da 'ya'yanta dukkan farincikin da suka rasa. Allah Ya sani ba don sa'anni suke da Ibrahim har ta bashi watanni ba itama da zata so hadasu ne. Farincikin Mairama yafi na kowa. Wadannan mutane masu dimbin karamci a gareta ace babu kyamar yadda su suka kara wayewa ita da 'ya'yanta suka sake ci baya ta fannin wayewa da sanin ababen rayuwa amma su nemi hada Radhiya da Awwab, Awwab dinta dai wanda ya mayar da ita da mijinta iyaye tun farkon haduwarsu. Hawaye ta shiga yi tana mika godiya garesu. "Bani da bakin godiya, Zainab kunji wani karamcin kuma?" "Idan kina haka sai mu ga kamar a wurinka Radhiya da Zayyan ba namu bane Ummin Awwab" "Haba Mami kada kice haka mana, farinciki ne kawai yayi min yawa" Mami ta tambayi Major "yaushe kake tunanin auren?" "Kuna ganin zamu iya hadawa da na su Zahra? Idan hakan yayi in sha Allahu karshen sati Alh Baba zai dawo daga Umara sai na fada masa" To waye ma zaice baiyi na'am da wannan hadi ba. Bakinsu duk yazo daya, abu guda ya rage a sanar da Alh Baba sai ayi shiri aje a nemi aurenta wurin wadanda ya dace wato dangin mahaifinta na Sakkwato da kuma marikanta ta bangaren uwa su Ardo Barkindo. ********** "Banza jaka bace min da gani ko inyi kwallo dake. Har yau ina tsananin mamakin yadda akayi na kwaso ki Salame" Janye tsumman jikinta tayi da ya gama karewa ya tsotse babu wani tudu a jikinta bayan cikin jikinta na wata shida. Gabadaya ta mokade baka ce Salame bace da tauraruwarta ta taba haskawa a gidan Salisu. Aure dududu bai wuce shekara takwas ba amma haihuwarta biyar ga cikin na shida. Da kyar take tafiya yunwa ta yiwa hanjinta mugun lahani ga yara tun asuba suke kira mata yunwa suna kuka. Ba ta daddara ba ta sake hada hannuwa a gaban Alh Indararo "Alhaji ko naira hamsin ce ka bani don Allah, bani da karfin karbo wankau da bazan tambayeka ba" Kallon kin ma rainani ya jefa mata "sai ki tafi inda kika saba zuwa gidan tsoho aje a ci abinda ya sauwaka" Duk magiya da rokonta ta bayan kunnensa tabi sai da ranta ya baci sosai ta tsaya masa kerere a gaba. Tulun cikinsa kadai ya isa ya tureta dashi ta fadi. "Ka sakeni in koma gidan ubana ai ba a titi aka daura mana aure ba. Wannan wace irin rayuwa ce ace matanka tsakaninka dasu bai wuce ka dirka mana ciki ba. Ci da sha da sutura sai dai mu yiwa kanmu. Ko kunya baka ji duk kudinka. Mune wankau, surfe da duk wani aikin kaskanci don mu ciyar da kanmu da 'ya 'yanmu" Marin da ya zabga mata ne yana faman nade hannun malum malum ya gigita ta ta kasa cigaba da maida martani. "Ki fita idona Salame, wannan jarababben auren naki kuma yanzu muka fara babu inda zaki je" Fuuuu ya fice daga gidan sai dariyar Maman Danmama da ta cika mata kunne. Bata saurara ba sai da ta fito daga dakinta tazo gaban Salame tana mata dariyar mugunta. "Mu dai sai dai muce Allah Ya kara karawa. Ki koma wurin bokanki kice masa kwabarki tayi ruwa. Irin wadannan ranakun tsakaninki da Alhaji su kan sani nishadi da wanke min zuciya. Anyi walkiya Salame mun ganki tsamo tsamo" Dan sauran kuzarin nata na fada marin da ta sha ya tafi dashi, shiyasa ta kasa maidawa Maman Danmama. Ita kuwa batayi shiru ba. "Ohhh ni 'yasu. Kamar ba'ayi zamanin da kike sa Alhaji ya zage ya zanemu a cikin gidan nan ba. Kika dawo kika saka shi sakin kowa banda ni wai na zauna nayi raino kema a gidanku uwargidan babanku aikinta kenan. Ai ance tsafi gaskiyar mai shi. Kinyi kin gama surkullen tazo ta kare miki" Wani dukunkunannen hijabi Salame ta saka taki kula Mama ta fita tare da yaranta ta nufi gida. A soro suka yi kicibus da Malamijo zai fita. Girma ya kara kama shi sai dai akwai kyan jiki tunda babu kiba kuma yanzu ya yarda da ci da sha wa kansa mai kyau a waje. 'Yar fara'ar da ya taho da ita sakamakon faranta masa da amarya tayi kafin ya fito ce ta bace yana ganinta. "Allah Yayi dare gari ya waye an kwaso jiki an taho cin banza. To baki isa ba Salame. Tunda na aurar dake ko dan ihsanin nan na tsakanin da da mahaifi bai taba giftawa tsakaninmu ba sai ma dai ki karkace ki fada min magana idan kinso. Amma 'yan kwanakin nan kullum ana fada min sai kinzo, kuma ba kya tashi zuwa sai kin daidaici an gama abinci. Ki kwaso yara rabe-rabe azo aci bati. To na gaji, ki juya sawunki a likkafa ki koma inda kika fito" Jikinta har bari yake saboda yunwar dake sasakarta fushi da maidawa mahaifinta martani ba nata bane yau dinnan idan ba so take daga ita har yaran yunwa ta kar su ba. "Ku shige gani nan zuwa" tace tana kadasu ciki. "Ya ina cewa ku koma kina turasu? Salame, Salame ki kiyayeni." Yace yana nunata da yatsa. "Gaisawa kawai zanyi dasu mu tafi" Tausayinta ya dan ji saboda ya tabbatar yadda ta fige dinnan tabbas kila mijin da har shi take iya yiwa rashin kunya a kansa ya juya mata baya ne. "Jeki amma daga yau na sake ganinki zanje na sami Alh Indararon inji ko har ya cinye sadakinsa ne shiyasa zamu fara raba nauyin. Mairama ma da take ruga ta fiki abin arziki. Makanta, rashin miji da nisa basu hanata yi min alheri ba." Kunci taji ya ziyarci zuciyarta saboda ya ambaci kamwarta da ta mayar kishiyarta ta karfin tsiya. Duk ita ce silar komai tunda dalilinta taje wurin boka aka rabata da Alh Indararo saboda kawai bata son ta ga tayi gaba ta barta ba wai don ita din sonsa take yi ba. Da asiri ta rinka cin galaba akansa da matansa komai na tafiya daidai ta kuma saki jiki tana ta haihuwa don ta tara magada sosai. Cikin jikinta na da wata biyu bokan nata yace ga garinku. Shikenan duniya tayi mata atishawar 'yan tsaki. Komai ya lalace wai ita da take mulkin gidan a tsakar gida Alh Indararo ya kalleta yace yaushe ya aurota. Da bakinsa yake cewa ina Mairama kanwarta. Rai a bace ta shige ta ce da yaranta su taso su tafi. "Ki barsu yanzu zan zuba musu abinci Salame" Yadikko tace mata tana kallonta da tausayawa. Ko bata ce komai ba kana kallonta kasan akwai yunwa daga ita har yaran. "Tafiya zamuyi, kai ku tashi mana" "Umma ki bari muci abinci" babbar 'yarta tace idonta cike da kwalla. "Ko ku tashi ko jikinku ya gaya muku ku duka. Aikin banza kai." Duk yadda Yadikko taso kin zama tayi saboda kawai an yabi Mairama ta gwammace su sake kwana da yunwa. ********** Karfe biyar da rabi Awwab ya sauka a Nnamdi Azikiwe International Airport da yake birnin tarayya. Ya saba tafiye tafiyensa babu wasu kaya sai 'yar jaka karama da yake saka kayan sakawa biyu ko uku ya danganta da kwana nawa zaiyi a garin. Wannan karon kuwa sai da ya hado da akwati mai kyau na turawa dan madaidaici. Jin kansa yake wasai babu tarin gajiyar nan saboda a fasinja ya taho ba pilot ba, tun daga tasowarsu sai minti goma kafin saukar jirgin ya farka. 💕[02/11 7:30 AM] My 2nd Mtn: 23💕 . Ruwa yaje ya watsawa fuskarsa yayi brush sannan ya dauko wani karamin hankici kamar tawul iya tafin hannunsa ya goge fuskar. Komawa yayi ya zauna yana jin kansa yayi wani fresh balle da ya tuna mutanen da zai gani. Kayataccen murmushi yayi shi kadai wata matashiya da suke zaune tare ta maida masa saboda ya dan fuskanceta ne yana laluben seat belt dinsa. "Hi handsome" tace dashi da ingantaccen turancinta. Sai da ya waiga bayansa ya tabbatar babu kowa sannan ya nuna kansa sai ta gyada kai. "Hello" ya maida mata da kyar don baya son mace mara kamun kai. Da ace magana tayi masa kawai bazai damu ba. Amma idan kaji ana handsome ko beautiful ai kasan kwanan zancen. "Kaima bahaushe ne ko?" Baiyi mamakin da ta gane ba tunda suna zama ya soma waya bai dena ba sai da yaga jirgin ya fara tafiya. "Kema haka ko?" Murmushi tayi, a rayuwarta tana son namiji mai kaurin murya. Ba da karfi ya amsa mata ba amma amon muryar ya isa ya sanya mata da yawa muradin son kasancewa da mai ita musamman idan suka hado dashi. Wankan tarwada, dogo, hanci madaidaici da ya dace da kyakkyawar fuskarsa. "Na kula baka ci komai ba tun tasowarmu." Bai wani kare mata kallo ba yace "bana jin yunwa ne" So take hirar ta tsawaita don tunda ta dora idanu a kansa zuciyarta bata kara samun sauki ba. Ta kula mutumin kamar yana da ji da kai sai dai kuma bazata bari shan kamshinsa ya hanata samun abinda take so ba. Dawowarta kenan daga Germany inda taje hutu wurin yayarta. Mahaifinta tsohon soja ne da ya tsunduma siyasa tun lokacin mulkin farar hula. Yanzu haka sanata ne da yake wakiltar mazabarsu a jihar Plateau. "Suna na Arifah" "Awwab" Daga haka ya kafa waya a kunne don tuni sun sauka an bada damar kowa ya tashi. Cikin cabin crew din wata 'yar Nigeria da tasan Awwab tazo suna gaisawa da ya tashi zai dauki jakarsa. "Captain yau fa ka yi mana wayo. Kasha bacci ka barmu da aiki" Sai yanzu Arifah ta ga ya sake sakin fuska harda dariya "ki dauki hutu kema sai mu koma tare. Yanzu ina da wata guda na mantawa da kowa sai family dina" 'Yar hira suka taba sannan suka yi sallama. Awwab na fita Arifah ta bi bayan matar da suka gaisa mai suna Chisom ta roketa numbar wayarsa. "Ki bishi ya baki da kansa, Captain Awwab baya son irin haka don an taba yi masa na gani" Marairaicewa tayi tana fada mata yadda take son shi tare da rokon ta taimaka mata. Kudi ta dauko daga jakarta za ta mika mata Chisom ta bata rai "ba sai kin sayeni ba, Awwab is a nice man ga number dinsa ki gwada sa'arki" Arifah kamar ta zuba ruwa a kasa tasha ta rubuce number din da ta karanto mata daga wayarta ta fita da sauri ko zata sake samunsa sai dai yayi mata nisa bata ma san ina yayi ba. Bata da damuwa tunda akwai numbar da zata same shi. Yana fitowa waje hasken rana ya kwale a sama kamar ba shida ke neman yi ba. Jacket dinsa ya cire ya sakale a hannunsa ya jana jan akwatinsa. Kamar ance ya kalli hagunsa suka hada ido da Ghazalatu. Taci kwalliya sosai don ta burge shi ta kuwa yi nasarar sanya shi murmushi. Daga ita sai dreba suka zo daukarsa kannenta suna makaranta. "Yayana" tace da ya zagayo wurin motar tana murmushi. "My G kinyi kyau fa" "Ba wani nan, kai dai kawai ka dade baka ganni bane" Gaisawa yayi da dreban ya shiga gaba ita kadai a baya suna ta hira. Ji take kamar ya dawo bayan motar su zauna tare. Ta rasa gane masa ne ana soyayya amma shi tamkar wanda ya taso a kauye. Baya irin yadda wayayyu suke yi. Ko gidansu taje hutu haka zata karaci zamanta hannu wannan bai san ya rike mata ba ko da su kadai suka fita. Yanzu wata hudu rabon da ya ganta amma simple hug ma su ji dumin juna ya gagara. Waya ya rinka yi a rabin tafiyar saboda tazarar airport din da cikin gari. Mami ta fada masa su Alheran suna Kano amma Ummi tana tare dasu. "In sha Allahu gobe asubanci zanyi zuwa Katsina. Sai na ga Ummi zanje wurinsu. Uhmm Mami tare zamu taho da Ghazalatu fa" "Jiya Gambo ta fada min, sai kun iso. Jirgi zaku biyo?" "Gamu nan dai sai abinda Mummy tace" Sunyi sallama Ghazalatu ta rankwafa daidai kansa yana jin numfashinta a kunnuwansa da wuya. "Daga kanki G" yace yana yin gaba da kansa saboda yadda yake ji. Komawa tayi ta gyara zamanta "na daga shikenan, dama tambayarka zanyi ko kayi min tsaraba nima kamar kowa" "Su waye kowa?" "Yarinyar da ka tambayeni jiya me zaka saya mata" "Allah Yasa ba kishi kike yi da yarinyar da ni dake duk bamu gani ba" yace yana dariya. "Akwai dalilin da zanyi kishinta ne?" "Ko kadan, please kada muyi abinda muka saba daga zuwana. A bar maganar haka ko." Bata sake cewa komai ba har suka isa gida. Mummy Gambo tasa an hada masa kayan tarbar babban bako. Ranar da daddare da kansa ya sanar da ita abinda ke tsakaninsa da Ghazalatu. Gambo tayi murna sosai tana ta dokin maganar ta kai kunnen Hassana wato Mami. Abu ne da ya shafi dangi gabadaya ta bangarensu da bangaren mazajensu. Ga Awwab din da shiga rai dole taji dadin wannan hadi. ********** Harun mahaifin Ghazalatu da ne ga Alh Baba. Babansu Mami kaninsa ne na uku yayin da baban Major ya kasance autansu. Harun ne ya biyawa Alhajinsu umara suka tafi tare. Mutumci, shakuwa da kyakkyawar alakar dake tsakaninsa da Major tasa ya kaishi Germany gashi yanzu shi ma ya tsaya da kafarsa. Major bashi da wani abokin shawara a dangi kamar Harun shiyasa a daren ranar da ya sanar dasu Mami game da hadin Awwab da Alheran ya kira shi ya fada masa. "Gaskiya kayi tunani mai kyau ko babu komai yanzu zaka fi ji a ranka cewa ka rike iyalin bawan Allahn nan. Allah Ya gafarta masa Ya nuna mana lokacin" "Amin Harun" "Zan fara yiwa Alh Baba maganar yadda muna dawowa za'a je neman aure. Bikin su Zahra duka duka baifi wata daya ba kuma gashi kace gara a hada" "Gara a hada din muma sai mu sami sauki" "Hakane, ga 'yarka can Ghazalatu ta tsaya ruwan ido da ta fitar itama ba sai muyi komai mu gama lokaci guda ba" "Barni da ita, gobe suna hanya ita da Awwab zan binciketa ko akwai wani" Hirarsu suka yi irin na 'yan uwantaka suna kulla shawarwari game da yadda bikin zai kasance. Washegari Awwab ya sauka a garin nasu cike da tsantsar farinciki ya rinka sallama a kofar dakin Mami. Tana sane wai sai ta ja masa rai taki amsawa. "Mami manaaaa" Dariya tayi "shigo dai ba don halinka ba" Da saurinsa ya bude kofar idanunsa suka sauka akan Umminsa Mairama maman Alheran. Murmushi take ta yi masa daga inda take zaune wai wannan muryar Awwab ce. Shi kuwa wani dumi yaji a idonsa da sauri ya karasa gabanta ya riko duka hannayenta biyu ya dago kai yana kallon fuskarta. "Ummi" Da hannunta daya take bin fuskarsa tana shafawa "Awwab kaine ka zama babban mutum haka" Mami tana gefe tana murmushin jindadi Ghazalatu kuma ta coge a bakin kofa. "Ummina kina lafiya? Kin rinka tunawa dani kuwa" yace yana matse hannuwanta cikin nasa. Yau gashi da Umminsa abinda ya dade da cire rai saboda yadda shekaru suke ta yawaita. Hawaye ta soma yi "ban taba mantawa daku ba Awwab. Ina ma zan iya ganinka da kyau in gani ko wannan tsayin kamar bulala ka dan cike shi da tsoka" A razane ya kalli Mami sai ya ga tana hawaye. Hannunsa yasa yana yawo dashi a gaban idanunta ya ga ko gezau. Awwab kasa mallakar kansa yayi ya kifa kansa a cinyarta yana kuka. "Kaji mutum kamar ba namiji ba, meye na kukan? Ai komai ya wuce da yardar Allah" Hawaye yake da gaske yaji bazai iya zama ba ya tashi ya nufi inda yasan nan ne dakinsa. Mami tace da Mairama ta dena damuwa zai hakura kamar kowa. Ghazalatu ko shiga dakin bata yi ba ranta ya baci da kukan da wannan makauniyar ta saka mata shi. A take taji wani haushin Mairama ya kamata. Dama akan wannan da kallo daya zai sanar da mutum daga kauye take yake ta damuwa harda kuka. "Ghazalatu shigo mana, kinga yayanki na kuka ko? Kada ki damu zanyi masa magana" Ba yadda ta iya dole ta shiga tana nadamar tahowa don gidan har ya fice mata daga rai. Akwatinta ta tura gefe sai da Mami tace "ga Ummin Awwab ki gaisheta mana" "Sannu" "Yauwa sannu 'yata. Yaya gajiyar hanya?" Mugun kallon da Mami ta watsa mata ya sa ta chanja salon gaisuwar tace "ina wuni" a dakile. Ba jimawa Mairama ta shiga bandaki ai kuwa Mami rai a bace ta soma yiwa Ghazalatu fada. "Kar ki yarda na sake ganin irin haka kina jina? Wannan matar da kike gani ba karamar daraja da kima gareta a wurinmu ba. Dangi kowa kokari yake ya tayamu karramata. Bazan lamuncewa dabi'ar banza ba kinzo kina wani cin magan" Abinka da makaho kunne ya kara fikewa. Mairama tana jinsu tayi murmushi kawai. To dama yaushe zata yi tunanin kowa nasu zai sota. Ita ce fa wadda mahaifinta har yau bai taba bin sawunta ba sai dai ita har sau uku taje kuma tana aika masa da 'yan abinda ba'a rasawa. "Kiyi hakuru gajiyar hanya ce" Ghazalatu tace da ta tuna Mami ce fa mahaifiyar Awwab. "A dai gyara" ********** Fauziyya da Zahra suna kallo a falo Zainab tana duba takardun asibitoci uku da likitann nan ya aiko mata. Ibrahim baya gidan yaje gaishe da kakaninsa Hadir kuwa bacci yake a daki. Radhiya ce ta fito yau babu hijabi tana dan murmushi fuskarta tasha kwalliua harda janbaki. Fauziyya da Zahra suka shiga gyara dankwalayensu. Zayyana daga shiga deban abinci a kitchen ta kasa fitowa tunda taji muryar Radhiya tana cewa. "Ha mutum ya fito yasha iskar Allah." Tana zama su Zahra suka mike, Zainab ta kwashe da dariya. Radhiya ta zama horror tunda tace zata yi musu balotelli. Jiya a gabanta Ibrahim ya nuna musu hoton Mario Balotelli wani dan ball baki na kasar Italy wanda yake kwashe kansa hagu da dama ya bar tsoro guda a tsakiya tun daga gaba har keya. A karkace ta kallesu "tashi kuma zaku yi daga zamana?" "Ni bacci nake ji" cewar Fauziyya "Fitsari zanyi ni kuma" Zahra tace tana matsawa gefe. "To sai kun dawo, gumi ne ya dameni yau na saka lasi" kawai sai ta tuge dankwalinta rantal ya bayyana. Wata irin dariya suka kwashe da ita har Zayyana dake kofar kitchen. Zainab na dago kai ta mayar dashi kan takardu kafin ta soma dariya itama. Radhiya ta bata rai "ayi dariya da kyau naje soja na dawo. Kuma na dena daura dankwali iska zan rinka sha" "Ki rufa mana asiri don Allah ki rufe" Zahra tace idonta harda hawayen ganin wannan gashi na Radhiya tsilli tsilli. "Allah bazan rufe ba iska nazo sha." Kyalesu tayi suka sha dariyarsu tana cewa su kiyaye kada tayi sanadin da zaa kai amare da kwalkwal. Daga nan hira ta kaure don daga Zahran har Fauziyya basu da girman kai duk da ba sa'arsu bace. Suna cikin hira ta soma gyangyadi Zainab tace ta koma daki ta soma musu irin na masu magagi wai ba bacci take ba. Kafin la'asar ta bingire akan doguwar kujera abinta. Ana kiran sallah duka suka watse sai Zayyana. Ta wayar Fauziyya Awwab ya kira yace yana kofar gida don dreban Harun ne ya kawo shi. Zayyana da ta amsa wayar taje ta bude masa gate tana murnar ganinsa. Suna shigowa falo idanunsa suka gane masa Radhiya. Kanta yake iya gani sai rabin jikinta ta rufa dankwalinta daga kasa kuma fuskarta jikin kujera take kallo. Ya dai tabbatar kayan mata ne a jikin mai wannan kan a sanyaye ya karasa shigowa Zainab tana turo Hadir ya kallesu da tausayawa. Da guda daya tilo da suka haifa ashe dan daudu ne jiya da Mami da Ummi suna bashi labarin komai yana kwalla basu hada masa da wannan ba. 💕[02/11 7:30 AM] My 2nd Mtn: 24💕. Zainab baki yaki rufuwa "Awwab, Masha Allah sannu da zuwa...zauna, zauna kasha hanya Shi dai murmushi yake yi amma hankalinsa gabadaya yana wurin wannan kan dake kwance akan kujera. Allah ne Ya taimaka Zainab ta kula da me yake kallo tayi saurin dora yatsanta a baki wai yayi shiru. Dankwalin da Radhiya ta rufe kafa dashi shi ta dauka a hankali ta mayar mata dashi kanta. Sai lokacin ya iya dauke ido daga kanta ya mayar garesu. Gaban Hadir yaje ya durkusa ya rike masa hannu yana jin kwalla ta taho masa. "Nasan ka gama jin duk wani labari a wurinsu Mami kuma ka gama kukanka. Kayi hakuri ka saki zuciyarka muyi murnar sake haduwa" Zainab tace tana kallon yadda Awwab din ya koma ingarman matashi. Motsi Radhiya ta soma yi dankwalin yana neman faduwa aka yi sa'a ya zauna. Ita dai Zainab a tsorace take kada ta tashi a hagu su rasa inda zasuyi da ita. "Ina Ibrahim da Zayyan karami?" Yayi tambayar har ransa yana fatan Allah Yasa ba wannan na kwancen da ya kasa tantance waye ba za'a kira da daya daga cikinsu. "Sun fita cikin gari amma nasan suna hanya" Iska ya furzar yana fadada murmushinsa "da gaske? Huhhh Alhamdulillah" Zainab sai tayi tunanin yana murna ne don tace suna hanya. Sake kallon Radhiya yayi shi dai hankalinsa gaskiya bai kwanta da ita ba. Kamar ta san tunanin da yake a kanta kuwa tayi mika ta tashi zaune. Dankwalin ya zamo daidai lokacin da ta sauke idanu akan fuskarshi. Shi ma ita din yake kallo daga sama har kasa don ya tabbatar da jinsinta sai dai fuskarta ta tsaya masa har ya kasa magana. Kai a lailaye ga fuskarta harda janbaki. A hankali idanunsa suka fara saukowa daga fuskar a kokarin kure mata kallo sai ya tsaya cak a wuyanta ya kasa karasawa yana jin wani yanayi da bai saba ba a jikinsa. A hankali ya furtawa kansa "mace ce". Tsuke baki Radhiya tayi tana jin ba don Innawuro ce tayi mata askin nan ba wallahi da abinda zata fara yi idan ta koma rugar Barkindo shine ta sauke mata nata gashin. Waye wannan da ya cika mata ido ta kasa sakin baki a gabansa ya gane mata sirrinta. Motsa bakin ta sake yi ko ihu ne ta kwarma musu amma ta kasa. Kumatunta na dama da yake lotsawa idan tayi yunkurin magana shine ya sake daukar hankalin Awwab ya kuma kallonta da kyau. "Kaddai? Nooo it can't be." Ya nanatawa kansa da sauri. Girgiza kai yayi shi kadai gamo da Radhiya yana nema tafiya da nutsuwa da tunaninsa. Su Fauziyya da suka taho yi masa barka da zuwa kowacce tayi shiru kamar ta hadiyi kota suna jiran su ga me Radhiya za tayi. Dankwali dai gashi nan amma rabin kai a bude yake. Hannunta ta dora a ka taji iya ina ne a bude. Tana ji ta janyo dankwalin a hankali ta tashi bata ce komai ba ta bar falon. Karar kofa suka ji da karfi wadda ta gwara saboda bacin rai. Zainab ta girgiza kai su Zayyana jiki yayi lakwas. Awwab yana lura da yadda suka sauya su duka ya daure yace "Alheran?" Da sigar tambaya yana tsananta addu'a kada ace wannan ce da ta tashi yanzu. Kamar jiransa suke suka bushe da dariya gabadayansu. Alheran din da yaci burin gani har ya kasa zaman Katsina ce. Babu wanda ya tsammaci zuwansa Kano a yau ana tunanin zai zauna ya huta amma doki ya hana. Ghazalatu har fushi tayi ya bata hakuri da alkawarin zai dawo washegari. Kin zama tayi a gidan yayi mata shiru da yawa ta tafi gidan Alh Baba wurin kakarta. "Ita ce ta shige ciki yanzu" Zainab ta bashi amsa da dan murmushinta. Da ba don da kanta ta amsa masa ba zai ce ko wani salon tsokana ne kuma suke yi masa don ansan yadda ya damu da ita kuma ya matsu ya sake haduwa da ita. Da hannu ya nuna hanyar da ta bi ya marairaice fuska "wannan din?" Basu dena dariyar ba kuwa Zainab tace "yau idan kuka shiga hannunta ko kafata bazaku gani ba" Rige rigen bashi labarin Radhiya suka shiga yi kowa tana fadin nata. Awwab bai san lokacin da ya saki murmushi ba wato bata chanja ba kenan daga sanin da yayi mata. Shiru kusan minti ashirin bata dawo ba abinda bata saba ba. Hadir yana ta kallon kofa Zainab ta fahimce shi tace su dubo mata ita. "Mama gaskiya ki tura Zayyana ita ce karama" "Wani sabon abu ne kuka koya a aikeku ku tsaya zaben mai zuwa?" Awwab yace yana dan bata rai. "Radhiyan ce ai Hamma" "Come on tashi ki karawo min ita Zayyana" Tana zumbura baki ta shiga kofar hanyar dakunan. Tun kafin ta karasa take jin shesshekar kuka. Da dan gudu tayi sauri ta bude kofar dakin. Radhiya ta gani kwance akan abin sallah tana kuka fuskarta har tayi ja. "Uhmm Adda Radhiya kizo inji Hamma Awwab" Zumbur ta tashi zaune Zayyana ta dan ja baya kadan ta share kamar bata gani ba, cikin yanayin damuwa tace "shi wannan na falon shine Hamma Awwab din?" "Eh" "Kunci amanata! babu wanda yace min zai zo kuma aka ki tashina daga falo da zai shigo" Radhiya tace tana sake fashewa da kuka. Yanzu da wane ido zata kalli mutumin da taci burin haduwa dashi saboda irin labaran da ake bata. Ance mata sun shaku da tana karama kuma yana sonta sosai. Ashe ma ya zama dan gayu irin haka kamar likita amma aka bari ya ga askinta. Zayyana komawa tayi tana jin tausayin Radhiya. Ko ita ce da kwalkwal bazata so ace kowa ya gani ba. "Ina take?" "Kuka take yi Mama" Da 'yar damuwa a fuskarta tace "Yanzu dai Awwab duk kaine ka janyo wannan rigima da ka ga kanta, yau ban san yadda zamuyi ba" "Ni kuma me nayi daga zuwana" Su Zahra ya tsare da idanuwa "me yasa baku tasheta ta rufe kan ba?" Kusa dashi Zayyana ta zauna "haka tace wai munci amanarta da bamu tasheta ba ma" Samun kansa yayi da rashin jindadi, ba haka ya tsara haduwarsu ba. Garin yaya ma aka yi mata aski irin haka don Allah? Sallamar Ibrahim da Zayyan ita ta katse tunaninsa. Zaratan samari ne dake ganiyar tashinsu. "Kunga Hammana" suka ji Zayyana ta fada tana murmushi ta nuna shi. "Naki ko namu?" Ibrahim yace yana mika masa hannu. "Da gani kaine Ibrahim, sau biyu Zayyana tana kawo min kararka. Baka san ba'a tsokanar autar Daddy ba?" Awwab yace cikin sakin fuska. "To kace ta dena shagwaba ko muma mu fara ko Emzee, mu dinma duka autoci ne" Kalmar tasa ta karshe ta sanyasu dariya. Awwab ya kalli Emzee yaron is very calm sai murmushi da yake yi kawai. Ji yayi ya burge shi, a fuska ya tuna masa da babansa Zayyan sosai amma wannan Zayyan din da gani ba mai hayaniya bane. Hannu ya mika masa suka gaisa Emzee yana dari-dari ba kamar Ibrahim mai saurin sakewa da sabo ba. "Dama kai nake jira taimaka ka fito min da yayarka wadannan duk matsorata ne" ya nuna su Fauziyya. "Kin fitowa tayi?" Ibrahim yace da mamaki "kullum fa zancenta idan ka dawo zata dena kula kowa a gidannan" " 'Yan cin amana sun saka mana ido ya muka iya yau sunci amanarmu" Awwab yace yana aron kalmar da Zayyana tace tayi amfani da ita. Ibrahim yace "Mama me suka yi mata?" Zayyana ce ta bashi labari kafin Zainab ta soma magana. "Anci amana gaskiya, bari na koma cikin gari na kwana don ga dukkan alamu yau mutanen gidan nan zasu kwana da balotelli" Emzee ya daki kafadar Ibrahim suna dariya kafin ya nufi dakin. Tana nan zaune hanci ya kumbura, idanu sun kankance sunyi ja saboda kukan da tasha. An cuceta da aka aske mata kai. Da an bar mata na zaman falon da ta roka ko babu komai zai rufa mata asiri yau. "Adda kizo inji Hamma Awwab" "Ni fa gida zan tafi" Daure fuska ta ga yayi "ke babu dama ranki ya baci sai kice zaki je gida? Idan Ummi taji abinda kike yi a gidannan zata ji dadi ne? Kowa na tsoron bata miki rai kina jin dadi kamar abin kirki" Mamakinsa ta soma yi. Emzee din da babu ruwansa ko me tace ta zauna shine yake mata fada. Jan hanci tayi "to ba kaina suka bari ya gani ba" "Ance iska kika je sha, kina da wannan kan da kike boyewa ki rasa wurin shan iska sai falo. Yanzu da Kawu Zakari ne ya zo fa?" "Bakinka ya sari danyen kashi, wannan ai mugun fata ne." tace tana harararsa ta tuna wanda ya dan gani a gidan Baffa Gide. "Tunda Allah Ya rufa miki asiri ba shi din bane ba sai kawai ki basar ba irin a zuwan baki ma san me ya faru ba. Da nine ke fa wallahi da magagin baccin karya zan bar falon" Sauran hawayen ta goge da bayan hannunta tana dariya harda kyakyatawa "shege Emzee ka iya bada shawara Yasin" "Shine zaki zageni to" ya harareta yadda take masa. Dan ture shi tayi bayan ta daure kanta da dankwali ta saka hijab "wasa ne dalla" ita ce a gaba yana bayanta. Sai da suka zo bakin kofar ta kasa fita tana jin kunya. Emzee na zuwa ya turata ta soma turjewa amma da ta ga kowa ita yake kallo sai ta dake yadda yace mata ta basar. Duk da kumburin fuskarta bai hana Awwab sake gano kamannin wannan Alheran din mai askakken kai da 'yar karamar kanwarsa mai rigima ba. Ta girma amma tana nan da dan jikinta don tafi karfin a kirata ramammiya sannan baza'a ce ta shiga sahun lukutaye kai tsaye ba. Radhiya a dire take ta ciko ta ko ina. Da kadan ta dara Zayyana a tsayi ita da ake yiwa kallon doguwa saboda tsayin kafa. Yayin da Awwab ke kokarin hada ido da ita, ita kuma su Zahra ta kalla tana ta kokarin kada ta kalle shi. Tunda Emzee yace ta basar to fa basarwar zata yi. "Shine baku tasheni nayi sallah da wuri ba Adda Zahra" "Naga baccin naki yayi dadi ne" Sai ta maida hankalinta ga Ibrahim "ka fadawa Umma ina gaisheta?" "Tace kafin ku koma kije kiyi mata kwana biyu" "Mama gobe zaki sa ya rakani?" "Sai dai jibi Radhiya. Gobe asibiti zan kaiki ko har kin manta?" Asibiti za ta kaita saboda makeron da yaki barin gashinta yayi abin kirki. Awwab sai binta yake da ido tana ta jan mutane da hira banda shi kamar ma baya wurin. Sai da Zainab tace "wai baki ga Awwab bane?" Radhiya ta wani bude baki da idanu irin mamakin nan "laahhhh Mama yaushe yazo? Hamma, oyoyo" Emzee tashi yayi ya sulale daga falon saboda tsabar kunya. Radhiya halinta sai ita. Yace ta basar kamar ba'ayi ba shine zata nuna bata ganshi ba gabadaya. Ji yayi kamar ya saka kuka da ma bai bata wannan shawarar ba. "Baki ma ganni ba sai yanzu?" Yace yana kallon fuskarta. Dimple dinnan da yake saka yatsansa a ciki idan tana dariya yake kallo yana tuna masa rayuwar da. Dakewa tayi abinta "ina na ganka na fito ina ta hira da 'yan uwa, yaya hanya? Ka ga Ummi?" "Baki ganni ba da kika tashi daga bacci dazun nan?" Radhiya an koyi basarwa da gaske ta wani langabe kai "yaushe? Ka dade da zuwa ne?" Wai raina masa wayo zata yi ne? Kowa kallonsu yake yi ana dariya kasa-kasa. Hadir kansa murmushinsa ya kusa zama dariya da ya gane so take ta nuna bata ganshi ba. Awwab da bai fahimta ba dama shima anyi masa tambarin wauta idan abin dan farin nasa ya tashi yace "dazu fa kin farka har muka hada ido." Tsuke baki ta soma yi. Ya kamata idan ta basar sau daya kawai a wuce wurin amma sai neman jan zance yake yi. "Ni din? Bacci fa nayi a kan kujerar nan sai farkawa nayi na ganni a daki su Adda Zahra sun rikeni sun kaini saboda nauyin baccina, ban san lokacin da ka shigo ba" Zahra ta soma kifta masa ido akan ya bar zancen haka shi kuma ya dage sai ya ga abinda ya turewa buzu nadi. "Lokacin da abin kanki ya zame haka " ya kwatanta da dan jan dankwalin Fauziyya " har na ga kan...." Ihu ta saka ta tashi da sauri tana jin kamar taje ta toshe masa baki kada ya karasa fadin ya ga kanta. Kamar zata yi kuka take kallonsa "idan nace ban ganka ba sai kawai ka yarda haka ake yi ko Em..." shiru tayi ta shiga waige da ta ga baya wurin "ina Emzee?" Tayi tambayar tana kallon Ibrahim da dariya tasa ko magana ya kasa. "Ya fice" "Ku ga min shegen yaro, shi yace idan na basar kamar ba'ayi ba komai zai wuce." Gabadaya falon ya sake kaurewa da dariya. Zainab ta tashi ta kama kujerar Hadir "bari naje na bawa babanku magani, Fauziyya ku kawowa Awwab abinci ko ruwa bai sha ba tunda ya shigo kun saka min 'ya a gaba" Gani tayi ya dace su baiwa yaran wuri don ba ta biye musu ana tunzura Radhiya ba. So take Awwab ya so kanwar tasa da wuri, gara su fara sabawa da juna. Taimakawa Hadir tayi ya kwanta ta dauko takardun asibitin ta koma kusa dashi tana yi masa bayanin kowanne don neman shawararsa. Da ido da yanayin chanjin fuska take fahimtar abubuwa da dama da yake nufi idan tayi masa tambaya. Sakale tayi tana kallon Awwab yana murmushi "ban san haka kike so ba, to koma ki sake fitowa. I promise zan tayaki basarwa" Ita ma sai da abin ya bata dariya ta koma ta zauna tana jiran fitowar Emzee ko ma ina yaje ya buya. Dama idan ba ganganci ba me zaisa ta karbi shawararsa. Wautar kanta take gani na biye masa. Yana jiyo me suke yi a inda ya tsaya ya girgiza kai. Bawa Radhiya shawara wataran kamar zuba gari ne a rariya. Kana fada yana zuba. Ibrahim da Zayyana suka tashi suka bi bayan shi zuwa waje. Ibrahim na cewa ta dena binsa ta murguda masa baki tace ita wurin Emzee zata je ba shi take bi ba. Ya rage su hudu a falon Awwab ya watsawa su Zahra idanunsa "bazaku bani abincin bane?" Da sauri Radhiya ta tashi don yau dai taji kunya fiye da yadda ta saba "bari na kawo maka" "No, dawo ki zauna" Inkiya yake musu su basu wuri sumsum suka tashi suna dariyar dramar Radhiya. Kai ta sunkuyar karon farko da zata iya tunawa a rayuwarta ta rasa bakin magana saboda kunyar da ta bawa kanta. Dan gayu kamar wannan kyakkyawa daga ita sai shi a falo ai dole harshe yayi nauyi tace a zuciyarta. Nazarinta Awwab yake yi ya dago kansa daga jinginar da yayi da kujera yana mamakin wannan yarinyar ta gabansa ita ce Alheran dinnan da yake dauka suyi ta yawo a barrack shekarun baya. "Alheran" ya ambaci sunanta a hankali taji wani yarr a jikinta saboda yadda muryar ta ratsata. "Uhmm" "Kin dena magana ne kuma?" Ya tsokaneta da ya ga kamar ma a takure take. Girgiza kai tayi sannan tayi kwafa da guntun tsaki "Wallahi kunya naji, ashe ba haka ake basarwa ba. Bari Emzee ya dawo zai gamu dani" "Balotelli zaki yi masa?" Dago kai tayi da sauri ya dage mata gira yana jin komai nata na burge shi. Ba haka yayi zaton ganinta ba. Yana ta kissima wata budurwa mai ji da kai da gayu sai ya hadu da Radhiya wadda kwatancenta sai wanda ya santa. Amma duk da haka yaji tayi masa a yadda ya sameta cikin kankanin lokaci 💕[02/11 7:30 AM] My 2nd Mtn: 25💕 Bata tsaya ko ina ba sai daki ta cire hijabin da dankwali ta fada kan gado. Wani tunani ne ya shigeta haka kawai kada a sake tsautsayi ta dauki dankwalinta ta daura. Awwab kamar bai san me yayi ba ya shiga cin abinci hankali kwance yana jin matan suna kuskus a junansu. To meye ma a ciki daga bata abinci. Da ace sun tashi tare baya jin akwai abinda zai kasa yi mata sai dai a taka masa birki tunda mace ce. Allah ne Ya hada jininsa da na iyayenta sai Ya sanya masa matukar kaunarta tun tana tsumman goyo. Emzee yaso dauke kai amma ya kasa. Karshe ya dauko wani littafi a kusa dashi ya bude shi ya kifa akan fuskarsa yana dariyar da ba sauti. Gaskiya yaji kunya kamar shi aka bawa abincin. Ibrahim ne ya fara tsokanarsa sai kawai ya tashi da plate dinsa a hannu zai koma daki. "Dawo ka zauna ka gama cin abincin nan" Awwab yace ko kallonsa baiyi ba. "Na koshi" "Kira min Alheran" Ba musu yaje ya fadi sakon, maimakon amsa sai ta kara dukunkune kanta ta tura a karkashin filo. Murmushi yayi kawai ya fita ya dawo ya fadawa Awwab taki tashi. Sai da yaci rabin abincin ya mika masa plate din "ka kai mata nata, sai da safen ku" Tashi yayi zai tafi dakin Ibrahim inda aka yi masa masauki Zayyana da ta kasa hakuri ta fara shagwabe fuska "Hamma ni baka taba yi min irin haka ba, harda bata a baki" "Ba kiji ta fada muku cewa a rashinta nake kulaki ba" ya fada da wasa. Kukan shagwabar da ta saba ta fara "kuma sai na...." "....fadawa Daddy" Ibrahim ya karashe mata yana kyabe fuska yadda take yi. Awwab ya kusa kofa don idan ya biye mata karshenta a daren sai ya ga wayar Daddy. Juye juye ta soma yi Emzee ya dawo daga ajiyewa Radhiya abinci ya ganta. "Wa kike nema?" "Kai mana" "Inyi miki me?" "Ba Hamma Ibrahim bane yake tsokanata" "In fada miki sunan Fulatancinsa ki rama?" Cikin sauri Ibrahim yazo ya tura shi daki yana magiya da yayi shiru. Tun da Radhiya ta fassara masa ma'anar Surbajo yake gudun sunan kuma dashi Emzee yake samu ya dan kashe bakin idan ya dame su. Da yake Mami ta fada musu cewa sammako zasuyi su baro Katsina su ma basu yi sanya ba wurin tashi da wuri. Zuwan 'yan matan ba karamin dadi ya yiwa Zainab ba. Su tayata hira ayi ta barkwanci sannan basa bari tayi komai. Zahra da Fauziyya sun jima da gogewa wurin aikin gida da girki. Saboda Mami taran safe zuwa taran dare tana gidan aikinta. Su ne suke komai. Shiyasa Zayyana ta shaku dasu sosai wani zubin bazaka ce yayyenta bane da suka girme mata da yawa. Kowa ya shirya cikin kayan kirki Radhiya ta bude jakarta kenan bayan ta gama shafa mai Zainab ta leko tayi kiranta. Dakinta ta bar musu dama. Yanzu kuwa da ta kai Hadir falo bayan ya gama breakfast sai ta kirata dakinsa. Ledoji uku ne a gabanta manya ta tura mata daya. "Ga naki kafin ku tashi daga bacci telan ya kawo" Radhiya ta bude baki tana kallon kayan da Zainab din take zarowa. Atampa guda uku, material daya, shadda daya da wasu yadika combination biyu. Kwalkwal tayi ta idanu zata yi kuka. Duk wannan ita kadai. "Bana son kuka fa kin sani ko yanzu naje na fada a hanaki yin sojan." "Mama nagode" tace hawayen yana fitowa. Yarinya ce mai rike abu a rai shiyasa bata manta alkhairi ko sharri. Da yake dai wasa da shirme sunyi mata yawa a ka shiyasa sai ka ga kamar bata da damuwar komai. Banda kaddara da Zayyan yana raye Zainab ta sani da yanzu sun kai wani mataki a aikinsu. Yadda yake da kwazo da himma tasan 'ya'yansa sai dai wani yaci arzikinsu. Babban dalilin kiran dama so take ta shirya Radhiya da kanta. Mama Zainab 'yar kwalliya ce ajin karshe. Idan ka ganta a yanzu da take cikin farincikin kasancewa da Hadir duk da a zahiri za'a iya cewa nauyi ne shi a gareta amma fes take kullum. Gogewarta a soyayya duba da tarihin rayuwarta yasa tun jiya ta daukarwa kanta nauyin sake hada Awwab da Alheran domin su cimma burinsu cikin sauki akan yaran. Kallo daya zaka yi musu kasan sun dace da juna amma idan ka san kowannensu ta fannin zamantakewar rayuwa dole ka chanja shawara. Awwab dan boko ne tashin turai. Yana da ilimi, wayewa da kudi domin kuwa pilots masu aiki da kamfanin KLM suna cikin mafiya samun kudi cikin tsararrakinsu. Alheran Radhiya kuwa yarinya ce da ta tashi a rugar fulani a cikin wata karamar hukuma. Wannan kadai ya isa zama wawakeken bambamci tsakaninsu indai zaman aure zasuyi wanda babu soyayya. Abubuwan da ya sani ko yake so bata sansu ba bare ta so su. Wayewarsu ba iri daya bace. Tayi nata karatun daidai gwargwado amma baza'a taba hada shi da nasa ba tunda iyakarta secondary. Shiyasa indai ana so zaman aurensu yayi karko to a samu soyayya mai karfi da za ta zama igiyar dauresu. Wani kaya Zainab ta ciro daga ledar ta mika mata "jeki ki saka wadannan gani nan zuwa. Ko hoda kada ki shafa sai nazo" "To Mama" tace ta fita da murnarta taje ta nunawa su Zahra su ka tayata murna. Yadi ne mai kala biyu. Mara adon light purple ne anyi mata skirt dogo da dankwali. Rigar kuwa yadinta duka zanen filawoyi ne manya pink da light light purple kamar skirt din. Tsayinta ya wuce gwiwa da kadan anyi mata dogon hannu mai dan fadi daga kasansa. Kadan akayi mata shape don kada ta kama jiki ba wani ado a jikinta sai maballai guda hudu na wuya amma tayi kyau musamman a jikin Radhiya. Wani juyi ta rinka yi tana jindadi su Zahra na zuga ta har Zainab ta shigo tace suyi sauri wanda basu ci abinci ba su je su ci nan da awa daya ko kasa da haka su Mami zasu iso. Duka su ukun su ka fita aka barsu su kadai. Hoda, kwalli da janbaki pink mara duhu ta shafawa Radhiya a fuska bayan tayi mata lining da jagira pink mai duhu a leben. Simple make up ne amma fuskarta tayi kyau. Cikas din kawai kanta ne. Zainab ta daura mata dankwalin da kanta ya danyi tudu daga keya sannan ta mika mata hijab mai kyau da kananun duwatsu a kasansa pink irin kayan. Iyakarsa ya sauko kirjinta da kadan. Radhiya harda hajijiya a gaban mudubi. "Mama nayi kyau ko?" Murmushi tayi ta yaba sosai da 'yar tasu "kinyi kyau amma don Allah bana son baragada kinji ko. Wannan hayaniyar da saurin fushi ko fada ki ajiyesu. So nake naga kina taku daidai yadda babu wanda zai raina min ke" "Idan nayi sanyi da yawa bazan kai labari ba a makarantar sojoji Mama. Anfi son mu da dakiya da fada saboda gudun raini" "Allah nagode Maka. Har yanzu kina jiran zuwa sojan ne bayan miji zan samo miki" Da murnarta tace "Likita?" "Idan ba likita bane ba fa?" "Gaskiya Mama ki barshi kawai. Idan ba likita ba sai dai ko soja irina. Sauran duk na rainasu, kada ayi auren su rinka kawo karata kullum" Hannuwa Zainab ta tafa tana dariya, yanzu ta gama cewa ta dena shirme gashi ta hade fuska tana buga kayanta a ganinta kuma ba laifi bane. "Jeki kici abinci kada azo ana jiranki" Kallon kanta ta sake yi yadda tayi kyau abinci zai iya goge mats jambakin ta dawo tayi zamanta akan gado "bana jin yunwa" "Ashe kuwa za'a tafi a barki" Zainab tace tana yin gaba. Ba don taso ba ta tashi itama. Tana saka kafa a falon ta tuna abinda Awwab yayi mata sai ta juya suka kusa karo da Zainab. "Wuce muje kici abinci" ta umarceta. Gani tayi babu alamun Awwab din sai ta saki ranta ta fara gaishe da Hadir da yake kallon labarai sannan ta tafi gaban dinning table inda kayan tea suke za ta hada taji Zainab tana tambayar ko Awwab ya shirya. "Da kyar idan ma ya tashi Mama, shi fa idan yana gida yafi zaman daki yayi bacci saboda yanayin aikinsa" Zahra ta bata amsa. Radhiya ta saki murmushi "kice kamar dai mu sojoji ashe nasa aikin shima baya samun isasshen hutu". Suna mata dariya za ta fara abin nata ta mayar da hankali ga abinda take yi. Madara da milo ta zuba a cup din nata ta mika hannu za ta dauki sugar Awwab ya bude kofar dakin ya fito. Wani hadadden kamshi ke tasowa tun kafin ya iso tsakiyar falon. Yayi kyau cikin wani lallausan yadi ruwan madara. Rabonsa da manyan kaya ya kwana biyu sai jiya da Daddy ya bashi su guda biyu dinkakku da zai taho. Su Zainab ya fara gaisarwa sannan ya amsa gaisuwar kannensa da Radhiya da jikinta yayi sanyi saboda kada a sake irin ta jiya. Tana tsaye ta kasa karasa abinda take yi balle ta ja kujera ta zauna. Jiya ke mata yawo a ka yadda ya bata abinci a baki kamar wata baby. Runtse idanu tayi tana son kawar da tunanin daga zuciyarta taji ya janye kofin daga hannunta. "Kawo na karasa hadawa naga ba kya sauri" Sakar masa tayi da sauri ya ture robar sugar din ya kara mata madara da milo ya fara zuba ruwan zafi. "Hamma ya isa haka" tace da ta ga ya wuce rabi. Bai saurareta ba sai da ya cika kofin ya ja kujerar gefenta ya zauna. Kujerar kusa dashi ya tura mata baya da kafarsa ta zauna tana waigen baya. Babu mai kallonsu Zainab da Hadir labarai suke gani a tashar Channels. Zahra da Fauziyya suna hirar angwayensu dake korafin sun makale a Kano. Zayyana kuwa ta tafi dafa indomie. Wani irin kallo yayi mata sau daya ya dauke kansa, tayi masa kyau sosai har yana tsoron kada kallon da yake mata ya wuce gona da iri "namu ne mu biyu" Turo baki tayi "Habaaa Hamma don Allah yunwa nake ji" "Okay fara sha ki bani" yace yana tura mata kofin. "Ni a'a, ka shanye na hada wani" Lumshe idanu yayi yana mata murmushi "wannan zamu sha, jiya dama ance abincin da na rage miki dawo dashi kikayi. Ko muyi kama-kama da shima baki bari munyi ba" "Na shiga uku" ta furta a hankali tana cike da kunya ta tura kujerarta baya za ta tashi ya bata rai. "Ki dena tashi idan muna magana bana so" Zama tayi tana ta zumbura masa baki ya sha rabin tea din ya mika mata ta karba ta bishi da harara. "Baka saka suga ba ni kuma dashi nake sha" ta mika hannu zata dauko robar ya riga ta daukewa. "Da zaki a haka, try it." Samun kanta tayi da bin umarninsa ta sha tea din shi kuma ya tashi ya koma daki bai taba doyar da aka soya da kwai ba. Tana nan zaune ya dawo da ledoji masu kyau a hannunsa da tambarin wani babban kamfani a kasar Germany. Su Zainab ya fara mikawa ta karba da murmushi ta bude. Turaruka ne na alfarma na mace da na namiji ita da Babansu Hadir da agogo set shima na mace da namiji. "Harda dorawa kanka wahala Awwab?" "Ku sa mana albarka kawai Mama" "To Allah Ya saka da alkhairi Yasa kafi haka. Allah Ya baku masu yi muku a nan gaba" "Amin" kowa ya amsa harda Radhiya. Leda ta biyu ya mika mata "na Ibrahim da Emzee, suna ina ne ma?" "Leka ta window wankin mota ake mana" Komawa yayi dinning table din ya zauna a inda ya tashi Radhiya ta kafe shi da ido. "Ya?" Yace yana gimtse dariya don ya kula ta fara cika tana jiran nata. "Ina nawa?" "Me din?" Kai tsaye tace "Abin cikin ledar" "Kina harar tawa zan baki abin cikin leda? Wanda na siyo da sunanki ma zan je in kaiwa Ummi tayi sadaka dasu" Kallon shirts da agoguna da Zainab ke fitarwa da sunan Emzee da Ibrahim yasa ta sake hade rai harda kwalla. Ita da tafi kowa cika baki akan Hamma Awwab amma ita ce ko tsinke bai bata ba. Abincin ma fushi tayi dashi ta ture. Sai yaji ta dan bashi tausayi ya gama dariyar abinda yake shirin kulla mata kawai don ya tsokaneta ya matso da kansa yana mata magana a hankali. "Kin yarda daga yanzu ko me zamu ci zamu ragewa juna har na koma?" yayi dan murmushin rigimarsa da Mami a baya "da ko me naci sai na rage miki Mami tayi ta fada wai ba komai zaki iya ci ba. Ni kuma tana barin wurin sai na tura miki a baki ko yaya ne ki cinye" Murmushin da tayi masa jinsa yayi har ransa saboda yadda take lumshe idanu batare da tayi la'akari da tasirin hakan gareshi ba "to ai kaine baka yi min bayani ba kawai kasa ni jin kunya jiya." "Silly girl me akayi na jin kunyar? Kinsan me kike yi min kuwa da?" Radhiya ta girgiza kai. Yafito ta yayi da hannu ta sake duku kanta tana shakar daddadan kamshinsa "abin bakina kike cirewa ki saka a naki idan na hanaki" Hannuwanta ta saka a gefe da gefen kumatunta ta bude baki da idanu duka a lokaci daya. Tana ta jiran Hamma Awwab ya dawo gashi ya dawo ya hadata da jin kunyar da bata taba sanin tana da ita ba. Abin bakinsa fa yace! Yanzu tana tashi kuma zai ce ta zauna ko yayi maganar yadda kowa sai yaji. Gara kawai tayi kamar bata ji komai ba ta bawa kanta shawara. Daurewa tayi kamar bata ji nauyin maganar ba tace "Yanzu dai kasan bazan ci abin baki ba" "Sure?" Yace yana mata kallon gefen ido. "Na fa girma" "If you say so" ya rausaya kansa sai kuma ya tashi tsaye "kinsan me? sai na sa kin karbi abin bakina kafin na koma Katsina" "Idan naki fa?" "Ki tambayeni duk abinda kike so. Amma nima idan nayi winning zan tambayeki" "Ka shirya bani tsarabata kawai" tace tana dariya ta tashi tayi waje da sauri. Sai da ta rufe kofar falon ta dafe kirjinta da yake bugu kamar zai ballo. Kofar ta kalla ta jingina da bango tana girgiza kai "Abin baki? Hmmuhmm, kai lallai ma Hamma Awwab dinnan idan ba bazan karba ba" kunya ta ji kamar me amma ta daure sosai tana bashi amsa saboda kada ya gane zancen na shigarta tana bashi wata ma'anar daban. Emzee yana kallonta shi ya gama wanke motar Mamansu Zainab har ya fara taya Ibrahim da yake wankin bus din da zasu tafi Sumaila a ciki. Dauraye hannuwansa yayi Ibrahim ya bata baya bai hangota ba ya karasa gabanta. "Ke da wa Adda?" Dantsen hannunsa ta riko tana dariyar jindadi "Emzee yau na koyi basarwa" Yasan Addarsa da shirirta "na tayaki murna, wa kika basar?" "Hamma Awwab mana, wai kasan me yace min kuwa?" Yatsunsa na nuni ya sanya a kunnuwansa ya toshesu "bana son ji don Allah" Shan kunu tayi tana harararsa "me yasa?" "Rike kayanki, hirarku ce" ya bata amsa yana komawa wurin Ibrahim. Haka kawai jikinsa ya bashi wani abin jin kunyar Awwab yayi don abinda zai korota waje ita kadai ba karami bane. Shi kuwa bai tashi jin ko ma meye ba a saka shi jin kunyar da za ta jima bata barshi ba su kuma su cigaba da harkokinsu. ********** 💕[02/11 7:30 AM] My 2nd Mtn: 26.💕 "Gulmata suka rinya yi maka?" Tayi maganar a cikin shagwabar da batayi niyya ba. Hakan yasa Awwab sake yin murmushi. Daga shigowarsa gidan zuwa yanzu idan ma yana da damuwa to tabi ruwa tabi iska Radhiya ta dauke masa ita. "Kinki zuwa na ganki ba sai na nemi labarinki ba" "Ba ga su Mama ka gani ba maimakon kayi hira dasu shine zasu kawo maka zancena?" Ta sake marairaice masa. "Kinsan me yasa na kasa zama na huta duk da tarin gajiyar da nayi?" "A'a" tace tana girgiza kai. "Because I missed you Alheran" yace suna hada idanu tayi saurin lumshe nata. Tayi karatu bare ace bata jin turanci bata fahimce shi ba. I miss you ai sai masoya a iya saninta. Shiyasa taji wata irin kunya ta saukar mata. Ko a jikinsa don iyakar gaskiyarsa kenan. Murna da sanin cewa ga inda take ya wadatar dashi ya hana shi sukunin duk wani hutu idan ba haduwa suka yi ba "sai da nazo na ga ashe ni kadai na damu dake, kina kallona kina basarwa" Maganarsa ta bata dariya kamar yadda ya fadeta yana yamutsa fuska shi ba'a kyauta masa ba "wasa ne wannan amma ni fa ban iya tuna ka ba ne sai labarin da Ummi ta bani" Hannu yasa ya karbi lemon da Fauziyya ta tsiyaya masa. Sai da ya kurba sau biyu ya sake kallonta "ko kadan?" "Me?" "Rashin tunawa dani din" "Ka ga fa nayi kankanta lokacin" Gefen girarsa ya shafa "kinga wannan tabon?" Daga inda take tana ganin duhun layin "bille ne ya karkace? Ko ka hadu da wanzamin da bai san aikinsa ba. Me ya hada tsakiyar goshi da gefen gira? Ko irin na gefen nan mai uku-uku aka so yi maka?" Ta rinka jero masa tambayoyi. "Na hadu da wanzamiya dai" Fauziya za ta fara dariya don gidansu kowa yasan tabon aikin Radhiya ne ya kalleta sai ta sake tashi. Wai meye ne Hamma yake korarsu...kodai, kodai...dan murmushi ta saki amma kuwa da tayi farinciki idan haka ne. Abincin da Zahra ta gama hadawa ta karbo don so take ta sake ganin gulma. "Ana wanzamai mata dama?" "Alheran sunanta ma" "Da gaske?" "Yakushina fa kika yi" yace yana kallon yadda ta ware idano ta saman kofin hannunsa. Tasowa tayi ta dawo kujerar gefensa yadda zata gani sosai tana ta karkata kai hagu da dama "Allah Hamma, ko dai don nace ban tunaka bane zaka dora min" ta rinka dage girarta duka biyu a tare tana cewa "eyye, eyye?" "Cute" ya furta a sanyaye ya rasa me yake damunsa tun da ta fito daga dakin. Wasu abubuwa take yi da suke tado masa da memories din kuruciyarsu. Ta bude ido ta lumshe, ta turo baki ta sha kunu ko murmushi. "Da kina yarinya kin fiye rigima da fada...uhmm harda kuka. Gashi naga alama babu wanda kika dena cikinsu." "Tsokanata akayi ne, amma yanzu na dena fada" Fauziyya da ta duka za ta zuba masa abincin a plate tace "A yaushe kika dena fadan?" "Babu ruwanki da hirarmu bar abincin ma zata zuba min idan na tashi ci. Tafi kawai ki barmu kinsan ba wurinku nazo ba" Dadi kamar ta zuba ruwa a kasa ta sha yace ba wurinsu yazo ba. Kai na rawa tana jujjuya idanu tace mata " yehhh sai a tafi kinji me Hamma Awwab dina yace. Dama na fada muku idan ya zo zai dena kula kowa sai ni, nima kuma in dena kula ku ehe" "Shikenan ka bata damar cigaba da raina mu ni da Zahra" Kallon tuhuma yayi mata "wai haka?" "Fada kawai take yi don ta hadamu, kowa ya shaideni a gidan nan wurin girmama manya ba daga nan ba" yanayin maganar kadai zai gane karya taje yi. Bata da innocent face, kana ganinta kasan akwai jini a jika. "Allah Ya shiryeki Radhiya" Fauziyya tace tana tafiya za ta je kaiwa Zahra tsirku. Abincin ya nuna mata ta soma zuba masa "ba kya son na kula kowa?" Ta dago kai "eh wallahi, ko na yau kawai kada kayi musu magana su gani duk kafi sona. Ni kadai ce kanwarka banda su" "Gobe zan koma Kt ba kya so nayi hira dasu Ibrahim?" Dena zuba abincin tayi tana jin babu dadi a ranta "gobe kuma Hamma ko sabawa bamuyi ba zaka koma?" Wannan karon shi ya fara janye idanunsa daga gareta. Ya rasa gane me yasa suna kallon juna sai yaji abu ya taba zuciyarsa. Ya dai alakanta hakan da dawo masa da tunanin baya da take yi ne. "Akwai wani sabon da ya rage msna bayan wanda muka yi in less than an hour?" Wuya ta shiga sosawa irin na marasa gaskiya tana sunkuyar da kai da murmushi. Dimple dinnan ya sake kallo ya miko hannu kamar zai saka yatsansa yadda ya saba yi mata a baya ya tallabo habarta da ragowar yatsunsa sai kuma yayi saurin janyewa. Alheran is not a child anymore ya yiwa kansa fada. "Na yarda kayi hirar minti goma goma da kowa su Baba kuma awa daya, sauran kuma duka nawa ne." "Bazaki gaji dani ba?" Bai san me ya kaishi yin tambayar ba. Yayi saurin datse bakinsa bayan ta fito. Da ido daya ta karkace kai tana kallonsa "hmmm na gane wato ka gaji dani ko? Nasan komai idan ana yi min irin haka saurin fahimta nake yi. Kora da hali kake min irin na Ummi idan ta gani da hirata" Hannu ya daga yana bata hakuri "ba haka nake nufi ba, yadda kike so haka za'ayi. A lokacin kowa ma sai a cire minti daya da rabi in kara miki" Murmushi ta saki tayi masa gwalo "na maka wayau" Girgiza kai kawai yayi yana jin nishadi da farinciki suna ratsa shi. ********** Malamijo ke zaune a tsakar dakinsa akan filo yana sharba gumi. Zafi ya ishe shi daga shi sai dogon wando Hajjo da tayi karkon zama kamar Yadikko saboda bakinta dake kwatarta a wurinsa tana masa firfita. "Ya kamata kaje asibiti fa, ka kwana ka tashi da abu daya ba'a zauna a gida ba" Daure fuska yayi ga azaba ta ishe shi da kyar yake magana "zaki biya min kudin asibitin ne?" "Lallai ma Malamijo, to don Allah zauna kada kaje ka gani idan zan damu. Ka bar kudin kar ka tabasu idan ciwo ya karasa ka a raba mana gado. Nasan a lalace idan ban saka dogon buri ba zan tashi da a kalla shanu uku manya." Ido ya ware yana jin kamar ya shakota amma jikinsa babu kwari. Ta turo dankwali gaba tana lissafi da yatsunta "kaga mafi girma a ciki in sa a danne a yanka min. In soya, in gasa, inyi miya. Kai har tafasasshe sai naci. Sauran biyun kuma in sayar nayi sababbin dinkuna kafin Allah Ya kawo bazawari" "Mmmugguwa, saaai kin riga..rigani mutuwa" "A hakan, karmai-kamai da kai kamar kazar mayu?" "Akwai mayyyyyyar da ta wuccceki ne?" Yace yana cije lebe. Yadikko ta dago labule ta shigo fuskarta da damuwa "Malamijo anya zaku cigaba da zaman nan kuwa haka? Use da Asabe fa suma irin lalurarka ta same su. Asabe sai kuka take da kyar na bata hakuri na fito" Hajjo na jin haka ta tashi da sauri "Yadikko kice ciwon na ango ne da amarensa. Wannan abu shi ake kira guzurin masoya. To ni nayi nan. Kayan lefen can da aka gama gani zan je in killace kada ayi sibare inzo banci nanin ba nanin ta cinyeni ace don ba ni na haifesu ba ina musu bakinciki na bari an kwashe musu kaya" Fita tayi tana rangaji da dariyar mugunta. Malamijo da amarensa duka sun kasa fitsari. Duka duka Asabe watanta uku a gidan ya cike gurbi da Use. Auren sati uku an wayi gari sun kasa fitsari. Shi tun jiya ya fara gashi yace a matse yake amma ko digo ya kasa yi. Bata gama gyara kayan ba Yadikko ta shigo babu walwala a fuskarta saboda yadda ta kula yana jin jiki. "Hajjo me ya kamata ayi ne, rashin fitsarin nan fa ba karamin abu bane. Malamijo sai zufa yaje yi yana numfarfashi" "Sai kiyi ta damun kanki Yadikko. Akan me? Nan yayi auren nan fa ya soma mana wulakancin da ya saba. Saboda alhaki kwikuyo ne da yace mu dena girki wai ya bamu hutu kannenmu suyi ai ga sakamako nan ya samo. Banda kwadayi irin na namiji yaran da basu fi yayi jikoki dasu ba wai sune kannenmu" "To dai a bar tone-tone mu kira su Habu yazo ko da motar da yake haya ne a kaisu asibiti. Zan tura a fadawa Salame ke kuma ki kira Innawuro ta fadawa Mairama itama su zo babansu ba lafiya sannan ga karbar lefe ma da basu san anyi ba" Ido Hajjo ta zaro "Ni shegiya inji dan daudu, da wane bakin zan fada musu mahaifinsu ya kamu da tagomashin soyayya? Kyaleni naji da aike gidan waccan mara mutumcin Salame. Amma Mairama ai akwai kunya taakaninmu, yarinyar mutumcinta yasa yanzu kunyarta ma nake ji" "Meye kuma tagomashin soyayya ni Yadikko?" "Sunan da ya dace da ciwon nasu kenan ai" Yadikko ma dariya ce ta kama ta. Sai yamma aka samu biyu cikin mazan gidan suka dawo. Dama daga Mairama sai taron maza. Matan da suka taso kuma halin Malamijo ke korar musu manema. To yanzu anyi sa'a mutum hudu cikinsu abin yazo tare. An aikawa Salame dan aiken ko kallo bai isheta ba kamar ba kaninta ba. Mairama kuma Bature ne ya kira lambar Baffa Habubakari ya fada masa. A daren ya nemi layin Major ya sanar dashi cewa a fada mata. ********** Hankalin Mairama ya tashi duk da bata san me ya sami Malamijo ba amma tunda aka fada mata tana ganin ba karamin abu bane. Major ya tsara musu tafiya washegari ganin duk ta tashi hankalinta. Dama motocin da yayi order biyu an riga an kawo su. Daya domin bukatarsa dayar kuma saboda Mami da kuma kai Zayyana makaranta da suke jiran a koma hutu ta fara SS1 sabon zangon karatu mai kamawa. Jibi zai tafi Sakkwato kaninsa zaiyi masa rakiya su kuma yace washegari su tafi sai su tsaya a Kano su dauki yaran. "Amma ina ganin motar zata yi muku kadan. Bus din da aka kai Awwab Kano kuma yace gobe zasu dawo. Dreban ya kamata ya huta haka shiyasa ba zan ce ya kwashe su ba" "Awwab ya tuka ba sai ya bimu a baya ba" Mami tace su kuma dan gidan Hussainarta Abdallah ne zai tuka su. "Bana son tukin Awwab a babbar hanya gudun nan nasa kamar yana iska". Mairama ta fara musu godiya sannan tace "da kun barshi Daddy a hakan ma nagode sosai wallahi. Ba sai an sake wata wahalar daukarsu ba. Shima Awwab din yana bukatar hutu" Mami ce mai kwantar mata da hankali tace "haba Ummin Awwab ki bar wannan godiyar mu dake duka daya ne. Babu matsala in sha Allah" Babban abinda zai kai Major wanda zasu hadu da Baffa Gide a Sakkwaton shine binciken dangin Zayyan na Nijar. Idan da gaske rashin idonsa a duniya yasa suka zare hannunsu daga kan iyalinsa ko kuma su ma karya Maikudi ya shara musu duk zai jiyo. Shi kanshi sojan da yake tura kudin zai baro bakin aikinsa ya taho don ransa ya baci fiye da ba Major akan rainin hankalin da Maikudi yayi masa. Idonsa idon Maikudi kawai yake jira. ********** Tun dare anyiwa Zainab waya game da zuwa Sumaila duba Malamijo. Ita bazata sami zuwa ba saboda Hadir gashi asibiti zasu koma. Tunda ba kwana zasuyi ba Mairama da su Radhiya ne kadai zasu kwana sai ta yiwa Ibrahim izinin fita duk da shine karfin taimaka mata akan babansa sai Emzee da yake taya shi sosai. "Yaya zakiyi da Baba" ya fara cewa da tace yaje. "Gara na fara sabawa, daga kai har Karami WEAC dinku ake jira a nema muku admission. In kana makaranta zanyi ta jiranka ne?" Godiya yayi mata don yana son bin 'yan uwansa amma baya son kwana saboda kada aikin yayi mata yawa. Dakin da aka sauki dreban gidansu Ghazalatu yaje ya tarar da Awwab ya karbi mukullin motar. Kudin mota da Zainab ta bayar a kai masa da zai koma Katsina yaje kai masa. Iyalan gidan su ma duka sati mai zuwa zasu taho Katsinan saboda bikin da yake na gida duka a garesu. Shi kadai ya koma ciki Awwab ya zauna akan dan ginin da ya zagaye flowers din da aka shuka daga jikin bangon gidan. Waya yake son yi da Ghazalatu yau tun da ya taho tana fushi basu sake magana ba. Da sauri ta dauka da ya kira sai kuma tayi shiru don ta nuna masa fushinta na kin kiranta da wuri. "My G fushin ne ya tashi?" Nishadi yake ji sosai yadda suka rinka hira da Alheran kamar basu rabu ba. Kusan komai na rayuwarta da zata iya tunawa ta fada masa sai yake ga kamar a gabansa ta tashi. "Idan nayi magana kace na fiye kishi ko korafi. Tun yaushe ka isa amma ko text ban samu ba talkless of waya." Sai yaji babu dadi don ya sani bai kyauta mata ba. Hakuri ya bata don bashi da girman kai ko kadan. Yayi mata laifi dole ya kwantar da kai ya rarrasheta. Kusan wayar minti talatin suka yi sai da yaji ana masa warning na karewar credit. "Zan kiraki gobe in sha Allah, zamu je duba baban Ummi a garinsu. Dawowarmu sai wurin jibi kenan dasu Mami" "Mami ba tana gida ba?" "Zasu taho da Ummina gobe sai mu wuce tare" "Yayana kace mata zani please. Da saasafe sai na koma gidan mu taho tare" Yaji dadi sosai saboda shima ya soma kewarta. Suna gama wayar yace ta kira Mami din credit dinsa ya kare. Ta kirata ta wayance da cewa wurinsu Zahra take son zuwa. Mami tace to ta zauna su zasu biyo su dauketa. Falon ya koma ya same su kowa na cin abincin dare banda Radhiya da tasa plate a gaba tana kallonsu. Akan doguwar kujera ya zauna ya kwantar da kansa baya. Alamun idanu yaji a kansa ya dago. Ai kuwa duka shi suke kallo har Radhiya "What?" Yace yana kallon kansa. Fauziyya ta nuna masa plate din gaban Radhiya. Taliya ce fara da sauce din ganyen alayyahu da ugu sai balangu mai dan karen dadi da Ibrahim da Emzee suka siyo. Dama yanzu sune 'yan zuwa aike. "Me ya sami abincin Alheran?" Kunya taji ta kasa fada masa bayan cika bakin da ta gama. Zayyana kuwa tace "kowa shaida ne Adda Radhiya zaki min gyaran akwatina tunda kin kasa" "Dama akwai abinda zaki kasa?" Yayi tambayar yana kallonta. Ta dai yi saranda inji bature kaudin nata bai kai nan ba ashe ta gama cika baki. Tana ganinsa taji ko da wasa bazata iya fada masa zaman me take yi ba. "Emzee me ya kama bakin yayarka ne ta kasa magana?" "Babu ruwana ni dai" ya cigaba da cin abincinsa yana murmushi. "Ni bari na fada maka Hamma" Ibrahim yace yana kallo Radhiya ta daure fuska "Zayyana tace kafi sonta shine Radhiya tace don bata nan ne dama. To shine Zayyana tace mata ita fa ko me take so kana yi mata. Idan kana gida hatta abinci tare kuke ci. Shine Radhiya tace wai wannan na gaban nata kaine kace ta zuba muku tare kafin ka shigo. Betting su ka yi" Zamowa yayi daga kan kujerar yana janyo plate din gabansa bayan ya tankwashe kafafunsa. "Babu ruwana da wasanninku, Alheran matso mu ci yunwa nake ji" Bude baki su kayi cike da mamaki harda ita Radhiyan. Kifta mata ido Awwab yayi a kunyace ta matso ya dauki fork a kan tray din da aka kawo kwanukan abincin. "Muyi kama-kama irin na yara?" Yayi magana yana kallon idanunta. Tsabar kunya tashi tayi zata gudu. "Ba fa ki isa ba, wannan abincin na mutum biyu ne so just sit mu cinye" "Kaci ka rage min Hamma Awwab" tace tana kallon su Zahra tana neman taimako. "Tare zamu ci kada a barki da gyaran akwati" "Babu komai zan iya" Hade rai yayi "ina wasa dake ne?" Ba shiri ta zauna tana bashi hakuri sai kuma ta waiga tana kallon kowa an zuba musu ido "don Allah ka bari su gama duka su tafi kunyarsu nake ji" "Kin tabbata zaki zauna muci idan sun tafi?" "Eh mana" "Kamar gaske" Bude baki tayi za ta sake magana kawai ya tura mata fork din da ya ciko da abinci tun dazu. Ibrahim ya dora hannu ya rufewa Emzee idanun da ya zaro sun ga abinda basu saba ba. Zahra ma sai ta rufe nata ta sakalo hannuwanta akan idanun Fauziyya da Zayyana suna faman dariya. Radhiya kasa motsi tayi sai idanu da take ta kiftawa ba kakkautawa. Awwab yayi murmushi duk da yayi ne kawai saboda kannensa amma abin ya tsaya masa a rai dakewa kawai yayi ya dauko kofin da aka cika da juice ya miko saitin bakinta. "Sorry na cika miki baki, hadiye ki sha wannan" A guje Radhiya ta bar falon kafin ta kasa numfashi. Yau ta gamu da gamonta. Ita bata taba kunyar wani mahaluki ba kamar yadda taji Awwab ya gama da ita ba yau. 💕[02/11 7:31 AM] My 2nd Mtn: 27 A.💕 Shadaya da rabi mutanen Katsina suka iso. Radhiya sai murna ta ga Umminta ta kara kyau. Mairama hadaddiyar mace ce da rayuwa ta yiwa cikas. Kwanakin da tayi a Katsina da kulawar Mami yasa jikinta ya kara kyau kamar ba ita ba. Zahra da Fauziyya na ganin Ghazalatu suka sa ihun murna don basu san da ita za'a zo ba. Mami tace bata san lokacin da zasu girma ba irin wannan tsalle da suke yi. Ita Ghazalatu hankalinta yana kan Radhiya dake zaune a gefen Umminta ana mata tsiyar Ummin na tureta bata ma san tana yi ba. Gaisawa suka yi aka dan taba hira Mami tace gara su zo su dau hanya saboda a ranar suke son dawowa. "Ku tsaya kuci abinci an gama tun dazu" Mami tace "muci abinci muji bacci kenan, ni kin sanni da na koshi sai na fara neman wurin kwanciya" "Shiyasa nake jin alamun kinyi ukun yadda na sanki ashe" Mairama tace tana murmushi. Yaran dariya suke yi Zainab tace lokaci ne ai, shekarunsu na soma ja zasu fara ajiye kiba ko da ta girma ce. "Mama banda ni a kibar, mu sojoji ina muka ga lokacin yin kiba muna faman guje-guje a daji" Sai da kowa ya dara Fauziyya ta tabo Ghazalatu "kinga kanwar Hamma ko, Radhiya ake ce mata. Yini daya kika yi da ita sai cikinki ya kusa ciwo don dariya" "Na ganta". Gabadaya ranta babu dadi tun da ta ga wacece Alheran din da Awwab yake ta rawar kafa a kai. Tayi zaton wata 'yar yarinya zata gani da bata fi Zayyana ko kasa da haka ba. Dama jiya saboda wannan budurwar mai idanu a tsatstsaye ya taho Kano ya barta. Shigowar Awwab da Abdallah wanda ya kawo su Mami dan Hussainarta daga waje kenan daidai lokacin da Mamin take ce mata. "Idan ke soja ce bakiyi kibar ba mijinki da ba soja ba zaiyi ne" Tsuke baki tayi tana kada yatsa "No, no, no, no , no Mami. Ni likita zan aura fa. Kinsan shima aikinsu babu zama bazaiyi kibar ba" "Mara kunya" Mairama tace tana daka mata duka a baya. Su Ibrahim an sami abinda ake so suna ta dariya. Zainab ta maimaita musu abinda Radhiyan tace dazu wai ta raina kowa idan ba soja da likita ba. "Mama mu dasu aikin ceton rai muke yi shiyasa kowa bai kai mu ba" Mairama sarkin kunya sai ta soma tsoron kada Radhiyan ta fadi wani abin da yafi wannan. Ta tuna ranar da tace mata tana abu kamar ba bafillatana ba. Ita kuwa ta ce dama ba ita bace, su Sakkwatawa ne. "Ku barni da ita kwanannan zanyi mata miji a aurar da ita mu huta" inji Zainab. Tun shigowarsu Awwab yake kallon yadda take ta zuba surutu. Dauke kansa yayi ya kalli Ghazalatu ya sakar mata murmushi ta maida masa. Ibrahim ne yace "Mama ki samo mata malamin makaranta kawai" "Tabdi, yo ni malamin makaranta ba sai dai na zane shi da dorinarsa ba. Tsorona zai rinka ji" Fauziyya da ta saka musu ido ita da Awwab tun jiya kuma take fatan hakan tace "ina jin zaki fi dacewa da dreban jirgin sama" Mami da Zainab har Mairama sai su ka yi murmushi. Ko dai Fauziyyan ta ga wata alama ne take hasashen abinda suke shiryawa. Awwab da yake shan ruwa cire kofin yayi yana son jin amsarta. Abinka da 'Yar soja ta hade rai "ke kadai ce bakya sona Adda Fauziyya. Me zanyi da dreba sai kace ta kare min?" Kowa yayi shiru yana kallon Awwab da ya zuba mata idanu harda Ghazalatu da misalin na Fauziyya ya kona mata rai. Bata san suna yi ba bare ta gyara zancen. Zahra ce ta tace "mun ganku a rana ke da Hamma Awwab tunda shima dreban jirgin ne" Ba arziki Radhiya ta tashi yana tsaye ya harde hannuwansa a kirji. Tayi zaton zaiyi fushi sai ta ga shi ya fara dariya kafin sauran "wato mu sai ta karewa mace za ta auremu ko" "Wayo Adda Fauziyya tayi min ba haka nake nufi ba. Maimakon tace pilot yadda zan fahimta" "Sannu Queen Elizabeth wato sai anyi turanci zaki fahimta" Ibrahim yace. "Ka kiyayeni Surbajo" A dolensa yayi shiru da yaji abin zai dawo kansa. Tsokanarta suka cigaba da yi tana karewa kanta. Awwab yana kallon Ghazalatu yace da Radhiya "ki shirya zata kare miki kwanannan kuwa don sai kin auri pilot. Kafin nan kuma ki zamarwa matata 'yar aiki" Mama da Zainab suka kalli juna suna gyada kai da murmushi. Bakin mota suka firfito Mami da Ummi zasu bi karamar motar sauran kowa yace bus din da Awwab zai tuka zasu shiga. Radhiya da jikinta yayi sanyi tana jin babu dadi akan maganar da tayi tace ita ma motarsu zata shiga sai ta zauna a gaba. "Koma cikin 'yan uwanki Radhiya" Zainab tace tana turata bakin daya motar. Awwab ta kalla ko zaiyi magana sai ta kula hirarsa kawai yake yi da Ghazalatu. Juyowa yayi ya kalli Radhiya duk ta zama wata salihar karfi da yaji "ina zuwa" ya cewa Ghazalatu ya taho inda take tsaye a jikin motar. "Zo in nuna miki wani abu" "Wai ba fushi kayi da abinda nace ba kake yi min magana" Murmushi yayi "Silly girl, kawai sai nayi fushi bayan nasan ta kusa kare miki kwanannan...auren dreba ba fashi" "Shine ka barni inata damuwa, kuma a gaba zan zauna inyi ta ganinka tunda yau zaku dawo" Wurin wata katuwar fulawa inda Ghazalatu ke tsaye suka nufa. Suna jiran iyayensu su gama maganar da suke yi su dau hanya ne shiyasa basu tafi ba. "Dama babu mai zama wurinki ne nima inyi ta kallonki" Dariya tayi fuskar Ghazalatu ta hade tsaf da kishi. Awwab yasan me yake bata mata rai don yanzu ta gama fada masa ita bata son yadda yake yiwa Alheran dinnan bayan ba karamar yarinya bace. Domin ya kwantar mata da hankali yaje ya kira ta. "My G, ga Alheran kanwata. Alheran ga Ghazalatu kanwata kuma matar da zan aura" Sai yanzu hankalin Ghazalatu ya kwanta sosai. Ta kurawa Radhiya ido sai ta ga yarinyar ko a jikinta sai ma dariyar ta take yi fuskarta ta tana wani annuri. Dage girrarta duka biyun ta rinka yi yadda ta saba idan zata yi tsokana " Eyye eyye Hamma shine kace zanyi aiki a gidanka? Naji zan rinka tayata indai itace matar" "Bana bukatar house girl so kiyi zamanki" Ghazalatu tace tana shan kamshi. Fuskar Awwab kadai zaka kalla kasan kalaman basuyi masa ba. "House girl?" Yace yana kankance idanu. Ta fuskanci ransa ne ya baci sai ta wayance "naji kace za tayi min aiki ne dazu" "Lallai wannan 'yar wulakanci ce" Radhiya tace a ranta. Ita bata san maganar wasa bane da zata yi tunanin da gaske aiki zata je yi mata. Hamma Awwab yafi karfin komai a wurinta tunda yake son Umminta da babanta da ita kanta. Kuma ba wani abu bane a wurinta ta taya matarsa aiki amma wallahi ba dai taje a house girl ba. Idan bata gwaba mata magana ko yaya bane tasan bazata ji dadi ba shiyasa ta ajiye katon murmushi a fuskarta tace "ko babu albashi zanyi miki aikin ma, kinsan mu 'yan kauye bamu san komai ba sai bautawa 'yan birni" "No ki barshi fa bana bukata, idan ina so Yayana zai nemo min" " Yes dai inzo inyi ko babu komai zan hutar da Hammana barnar kudi" Hannuwansa ya zuba a aljihu yana kallon ikon Allah. Rigima ke neman tashi tsakaninsu daga su gaisa. Daure fuska yayi yace "ku wuce ku shiga mu tafi" Suna zuwa bakin motar Ibrahim zai bude gaba ya shiga saboda yana son Awwab ya koya masa tuki Ghazalatu ta riga shi budewa itama tana son zama kusa da masoyinta. Radhiya da ta fisu iyawa tayi sauri ta shige ta kofar bayan ta haura gaba. Awwab kansa sai ganinta yayi ta kusa fado masa garin sauri. Gyara zamanta tayi ta ballawa Ghazalatu da Ibrahim harara suna tsaye suna kallon abinda tayi. "Ni dama ga wurina can kusa da Zeezee" Ibrahim yace yana shiga bayan inda Emzee ke yi masa dariya. Ghazalatu ta kalli Awwab tana jira yayi magana "kace ta koma baya ina son muyi magana" "Idan muna dawowa sai ki zauna a nan din kinji." Tsabar bakinciki ji tayi kamar tasa ihu. Mami daga cikin tasu motar tace ta shiga su tafi rana tana kara yi. Hararar Radhiya tayi ita kuma tayi mata gwalo. "Bansan mutum nayi ba sai naji a jikina" "Alheran" taji yace muryarsa a dake sannan ya kalli Ghazalatu da take ta cika tana batsewa "ki shiga ki zauna mu tafi" Daurewar da yayi yasa ta shige ba don ta hakura ba. Radhiya da take kusa dashi kuwa ji tayi kamar ta koma baya ita ma. Tukinsa kawai yake yi wanda baya masa dadi saboda bin bayan Abdallah da dole sai yayi tunda bai san hanya ba. Motar duk sai tayi musu shiru mai bakin tsoro ya hanata magana Zayyana har ta soma gyangyadi a jikin Zahra. Su basu ma san me yake faruwa ba sai Ibrahim da yake tunanin saboda zaman gaba ne kawai. Can dai taji shirun ya isheta ta dago a hankali ta saci kallonsa. Titi dai yake kallo har yanzu babu wannan sakin fuskar. "Hamma" Radhiya ta kira sunansa a tausashe. "Kar ki dameni please" Shiru tayi ran sojoji ya baci. Ita kadai zaiyi fushi da ita bai ji masoyiyar tasa tana kiranta housegirl ba. Tura baki tayi ta juya duk jikinta tana kallon waje. Shima satar kallonta yayi yayi gajeren murmushi. Da gaske dai Alheran dinsa bata chanja ba sai ma abinda yayi gaba. Su mata abin rigima baya yi musu kadan ya kula. Su biyun kowa matsayinta daban to me ya kawo rigimar. Ko don Ghazalatu tace mata house girl? Shima kalmar bata yi masa dadi ba. Duka su biyun sai yayi aikin basu hakuri kenan. Haka kawai zasu tayar masa da hankali kamar wasu kishiyoyi. Ta mudubi ya hango Ghazalatu ita ma fuska babu wakwala kamar ma kuka take shirin yi. A take ya jinjinawa masu mata biyu. 💕[02/11 7:31 AM] My 2nd Mtn: 27 B.💕 Sun isa Sumaila karfe biyu na rana a gajiye saboda tashin wuri da suka yi. Emzee ne ya koma jagora da suka shigo garin shiyasa tasu motar take gaba. Awwab ba tsayawa Emzee din ya fita da sauri saboda magana da yake son yi wa Ummin tasu. Gefe ya ja ta ana kokarin fitowa da kayan da ita kanta bata san da zamansu ba a boot. "Ummi wai kuwa sun san zamu zo da baki?" Yace yana rage murya. "Na fadawa Innawuro da ta kira nace ta sanar dasu tunda kaga ba waya gareni ba. Menene?" Da damuwa a fuskarsa yace "kada muje a rasa abinda za'a basu nasan bazaki ji dadi ba" Murmushi Mairama tayi. Zayyan dinta akwai hankali da nutsuwa ga zurfin tunani. Rashin abin tarbar baki tabbas zai iya faruwa don tasan halin gidan nasu "to yanzu me ya kamata ayi?" "Idan kina da kudi kawo naje na siyo gurasa da tsire kawai" Karamar jakarta ta mika masa. Dubu uku ya cire cikin kudin da Ardo ya bata ne da zasu taho. Ya tafi tana ta masa addu'a a zuciyarta. Radhiya kuma ta kama kofa za ta bude Awwab ya danna central lock. A zuciye ta juyo "bude min" "Ko nima balotellin zaki yi min ne? Zai fi miki sauki akan wannan juya idanun" bayansa ya juya "Ghazalatu zauna magana zamuyi" Murtuke fuska tayi itama ya kallesu ya tabe baki. Mata, mata halinku sai ku. Su Zayyana duk sun fita sun bi bayan iyayensu cikin gidan. Basu san me yasa ya tsayar da su Radhiya ba amma ko ma meye tabbas basu ga alamun wasa a tare da yayan nasu ba. "Kun gama fushin ko har yanzu da saura?" Ghazalatu dama jira take yi "don na biyoka shine zaka wulakantani akan wannan yarinyar kamar wata kishiyata? Tunda muka zo sai kayi mata magana sau uku baka yi min daya ba. Sannan nazo shiga gaba ta shige duka ka kyaleta. Idan wani abu ne tsakaninku gara ka fada min da wuri na san matsayina. Amma bazai yiwu ta rinka jin kanta kamar wata a wurinka ba tana neman shiga tsakaninmu" "Kin gama? To bari kiji in fada miki. Alheran wata ce a wurina Ghazalatu kuma bazan yarda kici mata mutumci ba. She is my sister kamar yadda na dauki su Zahra haka ita ma na dauketa. Idan ma kishi zakiyi ba da ita zakiyi ba. Ki bari sai kin hadu da wadda take da matsayi irin naki a wurina" Dazu gani take wannan Ghazalatun take ko wa tayi mata rashin mutumci amma maganar Awwab ta yanzu tafi kona mata rai akan komai duk da cewa gaskiya ce ya fada. Ita din kanwa take a wurinsa amma meyasa kalaman nasa suka yi mata zafi haka. Daga haduwa dashi kwana daya kawai take neman matsayi fiye da abinda zai iya bata. To me ma take nema ta tambayi zuciyarta. Ranta taji ya cunkushe gabadaya taji ta tsani zaman da take yi tare dasu a motar. Dago kai tayi kamar ba ita bace zuciyarta take kai kawo a abinda ta kasa gane zahirinsa ta kalli Ghazalatu. "Matar Hamma kiyi hakuri don Allah. Haushi naji da kika kirani house girl. Ke da kishiya sai dai mota in sha Allahu" Awwab kallonta yayi yadda ta nutsu tana magana kamar ba ita ba. Suka hada ido tayi masa wani murmushi da ya tsaya masa a rai yaji kamar ya dora hannunsa a kumatunta da ya lotsa. "Kaima kayi hakuri bazan kara ba" Tana kaiwa nan ta kama kofar zata bude sai ya cire lock din ta fita tare da duka tunaninsa kamar ta zare masa duk wani kuzari da yake jikinsa. A katon soron gidan ta ya da zango jikin wani dan tudun siminti da akayi domin zama. Abinda ya bata mamaki bai wuce kukan da ta fashe dashi sosai ba. Ji take idan bata yi ba ma zuciyarta zata iya bugawa. Kukan na meye? Oho, itama bata sani ba. Abu daya ne kawai ya tsaya mata a rai kalmomin Hammanta na karshe wai Ghazalatu ta jira sai ta hadu da mai matsayi irin nata a wurinsa sannan tayi kishi. Tsaki taja tana jan hanci "Mtswwww in kun ga dama ku cinye juna karewarta, aikin banza. Dadinta dai nima Kawu Zakari ina komawa zai ce yana sona. Mu za'a yiwa burga da wata soyayya? Maza na fita filin yaki ko su je ceton rai a asibiti kai ka makale a jirgin sama kamar tsuntsu wa zai so ka idan ba wannan mai kwalakwalan idanun ba dama" Hannu tasa ta share hawayenta bayan ta gama rarrashin kanta ta shiga gidan da sallama. A can mota kuwa Awwab da Ghazalatu an bude sabon shafi sai dai a wurinsa babu wannan dokin jikinsa kamar wanda aka yiwa duka haka yake ji. Su ma tana shiga suna shigowa. Tabarmi ne aka shimfida daga can gefe inda inuwa take don dakunan gidan babu mai girman da zasu zauna a wadace da su da kuma tawagar Malamijo da suka zo kallon 'yan gayu. Akan abin sallah yake zaune ya mike kafafu dawowarsu kenan daga asibiti an zuke fitsarin an hadosu da tulin magunguna. Sallamar baki yasa aka kawo masa babbar riga ya saka ya rufe kasusuwan kirjinsa. Radhiya ya hango zai fara tsokanarta sai da ta matso ya kula idanunta sunyi ja sosai. "Kukan me kika yi ke kuma?" Kamshin turaren Awwab kawai ta ji a bayanta ta gane ya shigo shima. Gashi ana ta kallonta idanunta sunyi ja haka saman hancinta. "Ji nayi kamar ana kuka ance ka tafi shine na fara nawa nima. Ashe ashe kana nan." "Kaniyarki" Malamijo yace ya yi mata dakuwa "Mairama ki rasa da wa zaki zo gidan nan sai da wannan aljanar 'yar taki, ko wancan hutun da kika turo su ni banji dadin zama da ita ba. Sau biyu tana yi min barna a gona" Awwab sam hankalinsa kasa kwanciya yayi da aka ce tayi kuka. Bayan ya gaisa da mutanen gidan da suke wurin fuskarta ya rinka lalube yana son hada ido da ita amma fafur taki. Baya so ya zama sanadin kukanta ko kadan. Muryarta ya tsinkaya tana cewa "wai me ya sameka ne Malamijo, ciwon me kake?" Hajjo ta soma dariya za ta tona masa asiri a gaban 'yan gayu yayi saurin cewa "zazzabi ne mai zafi ya damkeni kamar bazan kai labari ba. Ai naci wahala ba kadan ba. Yanzu ma daga asibiti nake" Sannu da adduar samun sauki suka yi masa. Yadikko ta soma cigiyar Emzee shine Mairama tace ya tafi sayen gurasa da tsire wai yana sha'awa. Hakanan Malamijo ya tsargu ya daure ya cije yace a kira guda cikin samarin gidan ya yanka kaji uku ayi musu farfesu. Mami ce tace " Kada ka damu Baba muna sallah zamu juya akwai tafiya a gabanmu. Ibrahim idan Karami ya dawo ku shigo da kayan nan ciki" Nan fa hankalinsa ya tattara yayi waje. Ba dadewa Emzee ya dawo da ledoji a hannu. Ya sayo gurasar da nama a wadace harda lemuka irin su cway, lacasera da maltina masu sanyi. Ashe 'yan matan yunwa suke ji. Kafin Hajjo ta gama dafa shinkafar da Malamijo ya aunar mata bayan ya koma daki daga buhu daya cikin wanda su Mami suka kawo don kwarewa a tsiya har sun koshi. Sallah kasaru suka gabatar azahar da la'asar sannan suka ce zasu koma. Idan sun isa da wuri ma Katsina zasu wuce kawai saboda kada su yiwa Zainab yawa a gida. Da sauri Radhiya ta dago kai rike da gurasa a hannu sai lokacin take ci ta kalli Awwab. Hada ido su ka yi shima tun dazu ita yake kallo. Kin kula shi da take yi shine yake damunsa. Kwana biyar Mairama tace zasuyi a nan sannan su wuce Rugar Barkindo. Sai bikin su Zahra ya rage sati daya zasu koma Katsina. "Wannan dan samarin baici komai ba zaku tafi. Radhiya ko saurayinki ne kika kawo baki gabatar min dashi ba?" Malamijo yace yana kallon Awwab. Yaron da gani akwai maiko maiko zai so ya auri jikar tasa. Murguda baki tayi da ta ga Ghazalatu ta sha kunu "idan ma kishi kake yi to ka dena Malamijo, ka jira sai na sami mai matsayi daidai da naka amma ba wannan ba." Yanzu ya gano bakin zaren. Da gaske maganarsa ce ta bata mata rai harda kuka don sai da ya gano ja da kankancewar da idanun nata suka yi. Da ya juya kalaman a bakinsu sai ya ga rashin dacewarsu a dazun. Mami haka nan ta fara zargin ko Awwab din ya yiwa Radhiya wani abin ne ya bata mata rai. Bazasu so ayi aure basa son juna ba. 'Yar dabarar manya ta kirkiro wadda bata baude da yanayin Awwab din ba a yadda ta san shi "haka yake baya son cin abinci, ga tuki a gabansa mai nisa" "Ke zuba masa abinci ki kai masa wajen soro tunda babu kowa a wurin. Kila kunya yake ji ko dan Ummi" Mairama tace tana murmushi. Hakan yayi masa daidai har ransa. Abincin da Hajjo ta dafa da wanda Emzee ya siyo ta zuba masa a plates biyu ta dora akan tray tayi gaba batare da tayi masa magana ba. Ghazalatu kamar ta bisu sai ta tuna bayan fitarta dazu daga motar yadda ya jaddada mata son da yake mata. Tayi ta gama iyayinta ta koma kauyensu kowa ma ya huta. Wurin yana da fadi daga kan tudun dazu ta ajiye abincin ta koma daukar tabarma suka yi kicibus. Wai sai tayi masa murmushi a zuwan komai lafiya shima ya maida mata. Da ta kawo tabarmar yana zaune a gefen abincin ta shimfida ta sauke masa a kasa. "Hamma sauko kaci kada kuyi dare" Kura mata idanu yayi sai da taji kallon ya hanata motsi sannan ya sauko ya zauna a kan tabarmar ya tankwashe kafafunsa. "Zauna mu ci" "Na koshi" "Ban isa da ke ba ko?" Taji yace a hankali yana daukar cokali. Bata so yana magana irin haka sai ta taji zuciyarta tayi wani iri. Zama tayi a daya bangaren tray din ta tankwashe kafa yadda yayi. Cokali daya ne a ciki ya debi abincin yaci ya mika mata. Satar kallonsa tayi ya dage mata gira da ido yayi mata nuni da taci. Sai da ta sauke numfashi tana kunyar wannan abu ta rufe ido taci da cokalin da ya fito daga bakin Hamma Awwab. Karba yayi ya sake ci ya kuma mika mata. Za tayi magana yasa hannunsa a kan lebensa sai ta hakura. Duk loma daya sai ya mika mata har suka cinye abincin gabadaya. "Wannan gurasar dai bani da inda zan cusa ta ki mayar ciki" Dama ta kagu ta tashi ta kinkimi tray din za ta gudu ya danne gefensa. "Ban gama magana ba" Komawa tayi ta zauna ba don taso ba taji yace "I am sorry Alheran. Nazo ina ta yi miki laifi ba da niyya ba" Sake karyar mata da zuciya maganarsa tayi. Shi kam bashi da girman kai. Wai ita dinnan kanwar bayansa 'yar kauye yake bawa hakuri. "An daure harshen ne? Talk" Rufe ido tayi sai hawaye sharrr kamar famfo. Ta rasa gane irin emotions din da suke yawo a zuciyarta yau dinnan. Hankali a tashe yace "Ya Allah, me nayi miki kuma?" "Nima ban sani ba Hamma" tace tana kara fashewa da wani kukan. Me ya sami zuciyarta ne a cikin kankanin lokaci? Rabonta da kuka tun farkon zuwan su Mami rugarsu da ana bada labarin abinda kawunsu Maikudi yayi. Kuka tayi harda shessheka Awwab bai hanata ba har ta gama don kanta ya bata tissue irin ya ledar nan karama ta goge idanunta. "Feeling better?" Ta gyada kai tana kallon kwanukan gabanta. "Good, yanzu ki fada min tsakani da Allah me ya same ki? Nine ko?" Rasa me za ta ce masa tayi ta kare da cewa "ba kaine kake murna zaka tafi ba" "Ke kuma ba kya so na tafi?" Kada fa ya fassarata ta soma tunani "dena fada kada budurwarka taji. Duk baka tambayeni labarin komai nawa ba zaka koma kila bazan kuma ganinka ba sai an dade. Shine naji raina ya baci" "Sai nake ji kamar dai maganata ta dazu ce ta baki haushi. Amma nima bana son tafiyar ko sabawa bamu gama yi ba ko" yayi yar dariya. "Eh, ko askina ban fada maka me yasa akayi min ba" Sai da yayi dariya sosai yace "an gaya miki ni bana tsoron kiyi min balotellin ne? Ina sane naki tambaya kada na janyowa kaina" "Ashe kai matsoraci ne" ta kyalkyale da dariya kamar ba ita ta gama kuka ba. Sweet ya dauko daga aljihunsa irin mai mint dinnan ya bare ya jefa a baki yana dariyar matsoracin da ta kira shi. "Dazu ka raba abin leda baka bani ba yanzu ma a gabana ka shanye alawar? Kuma nice karama ni ya kamata ka bawa" "Sorry gashi in kina so" ya cirota daga bakinsa dama niyyarsa kenan. Wata zuciyar tana kwabarta wata tana ingizata har ta mika hannu tayi saurin janyewa "wayo zaka yi min, na tuna me kace dazu" "Ke dai kina kyankyamin abin bakina kawai" "Haba dai..." bata rufe bakin ba ya saka mata sauran da ya rage har hannunsa yana taba lebenta. Saurin tashi tsaye yayi ita kuwa ta rasa me zata yi ma. "Ki rage min kinga kadan na sha" Lumshe ido tayi tana tsotsar alawar yana kallon yadda bakinta yake motsawa yana jin kamar ya taya shi. Girgiza kai yayi da sauri. Lafiyata kalau kuwa ya tambayi kansa. "Ahhhh" Radhiya tace ta bude bakin ta mike tsaye yadda zai gano cikin bakin nata sosai. Ta shanye alawar saura yar kadan. "Cewa nayi ki rage min fa" "Nima bata isheni ba. Babu kari?" "Zan gamu dake ne, muje ciki su fito bana jin zamu iya wucewa a yau sai dai mu kwana a Kano" tafiya ciki ya soma yi. "Hamma gashi" ya juyo ta miko masa yar karamar sweet din ya karba yana kallon cikin kwayar idonunta ya saka a bakinsa. Bata sani ba ko shima yaji amma ita dai wani abu ne ya zarga mata har kasan zuciyarta. [11/2, 6:42 AM🏽 M🏽 : 28. 💕 Basu dade da fita ba Daddy ya kira Mami yana tambayarta hanya da mai jiki, su ma shigarsu Sakkwato kenan. Ya bukaci gaisawa da Malamijo wanda hakan ba karamin dadi yayi masa ba. Da Mami ta sake karba ne yake bata shawarar me zai hana su kwana washegari su kama hanya da wuri. Banda dare da ya tabbatar sai sunyi a hanya yana ganin ko babu komai itama Mairama sun mutunta ta. Zata ji dadi su kwana yadda itama taje nasu gidajen ta kwana. Mami dama harda tsoron dora musu nauyi da take yi yace duka babu komai kwana daya dai ta sanar da Ummin Awwab yasan zata yi farinciki. "Ummi yanzu Daddy yake cewa gara mu kwana saboda dare" Murmushi Mairama tayi da ya nuna jindadinta kamar yadda Major yayi hasashe. Baza a rasa dakunan da za'a sauke su ba. Abinci kuwa bata da matsala tunda da 'yan kudadenta. Zata bayar ne a siyo abinda zata fita kunyarsu. "Wannan murmushi Ummi to me yasa baki fada min kina so mu kwana ba? Duk daya muke fa" "Nasan kinyi haka ne don kada ki dora min nauyi. Amma zanfi so ku kwana ko daya ne a gidan da bani da tamkarsa" Yadikko da Hajjo ta sanarwa Malamijo na ji yasa aka taso kannenta ya bada umarnin a gyara dakuna biyu daya domin mazan dayan kuma na 'yan mata. Ita Hajjo tunda ita ke da girki 'yarta zata gyarawa Mairama da Mami nata dakin. Baki masu alheri irin wannan karramasu ya zama wajibi a wurin Malamijo ko don ya kara samun wani ihsanin kafin su tafi. "Karami jeka ka fadawa yayanku ya nutsu yaci abincin tunda babu tafiyar" ********** Kallon kallo suke yi daga bayan Awwab da ya juyawa kofa suka ji ana gyaran murya. Ba kowa bane illa Emzee wanda ya gama ganin musayar sweet. Shi ba abin ya juya ko yace bai gani ba. Murmushi ne ya subuce masa da suka hada ido da Awwab. "Dama Mami tace na fada maka yanzu Daddy ya kira yace ku hakura da bin hanya yamma tayi" "Bari naje na sameta, ko Kano muka koma mun rage wani abin" Tafiya yayi Radhiya ta tsaya dauko kwanukan da tabarma. Emzee ya karbi tray din tana nade tabarmar yace "Allah Sarki bawan Allah" "Wa?" "Dr Kawu Zakari mana" Gabadaya daburcewa tayi "me...me..ya same shi?" Dariyar da bai fiye yi ba ya yi mata ganin duk ta rude irin na marasa gaskiya "babu komai na tuna irin son da kike yi masa ne a raina nace dan gata. Idan ku ka yi aure alawa zaki rinka bashi" Borin kunya ya kamata ta fara fadan da babu gaira babu dalili. Dariya ta sake bawa Emzee ya sakalo hannunsa a wuyanta "kinga dai bance komai ba, idan kika tona kanki ba ruwana" Baki ta bude tana harararsa, wai me yake nufi ne. Aljihunsa ya rinka lalubawa ya zazzagesu yana cewa "rufe bakin mai alawar ya shiga ciki ni kuma ko kuli babu a jikina" "Kwana biyu jikinka bai karbi sako ba shiyasa kake damuna" tace tana daga hannu za ta kai masa duka ya gudu tana jiyo dariyarsa. Har yanzu babu wanda ya tashi daga tsakar gidan. Awwab ta nemo da ido ya dan durkusa a gaban Mami yana rokonta ko Kano ne su tafi. Mairama tana jinsa tace wato bazai iya kwanan kauye ba. "Ba haka bane Ummi, bana so ki bawa kanki wahala ne kawai" "Wace wahala ga kannenka ko ta ina, yanzu Karami zai gyara muku dakin da zaku kwana. Yau kowa zai dana kauyenmu" "Ko don kada kice ina gudun kauye dole na kwana." Matsawa yayi gefen Malamijo da yake ta bawa Zayyana da Ibrahim labaran kiriniyar Radhiya. Awwab yaso su tafi da gaske. Ya rasa gane kansa da zuciyarsa akan kanwar tasa. Zuciyarsa ta gaza nutsuwa balle ya fahimci me yake damunsa. Har yanzu dandanon sweet din da ta bashi yake ji a bakinsa na daban da lokacin da ya fara sha. Shi kadai yake murmushi yana satar kallonta tana wurin wanke-wanke tana magana da karamar Antinta cikin amaren da za'ayi bikinsu su hudu. Hajjo ta yiwa Mami da 'yan matan tayin ganin lefen kannen Mairama. A lokacin Mairama tace tunda bikin haka yake kurkusa gaskiya ta fasa komawa Rugar Barkindo. Zata jira ayi bikin a gama nan da kwanaki sha biyu sai su wuce Katsina kuma. Idan an gama biki kaf su tattara su tafi. Tasan Innawuro da matan Baffaninta ma zasu zo idan an aika musu. Dakin Hajjo suka tafi su duka kafin a gama gyara inda zasu kwana. Radhiya ta biyo bayansu zata shiga kenan Malamijo ya kwalawa Emzee da ya zage abinsa yana shara kira yana hura hanci shi mai arziki. "Zayyanu yaka zo, bar wannan aikin zan sa a karasa. Ka raka wannan samarin gonata su gani" Da baya da baya Radhiya ta dawo "ai wallahi tunda naji muma sai munje. Bari naje na kira su Adda Zahra" "Ban gayyaceki ba fitinanniya, idan sai kinje ne na fasa kowa ya shiga daki ya kwanta dama kun kwaso gajiya" "Ni din? Ashe yau rabon kosashiyar saniya za ta kasa ne" "Buhun ubaki mai idanu a tsakar ka, Qur'anin Allah kika yi min barna a gona sai an biyani" yunkurin tashi yake don ya riga yasan hali. Muddin tace zata yi to da wahala idan basu dawo gida da nama ba. Shi yadda yake tsoronta ma yana tsammanin da kanta zata iya yiwa shanunsa rauni kawai don a yanka. Awwab da Ibrahim sai dariya suke yadda ta dage sai taje Malamijo ma ya dage. "Malamijo da dai ka kyaleta tunda kasan ko ka hana sai taje" Emzee yace da sigar laluma. Malamijo ya tamke fuska yana kallon Awwab "yaro ga amana, idan kuka je ko kaza ce ta sami matsala sai kun biyani." "An gama Malamijo" Awwab yace yana murmushi. Tsohon burge shi yake kamar yadda Zayyan Tureta yaji farkon haduwarsu. "Ni nafi zargin ita wannan ce ya kamata ta fito a namijin shi kuma salihin nan ya fito a mace sai aka sami mushkila. Yasin duk mai auren 'Yar soja sai yayi shiri da gaske" Murmushin Emzee ya fadada ya saci kallon Awwab da duk motsin Radhiya sai ya kalleta a ransa fata kawai yake ya ga ranar da za'a ce sunyi aure. "Kirawo su idan basu gaji ba" Malamijo yace yana binta da harara. Fatansa Allah Yasa suje su dawo lafiya kada yaji labarin da zuciyarsa bazata iya dauka ba. Da murnarta taje ta fada musu zasu je gonar Malamijo ganin dabbabinsa. Ghazalatu tana kashingide akan gadon Hajjo tace ita babu inda zata je. Gabadaya ranta ya gama baci da kwanan garin nan. Kana ganin gidan duk girmansa kasan gidan talakawa ne sai wani so ake a burge su. Tana ji lokacin da Yadikko ta tunawa Malamijo kajin da ya bayar ya hadiyi yawu don yayi zaton kajinsa sun sha kafin a sake shawarar kwana. Ba don yaso ba yace a dauka ayi miyar tuwon dare dasu. Zayyana da Fauziyya tuni suka tashi aka gyara fuska suna murna zasu je. Zahra ma tace bazata iya zuwa ba kan ta ya soma ciwo. Ita dama bata da juriyar tafiyar mota daga amai sai ciwon kai. Zasu fita Mairama ta dakatar da Radhiya "don Allah kada kije ki yiwa Malamijo barna kinji ko, kuma ana magariba ku dawo" Dariyar shakiyanci tayi tana kissima me zata yi don babu yadda za'ayi taje ta fito sikau basu ci nama ba. Jama'ar gidan dashi kansa mara lafiyan da amarensa da ta gani kowa yana bukatar protein. "Haka fa ya cewa Hamma wai ga amanata kada na taba komai. Ni yanzu Ummi da girmana me zanje in taba a gonar nan?" Da yake Mami ta san waye Malamijo yanzu tun bayan labarin gidan da Mairama ta basu ga kuma sanin da ta yiwa 'yar tata sai ta rinka dariya ita ma. Ghazalatu na jin Radhiya tace Hamma ta diro daga kan gadon tana cewa ita ma zata bisu. Radhiya ta tabe baki bata manta me tayi mata ba dazu "ba yanzu kika ce bazaki ba?" "Iska nake son sha" tace fuska ba annuri. Indai Awwab zaije kuma Radhiya ma zata dole ne ta bisu. Bata son wannan likewar da take yi masa daga gani irin abin nan ne na 'yan kauye an ga dan birni ana so a cusa kai ko Allah zaisa yace yana so. Emzee yace gonar a bayan gari take da 'yar tafiya shiyasa Awwab yace gara su je a mota tunda yamma tayi. Da sauri sauri Ghazalatu ta riga kowa fitowa. Awwab na bude mazaunin dreba lock din ko ina ya bude ta kama kofar gaban mota ta bude ta shige kamar wadda take tsere da wani. Burinta ta riga Radhiya shiga. Awwab na zaunawa ta kalle shi tana murmushi ya daure ya mayar mata. Ji yayi yafi son Alheran dinsa ta zauna ko da irin zaman dazu ne ta juya masa baya. Duk abinda Ghazalatu tayi na saurin zama a gaban Radhiya ta gani. To dama ita dinma yanzu bata ra'ayin gaban. Bata son zama kusa da Awwab din saboda yadda yake sawa tajita kamar ba ita ba. Kusa da Zayyana ta zauna a tsakiya tana ta zuba surutu. Awwab ya kasa hakuri ya gyara madubin motar yadda zai rinka ganinta da kyau. Yana saita madubin suna hada ido da Emzee. Hade girar sama da kasa yayi da Emzee ya dago masa hannu yana murmushin tsokana. Kansa ya janye gefe Awwab ya hango Radhiya tana nunawa Zayyana makarantar da tayi primary. "Ranar hutun da muka gama primary 5 muka yi dambe da Danmama a wurin bishiyar can, ko me yake yi yanzu oho" "Damben fada kika yi dashi?" Zayyana tace da mamaki. "Ke baki ji wulakancin da yayi min bane. Malamijo suke zagi ni kuwa na nuna musu matsayinsu." "Zan so sake ganin Danmama, yanzu sai dai muyi gaisuwar mutumci idan an hadu" Wani azababben kishi ne ya turnuke Awwab "duk yawan 'yan uwanki basu ishe ki ba sai kin hada da abokin fadanki? Wai shin ke namiji ce ne ma kike fada da maza?" Ita me tace da zai rinka yi mata fada daga labari. Kallonta yayi ta madubin ta murtuke fuska "kuma idan na zama soja ....." "Stop dreaming babu inda zaki. Idan bazaki yi karatu irin na kowa ba sai ki hakura" A duniya ita tana da burin da ya wuce zama soja ne? Duk mai son hanata bai nemi zaman lafiya ba. Ko da kuwa Hamma Awwab din da take ji dashi ne. A take ta bata rai "ai dai Daddy yace zai nema min" "To zamu gani" yace yana shiga kwanar da Emzee ya nuna masa. Fauziyya tace "Hamma ka barta tayi kawai mu sami soja mace. Ni har hangota nake yi. Kasan Radhiya bata daukar raini kowa zai shiga hankalinsa" "Idan kin haifi taki 'yar sai ki turata amma wannan dai na gama magana" "Kai Hamma kada fa mu ganku a rana wannan kanwar taka bata iya fada ba. Sai ku kwana kuna yi" Bai ce komai ba yayi parking a gefen gonar. Tun daga inda suke suna iya hango shanu da tumaki. Malamijo fa akwai kudi arziki ne kawai babu don bashi da zuciyar fitar da kudinsa a mora. Kowa ya fita saura Ghazalatu da Awwab a motar. Gani yayi bata da niyar fita ya koma ya zauna yana tambayarta me taki fita. "Yayana kaki zama muyi hira, nayi maka wani abu ne?" Ta marairaice masa. Tausayinta yaji domin daga baro Abuja zuwa Katsina, Kano da Sumaila duka tayi dominsa ne. "Kiyi hakuri, kinga ban samu na zauna bane" "Amma ka sami lokacin hira da kanwarka ko?" Tace cikin yanayin da ke nuna tsantsar kishi. "Me yasa Alheran ta tsaya miki a rai ne?" "Shakuwar taku tayi yawa Yayana, bana son abin ya koma wanda bazai mana dadi ba a gaba" "Idan zakiyi min adalci Ghazalatu kin sani cewa duk wanda yasanni da su Mami to dole ya taba jin zancen Daddyn Alheran, Umminta da ita kanta ko da sau daya ne. Family dinsu suna da matukar daraja a idanun iyayena" tunawa yayi da zancen rasuwar Zayyan da Daddy yayi masa a daren da zai taho Kano da nanata masa ko bayan ransa ya taya shi rikon amanar iyalinsa. A daren sai da ya zubar da hawaye. Yayi zaton idan ya ga Radhiya kawai shakuwarsu ta baya zai tuna kila ya ga ma ta sauya daga sanin da yayi mata. Sai ya zamana abin ba haka yake ba. Ganin kwana daya Alheran nema take ta shige kowane bangare na jikinsa. "Tunanin me kake yi ne?" "Fito muje ba dadewa zamuyi ba" yace yana fita. Dole tabi bayansa a ran ta tana jin dole ne ma suna komawa ya sanar da nasa iyayen idan ma kudin aure ko saka rana za'ayi duka ayi da wuri kafin abin yazo yafi karfinta. Yawo su Radhiya ke yi sosai ga masu kiwon dabbobin suna ta bin bayansu ana musu karin bayani. Wurin wata saniya suka je ana tatsar nono. Mutumin da yake tare dasu yace ta haihu ne wani sa ya tunkuye dan makarakin bai shura ba. "Ina son yin tatsar nima" Zayyana tace da Radhiya wadda lokaci lokaci sai ta waiga baya ta gani ko su Awwab sun fito. Haushi ne ma ya kamata saboda yace bazata yi soja ba a gaban mutane ta yi gaba cikin takaici tana jin zuciyarta tana nauyi. "Muje na koya miki" Emzee yace da Zayyana bayan ya gama karantar yayarsa. Irin hular kaba da suke sawa su kare rana mai fadin kasa Radhiya ta gani wani cikinsu ya cire ta dauka ta kwama a kanta ta sami kasan bishiya ta zauna akan wani dutse tana kallon su Fauziyya harda Ibrahim kowa tatsar nono yake yi. Idan wannan ya gwada sai ya matsa wani yayi. Awwab da Ghazalatu ta gani suna tahowa taji wani abu na taso mata daga kirji har wuya. Rufe idanu tayi ta ja hular ta dora akan fuskarta. Duk abinda take yi Awwab na kallonta har ya karaso inda take. So take ta bude fuskar saboda wani sihirtaccen hamami da yake tashi a ciki amma bata san ta ina Awwab ko Gayanatunsa zasu bullo mata ba. Babu wanda take son gani cikinsu. Wari ne ya isheta ba arziki ta cire hular tayi jifa da ita sai a cinyar Awwab da zamansa kenan. "Wai Allah, wannan shi ake kira gumama inji takari. Wannan uban wari....." Kasa karasawa tayi tana kallonsa da hular a cinyarsa tsabar mugunta ta rinka dariya. Shi da budurwarsa suka janyo mata saka hular ai. "Kina da matsala, kin gama bata rai kin zo kina dariya" yace yana kara rungume hular "Na ga ka kama hula ka rungume ne kamar ta ka" Miko mata yayi ta goce da sauri kada ta sake tabawa "nagode, ungo abinki tunda taki ce" "Warin maza take wallahi" ta kwashe da dariya da ta ga ya tashi da sauri hular ta fadi kasa. Yamutsa fuska yayi yana kallon yadda take jindadi hankali kwance "wannan wace irin kalma ce haka ko dadin ji babu?" Idanunta da ya yarda suna dauke masa hankali ta watsa masa "wace kalmar? au wai warin maza. Kada kace min baka ji ba. Dauko ka sansana" Dukawa tayi zata dauko yasa kafa yayi ball da hular yana kada kai yana kai hannuwansa wurin hancinsa ya kawar da kansa da sauri "dirty girl wannan kika dora a fuskarki" "Rashin sani, nasan yanzu fuskata wari take yi ko" "Ban sani ba" yace yana yin gaba. Daya daga cikin mutanen ya tambaya ina zai sami ruwa yace sai dai a rijiyar da suke debowa dabbobin. Ina wani bambanci da hular da ruwan da ya tabbatar shima bashi da tsafta. Emzee ya kira ya fada masa ruwa yake so da sabulu. Kallon rashin fahimta yayi masa "wanka zaka yi a nan?" Awwab ji yayi kamar ya hada shi da Radhiya ya musu duka. Ghazalatu da sauran duka kallonsa suke yi. "Abu na taba zan wanke hannuna shikenan!" Kamar yadda ya zata su uku suka tafi siyo ruwan da Ibrahim da Zayyana. Awwab ya koma wurin da Radhiya take zaune Ghazalatu za ta bishi Fauziyya ta sako mata zancen bikin da shirye shiryen da zasu yi. Tayi haka ne don tafi son yayansu da Radhiya su fara soyayya taji dadi fesawa Mami. Bata san su ma burinsu ba kenan ga kuma rashin sanin tsakaninsa da Ghazalatu. Kin yi mata magana yayi ita kuwa ta ga lagonsa ta biyo shi ta zauna a kusa dashi a kan katuwar jijiyar bishiyar da ta fito. "Ko ba komai na rama" "A'a kin dai yi kazanta kinji dadi. Me nayi miki ma da zaki rama?" Tura baki tayi cikin shagwabar da ta koyi yi masa "Cewa kayi fa bazanyi soja ba" Sai da ya fuskanceta sosai yace "haka kawai kamar courses sun kare a universities ki rasa abin zaba sai soja." "To, to ni ba so nake na gaji su Daddy ba. Kuma Babana ma ai 'Yar soja yake ce min" " 'Yar soja da Soja daya ne a garinku. Ki cire wannan tunanin a ranki da kaina zan zabar miki course. Kin ci SSCE din dai ko" Kumbura baki tayi cikin fushi "naci" "Bayan bikina gida na zaki koma sai kiyi karatun a Abuja. Gara ku fara shiri da Ghazalatu tun yanzu kada na fita watarana ku tayar min da gida" "Ha'ann lallai ma Hamma ni bazan yi auren ba har sai kayi na dawo gidanka?" Ya ma za'ayi yace haka. To zaman me zata yi musu idan ba housegirl din da Ghazalatu ta kirata ba. "Ashe aure kike so, gara da kika fada min" Hannu tasa ta rufe fuska wai ita kunya "kai Hamma to ai kaine wai na koma gidanka nayi karatu...shi kuma abin sai yaushe?" "You must be kidding" "Me kenan ka ke nufi?" Dariyar da baiyi niya ba ce ta biyo bayan tambayar ta ta. Yarinya 'yar shekara goma sha tara ke zancen aure. Karatu yake da burin tayi mai zurfi kafin maganar aure. Da kyar ya daidaita kansa bayan ya hango irin kallon da Ghazalatu take jefo masa. "Okay, seriously kina da wanda yake sonki ne?" Sama ta kalla kamar me tunani "akwai Kawu Zakari sai na koma gida zai gabatar da kansa sosai" Ransa yaji ya soma baci to amma yanayin maganarta ke bashi dariya "zai gabatar da kansa wurin su Ummi?" Innocently tace "a wurina dai, ai bai riga yace min I love you din ba" "Ya Allah" Awwab yace dariya na sake kama shi sosai. "Don na fada da turanci kake dariya?" Ita bata ga me tayi ba daidai ba. Wato shi yayi aure ita kuma ya hanata cikar burinta na zama soja sannan bazai barta tayi auren ba ita ma sai kace wata alhudahuda zai rinka kira mata karatu. Sai da yayi dariya mai isarsa ya fadi abinda yaje mata a bazata "Allah Ka bani Alheran Radhiya" yana kallon kwayar idonta. Wani irin abu ne ya fizgi zuciyarta zuwa gareshi a daidai lokacin taji farinciki ya saukar mata irin wanda bata taba ji ba. A nasa bangaren sai da maganar ta fito ya fahimci nauyinta. Maganar zuci ne ta fito fili. Sai dai kuma shi ya sani cewa zuciyarsa bata raya masa karya ba haka nan bakinsa bai fadi karya ba. Haduwar kwana daya jinta yake kamar basu taba rabuwa ba. Zuciyarsa ta ginu da son wannan yarinyar tun tana cikin mahaifiyarta. Tsayin shekaru bai sa ya manta da ita ba. Ya cigaba da rainonta a zuciyarsa har zuwa haduwarsu ta jiya a inda yadda ta koma ya sake kayatar da ruhinsa zuwa gareta. Da kwalkwalin kan, shirme, shiririta da fada duk yaji ya dauka yana son abarsa a haka. Dena kallonsa tayi don duk abinta bata da rashin kunyar da zata iya jurewa kallon da yake yi mata. "Ehemmmm ga ruwa ga sabulu a ina zan ajiye?" Aikin Emzee ne da tun kafin su karaso ya hangosu suna magana. Allah Yasa Ibrahim da Zayyana sunyi wajen wata tinkiya da take haihuwa ya taho wurinsu shi kadai da ledar purewater da sabulu. Kumatun Radhiya har wani ja yayi don tsabar kunya ta tashi da saurinta zata gudu. "Da fuskar taki mai warin maza zaki shiga cikin mutane? Dawo ki wanke" Emzee bai yi wata wata ba ya arce daga wurin. Ya kamata su Ummi su farga da wuri kafin a laluba a nemesu a rasa. Sabulun ya bata ya farke ledar purewater din ya dauko daya "fara wanke wannan hannun" Durkusawa yayi a gabanta tana cuda hannuwan yana zuba mata ruwa har ta gama wankewa. "Saura fuska" yace mata. Sabulun ta sake sakawa ta dage hijab din ta soma cuda fuskarta ya duku gab da ita "wai nan kunya na baki ne kika kasa magana? Kowa yasan Alheran ta Awwab ce baki da wurin zama sai gidansa" Kirjinta ne ya soma dukan uku uku ta kasa karasa wanke fuskar ya kuma cewa "cire hannunki in wanke miki" "Me din?" Tace tare da bude idanun ta da sauri tana matsawa kada yaje ya taba ta. Ai kuwa kumfar sabulun ta shige duka idanun biyu ta soma ihu tana tsalle sai da su Fauziyya suka taho garesu da sauri. "Kinji dadi kin tara min mutane" "Ka dena min mita ka hure min idona...wayyo yaji" Su Fauziyya sun kusa karasowa kuma baya son kowa a tare dasu yanzun da yake shirin daukan duka makaman yakinsa ya nemi daidaitawa da kanwarsa. "To cire hannun mana" "Naki wani ne zai shiga" A daidai nan Fauziyya ta fara zuwa gabanta ya mika mata wani ruwan ta zuba mata ta wanke fuskar. Da kyar ta bari ta hure mata idanun sunyi jazur dasu kuwa. Awwab da yake jin hankalinsa ya tashi yace mata ya idon. Harara ta maka masa kamar ba shine ya janyo mata ba yana wasu maganganu da suke juya mata tunani. Ana ta yi mata sannu tace su zo su tafi gida an kusa kiran sallah. "Mal Da'u yace mu tsaya tinkiyar can da ta haihu yanzu ta kasa" Emzee ya sanar da ita. Idanun da suka gama yin ja da kumburi ta zaro "ta kasa me?" "Ta haihu ya kasa cire mahaifar sai shure shure take yi. Yankata zaiyi kawai mu tafi da ita gida idan mahaifar bata fito ba" "Gida? Da wa? So kake Malamijo yasa ayi muku farfesu na kuci da burodi da safe?" Ibrahim da Fauziyya suna dariya ta fada musu Malamijo yace ko kazarsa ce wani abu ya sameta ita zai kama. "Hamma kai ya bawa amana kace ka karba" Ibrahim ya tuna masa. "Ku muje na ajiyeku kawai na nemi wurin kwana a waje da safe zan dawo daukarku. Naga alama kasawar ma zata yi" Hankalinta dama a tashe yake ta kyabe fuska yadda Zayyana take yi "bakinka ya sari danyen...." Da sauri ya dakatar da ita kafin ta karasa fadin kazantar "ahhhhh don Allah kada ki karasa. Bazai sara ba in sha Allah" Ya kama kansa kuwa ta sami kofar ramawa tayi shu'umar dariyar da sai ta tashi tsokana take yinta "danyen mangwaro fa zan ce ka hanani. Ka ga bishiyarsa can da nake hawa na tsinko mu rinka dangwala da siga" Shima harararta yayi na daukar hakkinsa da tayi sannan yace "kwadayi, meye abin dadi a danyen mangwaro da sugar?" "Kai dai kawai ka tsorata kayi zaton danyen ka...." Wannan karon shine fuskarsa kamar zaiyi kuka baya son jin kazantar da ta dage sai ta fada "habaaa mana Alheran!" Sai da ta kalli su Fauziyya tace "yanzu danyen kashu din ma ban isa in fada ba? Shima akwai bishiyarsa daga bayan can" Hatta Emzee sai da yayi dariya saboda yadda fuskar Awwab tayi. "Tsokanata kuke yi ko? Nasan me zanyi muku" yace yayi gaba Ghazalatu tayi saurin tarar dashi. 💕[11/2, 6:45 AM]: 29. 💕 Mota suka nufa cikin sa'a Mal Da'u ya sanar dasu cewa ya fitar da mahaifar tinkiyar ta tashi. Radhiya sai murna kamar wata mutum. Kafin ta bar gidan ta kudiri niyar sai anci nama amma bazata so yau da babu hannunta a ciki ba Malamijo ya kare mata tanadi a bainar jama'a. Kowa wurin zamansa na dazu ya zauna jiki yayi ligib bare ma Ghazalatu da ta hado da tafiya daga Katsina. Suna isa gida sallar magariba suka yi. Abin farinciki wurin Radhiya ashe bayan fitarsu Nene Marka ta iso. Danne tsohuwar tayi cikin murnar ganinta. Yau tsakar gidan ta san anyi baki kusan kowa anan ya zauna suna shan iskar Allah suna hirarrakinsu. Ana isha Ghazalatu ko abincin da ake yi mata tayi bata iya kallo ba tayi bacci ita kadai a dakin Zahra ma taji sauki ta fito wurin 'yan uwanta. "Nene muje in nuna miki wani abu" Radhiya tace cikin rada. Dakin da zasu kwana ta ja ta. Ganin Ghazalatu bacci take yi ta cire dankwalin ta nuna mata kan ta "kinga abinda Innawuro tayi min" tace kamar zatayi kuka. "Me zan gani ni Marka, aski akan budurwa saboda Allah" Caraf a kunnen Ghazalatu. Da dabara ta juyo idonta ya sauka akan Radhiya dariya ta kusa kwace mata. Ashe ma babu wani dalili da zai sa ta dami kanta akan wannan namijin. Ji take kamar ta jawo gobe ta ganta a Katsina. Yau din taki karewa tunda tazo yarinyar take like da Awwab. Bata so ta nuna masa zahirin yadda take kin mutanen nan saboda yanzu dai a cikinsu take a cikin gidansu ma. Zata jira ko ma meye sai sun koma inda tafi wayo. Da wayo da dabara sai ta kawo karshen wannan alakar tun kafin rayuka su fara baci. Tana ji Radhiya tana yiwa Nene bayanin makeron da tayi da kwarkwata da suka janyo askin. "Da kansa zai gudu makeron nan kinji 'Yar soja. Gobe da kaina zan shiga kasuwa akwai wani magani mai kyau idan nayi sa'ar haduwa da matar kanki har sai yafi na da in sha Allahu" "Yauwa Nene" ta rungumeta tana murna. Tuwo taje suka ci da su Zayyana. A dakin da mazan suke ma Emzee ya kai musu nasu ba kyama ko nuna gayu Awwab yaci nasa. Jakar kayansa ya duba bayan ya gama babu toothpaste ya manto shi a gidan Mama Zainab. Tun a hanya ya tuna bai damu ba tunda da niyar komawa gida suka taho. Bazai iya bacci baiyi brush ba. Ya ma tabbatar ko Emzee ya tambaya za'a bashi amma ransa yafi raya masa ya fita, fitar ma da Alheran bai gaji da ganinta ba. "Emzee wane irin toothpaste gareku na manto nawa a Kano" "Close up ne" Da murna sabanin rashin jindadi da ya kamata ya nuna yace "kash bana iya amfani dashi, akwai inda zan iya siyowa nan kusa?" "Kawo na siyo maka yanzun nan, da wane iri kake amfani?" Shiru Awwab yayi zancen gaskiya bashi da wani zabi indai yana da kyau yana saya. Da dai sabulun wanka ne to baya tsallake pears masu mabambantan kamshi da sinadaren gyaran fata. "Colgate nake so, amma zani da kaina kwatanta min" Emzee da wayo ya gano Hamman nasu. Kallonsu yake daga shi har Radhiya ya ga ina za'a dire wannan abu. "Ko in kira Adda ta raka ka ta fini sanin wurare. Idan ba'a samu a wani wuri ba baza'a rasa a wani ba" Ido ya kafe Emzee dashi yana tunanin ko dai yaron ya fahimci yadda ya damu da ita ne. Ba ya son bawa kansa kunya a gaban yara ba. To amma meye a ciki don ya damu da ita ba kanwarsa bace? Yana can yana musu da zuciyarsa Emzee ya fice ya tafi nemanta. Tana dakin da su Mami zasu kwana sun je ita da Zayyana suna damunsa da hira. Fauziyya da Zahra suna nasu dakin kowacce tana waya. "Adda kizo inji Hamma" "Tayi masa me a daren nan tara saura?" Cewar Mami . "Nima ban sani ba" Mairama addu'a take Allah Ya daidaita kansu kada a sami matsala. Zama da Radhiya idan babu soyayya fa to akwai daru. "Kai Hajiya yanzu bashi da ikon kiran kanwarsa?" Hajjo tayi maganar tana murmushi irin na ta fara gano manufar yaron. "Radhiya tashi kije" Sai dai tun suna magana Radhiya tayi gaba abinta. Nemanta suka yi suka rasa suka kwashe da dariya gabadaya. Ta riga tayi wanka bayan magariba da suka rinka layi ita dasu Zahra kowa jiki yayi datti. Wata riga ce cotton mara nauyi take bacci da ita sai zani da ta daura da hijabi a kai. Shima Awwab can dakin da suke a bangaren samarin akwai bandaki wanda Emzee ya wanke musu shi tas suka yi wanka. Lokacin da Awwab ya juya bai ga Emzee ba tunanin ina ya tafi ya fara yi sai gashi ya dawo yace Radhiya tana kofar gida inda ya turata yace ta jira shi. Yana fita shi da Ibrahim suka kwashe da dariya. "Zeezee malamin soyayya. Nima na fara ganosu fa" Ibrahim yace yana mika masa hannu suka tafa. "Idan ka sami ta ka kuma ka rasa yadda zakayi ka fada mata ka nemeni ka ga aiki da cikawa" Daure fuska Ibrahim yayi da wasa "an fada maka na shirya ganganci ne. Idan na samu ma sai ranar kai amarya zan tura ka daukota" "Dalili" "Kada kaje kayi min kwace kana wannan lumshe idanun da shan kamshi tace ta fasa na fiye surutu" Emzee sai dariya suka shiga tsokanar juna irin yadda dai matasa sa'o'insu suke yi. Tun daga ciki ya soma hangota tana tsaye suna magana da wani da sau biyu yana ganinsa a cikin gidan. Me yiwuwa dai shima kanin Umminta ne. Sallama Awwab yayi masa suka gaisa ya shige ciki. "Emzee yace kana kirana kuma wai a waje" Hannuwansa ya zura a aljihu yana kallonta "aikenki zanyi dama amma na fasa dare yayi" "Yo ni ina tsoron dare ne kamar ba soja ba" Tafiya ya soma yi kawai batare da sanin inda zashi ba ta bishi suna tafe gefe da gefe. "Alheran" ya kira sunanta daga can kasan makoshi sai da taji a jikinta. "Uhmm" "Bana son ki zama soja" Bata ga alamun wasa ba a fuskarsa shiyasa taji gabadaya ya karyar mata da gabbai. Yau sau biyu yana cewa bazata yi soja ba. Na dazu haushi ya bata sosai amma yanzu da ya fada sai taji tana son sanin dalilinsa na fadin hakan. Me yasa shi da take tunanin zai taimaka mata ta sami biyan bukata zai rinka neman rabata da abinda ta girma dashi a ranta. Kafin ta tambaye shi ya cigaba da yi mata bayani. "Ban taba tunanin zanyi wani karatun da bai shafi zama soja ba. Infact son da nake yiwa duk wata harka ta military ce tasa na zama pilot. Na rasa abubuwa da yawa saboda aikin soja. Mahaifina ya dawo gida da kafa daya da lalurar da taso dauke masa dukkan tunaninsa, Baba Hadir yana zaune a wheelchair babu motsi babu magana" tsayawa yayi ya juyo sosai yadda zasu fuskanci juna. Ba tsayinsu daya ba amma itama tana da tsaho daidai gwargwado, duk da haka sai taji kamar ta kankance a gabansa "na rasa mutum na biyu a rayuwata da na baiwa matsayin uba sannan kike tunanin Awwab zai iya bari ki zama soja?" Tambayar ta soki zuciyarta kamar yadda maganganun suka yi tasirin da ya sanya taji kamar tayi kuka. Babu wani abu daya da zata iya tunawa game da mahaifinta idan ka cire kamaninsa na hoto. Amma labaran da take ji game dashi ya sa take da burin zama kamarsa. Tana so nan gaba ko me ta zama idan an tashi ace 'yar Zayyan Muhammad Tureta ce. "I may be selfish Alheran amma daga jiya zuwa yau keman kin sani cewa bazan so wani abu da zai taba min ke ba." Kallonsa tayi ta ga idanunsa kyam a kanta sai tayi murmushi "me kake so na karanta?" "Are you serious? Kin hakura?" "Ba dole ba kana yi kamar zaka yi min kuka" tace tana dariya. Hamma yafi karfin komai a wurinta zuciyarta ke sanar da ita. Da sauri tayi hanyar gida dama ba nisa suka yi ba yabi bayanta yana murmushi har suka shiga soron. Tsayar da ita yayi ya koma mota ya dauko ledar tsarabarta ya damka mata. "Ga naki kayan ledar Allah Yasa komai yayi miki" Tayi murna sosai ta dauko takalmi daya ta gwada yana haskawa da wayarsa don ta gani saboda hasken soron bashi da yawan da zata gani da kyau. Guda uku ne takalman biyu da jakarsu sai turare biyu, dankunne da sarka da tarkacen kayan kwalliyar da bata san yaya zata yi dasu ba. Sai da ta gama godiyarta ta karbi wayarsa tace ya buda mata hotuna ta gani. Daya bayan daya take binsu wani tace yayi kyau wani ta tsokane shi. Da sannu ta iso wurin hotunansa da uniform dinsa. Nan fa ta rude tana ta yaba yadda kayan suka burgeta. Murmushi yayi mata yace "ko dai ta kusa kare miki ne zaki hakura da dreba" "Sai soja ko likita" "Time will tell" "Me kace?" "Babu komai" Cigaba da kallon tayi ta budo wani yana tsaye da members na cabin crew dinsa a wata tafiya da suka yi da ta dace da birthday dinsa. Shi ya ma manta kafin a budewa fasinja su shiga jirgin suka kawo masa cake da gifts saboda yadda suke jindadin aiki dashi. Yana sakewa da kowa ayi raha ya wuce. Kasa yin gaba tayi da hoton duk da yayi kyau sosai amma 'yan matan air hostess din sun wani saka shi a tsakiya. Tayi gaba a hankali sai da ta gwammace bata yi ba. Wata cikinsu ce take tura masa cake a baki sauran suna tafi aka dauka. Abinda bata taba ji bane a rayuwarta na tsananin kishi ya saukar mata a lokacin. Ji tayi ina ma Ghazalatu ce ke bashi akan wannan mai dan skirt din da tasha kwalliya kamar 'yar tsana. Gani yayi tayi shiru ya fada mata lokacin da aka yi hoton. Daga murya tayi ba da niyya ba sai dai bacin ranta a lokacin ya kai makura "ita ma wannan matsayinsu daya da waccan ne?" "Waccan?" Da gatse tace "Matar da zaka aura ba" "Abokan aikina ne fa" "To" tace muryarta tana rawa. Duk yada taso boyewa kasawa tayi hawaye kamar famfo suka shiga sintiri a kumatunta. Karbe wayar yayi ya haske mata fuska tayi saurin rufewa da tafin hannunta da kasan hijab din tana kara sautin kukan. "Ya Allah, me nayi miki kuma?" "Babu komai" Hankalinsa a tashe yace "amma kike wannan kukan, akwai abinda yake damunki ne?" "Nima ban sani ba" ta sake bare baki kukan yana karuwa. Hoton ya kula tana kallo ya dawo da wayar saitin da zata gani sosai. Gabadaya hotunan ranar birthday din nasa akan idonta yayi marking ya gogesu. Babu kunya murmushi ya bayyana a saman labbanta. Dage gira yayi yana mata wani irin kallo "silly girl! Kishi ko? Ko dai ta kare miki dinne ban sani ba?" Dinke fuska ta sake yi ta tashi. Yayi ta kiranta haushin kanta da kukan da tayi yasa taki amsa masa. Samun kansa yayi da sakin murmushi shima yaji dadi ta damu dashi. Girgiza kai yayi lokaci guda yana kwabar kansa da cewa ya kiyayi wuce gona da iri akan kanwar tasa. Duk abinda yake yi mata 'yan uwantaka da shakuwa ce ********** [11/2, 6:45 AM : 30.💕 ]🏽 Rtd Major Mustapha tun a hanya suna ta waya da Baffa Habubakari da babban dansa da ya rako shi wan Zakari. Da kuma wannan soja wanda a yanzu yake rike da mukamin Captain shima kansa. Rikon amana da cigaban zamani yasa bai taba gazawa a wurin karbar sakon Major ba. A harabar Giginya Hotel inda suke sa ran yin masauki suka hadu. Da motoci biyu hilux cike da sojiji majiya karfi wanda kallo daya zaka yi musu duk wani burbudin fitsara da rashin kunya su kama gabansu Captain Onomza ya zo wurin. Ya gaisa dasu Daddy ransa a matukar bace yace a yanzu fa zasu wuce a kamo mutumin. "Calm down Captain, muyi hakuri zuwa wayewar gari" "I am sorry Sir, I cannot wait Sir" ce amsar da ya bayar yana 'yar dariya saboda har yanzu yana girmama Major. Major ma burinsa ya ga Maikudi a hannu. Tunanin wadanda suka zo dasu yayi ga gajiya ga kuma firgicin ganin sojojin. To su ma sunyi na'am da a tafin shiyasa babu bata lokaci suka wuce gidan. Jume ce tsaye jikin bango domin baiwa kanta kariya kada ta fadi saboda zafin kalaman Maikudi. "Kannenka kayi musu tsawa nima kayi min tsawa ina mahaifiyarka?" "Idan bakya so sai ki bar wannan magana. Abinda ya faru ya riga ya faru amma sai tado zancen kike. To wa zaki burge cikinsu? 'Yan uwan matar nan suna da arzikin kula da ita da yaranta, meye don nima naci daga arzikinsu. Ba wan ubansu nake ba?" "Hakkinka ne da zaka ci?" "Ho Jume, kin ma manta lokacin da ki ka matsawa Zayyanun da kanki akan ya baki kudin gadonsa." Sai da taji ba dadi da ta tuna irin abubuwan da ta rinka yi wa Zayyan a wancan lokacin. Gashi ya tafi ya bar mata duniyar dan cikinta ya zame mata kadangaren bakin tulu. "Kinga ni tashi zanyi daga gidannan nan da sati guda zaki huta da ganina. Gobe zan zo da masu aikin kwashe kaya" yana kaiwa nan yasa kai ya fita ya bar mahaifiyarsa da kunar rai. Majalisarsu yaje ya zauna gefen wani gida inda suke wuni suna buga karta, gulmar duk mai wucewa da kallon 'yan mata. Hira suke gasu dai magidanta amma babu mutumci a tare dasu sai kyakyata dariya suke abinsu. Da yake lungun motoci bazasu iya shiga ba daga gefen titi suka yi parking sojoji suka rinka durowa daga motar harda masu bindigogi kirar AK47. Hankulan jama'a tuni suka tashi ana tunanin yau ko lafiya unguwar. Da karfinsu suke tafiya Baffa Habubakari da dansa Manu nadamar biyo wannan zugar sojoji suke yi. Tsoro suke kada su manta cewa tare suke a kafta musu hancin bindiga. Su Maikudi sai gani suka yi mutane na shigewa gida da sauri ga sojoji suna tafe da sassarfa. Wasu cikinsu zasu tashi ya ce su zauna. "Meye abin tsoro a soja, kanina ma har ya rasu soja ne. Ko wane mai tsautsayin suka biyo har cikin unguwa don jaraba wa ya sani" Kamar ance ya kalli tsakiya ya hango wani mutum cikin shadda dinkin tazarce ya karkace hula yana rike da sanda ruwan kasa daga samanta da yake a lankwashe kasan kuma baki ne. Dogo ne kakkaura mai cikar haiba da zati. "Banten uba" Maikudi yace da ya tabbatar wannan mutumin ne da suka zo neman Radhiya da uwarta kwanakin baya. Jikinsa har mazari yake don tsoro garin sauri ya bar wurin ya cambala kafa a cikin kwatar gabansa. Bai ko damu ba ya soma sauri. Captain Onomza ya gane shi da sauri ya bada dokar a damko masa shi. "Don't let him get away" yace da karfi. Mutum daya ne yayi kukan kura ya kwaso Maikudi gabadayansa sai gashi kwance a gaban Captain Onomza. Hanjin cikin Maikudi ya buga wani uban sauti shi ba na yunwa ba shi ba na lalacewar ciki ba. Kallonsu yake tsakanin Major Mustapha da Captain Onomza wanne ne zaifi dan dama dama wurin sassauci. Yawun bakinsa duk ya kafe ya laso lebe ga gumi ya fara jika shi. Muryarsa kamar an takewa muzuru jela da takalmin karfe yace da Major "me yayi zafi ne haka ranka ya dade? Yarinyar nan da kaina zan kaika garin da suke. Ko makon da ya gabata naje na fada musu kazo kana nemansu shine uwar tace babu inda zasu je. To amma yanzu tunda anyi haka ina maka rantsuwa irin ta addinin Islama ko a ka ne zan dauko Radhiya na kawo maka. Kai harda kanin nata Zayyanu." Gigitacciyar tsawar da Captain Onomza ya daka masa ita ta janyo mararsa ta saki fitsari ya soma tsartuwa. Mutane har sun fara fitowa kallo tunda sun fuskanci an kama wanda aka zo dominsa. "Nine ka yiwa kerya yace min wife na Lt Zayyan yayi aure, baby ya mutu and you have the girl with you. Ko ba anyi haka ba" Idanun Maikudi kamar an kasa kwai a faranti sunyi tsilli tsilli yace "ni ban fahimci me kake cewa bare na baka amsa" Wawan mari ya dauke Maikudi dashi sai ji kake garam-garam masu leke suna komawa inda suka fito ana rufe kofofi. Captain Onomza da ko cikin sojojin ma ana tsoronsa saboda baya sassautawa mara gaskiya shine Maikudi zai kawowa wargi. A take habo ya kama Maikudi. Major ya kawar da kansa su Baffa jiki ya hau tsuma. Da sunsan abin zai hada da sojoji babu abinda zai fito dasu daga rugarsu. "Ka fahimta wanna ko" "Kuyi hakuri yallabai yanzu me kuke bukata?" "Bundle him up" Mutum biyu ne suka taho kan Maikudi aka cukwikuye shi guda ya saba shi a kafada yayi gaba dashi. Major da Captain Onomza suka sake gaisawa Captain din yace zai kira shi ya tabbatar masa a daren yau kafin gari ya waye Maikudi zai fadi ina kudaden marayun suke. Gidansu na Kano ma zai fadi me yayi dashi haka zalika idan yana da hannu a dauke kafar da 'yan uwan Innar Zayyan suka yi shima duk zai fada da bakinsa. Da sassarfa suka bar lungun sannan Major yace su shiga gidan. Jume bata yi mamaki ba bayan ya gama mata bayanin me aka yiwa dan nata. "Yanzu sai yaushe zaku sake shi?" Ta tambaya cike da jimami ga matarsa da yara suna kuka don labari ya iso gidan tun kafin shigarsu ma. "Sati daya zaiyi in sha Allah" "Yanzu babu wani abu da zaku iya yi a fitar dashi?" Wani murmushi Major yayi da ya tabbatar musu babu wani abu da zasu yi da zai sa ya fito da Maikudi. Dole Jume taji babu dadi amma dan nata yana bukatar saiti ita kanta ta sani. Su Major sun tafi akan idan da wani abu zai nemesu. "Uhmm nace ko zaka nemi Mal.Aminu. Aminin Malam ne da suke zuwa Nijar din tare, dashi akayi komai na auren Malam din da ita Innar Zayyanu" Godiya Major yayi mata suka rabu zasu dawo washegari a raka su gidan Mal. Aminu. Captain Onomza baiyi sanya ba wurin ganin Maikudi ya samu tarba irin wadda ta dace da macuta irinsa. A wannan daren ya bambance aya da tsakuwa, ya gane waye soja da hatsarin dake tattare da shiga hurumin sojoji ko da a bayan ransu ne. Mutane ne masu hadin kai da tsayawa juna domin kare martabarsu koda a bayan idanunsu ne. Abinda ya kara tunzura Captain Onomza shine takaicin ace dan uwa na jini ne da wannan muguntar. Kuma ya rasa wa zai ha'inta sai iyalin Zayyan dinsu. ********** Matafiya suna ta shiri an gama wanka da cin abinci. Ummi da Mami ake jira basu gama hirar da suka dauko ba bayan wayar da suka gama da Mama Zainab. Zuwansu asibiti jiya likitan da suke gani ya gama bincike akan likitocin da ake kira neurosurgeons inda cikin sa'a ya sami wani kwararre da zai je Kuwait sati biyu masu zuwa. Likitan dan asalin kasar Philippines kusan yawo yake kasa kasa yana duba patients. Matsalar dai bata wuce samun shiga gurbin appointment dinsa ba karamin abu bane. Yini guda suna ta cuku cuku aka cusa Hadir a matsayin patient na karshe da zai gani a wani babban asibiti a Kuwait. Ba komai yaja hankalinsa ya karbe shi ba sai dadewar da Hadir yayi da lalurar da kuma jin cewa soja ne da ya sami rauni a filin daga. Tsananin rabo da addua suka sami alfarmar nan. Kudi dai Zainab zata kashe ba na wasa ba abu ya tasarwa miliyan tara. Zuciyarta ta karye hankalinta ya tashi. Idan ta bayar da wannan kudaden hakika zata tagayyara jarinta. Allah Ya taimaketa akwai kayan da tayi order daga China dake kan ruwa da basu sauka ba. Sune zasu riketa idan tayi sa'ar kasuwa. Mami ta kwantar mata da hankali za ta sanar da Major domin nauyin ba nata bane ita kadai. Ummi bata bata lokaci ba itama wurin neman Innawuro a waya. Shanu biyar cikin abinda iyayen nata suka bata bayan ta koma hannunsu manya manya ta roki alfarmar a saka a kasuwa a ga nawa zasu samu. Dama ajiyarsu take saboda karatun 'ya'yanta da auren Radhiya idan ya taso. "Abinda za'ayi Mami ku tafi da Karami domin su hadu da Ibrahim su taimaka mata. Bikin namu na kwana daya ne ana kai amaren washegari zamu tafi Kanon mu jira har su tashi" "Baiwar Allah wallahi ina tausayin Zainab. Hadir ya godewa Allah bana jin zai taba haduwa da matar da zata kaunace shi rabi rabin yadda Zainab take yi" Murmushi Mairama tayi ta bata labarin da Zayyan ya bata tun yana raye na ainihin waye saurayin Zainab din. Sun sha dariya su biyun yadda abotar su ta kasance. Kowa ya shirya sun fara fitowa amma babu Radhiya har Mami sai da tayi cigiya. "Tana kwance inda tayi sallar asuba tana bacci" "Bacci kuma?" Mairama tace tana mamaki don Radhiya ba mai baccin safe bace musamman ma dai na yau da su Mami zasu koma. "Taso ta Fauziyya tazo kuyi sallama" Mami tayi saurin hanata "A'a wallahi ku dauko kayanku mu tafi. Nasan bai wuce gajiya ba" Kusan kwana tayi tana kukan hotunan wayar Awwab. Duk da ya goge takaici take don me yasa ya tsaya har mace ta saka masa abinci a baki. Wannan ma salon ya jawo musu zagi ne ace yayanta bashi da kamun kai. Ko mutum nawa ne suka gani? Mata nawa ya bawa ko suka bashi abinci a baki? Alawar da ya bata ma sai da ta tuna ko sun taba yin haka da wata kafin ita. Wannan yafi tsaya mata a rai taci kuka ta godewa Allah shine fa bacci yayi awon gaba da ita da asuba. Ghazalatu dama jira take kowa ya fita daga dakin ta zauna kamar tana gyara daurin dankwali. Zahra na fita ta fiddo wayarta taje ta zame hijabin Radhiya da babu dankwali ta kasansa a hankali wani bangare na kan ta ya bayyana tayi saurin daukarta a hoto tana kunshe dariyarta. Awwab zata nunawa kawai don ta rage karfin alakarsu duk ta yadda ya samu. Awwab da yasan yadda ya rabu da kanwar tasa ya shigo tsakar gidan ya kai sau biyar ko zai ga gilmawarta. Da yaji ance bacci take yi hankalinsa tashi yayi fiye da zatonsa. Ta yaya zai tafi bai sake ganinta ba sai nan da sati biyu. Walwalar fuskarsa gabadaya ta bace yana jin kansa sukuku suka fito. Rakiya harda Malamijo shima yana cigiyar jikarsa mai fitina akace tana bacci. "Kun taba jikinta kuwa lafiya take babu zazzabi? 'Yar sojan ce zata yi bacci har goma na safe indai ba kwaya ta soma sha ba". Dariya ya basu sosai. "Mami ko dai bata da lafiyar? Hancinta na gani yayi swelling da saman idonta" inji Zayyana. Ummi tace "ko ma meye ku bari su tafi a taso ta don yanzu tana zuwa sai ta bata musu lokaci" Ba dai kukan ta sake yi ba Awwab ya tambayi zuciyarsa. Tamkar kada su tafi haka ya rinka ji. Ghazalatu motarsu ta koma Zahra ta shiga wadda su Mami suka zo don kada a barta ita daya. Kusan awa daya da tafiyarsu bayan Radhiya ya soma damunta saboda kwanciyar kasa ta bude ido tana mika. Dakin shiru babu kowa ta tashi da sauri babu jakunkunansu sun gyare dakin da katifar. Nauyin bacci gareta shiyasa bata ji motsinsu ba. Gabanta na dukan uku-uku ta garzaya dakin Hajjo wurin Ummi. "Ummi sun tafi ne?" Tace cikin tashin hankali. "Ina hankalinki ne, babu sallama babu gaisuwa" Fita tayi ta dawo cikin sauri ta gyara kuskurenta sannan ta maimaita tambayar da ta riga tasan amsarta tunda bata ga Mami ba kuma babu kayanta. "Sun tafi kina can kina bacci. Ko baki da lafiya ne?" Hawaye ne ya taho mata tayi kokarin boyewa "shine basu tashe ni ba?" "Kiji dadin isarsu da surutu ba. Sun wuce da Karami zai zauna a Kano..." Alamun kukan Radhiyan taji ta dakata tare da mika hannu inda take jin sautin tun yana tashi a hankali har yayi karfi. Wani irin kunci da bacin rai take ji hade da gagarumar kewar Hamma Awwab. Me yasa bai ce a tasheta ba sunyi sallama. Me yasa daga zuwansa zuciyarta take shiga mabambantan yanayi daga tsananin farinciki sai bacin rai irin na jiya da ta ganshi da mata. Yau kuma don bai damu da ita ba yayi tafiyarsa. "Ke menene?" "Ummi ba komai" ta amsa muryarta na sake karyewa. Ta dauki kanta jarumar mace mai dauriya amma lokaci kalilin ta zubar da hawaye fiye da tunaninta. Ita kanta bata san me ya sameta ba sai an mata karin bayani. Tun Ummin ta na rarrashi har ta koma fada amma taki cewa komai sai kuka. Daga karshe karamar wayar da Mami ta bar mata ta dauko. Ba kudin sayen bane dama ta rasa sai dai karancin wadanda zata kira. Emzee da Radhiya kuwa taki saya musu ne duk da tasan ana yayinta sosai tana jiran su gama sakandire. "Ungo ki kira Mami da sauran 'yan uwanki ku gaisa kiyi musu sallama kinji 'Yar sojan Daaadaa" Ba wuya anci galaba a kanta. Bare kuma rarrashi daga Umminta sai tayi dan murmushi. "Kyalesu ni na fasa tunda basa son tawa sallamar" ta basar a zuwan taba damu ba. "Ke dai ki karba kafin ki zo da kanki na hana" Sautin dariyar Radhiyan taji ta girgiza kai. Wannan yarinya sai addu'a. Radhiya na kira da taji ta shiga sai kuma kunya ta kamata ta mannawa Umminta wayar a kunne. Dauka Mami tayi tana fada mata inda suke yanzu. "Tsakanin ke da Maman yara bansan wanda ya koyawa yarinyar nan shagwaba ba. Ba karamin abu kesa aji kukanta ba. Yanzu kuwa kukan gaske take min wai bakuyi sallama ba" "Allah sarki Radhiyata, bata wayar mu gaisa" Karba tayi ta gaisheta kamar ba ita ke kukan ba ta kuma gaisa da Zahra "ina su Adda Fauziyya?" "Suna daya motar da Hamma ke ja. Yanzu zan fada mata ta kira ki" Katse wayar tayi ta kira Fauziyyan ta fada mata. Ita kuma tana jiran Zahran ta turo mata nambar take fada musu wai Radhiya tayi kuka da bata gansu ba. Motar sai ta koma hirarta da kewarta da suke yi. Ghazalatu haushi ya kamata kamar wadanda aka yiwa asiri kowa ya bude baki sunanta yake kira. Awwab tuki kawai yake yi kamar ruwa ya cinye shi. Matsananciyar damuwa ya shiga na son sanin dalilin kukan da kewarta da take ratsa shi ta ko ina. Yana ji suna hira da ita wannan ya karba ya bawa wannan amma bata yi cigiyarsa ba, shima bai nema ba tunda yana tuki ne. Daurewa kawai tayi bata neme shi ba duk a cikin fushin idan kowa baice a tasheta ba shi ya kamata yace. Ummin tana jin yadda muryarta ta sauya cikin jindadi ta gama wayar ta tashi ta tafi yin wanka. Sun isa Kano shabiyun rana. Mama tayi musu abinci tace su ci kafin su wuce. Aka zubawa Awwab ya kalli plate din yaji gabadaya yunwarsa ta tafi. Cin abincinsa da Alheran a soron gidan Malamijo yake muradin maimaitawa. Kasa daurewa yayi ya fita ya bar Abdallah da su Ibrahim suna cin abinci. Mami da Mama kuma suna can suna tattauna yadda al'amarin aikin Hadir zai kasance. Cikin motar ya koma ya zauna a baya sannan ya kira Fauziyya yace ta turo masa nambar da zai kira su Ummi. Dariyar shakiyanci ta rinka yi masa ya fara fadan da bata sanshi dashi ba tayi saurin katse kiran ta tura masa. Bugu biyu Ummi ta shafa wurin daukan kira ta kara a kunnenta. Muryar Awwab taji ta tambaye shi yaya hanya. Sun taba hira kadan kamar ta fuskanci me yake jira ta kwalawa Radhiya kira. Bata tambayi ko waye ba ta karba "hello" Shiru yayi yana jindadin amon sautin daddadar muryarta. Ita kuwa ta gaji da hello hello din tace "Ummi anki magana fa" "Ko ta katse, duba zaki ga nambar Awwab ce ki sake kira. Mami tace ta saka nambar kowa" Tashi tayi da gudu ta bar dakin, Ummi sai shiru taji ta koma inda suka kwana tana jin wani nauyi a ranta. A hankali tace "Hamma" [11/2, 6:48 AM] : 31.💕 🏽 "Kukan ne har yanzu baki dena ba?" Yace a hankali yana jin farinciki na shigarsa saboda jin muryarta. "Ni ba kuka nake ba" "Shine daga tashinki kika soma damun mutane da waya ina jin ko wanka bakiyi ba" "Ba kune ba sai kuka tafi bakuyi min sallama ba" Siririyar dariya taji yayi "Silly girl. Cewa zakiyi nine na tafi banyi miki sallama ba ko ba haka kike son fada ba zaki basar?" "Inji wa? Ni da munyi fada da kai" "Ke abu baya wucewa a wurinki ne? Kuma ba na goge ba. Wai ma in tambayeki fushin na meye?" Daburcewa tayi ta rasa me zata ce masa har ya sake maimaita tambayar "uhmm to ai zaka janyo mana ace yayanmu ne kai kuma kaje ana baka abu a baki" "Ba ma ki da kunya, kema fa na baki har sau biyu" "To ai ni kanwarka ce" tayi maganar da wasiwasin iya matsayin da take so daga gareshi kenan ko kuwa. "Tunda dai bakya so na dena. Da Ghazalatu kadai zamu rinka yi" Kit ta kashe wayar zuciyarta na tafarfasa. Ai sai yaje su karata ita dama meye ya dame ta dasu. Kallon wayar hannunsa yayi yana tambayar kansa meye tsakaninsa sa Alheran. Ta wuce kanwa shi kansa ya sani amincewa ta rage. Lokaci yayi da zai dena yaudarar kansa don bazai iya ba. Bashi da karfin zuciyar jurewa. Kallo daya yayi mata ranar da ya fara ganinta a gidan Mama aka kwance duk wani notin jikinsa. Sake kiranta yayi wayar na hannunta dama tana nadamar kashewar da tayi kada yaki sake kira. "Ke da na hana tashi idan muna magana shine kike katse min waya." Baki a kumbure tana fushi tace "kayi hakuri" "Bakin naki zan like tunda baya son yi min magana bashi da amfani" "Ashe rabon wani ma zai nemi nasa ya rasa ne" tace tana dariya da tayi tunanin abinda ta taba son yiwa Gwaggonta Salame wata rana da taji ta zagi Umminta. Wurin Hanne taje lokacin tana auren Malamijo da niyar karbar super glue ta saka mata a kunu tayi rashin sa'a ya kare. Jin kansa yake cikin nishadi yace "Ki gwada ki gani idan Ghazalatu bata zane min ke ba" " 'Yar soja ce fa Hamma ko ka manta ne" "Na dai ce bazaki yi sojan nan ba kuma kin yarda" Bata sanin tana shagwaba sai maganarta ta fito kamar yanzu da tace "to gaskiya ka dena cewa bakina bashi da amfani" Fuskarta kawai yake haskowa tana magana. A kasalance yace "fada min amfaninsa guda daya sai na kyale shi" "Shan sweet in rage maka" tace da sauri ta dora hannu akan labbanta ta rufe bakin tana jin matsananciyar kunyar kalamanta. A karo na biyu ta sake katse kiran tare da kashe wayar. Kan katifar ta hau tana shure-shuren kafafu kamar zata yi kuka tana mai kunyar maganar da tayi da yanayin da tayita cikin wata irin siga mai tsayawa a rai. Wani irin dumi yake ji yana ratsa shi tun daga tsakiyar kansa har kafa. Ya runtse idanunsa yana hangota cikin zuciyarsa. Abin takaici bashi da hotonta ko daya a wayarsa. Bazai iya sati biyu bai ganta ba shiyasa ya fara neman abinda zai fake dashi ya koma Sumaila cikin kwanaki kadan. ********** Mal Aminu yayi bakinciki mara misaltuwa da jin yadda Maikudi ya yi da dukiyar marayu bayan Captain Onomza ya fadawa Major. Gidan Zayyan na Kano yana nan tsahon shekaru ya zuba 'yan haya a cikinsa. Kudin da ya rinka aikowa da kudin hayar dasu ya tamfatsa katon gida mai bene a nan Sakkwaton a cikin wata sabuwar unguwa da yanzu ta fara cika. Bai kuma yi jayayya ba saboda dukan da yaci ya fada musu cewa yan uwan Zayyan na Nijar sun dauka iyalinsa duka sun rasu kamar yadda ya fada musu. Mal Aminu jikin girma bazai iya doguwar tafiya ba amma ya baiwa Major cikakken sunan gidan da zai nema da garin da suke. Harka ta zamani da kwarewa Major ya bayar da cigiyarsu ta hanyar amfani da sojoji ta bangaren Captain Onomza. Zasu koma Katsina su bayar da sati daya ko biyu idan babu wata nasara da kansa zai je Nijar din nemansu. Ko a haka baya jin ya biya Zayyan fansar ransa. ********** Kwana biyar da komawarsu Awwab Katsina. Kullum zai kira Ummi ke dauka Radhiya ta kirkiri wani abin da zai hanata karba. To ta karba tace me. Ta barshi da muguwar kewa ya gaza yin abin kirkin da yayi niyya wato zagayen gidajen 'yan uwa. A rana duk inda yayi biyu ko uku sai yace ya gaji. Sai dai fa duk dare suna tare da Ghazalatu wanda hira da ita ke debe masa kewar Alheran kadan. Yana takaicin yadda baya iya sake mata kamar da kuma hirar ma yana yi ne don kada ya wulakanta ta. Abin yazo ya fara damunsa ga tunanin Radhiya da rashin jin muryarta. Mafita ya nemawa kansa zuciyarsa kuma tayi na'am da shawarar. Major yayi musu bayanin yadda ake ciki Ummi har kuka sai da tayi. Saboda abin duniya Maikudi ya kasheta ita da 'ya'yanta da bakinsa ya rabasu da danginsu. Su Malamijo kuwa sauki ya samu daga shi har amarensa. Yau gidan an tashi da kukan Asabe tayi rantsuwar ko ana ha maza ha mata sai Malamijo ya saketa don bazata yarda ya kasheta da ciwo ba. Fafur taki karbar girki ita takarda take jira shi kuma yace bai gama cin sadakinsa da kudin da ya kashe na aurenta ba. Rigima taki ci taki cinyewa duk jama'ar gida yanzu sun san lalurar da ta kwantar musu da uba. Nene tana gogawa Radhiya maganin makeron da ta karbo wanda a cikin sati kan har ya fara hadewa yayi baki ta hanata fita kallon rigimar da take son taje ta yi. Kunkuninta ta gama da zumbure zumbure ta hakura. "Ni kuwa tun zuwanku Radhiya kinje gidan Gwaggonki Salame?" "Gaskiya kada kice inje Nene bazan iya zuwa ba" "Akan wane dalili" "Ita da ko Malamijo bata zo ta duba ba sai nice zani?" "Wannan kuma tsakaninsu ne. Ina ruwanki ko ke kika haifa masa ita?" Ranta dai bai son zuwa ta soma jan hanci Nene ta dungure mata kai "me tayi miki kike gudunta rigimanatu" Duk wani abu da zata iya tunawa da Salame ta taba yi musu ta rinka daukowa kawai saboda neman dalili. Karshe tace "kuma harda aurewa Ummi baban Danmama. Ai da na sani Ummina zai aura don ma dai bana so kawai kuma ana ta cewa an kusa biki fa sai Ummi ta makance ita kuma Gwaggon ya aureta." Tashi tayi jin rikon Nenen yayi sauki ta suri hijabinta ta tafi kallon kwal uwar daka a tsakar gidan nasu. Nene ko bi ta kanta bata yi ba sai dogon nazarin da ta samu kanta da yi. Tabbas anyi haka amma tun lokacin bata jin wani yayi tunani a kai ma. Makantar Mairama farat daya tazo duk da an san tana ciwon ido. Bata mantawa ita Mairama ta bawa firinjinta ta sayar wani lokaci suka je asibiti akace babu komai a idon nata. Ko dai da hannun Salame tunda tafi kowa sanin abinda ya taba hadasu da marigayi Zayyan. Saurin kawar da tunanin tayi. Duk bakin halin Salame ace harda makanta kanwarta saboda namiji? Kasa nutsuwa tayi ta nemo yaro cikin yaran gidan ta bashi wayarta ya kira maigidanta. Tayi masa bayanin zarginta ne tace ya kamata a nemo kaikayi koma kan mashekiya. "Haba Marka ina amfani wata ta warke wata ta makance? Yanzu dai tunda kin fara tunanin haka ki hadani da Mairama ko Radhiya din zan sanar dasu add'o'i da Ayatusshifa a karanta mata ana tofawa a ruwa tasha ta wanke idon. Zamu tsananta addu'a in Allah Ya yarda zamu sami makarin abin indai sihiri ne. Amma kada ki fada mata kada ki tada rigima idan zargi ne kawai. Ki bari mu gwada mu ga ikon Allah" Godiya tayi masa ta ajiye wayar zuciyarta tana karfafa mata zarginta akan Salame. *********** Washegari kuwa Nene bata yi kasa a gwiwa ba ta nemi Ayuba. Duk cikin yaran gidan shine ya tashi da ustazanci yana ma koyarwa a Islamiyya. Bayanin mijinta tayi masa shima ya hada da nasa ilimin da kansa ya siyo ruwan roba c'est bon babba yayi mata tofin nan yadda ya kamata. Ranar shi wuni tana sha tana shafe ido. Nene tace mata su gwada ko za'a dace ne ta karba da murnarta. Bayan kwana biyu Ummi ta fara jin jikinta yana canjawa tafi jindadinsa sosai gashi ruwan tofin saura kadan. Radhiya ta nema saboda ta jiyo muryarta tana cewa Malamijo yau kwadayi take ji yana rantsuwar kada ta bishi gonar da zai tafi a lokacin. "Kin raina min uba ko" ta tambayeta bayan ta amsa kiran. Sanye take da riga da skirt na atampa ta gama shirinta da hijab ruwan madara wanda ya dace da kayan iya gwiwa za ta bishi gona tayi barna. "Ummi balance dayet muke bukata" "Allah Ya shirya min ke, zo ki dauki kudi ki siyo min ruwa irin wanda Ayuba yayi tofi a ciki. Ki siyo guda uku sai a ajiye" Murmushi tayi "Ummi kin fara gani ko dan dishi dishi?" "Ke dai ki sakani a addu'a ido ya bude na ganku ke da kaninki" "Amin Ummi, wayyo dadi" "To wuce ki tafi banda yawo" sai ana jaddada mata kamar karamar yarinya. Tsokanar Ummin tayi tace "Ina zani ko azahar ba'ayi ba inje basu gama abinci ba balle na sa rai da balance dayet din" Muryar Malamijo ta ji yana magana daga soro ta yi murmushin mugunta. Daga masa hankali zatayi tayi ta binshi yana fada ta dage gonar zata je tunda a kafa yake zuwa. Sai sun isa wurin shagon da zata je sannan zata rabu dashi. Da dan gudunta ta taho kamshi da idanun da suka kafeta a gaban Malamijo suka kashe bakin da jikin nata baki daya. Wani murmushi Awwab yayi mata ta mayar masa idanunsu sarke da na juna. Malamijo bai kula ba yana ganinta yace "Allah Ya taimakeni yau ga yayanku na Katsina yace sako ya kawo muku ke da Mairama. Idan kika sake kika biyoni zai koma da kayansa sai in ga karyar cin balanciye din" Ficewa yayi ya barsu a tsaye. Wani irin kallo yake yi mata taji ta takura. "Muje wurin Ummi din" tace bayan ta juya masa baya saboda wani nauyinsa da take ji. "Wait" A nutse ya tako ya dawo gabanta ya tsaya. Jeans navy blue da layin fari da ya dusashe daga tsakiya ta gaba da shirt mai maballai ruwan toka ya lankwashe dogon hannunta zuwa rabin hannun. Fuskarsa a gyare sai hancinsa ya kara fitowa. Kanta ta sunkuyar ta ma kasa kallonsa. Da wannan muryar tasa mai kauri da tafiya da hankalinta yace "baki tambayeni me ya dawo dani ba, ko dama kinji a jikinki zan zo?" "Ba wurin Ummi kazo ba?" "Basarwar ce?" yayi tambayar yana son sake hada ido da ita. Hijabinta ta janyo gaban fuskarta zata rufe ya girgiza mata kai. "Ahhh" yace yana mata alamar ta bude baki. Kafada ta noke tare da murmushi. "Please Alheran" Sake nokewa tayi yace "dadin abin tare muke da My G tana mota" "Ahhhhhh" tace da sauri har tana bashi dariya domin kuwa ya gama tabbatarwa ba shi kadai bane ya fada wannan kogin da baya fatan fita. Irin sweet din rannan ce dai wadda ya taho da ita daga Germany ya fito da ita daga bakinsa ya kankance ido yana kallonta "See what you did. Kin cikani da surutu kinsa na kusa shanyewa" A bakinta ya saka mata kunya tasa ta rufe ido da tafin hannunta. "Kinsan wani abu" ya bijiro da maganar don kawar da hankalinsa daga kallon bakinta da take shan sweet din dimple dinta da yake matukar burgeshi yana ta sake shigewa ciki. Kai ta girgiza masa ya dawo gefenta ya tsaya "ta kare miki Alheran auren dreba ya tabbata a gareki" "Ni dai a'a" "Are you sure? Ko da dreban mutumin da kike shan sweet din bakinsa ne?" "Ya Allah" tace yadda yake yi idan yaga abin mamaki tana jin wani irin farinciki mara misaltuwa. "Na sani ai bazaki so kada ta kare miki ba in dai shine" Kokarin saita kanta tayi ga murmushinta yaki bacewa "inji wa" "Ba sai munje nan ba kawai ki amince kamar yadda na amince" Cike da shagwaba tace "Ni dai wallahi...." "Me? Ba haka bane?" "Alawar ce ta kare" tace tare da yi masa gwalo ta soma tafiya da sauri. "Zaki aureni?" Ita ce tambayar da taji ya jefa mata a daidai lokacin da kafarta daya ta fita daga soron. Tsayawa tayi a wurin ta kasa gaba ta kasa baya har ya karaso inda take ya rabe ta gefenta ya wuce har cikin tsakar gidan da sallama yana kiran Ummi. [11/2, 6:48 AM]🏽 ]🏽 : 31B.💕 Ummi kamar daga sama ta tsinkayi muryar Awwab. Yadikko ce ta amsa masa suka gaisa ta nuna masa dakin Hajjo. "Shiga tana ciki" Radhiya ta hango tsaye ta kasa yanke shawarar komawa taje aiken da akayi mata ko ta bi bayansa. "Ji min shirme Radhiya kina tsaye ashe kina kallonsa maimakon ki kaishi wurin Mairaman. Dauko filas din wajenta in zuba masa kunun nan da zafinsa" Kamar wadda kwai ya fashewa a ciki haka ta shiga dakin. Yana zaune daga gaban Mairama tana tambayarsa mutan gida da hanya. "Mamaki nayi da naji muryarka fa. Amma dai kowa lafiya ko?" "Ummi kada ki damu lafiya kalau." Dagowa yayi yana kallon Radhiya tana neman flask din ruwan zafi. Yana gabanta amma da yake hankalinta yayi nisa bata kula ba. Ummi ce tace "wai har kin dawo ne?" "Ban je ba, Yadikko ce tace na dauko flas za ta zubawa Hamma kunu" "Yi maza ki kai mata kije ki siyo min in samu yayi tofin kafin ya fita" Ita Awwab ya tsare da ido yana tambayar Ummi "aikenta kika yi?" Bayani Ummin tayi masa yaji dadi yana fatan Allah Yasa a dace. Da ido ya kalli Radhiya yana nuna mata ta zauna ta girgiza kai. "Bari naje na siyo Ummi ina zuwa" "Daga zuwanka, barta ba nisa bane da wurin" Tashi yayi ya sake cewa shi zaije. Ummi tace to ya bari ko ruwa yasha kafin ya fita. So yake kawai ya tashi ya samu kebewa da Radhiya don ba da niyar kwana yazo ba. Gabadaya ya shagala da kallonta. Takwanshe kafafu yayi ya tallabe kansa da hannuwansa da ya dora akan cinyoyinsa ya zuba mata ido. Hanata sakat yayi ta kasa dago kai saboda tsoron idanunsa take yi yadda suke matukar tasiri a kanta. Wayar Ummi da ta soma ringing ce ta sa ya dena kallon nata na dan lokaci ta tashi da sauri ta fita. Shi ya mikawa Ummin wayar ganin sunan Mami shima ya tashi ya gudu yana dariya bayan ya amsa mata kiran ya saka mata a kunne. "Dana kika biyo da kiran nan ko? Yanzu ya iso bai yi rabin awa a gidan nan ba" Sai da Mami tayi dariya tace "nifa ina jin mu saka ranmu a inuwa kawai yaran nan sun gama mana komai sai dai ma su jira mu" Labarin yadda suka kwashe dashi bayan ya dawo daga sallar asuba tare da Major ta bata suka rinka dariya. Yana shiga gidan yayi sa'a tana falo shine yake fada mata zaije Sumaila. Da ta tambayeshi ko lafiya shine yace wai Alheran bata da waya kuma ya san cewa irin haka ne yake sa 'yan mata su ji babu dadi sa'anninsu suna da abu su basu da shi. "Akwai waya a hannun Ummin taku ai" Ita ce amsar da ta bashi. Sosa keya yayi yace "So nayi na bata a matsayin gift na gama secondary school" "Ina ta Karami da Ibrahim? Duka tare suka gama" "Ibrahim yana da waya. Emzee kuma zan saya masa. Tunda ita ce babba shiyasa zan fara bata" "Ba sai kaje Sumailan ba, nan da 'yan kwanaki zaka gansu sun zo biki" Fuskarsa tamkar zaiyi kuka yadda ta dage tana neman kure shi. Tsokanarsa ta cigaba da yi daga karshe dai yace mata wai kewar Ummi ke damunsa. "Kewar Umminka kuwa duk gidan nan banga mai cike maka gurbinta ba. Sai ince a dawo lafiya ko" Amsar tayi yadda yake so amma kuma ta makale masa a rai. Ko dai Mami ta gane wani abu ne? Kai da wuya shi yasan baya yin yadda kowa zai san yana yiwa Alheran zazzafar soyayyar da take nukurkusar zuciyarsa. Daya motar ya dauko Mami tana korafin ranar zai takura mata yace tayi hakuri bazai kwana ba. Jinsa kawai tayi sai kace Katsina zuwa Sumailan tafiyar awa daya ce. To gashi dai a gidan Malamijo tare da Alheran Radhiya. Yana fitowa har ta kusa kure layin nasu ya bi bayanta da sauri. Sai da ta dan tsorata da taji muryarsa da ya kira sunanta. Ta juyo a nutse yayi mata nuni da gidan da hannunsa. "Ki jirani a wurin zaman nan ina zuwa" Wani salihanci ne ya saukar mata a yau din, babu musu ta koma ta zauna akan tudun nan tana jiransa. Hamma Awwab ne ya tambayeta ko zata aure shi. Tunanin maganar kawai sai da ya sanya zuciyarta kadawa tsigar jikinta ta tashi. Kankame jikinta tayi tana jin yadda farinciki ke mamayarta. Magana take yiwa kanta ita kadai tana murmushi "lallai ta kare min, dreba kuma nake so" Shagon babu nisa bata dade ba Awwab ya shigo da katan din ruwan roba mai manyan robobi. Za ta tashi yace ta bari ya kaiwa Ummi ya dawo. Gabanta ke dukan uku-uku wannan karon da ya kuma dawowa. Zaman me zasuyi take tambayar zuciyarta. Zance! Bai dauke idonsa daga kallonta ba har sai da ya zo gabanta ya durkusa a tsugunne. Kallon kofofi biyun da za'a iya shigowa wurin a same su take yi ta shiga gidan da ta fita tana addu'ar kada Allah Ya kawo kowa. "Amsar tambayata nake jira" Rufe fuskarta tayi da hannu sai murmushi da yake manne akan kyakkyawar fuskarta. Ba burinsa bane ta chanja daga Alheran din da ya sani don kawai matsayinta a wurinsa ya chanja. "Na takuraki ko?" "A'a" Tsoro ne ya dan darsu a zuciyarsa da sauri yace "Baki amince ba ne?" "A'a" "To menene?" Kofofin ya ga tana bi da kallo kafin tace "Hamma ni kunya nake ji kada wani ya shigo" "Sai ki bani amsar da nake jira in tashi. Nima bakiji kafafuna ba sun fara sagewa" ya kare maganar yana marairaice mata. Tsokanarsa ta fara yi kawai don ta ja nasa rai "kasan sojoji an sanmu da dauriya ya kamata kaima ka gwada jarumta ko na rabin awa ne" Idan ta kara minti daya yana jin kila zama zaiyi kawai a wurin ya lankwashe kansa gefe "habaaa mana" "Na amince" din da yake jira ta fada kamar mai rada ta rufe kanta tsaf baya ganin komai a fuskarta. Tashi yayi ya zauna a gefenta a kan tudun "wahhhsh, da kin kara jan lokaci sai dai ki daukeni idan mun tashi" "Kai" ta waro ido tana dariya. Ta ina za ta dauke shi. "Seriously, sai ya tuna min da punishment din primary dinmu a Sokoto. Frog jump haka kawai don a wahalar da mutane mu kasa tafiya" Da yake taji mugunta ta sami abinda take so sai dariya "yanzu harda zaman babur akeyi yafi frog jump wahala" "Bana fatan sanin yaya yake tunda ya saka ki wannan dariyar nasan ba abin kirki bane" Gyara zama yayi sosai ya kira sunanta domin yana son suyi magana ta nutsuwa da fahimtar juna "abinda zan fada miki ina so kiyi masa kyakkyawar fahimta kinji" ya kafa mata ido. "To Hamma" Nannauyan numfashi ya sauke saboda mahimmancin maganar da yadda ta rinka cin ransa har ya kasa zama dole ya biyota ayita ta kare. "I love you Alheran Radhiya, I miss you a duk lokacin da kika bacewa ganina. Da zan iya da na dora hannunki kinji yadda kike hana zuciyata samun nutsuwa saboda tunaninki" Tamkar ana zubawa jikinta ruwan dumi haka take jin saukar kalamansa suna kwantar da duk wani abu da yake yawo a ranta sai shi kadai da tunaninsa. "A cikin kwanakin nan da na kara saninki na fahimci kina da kishi" gefensa ta dan kalla kamar zata yi magana sai ta fasa. Tabbas tana kishinsa, kishi ba na wasa ba kuwa "gashi ni kuma na hadawa kaina zafi ina zaman zamana. Ban san inda zan kai mata biyu ba amma Alheran bazan iya rabuwa da Ghazalatu ba don ina sonki" Sake kallonsa tayi sai ya ga kwalla ta soma taruwa a idonta. Har cikin zuciyarsa yake jin komai na kanwar tasa. A zahiri zai iya boyewa amma a zuciyarsa yasan soyayyar gaskiyarsa tana hannun Alheran "kada kiyi kuka please. Ban zo gareki ba sai da nayi ta tunanin what will be the best for the three of us. Look at me!" Umarnin yayi mata tsauri a yanzu da ya gama da zuciyarta amma bata iya ketarewa ba ta dago idanunta hawayen zuna zubowa batare da sauti ba. Da zai iya da ya rungumeta sai dai ko da suka tashi nesa da gida Mami na aiki sauran tarbiyarsu ta koma ga mahaifinsu baiyi musu da wasa ba. Bai bar yaransa dabi'un nasara sunyi galaba a kansu ba ta hanyar yawan kulawa, tsawatarwa, ja a jiki da kaiwa Allah kuka. "I love you! I love you!! I love you!!!....kafin komai ki bar wannan ya zauna a zuciyarki. Kin tuna ranar da nace idan kin sha abin bakina zan tambayeki wani abu?" Jikinta a sanyaye ta gyada kai "kiyi hakuri amma alfarma zan rokeki da wannan damar. ALHERAN DON ALLAH KI YARJE MIN NA FARA AUREN GHAZALATU." Jin maganar tashi tayi tamkar saukar aradu a tsakar kanta. Tsiwa take son tayi masa ko tayi bore ko dai tayi wani abin domin nuna masa cewa bata yarda ba, zuciyarta ma bazata barta ba sai ta kasa sakamakon raunin da take iya karanta a idanunsa da suka soma chanja launi. "Mummyn Ghazalatu sister din Mami ce iyayensu daya. Daddy dinsu kuma cousin din Mami ne kuma cousin din Daddy. Iyayensu maza duka ukun brothers ne. Shekararmu biyu tare da ita sai yanzu muka yanke shawarar fada a gida bayan bikin su Zahra. Kina ganin na kyauta idan nace mata na fasa saboda ke?" Roko ne yake yi duk da bai furta yadda zata gane a magana ba amma ta gane a yanayinsa. Duk kishinta tana da hankali kuma tasan daidai. Indai zata zama mallakinsa itama wallahi zata iya hakura ya fara aurenta. Da dai ace da ita ya fara haduwa da labari ya sha bambam amma tunda ita ce tazo daga baya hakuri ya zame mata dole. "A'a" tace a nutse don ta bashi kwarin gwiwa. Farinciki ne ya bayyana a fuskarsa ma'abociyar yawan murmushi "Don Allah kin yarda zaki jirani ko na shekara daya ne na fara aurenta sannan na aureki?" Runtse idanunta tayi wasu zafafan hawaye na gudu ta gyada kai don babu bakin amsawa. Ajiyar zuciya ya saki yana hamdala. Daga Ghazalatu har Alheran yasan babu wata saliha a cikinsu. Ko yasha giyar wake bazai ajiyesu a gida daya ba ma. Rigima ce gagaruma ya hadawa kansa amma baya jin akwai yadda zaiyi ya sabule ko daya a cikinsu. Dukkansu akwai babban al'amari tsakanin iyayensu da nasa kuma babu wadda aka tura masa. Da kansa ya nemi soyayyarsu saboda haka dolensa ya tattaro duk wani karfin hali na maza ya dorawa kansa idan yana son zaman lafiya dasu. "A yau zan koma Katsina in sha Allah babban kakanmu ya dawo jiya bamu hadu ba na taho. Ina komawa zan fadawa Daddy komai don ya fada masa" "To" yaji tace muryarta tana rawa. Tun ba'aje ko ina ba tasan cewa tana da kishiya. Zoben da yake karamin yatsansa na farar azurfa mai matukar kyau da harafin A an rubuta cikin kayataccen rubutu ya cire ya dora mata a tafin hannunta "a hannuna yana nufin Alheran, da sunanki na saye shi da albashina na farko. Amma yanzu sunansa Awwab. Don Allah ina rokonki kada ki bawa kowa chance din neman aurenki. I know naso kaina da yawa amma nayi haka ne don kada wata rigima ta tashi da zata shafi iyayenmu." Son zuciya daban, zahirin rayuwa daban. Tana da kaifin tunanin taya shi hango faruwar abu mara dadi a danginsu idan ya guji 'yar uwarsa ta jini saboda ita. Wani girma ne na musamman taji ya bakunceta ta kara karfafa zuciyarta. Murmushi tayi masa bayan ta goge hawayenta duk ta dame idanunta da hijab din da kwalli. "Kin amince?" Ya sake tambayarta yana kallon kwayar idonta da nasa jajayen idanun da damuwar tsoron rashin amincewarta ta haddasa. "Eh" "Zaki jirani?" "Eh" "Babu ke babu Kawu Zakari da sauran sojoji da likitoci fa" Dariya suka sa a tare ta sake cewa "eh" "Do you love me?" Nauyin maganar taji ta dukar da kanta "eh" "Say it" yace cikin muryar umarni. Kafada ta noke tana dariya kasa-kasa "ni dai bazan iya ba" "Zan kira ki fada min a waya" "Idan Ummi taki bani fa" "Rufe idonki ki ga wani abu" Rufewa tayi ya fito da wayar da ya saya mata taji karamar kara ta bude ido daya a daidai lokacin da ya sake daukarta a hoto. "Mu gani, nayi kyau?" tace a kagauce tana son ganin yadda hoton yayi. "Kin bata min hoton da kuka. Da a haka zakiyi sojan abu kadan kuka?" "Kaine kake sani kukan nan amma ni bana kuka" "Na soyayya ne so ba damuwa, bazan baki hakuri ba ma" yace yana dariya. Kallonta yayi ta sanya zoben a yatsan kusa da karamin ta dago masa hannunta tana tambayarsa ko yayi mata kyau. Ya yaba sosai ya ja mata kunne akan kada ta taba cire shi wai na alkawari ne. Wayar ya mika mata taki karba wai Ummi zata yi fada. "Kinsan da ita na fake na taho garin nan da kunya mu koma tare. Muje na kaiwa Ummin da kaina a baki. Daga nan har na koma aiki sai kunnenki yayi ciwo da wayata" "Idan baka kira ba ma kuka zanyi" "Seriously? Kina sona haka" Bata iya amsa masa da baki ba sai kai da ta daga cikin farinciki mara misaltuwa. ********** A cikin gidan Alh Baba mahaifin Ghazalatu ya danyi karamin gini mai daki biyu, toilet biyu da kitchen saboda iyalinsa idan sun zo gari. Ana gobe zasu dawo daga Umara Gambo da sauran yaran nasu suka iso. Ghazalatu ma komawa tayi ta tayata gyare-gyare. Ana gobe Awwab zai taho wurin Radhiya cikin dare suna hira da mijinta ya sako zancen Ghazalatu. "Ki duba ki gani sa'ar Fauziyya ce gashi suna shirin aure ita sai taron abokai babu wani tsayayye. Tafiyar nan Alhaji kusan kullum sai yayi min fadan wai mun sangartasu gashi bai ji wata magana game da aure ba" Murmushi ya ga matar tasa tayi ya tsaya yana bin ta da kallon mamaki. "Ko gobe kana iya fadawa Alhaji ya fara shiri anyi masa kwacen mata" "Ahhh garin yaya labari ya wuceni?" Yace cikin farinciki. Nan ta labarta masa yadda suka yi da Awwab ranar da ya dawo. Shiru Daddy Haroun yayi har Mummy ta fara tunanin ko zai ce ita ta hada. Da sanyin jiki tace "Babu hannuna fa a ciki Daddy, wai ashe shiru suka yi 'yar banzar yarinyar nan tace sai ta gama makaranta." "Abinda ban gane ba shin Awwab din Major kike nufi ko wanne?" Gambo da saurin fushi ta soma harzuka "Awwab nawa garemu? Idan baka so ne sai inji saboda dan yayata ne kake kinsa ko me" Ya san halin matarsa da saurin hawa kamar farashi kuma dai daga dawowarsa bai shirya rigima da ita a wannan daren ba. "Idan Hassana yayarki ce ni kuma ko ban aureki ba kin san dai kanwata ce. Akwai maganar da naji game da Awwab din ne shiyasa kika ga haka amma gobe dama munyi da Major zai zo muyi magana da Alh Baba sai mu fara clearing issue din" "Wani abu ne ya faru da Awwab din?" "Kinsa batun matar nan da yaranta da yake ta damuwa dasu iyalin sojan da suka je Liberia tare?" "Sosai kuwa, Ghazalatu ma har gidan iyayenta taje ta kwana. Shine tafiyar da nace maka sunyi da Mami din" "Yarinyar wajenta Major yayi min magana akan yana son hadasu da Awwab. Gobe zai zo a gaban su Baba Karami ya gabatar da zancen domin aje ayi magana da iyayensu. Ni da kaina na fara sanar dashi tun a saudiyya" Ko a jikin Mummy Gambo wannan bayani "rashin sanin tsakaninsa da Ghazalatu ne ya janyo amma tunda yanzu sun fada ai shikenan" "Idan kuma ya riga ya fadawa iyayen yarinyar fa?" "Sai aje a basu hakuri. Daddy ba wani abu bane ba fa na tada hankali don Allah." ********** An wayi gari Major yana shirin tafiya gidan Alh Baba inda zai hadu da nasa mahaifin, baban Mami da ake kira Baban Biyu saboda sune manya a 'ya'yansa don bai sami haihuwa da wuri ba sai da ya auro mahaifiyarsu. Cikon na hudun nasu suna Germany ya rasu kuma bisa umarnin Alh Baba jikokinsa biyu daya na wurin mace dayan kuma na namiji za'a aurawa Zahra da Fauziyya. Mami ke fada masa tafiyar Awwab din da ya sulale ya gudu Sumaila duk da Major ya fada masa zasu je gidan Alh Baba da ya dawo daren jiya. Dadi yaji har ransa "kice ko yau aka bukaci sadaki na mika kawai. Allah Yayi musu albarka. Sun gama min komai" Amare Zahra da Fauziyya sun fara gyaran jiki. Wata mata ke yi musu anan cikin gidan. Da Major zai fita sai Zayyana kadai a falo itama zaman jiransa take yi. Hajiyar shagwaba ta rinka marairaice masa wai ya bata kudi Ibrahim yace mata anayin kanwar amarya day jiya da suka yi waya. Dariya yayi harda kyakyatawa "shi Ibrahim din da kansa ya fada miki haka?" "Eh Daddy don Allah ka bani kudin yadda za'ayi min nawa invitation card din" "Kece amaryar?" "Nice mai gayyata amma kuma bani da outfit da zai dace. Please Daddy" Hularsa ya cire ya dan sosa gaban kansa. Yanzu idan yace mata ba'ayi da wahala ta yarda. Ta rinka jero masa tambayoyi kenan shi kuma fitar ce a gabansa. "Jeki ki fadawa Mami kuyi shawara kafin na dawo" "Thank you Daddy" ta rungume shi tana murna sannan ta wuce sakin Mami. Daddy Haroun da Gambo ne karshen zuwa falon na Alh Baba. Sun shigo Major yana gaisawa da surukansa Bilal wanda zai auri Fauziyya da Fawaz mai auren Zahra. Su dinma zuwansu kenan yiwa Alhajin barka da dawowa. Suna fita bayan gaishe gaishe tsakanin su Mummy Gambo da iyayensu ta tashi ta koma bangarensu. Falon akwai 'yan uwansu maza manya wadanda duka tushensu daya ne banda iyayen nasu guda uku. Hira suka taba kadan ana tambayar iyalan juna da dan abinda ba'a rasa ba. "Mustapha" Alh Baba ya kira Major wanda ya tattaro hankalinsa ga uban nasu "Dan uwanka yayi min zancen akwai yarinya 'yar wajen abokin aikinka da kake son hadawa aure da Muhammad ko?" "Eh Alhaji" "Major nace me zai hana mubi abin a sannu kada a takura yaron nan saboda son kara kulla zumunci azo a bata shi" Daddy Haroun yace saboda yana bukatar damar kawo zancen Ghazalatu. Murmushi Major yayi "in sha Allahu wannan matsalar ina tsammanin ta riga ta kau. Maganar da nake maka yana hanyar Sumaila zai je wurin yarinyar" Baba Karami shine mahaifin Major kuma ya fada masa komai kafin ya kawo zancen nan. Murmushi yayi irin na dattijai "to idan sun hada kansu Alh Baba ina ganin ba sai an tsaya bata lokaci ba ko yaya kace?" "Kwarai kuwa, ya kamata ya ajiye iyali hakan ne zai sa ko ina yaje gida zai nufo ba yawon kasashe ba" Daddy Haroun sai ya rasa yadda zai bullowa lamarin. Kafin ya fito sai da ya tabbatar da magana daga wurin Ghazalatu. Shirun ba zai zama alkhairi ba kada aje ayi hukuncin da zai jawo matsala a gaba. "Jiya Gambo take fada min Awwab din da Ghazalatu sun daidaita kansu ashe. Ina ganin me zai hana mu jira ya dawo aji ta bakinsa" Murmushi sosai Alh Baba yayi yana nuna farincikinsa bisa yadda al'amura suka kasance. Lallai ba karamin kara hade zumunci za'ayi ba idan akayi wannan auren saboda iyayensu duka 'yan dangi ne. "Wannan shine tuwo na mai na" inji Baban Biyu. "Kai da baka san da wannan din ba kake kokarin nema masa auren wata?" Baba Karami ya tambayi Major wanda zancen gabadaya yazo masa a bazata. "Wallahi ban sani ba Baba" "Tunda abu yazo da haka Mustapha ita waccan yarinya a barta. Ko bai aureta ba daga ko ina zaka iya tallafawa rayuwarsu. Idan yaso sai ya auri kanwarsa" Baban Biyu yace yana bin 'yan uwansa da kallo domin neman amincewarsu. Hankalin Major tashi yayi sosai bai taba zaton da faruwar wannan lamari ba. To garin yaya shi bai sani ba kuma Mami ma baya tsammanin ta sani. "Gambo cewa tayi tana so a hadasu ko sun hada kansu ne? Wallahi ni ban taba jin zancen ba. Babarsu ma bana jin ta sani" Daddy Haroun sai ya ga tambayar kamar yana nufin kirkira suka yi shi da matarsa sai yaji ransa ya sosu "ba wani abu ne na jayayya ba Major, tunda da alamu kafi son ya auri ita waccan yarinya sai ayi haka din." Sassauta murya Major yayi duk kuwa da cewa nasa ran har yafi na Daddy Haroun baci "ba zamuyi haka ba, mamaki kawai nake yi nace ban sani ba amma ba wai na karyata bane." "Duk da haka ya auri wadda ka zaba masa tun farko ita Ghazalatu ayi maganarta daga baya idan ta sami wani" "To iyayen 'ya'ya. Idan kun gama yanke baku hukuncin sai ku saurari nawa. Mustapha, Haroun, nawa hukuncin shine Muhammad zai auri Ghazalatu. Ita kuma wannan yarinya tunda bamu riga mun shiga ciki ba Allah Ya bata wani. Bazan so wata baraka ta taso a cikinku ba saboda wannan dalili. Hakan yayi ko?" Ya juya ga Baban Biyu da Baba Karami. Duka su biyun sun nuna amincewarsu. Major bai yi shiru ba duk da haka saboda ance mai daki shi yasan inda yake yi masa yoyo. Shine yasan Zayyan kuma shi yasan me yasa yake kwadayin hada alakar auratayya a tsakanin zuri'arsu. Burinsa su dunkule ta yadda ko bayan ransu a gaba zuri'arsu zata zamo daya. Wannan shine tanadinsa ga Awwab kamar yadda yadda yake da kudirin hada Ibrahim da Zayyanatu. "Alhaji ku gafarceni ban tari numfashinku ba. Ina neman alfarmar don Allah a bashi damar hadasu duka. Yarinyar da nake magana a kai Radhiya ban baro kakaninnta ba sai da nayi musu alkawarin hadata aure da Awwab" "MUSTAPHA!!!" Baba Karami ya daka masa tsawa da kakkausar murya. Duk cikin iyayen nasu ma shine mara fada amma yadda ya kira sunnan dan nasa ya bashi tsoro. "Alh Baba ya yanke hukunci, mu mun amince sai kaine da ka haifi Muhammadu kake son nuna mana iyakarmu? Da can wane dalilin ne yasa kayi musu alkawari batare da kayi shawara da kowa cikinmu ba?" "Ku gafarceni Baba in sha Allahu yadda kuka ce hakan za'ayi. Zanje na basu hakuri." Babu abinda Daddy Haroun bai sani ba game da labarin dan uwan nasa shiyasa yaji tausayinsa da yace ya riga ya fadawa iyayenta. Ai da kunya ace kuma ya koma yace musu an fasa "Baba don Allah kuyi hakuri kada maganar nan ta janyo rikici. A bar Awwab ya auri yarinyar. Ghazalatu kuma ko cikin 'yan uwa sai a sama mata wani" "Ka bar wannan magana Haroun in sha Allahu Ghazalatu zai aura. Zanje nayi musu bayani" Alh Baba ma nasa ran ya soma baci yace "nace na gama magana kuma nan da wata uku za'ayi auren. Idan ya dawo ka turo min shi. Ku tashi ku tafi kuma kada ku yarda maganar nan ta kai kunnen iyalanku. Biki ne dasu ku barsu su gama a nutse bana son kananan maganganu" Sun fito Major ya rasa abinda yake yi masa dadi. Daddy Haroun yana son farincikin 'yarsa ta wani bangaren yana duba cikin tsakar da dan uwansa zai shiga. Jikin motar Major suka tsaya drebansa ya taso da sauri Daddy yayi masa alama da ya basu wuri. "Major ka bani lokaci zanyi magana da su Alhaji. Babu girma ka koma ka cewa mutanen nan an fasa ko abu makamancin haka" Murmushi yayi kansa ya kulle yana neman mafita "ka bar maganar, nine nayi abu bisa rashin sani dama saboda haka zanyi kokarin daidaitawa. Tunda sun hada kansu da kanwarsa bamubda dalilin cewa wani ya hakura" yayi maganar da tunanin cewa idan da gaske hasashen Mami akansa da Radhiya gaske ne ita za'a ce ta hakura kenan saboda ita ba danginsu bace? Kuma da kunya matuka ya kalli idon Daddy yace tasa 'yar ta hakura. "Mafi dacewa Major ya auri su biyun. Ka sa min ido zan sake magana dasu." Shima Major yayi wannan tunanin to amma yanayin aikin Awwab din anya auren mata biyu lokaci guda zai haifar musu da da mai ido kuwa? Kansa yaji ya soma sara masa yayi sallama da Daddy Haroun ya shige mota domin tafiya gida. A hanyar ma dai tunani yake ta yi yana neman mafitar da ta dace. Iyayensu idan ya koma garesu ma bai san me zai ce dasu ba kamar yadda bai san me zai ce da iyayen Radhiya ba. Gajeren tsaki yaja a lokacin da ya dauko waya ya fara laluben nambar Awwab. Gara dai yaji ta bakinsa kafin yasan me ya kamata yayi kuma. ********** Ayuba yana zaune gaban Ummi Mairama ya gama yi mata addu'a yana tofawa idanun yace "Adda Mairama anya ba sihiri bane wannan makantar? Ciwon kan nan da kike ji tun jiya sai nake ganin kamar addu'armu ce take ci." "Allah Yasa Ayuba, amma ni kuwa waye ya tsaneni haka da zai yi min asiri?" Roba biyu ya yiwa tofin ayoyin tsari da neman sauki ya kuma tofa mata a kan fuskarta sannan ya tashi zai fita. "Ka turo min yarinyar nan bana jin ko abinci ta baiwa Awwab sai suru....suruuuu" wani irin haske ne wal ya shiga cikin idonta ga alamun mutum tana gani sai wani matsanancin ciwon kai kamar an kwada mata guduma. Rike kan tayi da hannuwanta biyu sosai tana ji kamar zai fadi. "Ayuba....wayyo Allah kaina Ayuba" Da sauri ya dawo gabanta ya durkusa sai dai ciwon da take ji yayi tsananin da ya sumar da ita. Ayuba ya hanzarta fita yana kiran su Yadikko a lokacin Radhiya da Awwab suke tahowa dakin zai bawa Ummin wayar da ya siyo taki karba suka ga ana tururuwar shiga dakin ana cewa Mairama ta suma. A guje Radhiya ta shiga ta samu ana shafawa Umminta ruwa a fuska amma ko motsi bata yi. Kuka ta saka Awwab yace su fito da ita zai je ya matso da mota kofar gidan. Shima a kidime yake musamman ganin irin kukan da Alheran dinsa take yi. Ayuba yana ganin haka yace su kyale masa ita su matsa gefe. Radhiya dai babu inda zata je sai ma kan Ummin da ta dora akan cinyarta. Da alwalarsa dama ya dauko littafi mai tsarki ya bude suratul Baqara ya soma karantawa yana yi ya umarci Radhiya ta rinka shafa mata ruwan tofin nan. Atishawa tayi mai karfi a hankali ta soma bude idanuwanta wanda suka sauka akan fuskar 'Yar Soja Alheran 'yarta da Zayyan. Murmushi tayi ta daga hannu ta shafa fuskar Radhiyan wadda bata gane me yake faruwa ba sai da taji tace. "Ashe ma na fiki kyau" Tana kuka tana dariya tace "Ummi kina ganina? Me nake yi yanzu?" Ta murguda bakinta gefe yayin da Awwab ya dawo ganin me ya hanasu fitowa. "Hmmm bakin tsiwar kenan ake murguda min" Wata wawiyar runguma Radhiya ta kai mata tana murna. Kowa a dakin sai san barka. Ayuba kuwa cewa yake kuyi ta kabbara yau ko waye ya yiwa Adda Mairama asirin nan Allah Ya dandana masa abinda taji. "Malam da kanka?" Inji daya daga cikin amaren da za'ayi bikinsu nan da 'yan kwanaki. "To na janye...mu godewa Allah da wannan ni'ima da Yayi mana. Da kaina zanje wurin Malamijo a gona nayi masa albishir" Dariya suka yi Ummi tana binsu daidai da taimakon murya tana ganesu. Kyakkyawan matsashin da ta gani a jikin kofa yana murmushi fuskarsa mai cike da annuri ta yafito da hannu. "Haka Awwab dina ya koma" Hannunta ya kama ya rike gam ya kalleta ya kalli Radhiya da nata bakin itama yaki rufuwa. Wayar Ummin tasu ta dauka cikin hanzari ta kira Emzee ta fada masa wannan daddadan albishir. "Ki taimaka ki rufe fuskarki da zani sai na dawo ta ganmu tare" yace yana fita daga dakinsu zuwa falo ya fadawa Mama Zainab. "Sorry yaro ni ta fara gani" "Bata wayar" Ummi na karba ya soma rokon ta rufe ido ta bar ganin mutane haka sai ya dawo. Dariya dan nata ya bata. Sun gaisa da Zainab tace zata turo su a yau don bata jin Karami zai iya bacci. Awwab ma Mami ya fara kira ya fada mata sannan ya kira Major da yake hanyar komawa gida daga gidan Alh Baba. "Ina ka shiga ina ta kira tun dazu?" Hakuri ya fara bashi sannan ya fada masa abin alkhairin da ya faru "ina isowa na kiraka nima" "Na gani ina tare da Alh Baba ne." Murnar budewar idanun Mairama ta hana shi tambayarsa meye tsakaninsa da Ghazalatu. Zai jira shi ya dawo din sai suyi magana. Sai dai ciwon kan da take ji wanda da alamun haske ne yayi mata yawa ya fara addabarta. Awwab yace gara a kaita asibiti ko akwai abinda zasu bata. Shi ya kaisu asibitin suka bata magunguna aka koma gida. Hudu har gota Ummi tace yayi hakuri da tafiyar sai da safe. Abinci aka kai masa tsakar gida wurin Malamijo sai ga Radhiya ta tazo tace ciwon kan na Ummi ya sake tashi ko bude ido ta kasa. "Ko dai babban asibiti zaku kaita. Dama can fa tana da lalurar idanun kafin wannan makantar" cewar Nene Marka. Rabon ayi komai da Awwab yazo Sumaila a ranar. Nene, Ummi da Radhiya ya dauka suka nufi Kano domin a samu ta ga babban likitan ido. ********** Maza ne manya manya majiya karfi masu kirar da kai tsaye zata razana mutum su biyu aka budewa kofar karfen da mukulli ne kadai zai iya budeta saboda tsananin karfinta. Mutum hudu suka tarar a ciki kowa da katifarsa a jikin bango. Uku hira suke a junansu cikin wani yare yayin da cikon na hudun yake zaune ya tankwashe kafafunsa akan katifar yana tunani. Dogon mutum wankan tarwada wanda kallo daya zai sa ka gane wahala ce ta kara masa shekaru ba don ya kai hakan ba a zahiri. Kana iya ganin furfura kadan a cikakken bakin gashinsa. Dukkan wata cikakkiyar kamala ta mutumin kirki ta tabbata a fuskarsa. Sai dai zuciyarsa wadda kuncin rayuwa ya yiwa dabaibayi tasa baka ganin walwalarsa. Wanda yafi girma cikin mutanen yana zuwa da izgilanci yaje ya take katifar da kafa daya yana karkada masa yatsa a gaban fuskarsa. "Tashi nan nake son na rinka kwanciya" Dayan na bayanshi yana dariya a nan din ma sai sun gwada rashin mutumci irin wanda yayi musu sanadin fadowa wannan gida. Maza ukun da hira suna ganin abinda ake yi masa suka taso suna nade hannuwan riga "idan kana da matsala a dakin nan ka nemi daya daga cikinmu amma ba'a taba 3810" "Ku kiyaye Boss dina baya son raini fa" Dayan da suka shigo tare yace musu yana zaro idanu. "Alamu sun nuna kun shigo prison da zafin kai, sai dai ko zaku gwada hali kada ku taba shiga harkar OUR ZAYYAN. Muna jurewa komai banda bacin ransa" Basu daddara ba dayan ya daga hannu zai mari Lt Zayyan Muhammad Tureta mai lambar prison 3810 wadannan maza uku suka far musu fada ya kaure a tsakaninsu. Yana nan zaune inda yake har gandirobobi suka shigo rabasu. 🏽 [11/2, 6:51 AM] 🏽 : 32.💕 TUNA BAYA "Daga hannuwanka ka dora a bayan kanka" akace daga bayansa da gurbataccen turanci. Ruwa, iska hade da hayakin wutar da take ci sakamakon tashin bom din wurin yasa ganinsa yayi rauni amma duk da haka ya fahimci ba mutum daya bane a wurin. A kalla sun kai su takwas ko sama da haka kowannensu yana nuna shi da bindiga. Hankalinsa ne yayi mummunan tashi da ya tuna cewa muddin aka harbe shi dole zai daga kafarsa daga kan wannan land mine din. Yana dagawa kuwa banda wadannan mutanen harda Major da Hadir a cikin wadanda zasu iya rasa rayukansu. Dole ne ya kara musu lokacin yin nisa da wurin kafin mine din ya tashi. "Kuyi hakuri ko me kuke bukata daga gareni zanyi muku amma kada ku harbe ni. Akwai landmine a kasan kafata" Dariya suka kwashe da ita tamkar basu fahimci nasa turancin ba. Bai hakura ba ya cigaba da cewa su taimaki kansu suyi nesa dashi kada su mutu tare don bai san karfin abinda ya taka ba. "Get down" wani gabjeje yace masa fuskarsa babu digon imani a cikinta. Zayyan ya sake cewa akwai bomb a kasan kafarsa. Mutumin a fusace ya matso gabansa ya daga kasan bindigarsa wurin fadin ya maka masa a gefen fuska. Wani mahaukacin zafi, radadi da zugi yaji a take turame biyu cikin hakoransa suka fita ya furzar dasu tare da jini. Duk da haka kafarsa yake kokarin dannewa a kasan kada ya tayar da bomb din 'yan uwansa basuyi nisa ba. Idanunsa suna kan hanyar da Hadir ya bi. Mutumin ya bi wurin da kallo ya yiwa wani nuni da ka. Sai gashi a gaban idon Zayyan mutumin ya cizge irin abin kasan mulmullalan bomb dinnan ya dage ya jefa shi hanyar da suka bi din. Wannan shine bomb din da Major da Hadir suka ji wanda karfinsa yayi sanadiyar fadawarsu kwazazzabon da firgici yasa Hadir bai kula dashi ba. Mutum biyu suka zo suka damki Zayyan wanda ya saki ihu sosai sakamakon tashin bomb din yana mai cike da tsoron ko ya shafe su. Zuciya ce ta debe shi ya tuna irin ta'asar da suka yiwa gabadaya rundunar da suka taho wurin da niyyar taimako. Mutane biyun ya sakalawa hannuwansa a wuyansu ya daga kafar da niyar dukansu su mutu tare akan sai sun tafi ya mutu shi kadai. Ko babu komai ya sadaukar da rayuwarsa ya rage mugun iri. Runtse ido yayi yana jiran yaji ya tashi sai dai maimakon kararsa sai sautin dariyar muguntarsu yaji. Wani cikinsu ne ya taho daga shi sai dogon wando da singeletin da ba lallai a gane ainihin kalarta saboda mugun datti yazo ya durkusa a gabansa ya ciro abin da suka binne a wurare daban daban masu yawa domin danawa mutane tarko. Duk wanda yayi tunanin landmine ne yaki dauke kafarsa ya zama nama a wurinsu inda zasu fito daga mabuyarsu su kama shi su azabtar domin neman bayanai. Zayyan yana ganin haka yayi kukan kura ya kwace jikinsa daga wadancan biyun ya fada kan wancan. Abinda yaje dauka yayi sa'ar samu wato bindigar da take aljihun wandonsa ta baya. Baiyi wata wata ba ya saita kansa ya sakar masa harsashi. Wadancan suna daga inda suke suna kokarin harbe shi da bindiga yayin da ogan nasu yayi wani irin ihu saboda kaninsa ne Zayyan ya kashe ya sake saita mutane biyun da suka fi kusa dashi suma ya harbesu yana daga durkushe. A take wurin ya hade sai sautin harbi kake ji amma karfin ruwa ya bawa Zayyan damar kubcewa. Ya sadakar dama yau mutuwarsa tazo amma bai hakura da harbin ba sai da ya sake kara mutum biyu sannan aka same shi a hannun da yake harbin dashi. Dole ya saki bindigar kafin ya farga wannan ogan nasu ya kafta masa bindiga a tsakar kansa ya fadi a wurin sumamme. Wani irin abu yake ji kamar ruwa yana zuba a fuskarsa amma kuma a shake yake. Yayi ta yunkurin bude idanu amma ya kasa sai wani irin abu kamar an like idanun suna ta radadi. Duk wani tunaninsa ya tsaya cak kwakwalwar ta cushe. Sai bayan wani lokaci yana cikin wannan yanayi na shakewa da ruwa ya soma turjiya ya gane kafafunsa daure suke a jikin wani abu sannan hannuwansa ma an daure su ta baya. Hannun da aka harba dama tamkar ba a jikinsa yake ba saboda kumburi da ciwo. A kokarinsa na mikewa tsaye ne ya gane cewa akan kujera yake a zaune. An daure kafafunsa da jikin kujerar hagu da dama. Hannuwansa kuma suna daure ne ta baya harde da juna. A takaice ma tsumma ne aka dora akan fuskarsa ana kwarara masa ruwa wani ya rike kan ta bayansa. Sai da suka tabbatar ya azabtu iyakar azabtuwa aka cire tsumman. Tari ya rinka yi a wahale ruwa na fita ta baki ta hanci. Idanunsa sun juye ya kasa tantance a ina yake ga rashin wadatar haske a dakin. Hargagin mutane yaji aka bude kofar hasken rana kwal ta mamaye dakin. Wasu mutane ne suka shigo kai tsaye wurinsa suka nufa. Bayan sunyi magana da yare ne suka koma turanci aka tambaye shi mutum nawa ne a sansaninsu da sauran. Sojoji nawa ne Nigeria ta turo domin kwantar da tarzoma kuma a ina da ina suka kafa sansani. Idan ma zai iya magana bazai fada musu ba saboda duka jikinsa hatta bakinsa da hakora suka cire jiya da suka dauko shi ciwo suke yi. Dukansa suka fara yi saboda yaki yin magana sai yaji muryar wani shima a wahale yake yace suyi hakuri ya sami lafiya sai ya basu amsar da suke nema. Marinsa wani yayi suka ce yayi musu shiru. Sai da suka sake yiwa Zayyan ligi-ligi sannan suka yasar dashi a kasa suka tafi. Mutanen wasu tsageru ne cikin 'yan tada kayar baya da gwambatin kasar ke nema ruwa a jallo. Su kuma suna son dakile taimakon da kasarsu take samu na jajirtattun sojoji musamman daga kasarmu mai albarka Nigeria. Shiyasa suke yi musu dabaru suna kashesu suna kama na kamawa domin neman bayanai. Har yanzu dai babu nasara domin sojojin sun dauki amanar kasarsu jini da tsoka. Idan suka kasa samun abinda suke so sai su kashe mutum. Bayan fitarsu dayan mutumin da yake dakin ya janyo shi da kyar zuwa wani dan lungu. Tsohuwar katifa ce a wurin da 'yan tarkacen asibiti. Kwantar da Zayyan yayi akan katifar ya farke hannun rigarsa da ya kumbura. Ga dukkan alamu bullet din da ya same shi yana ciki ga uban kumburi fitar dashi zaiyi wahala. Shi kanshi mutumin wahala ta zuge shi duk ya rame. Wata siririyar wuka ya dauko ya kunna lighter da take ajiye a gefe ya rinka saka tsinin wukar a cikin wutar na dan lokaci ya dauki zafi sannan ya mika masa wani tsohon yagwalgwalallen filo ko riga babu. "Put it in your mouth" "Wwwwhat?" Ya fada idanunsa akan filon da babu kyaun gani. Bai rufe bakinsa ba mutumin nan ya tura masa filon lokaci guda kuma ya danna wukar cikin hannunsa saitin inda yake iya ganin alamun bullet din ya shiga. A maimakon kara Zayyan cizo ya kaiwa filon har hakoransa suka kusa hadewa ta ciki don azaba. Juyi biyu mutumin yayi da wukar sai ga bullet ya fado kasa. Zayyan yayi gumi ba kadan ba idanunsa sunyi jazur sai jijiyoyin kansa da suka mike. Kwanciya yayi mutumin yana masa sannu. Babu bakin amsa sai kai yake gyadawa. Daga wannan lokacin bai kara sanin me ya faru ba sai farkawa yayi yana jin kamar ana dukan wani ga dare. A take ya wartsake ganin mutumin da ya taimaka masa ne ake yiwa dukan kawo wuka. Mantawa yayi da ciwon jikinsa ya tashi a fusace yayi kansu. Ransa ya kara baci ne da ya fahimci dalilin taimakonsa da mutumin yayi ne ake masa haka. Dukan ya koma su biyo ake yiwa amma Zayyan bai hakura ya janye jikinsa ba. Sai da suka gaji don kansu suka fita aka barsu a kasa kowanne jiki yayi laushi. "Allah Ya isanmu tunda kunfi karfinmu....ashhh bakina" hannu ya dora daga gefen kumatunsa bangaren da hakoran suka zuba. Wahalalliyar dariya wancan mutumin yayi daga inda yake. Zayyan ya dinke fuska don ya jigata sosai yace "baka daku bane kake dariya, ni yanzu suka sake dawowa suman karya zanyi" Dagowa mutumin yayi da kyar Zayyan sai ya koma turanci "are you okay?" Dariya mutumin ya sake yi sai abin ya dan bashi tsoro ya ja jikinshi kadan ba dai mai matsalar kwakwalwa bane ko. "Duk wannan dukan da muka sha ka sani dariyar dole" kallon mamaki Zayyan yayi masa yana jingina bayansa da bango ya dora da cewa "ina kallonka nayi tunanin kaima bahaushe ne" "Kaima dan Nigeria ne?" "Soja kamarka" yace da muryarsa da take a kausashe kamar wanda ya tashi daga bacci ko aka shake masa wuya. Zama Zayyan ya gyara yana kallon mutumin sosai. Wannan zai girmewa Major Mustapha sai dai rashin khaki a jikinsa yasa a haka bazai iya gane mukaminsa ba. "Lt Zayyan Muhammad Tureta, Giginya Army Barrack Sokoto" "Colonel Nasiruddeen Aliyu, Bukavu Army Barrack Kano" Soja ya ga ubangidansa, da ciwon hannun nasa haka Zayyan ya yunkura ya mike yana dafa bango ya dan kame jikinsa yayi masa salute. Kai Col. Nasiruddeen ya kada yana dariya "baka daku bane shiyasa kake iya tashi, ni yanzu suka dawo cewa zanyi mace ne ni da kayan maza" Ga wahala ga ciwo Zayyan sai da ya bushe da dariya. Sun dan zauna shiru kafin Col. Nasiruddeen ya soma bashi labarin dalilin zuwansa wurin. Col. Nasiruddeen Aliyu mutumin karamar hukumar Wase ne ta jihar Plateau. Likita ne na sojoji wanda yake kwararren consultant a asibitin sojoji na Bukavu barrack a Kano inda yake base dinsa. Rabon wannan wahalar da kansa ya nemi a sanya sunansa cikin masu tahowa Liberia saboda burinsa na taimakawa sojojinsu. Sai aka shi turo a matsayin Cheif Medical Officer tare da wasu mutum uku su ma duka sojojin ne kuma likitoci. A lissafinsa yayi a kalla wata biyar tare da mutanen nan. Watarana sun sami rahoton rigima tsakanin sojojin kasar da abokan rikicin nasu inda mutane da yawa suka jikkata ana bukatar likitoci domin taimakon gaggawa. Shi da sauran da suke sansani guda inda yake a matsayin wurin kula da masu rauni suka dunguma da kayan kula da marasa lafiya da magunguna. Rabin tafiyar suka yi kamar yadda aka shammaci su Zayyan su ma haka aka yi musu. Bayan musayar harsashi an kashe mutum biyu cikinsu sauran kuma aka kadasu aka tafi dasu. Akan idanunsa saboda sun san shine babba a cikinsu aka rinka kashe na kasa dashi don sunki bada bayanan da ake bukata. Akwai takardu a jikinsa na bayanin sojoji masu tahowa, ranar isowarsu da ma adadin makamai, abinci da magunguna da zasu taho dashi. Tsoron kada a cutar dasu ya sanya ya fakaice su ya dunkule takardar ya cusa a bakinsa ya hadiya farat daya. Stapler din da take jiki wadda aka mannesu tare ita ce a lokacin hadiyar yana ji tana kartar masa wuya har ta wuce. Bai fahimci mugun rauni tayi masa ba sai da aka zo yi masa tambaya yana bude baki sai jini ya rinka zubowa ga uban radadi daga cikin wuyan nasa. Ya sha wahala sosai karshe muryarsa ta koma haka bayan wani lokaci. Babu ko mutum daya saura cikin abokan tafiyarsa duka an azabtar dasu an kashe. Shi kuma sun mayar dashi likitansu. Abubuwan da ya gani da idanunsa mutanen suna yiwa bayin Allah ba kadan bane, jiran amfaninsa ya kare kawai yake yi shima su kashe shi. Zayyan ya tausaya masa shima ya fada masa yadda ya fado hannunsu. Ranar hirar da suka yi kenan kafin wahala ta sa suyi baccin dole. Wurin da suke ba cikin daji bane hasali ma a cikin gari ne mutanen suka samu wani tsohon gini da rigima ta kori masu shi suke dabdalarsu a ciki. Tsaron da suke masa yasa har yanzu ba'a gano suna zuwa wurin ba. Sanyin asuba ne ya farkar da Zayyan ya tashi ya ga Col Nasiruddeen shima ya farka. Gefe yaja jikinsa ya bubbugi kasa ya dawo. "Rabona da sallah tun la'asar ta ranar da muka fito" "A haka zaka yi sallar babu alwala ko tsarki?" "Akwai ruwa ne a kusa?" Zayyan ya tambayeshi yana leka lungunan gidan. "A'a sai dan wanda suke kawo min tare da abinci. Idan yana da yawa dashi nake yin alwalar nayi sallolin da suka samu" Murmushi Zayyan yayi masa "shiyasa Allah Ya hore mana taimama domin saukakawa a inda ruwa yayi karanci." Col. Nasiruddeen bai nuna girman kai ba ya bari Zayyan ya koya masa. A zaune duka suka yi sallah jiki ya kara tsami. Zayyan ya dade yana yi saboda yasan wanda suke kansa da yawa. Addu'a yake ta yi Allah Ya tseratar dasu, Yasa su Hadir sun tsira kuma Ya maida shi ga iyalinsa. Sai da rana tayi sosai aka miko musu plate da wani abu da Zayyan bai gane shinkafa ce, gero ko wake ba. Gashi nan dai a cure wuri guda. Col. Nasiruddeen yunwa ta galabaitar dashi ya rinka turawa kawai. Shima Zayyan sai ya ga bashi da zabin da ya wuce ya taya shi ci. Ba dadi ba dadadawa amma haka ake basu wannan abincin suna ci. Sabo ne ya rinka shiga tsakanin wadannan bayin Allah da suke rayuwa a inda iyalansu da kowa nasu yake tunanin sun mutu. Kullum dare bayan 'yan tawayen nan sawunsu ya dauke daga dakin hirarsu sai ta karkata ga iyalansu. Dukkansu har jiran dare suke domin su saukewa juna nauyin zukatansu. Matsananciyar kewar iyalansu tana damunsu tana ci musu zukata. Yau ma bayan wata daya da kama Zayyan suna hira Col. Nasiruddeen yake cewa. "Idan Allah Ya fitar dani daga wurin nan ina komawa abu na farko da zan fara yi shine yin ritaya. Zayyan na bar aikin soja har abada wallahi" "Ka dena fadin haka Sir. Ni ka ga a duniya ban taba gani ko sha'awar wani aikin ba bayan shi." "Da kuruciyarka ni kuwa girma ya soma zuwar min. Sa'annina da kannena suna kwance comfortably da iyalansa a wannan lokacin ina zaune a inda Allah kadai ya sani cikin wari da kazantar najasata. Babu wanka babu abinci mai kyau sannan duk abinda zamuyi sai dai mu yi shi a inda muke kuma mu kwana a ciki" "Saboda abinda Allah Ya zaba maka kenan. Ya halicci mutane bayan kariyar da yake bamu da IkonSa kuma ya sanya mu garkuwa a garesu masu taimaka musu. I believe we soldiers are not made...we are born to protect (na yarda mu sojoji ba yinmu ake yi ba....haihuwar mu ake yi domin bada kariya)" "We are special, nima na yarda...." Col. Nasiruddeen ya amsa da murmushi a fuskarsa "amma bazan cigaba da sacrificing rayuwata ga mutanen da basu san nayi musu ba. Ni da wannan aikin sai dai idan mutuwa nayi a wurin nan" Dariya ya bawa Zayyan yadda ya hade rai da gaske ya gama da aikin soja "wannan magana fa kamar a kunnen Arifah. Nasan zata so ka cigaba da aiki muna biye daku" Kafada ya noke kamar yaro "ko me zata yi sai dai tayi kuwa. Idan na mutu bakin aiki wa take dashi da zai kula min da ita? Burina kawai na koma gida na cigaba da bata kulawa. Shekara da shekaru ina neman haihuwa amma don ganganci ban tashi barin gida ba sai da na sami 'yar. Idan na mutu fa duka duka shekara hudu muka yi tare. Kila ma ta manta dani gabadaya" Sai kuma ya bawa Zayyan tausayi. Col ya fada masa yadda ya kwashe shekaru shabiyar da aure tun da kuruciyarsa babu haihuwa sai akan Arifah. Yana son tilon 'yarsa kamar rai. Ranar da zai taho Liberia da kansa ya kaita makaranta nursery da take ta rinka kuka sai ta bishi. Zuciyarsa ta karye, ya baro mamanta tana nata kukan a gida itama tana yi kuma daga nan Lagos zasu wuce. Da kyar ya rarrasheta aka karbeta daga cikinsa tana ihu ya bar harabar makarantar. Ranar da yaji labarin iyalin Zayyan ya tausaya masa matuka. Cewa yayi kada Zayyan ya kuma kiransa da wani abu da zai alakanta shi da soja sunana Baban Arifah shi kuma yana kiransa Baban Alheran. Kwana uku a tsakani Zayyan ya soma tunanin hanyar guduwa. Sai da Col. Nasiruddeen yayi ta bashi shawarar kada ya fita ya fishi dadewa kuma shima ya gwada babu sa'a amma yaki hakura. Ta yaya zai hakura bayan kullum sai anzo an bashi wahala domin ya bada bayani shi kuma yaki. Sai ma zancen kashesu da aka fara wai zasu bar wurin an kusa gano su. Shiyasa yaga ya dace dole su nemi hanyar tsira. Lallabawa yayi yana neman hanyar fita ya hango tawagar 'yan tawayen sun shigo wurin a guje. Masu gadin nasu da wasu kowa hankalinsa ya tashi. Cikin ikon Allah ya hango mutum biyu da kayan sojojin kasar amma umarni suke badawa a tabbatar babu wanda ya tsira a cikinsu. Su duka masu laifi. "Shot on sight" (a harbe duk wanda aka gani) yaji ana bada umarni daga waje. A guje ya koma ciki ya gano wani bari na katangar da ya dade yana tunanin haurawa sai kuma ya fasa ya shige inda suke ya tada Col. Nasiruddeen da yake bacci. "Baban Arifah we need to run" "Baban Alheran nace..." Harbi suke ji da ihun maza da alamun guje guje. A gaggauce shima ya mike suka nufi wannan katanga. Zayyan ya haura saman ya miko hannu domin taimakawa Col. Nasiruddeen amma ya kasa saboda bashi da tsaho sosai. Ga tsira yana gani amma ya gaza. Idanunsa hawaye fal suna jin harbin yana kusanto inda suke yayi saluting Zayyan. "It was nice meeting you Lieutenant. Take care" Zukatansu sun karya su duka. Zayyan sai tuno Major Mustapha da dan uwansa Hadir yake yi. Soja shi kadai yasan ciwon soja. Durowa yayi kasa kafarsa tayi kara duk da haka ya kama Col. Nasiruddeen da mamaki mai tsanani ya kama shi na karamcin wannan yaro. A kafadarsa ya dora shi ya mike tsaye. "Baban Arifah haura" Col. Nasiruddeen ya mika hannu ya haye katangar bai sauka daya barin ba ya gano sojojin kasar da 'yan tawayen sun taho wurin gadan gadan. Su ma 'yan tawayen katangar suka zo haurawa. A gigice yace "yi sauri Zayyan" Zayyan ya mika hannu ya hau katangar bai haura da kafafunsa ba bullet ya shiga kafadarsa. Col Nasiruddeen ya ga sanda aka yi harbin ya sa hannu zai janyo shi wani bullet din ya sami Zayyan a baya. Jikinsa ya saki duk yadda Col. Nasiruddeen yaso ko da gawarsa ce ya fitar daga wannan tsinannan gida bukata bata biya ba domin fadawa yayi baya aka cigaba da harbe harbe. Col. Nasiruddeen ya sauka ta daya barin yasa gudu yayin da aka duba masu rai cikin 'yan tawaye harda Zayyan aka yi awon gaba dasu. Taimako daya aka yi musu shi da sauran masu ran an cire musu bullets din jikinsu. Amma an gwada musu izaya da azaba nau'i daban daban domin su fadi inda sauran suke abu yaci tura. Sauran uban taurin kai ne yake damunsu shi kuwa Zayyan banda rashin sanin komai ya dage shi dan Nigeria ne. Da suka ga ya dage sai suka yi bincike akan unit da yace a cikinsu yake. Tashin farko akace wani mai suna Hadir Murtala ne kadai ya tsira a cikinsu tare da mutum daya daga wani unit din wato Major Mustapha. Abu na ceton rai sauran ma kowa ya fara cewa shima wani ne baya cikin wadannan 'yan tawaye. Zasu fara dogon bincike aka kaiwa wani babban barikin sojojinsu mummunan hari wanda ya janyo gabadaya mutanen da aka kama harda 'yan wani kauye da tsautsayi ya ritsa dasu duka aka maka su a kurkuku. Da fari Zayyan kusan hauka yayi a wurin. Tunanin iyalinsa yake yi. Mairama da Alheran da cikinta da yake tsammanin ta riga ta haife shi yanzu. A wane hali suke koma waye yake duba iyalansa? Yakan dauki tsahon lokaci yana zubar da hawaye masu zafi da kona zuciya. Uzurinsa na cewa shi ba dan tawaye bane bai karbo ba domin mutanen da ake kamowa sun hada da magidanta da matasa bisa tsautsayi. Kowa cikinsu kuma ya dage shima ba dan tawaye bane. Sai ake rasa gane waye mai gaskiya da makaryaci. Dadin matsakar kasar babu zaman lafiyar da zai bada damar a bata lokaci wurin sauraren korafinsu. A irin haka sojojin kasashe da dama suke riskar kawunansu a kurkuku daga zuwa kai dauki ga kasashen da suke cikin rikici. Sannu a hankali ya karbi kaddararsa da hannu bibbiyu ya fawwalawa Allah lamuransa. Baya shiga harkar kowa a wurin sai ma shi da akan sami masu shiga tasa. Sai ayi masa duka bai ko daga yatsa. Rayuwarsa ta kuntata komai ya fice masa a rai. Daga baya ne ya sake rungumar addini fiye da baya har kusan kowa ya sallama masa hadda wadanda ba musulman ba kuwa. Zaman lafiyarsa da yanayin mu'amala yasa ya shiga zukatan jama'ar wurin. Zayyan Muhammad Tureta tun asalinsa mutum ne mai shiga rai shiyasa a nan din ma ya zama na kowa. Babu wanda zai yi yunkurin taka Zayyan wasu basu saita masa zama ba. Col. Nasiruddeen yayi nasarar komawa gida ga iyalinsa. Satinsa guda da komawa yasa aka binciko masa barikin su Zayyan. Daga can ya sami kwatancen gidan iyayensa. Da kansa yaje Sakkwato ba sako ba har kofar gidansu. Da yake wahala bata yankewa su Mairamu ba a wannan lokaci da yasa ayi masa sallama da dan uwan Zayyan ba wanda ya fito sai Maikudi. Ya ga mutum a fige saboda tsabar wahala sai hanci dan firit. Yanayinsa gabadaya kama yayi masa da mutanen Nijar yayi zaton aiko shi akayi saboda basu yarda da bayanin da yayi musu ba. Rufe ido yayi ya maimaita masa cewa Mairama ta haifi da ba rai, ita da 'yarta kuma sunyi hatsari sun mutu. Col. Nasiruddeen yaji babu dadi jikinsa yayi mugun sanyi ya koma Jos wurin iyalinsa cike da damuwa. Zayyan ya rasu a dalilin ceton ransa kuma iyalansa ma duka babu su. A satin yaje ya kai takardarsa ta barin aiki. A wurinsa rayuwar soja ba tasa bace. Asibiti ya koma neman aiki sai dai lokuta da dama idan ya ga yawaitar jini musamman idan hatsari ne jikinsa ya rinka rawa kenan. Likita da tsoron jini aiki bazai taba yiwuwa ba bisa dole ya hakura ya tsunduma cikin harkar siyasa ka'in da na'in. *********** SABON SHAFI [11/2, 6:51 AM] 🏽 🏽 : 33💕 . Asibitin Nasarawa aka tura su Awwab domin samun kwararren likitan ido. Da za'a basu daki yace dakin mutum daya yake bukata kada a hadata da kowa. Sunyi sa'a kuwa an samu. Dakin a gyare yake amma duk da haka ya dage sai an sake karkade shi an wanke toilet. Da ya ga matar zata yi masa gardama wai sai da safe zata sake zuwa ya bata dubu biyu. Kafin Mama ta iso da su Emzee da 'yan tarkacen bukata na kwana irinsu bargo da zanin gado an gyara dakin. Daure idanun Ummi aka yi da farin bandeji likitan yace bazai bude ba sai gobe a wurin gwajin ido. Budewar idanun lokaci daya da yawaitar haske ne ya janyo mata wannan ciwon kan saboda haka tana bukatar hutu. Da an sabunta mata glass din ido komai zai daidaita in sha Allahu. Emzee fa rai bai so ba. Abinda aka fi gani wurin Radhiya yau sai gashi yana yi. Zama yayi kusa da ita a kan gadon yana rokonta wai ko dan yaya ta janye daurin idon ta kalle shi. "Kayi hakuri mana Zayyanu gobe fa za'a bude mata." "Nene shikenan sai ta kwana ni bata ganni ba." Yau abin nasa harda turo baki musamman da Radhiya take masa gwalo. Ibrahim ya kalli yadda yake yi ya jinjina kai "yau kuma Zayyana ka koma? Ita ce bakinta kullum a tabe tsabar shagwaba" "Kai kuma sarkin sa ido ko" inji Mama ta kalli Emzee tana bashi hakuri. "Ka fita idona Surbajo" ya yi maganar yana nuna shi da dan yatsa. "Sunan nan ya fita a bakinka fa" "Kunga ku tashi mu tafi haka nan kafin ku cika mata kunne. Ummi bari mu gudu dare na kara yi" Kwanukan da suka bata na abinci Radhiya ta hada zata kai mota Mama tace tayi musu sai da safe don tare zasu wuce Nene kadai ce zata kwana. "Wayyo Mama nidai ki barni" "Shagwababbun da yawa ashe, ai kuwa sai mun tafi don bazan bari ki zauna ki dameta ba" Ibrahim da Emzee suka soma tsokanarta. A bangare daya kuma tasu rigimar su biyu bata kare ba. Mama dai kada su tayi duka suka fito wurin da ta ajiye motarta. Layin Awwab ta shiga nema don ya kusa awa daya baya dakin daga zuwa amsa waya. Ghazalatu ce take kiransa dama shiyasa ya fita daga dakin. Mota ya koma suna waya. Ta sanar dashi cewa tana tunanin Daddy Haroun yau ya yiwa Alh Baba zancensu don ta ga ya tambayeta da safe. Hira yake da ita babu wannan irin dokin da yake ji akan Radhiya da ya hadu da ita kwanaki kadan da suka wuce. Har ga Allah sai yake jin babu dadi saboda baya son zama maci amana kuma baya son wulakanta kanwarsa. Biye mata yayi suna hirar kawai don ya faranta mata. Wayar Mama da take ta shigo masa yace mata yana zuwa ya amsa kiran. "Awwab ina kayi parking ne? Ka taho mu tafi gida don nasan bazaka gane hanya ba. Nima ba don Ibrahim ba bata zanyi" "To Mama gani nan" Zagayawa yayi inda suke Ibrahim da Emzee suna rige rigen shiga tasa motar saboda rigimarsu ta dazu tace Radhiya taje ta shiga su bisu a baya. Ibrahim da Emzee su shiga tata. "Amma Mama ba mune maza ba sai mu bishi ki tafi da ita" cewar Ibrahim suna hada ido da Emzee suna dariyar shakiyanci. "Ita tasan hanyar ne? Ko mu biyu kuke son mu bata?" "Sai ku biyo mu a baya. Amma a haka kamar kinfi son ta bishi" Ganin idon Mama kadai ya hana Radhiya kaiwa Emzee duka. Kunya ce ta kama ta sosai. Allah Ya taimaketa Mama ta kama kunnuwansu shi da Ibrahim ta gwara musu kai sannan tace su wuce itama tana murmushi. Kwandon kayan abincin da ta dauko Awwab ya karba ya ajiye a baya sannan ya bude mata gaban. Ibrahim da Emzee kamar ba fada suke ba suka sake kwashewa da dariya harda tafawa. "Shakiyai Allah Ya shirya min ku" Mama tace kawai tana tada mota. Radhiya a kunyace ta shiga motar duk da cewa dazu tare suka zo a hakan daga Sumaila amma da Nene da Ummi. Yanzu kuwa su kadai duk bakin ma sai ya mutu. Bangaren window ta karkata gabadayanta tana kallon waje. Yatsantsa ya kada mata ta juyo amma taki kallonsa "tunanin me kike yi?" "Babu komai" "To in baki abin da zaki je kiyi tunani a kai?" Da ka ta amsa masa yace "baki da wani course da kike sha'awar karantawa?" "Duk ban sansu ba, soja kawai na sani" "Sojan ma ai yana karatu" "Training din kuma ayi yaushe? Na zata fada kawai ake koya musu da harbin bindiga" "Sai kace wasu 'yan ta'adda? Kinga kamar Daddy da yayi soja amma computer engineer ne." Dena kallon wajen tayi ta gyara zamanta yana mata bayani yadda zata gane. "Kin dami mutane da son zama soja bayan baki san komai akansu ba" Baiyi tsammani ba kawai yaji tace "Hamma ka zaba min wanda kake so in karanta" Kallonta da ya tsaya yi saura kiris motar Mama ta bace masa "kina son mass comm.?" "Na 'yan jarida?" "Yes" Zata bashi amsa wayarsa ta hau ruri. Da yake a kusa da giya ya ajiyeta idonta ya kai inda hasken yake ta ga ansa My G. Wani irin abu taji ya soki zuciyarta ta dauke kai da sauri ta koma kallon waje. Awwab sai yaji gabadaya hankalinsa ya tashi. Wai haka ake yi da mata biyu dama? Shi tun kafin yayi auren kowacce yana kokarin ya ga ya kawar da abinda zai tuna mata da 'yar uwarta saboda alamun kishi da yake ganin suna dashi su duka. Wannan shine dauko ruwan dafa kai. Bai taba tunanin hada girlfriends biyu ba ma a lokaci daya balle mata. Shi irin mutanen nan ne da rigima ta taho ta hagu sai yabi dama babu karkace hanya. Duk abinda zai tada masa da hankali gudunsa yake. Shi kadai yake kwankwasar kansa da cewa sai ya jajirce ne fa komai zai tafi daidai. Yadda Alheran tasan ba ita kadai bace yana komawa Katsina gobe Ghazalatu ma zata sani. Kai iyayensa ma zasu sani don ya fara ji a ransa wannan shekarar da ya diba ko kadan bazai iya jira ba. Zamanta yanzu cikin motar ba karamin jinsa yake a ransa ba. Kiran ya katse wani ya sake shigowa ya dauka yace mata tuki yake zai kira idan ya tsaya. Radhiya kuwa sai juya sunan take a ranta wai My G. Lokacin da ya gabatar mata da ita tun farko da haka ya ambaceta amma yanzu tafi jin abin a ranta. Har ya gama wayar bata kalle shi ba. Tunawa tayi da wayar da ya bata wadda bata samu nutsuwar dubawa ba ta dauko a hankali harda karewa da hijab don kada ya ga me take yi ta budo wurin sunaye. Suna daya tal ta gani a cikin contacts din. Hamma. To saura fatan akwai kudin kira. Satar kallonsa tayi idanunsa akan titi yana tunanin yadda zata kaya masa gobe a Katsina yaji waya ta sake kara. Ko kalla baiyi ba tunda yace zai kira yafi so ta kyale shi ya kira din. Kamar ba wadda ranta yake a bace ba Radhiya tace cikin karamar murya "Hamma ana maka waya" "Bari kawai zan kira idan na tsaya" So take ta ga da wane suna yayi saving number dinta. Ko bai ma saka sunan ba. Gashi ya tura wayar a aljihu. Da ta katse sai ta sake kira "Hamma ka dauka mana" "Yadda kika bata rai dazu idan na dauka kila kuka zaki yi min" yace daidai lokacin da Emzee yake bude gate Mama tana shigar da motarta Ibrahim kuma ya shige ciki ya fadawa kawunsa kanin Baba da ya zauna dashi sun dawo. Sake kiransa tayi na ukun ta turo baki "ni dai ka duba mana" Bai taba kawowa ita ke kiran ba ya dauko wayar da saurinta kuwa ta leka. Shi yana mamakin kiran me take yi masa ita kuma tsabagen bakinciki tana mamakin wannan wane irin suna ne ya lakaba mata. "Meye wannan Hamma? Nawa sunan kenan, meye sha...sha me ma?" Ta daga kai tana kara kallon rubutun wayar kuma ta katse bata gama hada harufan ta karanta ba. Idanunta taf da kwalla ta dagosu ta zuba masa "sake nuna min nawa sunan" tace kamar me bashi umarni. Ya kuwa danno sunan nata ya bata wayar. Kallon sunan ta sake yi ta ma kasa karantawa. Wata uwar harara ta doka masa ta kama kofar zata fita ya danna lock kafin ta bude. Dukan kofar ta shiga yi "ka bude min in fita, kuma na fasa soja zanyi, kuma likita zan aura" "Allah baki isa ba Awwab ne mijinki" "Ni na fasa ka bude min" sunan kawai take tunani ranta yana kara baci. Anya ma ba shashasha yake nufi ba. Kwafa tayi tana jinjina kai. "Calm down Schatzi, me ya faru?" Sai ga digon hawaye ya ziraro "nice shazi din? Ni ko? Ni ko?" Dariya ta bashi yadda ta kwabe fuska da gaske wai ranta ne ya baci. Gyara motar yayi a cikin gidan suna kallo kowa ya shige ciki ya sake tambayarta ta fada masa laifinsa. "To ba kaine..." "Me nayi ni Hamman Alheran sarkin laifi" Sai kuma taji nauyi amma dai dole ta fada ayita ta kare. Bazata yarda kawai don ita tana da hakuri ba a cewarta kuma yayi mata haka tun yanzu ba. "Ita da ta kiraka ba my G ka saka mata ba...." Ido ya lumshe yana dariyar kuruciyarta "shine kika kira ki ga me na saka miki?" "Eh, kuma kiran yayi min amfani gashi ni nawa sunan ko ma'ana babu. Mu sake gani ma don na kasa karantawa" "Schatzi" yace da wata irin siga da ta sauke mata tarkacen rigimar da ta debo ba shiri. Idanunta yake nema su hada da nasa taki dagawa "Schatzi yana nufin sweetie in german." Cusa kanta kawai tayi a tsakanin cinyoyinta saboda tsabar kunyar da ta dirar mata. Tana ji yana tambayarta "Idan kuma ba kya so sai na koma kiranki my A. Bari na chanja miki" ya fara danna wayar. "Don Allah ka bari" "Kina so?" Ta wani rufe fuska tana dariya ya kada kai ya bude motar suka fito tare. A daidai bakin kofa zasu shiga ciki yace "rigimammiyar Awwab". Da dan gudu ta shige ciki ta barshi a nan yana jin kamar an bashi dukkan farincikin duniya. ********** Washegari Awwab bai bar Kano ba sai da ya tabbatar an gama komai na gwajin da za'a yiwa Ummi. Ko kwandala basu biya ba shi yayi komai. Ummi da Nene sai addu'a kawai suke masa yayin da Radhiya take jin sonsa yana kara shigarta. Duk wanda zai mutunta maka iyaye hakika masoyi ne na kwarai. Ya fito daga dakin zasu raka shi bakin mota Emzee ya kawo mata wayar Ummi "Kawu Zakari ne yake son magana dake" Murmushi ta saki ta mika hannu zata karbi wayar "Allah Sarki Kawu Zakari kwana biyu" Yadda Awwab ya juyo da sauri Emzee sai da yaja baya ya fasa bata wayar. "Ba ka gaisa dashi ba?" "Eh mun gaisa" "To kace tana gaishe shi, ke kuma muje ki rakani" Sumsum ta wuce Emzee ya yi murmushi. Hamma yana burge shi kuma ya tabbatar da gaske yake son 'yar uwarsa shiyasa yake kara ganin girmansa. Mutum biyu ne damuwarsa a duniya, daga Ummi sai Adda Radhiya. Farincikinsa shine ya gansu cikin farinciki da kwanciyar hankali. A dole yayi masa karyar bata kusa. Yace to babu matsala gobe suna tafe duba Ummi dasu Innawuro. Saboda tsokana Emzee sai ya daga murya yadda zasu ji "Adda yace zaku hadu gobe zasu so duba Ummi" Tsayuwa Awwab yayi ya juya zai yanka masa magana tuni Emzee ya bace yana ta dariya. Hararar sai ta koma kan Radhiya ta dan ja da baya. "Ni kuma me nayi?" " 'Yar karamarki dake yarinyar nan kina da crush. Allah Yasa yazo kije kina masa murmushi zan sani ne" "Shi kuma meye crush din?" "Ko mutum baiyi niyya ba sai kin sashi dariya" yace yana murmushi. "Crush din wani ne?" "Yana nufin wani ya rinka burgeki kiji inama zai zama masoyinki" Sai da tayi dariya tace ko kishi yake yi ya amsa mata da cewa "sosai ma kuwa, Allah Schatzi kada na tafi ki fara kula likitocin asibitin nan. Gabana ya soma faduwa kada suyi min kwace" Wata dariyar take yana kallon fuskarta yana jindadi. Komai na Radhiya abin so ne a gareshi. Da kyar ya iya jan motar ya tafi tana ta daga masa hannu har ya fita daga harabar asibitin. Tunda ya hau hanya bai tsaya ko ina ba sai cikin gidansu. Wata irin gajiya yaji ta dirar masa ya samu yayi bacci bayan yayi wanka. ********** [11/2, 7:06 AM] 🏽 🏽 : 34💕 . Gagarumin taro aka hada na 'ya'yan marigariyi Alh Ghousman da jikokinsa manya. Hankulansu duka a tashe sai maganganu ake yi cikin harshen tamasheq. Alh Ghoumar da Alh Sidi sune manya a iyaye maza. Hamshakan 'yan kasuwa ne wadanda noma da kiwon da suka gada a wurin mahaifinsu ya zama tushen arzikinsu. Har ila yau a cikin taron akwai Ministan yada labarai Alh Issa Bouba miji ga Gwaggon Zayyan Aghaisha. Tana zaune a kusa da 'yan uwanta tana ta zubar da hawaye. "Abinda ban gane ba shine a wane dalili wannan yaro Maikudi zai ce mana sun rasu gabadaya?" Alh Sidi yayi maganar cikin kunar rai. Duk tsayin shekarun nan iyalin Zayyan suna raye babu wanda ya sani cikinsu. A tunaninsu tsatson Alheran 'yar uwarsu ya riga ya kare basu da wani ko wata da zasu kalla su dangantata dasu. "Ba wannan ba ma, ina suka zauna? Me yasa matarsa bata neme mu ba?" Cikin kuka Gwaggo Aghaisha wadda suke kira Mamme tace da Alh Ghoumar "ka manta yanzu fa mutumin nan da yace tare suke da Zayyan a filin yaki yace har makancewa tayi. Kuma yaushe zaka ga laifinta ma. Mune muka san inda take ita bata taba zuwa Agadez ba." "Haka ne kuma" yace jiki a sanyaye. "Duk shekarun nan kila ta yisu ne cikin jin haushinmu. Tana ganin kamar mun rabu da ita saboda babu idon mijinta a duniya" Mamme ta sake fashewa da kuka. Ko cikakken rabin awa basuyi ba da yin waya da Major Mustapha wanda yayi musu bayanin da zai yiwu ta waya. Bayan ya tura a binciko masa inda suke da takaitaccen bayanin cewa Mairama da 'ya'yanta suna da rai shine suka hadu cikin tashin hankali da mamakin wannan labari suka kira nambar da ya bayar. Sun dade suna waya inda ya fada musu abubuwan da suka sami wannan iyali. Basu da dalilin karyata shi tunda harda hoto ya tura musu domin shaida a lokacin da yace a nemo su. Sai da hankula suka dan natsa sannan Alh Sidi yace "ina ganin ya kamata mu shirya muje mu gansu. Yaran mu kawosu su ga 'yan uwa don kada irin haka ta sake faruwa" Kowa yayi na'am da wannan shawara. To sai kuma batun su waye zasu je. Babu wanda yake so a barshi a baya. Jirgi suka fara tunanin bi daga baya aka soke saboda zasu bukaci motocin hawa idan sun je. "Babu wani abin damuwa tunda zamu daukosu. A sanar da sauran dangi idan yayi muku nan da kwanaki kadan sai mu shirya duk abinda ya kamata mu tafi" Sati dayan ma suna ganin tsayinsa to amma tafiyar basu dauketa ta garaje ba. Danginsu, jininsu da kaddara ta rabasu. Ya zama wajibi a garesu su yiwa wannan tafiya shiri na musamman. ********** Bayan sallar magariba Awwab sunyi da Ghazalatu zai je wurinta. Yana shiryawa suna waya da Radhiya tana masa shagwaba yana biye mata. Kwankwasa masa kofa akayi tare da sallama yana makale da wayar a kafada ya budewa Fauziyya kofar. "Daddy yana kiranka" Da ka ya amsa ya koma ya gama fesa turare sannan ya yiwa Radhiya sallama da sakon gaisuwa ga Umminsa. A dakin Daddy din ya samesu tare da Mami. Yana shiga Daddy yace mata tayi hakuri ta basu wuri. "Ba sai kun koreni ba na dade da sanin kuna wareni. To dadin abin ina da 'yan mata na" "Zahra da Fauziyya ko? Kinsan dai ko da kudi bazaki saye min Zayyanatu ba" Daddy yace da murmushin dole saboda kwata kwata baya cikin nutsuwarsa tun jiya. Mami ta kula kuma ta tambayeshi sau daya yace babu komai sai taja bakinta tayi shiru. Ita ma din tana da danuwar da take dannewa bata so ta fada masa game da Zahra. Murmushin ta mayar masa "ka manta jiya baka bata kudin kanwar amarya day ba mun ganku a rana? Yanzu zanje na sayeta" Bayan fitarta Daddy ya maida kallonsa ga Awwab da yake zaune a kasa daga gefen wata duguwar kujera. "MUHAMMAD" Dago kai yayi da sauri saboda yadda kiran ya ratsa ko ina a jikinsa. Baya tunanin idan ba a makaranta ba ko za'a fadawa wani sunansa Daddy yana kiransa da Muhammad balle da irin wannan yanayi da yake nuni da babu wasa cikin maganar da zasu yi. "Na'am Daddy" "Meye tsakaninka da kanwarka Ghazalatu?" Dama yayi tunanin wannan maganar ce tunda Ghazalatu tace tana tunanin Daddy Haroun ya sani ko ma yayi zancen da Alh Baba. "Daddy maganar aure ce" "Awwab meyasa baka sanar dani ko mahaifiyarka ba?" Sunkuyar da kansa yayi yana mai takaicin biye mata da yayi tun a lokacin suka boye. Da an sani a gida zasu iya rokar alfarmar ta gama karatun kafin ayi aure tunda shine babbar damuwarta. Haka nan dai ya sanar da Daddy dalilin boyewar tasu. "Rashin sanin kana nemanta ya sanya nayi maka karambani. Zuwanmu Rugar Barkindo na yiwa kakannin Radhiya alkawarin za ka aureta saboda sharadin da suka gindaya min kenan na bani ita na dawo da ita cikinku tayi karatu." Murmushi sosai ya ga Awwab yayi ya sake dukar da kai. Wannan ya tabbatar masa da zancen Mami da tace tana ganin kamar yana sonta. "Daddy nagode kuma na karba" "Yaya zaka yi da kanwarka kuma?" Babu kwauron baki ya fadawa mahaifinsa cewa dama ya dawo ne domin neman shawararsa akan yadda ya kamata ya bullowa lamarin. "Bazan wulakanta Ghazalatu saboda Alheran ba, itama kuma ko ba ni na nemeta da kaina ba Daddy bazan bari kaji kunyar iyayenta ba" Hakika tunani da hangen nesa irin na Awwab suna daga cikin dalilin da suka sa Major yake matukar son yaron. Sai aka samu kyakkyawar shakuwa a tsakaninsu wadda tasa suke shawartar juna akan abubuwa daban daban. Yaji dadin amsar dan nasa sosai amma kuma ba abinda nasa iyayen suke so ba ne. "Ina zaka kai mata biyu a lokaci guda?" Cikin yanayi na damuwa yace "Daddy nima ban sani ba amma don Allah kada kace na hakura da kowacce bazan iya ba. Dukkansu ni na kai kaina garesu kuma suka amince min" "Muhammad kayi hakuri da Radhiya, su Alh Baba sun ce na bawa iyayenta hakuri Ghazalatu kadai zaka aura" A firgici ya dago kai yana mikewa tsaye baki daya "Daddy?" "Bana son jan zancen nan har Maminku taji. Alhaji yace a bari su gama biki to zan jira a gama din naji hukuncin da zasu yanke. Na sanar da kai ne saboda idan da gaske ka fara neman Radhiya ka janye. Bana son ka cigaba da sa mata rai har sai na gama iya kokarina akan neman amincewarsu ka hada biyun" Gumi ne sosai ya soma wankewa Awwab fuska. Idan zai iya hakura da Alheran dinsa tabbas zai iya hakura da aure baki daya. Gurfana yayi a gaban Major kamar mai rokon gafara. "Don Allah Daddy kasa baki wallahi zan iya aurensu su duka." "Tashi kaje dama yace yana nemanka idan ka dawo. Ka yawaita addu'ar zabin Allah" Jikinsa sam babu kwari haka ya fita kamar mara lafiya. Mami tana kallon fitarsa Zahra na yi masa magana bai ma san tana yi ba. Jikinta itama sai yayi sanyi. Tabbas akwai abinda yake faruwa wanda Daddy baya son ta sani. To ko ya gane abinda take boyewa na Zahra ne? Kai da wahala tace a ranta tana girgiza kai. Zahra bazata taba fada ba ta sani. Kallon yarinyar tayi a zaune bayan fitar Awwab bai kulata ba tayi shiru. Zuciyarta ce tayi mata nauyi ta rasa da wa zata yi maganar nan ta saukewa kanta nauyi. Fitarta kuma ba karamar illa zai iya janyowa zumunci ba. Shirun dai da ta yi kuma ta roki Zahra da tayi itama shine take ganin kamar zai zame musu maslaha. Kafin ya isa gidan Alh Baba missed calls din Ghazalatu sun kai goma. Kiransa take tun yana wurin Daddy tana masa tuni akan shiru da ta ji. Ransa gabadaya a cunkushe ya shiga ya gaishe da Mummy kafin ya fito da niyar gaisawa da kakaninsu mata. "Yayana ka bari sai zaka tafi kaje. Yanzu cinye mana lokacin hira zasuyi" "Kinfi so dare yayi sosai lokacin na shiga sunyi bacci? Ba dadewa zanyi ba" "Daddy yace in fada maka kaje wurin Alh Baba shima yana son ganinka. Ni duk za'a cinye min lokacina" Murmushi yayi duk don ya nuna mata komai lafiya "My G baki da dama, yanzu su Alhajin ne masu cinye miki lokaci?" Tana ta tura baki suka shiga wajen matan Alhajin daga nan ta bishi falonsa. Sun gaisa yayi masa barka da dawowa shi kuma Alhajin ya bashi karamar robar zamzam da dabino ya karba da godiya. Ganinsu da yayi da jikar tasa ya faranta masa rai sosai. A son ransa zuri'arsu suyi ta auren junansu yadda za'a sami hadin kai mai dorewa har jikoki. "Dan bamu wuri zanyi magana da yayanki Ghazalatu" Shikenan za'a sake ci mata lokaci ta ayyana a ranta. Zaman da tayi don ta sami damar fita dashi ne kada Alh Baba ya dauko doguwar hira a tsakaninsu. Iyakarta bakin kofa ta makale daga gefe da zummar idan taji hirar zata yi tsayi ta koma tace ana kiransa. Abinda taji Alh Baba yana cewa ne yasa ta sake matsowa sosai don taji da kyau. "Munyi magana da iyayenku jiya. Naji dadi kwarai da kuka hada kai da kanwarka. Kuma na yanke cewa ayi auren nan da wata uku. Ina fata zaka iya shiryawa kafin nan." Wani tsalle Ghazalatu ta daka daga inda take. Awwab godiya yayi masa sosai yana murmushi. "Sai dai Mustapha ya kawo wani hanzari na cewa ya nema maka auren yarinyar abokinsa batare da sanin kana neman Ghazalatu ba" Gabanta taji ya fadi don ta sani babu wadda ake nufi ko da ba'a ambaci suna ba sai Radhiya yarinyar nan mai kwalkwalin kai. Kansa a kasa cike da ladabi Awwab yace "hakane Alhaji" Tsohon ya gyara zamansa yana kallon jikan nasa "tun a jiyan na fada masa sai a basu hakuri tunda kana da wadda kake so bai kyautu ace sai ka aureta ba. Ni a tsarina ma Allah Ya gani nafi son ku rinka auren junanku. Ita idan aurenta ya tashi sai yayi mata duk abinda uba yake yiwa 'yarsa" Wannan shine son kai. Babu yadda za'ayi Awwab yayi shiru da wannan magana ya karbi hukuncin Alh Baba batare da ya gabatar masa da nasa uzurin ba. "Alhaji kayi min izini na auresu su biyu. Ina iya fara auren Ghazalatu sai na aureta daga baya" Rai a bace ya soma fada "abinda uban naka ya turoka ka fada min kenan. Wato saboda jiya nace ban yarda ba shine kai ka shafawa idonka toka zaka yi min rashin kunya?" "Alhaji kayi hakuri ba haka bane" "To nace na soke bazaka aureta ba. Banda son dorawa kai wahala ina zaka kai mata biyu Muhammad? Idan kana son yiwa mahaifinka biyayya ne kaje abinka shima ai karkashina yake" Ran Awwab sai kuna yake ya kasa daurewa "Alhaji wallahi ina sonta" Kallon da Alh Baba ya watsa masa a lokacin kallo ne na tsananin bacin rai. Ghazalatu da ta gama jin komai hankalinta bai tashi sosai ba sai da taji furucin Awwab. Kuka ta fashe dashi ga bakinciki ga kishi ta bar wurin a guje. Daga Alhajin har Awwab sun jiyo muryarta. "Ka tashi kabi sawun kanwarka ku daidaita. Na gama magana Muhammad bana son sake jin wata magana" "Alhaji...." "Ka tashi ka tafi nace" Yana fita daga falon waje ya nufa ya shiga mota ya kifa kai akan sitiyari. "Ya Allah" ya furta a hankali ko ina na jikinsa yana cikin tashin hankali. Bazai taba iya hakura ko rabuwa da Alheran ba. Ya barta a kira shi da me? Butulu ko mayaudari? A cikin abinda bai gaza sati biyu ba ya fada matsananciyar soyayyarta kuma itama ya koya mata sonsa. Akwai kunya da nauyi sosai tsakanin iyayensu wanda bai cancanci a sanadiyarsa ya kawo wata baraka a tsakani ba kamar yadda baya fatan kawo baraka ga danginsa. Shi da Ghazalatu sunyi dumu dumu a cikin dangi. Idan baka dubesu ta nan ba zaka dubesu ta can. Hadi ne tun daga kakanni an cakude da juna. Dakin mahaifiyarta Mummy Gambo ta wuce kai tsaye tana kuka kamar ranta zai fita. Babu abinda yake mata yawo a ka sai jin da tayi Awwab da bakinsa yace yana son wannan yarinyar. Mummy ta taso ta tarbeta da sauri "me ya sameki?" "Mummy Yaya ne...Yaya Awwab baya sona" "Ban gane ba, idan wani shirmen fadanku ne dama kada ki soma gaya min. Kije can ku sasanta" "Mummy wata yake so. Yaci amanata wallahi 'yar wannan makauniyar da ta zauna gidansu yake so" Nata hankalin sai yafi na Ghazalatu tashi "dena kuka bari na kira Hassana naji daga bakinta." Mami tana daki da Zahra wadda take ta kuka tana bata hakuri Mummy ta kira. Shawara ta yanke gara ta sanar da ita ko Hussaina su tayata bawa Zahra baki. Sai da ta saita muryarta don ita din ma zuciyarta a karye take "Mummyn yara yanzu kuwa nake shirin nemanki." "Kina shirin nemana ki fada min kun yiwa Awwab mata ko" tace cikin gatse. Mami da bata san wainar da ake toyawa ba tayi dariya "hala yazo ya fada miki. 'Yar wajen Mairama ce. Kin ganeta ai wadda tazo ta kwana mana biyu matar ....." Kit taji shiru Mummy ta kashe wayar. Kallon wayar hannunta tayi da mamaki sai kuma ta soma kiranta missed calls biyar bata dauka. Abin ya dameta ta lallaba Zahra ta fita ta tafi dakin Daddy. Mummy Gambo ta cika tayi fam. Ita Mami zata wulakantawa 'ya har tana fada mata wadda suka zabawa Awwab. Kenan basu aminta da ya auri Ghazalatu ba. A tunaninta tafi karfin haka a wurin 'yar uwarta ta. Kallon Ghazakatu tayi da take ta kuka tana rarrashinta ta kira Daddy Haroun a waya don ya fita unguwa. Cewa tayi kawai ya dawo gida babu lafiya yace to. Mami tana zuwa dakin Daddy shi kuma ta same shi yana waya da Alh Baba yana ta ban hakuri. Alh Baba yace ya fadawa Awwab lallai aurensa da Ghazalatu babu fashi. Wurgi ta ga yayi da wayarsa ta karaso kusa dashi da sauri. "Daddy lafiya?" "Ki bari muyi maganar nan bayan bikin su Fauziyya kamar yadda Alh Baba yace" "Wallahi hankalina ya tashi. Tun jiya ka chanja min gabaki daya. Yanzu Gambo ta kirani tana cewa munyiwa Awwab mata nace mata eh kawai ta kashe wayar kamar wadda na yiwa wani abu" Ran Major tuni ya soma baci kuwa. Yasan Gambo da masifa amma baya son duk abinda zai sosa ran Mami. Ga dadin haushin akan 'yarta ne ake son kirikiri a gwada son kai. Meye matsalar ya auri mata biyu da za'a ce dole sai an janye maganar Radhiya. Radhiya diyar Zayyanunsa. Sallamar Awwab din suka rinka ji kana jinsa kasan baya cikin nutsuwa. Izinin shigowa Daddy yayi masa yana zuwa ya zube masa. "Daddy Alh Baba yace bazan auri Alheran ba. To wallahi idan bai amince ba itama Ghazalatun na rantse da Allah ko an daura sai na saketa" "Kai Awwab, kana cikin hankalinka kuwa? Daddy me yake faruwa ne kun kara sakani cikin duhu" "Fita ka tafi dakinka" Daddy yace ransa shima a baci. Dakin gabadaya ya juye walwalar ma'abotansa ta fi kamar an kadata da iska. Tattaro nutsuwarsa ya daure yayi ya fadawa Mami halin da ake ciki. Boyewar bata da amfani tunda Gambo ta sani. "Innalillahi wa inna ilaihi rajiun. Yanzu sai Gambo ta ga kamar da gangan nayi" "Gambo kike ji ko kuwa halin da Awwab zai shiga da yaran nan" "Daddy ni fa ban ga wata gagarumar matsala a cikin wannan abu ba. Awwab namiji ne saboda haka zai iya aurensu duka. Ciki mu mun isa muce ga wadda zai zaba ya bar dayar? Babu wadda mahaifinta baiyi mana halacci ba saboda haka ka kwantar da hankalinka in sha Allahu komai zai zo da sauki" A sanyaye yace "Alh Baba yace bazai auri mata biyu ba kuma su Baba sun amince" Kanta ta dora akan kafadarsa ta kwantar da murya domin kwantar masa da hankali "mu bi komai a sannu saboda kuskure daya zai iya janyo mana rikici a dangi ko tare da iyayen Mairama wanda bana fata. Gobe muje mu roki arzikin suyi hakuri su amince ya auresu su biyun" Kalamai masu kwantar da hankali ta rinka amfani dasu wurin sanyayawa mijinta rai suka dauki dogon lokaci suna shawara akan wannan matsala. Tunda Awwab ya shiga daki bai fito ba sai asuba. Kallo daya Major yayi masa ya san cewa da wahala idan ya runtsa. Soyayyar Awwab da Alheran daga Allah ce. Ya tabbatar duk wannan tashin hankalin saboda an hanashi aurenta ne. ********** Da wuri aka gama komai na sallamar Ummi daga asibiti. Abin da mamaki matuka ta shafe shekaru kusan goma da makanta yau ita ce take da idanun kallon Radhiya da Karami. Bayan an bata gilashinta tana kallonsu ta fashe da kuka. Karami bai baro mahaifinsa da komai ba sai fari da ya dan dara shi wanda ta alakanta shi da kuruciyarsa sai kuma tsaho da shi Zayyan din yafi dan nasa. Radhiya kuwa tafi dauko kamanni da ita sai dai ta rasa inda ta samo wannan kirar jiki. Mairama doguwa ce siririya mai kyaun sura da daukar ido yayin da Radhiya take a murje babu rama amma baza'a a kirata mai kiba ba. Jikinta a cike yake ko ta ina. Yanayin hancinta sam baiyi kama da na Umminta ko mahaifinta ba. Idan tayi murmushi sai kaji kamar ka dauketa saboda yadda fuskar take nuna zallan yarinta idan kumatunta ya lotsa ciki. Lokacin da suka hada ido da Zainab sai sabon kuka. "Haka kika koma wata 'yar gayu Zainab dina" Yaran suna dariya iyayensu suka rungume juna. "Muje gida kafin ki bar garin nan sai kin zama 'yar gayu kema. Ba biki zakuyi ba....hmmm Allah Mairama sai nasa idanu sun koma kanki a wurin bikin nan" suka yi dariya. A gaban mota Ummi ta zauna Radhiya da Nene Marka suna baya. 'Yan samari kuwa adaidaita sahu tace su shiga su biyo bayansu. Sunje gida Ummi ido ya bude ta ga halin da Baba Hadir yake ciki. Tana kuka Zainab tace mata kada ta jangwalo idanun tayi hakuri haka. Motsi kadan Radhiya sai ta kalli wayarta babu kiran Awwab. Yadda baiyi bacci ba jiya yau ma hankalinsa gabadaya ya tashi ne saboda rigimar dake neman kunno kai a gidansu. Mami da Daddy sunje har gidan Alh Baba akan ya duba lamarin wanda zuwan nasu ya sake harzuka shi. Mummy da ta sami labari ko kallon arziki ta kasa yiwa yayarta. Ga Ghazalatu ta kwana kuka kuma tsabar wulakanci ko aurenta ba'ayi ba ace suna rokon a auro harda wata. Domin su tsayar da abin haka suka yanke shawarar bari a fara bikin da Ghazalatu. Idan yaso bayan ko da rabin shekara ne Daddy zai sake yiwa su Alh Baba maganar. Kwanaki biyu suka yi ana wannan tashin tashina. A Kano kuma Mama ta bude wuta wurin gyara 'yar uwarta Ummi da 'yarta Radhiya. Salon ta kai Mairama da aka gama gyara kan akayi steaming sai ta sake komawa yarinya kyaunta ya kuma bayyana. Radhiya ganin Umminta a steamer harda kuka wai ita ya kamata a yiwa wannan gyaran amma saboda Innawuro bata sonta gashi yanzu tana ji tana gani babu damar shiga. Mai salon taji sai mita take tana fulatanci tana hausa ana ta kiran Innuwuro tace mata tazo ta shiga. "Soya min fatar kai zaki yi ko" Matar tayi dariya "gyara dai kanwata" Bisa tsautsayi ta tuge dankwalin Radhiya wai zata yi mata gyara kyauta sai abin arziki ya bayyana kowa ya gani. Allah Yasa kan ya hade yayi baki sidik gashi ya soma tofowa. Amma duk da haka ranta ya baci ta tashi ta hade fuska tana kallon matan da ake yiwa gyara. "Yasin mace tayi dariya in rangada mata balotelli ta tafi dashi gida" Kana ganinta kasan ko bata aikata ba to dai zasu ji ba dadi. Mai salon ta koma bata hakuri sannan tace tazo tayi mata gyaran farcen hannu da kafa da steaming din fuska. Shikenan ta manta da fushin ta shiga jerin gyara tana ta firirita yau gata a salon. Kafin su bar wurin tasa mata da yawa dariya. Washegari ana gobe zasu tafi mai kunshi tazo ta rangada musu baki da ja. Ummi dai safa ta saka a kafarta tana jin wani iri. Rabonta da ado haka tun Zayyan bai tafi Liberia ba. Yanzu kam wa zata yiwa. Nene kuwa sai zuga Mama take yi wai a gyare mata 'yarta ta samo miji dan ubansu. Radhiya da Emzee suka taru suka rafka mata uwar harara sai da Mama ta hade kawunansu ta gwara. "Nenenmu kuke harara" "Mama wai miji fa take cewa, Ummi ke da aure sai a aljanna ke da babanmu" Emzee yace da dukkan seriousness. "Maza iyayen kishi" Mama tace tana tuna lokutan da Ibrahim yake yi mata kunkuni akan me yasa ta tafi tabar babansa. Ranar wuni suka yi ana ta gyare gyare saboda tafiyar su Mama da ta matso kusa sosai. Ibrahim zai koma gidan kakaninsa ya jira dawowarsu. Da safe ta kaisu tasha. Nene tayi ta yi musu addu'a ita da iyalinta tana fatan Allah Yasa a dace mijinta ya sami lafiya ya dawo da kafafunsa. Kamar kar su rabu ita da Ummi. Emzee ma dai dokin budewar idanun Ummi yasa zai bisu Sumaila. Ba don haka ba jira zaiyi sai sun tashi nan da kwana biyu sannan ya koma. Sai da suka tashi Mama ta koma gida tare da Ibrahim mai nuna hanya. Suna isa Aisha 'yar wajen Alh Musa ta kirata. Sun gaisa da ita da kanwarta tace mata ga Mamansu su gaisa. Matar mai mutumci suka gaisa da tambayar juna iyali. "Antin yara na bugo ne nayi miki godiya irin dawainiyar da kika sha da yaran nan. Na dawo gidansu biki ya matso babu abinda baki saya kin ajiye ba. Don Allah ina rokon mu cigaba da zumunci." "In sha Allahu. Nagode" "Ina fata kuma zaki zo bikin 'ya'yan naki" "Ahhh banyi alkawari ba." Nunawa tayi bata ji dadi ba har tana tambayarta ko don sun rabu da Alh Musa ne. Mama tayi dariya tace mata tafiya ce a gabanta zata kai mijinta asibiti. Maman su Aisha ta tausaya mata ta kuma jinjina mata wannan sadaukarwa da ta hanata zama gidan mutum kamar Alh Musa mai kudi da halin dattako. Bata yi kasa a gwiwa ba bayan ya dawo daga wurin aiki ta fada masa. Abin yafi taba shi duk da yasan ta koma gidan tsohon mijinta amma sai da yaji wani iri. Soyayyarta da tausayinta duka a hade. Nasa salon kaunar shine ya tura mata miliyan biyu da rabi a matsayin gudunmawa. Mama tayi kuka a ranar yadda Allah ke budawa bawanSa a lokacin da bai taba tsammani ba. Aurenta da Alh Musa ta yarda silar arzikinta ne da nemawa Hadir waraka. A Sumaila kuma su Ummi sun isa gida ya fara cika da 'yan biki. Yawanci 'yan uwansu ne na bangaren Malamijo. Washegari kuma sai ga dangin iyayen amaren mata su ma sun fara zuwa. Innawuro da matan su Baffa Gide duka sun iso. Ranar ne za'ayi Kamu amare kowacce dangin uwa na kokarin rufa mata asiri. Shi dai Malamijo tunda ya bada abinda zai iya ya janye hannuwansa. Duk wannan abu da akeyi Salame bata samu zuwa ba saboda bata ma da kayan sawa ta shiga taro ga yunwa kamar taci babu ita da 'ya'yanta. Ranar da yamma Nene ta rufa mayafi ta tafi gidan Salamen. A gaban murhu ta sameta tana ta uban kauri. Tsaki ta samu zata yi musu danmalele ita da yaranta suci. Girman kai ya hana ta kwantar da kanta gaban mahaifinta komai lalacewarsa ta nemi taimako. Taji labarin Mairama tana gidan amma bata gabanta tunda tasan ba ido gareta ba bata da abinda zata tsinanawa kanta ma. Kauyen da akace ta koma na dangin babarta ta tabbatar kila wahala kawai take sha daga ita har yaran. 'Yan lokutan da suke zuwa Sumaila lokacin tana shanawa a jikin Indararo bata ma zuwa gidan don kada a fara yi mata bani bani. Sai gashi a kasa da shekara guda duniya tayi mata juyin waina...sama ya koma kasa. Idanu jazur ta dago tana fyace majina da gefen mataccen zaninta sannan ta kakalo murmushin dole. "Nene kece a gidan namu yau?" Rai a bace Nene Marka tace "nice Salame, cewa nayi bari nazo na gaishe da hamshakiya matar Alhaji tunda kinfi karfin kowa." Kamar wata gaula tana fama da cikin da yake neman rinjayarta tace "to ni me nayi" "Ban sani ba Salame. Mahaifinki ya kwanta ciwo yaci ya cinye har ya warke babu ke babu inuwarki balle asa rai da mijinki ma zai je. An kai lefen kanenki baki je ba yanzu don tsabar bakin hali ana biki a matsayinki na babbar 'ya a gidan kin gagara zuwa kuna gari daya. Anya Salame kin dauko hanya mai bullewa kuwa?" Da kunya taje gidan nan bayan kowa ya santa a lokacin da take tsaka da jindadi dama kiris 'yan bakinciki suke jira ayi mata dariya. Jiya Ta Madina tazo har gidan itama ta kare mata tanadi wai kanwarta ta haihu bata je ba. Yaran da suka gama rainata suke murna da talaucinta. "Kin dai ga yanayin da nake ciki dama shi kuke buri shiyasa babu wanda ya damu dani" "Kaniyarki, idan zakiyi fitsararki kada kiyi min bazan miki da dadi ba. Idan ban ganki a wurin bikin nan gobe ba wallahi sai na saba miki. Mutuniyar banza wadda bata sawa zuciyarta komai ba sai kyashi da hassada. Malamijo ya cuceku wallahi" Bayan fitarta Salame kuka ta saka. Tana ji tana gani ta zama bolar gida kuma miji yaki ya saketa ko tasan matsayinta. Tana cikin wannan halin ne kamar daga sama Halifa yazo. Matashin saurayi dan gatan Alh Salisu. Yaron babu abinda ya nema ya rasa a wurin mahaifinsa sai dai abu guda. Da matukar wahala babansa yake bashi kudi idan zai zo Sumaila. Da can yana bashi sai ya zamana Salame tana karanta masa bukatunta idan zai sake zuwa. A hankali Alh Salisu ya fahimci cewa kudaden da yake bawa dan nasa aikinta ne ko kunya babu. A yadda yayi matukar tsanar halinta tuni ya dakile hakan. Taje can ta karata idan Halifa ya soma sana'a yayi mata da nasa gumin. Tsabar murna ji tayi kamar an ga watan sallah. Ta rasa inda zata saka kanta don dadi harda yada habaici wa Maman Danmama danta yazo. Shi dai kunyar irin wannan abubuwan nata yake yi to amma uwa uwace. Bai wani dade ba da zai tafi ya bata dubu biyar cikin abinda ya rage masa. Salame duniya tayi dadi ta rasa ina zata kai farinciki. Dreba ne ya kawo shi kuma yana jiransa ya tafi dashi. Dan cikinta a wannan hadaddiyar mota harda dreba. Kai inama dai ta kwantar da hankali a gidan Alh Salisu. Washegari bayan sunci fara da mai harda hadin salak da kifi sukunbiya ta shirya 'ya'yanta kowa cikin kayan sallarsa na bara kafin Alh Indararo ya banzatar dasu. Itama wani leshi ta saka cikin irin alkhairin da ta samu albarkacin aikin malamin tsibbunta wanda ya fita yayi yanzu. Mayafin ma irin mai bakin leshi da ta dade da dena sakawa ta dauko don na yayin duk sun mutu babu na mora. Tana tsakiyar yaranta dayake tafiyar kafa ce zata kaita gidan tana murmushin jindadi. Yau 'yan bakinciki sai dai su mutu. Tana nan kuma har yanzu tana damawa don tasan da wuya a sami mai dressing irin nata. Ta kusa gidan bai fi taku kadan ya rage ba ta ji dirin motoci a bayanta sun taho a guje. Kana ganinsu kasan tafiya ce ta jerentawa wato convey. Motoci ne da suka amsa sunansu mota masu masifar kyau da daukar ido duka a maimakon nambar mota an rubuta G. AGALI wato Ghousman Agali kakan Zayyan Muhammad Tureta na wurin uwa. Guda takwas ne sai kuma helux guda biyu da aka ciko su shakare da buhun hunan kayan abinci da lemuka na kwali da na roba. Mota cikon ta tara da ta fita daban da sauran duk da cewa itama tana da kyau sosai Awwab ne a ciki. Shine yayi musu rakiya zuwa garin Sumaila domin cika umarnin mahaifinsa da hada masoyiyarsa da dangin mahaifinta. Daga ita har Ummin an kasa samunsu a waya bare a sanar dasu zuwan bakin. Sanye yake da wando chinos mai kyau coffee da shirt cream wadda ta dan kama shi. Idanunsa ya karesu da bakin glass wanda ya kara haska fuskarsa ya kuma boye bacin ran da yake kwana yake tashi dashi tun komawarsa Katsina. Umarnin Daddy yake son bi na kauracewa Radhiya har zuwa ayi bikin gidansu sati mai zuwa a gama sannan su sake tayar da maganarta. Yana ganin wayarta da text wanda bayan kwana biyu babu reply ta dena yi. A tunaninta ya koma ga Ghazalatu ne ya manta da ita shine take kishi tayi fushi ta share shi. Matsananciyar kewarta ce ta sanya shi cewa zaiyi musu rakiya batare da an nema ba. Daddy yasan dalilinsa kuma yana tausaya masa. Lokaci guda har ya soma rama ga maganganu sunki ci sunki cinyewa a dangi. Salame dai sakin baki tayi tana mamakin wadannan kyawawan mutane mazansu da matansu da suke fitowa daga motocin alfarma irin wadannan wurin wa suka zo? Ko sunyi batan kai ne? Kila bakin Chairman ne ko gidan Hakimi. *********** Su Alh Ghoumar tun kafin su iso cikin garin Katsina suka sanar da Major suna tafe. Da suka zo gabadayansu sun kwana a wani hotel ne da safe shi da Alh Sidi da mutum biyu cikin 'ya'yansu suka je gidan Rtd Major Mustapha. Yayi farinciki da zuwansu ya sake basu labarin duk yadda ta kasancewa Mairama da su Radhiya. Guda cikin wadanda aka je dasu wanda shine auta a 'ya'yan Alh Sidi mai suna Ridwan yace zai maka Maikudi a kotu domin ya ha'incesu ya fada musu karya game da iyalin dan uwansu. Major baiyi yunkurin bada hakuri ba yace idan sun dawo daga ganinsu din sai su je Sakkwaton. "Amma meyasa baku ce a kawo muku su ba kuka taho gabadayanku?" Ya tambayesu da murmyshi a fuskarsa. "Domin mu nunawa duniya cewa Mairama, Alheran da Zayyan dangin mahafinsu suna kaunarsu. Waye zamu samu ya rakamu saboda drebobin namu biyu ne kawai 'yan kasar nan" Awwab kamar jira yake dama yazo gaishesu ne da Mami tace sun iso shine yace zaije. Daddy bashi da niyar hana shi saboda tausayinsa yake ji yana mamakin irin wannan soyayya mai karfi da ta shigi dan nasa farat daya. Fitarsu daga gidan ko awa daya ba'ayi ba Mummy Gambo da Hussainar Mami suka zo. Ba da mutumci suka zo ba su Fauziyya na gaishe su babu wadda ta amsa. "Ina babar taku?" Hussaina ta tambaya a dakile. "Hussaina kenan, gani...kai ku bamu wuri" tace dasu Zayyana, suka tashi kuwa suka yi daki da sauri. Zama tayi domin su gaisa Mummy ta soma fadan da ya kawota. "Saboda wata yarinya can bare da babu wata alaka tsakaninku Hassana kike neman bata mana zumunci? Awwab da bakinsa yace yana son auren Ghazalatu amma tashi daya zance ya sauya saboda kuna son ku burge wasu" "To banda ma abinta akwai wani abu da ita yarinyar tafi Ghazalatu ne? Alh Baba da su Babanmu sunce basu yarda ba ba sai ku hakura ba. Amma ace da kanki kuka je har gabansa don ya amince a bar danki shafaffe da mai ya yi auren gata mata biyu lokaci guda" Daurewa take yi suna ta caba mata maganganu a ganinsu ita ma bata son 'yan uwanta su rabeta ne. "Banda naci irin na Ghazalatu nace mata ta hakura da yaron nan taki. Wallahi ba don tana son shi ba har yanzu bazaki sake ganina a gidan nan ba. Nayi zuwan karshe ne inji menene ya sanya baki son auren nan?" "Gambo idan Hussaina bata fahimta ba ta biye miki kun hade min kai nayi zaton ke zaki fahimta tunda mun zauna tare kin kuma san komai game da iyalin Zayyan. Wallahi da munsan da batun Ghazalatu Daddy bazai taba zancen wannan hadi ba. Ku duba irin kunyar dake tattare da ya koma yace musu an fasa auren nan" "Ke kuma gara a kuntatawa 'yar kanwarki da yaji kunyar cewa 'yan kauye an fasa auren 'yarsu. Na tabbata 'yar dubu hamsin aka mika musu magana ta mutu har abada" cewar Hussaina. "Ki barta tunda Umma tace mu kyalesu mu zuba musu ido daga ita har yaya Mustapha din. Saboda rashin sanin darajar zumunci kun shirya batawa da kowa..." "Ke har zaki fada min zumunci Gambo" Mami tace rai a bace su Fauziyya suna jiyota daga daki kamar yadda Daddy yake jiyota daga falonsa da bai taso ba bayan tafiyar su Awwab. "Kinsan me na rasa saboda zumunci? Farincikin 'yata, irin wanda kike nemawa taki 'yar amma saboda zumunci, saboda bin umarnin iyaye, saboda kada nayi sanadin rushewar ginin da iyayenmu suka fara nasa kafa na take farincikin Zahra" Daga cikin dakin nasu Fauziyya ta zubawa yayarta ido yayin da Zahran ta fashe da matsanancin kuka. Mami kanta hawaye take yi yadda 'yan uwanta suka gagara fahimtarta da mijinta. Komai suna yi ne domin dabbaka zumuncin amma yanzu saboda fitinar Gambo Ummansu ma ta soma fushi da ita. "Ni Hassana banfi kowa cikinku ko cikin dangi ma haka ma 'ya'yana amma nasan cewa munyi kokari sosai wurin basu tarbiya duk da sun tashi nesa da gida. Zahra tana da wanda take so amma rana tsaka Alh Baba ya kiramu yace yayi musu mazaje ita da Fauziyya. Nafi kowa sanin irin soyayyar dake tsakanin Zahra da Raji amma na tausasheta nace tayi hakuri ta farantawa kakaninta zaiyi daidai da mune muka farantawa iyayenmu. Babu wani sabo, shakuwa ko soyayya yaran nan suka amince amma duk baku gani ba. Kullum kwanan duniya ina tashi da zulumin rayuwar da Zahra zata yi a gidan mijin da bata so. Ni da ya kamata na tayata neman farinciki nice na dage kada ta fitar da maganar ko mahaifinta bai sani ba balle 'yan uwanta. Ku har zaku fada min sanin darajar zumunci?" Shiru suka yi aka rasa me magana a cikinsu. Basu taba ganin fushin Mami irin wannan ba. Major yana tsaye basu sani ba yana jin abinda take fada. "Na gaji da cin kashin da kuke yi min daga ke har Hussaina akan auren Awwab. Babu wadda ta haifa min dan kuma na fada bazan taba hana shi auren wadda yake so ba. Idan yace zai iya hada duka su biyun Allah Ya dafa masa." "Gara ki fadi abinda kike son fada zaki nuna mana kece uwar Awwab" "Kamar yadda ke uwar Ghazalatu kike wanke kafa kika taho gidana domin taki 'yar ba. Wai ma me kuke so nayi muku ne? Ince Awwab ya zama silar kunyata mahaifinsa? Har abada bazan ce ba. Ni na san waye Zayyan a rayuwar Daddy kuma in sha Allahu bazamu ji kunyar iyalinsa ba." "Dangin dangiro sun fimu" Gambo tace rai a matukar bace. "Hussaina, Gambo. Ya isa haka kuzo ku wuce gidajenku" Major ne yayi maganar idanunsa sun kankance ya fito musu a rikakken sojansa. Basu iya sake tankawa ba suka fita suka bar Mami Hassana tana zubar da hawaye. 💕[11/2, 7:06 AM] : 35. 💕 Awwab yana tunanin yadda zai shiga gidan ya gabatar musu da bakin ga taron mata tun daga waje sai Allah Ya taimake shi ya hango Emzee yana tahowa tare da wasu samari sa'anninsa. Shadda ce a jikinsa light green irin wadda sai ka kula da kyau zaka gane kalarta saboda rashin turuwa da hular zanna bukar saka mai kyau. Yayi aski da gyaran fuska dan gemu da gashin bakin da ya fara tarawa an gyare su fuskarsa ta sake fitowa ga kamannin Zayyan karara. Muhammad Zayyan Tureta kenan yaro matashi da yake ganiyar kuruciya dan kimanin shekara goma sha takwas. Kayataccen murmushi yayi da ya hango Awwab ya taho wurinsa da sauri. "Innalillahi wa inna ilaihi rajiun. Zayyan?" Mammee tace muryarta da jikinta na rawa. "Na'am" yace lokacin da ya juya yana fuskantar mutanen. Idanu suka zuba masa suna mamakin irin wannan kamanni. To ai ko ba'a nemo su ba duk inda suka hado da yaron nan zasu rantse jininsu ne. Babu wanda ya sani cikinsu amma yadda ya gansu yawanci dattijai ne masu kuruciyar basu da yawa yasa ya rissina da zumar gaishesu wannan mata da ta kira sunansa kanwa ga kakarsa marigayiya Alheran Ghousman ta rungume shi a bainar jama'a tana kuka tare da ambaton sunansa. "Zayyan, Zayyannn, Zayyan kuyi hakuri" Mutanen da suke wurin sai suka fara kallonsu. Emzee ya shiga kici kicin kwace jikinsa tana kara nanikarsa. Daga gefe Salame matsowa tayi ta kare musu kallo da kyau. Bata iya ganin fuskar Emzee shiyasa bata san ko waye ba ta kada tawagarta suka shige gidan. Awwab ne ya riko hannunsa yana yi mata murmushi yaja shi gefe "nayi ta kokarin kiran Ummi ko Alheran bana samu. Daga Nijar suke" "Da gaske?" Emzee yace yana zaro idanu da mamaki. Da sauri ya shige ciki Awwab yace musu zai je ya sanar da Ummi ne. Duk basu damu ba suka ce zasu jira. A ciki mata musamman manya ne suke tsokanar Emzee wai ya shigo taron mata. Hankalinsa baya garesu yana ta wurga ido yana neman Umminsa. Radhiya ya hango ta fito daga daki da shadda kalar tasa anyi mata doguwar riga mai karamin hannu da bai kai gwiwar hannunta ba. A Kano akayi musu dinkin Mama ce ta bada. Kamar ba ita ba tayi kwalliya harda janbaki. Dauri akayi mata irin mai hawa hawan nan dayake dankwalin da girma babu mai gane yaya gashin yake. Ta sami mayafi dark green kalar zaren aikin rigar ta yafa ta bayanta iya kafada ya rufe mata hannuwa amma bata hade shi ta gaba ba. Da gudu gudu ta fito daga dakin tana mita saboda Ummi tace mata saura ta bata jikinta. Ta yaya za'ace kada ta bata jiki kamar yarinya. Ummin ta rinka dariya tace ta saba jin suna haka da Innawuro. "Sai na zata kazama ce" "Innawuro ai ba sona take ba. Ni da tayi min...."bata iya karasa me zata ce ba ta fito shine suka hadu da Emzee. "Ina Ummi?" "Tana ciki" "Hamma Awwab yana waje" yace da ita tayi hanyar kofar da sauri. Shiga yayi ya ganta tamkar ba Ummin da ya sani ba. Sanye take da irin kayansu dinkin da komai irin na Radhiya. Bata yi kitso ba amma ta tufke gashin ya wuce kafadarta yana ta kyalli. Mairama tayi matukar kyau babu yadda zaka ce ita ta haife su. Zamansu a ruga babu yunwa babu kishi sai dai kawai rashin wayewa wanda da karfin cin tuwo Mama Zainab take cusa musu. Tsallake matan dake zaune a dakin yayi ya karasa gefenta ya duka ya sanar da ita bakin da suka yi. Ummi bata san lokacin da taji kwalla ta taru a idanunta ba. Da gaske Major ya nemo dangin Awwab na Nijar har sun biyosu Sumaila? Da zafin nama ta tashi tunanin me ya kamata ta farayi domin karramasu ya darsu a ranta. "Su nawa ne?" Ta tambayi Emzee a yayin da take fita daga dakin. "Wallahi Ummi motocin da yawa" Tana fita dakin Yadikko tayi inda suke ta fama da baki ciki harda Innawuro da Nene Marka. Sanar musu tayi kowacce ta tashi da sauri aka shiga kiran kannenta masu kuruciya su taho za'a gyara bangaren samari inda babu kowa. Wurin akwai dakuna uku da baranda mai dan girma. A barandar suke tunanin saukesu idan an share. Hajjo, Yadikko, Innawuro da Nene Marka kowa ta bazama ana kokarin hada abinda ya dace. Allah Yasa akwai kofa ta waje da za'a iya shiga wurin ba sai sun shigo cikin turmutsin 'yan biki ba. Sai da Ummi ta ga komai ya fara daukan saiti tace da Emzee yaje yace suyi hakuri tana kokarin samun wurin da za'a saukesu ne saboda 'yan biki gidan a cike yake. Ya juya zai tafi fadin sakon sai ga Salame da 'ya'yanta ta rasa dakin wa zata je. Yadikko da Hajjo duka ta leka basa nan. Asabe da Hanne ba saninsu tayi ba kuma ma dai ta rainasu. Bai kula da ita ba ya rabe abinsa ya wuce. Yarinyar da ta yaye ce ta shiga jan zaninta tana kuka tare da nuna wasu yaran da suke cin shinkafa dafaduka. "Umma umfafa" "Rufe min baki dalla can za'a zuba muku" Na biyu a cikinsu shi kuma ya ja hannunta cikin tashin hankalin kuruciya ganin wadda yaran da suke kallo suke ci ta kusa karewa "Umma zasu wawashe bamu samu ba" Dagewa tayi ta make bakinsa ya sa kuka kuwa da ta ga an fara kallonta ta rage murya "dan ubanka rufe min baki maye" "Ya zaki kira shi maye? Haba kinsan yara sai hakuri ki zaunar dasu mana a zuba musu abincin" Ummi Mairama ce tayi maganar saboda zata wuce ta hango Salamen. Wani farinciki taji a ranta duk da rashin jituwar dake tsakaninsu tana kallon yadda 'yar uwarta ta chanja. Rashin lokaci saboda shirin biki da kuma hani daga Nene Marka duk da bata san dalili ba ya hanata zuwa gidanta bayan idonta ya bude. Isowarta taji suna wannan rigima da yaran. Batare da ta dago ba, har yanzu tana duke saboda bayanta da ya amsa garin saurin dukan yaron taji wani uban kamshi mai sanyi da ya mamaye wurin wanda ke fita daga jikin Ummi tace "barni da shegu basu da aiki sai cin abinci. Gudun kwadayi yau sukunbiya na saya musuuuuuu" bakin ya makale ta kasa shiru duk da ta kai karshen kalmar. Ido ta tsaya gogewa da hannu babu kunya babu tsoron Allah sakamakon gamon da tayi bayan ta dago. Wata take gani kamar kanwarta cikin shiga ta kece raini ta wuce sa'a. Daga sama har takalmin kafarta sai da ta bisu da ido tana jinjina kyau da haduwa irin na suturar da mai ita. "Mairama? Mairama kece ko dai kama ce?" Sassanyan murmushin nan nata mai kara kawata kyakkyawar fuskarta ta saki "Adda Salame nice mana" Tsananin mamaki bai bar Salame ta dakata haka nan ba sai da ta ciro hannu tana yawo dashi a gaban fuskar Mairama wadda farin gilashinta ya karawa kwarjini. "Kina ganin me nake da hannuna?" Tace baki na rawa. Ummi sai ta kama hannun ta rike. Nata yayi laushi sosai saboda gyaran da akayi musu a salon. Na Salame kuwa sai dai ayi shiru ayi kurum inji dogaran sarki. Kanta da lamba...a daiyi shirun kawai. "Adda idanuna sun bude cikin hukuncin ubangiji. Zamuyi magana dai ina da baki" ta fada tana yin gaba da sauri. "Banten uba, kai!!!" Salame tace a gigice gabadaya ta kasa gane me take yi. Ko dai gizo ne tayi mata ba ita din bace a zahiri? A'a Mairama dai kanwarta ita ce da wannan shigar ta chanja tayi kyau haka kuma wai TANA GANI? Zuciyarta bugu take yi kawai kamar wadda tayi tsere ga bakinciki da takaici sun taru sunyi mata rubdugu. Zaninta karamar yarinyar ta sake ja tayi nisa a tunani taji cikin kuka tana cewa "Umma, umfafa ta kare" Wata mahaukaciyar mangara ta kaiwa yarinyar wadda take rike da zanin leshin da dama da kyar ta hade shi a jikinta saboda ciki. Yadda yarinyar tayi gaba ta fadi haka ta tafi da zanin babarta Salame a hannu. Sai ga Salame matar Alh Indararo a tsaye da dan sket dinta na ciki ya fita hayyacinsa saboda tsabar jigata da kodewa. Dan lace din da akayi masa cin baki dashi ya barke yana reto a jikin kafafunta wurin gwiwa bari daya ne dinkin bai gama fita ba. Kuma gashi na silk mai santsi wani zare zare nan duk ya fara fita daga inda dinkin lace din ya fita. Bata ma ankara da wuri ba sai da babbar 'yar tace "Umma ina zaninki?" Baki ya goge da ashar har ta gama hado shi zata lafta mata ta ga mutane sun zuba mata ido wasu suna ta dariya. Sai a lokacin ta hango shi a hannun mai kuka. Kafafunta ta kalla kunya matsananciya da muzanta suka dirar mata. Ga ciki ga dan lace suna neman kayar da ita haka ta tafi da uban sauri ta finciko zanin ta daura mutane suna ta dariya. Duk masifarta sai ta rasa abin cewa ta shiga neman wurin buya saboda kofar gidan babu wani wurin wucewa an cika makil. Lokacin da Radhiya ta fita Awwab yana tsaye a gefe suna magana da daya daga cikin mutanen Nijar din amma da yake tun zuwansa hankalinsa gabadaya yana kan kofar yana fatan fitowarta shiyasa tana leko da kanta ya hangeta. Ajiyar zuciya ya saki da ganin fuskar da yake matukar so da kauna. Ita kuwa sai waige waige take tana yi tana komar da kanta saboda mutane. Alh Sidi ne ya fara ganinta daga inda suke tsaye ya tabo dan uwansa Alh Ghoumar yana murna "kaga Alheran" Alh Ghoumar ya juya shima yayi sa'ar ganinta "Allah mai iko, ka ga kamaninta da tamu Alheran din?" "Dalilin da yasa na ganeta ma kenan" Tana wannan leken taji an kamo hannunta an ja ta gaba. Zata yi magana ta ga Emzee ne. Ita fa bata san da wasu baki ba Hammanta tazo gani. Yana rike da ita bai saketa ba sai a gabansu. Kanta ne ya nemi juyewa dama ga yara sun yanyame motocin saboda kyaunsu ga kuma su kansu mutanen da yawa suna ta fitowa daga mota. Kukan Mammee da ta rungumeta har yafi na dazu domin yadda Radhiya take diban yanayi sosai da yayarta. Murmushin da Radhiya tayi ya kara karya mata zuciya saboda lotsawar kumatun sak na yayarta ne. Emzee yana yi mata bayani su ma suna ta yarensu suna dan hadowa da Hausa saboda jikokin nasu. Fada musu yayi su dan kara hakuri suka ce babu komai sun san gida ne na taro gashi ba'a san da zuwansu ba. Radhiya dai yau harda jin kunya yadda mutanen nan dukkansu suke ta rungumarta matan. Mazan ma ita dai taji wani ya kamo hannunta babba ne kuwa abokin wasan Zayyan sai dai kafin ta motsa taji wani tattausan hannu ya janyota baya sannan ya dawo gabanta ya tsaya tsakaninta da mutumin. Babu mai fahimtar mai Awwab yayi ko dalilinsa sai wanda yasan tsakaninsa sa Radhiya. Abinda yaji ya ratsa shi kuwa shima sai da yayi nadamar taba hannun nata. Daga inda yake tsaye yana kallon wannan runguma zuciyarsa ta tsinke da yaga mata sun kare kada a fara da maza. Kishin da ya yunkuro masa ba kadan bane. Allah ne Ya taimake shi ya taho da wuri yau da sai anyi abinda zai mutu bai manta ba, wato Alheran dinsa a jikin wani. Babu ruwansa da alakar dake tsakaninsu tunda ya tabbatar babu muharraminta ciki idan aka cire kakaninta biyu Alh Ghoumar da Alh Sidi. Sauran duk wanda ya tabata ya taba masa mata ne. Ummi da kanta ta rufo mayafi ta leko kiransu. Mutane suna darewa wadannan jama'a guda wadanda dukkansu kowa ka kalla kasan ya taka wani abu a duniya na arziki mazansu da matansu suka shige inda aka nuna musu. Tabarmi ne sababbi manya aka shimfide musu suka zazzauna babu girman kai da jin su din wasu ne. Mammee ta rike Ummi tana ta sharar hawaye. Rabon da su hadu shekara goma shatara tun ranar sunan Alheran Radhiya. Wurin minti goma ana ta matsar kwalla Ummi an fama mata rashin gwarzon namiji masoyin kwarai Zayyan uban 'ya'yanta. "Mairama yaya bayan saduwa? Kiyi hakuri. Don Allah ke da 'ya'yan nan kuyi hakuri" Alh Sidi yace yana duban su duka su ukun. Salame da kunya ta korota sashen mazan gidan nasu taci karo da wannan abin al'ajabi. Wurin gabadaya wani irin kamshi yake yi. Sakato tayi tana kallon mutanen. Maza biyu cikinsu wato su Alh Ghoumar sun dora rawaninsu na al'ada a kawunansu. Sauran kuwa sai ka rantse wasu larabawa ne. Buzaye ne gaba da baya da kudi ya kara gyarawa rayuwa suka kara fitowa. Bakinta bai iya neman abin fada ba na nuna mamaki taji muryar marainiyar wayonta Mairama. "Don Allah ku dena bamu hakuri ba laifinku bane. Kaddara ce kawai da kuma abinda Kawun yaran nan yayi mana" Kallo ta bita dashi suna zaune tsakiyar mutanen da ita da 'ya'yanta. Zuciyarta har wani girgiza tayi da ta kalli Emzee. Itama sai ya tuna mata da nata tsohon mikin na son mijin kanwarta. Babban abin da ya daure mata kai shine sanin da tayi Mairama ta makance suna kauye ita da gayyar yaranta. To tana ina ne ta warke kuma suka yi fes dasu ba yadda take tsammanin ganinsu ba? Ga wani kyakkyawan saurayi tsaye a gefe ya tokare kafarsa daya da bango shi kuma ko waye? Tambayoyi take ta yiwa kanta tana neman amsa ido rufe. "Matsa a wuce" taji ance daga bayanta. Matsawar tayi kuwa aka fara shigowa da tray-tray na kayan abinci da abubuwan sha. Duk abinda za'a tanada Innawuro ce ta kwance gefen zaninta ta bada kudi masu yawa har su Yadikko sai da suka yi mamaki. Bafillatana tana zaune haka cikinsu ana dariya ashe dukiya ce a jikinta. An dibar musu cikin abincin bikin sannan aka siyo tsire da balangu mai yawa da lemukan roba da ruwa masu sanyi. "Shiga ku gaisa mana 'yan uwan Marigayi ne daga Nijar" Hajjo tayi maganar tana wucewa ciki ita da su Nene Marka suka gaisa da bakin aka gabatar musu da abinci. Kamar zata hadiyi zuciya ta juya batare da ta cewa kowa uffan ba ta bar wurin. Su dinma babu wanda ya kula da ita suna murnar ganin juna. "Bari mu baku wuri kuci abinci don Allah. An tafi kiran babana sai ku gaisa" "Ki bar mana yaran idan tashi zaki yi" Wata mata mai faram faram tace cikin hausar da tafi kama da ta Kanawa. Ilai kuwa ashe aure ne ya kaita Nijar ita ce amarya cikin matan Alh Sidi amma mutuniyar Kano ce. Ummi tana murmushi tace dama wa ya aiketa. Inda Awwab yake tsaye ta kalla "dan Ummi zo muje kaci abinci" "Bazai ci cikinmu ba? Tare muka taho shima bako ne" saurayin da suke magana dazu dashi yace yana dariya. "Wannan naku ne kada ka damu dani" Radhiya ya kalla ta wani nutsu kamar ba ita ba "taso ki zuba min". Ummi na jin haka tayi gaba abinta tana murmushi suka tashi aka basu wuri domin su samu su sake musamman mazan. Emzee ne kawai bai tashi ba yana aikin amsa musu tambayoyin da suke yi masa game da rayuwarsu. Kofar da zata fitar dashi waje Awwab ya bi ba wadda zata sada shi da ainihin tsakar gidan ba. Radhiya sai tabi bayansa suka fito yayi hanyar inda ya ajiye tasa motar. Baya ya bude mata babu musu ta zauna shima ya zauna a gaba bangaren dreba kafafunsu suna waje. Lallen kafarta ya kalla ta saka daya daga cikin takalman da ya kawo mata tayi matukar kyau. "Shigar da kafarki ciki" Zumbura masa baki tayi sannan ta dauke kafafun. "Me yasa kika dena daukar wayata yau kwana biyu?" Ya tambayeta da wannan deep voice din tasa. Shagwabe fuska tayi kafin tace "to ba kaine ka dena kirana ba saboda ka koma Katsina wurin....wurin" Fada yaso yi mata na hora shi da tayi ta hana shi jin daddadar muryarta idan tana shagwaba ko ta hado wani shirmen nata sai ya kasa. Ganinta kawai da yadda tayi masa kyau ya kawar da komai. "Wurin wa?" Harara ta galla masa tana juya idanu ita anyi mata laifi sai dai gabadaya abin da tayi sauke masa kasala yayi "ai ka fini sanin wa nake nufi. Wurin My G mana ni kuma ka manta dani" Bushewa yayi da dariya damuwarsa ta ragu sosai. Babu wani abu da yake tunani sama da mallakar wannan yarinyar da take gabansa a matsayin matar aurensa. "Kema G dinki ce ashe" "A'a wallahi" tace da sauri, hakan ma yana kara bashi dariya har wani kada hannuwa take yi "taka ce kai dai" "Yanzu dai kishin dreba kike yi" ya dage mata gira "Allah sarki kanwata ta kare miki gashi dreban nan bazai barki ba sai kin amsa sunan matarsa" Tsuke baki tayi tana dariya kunya ta rufe ta. A hankali ta daga kanta suka hada ido tayi saurin rufe fuskarta da hannuwanta. Yatsun sun sha lalle kamar ya rikosu. "Schatzi" "Uhummm" "I miss you" "Zaka sa naji kunyarka Hamma" "Kuma I love you" Mayafi tasa ta rufe fuskar yanzu tana so ta tashi ta gudu tana gudun kada yace ya hanata. Langabe kai yayi yace "Baki bani amsa ba ko daya. Kenan bakiyi missing dina ba kuma ba kya sona" Radhiya ba wayo yana fadin haka ta dago da sauri "ba fa kaji nace haka ba" "Kina son nawa ne? Ba ni kadai nake abuna ba" "Kai Hamma Allah bance ba" ta fada kamar tayi masa kuka. Shi kuma ya sami na yi ya cigaba da cewa "do you love me?" "Eh mana" Yadda maganar ta fito a bazata haka itama ta fita daga motar harda tuntube ta kutsa ta cikin mutane tana jin kunya ta barshi da yi mata dariya. Wayarsa ce tayi ringing sai a lokacin ya kula ashe Mami ta kira shi sau biyar. Sunyi da ita suna zuwa zai hadata da Ummi tunda sun kasa samuta ya manta shaf. Bai yi tunanin amsawa ba yana gudun fada ya rufe motar ya koma ta bangaren da bakin suke don ya bawa Emzee ya kai mata. Ko da ya shiga ma sai yayi sa'a tana wurin dasu Nene tana basu labarin makantar da tayi da warakarta kwanaki kadan da suka wuce. Wayar ce ta sake shigowa ya mika mata yana cewa Mami ce. Karba tayi ta kara a kunne da sallamarta sai dai maimakon muryar Mami sai taji Fauziyya tana kuka sosai tana cewa "Hamma ka dawo gida ba lafiya" Ummi na jin haka ta mike tsam ta fita ta kofar waje saboda ko ina na gidan hayaniya akeyi ta sami gefen wani gida da bishiya a jikin gidansu ta tsaya. Hankalinta a tashe yake tace "Fauziyya me yake faruwa?" Gabanta ne ya fadi. Da farko kamar bazata ce komai ba sai da Ummin ta soma yi mata fadan cewa itama babarsu ce. "Ummi tun dazu Mami da Zahra suke kuka. Bansan me yake faruwa ba amma har Umma Hussaina da Mummy sunzo sunyi fada da Mami" Zantukan Fauziyya sun daure mata kai matuka ta kasa fahimtar me yake faruwa kamar yadda itama Fauziyyan bata gama ganewa ba. Kwantar mata da hankali tayi tace mata gobe zasu taho in sha Allahu da Awwab. Da ta koma su Mammee suka ce zasu tafi Kano su kwana biyu sannan su koma Nijar. Ummi bata ji dadi ba. Niyarsu matan su kwana a wurinta tun farko amma sun fuskanci hakan wahalarwa ne gareta saboda yanayin biki da ake yi a gidan babu masaka tsinke. "Yara muka zo gani dake kuma Alhamdulillah mun gani duka kuna lafiya. Sai dai muna son muji yaushe ne zaiyi muku daidai mu turo ku taho Niger domin ku hadu da sauran 'yan uwa" "Ba don bikin da zamuyi a Katsina na yara har biyu ba da tun yanzu zaku tafi dasu" Ummi tace tana kokarin boye damuwar da ta shiga tun bayan wayarsu da Fauziyya. "Kema sai kinje Mairama ba yaran kadai ne namu ba" Mammee tace sauran suna dariya. "In sha Allahu muna gama bikin zan sanar daku Mammee" Sallamar Malamijo ce ta katse zancen nasu. Bai yarda ya zo wurinsu ba sai da ya shiga cikin gidan yaje ya chanja kaya. Kayan da zaisa gobe na daurin aure ya sako saboda motocin da ya gani sun tayar masa da hankali. Ya saka babbar riga yana ta baza hannuwa. Saboda karfin hali ya sami irin farin abin nan da akan gani malamai sun ninka sun daure hularsu dashi na ustazai shima haka yayi ya fito ko karya babbar rigar baiyi ba don ya kara cika ido. Wurin bakin yaje ganinsu ya sake tayar da hankalinsa yasan lallai ba bakin rainawa bane. [11/2, 7:11 AM]🏽 ]🏽 : 36.**********💕 Yau falon na Alh Baba ya cika sosai sakamakon yawan wadanda aka zauna dominsu. Jikokin da abin ya shafa suna cikin gida sai an gama da iyayensu za'a nemesu. "Wace magana nake ji haka cewa jiya Gambo taje gidan Mustapha da Husaina yau kuma da Azumi ana rigima?" Babu wadda ta iya yin ko da tari ne saboda kwarjinin iyayen nasu. Alh Baba ya kara hade rai yace Mami ta fada masa me ya faru. Kai a kasa ta zayyane masa komai. Gabadayansu sun nuna fushi akan abinda kannen nata suka yi mata tare da Azumi. "Naga alama a kokarina na son inganta zumuncin zuri'ata al'amura suna kara tabarbarewa. A zamaninmu dai mace ko namiji sai dai ace ga wane za'a hadaku aure kuma ayi auren a zauna lafiya. To amma na kula daku da 'ya'yanku abin ba haka yake a wurinku ba" Baba Karami ya kalli su Mummy "Gambo baku kyauta ba ko kadan abinda kuka yiwa Hassana har gida kuma a gaban 'ya'ya. Ko bata girme ku ba ai ta ci darajar auren yayanku" Sun hadu sun yi musu fada akan abinda ya faru sannan Alh Baba yace to tunda abu ya koma kowa kanta ta sani da 'ya'yanta zai kira yaran ya sake tambayarsu. Duk abinda suka yanke shikenan. Kana ganin yadda yake magana kasan akwai bacin rai sosai a tattare dashi "Zabi ya rage tsakaninku da 'ya'yanku bazan sake saka muku baki ba balle inyi bakin jini" "Alhaji kayi hakuri don Allah. Muma kaine ka aurar damu in sha Allahu duk yadda kace akansu haka za'ayi" Daddy yace sauran 'yan uwansa suka nuna amincewarsu. Alh Baba sai kuma yaji nauyin yadda duk da yafi kowa sanin cewa son kansa ya nuna akan komai amma gabadaya yaran da iyayensu kai hatta kannensa kowa ya amince ne domin biyayya a gareshi. A tunaninsa wannan hadin kara dankon zumunci zaiyi amma zamani ya chanja. Bai manta ba daren jiya da Baban biyu yake ce masa auren hadi yanzu a cikin goma daya akan samu ana zaman lafiya. Biyu ayi zaman hakuri sauran bakwai din kuwa duk mutuwa suke yi wani lokacin ayi rabuwar da zata shafi har jikoki. Ya bashi shawara cewa idan jikokinsu sun hada kai a junansu a barsu suyi aure haka kuma masu nema a waje su ma a basu dama. Haka suka shigo masa Zahra, Ghazalatu da Fauziyya idanunsu a kumbure suna kan kuka ma. Awwab kuwa kallo daya yayi masa ya dauke kansa. Damuwa da bacin rai sun rufe kyakkyawar fuskar yaro mai yawan fara'a da wasa da dariya. Anya ya yiwa 'ya'yan Hassana da Mustapha adalci kuwa? Yara har uku yana neman tauye musu hakki akan abinda ba addini ba. Don dai kawai Baban Biyu yana da kawaici amma ace jikokinsa har hudu duka ya nuna shine mai ta cewa akan makomar rayuwarsu kuma nasu kakan ya nade hannu ya kyale shi. "Matso nan Fatima" ya yafito Zahra da hannu. A tsorace take ta tashi ta koma kusa da kafarsa ta zauna. Ya kira Fawaz shima yazo ya zauna daga daya gefen nasa. "Kana son auren kanwarka?" Shiru Fawaz yayi na 'yan dakiku kafin ya girgiza kai yace baya so. Haj Azumi tayi gajeren murmushi. Tun a gida tayi ta nanata masa idan yana son kansa da arziki kada ya yarda a aura masa yarinyar da bata sonsa. A nasa bangaren shi dai baya kin Zahra amma kuma ba soyayya bace tsakaninsu shiyasa bai ga amfanin aurenta ba. Alh Baba ba haka yaso ba amma dole ya karba tunda a gaban iyayensu ake yi. "Fatima waye shi wanda kike so din?" Kasa magana tayi ya mayar da tambayar ga Major. Shi din ma bai wani san kan zancen sosai ba shiyasa Awwab ya fada masa yadda suka yi da ita dazu. "Yanzu zuri'ata zan hada da kabilu?" Yace cikin wani irin yanayi. Baba Karami yayi saurin gyara murya "Alhaji kada mu koyawa yaran nan kin 'yan uwansu musulmi saboda bambancin yare da al'ada. Mun sani cewa babu haramci a tarayya dasu sai ma kara karfin alakar dake tsakanin musulmi da dan uwansa." "Haka ne, idan mun tashi daga nan a kira shi a waya yazo da magabatansa idan yana sonta. Daga yanzu na soke maganar aurenta da Fawaz." Mami harda hawayen dadi. Lallai mai hakuri shi yake dafa dutse yasha romonsa. Bata taba tunanin zata sauyi irin wannan game da auren Zahra ba sai gashi ya samu cikin ruwan sanyi. "Fauziyya da Bilal fa? Akwai wani korafi makamancin haka tsakaninsu?" Bilal yaro mai tsananin kunya yace indai bata da wanda take so yana son aurenta. Fauziyya ma bata bashi kunya ba tace ta amince. Haka ya sanya farinciki a zukatansu. "To uban gayya da aurensa ya janyo mana wannan tone-tone. Na baka izini Muhammad ka nemi amincewar Ghazalatu da waccan yarinyar ayi aurenku rana daya babu wadda zata jira wata" Yana dire maganarsa Ghazalatu ta dago jajayen idanunta "Alhaji ina da magana" "Ina jinki" "Ni dai na hakura ko wani zaka zaba min zan amince amma banda Yaya Awwab" Tsawa Daddy Haroun ya daka mata ta fashe da kuka. Tana da kishin da bata jin zata iya zama da Radhiya da take gani kamar wata kaskantacciyar yarinya. Amma ba wannan ne ya janyo mata kin amincewa ba sai zugar mahaifiyarta wadda itama Hussaina ce ta ingizata kan cewa su hada Ghazalatu da nata dan Nura. Hussaina gani take ta sami dama da zata dandali arzikin gidan Gambo yadda ya kamata. A zahiri Gambo da Mami sun fi ta rufin asiri. Sai dai bata sani ba Mami a nata gidan kafin Major ya sami lafiya har ya fara aiki guminta ake ci. Ita kawai gani take suna da kudi ne suke son hada nasu 'ya'yan ita ko oho. Mummy Gambo an hau dokin zuciya ba bata lokaci ta amince bayan sun bar gidan Mami a jiya. "Saboda ance ya auri wadda mahaifinsa ya nema masa?" Baban Fawaz ya tambayeta. "Ni dai kawai bana so ne yanzu" Alh Baba yace "babu wanda zan tilasta a cikinku na gama wannan yayin. Tunda ba kya so Allah Ya kawo miki naki rabon. Kai kuma ku gama magana da waccan ina bukatar amsa da wuri" yana kaiwa nan yace duka ya sallamesu su tashi su tafi. Ghazalatu kuka kamar ana yankar naman jikinta amma tasan halin Mummynta da masifa. Idan ta kuskura ta komawa Awwab sai taji babu dadi. Hussaina duniya shar ta kira Nura tace ya fara yakin neman soyayyar Ghazalatu ita ta gama nata aikin. Awwab bai jira kowa ba ya fita ya bar gidan. Jin kansa yake kamar an zare masa wata kaya da ta tokare shi. Lallai zuciya bata da kashi. Bai tantance zafin so ba sai akan Alheran. Kinsa da Ghazalatu tayi ko kadan baiyi masa ciwo ba don tunda Mummy taje gidansu sau biyu tana cin mutumcin mahaifiyarsa yasan ko ya aureta wani kaso mai girma na kimarta ya riga ya sauka daga idanunsa. Sallar magariba ya tsaya yi kafin ya shiga gidan. Shigarsa tayi daidai da isowarsu Mami a motar Daddy. Zahra ce ta tuku su Fauziyya na gaba su Mami na baya. Idan ka ga Zahra fuskarta tamkar wadda aka baiwa kujerar Makka. Murmushi ne yaki tafiya kamar an zana mata shi har tsokanarta Daddy yayi yace shima sai ta nemi amincewarsa sannan zai kira Imam Abdulwahab mahaifin Raji. Kunya taji ta ruga cikin gidan kai tsaye ta tafi dakin Mami. Ummi ta gani akan sallaya ta fada jikinta tana ta dariya. "Zahra me muka samu irin wannan murna haka" "Ummi Alh Baba ya amince" "Da me?" Mairama ta tambayeta tana tayata murna tun kafin taji. Sallamar Mami yasa ta kasa cewa komai ta tashi ta koma nasu dakin da tsalle. Sai da Mami ta idar da sallah ta fada mata yadda al'amura suka juya. Ummi bata ji dadin fasawar da Ghazalatu tayi ba kuma ga dukkan alamu Mami da 'yan uwanta basu shirya ba. Indai haka ne kuwa to babu makawa Radhiya ma bazata auri Awwab ba. Meye ribarsu ayi auren da ya taba zumuncin iyaye. Fauziyya da Zahra ma sallah suka shiga yi suka sami Radhiya ta dukunkune kanta ta cure wuri guda tana baccin wahala. Tayi kuka ne har ya saka mata ciwon kai shine bacci ya dauketa. Zayyana ta fito daga bandaki ta yayyenta kowacce da murmushi a fuskarta. Zahra ta rungumeta tana dariya itama tana tayata ta tabbata abinda yasa su kuka dazu ya wuce. Ihunsa ya tayar da Radhiya da kyar ta iya bude ido sun kumbura tayi musu sannu da zuwa. Fauziyya ta tuna cewa dazu maganganun su Mummy su ma daga dakin Awwab sun ji bare kuma ita da suka bari a nasu dakin. Sai taji tausayinta ya kamata "kinyi sallah kuwa ko sai nazo nayi miki balotelli?" Murmushi tayi kanta kamar ya tsage ta daure "da almakashina a jaka" Dariya suka yi su duka yanayin dakin yana chanjawa daga shiru shiru zuwa na 'yan mata wadanda ke tsaka da jindadi. Da bin bango Radhiya ta je tayi alwala ciwon kai yayi tsanani ga zazzabi. Bayan ta idar Zahra ta taba wuyanta ganin duka jikinta yayi la'asar. "Radhiya baki da lafiya kika zauna shiru a daki. Bari na karbo miki magani" Da saurinta ta fita taje dakin Mami tana tambayar panadol. Ummi sai da taji babu dadi tasan halin Radhiya da saka abu a rai. Karshenta kuka ta rinka yi ya janyo mata zazzabin da ciwon kai. "Nemo min Awwab yazo ya kaita clinic dai. Ga gajiyar hanya kuma an taho ana tsaka da biki duka babu wani hutu" Mami ta umarci Zahra tana bin bayanta zuwa dakin. Ummi ko motsi bata yi ba tana addu'ar Allah Ya kawo sauki cikin lamarin saboda tsoro da ya fara darsuwa a zuciyarta. Hankalin Mami ba karamin tashi yayi ba da ta taba jikin Radhiya. Jiki yayi mugun zafi fuskarta har wani ja take yi. Awwab yana cikin shiryawa bayan yayi wanka Zahra taje ta fada masa sakon Mami. Ya rigata fita daga dakin da sauri. Sallama ya tsaya yi a kofar nasu dakin amma da kyar ya daure bai kutsa kai ya shiga ciki ba. Mami ta fito da Radhiya da ta tallafo a jikinta. "Me ya sameta haka Mami?" Awwab yace a raunane. Abinda zai kashe bakin Radhiya da wannan kuzarin nata ba karami bane shima ya sani. "Kuje mota bari na dauko mayafi. Zazzabi ne ina jin da ciwon kai" A hankali ta rinka tafiya ganin Awwab ya sake tayar mata da hankali. Tana son shi dole ta barshi idan ba tana son abinda Ummi take guje mata ya faru da ita ba. Wasu hawaye ne suka zubo mata duk yadda taso daurewa ta kasa. Sai da ya dan matso da kansa kusa da ita yana son rage mata damuwa ya tsokaneta dacewa "come on Schatzi bana son shagwaba fa. Ke da zansa a yiwa allura kamar hudu kuma kike min kuka" Duk da ciwon haka ta harare shi yayi murmushi yana cewa "in dauke ki ne?" A dole ta daga kafa tana jin kunyarsa. Da Mami suka je asibitin aka dubata likitan yace banda zazzabi harda damuwa. Mami sai ta alakanta komai ga abinda ya faru a gidan zuwan su Gambo. A take ta yanke shawarar sanar da Daddy yayiwa yaran magana gobe idan sun amince wa juna ayi bikin kowa ya huta. Da suka koma gida ta fita tana jiran Radhiya shiru Awwab ya hanata fitowa ta shige ciki tana fadawa Ummi wai ta ga alama ciwon soyayya ne yake damunta. Ummi dai dariyar yake tayi, neman abokin shawara take gashi Zainab bata nan. A wajen Awwab ya tsare Radhiya da tambayoyin son jin damuwarta duk da shima yana tunanin ko abin dazu ne "me kika sa a ranki har ya saka kiki fever?" "Babu komai Hamma" "Saboda zuwan Mummy ne dazu ko? Komai ya wuce kinji yanzu babu zancen Ghazalatu ma. Ke kadai ce dani Schatzi kuma kin isheni don son da nake miki bana jin akwai wadda zata sami rabinsa a wurina" Kalaman sun mata dadi, da babu wannan matsalar da tafi kowa farinciki amma yanzu bata da wani abin yi sama da murmushi ta fake da rashin lafiya. Shima da ya ga shirun nata yayi yawa duk sai ya damu. "I miss my Alheran, wannan mara lafiyar duk ta hanani ganinta. Kije ki kwanta and please take care of yourself for Awwab" "Hammana sai da safe" yaji tace da karamar murya tana tafiya sai bayanta kadai yake iya gani. Haka kawai yaji jikinsa yayi sanyi zuciyarsa tana tabbatar masa da cewa akwai wani babban al'amari a tattare da Alheran. Ko ma meye yayi niyar jira zuwa wayewar gari taji karfin jikinta sai ta fada masa damuwarta. Daddy kuwa a daren ya kira Imam Abdulwahab ya fada masa basu da masaniya akan cewa akwai alaka tsakanin Raji da Zahra har aka yi mata miji. Imam yace basu yi sati da sani ba shi da matarsa. Sai da suka ga shige da ficen asibitin nasa yayi yawa suka matsa Munnirat kanwarsa ta sanar dasu. A lokacin hakuri kawai ya bashi tunda suna da labarin aurenta ya kusa. Major yace to aure ya tashi saboda ta sanar bata son angon nata. Yanzu haka ya kira ya sanar dashi ne cewa asabar mai zuwa ya kamata daurin aurenta amma za'a basu dama idan sun amince ya turo Raji neman aurenta. Bayerabe yasan darajar alkhairi kuma yana mutunta duk wanda ya karrama shi. Imam Abdulwahab ya rinka kwararowa Major da iyalinsa addu'a kuma ya tabbatar masa in sha Allah ranar asabar Zahra zata yi aure kamar yadda aka tsara tun farko. Da kansa yaje dakin Raji da yake kwance yana jinyar zuciyarsa yayi masa kyakkyawan albishir. A take ya wartsake sai gashi har asuba suna waya da Zahra wadda itama ta ware baka ce ita ce take ta koke koke a kwanakin da suka gabata ba. SABUWAR RAYUWAR "To Alhamdulillah al'amura sun daidaita Alh Baba ya amince da auren Awwab da Radhiya sannan duk da ba haka muka so ba Ghazalatu tace ta fasa. Allah Ya sani Ummin Awwab ban so kuka san wannan matsalar ba ko kadan a madadin Gambo muna masu baki hakuri akan cin zarafin da tayi muku jiya" Ummi ta shiga girgiza kai "bamu hakurin tamkar kuna nuna akwai bambanci tsakaninmu ne Daddy. Wallahi har raina banji haushi ba saboda haka magana ta wuce" Mami tayi murmushin jindadi sannan Daddy ya kalli Awwab da duk motsin Radhiya akan idonsa yake yana kokarin hada ido da ita amma taki dago kai. Gyaran murya yayi Awwab din yayi saurin juyar da kansa daya gefen yana murmushi. "Awwab ga kanwarka nan na baka amana ko bayan raina ban yarda ka rabu da ita ba. Idan ta bata maka ko tayi ba daidai ba ka hukuntata amma ban yarda diyar Zayyan tayi kuka saboda rashin adalcin gidan aure ba" Farincikin da Awwab yake ji a wannan lokacin bazai misaltu ba. Dan taki kalilan ya rage masa da mallakar abar kaunarsa. Yana sake dawowa ko sati daya ne hutun yake so a daura aurensu. "In sha Allahu bazan baku kunya ba" "Radhiya baki ce komai ba" Daddy yace yana kallonta yana murmushi. "Ai ka kashe bakin nata Daddy yau daya dai ga kunya ga sauran zazzabi 'yata bata da ta cewa" inji Mami. Hawayen zuci Radhiya take yi na samu da rashi da ya sameta a lokaci guda. A hankali sautin kukanta ya fito fili. Yadda Awwab ya gigice sai ya baka tausayi ana ta tambayarta ko jikin ne ta kasa magana. Ummi jikinta yayi sanyi amma ta san har ga Allah hakan da tayi shine daidai. Tafi kowa sanin ciwon da ta kunsa saboda juya mata baya da Salame tayi da rashin kyakkyawar alaka mai tattare da shakuwa da tayi karanci a nasu gidan. Banda ma yanzu da abubuwa suke dan chanjawa amma a da kam gidansu nafsi nafsi kawai akeyi kuma bata cire kanta a ciki ba saboda haka a ka sabar musu. "Radhiya ko bakya son auren ne?" Daddy yace bayan ya karar da duka tambayoyin da yake jin zaiyi mata. A razane Awwab ya kalle shi yace "Daddy?" Ga mamakin su duka ukun Radhiya ta gyada kai. Daddy kansa sai da ya girgiza ba Awwab da ya daga murya yace "karya take yi Daddy" Daddy yace "Awwab ka nutsu ko ka fita" Zama ya koma yayi amma babu nutsuwa bare kwanciyar hankali. Ita wadda akeyi dominta kuka kawai take yi idanunta sunyi luhu luhu dama shi ta kwana tana yi. "Muna sauraronki Radhiya" "Daddy karatu nake son yi" "Banda abinki Radhiya waye yace miki aure na hana karatu?" Mami ta tambayeta tana dan sakin rai a zatonta wautar ce ta motsa. "Ba nace miki zan samar miki admission a Abuja ba?" Awwab ya ce muryarsa tana rawa yana kokarin danne bacin ransa. "Daddy ni dai don Allah bana son auren nan gabadaya" "Alheran!!!" Awwab ya daka mata tsawa ta kuwa sake tsorata ta fashe da wani kukan. Gaban Daddy ya koma ya durkusa "don Allah kada ka saurareta wallahi karya take yi Daddy. Ka aura min ita ko ranar asabar ne tare dasu Zahra please Daddy" Ummi ma dai kukan take yi tana tausayawa yaran har ta fara jin ko dai tayi kuskure ko matakin da ta dauka yayi tsanani da yawa. "Ba kya son auren ko Radhiya?" "Eh Daddy" "To tashi ki tafi wurin 'yan uwanki na kashe maganar zan nemeki daga baya" Baki Awwab ya saki yana karyata abinda kunnuwansa suka ji daga gareta da kuma Daddy. Jiki a mace ta tashi zata fita yasha gabanta. Da fada ya fara cewa "Ni zaki yiwa haka Alheran? Ba sai da na nemi izininki ba kafin nazo na fadi cewa zan hadaki da Ghazalatu ba? Kuma yanzu ta fasa bazan hadaki da wata ba I promise" ya kare da kwantar da murya. Daddy sai da yayi masa tsawa ya fita a fusace jikinsa yana rawa. Dakinsa ya tafi yana shiga sai ga hawaye. Ransa yaji ya kuma baci ya rasa me zaiyiwa kuka tun girmansa sai mace. Macen ma Alheran da ya bawa dukkan soyayyarsa a cikin abinda baifi wata daya ba amma tasa kafa ta ture saboda dalilin da bashi da muradin sani. Itama tana fita dakinsu Zahra ta nufa tana nata kukan kamar ranta zai fita. Bata hangowa kanta sauran farinciki tunda ta rasa Awwab. Shiru falon yayi Ummi na goge hawaye Mami ta rasa me zata ce ma. Tashi Ummi tayi zata fita taji muryar Daddy a sojansa. "Mairama dawo ki zauna ki fada min dalilinki na raba yaran nan" Gabanta ne ya fadi Mami ta bita da kallon mamaki. Soja ba abin rainawa bane. Yanayinta kadai ya sa shi saurin fahimtar tana da hannu a abinda Radhiya tayi. Zama tayi ta nuna musu babban kuskuren da yake tattare da batawa da 'yan uwansu saboda yara. "Yau da Allah Ya dauki raina bayan rasuwar babansu Karami ina mai tabbatar muku dawowar nan da kuka yi zaku sami yaran nan cikin mafi munin yanayi ne saboda babu wanda zai tsaya min ya kula dasu a gidanmu yadda ya dace. Gidan nawa mahaifin babu shakuwa babu sabo tsakaninmu sama da mutum ashirin. Wadda muke tamkar 'yan biyu da ita komai namu tare tazo ta juya min baya a dalilin son da ta yiwa Zayyan tun yana raye. Tun kafin muyi aure ta dauki gaba dani har yau bata sake zani ba. Ba yau da muke tare da 'ya'yanmu bace abin ji, gaba da bata da kadan Daddy ita ce abin dubawa. Mami don Allah ki sasanta da 'yan uwanki kafin kiyi tunanin auren nan. Kada ki manta a dalilinsa rigimar ta faro na tabbata ana yinsa sai abin yafi haka" Sai yanzu Mami ta soma hawaye itama ta san cewa gaskiya Ummi ta fada. Duk da haka Daddy yace "da sai kiyi mana bayani ba sai kin raba su ba. Ummi yau kinsa Awwab da Radhiya kuka anya bazamu hukuntaki ba?" Ya kare da murmushin dattako. "Nasan idan da ta amince babu abinda zai hanaka daura musu aure. Radhiya dai 'yarka ce wani ma zaka iya bata bare Awwab. Alfarma daya nake nema ayi sulhu a daidaita zumuncin da yake neman lalacewa. Idan haka ta faru ko gobe ne wallahi ayi musu aure" Tana kaiwa nan ta tashi ta bar falon. Mami tana kuka tacewa Daddy hakika Mairama tayi zurfin tunani bata so kanta ba ta hakura da farincikin 'yarta dominsu. Sun yabawa Zayyan a baya yau suna yabawa matar Zayyan saboda a karo na biyu wannan iyali sun sadaukar da nasu jindadin don su kyautata musu. BAYAN SHEKARA DAYA Matashiya ce kyakkyawa sanye da riga mai dogon hannu baka mai kanun fulawoyi jajaye wadda ta tsaya mata a rabin cinya da skirt mai fadi shima baki tayi rolling da mayafi ja. Takalmanta loafers ne bakake da bakar jaka mai fadi wadda ta saka computer da tarkacen litattafai. Siririn agogon hannunta ta kalla tasan cewa kowane lokaci daga yanzu Yousuf zai iya kiranta su tafi gida. Watanta tara tana daukar kos na koyon turanci da faransanci sannan aka samar mata gurbi a University of Grenoble dake kasar Faransa inda ta fara karatu sati uku da suka wuce a fanin aikin jarida wato mass communication. Kamar yadda tayi hasashe wayar Yousuf ce ta shigo mata ta taso tana tafiya kai baka taba cewa Radhiyan rugar Barkindo bace. Ta koma hadaddiyar budurwa mai ji da gayu da wata irin nutsuwa kamar ba ita ba. Kamar kullum sai da ya bude mata ta zauna sannan ya shiga ya tayar da motar. Gaishe shi kawai tayi ta soma waya da Umminta wadda take karatun jarabawa saboda tuni itama ta koma karatu ta sami gurbi a jami'ar Bayero ta Kano tana karanta Adult Education. Mairama Ali Gidado ta zama babbar mace da maza suke kawowa hari ta kowane fanni suna neman aurenta. Da yawa basa yarda ma tana da yara biyu matasa da suke karatu a jami'a. "Ina Tante din taki ko kina makaranta ne?" "Ina hanyar komawa dai Ummi" "Kice ina gaisheta. Gobe zamu je NDA na fada miki za'ayi taro kuma Karami yana cikin masu yin match pass" Turo baki tayi cikin shagwabar da Tante dinta take kara ingizata take yi yanzu tana biye mata tace "ni yanzu bazan gani ba kenan? To ku daukar min video kinji Ummina" Dariya Ummi tayi ta rasa yaushe Radhiyanta zata girma "zan dauka in sha Allahu 'Yar soja rigima" Dariya tayi mara sauti Yousuf ya kalleta yana jin lokaci yayi da zai sanar da mamansa ya mugun kamuwa da son 'yarta. Sun cigaba da hirarsu da suka gama ta kira Ibrahim tana tambayarsa progress din jikin Baba Hadir. "Akwai babban albishir sai na koma gida zamuyi skype. Ke dai bari kawai na tsakura miki, ya fara tafiya babu sanda" Wata dariya da tayi sai da Yousuf ya manta me yake yi na dan lokaci. Tana zuwa gida da sauri ta shiga ta haye sama dakin 'yar Mammee wadda ta kasance kanwa kenan ga mahaifinta Zayyan mai suna Nasara ta fada jikinta tana murna. "Tante Babana Hadir ya soma tafiya babu sanda" "Da gaske Alheran" tace tana tayata murna. "Oui Tante" (eh anti) tace tana rungumeta. "To maza kije kici abinci kizo" Radhiya na fita Nasara tana kallonta zuciyarta fes. Bayan fasa aurenta da Awwab wanda yayi sanadiyar da ya bar gidan ana dawowa daga daurin auren kannensa ya koma Abuja kwana uku kafin hutunsa ya kare. Yayi fushi sosai da Radhiya wanda har Daddy yayi masa bayanin dalilin yin hakan bai dena jin zafin abin ba. To bayan komawarsu ne aka turo daukarsu daga Nijar inda suna zuwa Nasara diya ga Mammee tazo hutu da mijinta da dansa Yousuf wanda mahaifiyarsa ta rasu ta shiga rokon arzikin a bata ita. Bata taba haihuwa ba gashi tana da son yara. Ita tana yi mijinta na tayata aka kai maganar gaban Ummi ita kuma tayi kawaicin hadasu da Daddy. Ba tare da bata lokaci ba ya amince ko babu komai yana sa ran zata samu kyakkyawan sauyi a rayuwa. Zamanta tare dasu ba'a cewa komai sai son barka. Nasara tamkar ta goya Radhiya don so. Babu ta inda ta rageta ta fanin gyara shiyasa tun a yanzu tayi fice ta wuce raini nesa ba kusa ba. Kakaninsu ba a barsu a baya ba wurin yi musu aike ita da Emzee duk karshen wata. Emzee ma sun so rike shi a Nijar amma fafur yaki shi soja yake son yi abinda bai taba fadawa kowa ba. Cikin dan kankanin lokaci Daddy da taimakon Captain Onomza suka samar masa admission. Ibrahim kuma ya sami Law a Buk itama Ummi ta sake WAEC shekara na zagayowa ta koma makaranta. Gidan Zayyan na Kano Alh Sidi yayi mata gyara na gani na fada ta koma tare da kanwarta daya da kaninta wadanda su ma suke karatu kuma take ta kokarin gyara zumuncin gidansu shiyasa ta taho dasu. Baba Hadir kuma watansu uku suka dawo yana motsa hannuwansa da kafa amma tafiyar bata kankama ba sosai sai yau da Ibrahim ya fadawa Radhiya. *********** "Dad please kaje dani mana" "Ke komai kike so sai anyi miki ne kamar wata yarinya?" Inji mamanta "Kina matsa mata da yawa fa. Meye a ciki don ta raka babanta taron karrama sojoji masu fita (POP)" "Naga official taro ne your excellency " maman tace tana murmushi. "Official baya nufin naki zuwa da 'yata. Arifah ki shirya dake zani Kadunan" Bayan ta fita daga dakin nasa tana dariya mamanta ta sake sako masa zancen rashin aurenta da yake damunta. "Kasanta da jin kai gashi masu yawan zuwa yanzu yawanci duka saboda mukaminka suke son ace sun zama surukan gwamna" "Ki dena damuwa mijinta yana tafe in sha Allah. Ni fa tafiyar nan wani dadi nake ji game da ita na rasa dalili." Murmushi tayi tana tunanin ko don yana kewar harkokinsu na sojoji ne. Gashi a matsayinsa na tsohon soja an gayyace shi bako na musamman a taron POP din sababbin jaruman da kasa zata yaye bana. 💕[11/2, 7:11 AM]: 37. 💕 Sabon salon make murya yayi don ya ga alamun larabawa ne mutanen nan "Assalam alaikum ya 'yan uwa. Kaifal durus wa ayna kaifal amal" Allah Yasa akwai hayaniya a wurin kuma ya make murya ba kowa yaji ba sai Ummi da Radhiya. Kunya kamar Ummi ta nutse Radhiya kuwa juyawa tayi zata bar wurin saboda kunya ga dariya na cin ta. Malamijo ko a kwalarsa ya rinka mika hannu ana gaisawa. Ya sha mamaki ashe Zayyan yana da wannan dangi masu arziki haka amma yaron nan Maikudi ko tsinanne wallahi. Yayi musu tsakani da arziki irin wannan. Magariba har ta kawo kai suka tashi aka rako su waje. Mammee tana kallon Ummi da murmushi tace "ni kuwa ina wani yaro nan lokacin taron sunan Alheran wanda baya son kowa ya tabata. Har yanzu ina da hotonku tare" Ummi ta kalli Awwab tana dariya lokacin ya gane dashi ake ya zubawa Radhiya ido aka rinka dariya da Mammee tana fadin irin rigimar da aka rinka yi dashi da masu son daukar baby. "Ina fata dashi zamu yi bikin ko?" Alh Sidi yace yana riko hannun Radhiya da ta dukar da kai. Malamijo sai dariya "au, au, ashe anata abu bani da labari. Kai abu kyau" Awwab ya kurawa Radhiya idanu fuskarsa dauke da murmushi ko kunya, yadda kowa sai da ya fuskanci akwai wani abu a tsakaninsu. Iyaye sai murna don abin yayi musu dadi. Sun fadawa Ummi zasu shigar da kara akan Maikudi amma sai bayan sunje musu tukunna. Bayan tafiyarsu Radhiya da wasu suka je suna kwashe kwanuka a can gefe kuma Ummi ce ta zaunar dashi da plate din abinci. "Na kula ba ka son cin abinci Awwab. Ko yanayin aikinka ne yasa ka zama haka? Ace mutum da ance abinci sai yace baya jin yunwa" Janyo plate din yayi yana kallon inda Radhiya ta duka tana daukar food flask. Ummi ta kawar da kai tana murmushi har sai da ya gama cin abincin sannan ta nutsu ta fara magana. ''Awwab akwai abinda yake faruwa ne a Katsina?" Da sauri ya dago don da fari wata 'yar kunyarta yake ji. "Me kika ji?" "Ka fada min dai idan akwai abinda ke faruwa wanda ya kamata na sani. Gobe in sha Allah zamu bika mu tafi tare don yadda naji kukan Fauziyya hankalina ya tashi" Wayarsa ta ga yana lalube a aljihu hankalinsa duk a tashe ta mika masa saboda ya manta ya bata dazu da aka kira. Ita kuma bata son boye masa saboda iyaye ba abin wasa bane. Ta yiwu zai iya magance matsalar a matsayinsa na babba. Yana karba ya shiga kiran Fauziyya wayarta tana chaji bata ji ba. "Ummi akwai bayanin da nake son yi miki" A raunane yayi maganar shiyasa kafin ya fara hankalinta ya sake tashi. Bai boye mata komai ba dangane da Ghazalatu da Radhiya da yake son hadasu. "Ita wannan din ce take tayar maka da hankali akan bazata zauna da Ghazalatu din ba ko yaya?" Dukar da kansa yayi nauyin maganar yasa bai iya bude bakinsa yayi mata gaskiyar bayani ba. "A'a Ummi ta amice" Hakura tayi bata matsa masa ba saboda tana ganin akwai abinda bai dace ta matsa sai ta sani ba musamman idan danginsu ya shafa. Fatanta bai wuce kada ya kasance matsala aka samu game da neman Radhiya da yayi ba tunda Fauziyya tace Mummy din taje sunyi fada da Mami. Wannan damuwar ita ce ta karfafa mata gwiwar son zuwa Katsinan a washegari. Daren ranar suka yi waya da Zainab suna airport zasu tashi. Ummi tayi ta jero addu'o'i suna fatan Allah Yasa ayi komai cikin nasara Baba Hadir ya dawo musu da kafafunsa. Washegari kuwa bayan daurin aure Ummi suka shirya tafiya Katsina ba zata sami kai amaren ba. Babu irin tunanin da bata yi ba a matsayin dalilin da zaisa 'yan uwan Mami su zo gidanta suyi fada da ita da ya wuce kin amincewa ace ko auren Ghazalatu ba'ayi ba Daddy ya newa Awwab wani auren shi kuma ya karba. Emzee ne a gaba Radhiya da Ummi a baya. Ba wata hira suke yi sosai ba. Ummi da Awwab tunanin me zasu tarar a can ke damunsu. Radhiya kuma shirun da ta ga yayi tun jiya bai sake nemanta ba shine yasa itama ta kama nata bakin. ********** Sallah Ummi ta idar ta kasa taba komai cikin kayan abincin da aka ajiye mata. Tunda idanunta suka bude sai yau suka hadu. A waya Mami ta nuna tsananin farinciki ta tayata murna amma yau da suka hadu abu na farko da ta fara gani a fuskarta shine damuwa. A haka ma Mami tana ta kokarin boyewa ne. Taji dadin dai ganin Mamin tayi kyau haka ma su Zahra. Sai dai kaifin tunaninta yasa tasha jinin jikinta da wuri. Yaran da iyayensu duka suna tattare da wani abu na rashin jindadi a zukatansu. "Ummin Awwab har yanzu baki tashi kinci abincin ba? Ko na zuba miki da kaina ne?" Mami ta fada lokacin da take shigowa dakin rike da katunan daurin aurensu Zahra da aka aiko daga gidan Alh Baba. "Gajiya ce take tambayata Mami" "Ga kuma wata da zata tarar miki ke kadai tunda Zainab bata nan" Ummi ta mike tsaye tana ninke sallayar "dadin abin Maman Ghazalatu da Anti Hussaina suna nan sai muyi tare" A take yanayin fuskar Mamin ya sauya wanda shi Ummin ke nema don ta tabbatar da cewa lallai akwai wata a kasa. Mami sai ta chanja akalar zancen ta dauko hirar mutanen Nijar. A bangaren 'yan matan ma Radhiya ce kadai a daki. Zayyana tana falo tare da Emzee yana cin abinci tana zuba surutu da labarin shirin biki da take yi. Fauziyya kuma tana can wurin Awwab tana yi masa bayanin abinda taji kuma ta gani a jiya suka rutsa Zahra akan sai ta fadi waye take so tana ta kuka. A hasale yace "shirunki bashi da wani amfani da zai mana" "Kamar yadda fadar ma bata da amfani. Hamma na riga na hakura ba shikenan ba" "Zahra please ki fada mana" Fauziyya tace idanunta suna taruwar kwalla. "Let us help you Zahra" Awwab ya sassauta muryarsa yana kallon kanwar tasa. "Raji ne" tace da muryar da kuka ya sauya ta. "Raji Abdulwahab?" Awwab yace mamaki na bayyana a fuskarsa. Abokinsa ne duk da cewa Raji din ya dan girme masa. A zuwa masallaci sallar juma'a da suka mayar al'adar gidansu a zaman Germany suka hadu da iyalin Ayodeji Abdulwahab mahaifin Raji. Wani abin dadi shine limami a community din da suka hada nasu na musulmai a wurin 'yan kasashe daban daban. Tasu tazo daya da Raji babban dan Limamin wanda yake aiki a kamfanin Benz. Yana yawan zuwa gidansu ashe Zahra yake so babu wanda ya sani. Kai ta gyade ta kuma fashe musu da kuka "nasan babu mai yarda na aure shi saboda bayerabe ne shiyasa na kasa fada da wuri. Daga baya Mami ta sani kuma lokacin tayi alkawarin fadawa Daddy su yiwa Alh Baba magana sai kawai muka ji zancen Fawaz. Wallahi Hamma Raji har kwanciya yayi a asibiti" Kukanta yana taba masa zuciya fiye da zato da tsammani. Shi kam Allah bai dora masa kabilanci ba musamman ga dan uwansa musulmi a duk inda yake. Sai dai a yadda ya fuskanci akidar su Alh Baba son kansu da yasa suka dagewa auren zumunci kadai babbar matsala ce balle kuma ace wani yaren daban. "Daddy yayi miki magana ne jiya bayan Mami ta fada?" "Yayi min da daddare. Baiji dadi ba da bamu fada masa da wuri ba gashi lokaci ya kure. Hamma yaya zanyi? Shekaranjiya da Munirat ta kirani kuka take yi wai bashi da lafiya har yanzu" Tana kuka ne Fauziyya ma na tayata aka bar Awwab da aikin rarrashi. Kamar ance Mami ta leka su ta gansu a wannan yanayi ta kuma ji karshen maganganun nasu. Kwalla ce ta cika mata idanu ta koma batare da ta bari sun ganta ba. Rayuwar 'ya'yanta duka ta shiga wani yanayi. Fauziyya ce kadai take tunanin kila sun hada kai ita da Bilal ta kula ya ma fi Fawaz zuwa dama. Abin dai duka kadaran kadahan babu wani karsashi ko doki a bangaren amaren da angwaye. Wurin Ummi ta koma suna dan taba hirar Zainab taji sallamar babar Fawaz matar cousin dinta saboda ta bangaren namiji suka hadu. A harzuke ta shigo gidan ranta yayi masifar baci ita da Mummy Gambo. Zayyana da take falo da Emzee aka dakawa tsawar ina mahaifiyarta ta ruga daki ta kirawota. Mami na ganinsu tasan ba lafiya ba ta dai daure tana cewa su zauna mana. "Ba zama nazo yi ba Hassana" Haj Azumi tace cikin kaushin murya "ni zaki wulakanta har kike ikirarin 'yarki bata son Fawaz? To wallahi ki jika abarki ki sha indai ni na haife shi ko ana muzuru ana shaho a dangin nan naku Fawaz bazai auri Zahra ba. Ke wallahi bari kiji in fada miki ko aurena ne zai mutu sai dai ayita ta kare" Mami ta daga kai ta kalli Gambo tana mamakin wai kanwarta da suka fito ciki daya ce take ingiza wannan rigima. Ummi bata fito daga daki ba amma tana jin komai. Haka ma su Awwab dake daki ya hana kannensa fitowa saboda a ganinsa hakan bai kamata ba. Radhiya kuwa tsurewa tayi ita kadai a daki tana jin ana wannan daga murya. Ita fadan ba shine ya dameta ba kamar cewa da matar take yi danta bazai auri Adda Zahra ba. Me yayi zafi haka za'a raba masoya? "Haj Azumi ki zauna muyi magana don Allah. Gidan nan da baki ga yara" "Baki? Ke suka dama bakin. Idan 'yan biki ne suka fara zuwa gara su ji su tattara su koma inda suka fito. Aure ne nace a bawa Zahra da ta tashi a kasar waje tafi karfin dana wanda take so. Shi kuwa zan baku mamaki muna nan tare daku mata biyu zan aura masa a rana daya wanda suka fi taki komai da komai" "Gambo kinga abinda kika jawo ko?" Mami tace muryarta na fallasa yadda abin yake mata ciwo. "Sai kiji idan da dadi, ni ba tawa 'yar kike neman hanawa nata farincikin ba. Ko bikinsu ba'ayi ba kunje kun nema masa auren wata saboda tsabar son burgewa ace kuna da zumunci. To amma banda abinki zumunci ya wuce ka fara yi da jininka. Mutanen nan 'yan kauye n....." Wani lafiyayyen mari Mami ta saukewa Mummy Gambo idanunta jajir kamar garwashi. Gidan gabadaya shiru yayi Ummi ta kasa daurewa duk da ta soma hawaye ta fito. Awwab ma fitowar yayi bayan ya gama waya da Daddy ya sanar dashi rigimar da ake yi. "Gambo ki kiyayeni wallahi. Ba tsoronki nake ji ba sannan baki fi karfina ba. Ki fice min daga gida kafin mu kaiga abinda rayuka zasu fi haka baci" "Ni kika mara Hassana saboda wasu can bare da kika hadu dasu rana tsaka?" Mummy tace hawaye na neman zubo mata. Ummi lokacin ta fito zuciyarta ta gama karaya ace saboda ita ko 'ya'yanta ake wannan rigima "Mami don Allah kuyi hakuri" "Au dama kina ciki? Kun lallabo a cigaba da cusa masa 'ya don ya aura" Awwab zaiyi magana aka kira shi. Zuciyarsa har suya take saboda bacin rai amma ya tabbatar idan yayi wani abu na rashin da'a ga matan da suke da matsayin iyaye a gareshi ba karamin fushi Mami zata yi ba ko da kuwa yayi haka ne domin rama mata. Sunan Alh Baba ya gani sai da yasha jinin jikinsa. "Muhammad da kai da kannenka da iyayenka dake cikin gidan nan kuzo gabadaya yanzu ina jiranku" Sai da ya dan rissina ya amsa masa sannan ya fada musu sakonsa. Haj Azumi da Mummy suka fita suna ta masifa. Mami ta kalli Ummi kunyar baiwar Allahn nan ta sa ko idonta ta kasa kallo. Murmushi Ummi tayi ta saki fuska. "In sha Allahu komai zai daidaita" "Kiyi hakuri Mairama ban so kika tarar da wannan rigimar ba" "Haba Mami waye bai san ire iren wadannan matsalolin na dangi ba? Kuje ku dawo Allah Ya kawo mana mafita" Daki Mami ta wuce ta sako hijabi ta fito. Fauziyya da Zahra harda Zayyana su ma kowacce da lullubinta. Ta kalli Zayyana tace mata ta zauna kiran bai shafeta ba. Dama a firgice take saboda haka bata ji komai ba sai murna da aka hanata zuwa. Suna fita Mairama ta dubi Emzee. "Ina yayarka?" "Tana dakinmu Ummi" Zayyana ta bata amsa. "Turo min ita dakin Mami ku zauna a nan ke da Karami." Hawaye ne sharbe a fuskar Radhiya lokacin da ta shiga dakin ta fada jikin Umminta tana kuka sosai. Taji komai kuma ta fahimta. Duk da bata ga fuskokinsu ba amma ta gane akwai maman Ghazalatu kuma bata so ta auri Awwab. Ita kuwa wani irin mugun sonsa ma take ji yanzu bata fatan giftawar abinda zai iya raba su. Bata ki ba ko mata uku za'a aura masa a danginsu indai itama zata sami gurbi a zuciyarsa da gidansa. "Alheran" Faduwar gaba taji saboda bazata iya tuna yaushe ne taji sunanta ya fito daga bakin mahaifiyarta ba. "Na'am" "Kina son Awwab ne?" Da ka ta amsa sababbin hawaye na gudu akan kumatunta. "Meye matsayina a gareki?" Mairama tace babu alamun wasa da ta bari a fuskarta duk kuwa da cewa abinda take niyar yi tamkar ana yankar zuciyarta ne. Iyalin Major Mustapha wani bangare ne na rayuwarsu da bazata taba mantawa da alkhairinsu ba. Daga dawowarsu sai fadi tashi yake a kansu musamman na hadasu da danginsu da yayi. "Babata ce" cewar Radhiya gabanta na sake faduwa. "Daga yau babu ke babu Awwab kina jina?" A gigice Radhiya ta dago kai Ummi ta cigaba da magana nata hawayen na zuba "bani ba ko mahaifinki bana jin akwai mutumin da zaiso bawa aurenki sama da Awwab amma daga ke har shi farincikinku yayi kadan ya haddasa husuma a tsakanin iyaye. Saboda soyayyarku Mami yau ta daga hannu ta mari kanwarta. Zaman da nayi dasu na kwanaki da kuna Kano babu ranar da Mami bazata ce Gambo ba saboda yadda take sonta ta amma yau akanki ta mareta" Jiki na rawa Radhiya tace "Ummi kada ki rabani da Hamma don Allah. Ummi tunda na fada da bakina wallahi kinsan ina son shi....Ummi don Allah" "Kina sha'awar aure a dangin da basa sonki? Ko an fada miki idan kika aure shi daga ke sai shi sai iyayensa? Bazaki yi mu'amala da sauran 'yan uwansa bane?" Shiru tayi babu amsa sai kukan da take yi mai sauti tana gurfane a gaban mahaifiyarta. "Gata nake son yi muku ke dashi. Aurenku a yanzu babu abinda zai kawo sai tashin hankali da rabuwar zumunci. Mu da muka tashi da karancin dangi ai kinga yadda abubuwa suka kasance mana kafin zuwansu Innawuro ko? Kina sha'awar ki mutu a rasa mai kula da 'ya'yanki saboda kiyayyar da ake yi miki ne?" "A'a" "Alheran Daddynku Major da Mami da 'ya'yansu duka suna son mu suna mutuntamu. Sakayyar da zamu yi musu kenan mu rabasu da da nasu 'yan uwan? Kina ganin zaki taba yafewa wata mace ta gida ko bare da zata yi kokarin rabaki da Karami misali? Ki tayani sakawa su Mami da alkhairi na tabbatar miki wallahi Allah bazai bari ki wulakanta ba. Ki taimaka kada ki zama sanadin datse igiyar zumunci ki gani idan Allah bai saka miki da alkhairi ba. Ana barin halal ko don kunya kinji. Kin girma ke ba wannan karamar yarinyar bace da take fita ayi dambe da ita. Kece kike da burin yin abin alkhairi domin a nuna ki ace 'yar Zayyan Tureta ce ga dama ta samu gareki." Babu abinda Ummi ta fada mata wanda ba gaskiya ba. Baza ta taba yarda ta batawa Umminta ba bayan wahalar da tasha akansu kuma ta sani cewa rabuwarsu zata taimaka kwarai wurin daidaita lamura. Tana share hawaye saboda yadda take jin zafin zuciya har dafe kirjinta tayi tace "Ummi to yaya zanyi da son shi?" muryarta can kasa kamar ba Radhiya ba. Tsantsar tausayi da soyayyar 'ya da uwa suka sa Mairama kuka itama. Rabuwa da masoyi akwai ciwo mai radadi. Bata taba mantawa da Zayyan ba haka nan har yanzu zuciyarta bata rabo da tasowar kunci lokaci zuwa lokaci idan ta tuna sun rabu kenan har abada. Soyayya ciwo ce da bata warkewa sai dai hakuri babu abinda ya bari. "Kiyi hakuri a hankali zaki rinka jin sauki a zuciyarki. Da kaina zan fada musu cewa ba kya son auren. Ina ganin ma idan munje Nijar din in barki a can har komai ya lafa" Duka zantukan da suka yi tun shigar Radhiya dakin zuwa yanzu a kunnuwan Umman su Mami ne. Ta taho gidan cikin fushi ne saboda a ganinta Mami ita ke neman raba zumunci tsakanin kannenta. Ko gaisuwar Emzee da Zayyana da suke falon bata amsa ba tace ta nuna mata dakin Mamin batare da ta saurari bayanin da take mata na cewa basa gidan ba. Juyawa tayi ta tafi batare da ta yiwa kowa magana ba. [11/2, 7:11 AM] 🏽 🏽 : 39. 💕 Mami sai da ta waiga baya ta tabbatar su kadai ne sannan ta girgiza kai "kinyi sa'a da yara a gidan nan da na miki dan biki. Zan zo har gida na sameki" Da dariya Mama ta bi bayan Ummi saboda yadda ta tsani gidan nata. Komai warinsa take ji ta rinka amai kenan. Ibrahim abu duk ya dame shi Allah bai sa ya fahimci kani ko kanwarsa ke tafe ba. ********** Kwana biyar da dawowarsu Mami Major ya sami waya daga His Excellency yana shaida masa ya shigo Abuja ko zasu zo shi da Hadir su gaisa. Mami ya fadawa ta rike baki "yanzu Daddy gwamna da kansa yake kiranka?" "Mutumin kirkinsa yayi yawa har ina jin tsoro. Ni bana son shigewa 'yan siyasa" "In sha Allahu alkhairi ya kawo shi garemu. Allah Ya sani bamu cuci kowa ba bazai hadamu da macuci ba" "Shiyasa nake son Hassanata." Dariya tayi tana jindadin yadda mijinta yake yaba mata komai kankantar abu. "Ki sanar da danki ya shirya muje tare" "Yau kuma? Awwab ya ga ta kansa. Umminsa ta saka shi a gaba akan zuwa gidan Gambo sai cewa yake zaije amma har yau shiru. Ni dama abin nasu da Hussaina ya dena bani mamaki. Biki ne zasu yi na huce haushi anki sakani cikin komai ba sai na kawo ido na saka musu ba" "Kece babba fa Hassana, lokaci yana tafiya. Ina ganin ya kamata kiyi yunkuri da kanki kamar yadda Mairama ta baki shawara. Kunje kuna rigimarku ta mata kun bar min yaro yana hanging" "Ya bar kansa dai. Idan yayi sake wani ya nemi Radhiya a Nijar shi ya sani" Daddy ya mike "to ba dama na baki ba ki saka min yaro a gaba." "Na nawa kuma" tace tana murmushi. Washegari da yamma Major, Baba Hadir da Awwab suka tafi gidan gwamnatin Plateau da yake unguwar Asokoro a Abuja. Kofar gida ya fito da kansa ya tarbesu bayan an bude kusu gate sun shigo. Da murmushi a saman fuskarsa yace "wannan me Awwab ko?" Awwab ya rissina kai Excellency ya kamo hannun damansa suka yi musabaha sannan suka shiga ciki. "Nayi zaton zaku taho da iyalinku shiyasa muka taho da Arifah da mamanta. Bari na kirasu ku gaisa" Waya ya kira sai ga matarsa Haj Rabi da Arifah sun fito. Suna shigowa idanun Arifah suka sauka akan Awwab mamaki karara ya bayyana akan fuskarta. Sunfi shekara da haduwa amma ina zata manta shi bayan bata sati biyu bata kira shi a waya ba. "Captain M.A Mustapha?" Tace tana rike baki. Excellency ya saki fuska "kin san shi ne?" Murmushi tayi ta gyada kai tana hango nasara a tattare da soyayyar da take yi masa. Ace gashi har cikin gidansu kuma da ga mutumin da Dad dinta ya daukesu da matukar kima a idanunsa. "Ikon Allah, ashe sun san juna mu sai yanzu Allah Ya nufa" Arifah dai murna kamar me ta fita taje ta sake kwalliya ta tura wata mai aikin ta kira mata shi zuwa garden din gidan. Mai aikin kuwa taje ta isar da sako gashi a gaban mahaifinta dole ya tashi. Shi gabadaya tunaninsa ya kasa tuna wacece ita. Takunsa kadai abin kallo ne a lokacin da yake tahowa gareta cikin shiga ta manyan kaya. Dinkin irin wanda matasa suke yayi ne riga ta dan zarce gwiwa amma hannunta da kadan ya wuce gwiwar hannu. Yadin yayi masa kyau sosai babu hula a kansa sai gyaran fuska da yayi batare da sake aski ba. Tana zaune akan wata kujera karkashin wani abu da akayi da kaba ya bada sassanyar inuwa ya iso ya tsaya bayan tafiyar wadda tayi masa jagora. "Zauna mana" Arifah tace tana murmushi. Kamar bazai zauna ba sai kuma dai ya tuna cewa nan gidansu ne ga kuma irin karamcin mahaifinta ga nasa iyayen. Tunda ya zauna bata ce komai ba sai aikin kallonsa tana yaba komai na halittarsa. "Ya dai?" Ya tambayeta yana hade rai. "Hmmm Captain baka ganeni ba da gaske?" Kalmar Captain din kawai tasa ya tuna a ina ya saba jinta "kece mai kirana?" "Arifah sunana" ta bashi amsa da murmushi "Captain ka wahalar dani ko ince kana kan wahalar dani sai kuma ga ka a gidanmu abinda ban taba zata ba" "Allah Yasa dai bazaki sa a kulleni ba a yar da key din" Dariya tayi "ko daya sai dai ina neman sanin dalilin wannan mugun jan aji da yakamata ace ni nake yi maka" Kai tsaye yace mata "na sha fada miki na kusa aure" "Na dade ina kiranka Captain amma har yau ba'ayi auren ba sai kora da hali da kake yi min." Kunyar abubuwan da ya rinka yi mata yaji da kuma rashin dacewarsu "kiyi hakuri maybe mun fara on the wrong side. Sunana Awwab ke fa?" "Arifah" "Arifah ina da wadda nake so sabani ya shiga tsakaninmu. Kiyi hakuri idan hakan ya bata miki amma iya gaskiyata shine bazan iya hadata da kowa ba" Ya dade yana fada mata shiyasa bata yi wani mamaki ba "she is lucky amma nima zan gwada tawa sa'ar idan ka amince" "Kada muyi haka dake Arifah. Akwai danganta mai girma yanzu tsakaninmu. Mahaifinki ya taimakawa nawa iyayen kamar yadda naji labarin wadda nake so din itama nata mahaifin ya taimaki naki. Mu duka wata alaka ce tsakaninmu da bazan so soyayya ta sake batawa ba kamar yadda tayi min a abaya." "Wai kana nufin Alheran kake so?" "Ya akayi kika gane?" "Saboda ita kadai ce wadda nasan babanta ya yiwa Dad abinda kullum baya gajiya da bada labarinsa yana binsa da addu'a" Awwab da ya koma mai wuyar sha'ani sai gashi saboda hirar Alheran ce ya sake yana yiwa Arifah labarinta. Taji tausayinsu matuka da taji dalilin rabuwarsu. "Na hakura ba don bazan iya ba sai don Alheran din nan da ban taba gani ba nasan tafi karfina indai a kan ka ne. Dad dina da naka duka owe their lives to hers. Ina son Dad dina dole ne in taya shi kyautatawa Alheran da family dinta" "Nagode sosai Arifah" Awwab yace yana mikewa tsaye. "Tunda na zama kanwarka Allah Yasa ka dena kin daukar wayata" Yana tafiya ta jiyo shi yace "daga yanzu da kaina zan rinka kiranki" Kyakkyawar alaka da aka gina bisa gaskiya da amana ita ce ta cigaba da wanzuwa tsakanin gidajen mutanen nan guda hudu. Wato gidan gwamna, Major, Baba Hadir da Mairama matar Tureta. His Excellency Nasiruddeen ya cika alkawari domin kuwa har cikin gida aka je aka dauko masa Maikudi yasa aka kulle shi. Idan mutum yana cin kasa ya kiyayi ta shuri. Radhiya ta mayarda kai sosai a karatunta Nasara tana goya mata baya. Akwai shakuwa mai karfi tsakaninta da Yousuf yana bata kulawa sosai duk domin sharar fagen gabatar da soyayyarsa gareta a gaba. Abubuwa da dama na halayenta rashin Awwab ya sanyata ta barsu sai dai shagwaba kam ko Zayyana albarka. Tazo Nigeria daga Niger ta zaga dangi sosai lokacin Awwab ya koma aiki. A lokacin ne kuma akayi bikin Ghazalatu da Nura. Hadadden gift Awwab ya aiko mata dashi na aure amma bai sami damar zuwa ba saboda training course da ya tafi na shekara daya a Ukraine zai sami karin mukami idan ya dawo. Habaici da bakaken maganganu duk da Mami tana bakin kokarinta akan kannen nata sai da suka rinka yaba mata. Ummansu har tara su tayi ta sanar dasu cewa saboda zumuncinsu kada ya baci Mairama ta raba 'yarta da Awwab gashi har yanzu ya kasa aure. Hussaina sai cewa tayi dama can kwadayi ne ya kawosu da suka ga anfi karfinsu sai suka ja baya. Maganar ta yiwa Mami ciwo amma bahaushe yace wai gani ya kori ji. Idan kuwa hakane to zata basu mamaki su duka wallahi. Bazata ce musu komai game da tsatson da Radhiya ta fito ba sai dai ido ya gani anayi. Duk wannan maganganun anyisu ne ranar Kamun Ghazalatu a Katsina kuma Mama taji saboda cikinta ya fara nauyi tafi son zama wuri daya shiyasa tana dakin suke yi. Da daddare suna dakin Mami a gidansu na Katsina daga ita sai Ummi ta tayar da maganar. "Mairama dan taso muyi magana don Allah" "Allah Yasa lafiya uwar 'yan hudu" "Ba amin ba wallahi wannan addu'a sai 'ya'ya" "Matsoraciya, tunda kika kunso gara kiyi da yawa kawai" Dariya tayi tana fatan Allah Ya kawowa Ummi miji tayi aure itama. "Dama magana ce akan Radhiya da Awwab. Ki taimaka mu fitar da Mami kunyar marasa kunya Mairama. Dazu idan kinji irin kalaman batanci da suke fadawa Mami a gidan da akayi kamu sai kin kusa kuka." Shiru Ummi tayi tana nazari. Itama sun yi da ita batare da sun gane ita bace suka zageta tas akan ta likewa Mami ita da 'ya'yanta. Ai kuwa zata taya Mami nuna musu kurensu ita ce fa Mairo 'yar kunamar Malamijo. "Zainab kisha kuruminki kawai ki zuba min ido wannan karon. Ni har za'a nuna min rashin mutumci ina diyar Ali Gidado? Kawaici ne kawai nake yi domin inganta musu zumunci amma tunda abin ya zama haka idan kinje gida ki fadawa Baba Hadir suyi magana da Major. Awwab na dawowa daga Ukraine a daura musu aure da yarinyar nan" Da karfi Mama ta mike saboda farinciki har sai da cikinta ya amsa amma bata hakura ba ta rungume Ummi. "Wani sha'ani sai bikin 'yar mutan Agadas. Kin biyani ko ba soso da sabulu kin wanke ni da kyau. Su Awwabu za'a shiga sahun manya kice" Ummi ta dafe kai da kunya "wannan zancen ba dani ba" "Wai da mu fara gyara amarya tun yanzu in soma aike" ta fada da shakiyanci ai kuwa tayi nasarar korar Ummi daga dakin tana cewa abu kusan wata goma gaba take wannan tunani tun yanzu. ********** "Is it true you be Aboki?" Inyamurin ya tambayi Zayyan da gurbataccen turancinsa wanda aka fi sani da pidgin english. "Ni bahaushe ne idan abinda kake nufi kenan" ya amsa masa da turanci cikin calm and gentle voice dinsa. Ko a zaman kurkuku Zayyan ya fita daban saboda yadda zuciyarsa take mai kyau Allah Ya sanya masa kwarjini da haiba a cikin mutanen da yake. Inyamurin ya daka tsalle yaga dan kasarsu ya rungume shi. Zayyan bai nuna kyama ga mutumin ba shima ya rike shi. Magana ya koma yi da normal turanci "Sati na biyu a Wing B cikin wahalar mutanen da muke daki daya dasu. Wani Warden (gandiroba) ne jiya yace idan sun sake tabani nace ni dan uwan Zayyan ne." Kallon Zayyan din yayi sosai "kasan me ya bani mamaki?" "Sai ka fada" "Ina ambaton sunanka nace kasarmu daya suka watse. Nayi mamaki matuka gaskiya. Who are you?" Bai cika son yawan magana ba amma kuma baya son wulakanta mutum ba farko da ya gani a wurin da yake matsayin dan uwansa na kasa daya. Takaitaccen tarihin rayuwarsa ya bawa mutumin sai gashi yana hawaye. "Yanzu kai soja ne kuma kayi wadannan shekarun babu wanda ya taba nemanka?" "Nawa kundin qaddarar kenan" "Aboki ni sunana Chibuzor Kalu. Matata ce 'yar kasar nan amma a UK muke da zama. Ta haihu ne tazo ganin gida da baby, to dama munyi da ita ni zanzo daukarsu. Ni dai bansan yaya akayi ba aka kamani da kwayoyi a jakata. Ka ganni nan ko taba bana sha amma anyi mana kudin goro kowa ya ga Igbo man sai yayi masa kallon mai ha'inci. Sun kulleni ne ana can ana binciken ainihin wanda ake zargin ya saka min kwayoyin a cikin kayana" Zayyan ya tausaya masa domin yakan sami labarai akan masu harkar kwayoyi irin tsananin da suke shiga idan an kama su. Shi da yake da saurin sabo sai gashi Chibuzor ya zama tamkar wani dansa. Ko ina tare zaka gansu a cikin prison dinnan har aka gama zaman shari'arsa na tsahon wata bakwai ana fafatawa aka gano sharri ne kawai aka yi masa. Ranar da zai fita yayi kuka har ya gode Allah. Bai san haka shakuwa take da tasiri ba sai da zai rabu da Lt Zayyan Muhammad Tureta. "Sir please ka bani address dinka, a ina zan sami Maman Alheran?" Karo na farko tun bayan shigowarsa wannan kangi Zayyan ya sami kansa da zubar hawaye. Shin yasa rai da zai sake shakar iska freedom ko kuwa? Akwai rabon idanunsa su sake kallon na Mairama masoyiyarsa da Alheran da kuma abinda Allah Ya azurtasu dashi? Rungume Chibuzor yayi yana hawaye ya fada masa sunan barrack din da ya zauna. "Tell them Lieutenant Zayyan Muhammad Tureta is alive" 💕11/2, 7:11 AM] : 38. 💕 Harabar Nigerian Defence Academy (NDA) ciki da waje cike yake da motoci kala kala na dunbin jama'ar da suka zo musamman domin taya 'yan uwansu murnar gama karatu da fita da mukamin second Lieutenant ga mafiya yawansu. Kalilan a ciki irin su Mairama sun zo ne domin karfafawa 'ya'yansu gwiwa. Daga Kano Ummi sun taho da Mama, Baba Hadir, Ibrahim da kanwarta Laila da take tsarar Emzee. Daddy shi kadai ya taho daga Katsina saboda Zayyana ana makarantar kwana kuma satin Mami daya da tafiya Germany wurin Zahra haihuwa ko yau ko gobe. Fauziyya nata dan Amin watansa biyu. Ansan bahaushe da karamci da kawaici bisa ka'ida idan da hali da kuma lafiyar yi Hussaina ko Gambo ya kamata su tafi. Amma kowacce ta shafewa idonta toka har yau ana nan babu wani chanji. Ummansu tayi fadan har ta gaji yanzu maganar Hussaina kadai Mummy Gambo take ji. Bikin Nura da Ghazalatu watanni ya rage don ma an daga saboda korarsa da akayi daga wurin aiki sai da Daddy Haroun ya shiga ya fita ya sama masa wani. Tun a lokacin Mummy ta soma shan jinin jikinta game da auren amma tasan ko tasha giyar wake Alh Baba bazai saurari wata magana akasin wadda suke a kai ba. Ummi tana tsaka da karatu Mama kuma dama dole ke dauketa daga gefen Baba Hadir. Sau daya taje China bayan dawowarsu ta saro kaya masu uban yawa. Da suka kusa karewa sai sako ta bada Ibrahim bashi da isasshen lokaci saboda karatu bare ta barsu tare ta tafi. Yanzu lafiya ta fara wadata gareshi magana ce dai har yanzu suke ta sa rai. Sai kuyi dogon zance dashi yanzu ta hanyar rubutu a takarda ko text a waya. Sai yayi awa guda da Radhiya suna musayar sakonni tace wannan tace wancan duka yana biye mata. Haka Emzee duk wata hira da uba yana yi da Babansa Hadir ne. Sunfi jin nauyin Major kasancewar shine babba. Basu sami ganin Emzee ba yana tare da wadanda zasu yi marching din tare dasu. Sanye suke da kayan sojoji dalibai koraye kowannensu yana jin kansa wani ne saboda samun gurbin karatu a NDA sai anyi sa'a. Shima sai yanzu yake jin da baizo ba da ya cuci kansa. Har tsokanar Radhiya yake yi wai tana missing. Convey din babban bako na musamman gwamnan jihar Plateau Rtd Col. Nasiruddeen Aliyu wanda tun lokacin kamfen jama'ar gari suke kira da Tsohon Soja ta shigo makarantar jiniya ta karade wurin. Watan shida kenan da rantsar dashi a matsayin sabon gwamna bayan zaben da aka gabatar a farkon shekara. Motar da yake ciki tare da Arifah sai da ta kawo shi kusa da inda aka tanada domin zamansa sannan aka bude masa ya fito. Kwarewa a siyasa da kuma tuna baya shima kayansa da suka dace da tsohon mukaminsa ya sanya sababbi fil sai ya fito a sojansa don ma dai ya fara ajiye tumbi. Arifah kuwa wani dankareren lace ta saka yellow da fari anyi mata dinki irin na zamani. Bata sa dankwali ba sai mayafi fari da ta yafa kashka mai matukar kyau da tsada. Komai na jikinta kudi ne tayi kyau sosai abinta. Commandant din NDA din wato shugaban makarantar gabadaya ya taso ya tare shi har mazauninsa. Sai da ya zauna sannan aka shiga gabatar da events din taron. Abubuwan da suke yi sun kayatar da Ummi da Mama, Ibrahim kuwa cewa yake ko dai shima zai taho ne ya kyale BUK. Major da Baba Hadir kowannensu sai ya sami kansa da tuna lokutan baya da suke training tare da Zayyan a Giginya barrack da irin zaman da suka yi har rabuwarsu. Suna ta sauraron jawabai daga manyan baki da kuma ganin abubuwan da sojojin suka tanada domin kawatar da taron Ummi ta kula motsi kadan Mama sai ta dauko wata danyar goba a jakarta ta gutsira ta mayar. Suna hada ido Mama ta kawar da kai gefe tana dariya Ummi ta kusa yin ihu don murna. "Kice Allah abinda nake zargi ne" ta riko hannun Zainab tana binta da kallo ko zata gane wani sauyi a jikinta. "Bansan ki da sa ido ba Ummin Awwab" tace mata tana boye dariyarta. "Harda hanci da baki babu abinda bazan saka miki ba. Taimaka ki fiddani duhu 'yar uwa. Shin da gaske ne?" Doki da murna sun kamata kai kace kananun yara ne. Sai da Mama ta rage sautin muryarta ita kuwa ta kawo kunne ta kara mata "ban yi test ba amma jikina ya bani" Hannunta Ummi ta damke tana murna sosai "yau Mami zata sha story, ahhh su Zainab an girma ashe ba'a girma ba" Dariya tasa daga baya ta shiga nunsta da yatsa "Kinga Mairama ki kiyayeni, wallahi aure zan miki ko don na rama" "Aure sai na 'ya'yanku idan sun shirya amma ni kam mijina yana jirana" Murmushi Mama tayi ta gane wa Ummin take nufi. A hankali hirar ta koma ta Awwab da Radhiya. "Kinci amanar soyayya da kika raba min su. Yaushe zata zo hutu ne in samu in hadasu a gidana. Dama anan aka fara..." "Dandalin soyayya zaki ce, tunda ga babbar shaida na gani" "Ya son ranki hajiyata, ai ko sati baiyi ba da fara motsa jikinsa aka..." Duka Ummi ta kai mata a cinya saboda Ibrahim da ya taso da sauri yayo gaba. Zainab ba dai barin zance ba. Tun zamansu na baya haka take ta fadi magana ta barsu da kunya musamman Ummi. Shi kuwa ashe Emzee ya hango a cikin masu wani irin style din marching abin gwanin sha'awa da burgewa suna wasa da takubba amma na katako anyi musu fentin tutar Nigeria. Abin ya kayatar kuma Emzee shine yake jagorantar wasan nasu. Shi yake bada command sauran suna yin yadda yace. Karshen abinda suka yi shine hada kalar tutar Nigeria wato green white green. Jeruwa suka yi layi biyar kowannen layi mutum bakwai. Ukun da suke tsakiya a kowanne duka hulunansu farare sauran biyun na gefen hagu da dama nasu koraye. Sai suka durkusa a kan gwiwa daidai a haka aka fi ganin ma'anar abinda suka yi. Wurin ya kaure da tafi ga irin kidan band din sojiji ana yi musu suka tashi suna wani murda takobin hannuwansu a kan layi suna shirin barin wurin Ibrahim ya daddage yace "MUHAMMAD ZAYYAN TURETAAAAAA" Mama ta kai masa dundu a baya kuwa "sai kasa yayi mistake ko" "To nayi shiru" "Ka daukarwa Radhiya a waya ko kuwa naka idanun kadai ka bawa abinci?" "Na dauka fa Mama" Kararar kade kaden baisa mutane sunji kiran da ya yiwa Emzee ba amma tabbas idan ba karya kunnuwansa suka ji ba His Excellency yaji kalmar Tureta kamar a iska. Bai sani ba ko yawan tunanin Zayyan da ya fado masa a wurin nan tunda yake ta ganin sojoji ne ya sa shi jin haka. An kira shi domin yin jawabi ya fara da taya daliban da suka gama murna kafin ya nusasshesu kalubalen da yake gabansu. Muryarsa ta karade ko ina saboda spikun da aka saka a wurin gashi harka da masu sanin doka da oda babu hargagi ko hayaniyar da zata hanaka jin me yake cewa. Cikin harshen turanci yake jawabinsa. "Akwai kanina, abokina kuma saviour dina wanda ba don shi ba da bazan kasance tare daku ba yau. Wannan mutumi ban taba gani ko jin labarin mutumin da aka haife shi domin ya zama soja ba sai shi. Officer ne wanda ya san ma'anar sadaukarwa kuma ita ce nake baku shawara da ku runguma hannu bibbiyu. Kunga kowa a cikinmu akwai inda arzikinsa da abincinsa yake. Kamar yadda kanin nawa yake cewa sojoji ba yinsu akeyi ba...haifarsu ake domin domin su bada kariya. Saboda haka duk wanda yake tsaye a cikinku yanzu ina so ya sawa ransa cewa babu kudin da za'a biyaka ya maye gurbin iyalinka da zaka yi nesa dasu idan bukatar hakan ta taso. Babu wata karramawa da za'ayi muku ta fanshe hatsarurruka da zaku iya haduwa dasu domin kare rayukan al'umma. Ku din zababbu ne ku yarda da haka, kuyi aiki da haka ku tsira da mutumci da kimarku a ko ina cikin duniyar nan. KU RIKE KU SANI CEWA SOJA SHINE JARUMIN DA IDAN YA GA AN KAWOWA KASARSA HARI SAI YA DAUKI KOWACCE MACE A MATSAYIN MATARSA , 'YARSA KO BABARSA SANNAN KOWANE NAMIJI BABANSA KO DANSA YAYI KOKARIN CETON SU KAMAR NASA. Wannan shine zai sanya ku jajirce wurin taimako da kariya batare da tunanin bambancin addini, yare ko akida ba. Sadaukarwa irin wannan kuwa sai ga haifaffen soja jarumin kasata." Tunda ya fara magana ya tafi da hankulan da dama daga cikin mutanen dake wurin. Sojojin kuwa ya kara musu wani karsashi da son aikin da suka zaba suna jin babu ranar yin nadama a shirye suke kodayaushe su bada rayuwarsu domin zaman lafiyar kasa. Sowa da tafi aka rinka yi bayan ya gama jawabin nasa ya koma mazauninsa. Arifah da ya gama burgeta tayi masa murmushi "I am proud of you Dad" "Ba dadin baki ba saura anjima inji kin fara rokona wani abu" yace yana dariya. Juyawa yayi ga Commandant din yace masa zai tafi yana so ya wuce Abuja a yau. Gwamnan Kaduna baya kasar a lokacin shiyasa ba'a gayyace shi ba balle yace zai kai masa ziyara tunda garinsa yazo. PA dinsa ne ya kira dreban ya kawo mota inda ya ajiye shi dazu domin su tafi. Sun kusa tashi kenan Commandant ya soma wani bayani da ya dauki hankalin His Excellency ya dan dagawa PA dinsa hannu cewar yana zuwa. "Kamar yadda kuka sani sati biyar da suka wuce an sami gobara a daya daga cikin hostels dinmu sanadiyar konewar socket. Babu wanda yaji ciwo duk masu 'ya'ya a wannan hostel din sun sani. To amma abinda da yawanku baku sani ba shine waye ya yi sanadiyar ceton rayukan mutum sama da hamsin single handedly. Nafi kowa mamakin jarumta da kaifin tunani na wannan yaro da yake shekararsa ta farko a makarantar nan. A lokacin da kowa yake gudun ceton nasa ran wannan Cadet din ya koma ya rinka buga kofofin dakunan wadanda basu sani ba saboda abin ya faru cikin dare ne. Bai tsaya a nan ba duk da kiran da abokansa da malamai keyi yaje inda fire extinguisher take da zafin wuta da hayaki da komai ya cirota ya tsaya a kofar dakin da wutar ta fara ci yana kokarin kashewa yana kuma commanding sauran 'yan uwansa cadets da su bi dakuna su tabbatar kowa ya tashi." Yana kaiwa nan yayi musu alama da hannu "Please lets all stand in honour of Cadet Muhammad Zayyan Tureta" Baba Hadir ne ya fara tashi zumbur da yaji an kira sunan dansa. Ummi kam tamkar ta saka ihu duk da ance sati biyar kenan da yin gobarar. A tunaninta Karami ya dena miskilanci ashe abu irin wannan zai faru ya boye mata? Bata san lokacin da ta soma hawaye ba. Major bai tuna kowa ba sai nasa Zayyan din. Karin maganar bahaushe ya tuna da ake cewa barewa batayi gudu danta yayi rarrafe ba. Duka duka Emzee shekarunsa da yasan ya koma ceton rayuwar wasu. His Excellency Rtd Col. Nasiruddeen Aliyu ji yayi tamkar an saukar masa da guduma a tsakar kansa. Kunnuwansa sun jiye masa da kyau kuwa? Ya san nasa Zayyan Muhammad Tureta din yau kuma yaji ana kiran Muhammad Zayyan Tureta. Me yake shirin faruwa ne? Bai karasa tsinkewa da lamarin ba sai da kyakkyawan matashin mai dauke da fuskar da ko yasha giyar wake baya jin zai taba manta ta ya taso cikin shigarsu da dalibai wato cadets da hularsa a karkace yayi matukar kyau ya hawo kan stage din inda Minister of defence zai bashi kyautar Cadet of the Year. Emzee kenan, yasan da award din shiyasa ya matsawa Umminsa dasu Daddy akan su zo domin yayi surprising dinsu. Excellency fa sai yaji tsayuwa tana neman gagararsa ya lalubi kujera ya zauna kansa ya daure gabadaya. Masu hoto suka yi caaa akansu lokacin da Minister yake baiwa Emzee award din. Da murmushi a fuskarsa ya rinka baza idanu har Allah Ya bashi ikon hango iyayensa. Daga kambun da aka bashi yayi ya nuna shi saitin inda suke yana kara fadada murmushinsa. Sosai ya burge Minister ya dafa kafadarsa suna tsaye a gaban loudspeaker yace "Cadet baka da abin cewa?" Wadanda suke kusa zasu iya ganin kunyar da ta bayyana a fuskar Emzee. Duk da haka ya dan saita bakinsa a jikin speaker din yayi godiya ga Commandant dinsu, dukan mutanen academy din sannan ya kare da cewa "I dedicate this award to my late father LT. ZAYYAN MUHAMMAD TURETA" Ummi kuka Mama kuka suka rungume juna. Kukan farinciki, famin ciwo da kuma tsantsar godiya ga Allah akan kowane yanayi take yi. Emzee zai sauka daga wurin har lokacin baiyi nisa da speaker din ba ga mamakin dumbin jama'ar da suke wurin yaji hannu ya sauka a kafadarsa an damke shi. Da sauri ya juyo ya ga mutumin da aka kira da gwamnan Plateau ne sai yaji ya firgita. Idanun Excellency sunya ja sosai hankalinsa tamkar baya jikinsa yace "sunan mahaifinka Zayyan Muhammad Tureta?" Emzee ya gyada kai a dan tsorace. Ummi tashi tayi daga seat dinta tana jin me yake fada tana kuma tsoron ko dan nata yayi laifi ne. Kwalla ce Emzee ya tabbata ya gani a idanun Gwamnan sai kawai ya rungume shi a bainar jama'a. Commandant din yana ganin haka ya kira wasu da zasu jagoranci taron shi kuma ya duka kadan yadda Excellency din zai ji yace "kana bukatar kebewa tare da yaron ne" "Kwarai kuwa dan kanina ne, zaku iya bashi pass na kwana daya? Shekaru sama da shabiyar nayi zaton sun mutu" Sai da Commandant din ya girgiza da jin wannan magana daga bakin Gwamnan yace su tafi. Emzee yaji mamaki matuka da furucin mutumin nan. Yana rike da hannunsa motocin suka yo gaba aka fara sakin jiniya suka sauka Arifah tana take musu baya itama mamaki ya kamata. Da sunan Zayyan Tureta a bakin mahaifinta ta girma yau ace ga dansa bayan Dad din da kansa yace mata iyalinsa sun mutu. Kafin su shiga motar Ummi tayi gaba hankalinta a tashi Gwamnan garin da ba nasu ba kuma basu da mahadi dashi yayi mata gaba da danta. Major da Baba Hadir suka nufo stage din aka nemi hanasu hawa. Daga murya yayi yace "danmu ne aka tafi dashi kuyi mana bayani." Commandant sai ya zaro waya ya nemi PA din gwamna ya sanar dashi ga iyayen yaron fa. "Fada musu guest house din da zamu je. Ina bukatar magana dasu privately." Ibrahim ke jan mota daya dreban Daddy yana jan dayar suka bi bayan motocin. Dakatawa ma akayi suka shiga tsakiyar convoy din sannan suka wuce cikin garin Kaduna. Wata unguwa da ta yi nesa kadan da hayaniya ga maka makan gidaje suka je. Emzee ya dena tsoro sai mamakin yadda tunda suka shiga motar Gwamnan yake rike da hannuwansa yana kallonsa yana murmushi ya kasa cewa komai. Abin ne da matukar mamaki da daure kai. Dan Zayyan dinsa ne yake gani a gabansa. Sun shiga harabar gidan aka fito daga motoci. Excellency yana rike da Emzee su Ummi suka firfito daga mota yana jiransu. Kan kace meye wannan an bude gidan da ya wadatu da kayan alatu. Arifah da PA dinsa ne kadai suka bisu cikin wani wawakeken falo. PA din yace su zauna amma duka hankulansu basu kwanta ba sai da gwamnan da kansa yace su zauna. Tambayar farko da ya fara watso musu ita ce "ina Alheran?" Idanu ya ga sun dora masa kawai yayi dariya sosai ko ya tsorata su ne? Farinciki ne ya cika masa ciki da zuciya tamkar kirjinsa zai fashe. "Bari na faro muku daga farko dai. Sunana Nasiruddeen Aliyu....." bai dire labarin ba sai da ya kai zuwa lokacin da aka harbe Zayyan yana rike da hannunsa bayan ya sauko ya taimaka masa "duk abinda na zama a rayuwa wallahi Zayyan ne sila, ina kuka shiga aka ce min kun mutu? Ina matar Zayyan da yace min yana kiranta Fillo, ina 'yarsa Alheran Radhiya...kada kuyi mamaki ban taba manta Zayyan ba. Da Allah Ya sake bani haihuwa babu makawa idan namiji ne sunan da zai amsa kenan" yace idanunsa na fitar da kwalla. Wani irin kuka Ummi take yi wanda duk mai sauraronsa zai tausaya mata matuka. Kirjinta kawai ta dafe tana jin wannan sabon al'amari. Emzee bai san komai akan mahaifinsa ba sai hoto sai labari amma ya tayata kukan saboda girman abinda suka ji. Daddy da Baba Hadir sai suka ji abin kamar almara. Daddy ya kada baki yace "kana nufin kace min Zayyan bomb bai tashi dashi ba?" Excellency yayi ajiyar zuciya ya sake yi musu bayanin ainihin abinda ya faru na binne landmine din karya da 'yan tawayen suke yi "tabbas bomb ya tashi domin har zuwa lokacin rasuwarsa Zayyan yana ta fargabar bomb din ya shafi 'yan uwansa Hadir da Major Mustapha ko kuwa Allah Yasa sun tsira. Kamar yadda na fada muku ni da Zayyan munyi wata irin rayuwa ne da bamu da sirri ga junanmu. Zayyan was my last patient daga kansa ban sake iya duba wani mara lafiya ba." Hawaye ya gani sharkaf a fuskar wanda tun zuwansu baiyi magana ba. Mai yin maganar kuma wato Daddy sai sunkuyar da kai yayi ashe shima hawaye yake digarwa. Kaddara ta riga fata. Ashe da rabon Zayyan zai sake ceton rayuwar wani shiyasa suka yi masa zaton mutuwa. Yau gashi mutumin ya zama gwamna bayan yayi dan majalisa da sanata. "Kunyi shiru ina Fillo na manta ainihin sunanta" Mama ce tayi karfin halin nuna masa Ummi wadda kuka ya hanata katabus. Abin ya taba Excellency sosai ya sake cewa ina Alheran ita yake son gani. "Tana karatu a France" Ibrahim yayi karfin halin bashi amsa. Murmushi ya sake "Alhamdulillahi rayuwarku bata lalace ba kamar yadda Zayyan yayi ta jin tsoro. Ko sati banyi da dawowa ba naje har gidan iyayensa wani da yace min shi yayansa ne yace matarsa ta haifi da babu rai kuma sunyi hatsari sun rasu ita da Alheran" Gyaran murya Major yayi da kyar ya iya tattaro kuzarin cewa "nine Major Mustapha, wannan kuma shine Hadir" Tashi yayi yazo inda suke ya tsaya "daya daga cikinku kafarsa ta fita a ambush din Liberia?" Kafar damansa Major ya taba yana kwankwasata "katako ce" Hannunsa Excellency ya kama ya damke sosai "nice to meet you Major" sannan ya koma ga Hadir "dan uwan Zayyan baka ce komai ba" "Maganarsa ta dauke tun ranar da abin ya faru....." Major bai dire ba shima sai da ya bashi labarin tashin hankalin da suka fuskanta da rayuwar da suka yi su duka har tasu Mairama. Yau din sai ta zama wata rana ta tuna baya da kuka a garesu. Sannan kuma rana mafi farinciki ga His Excellency Nasiruddeen na haduwa da mutanen da baisa rai dasu ba. Sai dai wani tunani da ya darsu a zuciyarsa ya sanya shi dagowa kana iya ganin fushi mai girma a idanunsa. "Who the hell is Maikudi? "Yayan Zayyan ne amma ba uwa daya ba. Ina tunanin kaina dashi kuka hadu" "Sai yayi nadamar kallon tsabar idanuna yayi min karya. Na dawo da hope na daukar nauyin komai na rayuwarsu mutumin nan yace min sun rasu" yace cikin bacin rai da jin inama dai yayi ido hudu da Maikudi yanzu. "Your Excellency mun riga mu sa an kama shi. Gidan magada an karbe sannan wanda ya gina da kudin da na turo da kudin hayar gidan shima yanzu haka mun saka a kasuwa saidawa za'ayi. Family dinsu na Nijar sun shigar da kara sai da yayi wata shida a rufe sannan yana kan biya tara" Major ya sanar dashi. "Ahaf, wannan tsakaninku ne ai. Kowa kawai ya dauki tasa fansar shine zan fi fahimta." Baba Hadir sai da yayi dariya mai dan sauti yana ganin yadda mutumin nan ya dace da 'yan uwantaka da Zayyan saboda yanayin halinsa. Murmushi shima yayi yana kallonsa "na baka dariya ko? Seriously ni yanzu ko Zayyan ne da kansa bai isa ya hanani kulle Maikudin nan ba so please a bar maganar. Zan sa a kira CP har gida za'a je a dauko min shi. Gobe idan an nuna masa maraya ba kudin maraya ba ma ko kallonsa bazai yi ba" Ummi ma dai murmushi tayi tana jindadin ace hali nagarin da Zayyan ya nunawa wadannan bayin Allah shine yasa su tsayawa domin kula dasu. Addu'a take ta yi masa a zuciyarta na fatan dacewa da Rahamar Allah. Hira sosai Excellency ya rinka jansu da ita yana cewa su saki jikinsu shi dasu zumunta ce mai karfi da Zayyan ya hada. Abinci aka rinka shigo dashi kala kala na alfarma yace kowa ya ci abinda yake so. Idan babu ra'ayinka ma ka fada a nemo. "Arifah ga uwayenki ki kaisu wancan falon nasan zasu fi sakewa" "Okay Dad" ta mike tsaye da fara'arta. Dauko musu abinci wani cikin guards din baban nata yayi aka kai musu inda yace. Kamar mahaifinta sai gata ta saki jiki dasu tana hira da tambayarsu sunayen yaransu mata su zama kawayenta. Bayan sun gama ci a bangaren mazan Excellency ya nemi jin ko suna aiki. Major dama Daddy Haroun ne yake nema masa, to rabuwar yaransu ya sa yaji kunyar sake tuntubarsa. Shi kuma rashin samun wani abin kirki yasa baiyi masa magana ba. "Major me zai hana in nema maka aiki a NITDA (national information technology development agency) tunda software engineer ne kai. Hadir kaima fa dole ne ka fita. Tunda jikinka yana motsi sai a nemi aikin da ba sai kayi magana ba. Rashin shiga mutane ma lalura ce mai zaman kanta " "Your Excellency kada ka dorawa kanka nauyi daga haduwarmu yau don Allah" cewar Major. "Wane irin nauyi? Bari na fada maka abinda baka sani ba. Ka ganni nan, ko da nayi retire amma har yanzu zuciyar tana tare da Army. Soja shine yasan soja. Mune muka san fadi tashin juna saboda haka dani daku bamu da zabin da ya wuce rungumar juna a matsayin 'yan uwa. Ko kuna ganin haduwar tamu anyita ne aci abinci a tashi ana shafa tumbi?" Dariya yake yana maganar suma dole suka dara. Wannan mutum da saukin kai yake tamkar ba gwamna ba. Sai bayan la'asar suka kama hanyar komawa bayan yace zai sanar dasu ranar da zasu taho duka da iyalansu. "Sannan a bawa Alheran numberta zan kirata da kaina ku tabbatar dai an fada mata matsayina gareta. Tana samun hutu a turo min ita don Allah." Mota guda ya bayar aka mayar da Emzee makaranta bayan ya jikasu dukkansu da kyautar kudin da bai san adadinsu ba. ********** Radhiya tasha bayani kala kala daga wurin dukkaninsu. Ranar itama kusan kwana tayi kuka tana tausayawa Umminta don sai da Nasara taji babu dadi an sa mata 'ya kuka. Kwanaki kadan bayan haduwarsu sai ga offer din aiki har gida ga Major da Hadir. Kasar wa ka sani wa ya sanka kenan. Ba tare da bata lokaci ba an gama duk wani abu da ya kamata cikin sati guda. Major sai yayi wani course na wata uku a nan cikin sabuwar ma-aikatar tasu. Shi kuma Hadir an samar masa aiki mai sauki a Ministry of defence. Abu na karshe da yayi musu shine kama musu wasu gidaje flat a estate daya kusa da juna guda uku harda na Ummi wai idan tayi hutu ta taho ba sai ta takurawa kowa ba. Sai suka rasa da me zasu kwatanta karamcin wannan mutumi. A nasa bangaren kuwa yana musu kallon sun cancanci fiye da haka. Shine ya zauna da Zayyan a karshen rayuwarsa, shine suka ga kisa da mugunta tare zahiri suna kwantarwa juna hankali. Saboda haka nauyin iyalin Zayyan a wuyansa yafi cancanta. Daddy sunyi waya da Mami yana yi mata bayanin komai sai hamdala take tana jin kamar ta taho. Dama kuma Ummi bata iya shiru ba Mama tana yin pt ta tabbatar ciki gareta ta kirata ta fada mata. Kwanaki hudu a tsakani Zahra ta sunkuto jaririnta kyakkyawa tubarakallah. Mami sai dada godewa Allah take da aka amincewa aurenta da Raji. Dan zaman da tayi dasu ta kara sakankancewa ba karamin so yake yiwa diyarta ba. Da yake kuma ba bahaushe bane babu ruwansa a gaban kowa matarsa ce tauraruwarsa. Kullum Zahra tana cikin annashuwa babu ta inda mijinta ya rageta. Ranar da jariri ya cika kwana bakwai aka saka masa suna Olufemi Abubakar Assiddiq amma suna kiransa Femi. Maman Raji kusan ita take komai na gyara da kula da maijego shiyasa suna cika sati uku lokacin Mami ta wuce wata a garin tace ita dai gida zata dawo. "Mami bazaki jira nayi arba'in mu tafi tare ba?" "Lada ya isa haka nima a barni na tafi wurin mijina" "Laaaaaa Mami" Zahra tace tana dariya. "An fada miki ku kadai kuka san kula da miji, ki fadawa Raji ya dawo min da booking dina jibi Allah guduwa zanyi sai kun taho" Mami fa da gaske ta tubure dole aka fara shirin komawarta. Shatara ta arziki Raji ya hada mata da alkawarin suna hanya da zarar Femi ya cika wata uku. Da Awwab yaji labari da kyar ya samu ta kara kwana hudu akan yadda tayi niyya don su koma tare. Ba karamin kewar gida yayi ba duk da shi ya zabi rashin son komawa lokuta da dama. A ganinsa kawai an hade masa kai an biyewa su Mummy anki aura masa Alheran. Har lokacin kuma yaki saukowa daga fushin da yayi da tace bata son aurensa. Ko yaya ya tuna sai yaji bacin rai. Awwab mai sakin fuska da yawan wasa yanzu ya zama a lallaba. Ba wai fada yake yi ba, shiga sabgar mutane ce gabadaya ya ja baya da ita. Ya rasa walwalarsa daga ranar da Alheran tace bata son aurensa. Siyayya sosai ya yiwa Femi kamar yadda ya yiwa Jawad dan Fauziyya. Munirat kanwar Raji ce ta kawo masa yaron Mami da Zahra suna zaune dashi an kawo masa abinci. Ya kara kyau da jiki ga wani gashin baki da gemu da ya hada ya zagaye kyakkawar fuskarsa sai gyara da ya sha an rage shi sosai ya kwanta a fatar fuskar ya sake fiddo kyaunsa. Rike yaron yayi yana jin inama nasa ne da Alheran...tsaki ya yi batare da ya sani ba da sunanta ya fado masa. "Lafiyarka kuwa?" "Mami gajiya ce kawai. Zahra ki barmin shi kawai ki haifi wani" yace yana shafa kwantacciyar sumar kan yaron gwanin sha'awa. "Ba dai ka tsaya tuzuranci kake jira ya cimmaka ba. Allah Ya bada sa'a. Idan rabon ayi aurenku tare da 'ya'yan naka ne mu ai bamu da ta cewa" Mami ta fada tana kawar da kai. Wai shi zuciya sai tayi masa maganar Radhiya yace ai sune suka bata izinin tafiya shi bazai bita ba. Mami takan ce masa maji ma gani idan rabon ka ga katin auren Radhiya ne ba shikenan ba. Duk lokacin da tace haka a zuciyarsa sai yace ba amin ba. 'Yar halak sai ta zabi daidai wannan lokacin ta kira Zahra. Har wani dan murmushi Zahran tayi tana dauka ta saka wayar a speaker ta karbi Femi da yake kuka za ta shayar dashi. Mami ta tashi ta koma cigaba da hada kayanta. Awwab bai san me tayi ba kawai sai jin zazzakar muryar Radhiya yayi "Adda please please ki saka min naji muryar babyna" Zahra tana kallon yadda ya dauke wuta ko motsi ya kasa yi. Wani irin yanayi na shauki ya bakunce shi. Shekara guda da watanni rabon da ya sanyata a idanunsa ko yaji muryarta. "Adda kina jina?" Tace tana karyar da murya. "Ina jinki Radhiya...fushi muke ni da Femi yau kwana uku baki kiramu ba" "Exams....gidan ma bana zama sosai fa. Yanzu dai ki dan zungure shi kadan yayi kuka naji" Duk abin Awwab sai da yayi murmushi suna hada ido da Zahra ya cigaba da tsakurar abincin dake gabansa. Tana nan da halinta wato. "Dan nawa zan zungura Radhiya? To ko dai balotellin kike so nayi miki? Ina da sabon scisssors mai kaifi" Dariya tayi da tasa tsigar jikin Awwab tashi saboda yadda yaji muryarta har tsakar kansa. Dannewa yake kada Zahra ta sami damar tsokanar shi tace tayi galaba a kansa. "To ni shikenan bazan ji muryarsa ba" ta fada cikin shagwaba. Idanunta akan Awwab tana ganin wani annuri da yake bayyana gareshi a hankali tace "zan ga ranar da zaki girma. Anyway yaushe zaki je Nigeria?" "Saura na exams biyu amma Yousuf yace na jira mu tafi tare nan da kamar two weeks I think. Zamu fara zuwa Agadez ne sannan mu taho" "Yousuf dinnan yana ji dake" Zahra tace tana dage gira daya tare da kawar da kai daga kallon Awwab da ya tattaro hankalinsa garesu batare da niyya ba. "Kawai yana da kirki ne. Kiyi min addu'ar exams" "Allah Ya bada sa'a, ni dai ki tabbata kinzo lokacin da zani" Muryar namiji Awwab yaji yana kiranta da Alheran ya tashi a fusace ya bar falon. Meyasa shi bazai kirata Radhiya ba kamar yadda kowa yake fada. Da takaicin wannan abu ya kwana. Washegari jirgin dare suka bi zuwa Abuja. A hanya ya rasa yadda zaiyi ya tambayi Mami waye Yousuf kada tace har yanzu ya damu da Radhiya. Shi ba damuwa da ita yayi ba kawai dai curiosity ne. Dreban Daddy da Ibrahim ne suka je daukarsu. Mummy ta kasa boye murnarta da suka shiga estate din. Wai sune a gida irin wannan mai kyau kuma Major ya sami aiki. Awwab ma yayi murna sosai ya kuma yaba da unguwar da iyayen nasa suke. Nata gidan da sauran gyara na kayayyakin da zasu saka saboda bata nan. Abubuwa kadan ta iya fadawa Daddy a dauko mata daga Katsina. Sauran kuwa sai tazo da kanta. Daddy yana gidan Baba Hadir saboda Mama da Ummi sun hadu a gidan Mami suna girki. Suna shiga Awwab yayi ido hudu da Ummin da yake yiwa wasan buya. "Allah Ya kamaka Awwab babu alkawari...oh ni Mairama 'yan sa ido sai su zuba ruwa a kasa su sha sunyi nasarar shiga tsakanina da dana" Mama sai dariya "wai 'yan sa ido, kaga Awwab gara ka kamani don Ummi da Mami 'yan hamayya club ne" Shi dai kunya ma suke bashi ya gaishe su duka yana neman wurin zama Ibrahim ya nuna masa dakin da aka tanadar masa don zaman hotel ya kare masa a garin tunda babu fuskar zuwa gidan Mummy. "Kunga yadda Awwab ya sake zama babban mutum kuwa? Ni dai gaskiya ayi masa aure haka nan" cewar Mama "To ya hau dokin zuciya yana ta fushi damu akan tafiyar Radhiya" Mama ta bata amsa. "Shashanci kai, yana nan wallahi buzayen can zasu fara kawo mata hari. Wami hotonta da ta turo min fa Allah nayi mamakinta sosai. Ki turo min shi Mami idan kun huta ya kamata na karanta masa fari da baki" Ummi tace "gidana zai fara zuwa akwai tamu dashi, duk abinsa sai yaje gidansu Ghazalatu ya gaishe da iyayensa wannan karon" Mami ta ce "ni dai a nuna min nawa dakin naje nayi wanka yunwa nake ji" "Ummi inkiya akeyi mana mu fita fa...kinga ni nayi nan kafin ki fara jin gyaran murya Daddy ya zo oyoyo" "Innalillahi wa inna ilaihi rajiun, Zainab baki da dama wallahi. Amma zan fada masa tunda sharrin naki harda shi" "Rufa min asiri don Allah" sai da ta kusa kai bakin kofa ta juyo "yo ai dai gaskiya na fada idan kin musa mu dawo mu tayaki wuni" "Allah Ya shiryeki kina nan kina zance sai ya shigo" Ummi tace ta rigata fita. Dawowa da baya Mama tayi tana nunawa Mami fridge "nayi miki ajiya fa ya kamata ki fara dubawa ki sha..." 💕[11/2, 7:11 AM] 40.💕 "Alheran ZM Tureta Gajeren faduwar gaba taji lokacin da daya daga cikin malamansu kuma supervisor dinta ta leko da kanta ta kofar seminar hall din ta kira ta. Duka daliban da suke aji daya tare su kadai suke zaune banda ita. Nasara tana zaune a kusa da ita cikin kujerun da aka zube a korido din domin zama ko hutawa tana karfafa mata gwiwa. "Tante" Radhiya tace kamar tayi kuka. "Ina nan ina jiranki kinji ko...jeki" Nasara tace da murmushi. Kungiyar ma'aikatan jarida na kasar France ne suka rarraba kudade a fitattun jami'o'insu suna neman zaratan dalibai. Gasa ce suka saka na neman zakaran gwajin dafi inda aka baiwa daliban damar kowa ya kawo wata matsala da yake tunanin zaiyi kyau a bude program a kanta imma ta gidan TV ko rediyo domin wayarwa al'umma kai da kuma taimakawa ga wadanda abin ya shafa. Dalibai uku ake son zaba a kowacce jami'a 'yan aji uku ko hudu za'a basu grant (tallafi na kudi) suje suyi aikin da suka kawo na wata shida su dawo makarantar dashi. Wandanda suka yi nasara kofa ce babba zata bude musu ta arzikin samar da program da kila duniya duka sai tasan da zamansu. Radhiya ta kusa wata tana ta bincike akan topic din da ya kamata tayi karshe ta tsaya akan abu guda bayan tayi magana da Ummi da Baba Hadir. Su kadai suka sani sai Nasara. Jiya ko runtsawa ta kasa yi ta gama hada slides na power point da zata yi presenting sannan ta dukufa sallah da addu'a. Yousuf shine babban malaminta na addini bayan ta dawo kasar. Bakin gwargwado tana da nata ilimin tun a gida don kafin su gama secondary ita da Emzee sunyi sauka. To amma ilimi na sauran fannonin addini Yousuf yayi fice wurin zaburar da ita a kansa shiyasa matsayi daban ta bashi. Tana girmama shi sosai idan suna tare sai ka rantse wata muguwar nutsattsiya ce babu rigimar nan. Sai da ta gama addu'ar Annabi Yunus da salatin Annabi SAW sannan ta kalli zoben hannunta mai harafin A, aa hankali ta kaishi bakinta ta sumbata. Computer dinta ta bude aka jona ta projector wakilan kamfanin Dupont Broadcast Corporation (DBC) da malaman jami'ar da suke musu alkalanci suka fuskanceta. Bakar abaya ta saka mai kyau da karancin ado irin wadda wuyata zagaye ne kawai bai sauka kasa ba. Adon duwatsunta maroon ne shiyasa tayi nadi da maroon din mayafi tana sanye da loafers suma maroon da suka zame mata yawancin takalman zuwa makaranta. Hall din an kashe duka fitilu babu sauran haske sai wanda yake fita daga makeken screen din projector din. Bata ce musu komai ba sai wani gajeren video na sakan goma sha biyar da ta kunna musu. Filin yaki ne baka jin komai sai tashin bomabomai da harbi gami da ihun mutane da kukan yara. Wuri ne na firgici da tsoratarwa ga wanda bai san yaya mutanen da suke da 'yan uwa a wuraren da rikici ke ballewa suke ji ba. A tsakiyar wannan tashin hankali sojoji ne wani ya kwanta akan yara biyu ya toshe musu kunne saboda karar bomb. Wani ya dauko wata mata mai tsohon ciki yana gudu da ita ga jini ya wanke masa fuska alamun shima yaji rauni. Wani likita ne a cikin sojojin ya duka gaban dan uwansa soja da hannunsa ya fita saboda tashin bomb. Kai jama'a mutane ne a cikin tsanani basu san ina suka dosa ba. Duka mutanen da suke wurin tuni Radhiya ta kwashe hankulansu da tunaninsu ya dawo ga abinda zata gabatar. Hoton karshe ya tsaya ne akan wadannan sojoji kowa da abinda yake yi na ceton al'ummar da babu lallai ma na kasarsa ne ta dora musu katon question mark (alamar tambaya). Cikin turancinta da sautin muryarta zai baiwa mai sauraro damar gane cewa faransanci ya zaunu a bakinta tace. "Who are they?" Alkalai basu san me zata gabatar ba amma sun fara gyada kai in approval. Murmushi tayi da ya kawata fuskarta ta dora da cewa "My name is Alheran and this. Is. The Military Voice" Hotunan screen din sai suka sauya inda zaka ga wani sojan rungume tsakanin iyayensa, wani da 'ya'yansa, wani amaryarsa, wani matarsa da tsohon ciki wani kanne da yayyensa suna dariya, suna murmushi ko suna hawaye. "Tun farkon lokaci yana daga abinda yake daga darajar kasashe yawan rundunar sojoji ko mayakansu. Sai dai mukan manta da cewa wadannan sojoji 'ya'ya ne, maza, iyaye kuma 'yan uwa ga wasu. Suna tafiya filin daga a lokutan da iyalansu suke tsananin bukatarsu. Sauran mutane suna zuwa wurin aiki su koma gida soja idan ya fita filin daga shi da jindadi sai ranar da yayi sa'ar komawa ga iyalansa lami lafiya. Cikinsu ko kunsan mutum nawa ne suka tafi iyalansu suna kuka suma suna na zuci amma basu dawo ba?" Hotunan suka karkata ga iyalan sojoji suna kuka, wani wurin kuma gawarwarkin sojoji ne, wasu kuwa sojojin ne da nakasar rasa wasu bangarori na jikinsu. "Kama daga KIA (killed in action), MIA (missing in action), dawowa gida da nakasa ta gabobi ko lalurar da take shafar kwakwalwa wadannan sojoji suna wahala matuka a duniya. Amma duk wanda ya dawo da wata tawaya ta jikinsa sai ya zama mutum mara amfani ga al'ummarsa. Babu abinda suka sani ko suka iya sai tsaro amma tunda basu da lafiyar yinsa shikenan amfaninsu ya kare. A haka rayuwar sojoji nawa muka manta saboda babu abinda zamu mora a tare dasu. Idan sun mutu iyalansu kadai ke da asara. Wasu sai dai su koma garuruwansu babu abokai, wasu matansu sun kasa zama dasu, yaransu kila sun girma sai dai su kare rayuwarsu cikin kadaici da jin kawunansu tamkar basu da wani sauran amfani" Hotunan da suke ta tafiya akan screen din masu ban tausayi ne da taba zukata. Wani ka ganshi a gidan giya, wani fuska da jiki bab u gyara, wani ya zama manomi a kyauye, wani yana nan banda tuna lokutansa a filin yaki ko azabar da yasha a hannun abokan gaba babu abinda yake yi. Wasu ma karamin hauka suke dawowa dashi duka a dalilin bautawa kasarsu. "Da wannan nake rokon ku bani dama in zaga in fito da rayuwar sojojin nan duniya ta sansu ta kuma san cewa ko yaya suka dawo duk abinda ya samesu ya faru ne a kokarinsu na kare dukiya da rayukan al'umma. Ina so sojoji da iyalan da suka bari duniya ta kasa dubansu su sani cewa har yau har gobe suna daga cikin mutane mafiya girman daraja a bainar al'umma saboda sadaukarwasu garemu. Nagode" Fitilun hall din aka kunna gabadaya mutanen wurin suka mike tsaye ana tafawa Radhiya. Cikin matan kuwa harda masu zubar da hawaye saboda tausayi daga hotuna da video din da ta nuna musu. Sallamarta akayi akace ta jira tare da sauran da suka gabatar da nasu. Sai bayan kusan awa guda an gama sauraron kowa aka kirasu domin jin sakamako. Tante Nasara tana nan a korido din ta kasa zaune ta kasa tsaye motsi kadan sai ta kira Ummi tace wallahi ta saka mata 'ya a addu'a. Ummi sai dai tayi dariya tace ai tana yi. "Tanteeeee" taji muryar Radhiya kafin ta farga daga ina ne taji ta rungumeta tana murna. "Nayi ta daya Tante, zanyi Military Voice a Nigeria da Nijar" Nasara ta rungume Radhiya tana ta murna. Ita take tuka su zuwa gida yayin da Radhiya take ta waya da mutanen gida. Ummi, Mama da Baba, Daddy da Mami, Mammee dasu Alh Sidi. Ibrahim da Emzee babu wanda bata kira ba tana sanar dasu cewa su fara shiri tana nan tahowa Nigeria nan da sati daya. *********** Sai kai kawo Ummi da Mami suke yi a hanyar dakin theatre din da aka shiga da Mama. Ciki ya wuce kwanakin da ake sa ran haihuwarsa harda sati takwas yana cikin wata na goma sha daya yayi mugun girma. An so inducing dinta da wuri taki saboda tsoro ga dadewa bata haihu ba. Daga baya da kyar Baba Hadir ya lallabata sai da Ummansa da Mamanta suka sa baki ma. Shine aka yi inducing din nata kwana biyu tana fama da matsananciyar nakuda amma haihuwa shiru. Yammacin rana ta biyu ne aka yanke shawarar yi mata CS. Baba Hadir yana mota hankalinsa ya tashi matuka. Shiyasa ya bar inda su Mami suke kada su ga shima namijin yayi rauni. Zainab dinsa bazai taba iya hada soyayyarta da ta kowa ba. Tayi masa abinda har ya mutu bazai taba iya biyanta ba. Inama cikin zai dawo jikinsa da ya hutar da ita. Text din Ibrahim ne ya shigo wanda tun safe yake yinsu ya kasa amsa masa. Sauran kwanakin tana daurewa ta dauki wayarsa su gaisa. Sauransa jarabawa biyu ya gama level 2. Ummi ta riga shi gamawa dama ba department dinsu daya ba amma tare suke tafiya a karatun. Kwana biyu taje tayi a Sumaila ta wuto Abuja saboda sanin halin da Mama ke ciki haihuwa ko yau ko gobe. Yau da ciwo yaci karfinta har aka shiga cs din Ibrahim bai sami kowa ya daga wayarsa ba shiyasa gabadaya ya kasa sukuni. Baba Hadir yana kokonton amsar da zai turawa dan nasa Major ya kira shi ba wai don ya amsa masa da baki ba, ya dai san zaiji me yace. "Hadir ka bar mata a ciki suna ta nemanka an fito da Zainab. Mun sami namiji" Kabbara Baba Hadir ya shiga yi a zuci yana ta kokarin ya iya fitar da sauti da bakinsa ma. Waye zai karyata Kadaitar Allah a matsayin Ubangijin talikai? Shi Hadir da ya shafe shekaru yana kwance sai yadda akayi dashi. Fitsarinsa da kashinsa tun dansa Ibrahim yana da karancin shekaru yake wannan dawainiya shine a karo na biyu ya sake haihuwa da Zainab. A take ya turawa Ibrahim kyakkyawan reply sannan ya fita daga motar ya koma ciki. Dakin da aka tura Zainab din aka nuna masa. Ummi na rumgume da baby din an nado shi da shudin shawl mai laushi sai raba idanu yake yi. Mami kuwa ta saka shi a gaba wai yasan yana son kallon duniya me ya zauna yiwa kanwarta a ciki. Sai da ya dan kwankwasa sannan ya tura kofar ya shiga. Zainab baki ya mutu tana kwance allurar anasiziya bata gama sakinta ba. Sai dai da yake ta ido biyu ce tana jin me suke yi tana murmushin wahala. A kusa da ita ya zauna a gefen gadon Ummi ta dora masa jajirinsa a hannuwansa da ya bude. "Zz..Zayyyyan" Baba Hadir yace da dukkan dagewar da zai iya yana rungumar yaron a jikinsa. Idanun Ummi tuni sun ciko da kwalla har ta fara zuba Mami ta riko hannunta suka fita domin a basu wuri. "Hadir magana kayi?" Mama tace tana kallon fuskarsa. Murmushi yayi mata yana shafa kanta da hannu daya ya kuma cewa "Zayyan" "Alhamdulillah...don Allah ka rinka kokarin magana kaji. Ina son jin muryarka Baban Ibrahim da Zayyan" Kai ya gyada yana ta murmushi idanunsa na yawo tsakanin baby Zayyan da Zainab. Tun ranar da aka tabbatar mata da cewa namiji ne ta sani ko bai fada ba sunan yaronta Zayyan. Ko yana da rai tasan su biyun masu musayar sunayensu ga 'ya'yansu ne bare kuma daya baya nan ya bar musu wawakeken gibi a zukatansu. Kafin gari ya waye duk wanda ya kamata yaji haihuwar nan yaji. Iyayen Mama da na Baba murna ba'a cewa komai. Har waya suka yi suna yiwa juna barka. Soyayyar nan daga Allah ce. Dubi shekarun da tayi a gidan Alh Musa sau daya tayi bari sai gashi daga samun lafiyar Hadir anyi ciki har an haife. Wannan shine dan soyayya inji Mami. Radhiya kamar ta jawo tafiyarta da ta rage kwanaki uku. Wani babban mall ta shiga ta jidowa kanin nata kaya na ga na fada ta kara akan tsarabar da ta gama hadawa. Duk zuwa gida sai tayi wannan tsarabar saboda bata ga me zata yi da kudaden da suke jibge a account dinta ba. Mijin Nasara yayi daga Nijar kakaninta kamar masu gasa da juna wurin yi musu aike ita da Emzee. Ga uwa uba His Excellency ya mayar dasu kamar masu daukar albashi. Kwananta Mama biyu a asibitin aka sallamota. Ummi ita ce uwar da tsakaninsa da Mama shayarwa ce sai kuma dare idan zata koma gidanta. Mami kuma duk wata bukatar maijego tana wuyanta. Baba Hadir gani yake sunfi kowa sa'ar zumunta a duniya. Babu ta inda jini ya hadasu amma dangantakarsu kullum kara karfi take yi. Fauziyya ta matsawa Bilal da zaiyi tafiya Lagos wani aiki ya kaita Abuja ita da Jawad dinta da ya fara yawo ko ina. Zahra ma Radhiya tana sayen ticket ta fara yi mata famfo har yau bata taba ganin Femi a zahiri ba. Ba don yaso ba Raji yace zai kawota amma da sharadin idan ya kasa hakuri zata ganshi kuma dole su tafi. Shima yana son zuwa gaishe da yan uwan iyayensa ne a Osun state shine zasu fara zuwa kafin.ya dawo da ita Abuja. Gidajen uku sun fara shiri duk da an dage suna ma sai sunyi sati biyu maijego ta kara samun sauki. Yau da wuri Ummi taje ta yiwa baby wanka ta dawo gida. Dakuna uku ne a gidan daya nata sai na Emzee da Radhiya idan sun zo hutu. Rigima irin ta Radhiya wai dambun shinkafa take so taci shiyasa Ummi ta koma gida ta dora. Idan ba haka ba tunda da Nasara zasu zo tasan sai sun hanata sakat da mita. Hadi na musamman ta yiwa dambun nan da kayan lambu da hanta gida ya kaure da kamshi. A wadace tayi shi kuwa saboda dawowar Radhiyan rana dayane da Zahra. Dama shirya abinsu suka yi wai sun dade basu hadu ba ana kewar juna. Mami ta aiko mata da farfesun kayan ciki cikin flask wanda ta hada dasu da zata yiwa Mama saboda a nan duka zasu ci abinci bangaren Ummin. Fauziyya tuwo tayi musu Zayyana 'yan mata kuma salad da drinks ta hada aka jere komai a gidan Ummi. Su Zahra da azahar zasu sauka Radhiya kuma sai biyar na yamma. Major jiran zuwanta kawai yake yi saboda murnar nasarar da ta samu na project dinta. Ita da Zayyana da ta gama secondary bana ya tanadar musu wani babban surprise. Duka suna wannan abu Mama ta kira Awwab kwanaki biyu da suka wuce ta tambayeshi yaushe zai dawo ne yace sai nan da sati uku. Yanzu haka ya koma Germany babbar hedikwatar kamfanin nasu akwai abubuwan da zai karasa ya taho gida. "Babu yadda za'ayi ka dawo ranar Juma'a?" "Mama so nayi na gama komai yadda idan na dawo sai na cike wata biyuna kafin na koma aiki" ya bata amsa. "Ni dai idan da hali ka taho ina son ka taho iyayenka na bukatarka. Ka kusa shekara fa rabonka da gida duka ka barmu da kewa." "To Mama zanyi kokarin tahowa tare da Zahra tace min jibi zata taho. Idan na kwana biyu sai na koma na karasa aikin" "Allah Ya shi albarka Awwabun Ummi" "Amin amma naki ne yanzu. Ummi ta dade da yayeni ai. Kada ma kice musu zanzo ita da da Mami ba murna zasu yi ba." Mama sai murna ta dana tarko zata sha kallo. Ta san idan Radhiya ta iso baifi sati biyu zuwa uku zata yi ba zata fara aikin da ya dawo da ita. Shi kuma kullum yana sama kamar tsuntsu har sai yaushe zasu daidaita ta ga ta fara shirin bikinsu. An gama komai dreban Daddy ya tafi dauko masu fara sauka idan ya kaisu ya dawo daukar na biyun saboda motar tayi musu kadan kuma babu mai tuka ta Mama. Ibrahim sai laraba zai dawo shi kuma Emzee nasa zuwan sai kwana biyu kafin suna. Ya gama mita wai kiran me ake yi musu don za'ayi suna Ummi tace yaushe rabon da su taru lokaci guda duka. Kuma ma ana gama sunan Rugar Barkindo zasu je da Sumaila kafin Radhiya ta fara aikinta. Su uku suka fito daga cikin airport din. Raji, Zahra da kuma Awwab da yake dauke da Femi. Mutan gida kowa yayi mamaki da murnar ganinsa. Yayi wani irin haske da kyau saboda kasar Ukraine akwai sanyi sosai. Ga girma da cika ido tamkar Major zamanin kuruciya. Dukkansu gidan Mama suka shiga ya mikawa Fauziyya Femi ya koma gefen Ummi da hannuwansa a mike yana jira ta ajiye masa baby Zayyan. "Naki din, yanzu zaka zo Awwab sai dai in ganka kuma jiya ma munyi waya fa" tace tana bata rai. "Ummi kin dena sona ne, a wayar ma fada kike yi min" yace yana dariya. Sauran ma sai suka soma dariya ana tsokanar Ummi wai Mama tayi mata kwacen da. "Ga sabo me zanyi da wannan katon nima. Na barwa Mama dama haka take so" "Ke dai kawai don kinga munfi shiri yanzu shine zaki tashi hankalinki" Sosai ta rinka zolayar Ummi ta kuwa hana shi baby din ya gama nacinsa ya hakura. "Abincinku yana gidan Ummi. Zahra mijinki zai ci a can ko a kai masa dakin Awwab?" Mami ce tayi tambayar tana rike da Jawad da ya hanata zama yace wannan ya nuna wancan. "Ni dai na koshi" Awwab yace ya tashi zai tafi daki. Ummi ta tabe baki "kun gani irin halin nasa, mutum yaki cin abinci kullum koshi yake kira alhalin baici komai ba" "Ummi ki rabu dashi yunwa ai ba kanwar uwa bace. Zata koro miki shi anjima" Daga shi har su Zahran a gajiye suke. Dakinsa wanda aka gyara domin zuwan Raji suka shiga suyi wanka. Fauziyya ce ta yiwa Femi ya ware suna wasa da Jawad. Mami sai murmushi wadannan yaran jikokinta ne. Sai karfe shida da rabi su Radhiya suka iso gidan suma a gajiye sai dai murna da doki bazasu bari taji da gajiyar jikin nata ba. Ita da Tante Nasara ne da Yousuf. Suna sauka daga mota tayi gidan Mama da sauri. Irin shigar da ta saba tayi na skirt mai fadi da riga iya cinya mai dogon hannu madaidaiciya wadda bata kamata ba bare ta fito da shape din jiki sai rolling din mayafi da tayi. Yousuf yana kallon yadda take sauri ya girgiza kai. Wani zubin kamar ta girma amma idan abin ya motsa sai tasa mutum dariyar dole. Yanzu ma saurin da take yi wai kada a gama rigata daukan baby ne. Tunawa tayi da jan kunnen da Tante take yi mata akan rashin nutsuwa sai ta tsaya ta daidaita kanta sannan ta shiga da sallama. Mama tana zaune kasa hakuri tayi ta taso ta tarbi 'yar tata cike da farinciki. "Radhiya kece kuwa? Bari dai maman taki tazo naji ko an baro min tawa a can ta kawo min ta bogi" "Kai Mama" tace tana murmushi amma duk iya dauriyarta rashin ganin baby din yasa ta soma bata rai "Mama ina Daada?" "Wai da gaske haka zaki rinka kiran sa?" "Oui Maamon" Ta amsa da dariya tana mata salute suka sa dariya tare. "Yana bayan Mami yanzu ta fita zata dawo am....." Radhiya har ta kofa tafiyar da bata kai minti guda ba ta kaita gidan Mamin. Tana iya jiyo muryoyinsu Zayyana ta fada da sauri tana murna. Su duka Mami ce tace su fita a bar Mama tayi bacci ko ta huta dai. Kan kace meye wannan sun cika gidan ba babba ba yaro daga kan Zahra har Zayyana. Murnar ganin juna suke yi sosai. Kowa yayi mamakin Radhiya ta canja sosai ta zama wata rabin baturiya. Ta dauki Jawad da Femi duka lokaci guda tana juyi dasu. "To dai ku rage hayaniya kunga mijin Zahra yana ciki kada ku hana shi hutawa" Mami ta fada tana ficewa da baby a bayanta don bazata yarda suna wannan hayaniyar ta damka musu dan amana ba. Suje can su karata da nasu 'ya'yan tunda su da kwarinsu. Zahra ta dora hannu a baki tana kunshe dariya "Hamma Awwab kai Mami, shi yafi kowa gudun hayaniya yanzu." Dif Radhiya tayi gabanta na faduwa. Hamma Awwab yana cikin gidan bata sani ba. Da yaran a hannu ta juya zata fita ta rasa murna ce ko tsoro ko kuma bacin rai na shareta da yayi. Suna zuwa kofa Femi ya bare baki yana mikawa Zahra hannu. "Tafi can nima bana yi da kai mai kyuya kawai. Kuma zaka ganni na goya Jawad ne na bashi chocolate" tace tana mikawa Zayyana shi tunda tafi kusa. Kukansa da Raji yaji yasa shi bude kofar dakin Awwab kuma a lokacin ne tayi wannan maganar a kunnuwan Awwab din. Comb ne mai brush mai laushi yake sake kwantar da sumar kansa duk da yayi aski saisaye amma gashin ya soma fitowa. Dena brushing kan nasa yayi ya kallo kofar yayi sa'ar ganinta tana hararar Femi da ganin babansa yasa shi dariya. Murmushin da baiyi niyya bane ya kwace masa yana kallon yadda take hararar yaro a gaban iyayensa kuma wai nan fushi ne kawai don yaki binta "Silly girl" ya furta a hankali idanunsa a kanta har ta fita daga gidan. Ko da ta isa gidan Tante da Yousuf suna tare da Ummi suna cin abinci. Dukkansu dama yunwa suke ji tun a hanya. Wurin Ummi taje ta rungumeta tana dariya. "Umminaaaa" "Meye haka, tashi ni ki dagani" Ummi tace tana jin kunyar Tante ba don bata murna ta ganin 'yarta ta ba. "Alheran rabu da ita kinji. Zuba abinci ki ci" "Wanka zan fara yi. Ummi yaushe Emzee da Ibrahim zasu zo?" "Kafin ki fara aikin in sha Allahu. Kiyi wankan sai kuci tare da su Zahra su ma basu ci ba muna gidan Zainab tun dazu ana hira" "Ai sai an dawo da komai baya bari na shirya dai." Dakinta ta wuce akwatunan Fauziyya da Zahra suna gefen inda Ummi ta tura mata nata. Su ukun a nan zasu kwana. Yousuf a dakin Emzee ita da Nasara a dakin Ummin. A can gidan Mami kuma Zayyana ce kawai sai Awwab da Raji. Tana wanka tana tunanin wai Awwab yazo. Yaushe rabon su da haduwa. Gabanta har wani faduwa yake ta koma shiryawa a hankali. Duk yadda yace yana sonta ko sau daya bai nemeta a waya ba tunda ta tafi wai shi fushi. Kwafa tayi ita kadai. Ranta taji ya baci tayi siririn tsaki tana tazar gashinta da ya zarce kafadunta. Dama ita kanta akwai cika ga santsi shiyasa duk gyaran da take masa bai wuce amfani da shampoo masu kyau ba sai steaming da Tante take mata a shafe shi da mayuka. Tana daure shi yake kwanciya a kanta sai tayi rolling dinsa a keya ko tsakiya da ribbon. Ita da kitso sai sunzo Nigeria ko Nijar. Doguwar riga ta saka ta wani yadi mai laushi anyi mata free style da dogon hannu. Karamin mayafi ta yafa bayan ta shafa hoda, kwalli da wani lip gloss light brown. Sassanyan body spray ta feshi jikinta dashi ta kuma saka turarensa a kayanta. Kamshinsa bashi da karfi very cool daidai da mata. Ta bata lokaci sosai sai da tayi sallar magariba da isha ta fito. Fauziyya da Zahra ta gani da yaransu su Ummi suna gidan Mama har Tante. "Kunci abincin?" "Au wai da baki ci ba Radhiya? Shine kika makale a daki" Inji Zahra Hira suka dasa suna yiwa juna tambayoyin yaushe gamo ta durkusa gaban kwanukan abincin da aka sauke a tsakar falon ta debi dambun yadda take jin zai isheta da farfesun a karamin bowl. Kan dinning table ta ajiye komai ta karkata kujerarta yadda zata ji dadin hira dasu Zayyana ta shigo tana waya da Emzee. Wuri ta samu ta zauna a kujerar kusa da Radhiya suka ji wannan deep voice din ta Awwab yana sallama. Kowa ya amsa sallamar harda Yousuf da ya fito daga daki a lokacin amma Radhiya ta kasa bude baki kamar wadda ta hadiyi kota. Ko dago kai ma ta kasa yi tana rike da cokali a hannu tayi kasa da kanta. Zuciyarta na tsananta bugu. Fuskar Awwab a sake yaje ya mikawa Yousuf hannu suka gaisa tare da fadawa juna sunayensu. Zama Yousuf yayi a kan daya daga kujerun falon suka gaisa da su Zahra. Shi kuma Awwab ya tako a nutse zuwa dinning table din da yake kusa da bango daga bayan kujerar da Yousuf ya zauna. "Bani wuri" yace da Zayyana yana mata nuni da kujerar da take zaune a kai. Da sauri ta tashi ta koma wurin su Fauziyya shi kuma ya zauna. Gabadaya ji tayi falon yayi mata kadan tamkar cikin akurki aka kulleta tare dashi. Bai ce mata komai ba ya karbi cokalin hannunta ya zuba farfesun akan dambun ya diba yasa a baki sannan ya mika mata. Sai a lokacin ta dago kanta suka hada ido. Babu wanda zuciya da gangar jikinsa bai aika masa da sako mai girma a tattare da dan uwansa ba. Sun chanja sosai shekara kusan uku ba yau ba. Sauke nata idon tayi da sauri ya sake mika mata spoon din. Dan cije lebenta tayi tana tuno wani lokaci da abu makamancin haka ya taba faruwa dasu a Kano da Sumaila. Tana ji a jikinta ma mutanen falon kallonsu suke yi sai kawai ta dake ta karba. Idan bata basar ba zato zaiyi ta wani damu dashi ne har yanzu. Diban abincin tayi ta saka a bakinta cike da kunya. Kafin ta mika masa ya zura hannu ya sake karba ya ci sannan ya bata. Falon kamar anyi ruwa an dauke. Ita ta kasa kallon gefen da sauran suke shi kuma nasa idanun a kanta suke ba ma kallon plate din gabansa yake yi sosai ba. Yousuf yana ganin wannan abu yaji wani daci daci na taso masa dole ya tashi ya koma dakin Emzee. Awwab yayi wani murmushin gefen baki. Shi kuwa tunani yake wai dama Hamma din da take fada saurayinta ne ko me? Anya shakuwa zata sa Alheran cin abinci plate daya dashi kuwa? Ko da wasa duk zamansu bata taba kwatantawa ba. Sun cinye abincin dama ba wani yawa ne dashi ba Awwab ya janyo flask din "in kara miki?" Yace yana kallon zoben nan da ya bata har yanzu yana yatsanta To a gaskiya ba koshi tayi ba ta langabe kai har yanzu taki yarda su hada ido "kadan" Zubawa ta ga yana yi fiye da yadda take bukata ta kuma dago kai tana ware masa idanu "its ok" Sai da ya zuba wanda yake ji zai ishesu su biyun ya sake mika mata spoon din taci ta bashi. Da za'a ce mata kyat a guje zata bar wurin saboda kunyar da take ji amma ita a dole sai ta basar kada ya rainata. Shi kam rabonsa da jin nishadi irin na yau ya manta. Ya kasa dena kallonta kamar ba Alheran dinsa ba. Tayi masa kyau sosai ga wata zazzafar soyayyarta tana fizgarsa kamar yadda ya kamu da sonta farkon haduwarsu. Ba don abinda tayi masa ba da yanzu kila suna da yara kamar nasu Zahra. Ba komai ya kawo shi gidan Ummi ba a lokacin sai zuwansa wurin Mama suka shigo da Tante Nasara. Mama da gayya ta dauko zancen Yousuf saboda yaji. Ai kuwa ta tayar masa da hankali. "Haj Nasara wato kin mana kwacen 'ya sai munyi da gaske muke ganinta" Dariya tayi tace "kuma ko na tafi wallahi a bar min yarinya ta sake. Ni da Yousuf duk mun shagwabata. Idan naji ba daidai ba ke zan fara kamawa" "Bama zaki ji komai ba. Yaron nan naki akwai nutsuwa Nasara. Naji kamar Radhiya tace likita ne ko?" Gaban Awwab sai da yayi wata rawa kamar ance masa anyi auren Radhiya ne. Likita??? Alheran da shegen son likitoci shikenan Ummi ta cuce shi wallahi. Wa ya sani ma ko sun fara soyayya an barshi a nan akan su Ghazalatu. Bai ko zauna ba ya wuce gidan Ummin sai yayi sa'ar ganin Yousuf din shine ya tsiri cin abinci tare da ita. Juice din kankana mai sanyi ta zuba a glass cup bayan sun gama ci ta kurba sau biyu ta ajiye masa a kusa da hannunsa ta mike abinta ta koma wurinsu Zahra. Daukar cup din yayi ya shanye ya yi hanyar kofa tare da kiran Zayyana wai zai bata sako. Wani shu'umin murmushi takeyi na abinda ta gama gani wanda dole ma ta labartawa 'yan uwanta Emzee da Ibrahim amma suna hada ido da ta ga kallon da yayi mata ta gyara fuskarta. Radhiya na jin karar rufewar kofar ta tashi da sauri tana dafe kirji. "Kuturin bala'i...wai... kunji kirjina kuwa? Har wani zazzabi zazzabi ne ya kamani fa" Zahra da Fauziyya suka kwashe da dariya harda kyakyatawa. Fauziyya ta karkace kai tana kallonta a tsaye hannuwa a kirji tace "shegiya Radhiya ashe kina nan baki mutu ba" "Lallai ma Adda to wace wannan a gabanki?" "Nufina Radhiyanmu dai mai balotelli ashe tana nan kin boyeta." Dariya suke sosai su ukun Zahra tace "Fauziyya auren bakatsine ya koya miki zagi" Juya idanu tayi tana dariya "Ke Radhiya auren Katsinawa akwai riba wallahi ku dena gulmar nan haka don naga take taken Hamma wata rana sai yayi hugging dinki a gaban mutane" Kunya taji harda dora hannu a ka "haka kika koma maman Jawad?" "Gaskiya ta fada miki ai, ni da wannan spoon exchange din da aure kuka yi kawai sai ayi wacce za'ayi ko Fauzi" "Na shiga uku zasu bata yarinya" Radhiya tace tana dariya sosai. "Wallahi balotelli na nan ashe kike disguising dinta da wannan hot chick din" "Kinsan Allah Radhiya ki hana Hamma zaman lafiya...yarinya kill him with love sai ya dawo yana baki hakurin wannan fushin nasa mara dalili" cewar Fauziyya. "Ni dai kiyi masa a hankali amma bance a sassauta ba" Zahra ta kawo tata shawarar. "Ance muku son sa nake yi ne?" Ta basu amsa tana dage gira. Fauziyya tace "Eh to gaskiya baki ce ba. Na fuskanci shi da Arifah kamar akwai wata a kasa don yarinyar tayi 100%. Kamar ance zata zo kuwa gobe zanyi kana confirming meye tsakaninsu" Nan da nan fuskar Radhiya ta chanja tana jin dan mutumcin da suka fara da Arifan ta waya yazo karshe. Zahra da Fauziyya sunyi dariya son ransu bayan ta fice zuwa gidan Mama. ********** Washegari tsabar gajiya kasa tashi sukayi da wuri gashi sun raba dare suna hira. Ummi bata sauraresu ba ta shiga kitchen tare da Tante Nasara da ta biyota itama ta tashi da wurin. Cikinsu Fauziyya ce ta fara tashi taje ta karbi aikin kusan komai ita ta karasa shi kafin Ummi ta dawo daga yiwa Daadaa wanka don Radhiya ta lakaba masa daga zuwanta tace ita bata yarda a kira mata sunan baba ba. Goma saura kowa ya tashi banda Radhiya. Tafi sati bata baccin kirki kullum yawon tsaraba da kuma kammala shirye shiryen project din ga tafiya a gabanta. Ummi tayi magana Tante tace a kyaleta ta gaji ne. Sai shadaya ta tashi babu kowa a dakin. Wanka tayi ta gyara gadon sannan ta shirya cikin atampa blue da baki riga da zani wrapper. Tayi missing irinsu don bata cika sakawa ba a France. Ta gama daurinta mai kyau ta tuna ba zama zata yi ba sai kawai ta tuge shi ta tafi dakin Ummi. A can ta sami bakin mayafi mara nauyi ta yafa ta sake gyara fuskarta ta fito falo. Nan ma shiru, tana son magana da Yousuf amma bashi da sim din Nigeria. Ba ya nan yana wurinsu Awwab da Raji duk sun hadu dasu Daddy da Baba Hadir ana hira a gidan Mami. Tasan basa wuce gidan Mama shiyasa ta tafi can. Ko neman abinci bata yi ba ta gaishe da iyayen nasu itama ta zauma zaman hira. Daadaa ta dauka ta shagala da yi masa wasa sai hamma yake. "Kawo shi na goya shi bacci yake ji tunda akayi wanka bai koma ba" Ummi ta mika hannu za ta karbe shi. "Don Allah goya min Ummi" tace tana ajiye mayafinta a gefe ta duka baya. Ummi ta gyara tsayuwa "me? Rufa min asiri indai goyon ne ga masu karfi nan ki dauka" "Tante" tace tana tura baki. "Don Allah goya mata mana Mairama" "Nasan halinta sarai. Dama can ba wani iya raino tayi ba bare yanzu da ta dade babu wani yaro a inda take. Da dai girki ne sai na sakar mata" Zahra tace "Ummi ni zan bada labari. Cewa take fa na zunguri Femi don kawai taji muryarsa" Dariya suke ta yi mata Tante na tarewa. Mama ma dai sai ta goyi baya "idan bata koya ba yanzu ba sai yaushe ni da nake fatan kafin shekara ta zagayo mun rike sabon jika" "Yauwa Mama" tace tana murmushi ta sake dukawa. Ummi tace babu ruwanta Mami ce ta goya mata shi aka daure shi sosai don Radhiya kam bata iya goyo ba. Ana goya mata shi kuwa ta mayar da mayafinta aka bude fuskarsa. Zama tayi akan kujera ko motsi bata son yi tana tsoron kada goyon ya kwance ya fadi. Tashi su Fauziyya suka yi zasu je suyi wanka Ummi tace bayan azahar su hadu duka da yaransu Awwab ya kaisu gidan Daddy Haroun su gaishe su. Bashi da labarin fitar tace Zayyana ta turo shi don tasan a waya bazaiyi yadda take so ba. Can ya baro sauran mazan ya shigo falon da sallamar da ta tsinka zuciyar Radhiya. Dauke kai tayi tana wasa da wayar hannunta ya shigo yana kamshi ya tsaya a bayan kujerar da take zaune. Na shiga uku tace a ranta tana jin kusancin dake tsakaninsu yana affecting dinta. Rikicewa tayi sosai amma bata so ta nuna shiyasa taki yarda ta dago kanta. "Ummi gani" "So nake bayan azahar ka hada kan kannenka ku je gidan mamanku Gambo ku gaishe su. Ga Raji da Yousuf ma duk ku tafi tare" Shiru yayi amma yasan yanzun nan sai ta fara fada idan yaki amincewa ga mutane a wurin "to Ummi" "Radhiya kun gaisa da yayanki ne?" Mama tace saboda dazu ya shigo sauran duka sun gaishe shi. "Ina kwana" tace a hankali ko shi da yake bayanta baiji sosai ba. Kin amsawa yayi tunda dama baiji me tace da kyau ba. "Nasara muje ki huta ko kin tashi da wuri ga gajiyar tafiya" Ummi tace suka tashi tare sai Mami da Mama. Mami ma sai tace zata tafi gida a turo mata Zayyana ta tayata girkin rana. Yana kallonsu duka suka fice Mama ma ciki tayi abinta dama duk hanyar barinsu tare nemanta take yi. Dukuwa yayi da kansa gefen fuskarta taji tsigar jikinta na tashi abinda shi yaji fiye da haka "kin dena gaisuwa ne?" Taji yace muryarsa na dukan dodon kunnenta. Muryarta ta sake ragewa tace "na gaisheka fa" "Sai a sake tunda banji ba" Humm'umm bai san itama taci ganye bane yanzu ko. Kin magana tayi yana nan tsaye a bayanta har lokacin har ya soma amsa wayar Arifah tana masa barka da dawowa da sanar dashi zasu shigo gari da Mamanta kafin suna. Haushi ya kama Radhiya da ta fahimci da mace yake magana. Gara ta bashi wuri idan ma akwai wata I love you da zamanta a wurin ya hana a fada sai yaji dadin sakewa. Tashi tayi da karfinta ai kuwa goyon nata taji gabadaya yayi sako-sako yana neman kwancewa baby ya fado. Yadda gabanta ya fadi sauri tayi ta duka jikinta na rawa ta tallafo Daadaa da hannuwanta ta baya. A hankali ta saki tana kokarin gyara gaban da ya kwance duka yaron yayi motsi a gigice tace "Hamma" Yana da kallonta amma a zatonsa goyon zata gyara. Kuma tsabar tsoro ta kasa daga murya kada yaron ya tsorata ya fado. "Hamma ka ajiye wayar mana" tace tana daga murya. Sai lokacin ya cire wayar daga kunnensa "me kika ce?" Kafafu biyu Daadaa yake dan shureta dasu alamun baya jindadin yanayin da yake. Kuka ne ya taho mata kada ta saki dan mutane "Hamma please help" tace tana rike gaban zanin sosai kuma taki dagowa. Wayarsa ya ajiye da sauri akan kujerar da ta tashi ya zagayo yana dukawa ya ga me ya sameta "meye?" A rikice take bata san ya zasu kwashe da Ummi ba idan ya fado "goyon ya kwance" "To ki gyara mana" yace yana mikewa ya gyara tsayuwarsa. "Ban iya ba fa Hamma" "Seriuosly?" Shima ya soma rikicewar ganin tana ta saka hannu daya a gaba daya a baya. "Zai fadi" ta sake cewa da yayi wani irin zillo yana canyara ihu ya gaji. "Kwace zanin da sauri" yace yana saka hannu a bayan yaron ita kuma ta kwance gaban "tashi a hankali" Tana tashi yaron ya fada a hannunsa ya kankame shi a kirjinsa "are you okay?" ya tambayeta yana kallon yadda tayi wuri wuri. "Allah Ya soni da ya fado..." "Da sai mu haifi wani" yace yana kallon dimple dinta. Idanunta ta dauke daga kansa maganar tana dada shiga kwanyarta. Duk wasu matakan nuna masa yanzu ba da bane ta nemesu ta rasa sai uwar kunyar da ya hadata da ita. Ya san me yayi mata amma sai ya wayance irin yadda ta taba yi masa. "Silly girl, me kike tunanin ina nufi?" "Ba nufinka idan ka haifi naka nima na haifi nawa sai mu kawo mu hada mata ba?" Kanta tsaye tayi maganar kafin ya gama gano lagonta ta tafi ta barshi da baby a hannu. ********** "Wurin wa kazo?" "Waye shugabanku a nan barrack din?" Dariya ya basu suna masa kallon wanda bai san me yake yi ba. Barrack ai ba wurin da zaka zo kai tsaye bane idan baka san wanda kake nema ba. Chibuzor ya rasa wa zaice musu. Sai da yayi sati a garinsu ana ta jajantawa iyayensa abinda ya same shi sannan da kyar ya kwaci kansa ya taho Sakkwato saboda cika alkawarin da ya daukarwa kansa da Zayyan. Bai san komai game da tsarin sojoji ba kamar chanjin mukami shiyasa kawai yace "Lieutenant Hadir nake nema" yana fata daidai ya fadi sunan. Duk wani hargagi da zasu yi masa sunyi a ganinsu bai san me yake yi ba. Gashi dai a haka yayo fes dashi. Kin tafiya yayi tun safe har yamma ana ta abu daya yana tsaye a bakin gate. Wani ne cikinsu ya shiga ciki bangaren ofisoshinsu suna hira da wani da yake zaune a bayan wata kanta yake bashi labarin wani msi naci a waje. "Baku saka shi tsallen kwado ba?" "Tausayi ya bani. Ya dage wai sako ya kawowa Lt Hadir. Ban taba jin sunan ba ma. Amma an chaje shi babu komai a jikinsa" Wani yazo wucewa suka tambaye shi ko ya taba jin mai wannan sunan. Wanda yake bayansa ne ya amsa "an taba yi mana amma shi fa yayi retire saboda rashin lafiya tun bayan dawowarsu daga Liberia an dade don tun ina non-commisioned officer" Wanda ya kawo zancen ya mike "yayi zancen Liberia fa. Bari dai na koma naji" 💕[11/2, 7:11 AM] 42💕. .Mamaki sosai yayi da aka sanar dashi bakon nasa yace da sakatariyarsa tayi sauri ta shigo dashi duk da cewa ya gama shiri zai tafi gida ne lokacin tashi yayi. A bakin kofa ya tsaya ya tarbe shi yana murmushi suka kama hannuwan juna suna gaisawa. Kowannensu sanye yake da manyan kaya da babbar riga. Kana ganin bakon kasan naira ta zauna da kyau. Daga hularsa har zuwa takalmi babu wani abu da kudinsa yake kasa da dubu ashirin. "Alh Salisu wai kaine nake gani ko dai mafarki nake yi?" "Tuba nake Alh Musa ni din mai laifine a wurin mutane da yawa. Nine da kaina ba sako ba na yakice ayyukan gabana nace sai nazo" Alh Musa ya nuna masa wuri ya zauna sannan ya tashi ya kira sakatariyarsa ya soma fada mata me zata hadow bakon ya dakatar dashi. "Kada ka damu kanka a koshe nake." Zama ya sake yi suka kuma gaisawa da tambayar juna bayan rabuwa. "Yara suna dakunansu ko?" "Wallahi kuwa" "Naso zuwa daurin auren nan amma wallahi Musa zama a wuri daya na sati gagarata yake yi" "Ya fa kamata ka sassautawa kanka Alh Salisu. Mutum yana fafutukar neman kudin nan fa kawai sai mutuwa ta riskeshi. Sai ya laluba ya ga babu wani abin arziki da ya tara sai wahala. Shiyasa ka ga na makale wuri daya yanzu" "Mtsww ni zan fada maka yawon nan baiyi ba ko kadan. Amaryata fa mai aiki ta kama da dreban da na daukar mata a cikin gidana don bala'i" "Subhanallahi garin yaya haka ta faru?" "Kaima ka sani ai, cewa tayi bana zama bani da lokacinta. Inda na gode Allah bamu haihu ba da ta saka ni wasiwasi" "Ka chanja tsari Alh Salisu. Girma sai dada kamamu yake yi da kunya irin wannan na fitowa daga gidajen aurenmu. Ai kamata yayi ace macen kwarai ko bata sonka ta san kiyaye addini da darajar kanta" Daya daga cikin wayoyin Alh Salisu ce tayi kara ya kasheta sannan yace "ka tuna Halifa ai babban dana. To mahaifiyarsa wallahi ita ta cire min son mata gabadaya shiyasa bana damuwa da zama dasu tunda nasan kudin ne ya kawosu sai na basu kawai. Da bamu rabu ba ina mai tabbatar maka ko zanyi yawo ba kamar yadda nake yanzu ba. Sannan mafi yawa tare zamuyi gani gata" "Kace kun zuba soyayya" Alh Musa ya fada da dariya. "Wace soyayya? Matar da ta aureni alhali tana son mijin kanwarta. Kaji fa kanwa da suka hada uba kuma bata iya boye min. Kishi take da kanwar abin babu kyaun gani. Shiyasa da na saketa bayan abin ya fito da mijin kanwar ya rasu ko shi Halifan bana bari yaje wurinta sosai" "Amma kuwa kayi kuskure Alh Salisu wa yake raba da da uwa banda abinka? Nima nayi irin auren nan amma wallahi Zainab 'yar halak ce. Ka tuna kazo daurin aurenmu. Ita dole aka raba auren mijin ya sami paralysis ga rashin magana amma ta kafe sai ta zauna dashi. Kasan Allah ko zanyi rantsuwa bani da kaffara tunda na aureta Zainab bata sake zuwa Kano ba sannan ko a bayan idona idan tayi waya da danta bata taba cewa ina mahaifinsa. In karkare maka zance na saketa kuma mijin ya sami lafiya. Aisha ma ta kirani wai ta haihu...kai kaji kudura ta Ubangiji" Sosai Alh Salisu yaji dadin shawarwarin Alh Musa don gaskiya yasan bai kyauta ba. Kasuwancinsa ya bunkasa sosai amma zumunci dai bashi da lokacinsa. Yana China babansa ya rasu haka yana India babarsa ta rasu da kyar ya roki yayyensa aka jinkirta jana'izarta. Kudi dai danginsa sun warke amma ganinsa yayi wuya. "Nagode Alh Musa, zan gyara don ina komawa zansa a kai Halifa Sumaila wurin babarsa da kakaninsa. Bai saba da kowa ba sai ni. Cikin gidan ma kannensa ba shirginsu yake shiga ba ni kuma ban damu ba ganin duka mata ne" "Matan idan babu kai ba shine gatansu ba?" "Hakane, sai ka tuna min da abokaina na kuruciya da duka na watsar da kace mijin matarka na da yana da paralysis. Akwai aminina soja ne a yaki ya kamu da wannan lalura. Sau biyu naje duba shi shikenan kamar wani sallamamme na dena waiwayarsa. Daga baya kunya da nauyin jinkirin yasa na kasa zuwa kuma" "Tunda kana da rai ai babu wani jinkiri. Itama Zainab din mijinta fa a yaki ne tasa lalurar sunansa Hadir" Alh Salisu sai ya gyara zama da kyau "Hadir Murtala mutumin Kano?" Da mamaki sosai a fuskarsa yace kwarai kuwa "shine aminin naka?" "Shine Alh Musa wallahi shine. Ina zuwa Kano gidansa zani...ni kam kudi naga sharrinsa tunda ya nesanta ni da makusanta na" Alh Musa yayi matukar mamaki. Da Alh Salisu ya rike zumunci da Hadir bai kwashi wadannan shekarun a kwance ba. Kudi ne dashi fa na ban mamaki don shi a haka bai kama kafarsa ba. Duniya komai sai Allah Ya nufa amma sakacinmu ke janyo mana. Adireshin gidansu na Abuja ya nema wurin 'yarsa ya bashi. "Daga nan ni sai birnin tarayya inji mutanenmu." Godiya mai tarin yawa ya yiwa Alh Musa sannan ya koma katon gidansa dake garin Port Harcourt din. Halifa ya kira yace masa ya shirya gobe ya taho Abuja. Bautar kasa zai fara dayake a turai yayi karatu ya gama da wuri. Sake tunani yayi na tuna cewa yaron da kannensa ma babu shakuwa yace masa dashi da kannen nasa mata ne su hudu su taho tare. Sai kuma ya kira matarsa uwar uku cikin yaran Farida, Husna da Meena. Dayar mai bin Halifa a jerin haihuwa Hibbah tata maman ta dade da fita itama ya fada mata tace yaran su shirya. Baiwar Allah har ranta taji dadi yau da kansa yana wani garin yace a tura masa 'ya'yansa kuma wai kuma su da Halifa. Bata taba kin yaron ba duk miskilancinsa da shiru shiru. Irin 'ya'yan baba dinnan ne sangartattu amma ba wai ya lalace da dabi'un banza bane sai son jiki. Halifa yaro ne sa'an su Ibrahim sai dai ya fisu duka girman jiki. Ga tsaho kuma da 'yar kibarsa daidai misali ta hutu da jindadi. Bashi da matsalar komai a rayuwa sai mahaifiyarsa Salame. Duk kudin babansa yafi ganewa ya saya masa abubuwan bukata ya bashi kadan kawai don kada ya kai mata. Ita kuma da zarar ta ganshi tamkar ta ga nama ta rinka bani bani kenan. Ga matsalar muguwar kazantar gidanta ko yawu baya iya hadiya idan yaje. Kannensa na gidan idan suka yanyame shi ya rinka yamutsa fuska kenan. Daya kanwar tasa wadda Salame ta auri babanta farkon mutuwar aurenta bai fi sau biyu ya taba ganinta ba. Itama nata baban sai a hankali babu kudi amma dai bata da roko, sunanta Rahima. A haka itama bata huta da bani banin Salame ba idan taje gidanta idan tace babu ta hadasu ita da mahaifin nata da danginsa ta zagesu su tas. Yarinyar da iyakarta secondary don ma tana sana'ar kunshi da abin sai ya fi haka mun. Washegari Alh Salisu da 'ya'yansa suka sauka a gidansa na Abuja yace su huta ana magariba zasu je gidan abokinsa. ********** A can Jos Excellency bai huta ba Chibuzor bai huta ba. Bincike da tambayoyi yasa ake ta yi masa sai yau ya gama samun duk wata shaida da zata tabbatar masa cewa Chibuzor ba dan aiken 'yan hamayya bane sannan ba wata damfara bace ta kawo shi. Hankalinsa in yayi miliyan to a tashe yake da yasa shi a gaba yana bashi labarin rayuwarsu a kurkuku. Abu dai sai da ya kai Gwamna da zubar hawaye. Duk wani aiki da yake gabansa yasa an dakatar dashi domin ya samu yayi aikin Zayyan kawai. A ka'ida Major Mustapha da Hadir ya kamata ya nema amma sai ya tuna cewa yadda suka yi zaton Zayyan ya rasu haka shima yayi wannan tunanin. Abinda yaga yafi dacewa shine yaje ya kawo Zayyan Nigeria ya dangana shi da iyalinsa. Shawarar tayi masa, shi kadai bayan sunyi waya da matarsa akan zuwan su Awwab gidan ya sake shawarar gara ya tafi dashi ayi komai a gabansa har zuwa dauko shi. Da wannan shirin suka kwana gobe zasu tafi Abuja shi da Chibuzor hedikwatar sojoji dake unguwar Garki. Mukaminsa na Gwamna kuma tsohon soja yasa tun a daren da yayi waya ya nemi ganawa da Chief of Army Staff Lieutenant General Enejo Adaji mutumin Kogi aka saka masa appointment din karfe biyu da rabi na rana. Dukkan wata kulawa da ta dace da bako mai mahimmanci ita ake yiwa Chibuzor. Emma tayi murna sosai da ya fada mata yadda komai ya kasance. Da safe suna tashi da wuri aka dangana su da filin jirgi. Convoy din Excellency dama a Abuja suka kwana. Arifah da Mamanta sai ganinsa suka yi da bako kuma ko minti talatin basuyi a gidan ba suka wuce Nigerian Army Headquarters. Bayan 'yan gaishe gaishe irin na manyan mutane Rtd Col. Nasiruddeen ya gabatarwa da Lt.Gen Enejo da Chibuzor da bayanin da yazo dashi. Hankali a tashe Chief din na army staff ya soma buge bugen waya aka hau bincike a bangaren aiki da na'ura mai kwakwalwa akan waye Chibuzor Kalu, asalinsa da sana'arsa domin a tabbatar da ingancin zancensa. Yaga tasku ranar duk da babu duka amma fa an kaishi dakin bincike ace wannan ace wancan duk don su ji ko zai chanja magana idan bashi da gaskiya. A bangare guda kuma an binciko files din sojojin da aka tura Liberia daga Giginya Army Barrack na Sokoto a shekarar 1993. Zancen gabadaya an saka shi a jerin CLASSIFIED INFORMATION ba kowa ya sani ba sai mutane kalilan. Sunci karfin bincikensu washegari zasu nemi sa hannun shugaban kasa domin ya bada izinin ganawa da gwamnatin kasar Liberia. Excellency dai yayi ta rokon a gaggauta komai don a matse yake da yaga an fiddo Zayyan Tureta daga kasar nan. ********* Alh Musa ne ya kira Ibrahim ya fada masa bakin da zasu yi yace ya sanar da mahaifinsa. Gobe zasu taho shi da Emzee. Ya gama jarabawa da kwana biyu kenan ya tsaya jiran Emzee su taho. Bayan ya fada masa shine ya kira Mama ya fada mata. Mamaki kwarai kuwa ya kamata ta sanar da Baba Hadir. Shi din ma mamakin yake. Yaushe rabonsa da Salisu, har ya manta. Rubutawa Mama yayi cewa ta fadawa Ummi tunda a iya saninsa akwai haihuwa tsakanin yayarta Salame da Salisu. Itama tayi mamaki sosai nan fa suka hau shirin tarbar baki tunda ance shi da yaransa ne. Mama da Ummi suka yi ta mamakin wai yau Salisun da ko ita Ummi da ya taba auren yayarta rabonta dashi tun gaisuwar Zayyan. Halifa kuwa zata iya kirga sau nawa yaje gidan Malamijo tun tana makauniyarta. Sun shirya komai a gidan Mama suka tafi yin sallah. Awwab, Yousuf da Raji basu wuni a gida ba ya kaisu ganin gari suma sai magaribar suka dawo. Motocin biyu su Alh Salisu suka yi shi da 'ya'yansa. Daddy yaje gidan Daddy Haroun sada zumunci da magana akan halin da Ghazalatu take ciki a gidan Nura da ya fada masa. Shawara yake nema akan yadda zasu fadawa Alh Baba kada rigimar ta wuce yadda take yanzu don Gambo da Hussaina harda zage zage tsakaninsu. Rufa rufa suke yi kowacce bata son fitar da maganar kada aji ayi musu dariya. A kofar gida Baba Hadir ya taresu suka karasa ciki shi da yaran. Zayyana ta tafi bangaren Mami da Hibbah wata uwar surutu da karadi irinta. Yanzu take SS3 saboda haka hirar ta 'yan mata ce masu tashen girma. Kanenta su Husna suna can suna fadan daukar Femi da Jawad suna ta musu wasa. Dukkansu son yara garesu kamar su daukesu suke ji. A falon gidan Mama su Zahra sun gaishe da Alh Salisu suka koma bangaren Ummi a falo suka dasa tasu hirar. Baby Zayyan Ummi ta mikawa Alh Salisu yace "Mairama ko ina da bakin wanke kaina a wurinki da Hadir? Duk wani rikicin gadonku bani mantawa anyi dani haka lalurar Hadir amma neman kudi ya hanani yin abinda ya kamata. Tabbas ba karamar kunyarku nake ji ba ko ban taba auren Salame ba a matsayinki na matar Zayyan baici ace na yanke zumunta daku ba" "Komai ya riga ya wuce sai dai mu fuskanci gaba. Kurakuranmu sai muyi kokarin mun gyara saboda kada yara su tashi basu san juna ba" Halifa ya kalla da yake zaune ya karbi babyn yana masa wasa "Halifa wadannan duka iyayenka ne saboda haka a rike zumunci" "In sha Allahu" "Ina Ibrahim ne da Zayyan?" Alh Salisu ya tambaya. Mama ce ta masa bayanin suna makaranta amma zasu taho gobe. Sai Radhiya da ya gani cikin matan da suka shigo dazu. Awwab dasu Yousuf da suka dawo sun shiga bayan sun gaisa dashi Mama tace ya nunawa Halifa bangaren Ummi ya gaishe da Nasara tunda can zasu koma cin abinci. Fadan su Farida akan daukar yara har waje Radhiya tana alkalanci. Jeans ne baki a jikinta da top sai da dora hijab mai hannu da ya wuce gwiwarta kadan. Suna shigowa ta koma tana sulhun daga zaune. Halifa ya kalleta ya kara duka akan idon Awwab yana mamakin yadda ta zama. Da kuruciya basa shiri saboda Salame ta koya masa kinsu haka itama bata son shi tunda dan Gwaggo Salame ne wadda bata son Umminta. "Radhiya bazaki gaisheni ba" yace bayan ya zauna. Murmushi tayi tace "Ka rainani Halifa ko don kana ganin ka zama basamude" Yadda take magana ya sashi dariya "ance Emzee yana NDA ko, ke kuma me kike yi yanzu? By the way you look great and ...beautiful" Turnuku, ya kai Awwab wuya Yousuf ya koma kallon Awwab din yana dariyar mugunta. "Thanks" tace da murmushinta. Bai da son hayaniya amma yaji yana son tsawaita hira da 'yar uwar tasa da ya jima basu hadu ba. "Da gaske fa da a waje muka hadu bazan ganeki ba. Nafi gane wannan terror din abokiyar fadana...tsoronki fa nake ji da" Fauziyya sai ta tattara 'yan matan da yaransu suka koma daki saboda kada Awwab ya fashe musu a wurin. Da Halifa zai ga irin kallon da yake masa kila da yayi shiru. Radhiya ta gani sarai ko zama ya kasa yi amma ta biye masa. "Ta da dinma tana nan sai dai idan ba'a tabota ba" "Halifa mu bazaka yi hirar damu bane sai 'yar uwarka?" Yousuf yace domin ya kawo karshen hirar. A fusace Awwab ya juya ya fita. Kalmar great and beautiful ta tsaya masa. Jikin mota yaje ya tsaya sai ya sami kansa da kiran layinta. Su uku suka rage a falon saboda Zahra tana can dakin Awwab da mijinta tunda ya leko suka fice. Yanzu hirar da Yousuf ake yinta yawanci akan makarantar da ya gama a Dubai da kuma wadda take yi yanzu. Allah Yasa wayar na gefenta ta ga kiran ta dauka. "Fito" kawai yace mata ya kashe. Tashi tayi tsam ta saka wasu flat shoes dinta masu kyau ta fito wajen ta hango shi zaune cikin mota. Kallo daya tayi masa tasan ransa ne a bace sai taji babu dadi kuma. "Hamma" tace a dan tsorace. "Get in" ya umarceta. Bata ce komai ba ta shiga gaban ya daga waya ya kira Ummi yace mata Alheran zata raka shi siyan magani ba jimawa zasu yi ba. "Hamma baka da lafiya ne?" Idonsa akan titi yaki kulata. "Ko mu koma gida a taho da namiji ka ga idan lalurar tayi tsanani sai an daukeka ni ba karfi gareni ba Allah." Bai san lokacin da ya soma dariya ba tun yana yi a hankali har ta fito. "Yanzu fushin ma bazaki bari nayi ba?" "Fushin me?" Tace kamar bata sani ba Murmushi yayi "Ya wuce" Daidai nan ya wuce wani kanti ta hango katan din lemuka an jere a waje harda na maltina. Kwadayin ne ya motsa ta dube shi. "Hammaaaa" muryarta ta doki kunnensa da shagwabarta da take bashi sha'awa yanzu. "Uhmm" "Ka saya min maltina don Allah yanzu ka wuce shop din a can" ta nuna da hannu. "Kinyi dinner ne?" "Sai anjima" "Bazan saya ba, na kula ba kya son cin abinci kema" Sake narke masa tayi sai da ya dage ya iya controlling kansa daga barin janyota jikinsa. "Hamma manaaa..." Bashi da zabin da ya wuce juya kan motar ya barta a mota yaje ya siyo. Katan uku aka saka masa a booth sai guda hudu masu sanyi a ledar hannunsa. Yana zama ya mika mata ta balle saman gwangwanin tana sha tana lumshe idanu. Rabi tasha ta mika masa ya karba sai da ya kalleta ya dora bakinsa a kai ta kawar da kanta gefe. "Tell me about your project tunda jira kike na roka" Sun kusa gida lokacin ta soma yi masa bayani dalla dalla kamar ba Radhiyan da ya sani ba. Shirmen yana nan amma ta fannin karatun bata wasa. Wannan ita ce Alheran din da ya fada soyayyarta. "Impressive. I am proud of you. Amma why mass comm? Meyasa baki zabi wani course din ba?" Ya tambayeta bayan yayi parking din motar. Gwangwani na biyu take shirin budewa ya karba ya bude mata. Kafin ta karba ta nuna masa wannan zoben nasa. "Ka ga wanda ya zaba min nan. A hannuna sunansa Awwab shi yace yafi son nayi mass comm" Duk kalma daya dake fita daga bakinta tana kara hura masa wutar soyayyarta ne. Bazai sake yarda da wasu dalilai ba da zasu sa yaki aurenta wannan karon. Baya ma tunanin komawarta school babu igiyoyinsa a kanta. So yake yaje ya kammala abinda Mama ta katse masa ya dawo ayi komai a gama kafin ya koma aiki. Kwantar da kansa yayi baya a jikin seat yace "Kin shirya aurensa yanzu" "A'a" "Reason?" "Sai ya dena fushi dani" Gwangwanin hannunta da ya bude mata ta mika masa "rage min". Kurba daya yayi ya bata ta dauki ledar ta fita batare da ta sake cewa komai ba. Yana kallonta har ta shiga gida ya fiddo wayarsa da niyar kiranta ya fallasa mata duka sirrukan zuciyarsa ya ga kira da bakuwar namba. Yana karawa a kunnensa ya gane muryar mai maganar mahaifin Arifah ne. Tambayar farko da ya fara yi masa shine yana son sanin idan shi kadai ne a inda yake. Idan ba shi kadai bane kuma ya tashi ya kebe akwai maganar da yake so suyi. Awwab ya tabbatar masa da cewa shi kadai ne sannan yace masa yana bukatar passport dinsa a daren saboda gobe da sassafe za'a zo a karba. Dakinsa yaje da sauri ya dauko yanayin muryar Excellency yasa shi jin cewa akwai abinda yake faruwa. Bai sanar da kowa ina ya tafi ba yaje gidan wanda kamar jiransa suke masu gadin aka bude masa gate. Wani falo PA dinsa ya jagorance shi suka je ya same shi tare da bakon da bai sani ba. Duk da haka ya mika masa hannu suka gaisa bayan ya gaisa da gwamnan. Da turanci domin kowa ya fahimta ya soma magana. "Awwab wannan sunansa Chibuzor Kalu" Murmushi ya sake yiwa mutumin wanda ya dauke a lokacin da yaji Excellency ya fara fada masa abinda ya kawo Chibuzor garesu. "Zayyan is alive and in prison" Mikewa yayi tsaye yaji kansa ya kulle. Gaban Chibuzor yaje ta idanunsa suna nuni da rauni matuka "is this some kind of a joke?" [11/2, 7:11 AM]🏽 ]🏽 : 41💕 Da ya fito Chibuzor yana tsaye can gefe ya gaji da magana ya koma yana sabunta tunani da nemarwa kansa mafita. Baiyi zaton haka abin zai zama ba gabadaya ya shiga cikin tashin hankali saboda tsoron kada ya kasa fitar da Zayyan. Wancan mutumin ne ya dawo gareshi yace masa akwai mai wannan sunan da ya taba zama amma yanzu baya nan. Wani sanyi yaji ya ratsa zuciyarsa "a ina zan same shi? Sako nake dashi mai mahimmanci" "Kana iya fada min sai na gani sakon yana da amfani ko babu" Da dukkan murnarsa yace "na hadu da dan uwansa ne a prison...." "You must be crazy" Sojan ya daka masa tsawar da ta janyo hankalin sauran da suke gefe. Shi kuwa Chibuzor jikinsa rawa ya soma yi. Tun ba yau ba yaki jinin duk wani abu da zai hada shi da hukuma. Sauran suka taru a kansa ana ta daga murya ya gigice. Fada suke yi kawai akan yazo musu da zancen banza. Meye hadinsu da prison da zai ce ya hadu da dan uwan dayansu. Dadin kayan haushin ma wanda yake magana a kai baya nan. Basuyi masa uzuri yayi musu bayanin da ya dace ba suka nemi dukansa ya gudu. A gajiye ya koma hotel din da yayi masauki ya kira matarsa Emma ya fada mata yadda ta kasance. "Ka koma gobe ka dage sai sun barka kayi magana da wani mai mukami a ciki. Banda abinsu waye yake yanke hukunci babu sauraron bayani?" "Gaskiya bazan iya komawa ba. Akwai matsalolin tsaro a kasar nan. Nayi sa'a da basu kamani sun rufe ba. Kallon wani mara hankali ina jin suke yi min" "Yanzu me kake tunanin yi a kai?" "Ban sani ba" ya fada cike da damuwa. "Darling, me zai hana kayi amfani da media? Ka tuna nima fa a TV kawata ta ganka a news lokacin da aka kamaka a airport shine ta fada min" Ihun murna Chibuzor yayi yana gode mata. Sam baiyi wannan tunanin ba yaje zai jefa kansa ga wahala. Karfe goma washegari a gidan talabijin na NTA reshen garin tayi masa. Filin cigiya da sanarwa ya nema saboda a ganinsa gidan TV musamman na kasa wato NTA zai fi saurin zama hanyar yada cigiyar. Idan ya gama da nan niyarsa ya nemi gidan rediyo kuma a nan Sakkwato da Kano. Wata ma'aikaciya ce tayi masa bayanin cewa zai biya bayan ya fadi na kwana nawa yake so a rinka sanya sakon. Da suka gama da wannan ya fahimci komai ta bashi form da zai cike abinda yake nema. "Idan akwai hoton wanda kake nema ko naka idan sun san fuskarka sai ka kawo" "Babu hoto sai sunaye" "Rubuta min a nan..." ta saka yatsanta a inda take bukata. Chibuzor bai rike sunayen duka ba amma ya rubuta abinda ya tuna. (Ina neman iyalin Lt. Zayyan Muhammad Tureta na Giginya Barrack Sokoto wanda ya tafi Liberia a 1993. Sunan matarsa Mariyama, yarinyarsa Al.....) duk yadda yaso ya kasa tuna sunan Radhiya da Zayyan ya fada masa wato Alheran (abokinsa Hadir da Mustafa da kuma Col. Nasiruddeen Aliyu). Sunan karshe shine wanda yafi zama sosai a kansa. Matar ya mikawa takardar zata duba domin tsara yadda sanarwar zata kasance ta karanta bayanin nasa bai wani gamsar da ita ba. Dole sai sunyi masa tambayoyi kenan yadda zai iya fadar me yake bukata kada ayi asarar kudi. "Su wadannan baka san sunayen iyayensu ba domin saurin gano su?" "Akwai matsala ne? Ban sani ba" ya bata amsa yana fatan kada tace bazai yiwu ba. "Amma ai wannan na rike, Col Nasiruddeen Aliyu.." Daga bayansa wani ya taho rike da takardu ya dakata da sauri "Col Nasiruddeen Aliyu dai gwamnan Plateau? Me yayi? Ke akwai sabon news ne?" "Ka sanshi ne? Nemansa nake" Chibuzor yace shima da sauri. "Gwamna ne fa, waye bai sanshi ba? Me yake faruwa ne?" Ya tambayi matar. Hannunsa Chibuzor ya rike "shi gwamnan soja ne? Yaje Liberia tsakanin 1993 da 1994?" A dan tsorace mutumin ya zame hannunsa "tsohon soja ne yayi retire, amma ban sani ba ko yaje Liberia" A gigice Chibuzor ya fito da wayarsa daga aljihu ya rattaba sunan Col. Nasiruddeen Aliyu a google search. Tashin farko sai ga bayanai sun bayyana game dashi. Inda yasan ana saurin samun bayani ya fara dubawa wato wikipedia. Karatu yake yana tsallaken layi kamar wani zai riga shi. (Tsohon sojan kuma kwararren likita a wancan zamani ya tsunduma cikin siyasa ne wajajen 1996 inda tauraronsa ya rinka haskawa yayi suna cikin kankanin lokaci. Mutane suna alakanta wannan nasara tashi da cewa an sanshi a matsayin sojan da ya kwashi kimanin watanni takwas a hannun 'yan tawayen kasar Liberia kafin Allah Ya kubutar dashi wani dare da sojoji suka kai sumame a mabuyarsu. Tausayi da jarumtarsa da aka gani yasa bai taba tsayawa takara ya fadi ba) Mahaukacin ihu Chibuzor ya saki yana dariya "thank you Jesus" sannan ya kaiwa mutumin nan wawura ya rungume shi kamkam sai da takardun hannunsa suka fadi. Bai tsaya bata lokaci ba ya dire mutumin ya fita daga ofishin a guje. Kai tsaye hotel din ya koma ya tattaro kayansa ya tafi airport. Ba shi ya sami kansa a kofar gidan gwamnatin dake Jos ba sai yamma. Tunda ya gane wurin shawara ita ce ya nemi masauki gobe ya dawo. Haka kuwa akayi domin washegari takwas ma a bakin gate din ta riske shi. Ganin gwamna ba abin wasa bane. Masu gadi suka saka shi a gaba aka fara masa tambayoyi akan dalilin zuwansa. "Sako ne zan bawa Col. Nasiruddeen" Ganin wani mara da'a suke yi masa. Idan ba mara da'a ba ya za'ayi ya kira sunan gwamna a kofar gidansa kai tsaye irin haka. Shi kuwa dadewa rabonsa da Nigeria da kuma idan yazo ba yawo yake irin haka ba yasa ya manta abubuwa. "Nasha wahala ku taimaka min" "Ka koma ka nemi appoitment dashi ba wai kazo haka kawai gida ba. Idan kowa na iya ganinsa a gida duka garin nan zasu tare a nan kenan" "Naji ta yaya ake neman appointment din?" "Ka je office dinsa ka nema a can. Idan kayi sa'a ka ganshi a wata daya" Suka kece da dariya. Wannan ko kadan baiyi kama da wanda Gwamnan nasu zai saurara nan kusa ba saboda ayyuka da suka sha kansa 'yan kwanakin nan. Sannan kuma ai ba haka nan ake ganinsa ba, akwai matakai da ake bi. Bai hakura ba yace "yana gida yanzu ko office?" "Yana office" "Nagode" Gefe ya koma abinsa ya tsaya a jikin katangar gidan. Da sauri cikin masu gadin mai kayan sojoji yazo yace ya bar wurin. Gaba ya kara amma duk inda yayi sai ace ya matsa wai ba wurin tsayuwa bane. Chibuzor baiyi zuciya ba don biyan bukata yafi dogon buri. Ainihin titin da ake yin kwanar dama a kansa a shigo titin gidan gwamnatin yaje ya sami inuwar wani gida da filawoyinsa suka hauro ta saman katanga ya tsaya. A nan ya wuni ko ruwa bai matsa ya saya ba saboda tsoron kada ya rasa abinda yake nema. Gajiya, yunwa da shigowar sanyi wanda baya yiwa mutane da sauki a garin na Jos sune suka sarke shi amma da yake mutum ne mai juriya da amana bai gajiya ba. Tunawa kawai yake yi da shekarun Zayyan a prison dinnan yana ji a ransa da yana da hali ko sakan daya bazai bari ya sake yi ba. Tara da rabi na dare sai ga jiniyar motocin gwamna sun taho a sukwane. Ko kallon titin da zai tsallaka baiyi ba ya bi zugar motocin nan a guje yana harin ta tsakiyar wadda yafi tsammanin ita ce gwamnan ke ciki. "Zayyan Tureta is alive" "Zayyan Tureta is alive" "Lt. Zayyan Tureta" "Liberia prison" Wadannan kalmomin ya rinka maimaitawa yana bin motocin yaki sauraron ihun da sojoji suke yi masa. His Excellency Nasiruddeen yana bayam mota tsabar gajiya har soma gyangyadi yaji kalmar TURETA da LIBERIA. Firgigit ya bude idanu ya soma cewa "stop da car" cikin gaggawa. Dreban sai da ya tsorata amma shi da PA sun kula kamar ba a hayyacinsa yake ba duk ya rude shiyasa ya danna trafikato zuwa barin dama sauran motocin bayan suka tsattsaya suma. Yau babu batun jiran a bude masa kofa da kansa ya bude don sauri ya kusa faduwa saboda babbar rigarsa da ta harde shi. Wurin da sojoji masu tsaronsa suka danne Chibuzor a kasa ya isa yana yi musu tsawar su daga shi. Kowa darewa yayi gefe da suka ga ya durkusa ya tayar da Chibuzor zaune. Cikin harshen turanci yace masa "Me kace?" Jikinsa babu kwari sosai ya dago kai yana kallonsa "kaine Col. Nasiruddeen Aliyu?" "Nine, nine" ya rinka nanatawa yana gyada kai. Yana jin wata kakkarfar ajiyar zuciya da yaron ya saki don bazai fi sa'an Awwab ba. "Sir, Lieutenant ZAYYAN MUHAMMAD TURETA..." "Ina jinka, Tureta nawa kake nufi? Wa ya aikoka? Daga ina kake?" Ya rinka jero tambayoyin yana jijjiga shi. "Liberia prison, the Lieutenant is waiting" Hularsa ya tuge bai sani ba saboda yadda ya tashi tsaye da sauri "Lieutenant Zayyan fa kace" "1993 Liberia Peace Keeping Troop" Zuciyarsa bugawa ta rinka yi da sauri da sauri yana tsoron kada ya gaskata maganar mutumin ya tashi yaji ashe mafarki yake yi. "Daga ina kake?" "Liberia Prison" "Innalillahibwa inna ilaihi raji'un" yace gumi na karyo masa "Zayyan yana da rai dama?" "Yace akwai Hadir ko shima yana da rai?" Hannuwansa Excellency ya riko ya tayar dashi tsaye "nasan Hadir, nasan Mustapha, nasan matarsa da 'ya'yansa kowa yana nan" "Ahghhhh" Chibuzor yace da kyar saboda murdewar da cikinsa yayi ga dukan da ya soma sha. Excellency da kansa ya tallabo shi a jikinsa ya ja shi zuwa motarsa jama'arsa suna kallonsa da mamaki. Wani ne yayi karfin halin cewa "Your Excellency kawo shi mu saka shi a motarmu" "Noooo muje kawai" ya amsa yana kankame Chibuzor a jikinsa. Da suka isa daidai kofar shiga cikin gidan ma da kyar ya bari aka shigar masa dashi ciki. Kansa ya kulle so yake yaji gamsasshen bayani. Matarsa da Arifah a ranar suka tafi Abuja daga shi sai ma'aikata. Abinci yasa aka kawo masa yana zaune yana jiran ya gama ci ya kara yi masa bayani. Shima a nasa bangaren baya jin zai iya yin komai sai ya sauke wannan nauyin. "Sunana Chibuzor Kalu" "Ci abinci tukunna sai muyi magana" ya fada batare da maganar ta kai zuci ba. "Bazan iya ba..." Cikakken labari ya samu daga wurin wannan yaro tun daga rabuwar Zayyan dasu Hadir zuwa yanzu. Sai ga His Excellency the Executive governor of Plateau state yana zubar da hawaye. Shekaru daidai-daidai har ashirin da biyu rabon Zayyan da iyalinsa. Kurkukun ce ta fado masa yaji wani kunci yana sauka a ransa. Garin yaya bai taba tunanin komawa su duba wurare ko za'a same shi ba? To amma a gaban idonsa aka yi masa harbi guda biyu ya fadi kamar matacce. Wayarsa ya zaro wadda mutane kakilan suke da layin ga gumi duk ya jika tafin hannunsa saboda girgiza da yayi ya soma neman sunan Major Mustapha. Bai kai ga dannawa ba ya kwabi kansa. Bincike ya kamata ya fara yi ya tabbatar ba wai ya tayar musu da hankali bisa abinda bashi da tabbacinsa ba. ********** Kwanansu Radhiya biyu da zuwa kuma gobe Tante da Yousuf suke sa ran tafiya Nijar. Jiya da Ummi tace suje gidan Daddy Haroun kafin lokacin fitar tasu dreban Major ya kawo rahoton wahalar mai da aka fara tun daren jiya shima bai sami labari da wuri ba. Yawancin masu ababen hawa kowa yana kan layin mai ko kuma ka daure ka saya wurin 'yan bumburutu idan kana da hali. Awwab na ji yace idan sun fita sai suyi full tank a wurin nasu. Raji ya nemi fassarar bayani a wurin Zahra da ta kawo masa dankadafinsa Femi ta fada masa da turanci. Sai cewa yayi wai yana son yayi experiencing bin layin mai irin wannan. Shi da kanwarsa a Germany aka haifesu kuma bai taba katarin samun wannan matsalar ba a duk zuwansa Nigeria. "Raji ba fa wurin shakatawa bane, nima ban taba bi ba amma nasan labarinsa. Wahala ce kawai harda fada wani lokacin" "To ba sai mu kafa tarihi ba" cewar Yousuf da yake jin hausa sosai kasancewar babansa ba yarensu daya da Nasara ba. Hausar Nijar suke yi mai kamanceceniya da Sakkwatanci. "Gaskiya ba dani ba" Awwab ya fada zai gudu daga falon saboda ya ga zasu jajibo masa wahala baiji ba bai gani ba. Magana har wurin Daddy saboda Raji ya matsa wai yau daya dai su dana. Ba don yaso ba aka ce ya tuna bakinsu ne ya karramasu da abinda suke so. Sai da suka yi la'asar suka bar gidan. Raji yasa Zahra ta hada masa 'yar jaka da irin pillon nan na matafiya a jirgi na kafada, abin rufa, touch light da 'yan kayan ciye ciye. Awwab da baya son zuwa sai gashi yana dariyar mugunta. Wai shi nan Raji hango abin yake kamar wani picnic ko camping. Yousuf ma da nasa shirin suka shige mota Awwab ya bi bayan dreban da daya motar. Sa'arsu daya yau tun safe garin dama da hazo da sanyi sanyi ba kamar jiya da suka iso ba. Amma fa abu tun ana dariya sai gasu sunyi kicin kicin da fuska zukata sun matso kusa. Layin mai ma ana alfarma. Ga rigimar cin layi da dai sauran abubuwa marasa dadi da kan biyo bayan zama a layin mai. Layi har dare ko tafiya suka ce zasu yi yadda wurin ya cushe da wahala su sami hanya ta dadin rai. Haka suka zauna dare ya gabato sauraye suka ce salamu alaikum sanyin da zai koresu bai kankama ba gara suma suyi full tank. Dukkansu jikinsu ya fada musu kuwa. Ba su suka koma gida ba sai hudun dare. Zahra da Ummi ne kadai ido biyu. Take taken Raji na makalewa Zahra yana ta korafin wahalar da yasha yasa Awwab bin Yousuf bangaren Ummi yana girgiza kai. Zahra na ta zillewa amma yaki barinta. Awwab na jin yana cewa da a gida suke wanka yake so ta taimaka masa yayi ya dauki kayan bukatarsa ya fita. Baya son ganin abinda zai dame shi yazo yana jin kunya shi da kanwarsa su zama surukan juna. Gara ya basu wuri ko yaya ne ta kula da mijinta. Radhiya ce ta fado masa a rai lokacin da yake kwanciya a kan bargon da ya jefa a kan kafet din dakin Emzee ya buga tsaki shi kadai yana ayyana wai ta cuce shi da yanzu shima...kwafa yayi kawai ya kwanta. "Kasan babu dadi ko? Ka dawo nan gadon zai ishemu" Yousuf yace da ya jiyo tsakin. "Its okay mantuwa nayi mai mahimmanci, kaji ina tsaki ko" a rayuwarsa babu abinda yake masa wahala kamar kwanciya kusa da mutane. Sai yayi ta ganin kamar zai takura musu kuma shima baya son tasu takurar. Karamar dariya yaji Yousuf yayi yana cewa "Raji yayi mana wayo. Mun sha wahala tare wato shi mai mata ya gudu" "Kai me kake jira" Awwab ya tambayeshi cikin duhun dakin yana fata kada yace abu guda suke so. Yinin yau kadai Yousuf din ya kwanta masa akwai ilimi amma a wani kamfani yake aiki ba likita bane. Ko me yasa jiya yaji Mama tace likita? "Da dai na fara shiri amma na kula kamar bazai yiwu ba." Yanayin maganarsa zaka san abin baiyi masa dadi ba sai dai a rayuwarsa bai yarda da cusa kai inda ba'a nemansa ba. Yana son Radhiya kuma kanwa ce gareshi har kullum amma jiya shi kadai yasan me ya gani suna yi da sunan cin abinci. "Allah Ya musanya maka da mafi alkhairi" "Amin, amma meyasa nake ji kamar kasan da wa nake?" Ya kuma yin dariya. Wayancewa yayi shima yana dariyar "Ban sani ba fa...kawai fatan alkhairi nake maka" "Sai ka tayani nema tunda kasan irin wadda nake so" Abin rufa Awwab yaja ya rufe kansa yana dariya lokacin da Yousuf yace kuma idan ya cigaba da jan rai zai ji ana biki a Nijar. Yasan so yake ya nuna masa ya gano wa yake so, shi kuma sai yaji kunya kada ya nuna abinda zai iya sosa ran Yousuf din. Da kyar suka yi sallar asuba jam'i su biyu don sai da aka idar Awwab ya iya farkawa saboda gajiyar da suka tara. *********** Yau da Radhiya akayi aikin breakfast ita da Ummi suna yi tana kara yi mata bayanin project dinta. Abin ya kayatar da Ummi matuka tace me zai hana tayi magana da Daddy sai a nema mata alfarmar samun adireshin wasu daga cikin matan da suka zauna tare a Sakkwato wadanda mazansu suka rasu ta saka su a sashen shirin nata da ta kira da (Hidden Heroes). "Ummi kece ta farko a cikinsu sai dai bazan iya saka ki a ciki ba saboda kuka zamuyi ta yi" tace da kwalla a idanunta. Da murmushinta mai ciwo tace "Allah Ya jikan Daadaa dinku. Halinku kadan ne da bambanci. Shi baya shagwaba irin wadda kika koyo wurin Nasara sai dai ya shagwaba wasu" Dan tsalle tayi tana son hirar babanta "Ummi yana shagwabani?" "Kamar ba gobe" ta amsa mata tana tuno rayuwarsu ta da murmushi na kufce mata. "Kema yana shagwabaki ko?" Ta tsare Ummin da idanu tana daga gira daya da wani dan banzan murmushi. "Kaniyarki, fita ki bani wuri" ta biyota da cokalin miya. Dariya ta saka ta gudu daki. "Na fa zata ta kintsu ashe nutsuwar ta karya ce" Ummi ta cewa kanta ita kadai tana girgiza kai. Mai hali baya fasa halinsa. Yau ma atampa ta saka amma riga da skirt. Ita kadai take juyi a gaban madubin bayan ta gama kwalliya ta karkata nan ta karkata can tana turo baki. "Fita mana kije kiyi a gabansa sai ya fada miki inda yake bukatar gyara idan akwai" Ta madubin ta harari Fauziyya kamar idanu zasu fado ta zagaya karbar Jawad zata shirya shi Fauziyyan tayi wanka sai ga Zahra kamar an korota ta shigo da sauri kana ganinta farkawarta kenan. "Jama'a na shiga dubu a gidan nan yau" "Me ya faru Adda?" Kasa fada tayi wai saboda Radhiya ba aure gareta ba. "Babu komai dai" "Ina fa babu komai dazu Mami ta aiko Zayyana da Femi wai tana ta zuba ido jiya da daddare kije ki karbe shi taji shiru ko kinzo kin kwanta ne kin bar mata shi. Bai dade da komawa bacci ba yana dakin Ummi" "Duk dad dinshi ya ja min" tace kamar tayi kuka. Fauziyya ta zauna a gefen gadon kusa da ita harda rage murya za'ayi gulma "kwana kika yi a can tare dashi?" Duka ta daka mata a cinya kafin tace "dawowa yayi fa duk cizon sauro yayi wani iri...daga hada masa ruwan wanka bacci ya daukeni" "Allah Sarki...kinsan bacci babu ta yadda baya zuwa. Ina fata dai kinyi ya isheki" Fauziyya tace tana dariyar ta dago me ya sami yayartata. Radhiya taji sun sakata a duhu ta kasa fahimtar me suke nufi ga son jin zancen na cinta tace "don Allah kuyi min bayani dalla dalla" "Ke da wannan bayanin sai a gidan Hamma" Fauziyya ta sake yin dariya. Bakinta ya kara budewa ta zama mai tsokana sosai. "Me? Aure zaiyi? To ni ina ruwana ai dai ba zuwa gidan zan rinka yi ba" tace tana bata rai. "Nasan ba fahimta zakiyi ba dama. Shirya Jawad ga kayansa nan zanyi wanka." Hannu ta mika zata dauki yaron ya zille ya koma wurin mamansa ta kuwa harare shi kamar sa'anta ta fice daga dakin tana mita. "Yara ku cigaba da yi min kyuya sai na baku mamaki. 'Yan mata zan rinka haifa in hanaku aurensu" "Allah Ya tashemu zaki fara ko, ke da wa kuma?" Ummi tace ta fito da Femi ya farka yana neman mamansa. "Jawad mana Ummi. Wai ni suke yiwa kyuya shi da Femi." "Baki iya yi musu yadda zasu sake dake bane. Harararsu fa take yi Ummi" Faduwar gaba taji tun da ya fara magana. Tabbas taji wannan kamshin mai shiga ko ina a jikinta yana tasiri amma duk a zatonta ya shigo ya fita ne. Ashe yana tsaye ne a bayanta da kofin kunu a hannu. Diba yayi zai koma daki ta fito tana mita. Tayi matukar kyau kayan sun kara fito da ita. Rashin sanin yana wurin karamin mayafi ta yafa da ya dan zame baya yadda gaban gashinta da ta daure da ribbon ya kwanta ya bayyana. "Kuma gara ta koya tun wuri don ni dai babu mai kawo min ajiyar 'ya'ya" Ummi ta fada tana kokarin barin wurin. "Ummi kawo shi ki gani" ta zura hannu zata karbi Femi dan albarka sai ya yarda "kin gani ko..." Zahra ce ta bude kofar dakin a lokacin yana ganinta ya soma kuka yana mika hannu da zillo. Radhiya taji kamar zai fadi ta mika mata shi. Tana karbarsa yayi shiru harda dora kansa a kafada ta shiga shafa masa baya. "Nima dai inzo in haifi nawa su rinka like min ina muku yanga" Ummi kada kai tayi ta fita tana murmushi da taji me take cewa. Sai yanzu Mama tayi mata wayar baby ya tashi don Ummi bata tashinsa yin wanka sai dai ta jira shi wai duk cikin 'ya'yan nasu shi tafi so dole ayi masa yadda yake so ba takura. "Waye ya fada miki yara masu likewa iyaye dadi ne dasu?" "Ba gashi kuna gayunku ba ke da Maman Jawad" "Allah Ya baki muna gefe ai musha kallo. Wa yaga Radhiya da baby" Zahra tace tana komawa dakin domin bawa Femi abinci. Satar kallon Awwab tayi da yake tsaye a bakin kofar dakin Emzee tun dazu ya tokare kafarsa da bango ya jingina. Hanyar fita tayi ya dakatar da ita. "Kinyi breakfast ne?" "Bana jin yunwa" tace a takaice. "Realy? Kwaikwayona kika soma yi kenan" yace yana matsowa inda take tsaye. Yadda take ganin yayi matukar kyau haka shima yake ganinta. "Kai ba gashi zaka sha kunu ba" ta dan tura baki tana lumshe idanu. "Na Yousuf ne..nima bana jin yunwa" ya sami kansa da cewa. Kawai don kada ya yarda shi take kwaikwayo har ya fassarata ta dauko kofi a cikin wata drawer mai kyan tsari dake gefen dinning table ta zuba kunu. Gefenta ya tsaya ya rage murya tana jin wani abu na kwasarta "ki dena yi mana addu'ar yara masu kyuya don nima ina da son kulawa kada su rinka shiga lokacina" Ta riga ta gama zuba kunun ta ajiye flask din da babu abinda zai hana ta sake shi yadda ta saki teaspoon din hannunta jiki na rawa saboda mamakin kalamansa. "Careful and please kisa babban mayafi" yace yana kashe mata ido sannan ya ajiye mata kofin hannunsa ya dauki wanda ta zuba yayi gaba ya barta da bude baki. Jiki a sake ta zauna zuciyarta da gangar jikinta suna neman karkata akalar tunaninta daga basarwa da jan aji zuwa sake fadawa cikin soyayyar Hammanta da bata taba fita a ranta ba. Ta dade da fahimtar manufar Yousuf a kanta amma sai tayi kamar bata sani ba saboda bata jin akwai wanda zata iya sakawa a gurbin da Awwab yake zaune cikin zuciyarta. Kwantar da kanta tayi akan table din tana bubbuga kafa "wai ni nake wahalar dashi ko shi yake wahalar dani...ahhhhhhh sai na rama nima" Ta fuskanci da gangan ma ya fadi maganar don yasan me zata yi mata. Shikenan a tafi a haka zata sake dammara don so take taji ya fada da bakinsa yana sonta kafin ya koma aiki. Kai so take ya sota fiye da yadda a baya yayi ikirari. Yaji ta a ransa kamar yadda take jinsa a nata. Kwalla taji ta taru a idonta...soyayyar da take yiwa Awwab kamar tafi karfin kirjinta take ji lokuta da dama. Amma shine ya iya shareta duk tsahon lokacin nan kawai don tabi umarnin Ummi a abinda yake gyara ga zumuntar danginsu. Don dai yayi sa'a tana son shi ne amma ba hakura zata yi ba idan ba sai ta rama. Ta nanatawa kanta kafin ta dauki kunun da ya ajiye mata ta shanye duk da ya huce sai dumi kawai. Karfe uku suka firfito Daddy yace su biya har Asokoro gidan Plateau state government house su gaishe da maman Arifah da take ta cigiyarsu. Taron matan gwamnoni ta taho Arifah tayi mata rakiya. Dakin Ummi taje shiryawa ta samu ta sanar da Tante gidan wa zasu je fa. "Kada kice min tsoronsu kike ji saboda abinda ya taba hadaku" "Ni bana son zuwa ne kawai" tace a sanyaye da gaske tana jin karayar zuciya. "Ina sojan 'yata ta shiga ta bar min wannan mai tsoron? Sunyi zaton suna da abinda zai kaiki kwadayi ne ina ga tun farko shiyasa suka kara rainaki." "Duk fa akan Ghazalatun nan ne" "Ai da baifi da ba amma Mairama tayi musu kawaici don a zauna lafiya. Ki saki jikinki in kunje idan ba haka ba za'ayi aurenku ne kina kin shiga dangin miji?" Shagwabar ce ta motsa tace "Ni nace zan aure shi ne Tante?" "Baki ce ba shiyasa tunda na kula Yousuf dina na sonki zan fadawa Papa" Tashi tayi da sauri zata gudu Nasara ta rinka dariya tace ta saka kayanta ta gani. Tana taimaka mata ta shirya tana bata sirrikan sake janyo Awwab gareta "idan na gaji da gulmar taku zaki wayi gari watarana kawai a kaiki gidansa an daura aure kuna bacci" "Kamar wata 'yar tsana" "Yi sauri kafin Mairama ta shigo ta fara mana fada daga ni har ke" Abaya ce ta gani a fada kalar lilac mai ado ruwan madara. Duwatsun jikinta kadan ne ba irin mai daukar ido daga nesa ba an jera su sunyi zagaye zagaye daga wuya har kasa a tsaye ta tsakiya. Gefen mayafin ma haka yake sai dai kafin tayi rolling sai da daura wani karamin dankwali saboda wancan yana da santsi kada ya zame ga maikon kanta. Kayan kwaliyar Laura Mercier take amfani dasu. Tayi light make up dinta tasa janbaki nude bayan tayi lining lebenta da lip liner purple. Sai ya tashi ya bada wata kala mai kyau. Wani killer smile ta saki tana kallon Tante tana gode mata a ranta. Matar nan ba karamin kulawa da gyara take bata ba. 'Ya take yi da ita da zuciya daya shiyasa itama ta bata matsayin da ya kamaceta na uwa. Garin yayi lufluf sanyin bai fara hana sukuni ba. Takalminta heel ne shiyasa tana tafiya taku daidai irin na matan da suka san kansu ta fito da karamar sling bag wadda babu komai sai tarkacen su hoda da wayarta a hannu. Tun daga kofar gidan Mami da suke jiranta saboda motocin a can aka ajiyesu Awwab yake kallonta ya kasa dauke ido. Wani mahaukacin kishi ne ya taso ya rufe shi da ya ga kamar duka hankula suna kanta ne. Itama shi take kallo tana murmushin da yake kara susuta tunaninsa. Gaskiya motar da zai ja yake so ta shiga ta zauna a kusa dashi. Da ka yayi mata alamar ta taho ai kuwa ta nufi motar. Sai da ta tsaya a gaba kamar zata bude ta juya wurinsu Fauziyya. "Adda wannan zaki tuka?" "Wannan Hamma ne zai ja" "Ohhh" ta juya ta koma jikin daya motar ta shiga baya ita da Zahra da Femi. Gaba kuma Zayyana ce da Jawad sai Fauziyya da zata ja su. "Rufe bakin mana loverboy" Raji yace da turanci suka tafa da Yousuf suna yiwa Awwab dariya. Wai shi zata yiwa haka ta sa masa rai ta basar. Ba don gudun fadan Ummi ba da babu inda zai je saboda bashi da kuzarin tukin ma. Wani kallo ya watsa musu suka sake kwashewa da dariya sannan suka shiga motar yana gaba Fauziyya na binsa a baya. "Radhiya ba sauki yau kin motsa mana Hamma. Jikina yana bani kamar da wuya ki koma France babu aure fa kila ma da dan guzuri" Zahra ce ta zunguro Fauziyya rainon Mama zata yi barin zance a gaban Zayyana. Jinsu kawai take tana murmushi da kewar 'yan uwanta Ibrahim abokin fada da Emzee mai lallabata. Da suna nan ko kallon wannan motar bazata yi ba. Radhiya tayi murmushi kawai zuciyarta fes. Masu sayar da irin lemukan nan da ake saka kankara a leda ta hango maltina yawunta ta tsinke. Da can bata iya sha har cewa suke giya ce. Zuwanta na karshe ta dandana shikenan ya zama abin shanta har da guzuri da zata koma. "Adda don Allah saya min maltina" "Wacce a ciki? Nima fakiriya ce irinki babu chanji a hannuna" Zahra ta amsa mata. Dan turo kanta tayi gaba "Adda Fauzinmu taimaka" "Ni da kika ki shirya min yaro harda harara" "Yanzu kullata ta kika yi a ranki kamar ba babba ba? An dai yi abin kunya" Yadda tayi maganar yasa su duka dariya. Zahra tace "Wani idan ya kalleki a haka dai zai ce irin high class babes dinnan ne. Sai an zauna dake a gane ashe 'yar soja ce mai balotelli" Rokon maltina ta cigaba duk junction amma Fauziyya taki saya. "Ki roki Hamma idan mun tsaya" "Roko zaki koya min?" Ta zaro idanu. "Kayan masoyi ai naki ne...ke da kuke sharing spoon meye don ya saya miki maltina?" Bata sake iya magana ba taji kunya ta koma ta zauna shiru har suka isa. Ita bata taba zuwa gidan ba. Su kuma rabon su da zuwa tun bikin Ghazalatu farkon tafiyar Awwab Ukraine. Su ne a gaba ita a karshe suka bi bayan mazan zuwa cikin gidan. Zahra ke ta sallama shiru ba'a amsa ba. Mai aiki ce ta leko daga baya lokacin Awwab ya fara jin haushin zuwan nasu tace su shigo Mummy tana sama za ta yi mata magana. "Kice mata su Zayyana ne" Zahra tace su duka suka sami wuri suka zauna a falon da mai aikin ta kaisu. Muryar mace tana kuka suka ji wata tana daga murya "Mummy ba fa zan koma ya kasheni ba" Kafin Mummy Gambo tace wani abu mai aikin ta fada mata suna da baki. "Su waye?" "Wai su Zayyana" A dan tsorace tace "ba dai falon kasan nan kika kawo min su ba ko" "Mummy ke kika ce nan zan rinka kawo bakinki" Ranta a bace kamar ta kai mata duka ta fasa tana huci. Karshenta sun ji hargagin Ghazalatu. Tsaki tayi tace ta kai musu abin sha tana saukowa. Bayan fitarta ta koma kallon Ghazalatu da ta rame tayi baki kamar ta dade tana cuta. Ga fuska a kumbure. Ido daya yayi ja jini ya kwanta. "Sami wuri ki kwanta zan kira Hussaina idan sun tafi ba aura masa ke akayi don ya kasheki ba" Cikin takun kasaita ta sauko ta ga falon nata a cike. Duk yadda taso daure fuska kasawa tayi tana ganin Jawad da Femi suna ta kai kawo babu mai shekara biyu cikinsu amma duka akwai girman jiki da lafiya. Iyayensu sun gaisheta harda Radhiya da bata gane ba ta dan saki fuska tana yiwa su Jawad wasa. "Yaya Mamin taku kowa lafiya ko?" Zayyana ce ta amsa da "lafiya kalau" "Madallah, ku masu gida ina cefane ko haka kuka zo min hannu na dukan aljihu?" Dariya ce su Fauziyya ke yi ta yake kowa ta ciki na ciki yadda ta yiwa Maminsu rashin mutumci musamman da bikin Ghazalatu. "Awwab yaushe a gari? Yaya aiki?" "Shekaranjiya muka zo da Zahra. Ga mijinta Raji" A ladabce Raji ya sake gaisheta don Yarbawa akwai ladabi sosai. Kyakyawan mutum a haka harda dan gemunsa na ustazai amma ita ce mai yadawa a dangi cewa Zahra ta rasa miji an buge da auren bayerabe. Sai gashi a gidanta ido ba mudu ba yasan kima tasan cewa babu tsiya a tare dashi. Kyakkyawar yarinyar da take ta wasa da Femi ta kalla "wannan fa, bakuwa kuka yi?" "Radhiyan Hamma Awwab ce" Fauziyya tace kai tsaye lokacin da Ghazalatu take saukowa. Ita da Mummyn suka zuba mata idanu sai ta basar duk da ta sake takura ta koma gaishe da Mummyn. Ghazalatu kamar ta juya ta koma don bakinciki. Radhiya dai da ta sani 'yar kauye mai askakken kai ce a haka kamar wata balarabiya. Murmushin da Radhiyan tayi tana kallon Awwab shi ya gaskakata mata ita saboda wannan dimple din nata. Mayar mata da martani yayi har yaso ya manta a ina suke. Kishi fal a cikin Ghazalatu ta kalli Awwab yadda ya sake zama babba ga cika ido. Sai zaman ya koma na kurame tunda akace Daddy Haroun baya nan. Mummy tana hango wautarsu Ghazalatu tana jin takaicin rabasu da Mummyn tayi. Nura dukanta yake kamar jaka idan Mummy tayi magana sai Hussaina tace Ghazalatun ce bata da tarbiya. Kudi ne suka so tatsa Mummy taki saki shiyasa suka dorawa 'yarta karan tsana. Drinks aka kawo harda maltina amma Radhiya ta kasa sha musamma da Ghazalatu ta rinka jan Awwab da hirar aiki da course da taji yaje Ukraine. "Muna jiran tsarabarmu" Tausayi take bashi yana son tambayar me ya sami idonta yana tunanin kada ya bata kunya sai yace "zan kawo miki kafin ki koma KT. Bari mu wuce muna sauri ne" "Da wuri haka Awwab ina zaku je, zaku dawo ku gaisa da Daddy ko" Fauziyya ce ta sake cafewa "gidan abokin baban Radhiya" Ghazalatu tace "a nan din? Nufina a Abujan nan? Cikin Nyanya hala" Cin fuska Awwab ya hade rai Zayyana ma da abin ya bata haushi tace "gidan gwamnan Plateau a Asokoro" Mummy sai ta hangame baki tsabar mamaki. Kai gidan gwamna ai da mutane kila dai maigadi ko irin gardiner dinnan. "Hamma kafin ya fara kira yace ya jimu shiru. Kasan halinsa da yaji Radhiya tazo Nigeria ya rinka damuwa kenan" Sakato Ghazalatu tayi tana kallon su "ba a Nigeria take ba?" Tace da mamaki Radhiya kunya ta kamata yadda su Zahra suke jindadin abinda suke yi musu. "Kakanta ya kaita France ai can take karatunta" Awwab kasa jurewa dramar matan yayi yace su fito haka. Harabar gidan Mummy ta rakosu tana takaicin me ya rabata da yayarta mai sonta da zuciya daya da yaranta. Ta dawo daga rakiyar Hussaina amma kunya harda ta Ummansu ta kasa fadawa kowa halin da ake ciki. Suna mota Fauziyya tace "dalla muna ta wasa ki maimakon ki turance su ko kiyi french ke da Yousuf tunda ba kowa ke jinsa ba ki tada hankalin 'yan bakinciki" "Naga alama kin fini rigima yanzu Adda" "Hmmm ai dole bakina ya bude in fada miki 'yan mata sun saka min miji a gaba da waya. Shi kuma ya fiye shiru shirun wai wulakanci babu kyau. Tuni na mike kafin ya dauko min qaya" "Su Fauziyya an iya kishi" "Allah Yasa my in law ya kyallo wata idan kunje garinsu" "Ba amin ba" Radhiya da Zayyana suka rinka dariya yadda yayyen nasu ke fadan sakuwa da sakuwa. An san da zuwansu gidan Excellency suna isa aka bude musu gate. Cikin girmamawa aka kaisu falon matar gidan. Bata da ji da kai kamar mijinta ta rinka jansu da hira tana fada musu me yiwuwa fa sai sun dawo cikin sati saboda jibi Excellency zai taho. "Munyi waya nake ce masa zaku zo yace gobe yana son ganinka da wuri Awwab wai akwai important issue da zakuyi discussing" "Ko maganar Arifah ce" da yake ta nuna sha'awar zuwa Ukraine masters yace sai ya tambayi Awwab yanayin kasar. Radhiya sai ta zaci ko maganar hadin aure ce kishinta ya motsa. Suna haka Radhiyan ta shigo tabi matan nan kowacce ta rungume tana murnar ganinsu. "Ashe duka kunzo babu gayyata. Mom kinga ni nake son zumunci dasu basa nemana. Captain ne nawa shi kam bama kwana uku bamu gaisa ba" Ta sake kunna Radhiya bata sani ba. Wancan karon Ghazalatu yanzu kuma Arifa. Itama haka zai zo yace ta hakura ya fara aurenta? Zaman sai taji ya isheta so take su tafi kawai. Tana kallo suka tashi suka bi wata kofa Mom dinta na cewa dama an dade ba a hadu ba yau tasan zasu sha hira ne. Haushin kowa ta rinka ji harda su Fauziyya. Basu dade ba suka dawo ta fada masa ne Excellency ya karbi nambar wayarsa a wurinta yace zai kira shi kada yaji waya bazata ya dauka wani abu ne. Suna dawowa yace zasu tafi Mom ta hada kowa da gift tana ta godiya. A jikin motar da matan suke Arifah tace musu gobe idan suna da lokaci me zai hana su je park. So take su saba da juna sosai. Zahra ta amince ko don mijinta mai zuwa camping a filling station. 💕********43. 💕 "Nima haka nayi tunani. Zauna Awwab. Duka wani protocol da gon kamata nabi domin sanin gaskiya nabi. Yanzu haka ina jiran kira daga Mr President ya bamu go ahead mu nemi ganawa da gwamnatin kasar domin a sake shi" "Kana nufin Babana Zayyan yana da rai duka tsahon shekarun nan a prison" hawaye ne mai zafi ya zubo masa baiyi yunkurin dakatar dashi ba. Dukkan bayanai Excellency da kansa yayi masa yaci kuka tamkar kankanin yaro. Zancen da girma kuma da nauyi. Gashi yace yayi shiru har su dawo saboda yana tsoron sakawa iyalinsa rai da abinda ba gaskiya ba. "Ka samo min hotonsa, na matarsa dana 'ya'yansa. Idan da hali harda copy na national identity card dinsu ko international passport domin mu tabbatar musu bashi da alaka da Liberia" Kamar anyi masa duka haka ya koma gida zuciyarsa tana ta bugu da karfi. Zahra bata dakinsa a nan ya kwana sai dai ko digo bai iya runtsawa ba. Kwana yayi yana tunanin ta yadda zai samo hotunan da ake bukata. Duk da yace kada kowa yaji dole ne ya nemi mai taya shi. Jira yayi sai da su Yousuf da Tante suka tafi airport zasu wuce Nijar, shi dai bai bisu ba su Radhiya ne suka tafi rakiya ya shiga bangaren Mama. Baba Hadir yana falo sai ya wayance da ganin Daadaa ya tafi. Mintu talatin bai cika ba ya kuma dawowa har yanzu yana falon ita ta tashi. Zama yayi kamar akan kaya yana jiran Baba Hadir ya fita ko ya koma daki shiru. Mama tun da ta dawo take karantarsa daga karshe tace wa mijinta ya basu wuri zasu gana da danta ta ga alama son aure yake yi. Baba Hadir ya girgiza hannuwa wai babu ruwansa ya tashi ya shiga ciki. Sai kuma ya kasa cewa komai. "Awwab ka fara bani tsoro. Akwai abinda ke damunka fa" Siririn hawaye ta gani ya ziraro daga idonsa ta soma tafa hannuwa "Radhiya ta sake cewa bata shirya auren bane?" "Ni ai na shirya so bana bukatar amincewarta" yace yana kakalo murmushi. "Good, me kake boye min?" Yanayin da ya shiga da Excellency yake masa bayani har tafi shi. Zainab kuka take rikewa Awwab yana bata baki da ta daure saboda kada a gane. Abubuwan da yake bukata ya zayyane mata tace zata yi masa kokari zuwa dare. Daurewa kawai ta rinka yi kada ayi saurin ganota musamman da Ibrahim da Emzee zasu dawo yau gidan zai kara cika. Dakinsu ta shiga cikin kayan Baba Hadir ta dukufa bincike. Bata yi mai yawa ba ta samo hotunan Zayyan da khakinsa shi da Hadir. Da wayo da dabara tasa Radhiya ta kawo mata passport dinta wai zata gani. Hadawa tayi da hotunan ta bawa Awwab cikin wata leda wai sako ne. Yana karba yaje yayi photocopy na passport din ya dawo mata dashi. Sauran hotunan ta waya ta tura masa duka yayi printing ya kaiwa Excellency. A hanyarsa ta komawa gida ya kira shi ya sanar dashi shugaban kasa da kansa ya nemi shugaban kasar Liberia zai bada umarnin a duba masa mai wannan suna a prison din. Wannan dare ma bacci barawo da kyar ya dauki Awwab, Mama Zainab da Col. Nasiruddeen. Dare ne mai tsayi a garesu wanda a safiyarsa ne zasu ji dahir. Ayi ba ayi ba sai gabanin magariba wayar Excellency ta shigowa Awwab. "Karfe tara na safe zamu tashi gobe, Zayyan has been found" "Alhamdulillah" Awwab yace idanunsa na cika da kwalla. Baya jin komai don yayi kuka saboda abin kukan ne ya same su. A daren ya sanar da su Mami tafiyar gaggawa ta kama shi Lagos wai kamfanin jirgin da yake aiki zasu gabatar da wani shiri. Ita kadai ce karyar da ya iya nema ya fada musu. Rashin zamansa a gida yasa bashi da lokacin neman Radhiya abin har ya soma damunta. Tun daren da akayi masa wayar sai yau yaje wurin Ummi saboda yana gudun ta fahimci wani abu a tare dashi kamar yadda Mama tayi. Zancen tafiyar yayi mata tayi masa fatan alkhairi. Yaso ganin Radhiya sai dai tayi bacci da wuri period pain ya kwantar da ita. Da safe kafin ta tashi ya tafi sai labari taji wai ya tafi Lagos. Fada ta soma yiwa kanta na saurin bada kai da taso yi bata san babban aikin da yasa a gaba domin iyalansu gabadaya ba. Da yaje airport yayi mamakin ganin official plane din shugaban kasa aka bayar dungurungum domin dauko Lt Zayyan Tureta. Su tara ne duka a tawagar. Shi, gwamnan Plateau, Deputy chief of army staff, Chibuzor da wasu sojoji guda biyar. Gani yake kamar da shi yake tuka jirgin sai yafi haka gudu amma sannu sannu bata hana zuwa sai gasu sun sauka a filin jirgin Monrovia babban birnin kasar. Su ma sojoji suka turo domin daukarsu ana musu zancen tafiya hotel Excellency yace ko ruwa bazai iya sha ba sai ya ga Zayyan tare dasu. ********** Kararrawa aka buga lokacin cin abincin dare yayi 'yan prison din suka soma fitowa daga dakunansu da aka bude. Kusan kullum cin abincin tamkar yaki ake yinsa kowa na sauri ya sami abin arziki. Tafiyar nan tasa da dogayen kafafunsa yake yi cikin nutsuwa ya isa layin ya tsaya kenan wani kato yazo ya sha gabansa. Sai ya ja baya ya bashi wuri saboda gudun rigima. Sati uku da kwanaki da tafiyar Chibuzor dan guntun hope din da yake dashi gabadaya ya tafi. Fadawa kansa yake yi ya cigaba da hakuri da kaddarar rayuwarsa me yiwuwa shi da iyalinsa sai a lahira. Shi da kasarsa kuma sunyi bankwana kenan. Rikici ne ya kaure daga gaban inda ake rabon abincin garin dambe aka zubar da kulolin abincin a kasa. Mutane kuwa suka dira akansa suna wawaso ga gandirobobi suna ta kokarin raba su. Yau ma bashi da abinci kenan zaiyi kwanan yunwa ya juya a nutse zai koma dakinsu. Da rana wani tsoho ya barwa nasa saboda ya taho zai zauna irin shakiyan nan wani yasa masa kafa yayi tuntube ya fadi. Yanzu kuma abincin duka an zubar. Ya kusa isa dakinsu yaji da karfi ance. "LIEUTENANT ZAYYAN MUHAMMAD TURETA" Tunda ya shiga kurkukun nan sunansa 3810 sai ko mutanen da suka san sunansa kalilan amma su dinma numbar tasa suke kira. Gabansa ne yayi mugun faduwa ya juyo da sauri. Babban prison Warden dinne da kansa ya shigo wurin. Wannan salon tafiyar tasa da shi kadai ya iya kayarsa yayi zuwa gaban mutumin. Ga mamakinsa sai ya ga ya cire hularsa ya maketa a kasan hannu daya sannan ya gyara tsayuwa ya sara masa. Habawa sai idanu suka tattaru a kansu shi ma sai yayi saluting mutumin yana jin idonsa ya soma ruwa domin hasken da ya fara hangowa na rayuwar 'yanci "This way Sir" Chief Warden yace masa ya bi bayansa. Sun fara tafiya ya juya ya kalli prison din da jama'ar cikinsa sai ya tsaya at attention ya kame yayi saluting dinsu. Da yawansu su ma sai suka yi masa wadanda suka taba jin cewa soja ne suna taya shi murna. Wani office aka kaishi Chief Warden ya bashi takarda ya saka hannu a kai sannan ya kuma gyara tsayuwa. "Kai jarumi ne da ban taba ji ko ganin kamarsa ba. Kasarka bata san kana raye ba tsahon shekaru ashirin da biyu sai yau zaka koma gida. Ba kai nake tausayi ba sai ire irenka da dama da suke da rai a hannun abokan gaba ko kurkuku irin wannan batare da an sani ba. Goodbye Lieutenant" Musabaha suka yi sannan ya kuma nuna masa kofa suka fito tare. Wani gate da bai raba sanin akwai shi ba duk tsayin zamansa a wurin suka bi sai ga motoci biyar a jere na Nigerian Embassy dake Liberia a baya kuma wasu uku ne na sojojin kasar. Motar tsakiya aka nuna masa ya shiga yana jin kansa kamar a ire iren mafarkan da yake yi na komawa gida. Cikinta ma sojoji ne da sai suka yi saluting dinsa suka shiga aka tayar. Jiniya ce tun daga prison din har babban ofishin jakadancin Nigeria dake Liberia. Awwab ya kasa zaune ya kasa tsaye haka ma Excellency. Duka a waje suke daidai kofar shiga tare da Ambasadan suna tsaye zugar motocin nan suka jeru a gabansu. Kafin ya yunkura an bude masa kofa ya sako kafarsa waje sanye da takalmin roba da ya mutu murus. Kayan jikinsa a kode suke sosai. Fatarsa kuwa bai san cewa ta shiga wani yanayi ba sai da ya ga mutanen dake tsaye a wurin sun zuba masa ido. "Uncle" yaji ance da muryar da ya sani. Chibuzor ne ya taho wurinsa da hawaye yabe yabe a fuska. Zayyan ya rungume shi. "My son I owe you my life" "And I owe you mine" yaji wani ya fada daga bayansa. Sannu a hankali ya juya yana kallon mutumin dan lukuti ga tumbi amma komai nasa yana nuni da cewa ba karamin mutum bane. Ina yasan fuskar nan yake ta tunani. "Baban Alheran kayi hakuri banzo da wuri ba" Zuciyarsa ta nemi bugawa don bai manta mutumin da yake kiransa da wannan sunan ba. Sai yanzu yaso ganin kama. Bakinsa yana rawa yace "Baban Arifah? Col. Nasiruddeen?" Rungume shi yayi suka fashe da kuka a tare mutane na kallonsu wasu suna yi. Ga Awwab kuwa babu inda baya rawa a jikinsa. A yau ya yarda soja daban namiji daban. Duk yadda yake son ya dake kwanansa nawa yana kuka saboda jin cewa Babansa Zayyan yana nan amma babu tabbas sai ido ya gani. Shekarun da yawa amma tabbas shine wannan mutumin da ya ga duniya kuma duniya ta ganshi. Muryarsa tana rawa yace "kaine Tureta?" Yadda ya taba yi masa farkon haduwarsu. Zayyan ya dago kansa daga kafadar Excellency yayi masa murmushi "nine yaro. Ka sanni ne?" Tsigar jikin Awwab har tashi tayi a lokacin da ya kamo hannuwan Zayyan duka biyun "sunana Muhammad Awwab Mustapha...ka tuna ni?" Ya kare tambayar da kuka. Wasu sababbin hawayen suka sauko daga idanun Zayyan jikinsa shima yana rawa ya sanya hannuwansa biyu a gefen kumatun Awwab da suke tsayi kusan daya. "Awwab din Mairamata?" Awwab ya gyada kai nasa hawayen suna gudu kamar famfo baya tunanin yin komai domin tsayar dasu. "Major da Hadir fa?" "Suna cikin koshin lafiya" "Mairama?" "Na barota lafiya" "Alheran dinka?" "Tana jiran Daadaa yazo ya aura mata Awwab" yace yana murmushi mai hade da kuka. Zayyan ma sai ya fadada murmushinsa. "Cikin jikin Umminka?" "Alive and well sai munje gida zaka ga ko mene" "Awwab?" "Daadaa" "Nayi kewarku, nayi kuka, nayi hakuri nayi hauka duka a rashin sanin makomar rayuwata. Ku kaini gida...ku kaini wurin iyalina" Kankameshi Awwab yayi suna kuka sosai abin tausayi da tsinka zuciya. ********** 💕[11/2, 7:11 AM] 44.💕 *SAKAMAKON ALKHAIRI...ALKHAIRI NE* Awwani hudu bayan dauko shi Awwab da Excellency suka saka Zayyan a tsakiyarsu suna zaune a cikin jirgi domin komawa Nigeria. Sai da aka hadu so da takardun neman afuwa kuma mataimakin shugaban kasa yace zasu zo Nigeria officially bada hakuri. Sun kama hanya cikinsu babu wanda zai iya bacci a wannan kasar idan basu ga kafafun Zayyan sun sauka a kasar haihuwarsa ba. Babu wanda ya damu da wata tafiyar dare ko nisa. A lokacin da suke hawa jirgin Zayyan ji yake kamar ana zare masa wata kaya mai tsini daga cikin zuciyarsa. "Baban Alheran" Excellency ya kira shi ganin idanunsa sun kasa daina zubar hawaye. Kukansa kuwa kara raunana Awwab yake yi suke ta yi tare. Kallonsa yayi suka hada ido yaji mugun tausayinsa ya mamaye masa zuciya. Har yanzu kyakkyawan mutum ne da ya wadatu da arzikin kyakkyawar zuciya, amma yasha wahalar rayuwa fiye da zato da tsammani. Ciwon da yake tattare da rabuwa yafi karfi a gareshi domin shi yasan ya baro iyalinsa da rai ya azabtu da begen sake ganinsu sabanin su da suka dangana saboda tunanin ya rasu. Akwai lokutan da yake jin kamar zai zauce saboda kewarsu. Wani zubin kuma hakuri yake sakawa ransa, wasu lokutan kuma yayi kuka har sai yaji kamar bashi da sauran hawaye. "Baban Alheran kayi hakuri shine abinda zanyi ta fada maka har muje gida. Ni dasu Hadir da Mustapha duka zaton mutuwa muka yi maka" "Ka dena bani hakuri domin Allah Ya riga Ya warware min ciwon da yake raina. Ku bani labarin me ya faru daku da matata" "Bazaka jira mu koma ka nutsu ka huta ba?" "Labarin ne kadai zai sa na cigaba da dauriya har mu sauka. Idan ban manta ba ana cewa aski idan yazo gaban goshi..." yayi murmushi. A takaice Excellency ya labarta masa dalilin tunaninsu na cewa ya rasu, ya kare da cewa "sauran bayani zaka ji idan mun isa gida ka huta yanzu" Ruwa da abinci aka kawo musu amma shine ya fara daga hannu domin dakatar da air hostess din daga ajiye masa. "Daadaa kaci wani abu mana. Kafin mu taho ma ko ruwa baka sha ba duk wannan lokacin da aka bata" Awwab yace yana rokonsa. Murmushi yayi sai ka rantse Emzee ne a wurin yace "babu abinda zan sake ci ko sha sai naje gida in sha Allahu Mairama ta bani." Yana so ya tambayi Awwab ko tayi wani auren amma baya tunanin zuciyarsa zata iya daukan nauyi irin wannan komai kankantarsa a yanayin da yake ciki shiyasa ya ja bakinsa yayi shiru suka cigaba da tafiya kowa yana murmushin farinciki da jindadi. A awa uku mintuna kalilan ne babu a tafiyar suka iso Nnamdi Azikiwe International Airport na birnin tarayya Abuja. Jirgin yana sauka Zayyan sai ya soma jin kamar mafarki yake yi. Anya shi din da ya yi bacci ya farka a kuntataccen dakin kurkuku dazu da safe wanda suke sharing shi da mutane shida kowa akan katifa mara kyaun gani a wata kasar da ko sunanta baya son ji shine yake sauka a kasa mai dimbin daraja kamar Nigeria? Ana bude kofa ya hango hasken lantarki na ciki da harabar filin jirgin saboda dare sai yaji wasu zafafan hawayen da suka fi na dazu. Excellency ya nuna masa kofa da murmushi a fuskarsa "ka fara fita". Sannu a hankali yake takowa ga wasu sojoji kowa da bindiga a hannu suna jiran saukowarsa. Sojijin da suke da alaka ne da binciken dawowar dan uwansu bayan shekaru masu yawa a prison. Babu abinda yake kallo sai kwaltar dake shimfide a makeken filin da jiragen suke sauka da tashi. Kafarsa na taka kasa ya sake fashewa da kuka. Wani soja ya daga murya yace "Atteeeeention!" Sauran suka jeru a layi guda kowanne ya gyara daga bindigarsa sai kuma suka sauke suka sarawa jarumin jarumai mazan fama Lt. Zayyan Tureta domin duk da sai an sake ji daga bakinsa amma basu sami wani dalili na karyata komai nasa ba a bisa bincikensu. Ayya, sake karyar da zuciyarsa suka yi ya daure ya kame shima cikin kayansa na kurkuku ya sara musu sannan kawai ya fadi ya kai goshinsa kasa domin nuna tsantsar godiya ga Sarkin Sarauta wanda MulkinSa shine cikakken Mulki Allah Azza wa Jallah. Sujjada yayi ya rinka kwararo kirari ga Ubangijin sammai da kassai yana hamdala da ganin wannan rana. Shi shaida ne akan kansa cewa ba don Allah Ya so shi ba da tuni ya sami tabin kwakwalwa a prison dinnan saboda yawan tunani. Sumbatar wannan kasar da muka raina, muke zubar da jini, zina, sata da manya manyan laifuka akai yayi saboda shi uwa ya dauketa wadda idan 'ya'yanta sun lalace ba ita bace ta lalace sai dai a kawo mata gyara. A yayin da daruruwan mutane suke fatan budewar kofar da zasu bar Nigeria idan suka tafi ko ta halin kaka bazasu dawo ba mutane irin Zayyan da dama zasu iya fansar da rayuwarsu domin suyi yini guda da iyalansu a cikin wannan kasa. Tabbas Nigeria bata lalace ba sai dai a cikin 'ya'yanta akwai bara gurbi. Ya Allah Kayi mana maganinsu Ka shiryemu baki daya. Baso wani bata lokaci a airport din ba motocin mai girma gwamna dana sojoji zuga guda suka rankaya zuwa ga babbar headquarter dinsu. Dare ya riga yayi ana neman goman dare amma ga mamakin Awwab sai yake ganin baban nasu da kuzari babu alamun gajiya ko yunwa. Shi da yayi shekara ashirin da biyu yana jiran wannan rana ba karamin abu bane zai sarar masa da gwiwa bayan isowarta. Excellency ne yake masa bayani da cewa zai amsa tambayoyi ne domin keeping record da binciken da ba'a rasa ba kamar yadda aka yiwa Chibuzor. Idan yana so zaiyi magana a barshi ya wuce wurin iyalinsa gobe ya dawo. Wani irin kallon anya kana tausayina ya yiwa Excellency din yana komawa Zayyan dinsa na da "idan akace maka zan fito gobe sai ka yarda?" Dariya yayi "ina zan yarda kuwa Baban Alheran....to muje in sha Allah ba dadewa zamuyi ba" "Suna Sumaila ne ko ta zauna a Sakkwato?" "Duka muna nan Abuja Daadaa, ka shiga ku gama mu tafi gida" Awwab yace yana dauko wayarsa daga aljihu. "Mu gani Awwab" Zayyan ya mika hannu zai ga abin mamaki. Juya wayar ya rinka yi yana shafawa "Allah mai Iko, a prison dinmu na kan hango su a hannun wasu maaikatan sai aka ce wai cellular ce. Ni dai nayi mamaki sosai ace 'yar wannan abar ita ce waya yanzu. Kuma kamar nawa take?" Maimakon amsa kuka ya sake sake Awwab. Duniya ta cigaba sosai amma Zayyan bai sani ba saboda a prison da yake na masu manyan laifuka ne sosai wadanda gwamnati bata musu sassauci. Musamman ake kai firsunonin yaki da 'yan tawaye wadanda suka kawo asarar rayuwa da dama da dukiya a kasar. "Yi hakuri na dena magana tunda kuka nake saka ka" suka rungume juna sannan Awwab yace ya tsaya tare da Excellency da Chibuzor Zayyan a tsakiya ya mikawa wani soja wayarsa ya daukesu a hoto fuskar kowa cikinsu a sake. Ai da ya nunawa Zayyan sai ga dariya yana kada kai "kara mana daya dai na sake gani" Awwab ya yi dariya a ransa yana ayyana irin abinda Alheran zata aikata ne idan abu ya burgeta. Wata matsananciyar kewarta ta soki zuciyarsa ya fara matsuwa da su tafi gida haka. Hoton Chibuzor ya daukesu su biyu dashi da Zayyan sun sakala hannuwa a kafadun juna sannan aka shige dashi wani daki da manyan sojoji aka rufe kofa. Tambayoyi ne dai kamar bazasu kare ba daga manya manyansu da aka hada comittee na bincike akansa. Komai nasu anayi ne bisa tsari daki daki. Da ya gama bayani a dauko wani. Suna yi suna duba takardun da aka basu daga can Liberia da kuma information da suke dashi akansa saboda har file dinsa sai da aka binciko wanda aka buga masa KIA wato killed in action. Sai gashi suna bin komai da kyau aka gane gaskiyarsa daga kwanakin wata da abubuwan suka gudana. Babu wanda ya iya tafiya saboda su ma takaitaccen lokaci Mr President ya basu su hada komai. Ga Excellency shima nasu ne tsohon soja ya roki alfarma shima. Lokaci ne da siyasa ta gabato zabe saura wata uku. Dawowar Zayyan wata gagarumar sa'a ce da dama da ta fadowa shugaban kasa mai ci a lokacin zaiyi amfani da ita wurin karkafa kamfen dinsa. A matse yake da ya samu a fito da komai fili domin duniya ta shaida irin kokarinsa da jajircewa. Su kansu sojojin yana son samun hadin kansu ne. Da farko ranar da aka ce masa gwamnan Plateau na son magana dashi kamar bazai amince da wuri ba saboda dan jam'iyyar hamayyarsu ne wanda suka tsayar da wani jajirtaccen tsohon soja a matsayin dan takarar shugaban kasa. Sai da yaji me yake faruwa shine fa ya sako kansa ayi dashi. Shine fa tun daga saukar jirgin da ya dauko su zuwa yanzu ana ta daukar komai a video ne da hoto. Idan komai ya tafi daidai a saki al'ummar Nigeria ta shaida. Karfe uku na dare ranar talata shabiyu ga watan november 2015 aka kammala bincike akan Lt Zayyan Muhammad Tureta. Babu wanda bai nuna gajiyawa ba sai shi kadai. Da sun bukaci a wayi gari a haka da matukar wahala su ga gazawarsa. Ko da ba a filin training bane, Zayyan ya horo matukar horuwa da hakuri da juriya a zaman gidan yari. Wani Lt. Gen mai mukami daidai da Cheif of army staff ne ya fara tasowa zuwa gaban kujerar da Zayyan yake zaune sai ya mike shima. Hannu ya mika masa yana murmushi da alama shine yake shugabantar committee din. "Welcome home Lieutenant" Zayyan ya karbi hannun ya rike kafin kuma ya gyara tsayuwarsa. Sauran mutum hudun da akayi tare dasu kowa yazo ya bashi hannu suka gama sannan shugabansu a zaman da ya fisu nuna shekaru ya murmusa. "Nasan akwai dan sauran kananun abubuwa da suka rage kamar cike-ciken takardu da sake daukar biodata dinka. Da kuma daukar statement din Rtd Major Mustapha da Rtd Lt Hadir. Amma duk da haka ina da tabbacin cewa a karshen komai da zamu iya gamawa a cikin sati guda kaine zaka fito da nasara kamar yadda muke tsammani." Kansa ya sunkuyar kawai, emotions kala kala suna kai kawo a zuciyarsa. Mutumin ya sake kallonsa yace "kana da ra'ayin cigaba da bautawa kasarmu ko kafi son yin retire? Wannan tambaya ce da ya kamata nayi maka idan an kare komai..." ya dakata yana dariya "but I realy can't wait naji amsarka" Zayyan ya kalli mutanen nan daya bayan daya. Dukkaninsu a shekaru sun girme masa amma kayan jikinsu sune suka fi komai fito da cikarsu a matsayin zaratan sojoji irin wadanda kasa take tinkaho dasu. "With all due respect Sir, I remain a soldier" Gyada kai suke yi in approval. Shugaban ya kallesu sannan ya dafa kafadar Zayyan yace "Although unofficial amma bazan iya tafiya gida ba batare da na gabatar muku da precious mutum kamar wannan ba. GENERALS, I GIVE YOU A HERO LIKE NO OTHER...MAJOR GENERAL ZAYYAN MUHAMMAD TURETA" Gaisawa suka sake yi dashi sannan shugaban ya sake cewa Zayyan "strictly unofficial" wato yana nufin yayi shiru har sai sun gama. Doki ne kawai ya debe shi da yadda Zayyan din ya burge shi. Bude musu kofa akayi daga waje aka kaishi wani babban hall sanyin AC na ratsa ko ina. Chibuzor yana ta gyangyadi, Awwab na kallon agogo. Shi kuwa Excellency kamar ba dare ba amsa waya yake ta yi ta 'yan uwansa 'yan siyasa da suke akan kayar zabe mai zuwa. Basu sha wahalar shawo kan Zayyan akan ya hakura gobe zasu kaishi gida ba saboda shima ya san yanzu dare yayi da yawa kada ya firgita iyalin nasa. Kalle kallen garin yake kamar ba cikin duniyar da ya sani ba har suka isa gidan gwamnatin Plateau din. Maman Arifah tasan maigidan nata zai zo da baki amma bata san ko su waye ba. Dawowa cikin dare da baki kuwa ba sabon abu bane ga 'yan siyasa irinsa bare ma saboda harka da kamfen. Dakunan da za'a basu a gyare ga abinci sai da Zayyan fa yaci alwashin wallahi shi da abinci sai na matarsa. Awwab out of solidarity sai yaki ci shi ma. Chibuzor ne kawai yaci bacci ya kwashe shi. Awwab da Zayyan kuwa sabuwar hira suka bude idanunsu sun soye. Hirar dai game da iyalinsa ne shiyasa Awwab ya rinka kaucewa wasu abubuwan saboda yana gudun tayar masa da hankali daga dawowarsa. Ai bazai so jin kalubalen da suka fuskanta su duka gidajen uku ba kafin komai ya daidaita yanzu. Zayyan tuni ya fahimce shi. Dama can yana da saurin karantar mutane shiyasa ya hakura aka mayar da hirar ta Alheran. Ai kuwa baiyi danasani ba don ya sha dariya sosai. Bayan sallar asuba Excellency ya kawo musu kayan sakawa da kansa. Duka kayansa ne dai sun yiwa duka su ukun har Chibuzor yawa. "Ko nasa a dinko maka kaya kafin muzo tafiya anjima?" "Na fuskanci kamar da gayya kake son ja min lokaci. Wane irin dinki kuma ana zaune kalau." "Kasan Allah bazaka je wurin Maman Alheran a haka ba. Infact mai aski za'a dauko yazo ya aske maka wannan kasumbar a gyara fuska sannan kayi wanka. Ko so kake su rinka mafarkinka idan kaje a haka?" "Baka tausayi na ne ko? To askin ma bazanyi ba" Zayyan ya koma ya zauna ya bata rai. Excellency yace idan ta kama ya danne shi zai danne shi ne ayi askin kuma a kulle shi a bandaki yayi wanka. Awwab yana kallonsu yana dariyar yadda suke wannan rigima. Rtd Col Nasiruddeen tamkar babban wa yake ga Zayyan. Ya dauke shi kamar kaninsa da suka fito ciki daya. Sarai ya fahimci yana kewar iyalinsa amma ko yaki ko yaso bazai barshi yaje garesu a mummunar kama ba. "Kai Awwab kalli babanka da kyau banda aski me ya kamata ayi masa" yace a commanding voice. Shima bai tsira ba sai da ya sami guzurin harara daga Daadaa. Ya daga kai yace "da dai zamu samu a gyara harda farce" "Kai Awwab haka zaka yi min?" Yace da muryar ban tausayi. Excellency bai saurare shi ba ya kira PA dinsa ya fada masa abubuwan da yake bukata saboda yana so yau Zayyan yayi sallar azahar a cikin iyalinsa. Harkar kudi sai da kudi. Karfe goma na safiyar laraba an siyowa Zayyan kaya readymade shadda da yaduka kala goma da takalma. Shima wai kawai don ya zabi wanda zai saka ne. An dauko mutum biyu daga wani sanannen wurin aski na zama masu shegen tsada kamar idan anyi askin baza'a kuma yi ba. Suna zuwa suka fara aiki. Mutum daya yana askin dayan kuwa dakalalliyar kafa da faratan Zayyan ya tasarma da gyara. Bakinsa bude yana ta al'ajabi wai ace zamani ya kai harda masu gyaran kaushi. Ana wannan aikin Awwab ya samu ya kebe kansa ya kira Mama. Cikin rawar jiki ta dauka a can kuryar dakinta duk da cewa ma babu kowa a bangaren nata sai Ibrahim da Emzee suna nasu dakin. "Awwab yaya" tace cikin tashin hankali. Jiya da kyar ta iya bacci tana ta juye juye ga fargabar kada ta kira taji mummunan labari ko wani yaji. "Mama na turo miki sako ta whatsapp. Ki duba zan sake kiranki" yace yana karamar dariya. Ita ta fara kashe wayar don sauri ta duba whatsapp dinta. Alamun Awwab ya turo mata hoto ta gani. Hannu na rawa ta bude. Bata san lokacin da ta saki wayarta ta fadi a kasa ba ganin hotonsa da mutumin da babu tantama aminin mijinta ne. "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un. Zayyan...." dukawa tayi ta dauki wayar ta sake kunnawa daidai da kiran Awwab ya shigo. Kuka kawai ta fashe dashi "Awwab kuna ina?" "Zamu taho daga gidan baban Arifah tare muke. A nan gida zamuyi azahar in sha Allahu. Sai dai tun jiya yaki cin komai wai sai yazo gida zaici na Ummi" Dariya tayi ga hawaye a idanunta "Zayyan kenan, yaushe Mairama zata iya girki idan ta ganshi. Amma kada ka damu abincinta zai ci in sha Allah. Sai kun iso" Mayafi ta yafa ta fita zuwa gidan Ummi. Baby Zayyan yana can a bayanta tun da tayi masa wanka. Tayi mamakin fitowar Maman saboda sun hanata yin komai ita da Mami. "Jikin ne Zainab?" Ta tambaya da kulawa. Jiya tsabar damuwa kasa komai tayi sai tsananin fargaba. Da aka dameta da tambaya tace zazzabi ne da ciwon kai suke damunta. Karshe dai Mami tace a dage taron sunan da ya kamata suyi a jibi sai wani satin ta kara samun sauki. A ganinsu cikar da gidan yake yi ne ya hanata hutawa. 'Yan uwa masu tahowa a yau kenan duka ta dakatar dasu da kanta. Bata san me zai faru ba amma bata da wani kuzarin yi taron suna wanda su Ummi ne suka takura sai anyi. "Na ware sosai. Gajiya nayi na fito, kina da garin masara kiyi min tuwo? Miyar kukar rannan kinsan ta min dadi sosai" "Kinyi sa'a akwai saura kuwa." Fauziyya na wurin tace bari ta yi Mama tayi saurin cewa akwai fruits a bangarenta ko zasuyi fruitsalad kada su lalace. Radhiya taje ta kira suyi tare duk tayi laushi saboda rashin wayar Awwab da shareta da ya rinka yi kwana biyu. Ta ma kudurta a ranta ta dena basarwa idan ma dalilin haka ya janyo ya dena kulata. Ummi bata kawo komai ba taje ta jika busasshen kifinta da ruwan zafi ta bara ta wanke shi tas. Bata rabo da jajjage ba bata lokaci ta hada wake, naman sa da kifin nan ta soma dafawa tare da daddawa da gishiri bayan ta kara albasa da kayan kamshinta da Innawuro take hada mata garin tafarnuwa, citta, kaninfari da masoro. Maggi sai miya ta dauko dahuwa. Girkin baifi na mutum uku zata yi ba yadda zai ishi Mama har dumame. Tana yi suna taba hira Mama sai ta kalleta ta kawar da kai ta share kwalla. Mairama komai nata da nutsuwa take yinsa gwanin sha'awa. Sabon flask da ba'a taba budewa ba Mama tasa Radhiya da suke aikin fruitsalad ta kawo mata ta zuba tuwon da ta kukkulle a leda. "Yau kice da Baba Hadir za'a ci tuwon nan" "Ko daya ki boye min a dakinki sai anjima zan zo naci" Mama tace tana mikewa. "A daki kuma? A kawo miki mana" "Ke dai ajiye min ko a nan ne kada a taba. Da zaki taimaka min da wannan shayin naki mai kayan kamshi da kin gama min komai" Ummi ta girgiza kai "anya baki kunso wani ba? Wannan abu kamar me yaron ciki" "Rufan asiri ina fama da kaina. Zainabu tayi sanyi in fada miki. Idan ba gani nayi ya fara takawa da kafarsa ba ko kallon babansu na dena yi" Me Ummi zata yi kuwa banda dariyar mugunta. Allah Sarki Mama an ga haza. Dakinta suka koma da hira da dabara Mama tasa ta kuma gyara shi duk da ma Radhiya ta gyara da safe ta wanke toilet. Amma Mama tace wai ana sanyin nan da yakunno kai gadan gadan ina ita ina bedsheet single. Ta fito da mai hade da duvet ta shimfida mana. A take Ummi ta fara zargin wani abu amma duk iya tunaninta ta kasa. Wani mai masifar kyau da laushi tsarabar da Radhiya tayi musu su uku zuwanta na karshe kafin wannan ta shimfida. Tana gamawa Daadaa wato baby Zayyan ya farka. Yana cinyar Mama dama da zata gyara gadon. Shigewa tayi tana wanka zuciyarta na tunanin manufar Mama. Gabanta ne ya fadi da tayi tunanin ko shammatarta akayi ne aka daura mata aure? Idan ba haka ba meye na sa ta a gaba ta gyara daki. Hmmm zasu sha mamaki kuwa idan aka nemi turo wani cikin rayuwar da bazata taba sake irinta ba tunda ta rasa Sojanta. ********** Shabiyu da rabi kowa yayi wanka mata na gidan Ummi maza na bangaren Mama wurin Raji suna ta hira. Mama ta koma wurin Ummi ta sallami duka yaran nan zuwa gidanta tace baki zasu yi zata kira su su gaishe su. Ya rage daga ita sai Mami da Ummi. Zahra ce karshen fitan tana tafiya Mami tace "Wallahi Zainab mun gaji da wannan nuku nukun naki. Yanzu Daddy yace wai Excellency ma ya kirasu su dawo gida, suna hanya shi da Baba Hadir. Kin saka mu a duhu" Kwalla ta share duk yadda taso daurewa "kuyi hakuri nan da mintuna kadan ne komai zai fito" ********** Zayyan kallon kansa yayi yana karawa. Babu abinda ya kai tsafta da gyara dadi. Shi da mayar da jikinsa da yin kyau sosai sai an kwana biyu amma ko a haka sai dai ace Alhamdulillahi. Fuskarsa ta fito an gyare shi sosai. Wanka kuwa kamar bazai fito ba saboda jindadin ruwan da yayi da yadda yake cire dattin jikinsa. Lallausan yadi irin na masu hannu da shuni fari kal Awwab ya zaba masa a cikin kayan da aka siyo da bakar hula. Yau ya ga me ake kira turare designer da ko sunansa bai taba ji ba a da. Komai na shiryawa hatta links din hannu Awwab ne ya saka masa. Shima yayi wanka amma kayansa ya mayar suka fito duka aka dunguma motocin da suke jiransu. Yau mota biyu akayi saboda gwamna baya son a gane shine. Tafiyar minti shabiyar suka shigo cikin estate din bangaren gidajen guda uku da suke gefe da gefe da juna. Ana tsayawa Zayyan ya damki hannun Awwab. "Tabani in tabbatar nine" yace muryarsa tana rawa da iyakar gaskiyarsa. Awwab sai ya kara karfin rikon dake tsakanin hannuwansu. Gabansu duka faduwa yake Zayyan ya runtse ido ya kuma budewa a hankali yake cewa "Ya Allah kasa ba mafarki nake yi ba. Idan kuma mafarki ne Allah kasa na mutu a cikinsa" Hannunsa Awwab ya sake rikewa suka fara takawa sannu a hankali bangaren Mairama Ali Gidado uwar Alheran da Muhammad Zayyan. "Ba mafarki kake yi ba Daadaa. Ka tsaya a nan minti daya in fara shiga" yace lokacin da suka taka matattakala biyun da ake hawa kafin ya shiga gidan. Da sallama ya shiga ya sami iyayen nasa duka a zazzaune sun saka Mama a gaba harda Major ana son jin bayaninta. Tana ganin Awwab ta mike sa sauri. "Yauwa Awwab kun iso? Ina yake?" Sai suka kara daurewa kowa kai da Awwab yace yana bakin kofa zai shigo dashi. Komawa yayi da baya ya bude kofar ya riko hannuwan Zayyan suna tsaye da Excellency ya iso wurin. Awwab ne ya daga labule yayin da muryar Zayyan ta karade falon a lokacin da yake cewa "Assalamu alaikum" [11/2, 7:11 AM]🏽 ]🏽 : 45💕 Gabadayansa ya bayyana a gabansu kafin muryar ta gama shiga kunnuwansu. "Daddy, Baba...." Awwab ya soma cewa sai dai tuni Zayyan yayi gaba haka ma Daddy din da Baba sun taso daga wurin zamansu sun tare shi a tsakiyar falon. "Zzzzayyyannn kaine?" Baba Hadir yace da karfinsa. Manyan maza magidanta duniya ta sanyasu kuka tamkar yara. A wannan lokacin Hadir ne tsaye a gaban Zayyan dinsa. Hannuwansa yasa yana shafa shi kafin su kankame juna. Major da ya tabbata ba mafarki ne ba ya ware hannuwansa ya rungume su su duka biyun a tare yana nasa hawayen. Excellency ma nasa yake yi a gefe yana jinjina karfin soyayyar wadannan mutane. Duk abinda suke yi Mairama tana zaune kamar an dasata ta kasa motsi. Tana iya jiyo kukan Mami da Mama sama sama ita kuwa ta kasa. Wai shin ta cigaba da zama ne a wurin tana kallon Sojanta ko kuwa ta tashi itama taje ta rungume shi ko sau daya ne kafin ta farka daga wannan daddadan mafarki. Tunda take mafarkin Zayyan bata taba irin wannan da zata gansu a wuri daya duka tare ba. Ina ma Radhiya da Emzee zasu shigo suma su karasa cike mata mafarkin. Tayi nisa a wannan tunani bata san Zayyan ya iso gabanta ya duka ba. Hannuwanta da ya rike masu laushi wani irin shock yaji na soyayya, tausayi da girmamawa a gareta da ta dauki shekaru ashirin da biyu tana dakon soyayyarsa bata yi aure ba. Runtse idanu tayi tana ayyana da gaske ne haka Zayyan zai dawo mata duk ya rame? Ashe kuwa zata dauki lokaci wurin ganin ta ciyar dashi duk abinda zai taimaka ya sake gina masa jiki. Rikon da yayiwa hannunta da kakkarfan hannunsa sai kuma yatsansa da yasa yana kore mata hawayen dake gudana a fuskarta batare da ta sani ba shine ya sanyata dawo cikin hayyacinta daga tunanin da tayi zurfi tana yi. Tsigar jikinta ke tashi a lokacin da Zayyan ya mikar da ita tsaye ya dora hannuwansa akan kafadunta yana tayata kukan. "Wai kuka zamuyi ta yi ne? Bazaki yiwa mijinki barka da dawowa ba?" Yayi maganar kamar baya so saboda shaukin dake dibarsa. Wani hawayen ta matse ta hanyar runtse idanunta sannan ta budesu ta kalle shi da kyau wani abu yana sauka a kahon zuciyarta. A hankali ta daga hannunta daya ta shafa kumatunsa da wahala ta ramar. "Ashe ba mafarki nake yi ba" tace lokaci guda ta sulale a jikinsa ta fadi sumammiya. "Fillo" ya kira sunanta hankalinsa a tashe. Mama ta daure tace ya kwantar da hankalinsa abin ne yayi mata yawa. Ita kuma Mami ta samo ruwa a kitchen. Ana shafa mata ta bude idanu suka sauka acikin na Zayyan. "Da gaske ba mafarki nake yi ba?" Hawaye na gudana a idanunta take yi masa wannan tambaya. "Nima tsoro nake kada a tasheni daga bacci" "Ina ka tafi ka barni?" Tace tana fashewa da wani irin kuka. "Wurin da ko makiyina bana fatan yaje. Kiyi hakuri Fillo na aureki na barki cikin..." Kai ta shiga kadawa tana daga zaune akan kujerar da aka kwantar da ita da ta suma "kada kace komai sai godiyar Allah" Sun bawa kowa na wurin tausayi. Major ya katse maganar tasu saboda kada aji kunya gasu a wurin ga Awwab da yake ta aikin share kwalla ya zama a koke. Zayyan ya dago ya sake kallonsu yana fitar da murmushin mai karawa fuskarsa annuri. Ya tambayi Awwab "ina kannenka?" Da sauri ya nemi nambar Zahra tana dauka yace su zo su duka falon Ummi anyi bako. Duka suka taho harda Raji. Baby Zayyan yana kafadar yayansa Ibrahim wanda Allah Ya sanyawa kaunarsa daga haduwarsu jiya. Daya bayan daya suka shigo falon. Kowa na zaune banda Awwab da yake daga gefen kofa sai kuma wani dogon mutum da suna fara shigowa ya tashi yana murmushi. Awwab yace da kannen nasa da dan karfi "introduce yourselves" Radhiya ta juyo suka hada ido ta kawar da kai ita tana fushi kuma a ranta bata da niyar fadin nata sunan. Fauziyya ce ta farko ta matso gabansa zata gaishe shi ya mika hannu ya karbi Jawad "Fauziyya?" Tayi mamaki har ya nuna a idanunta. Shi kuwa ya tuna ta ne kasancewar duka 'ya'yan Major ita kadai ya sani fara sauran duka wankan tawarda suke. Yaronta ya bata saboda ganin wani da yayi a hannun ta kusa da ita ya karbe shi shima "Zahra?" Duk da bata sanshi ba taji dadi ko waye wannan mutumin mai kwarjini itama ya santa. Wani jaririn ya kuma gani a hannun wani matashi da babu tantama kamanni sun nuna dan Zainab da Hadir ne. Kafin ya ambaci sunansa Ibrahim yana murmushi tare da mika masa yaron yace cikin alfahari "Ibrahim Hadir da Zayyan Hadir" Zayyan ya juya ya kalli Hadir ya yi murmushi sannan ya bashi yaron. Wata 'yar budurwa ya gani ta kusa da wadda yake kallo tun shigowarsu wato Radhiya ta turo ta gaba ita kuma sai kunya take ji ya dan rage tsayi "kema in daukeki ne?" 'Yan uwanta ta kalla ta dan marairaice a kunyace "a'a nima ka fadi sunana" Ibrahim ya girgiza kai, ashe bata dena shagwaba ba. Ji yadda take tale baki ita da ta gama secondary. "Kiyi hakuri ki fada min da kanki inyi miki babbar kyauta" "Zayyanatu Mustapha" tace saboda taji Ibrahim ma ya fadi harda sunan babansu. Baki bude Zayyan ya kalli Major da ya kafe shi da ido kamar idan ya rufe zai bude ya neme shi ya rasa. Emzee ne ya rage a gabansa. Yaron tunda suka shigo yake ta kallon wannan mutumi yana tunanin a ina ya taba ganin fuska shigen wannan. Kallon kallo suke yi Zayyan yana jin kamar yana kallon younger version dinsa ne. Ashe Radhiya ma ta soma tunanin inda tasan fuskar ita da ta haddace kamanin mahaifinta a hoto. Emzee ya bude baki kenan ta matso da sauri tana jin jikinta yana rawa. Tunda suka shigo ya gama gane wacece dinsa shiyasa ma ya bar yi mata magana sai a karshe. "Kamar na san ka wallahi" tace muryarta a kasa kamar mai rada. Hannu yasa ya janyota gabansa sosai ta tsare shi da manyan idanunta "Alheran Radhiya baki gane Daadaa ba?" "Ya Allah" ta furta a gigice ta rungume shi tana kuka mai sauti. Bayanta kawai yake shafawa yana kokarin mayar da nasa hawayen. "Ehemm..ni sunana..." Emzee yayi gyaran murya shima yau dauriya ta kare sai hawaye "Muhammad Zayyan Tureta" Haba...koda yaji wannan yaro zuciyarsa ta bashi cewa jininsa ne. Sakin Radhiya yayi hawayen da yake kokarin kada ya zubar a gaban 'ya'ya suka fito suka rungume juna cikin farinciki suna kuka. Zayyan ya dago yana ta shafa fuskar Emzee wai wannan ma nasa ne. "Kafi jindadin ganinsa a kaina ko?" Yaji Radhiya tace a raunane tana kara karyar masa da zuciya. "A'a Alheran" yace yana sakin Emzee ya sake rungumeta. "Kenan ni bakayi murnar ganina ba?" Shima Emzee yace yana jin haushin tayi masa kauron jin dumin babansa ya koma wurinta. Zayyan sai ya rikice yana soma cewa "ba haka bane" ya ga Alheran ta kafe shi da ido shima Emzee ya tsaya yana jiran amsarsa. Dariya suka ji daga bayansu. Falon da ake ta kuka ma'abota cikinsa sun koma dariyar wannan haduwa ta uba da 'ya'yansa. Hadasu yayi kowanne a bari daya ya rungumesu kamar za'a kwace masa su ********** Kowa yana son jin yadda ta kasance dashi su duka suna zaune a falon. Emzee da Radhiya kusan danne masa kafafu suka yi kowannensu yana so ya rabi jikinsa. Dagawa yayi suka hada ido da Ummi da take ta kallonsa sai taji kunya sosai ta kama ta. Major ne yayi gyaran murya yace a yiwa Annabi SAW salati. A tare suke yi da karfi suka karanta Fatiha, Ayatul Kursiyyu da Amanar Rasul sannan ya dade yana jan su da addu'a duka domin godiya ga Allah SWT. "Alhamdulillah, Alhamdulillah, Alhamdulillah...wannan rana ce da bazamu taba mantawa da ita ba har mu bar duniya. Amma kafin mu zauna jin yadda al'amura suka kasance Zayyan ka zauna kaci abinci ka huta. Ku kuma kowa ya tashi mu bashi wuri ya huta" Dukkaninsu suka fita Ummi ta tashi tayi kitchen tana godewa dabara irin ta Mama aka bar Zayyan da 'ya'yansa an rasa wanda zai fara tashi cikinsu. Emzee yasan ya kamata su tashi amma Radhiya ita ta ga wurin kwana. Kallon babanta kawai take yi tana cewa Daadaa yana amsawa da murmushi. Ta kira yafi sau goma bai gajiya da amsawa. "Emzee kuma wai nan ba mafarki nake yi ba ko?" Tace tana lumshe ido tana sake budewa a kansa. "Ko in mintsineki ne?" "A gabana Zayyan?" Wani dadi yaji ya kama shi mahaifinsa ga kira sunansa da sunan raba gardama tsakaninsa da Addarsa. Kai wannan abu da me zai kwatanta shi. Muryar Umminsu suka ji tana cewa "in fara kawo maka abinci ko tea?" "Duk wanda kika kawo zanci Fillo. Saboda jiran abincinki rabona da saka wani abu a bakina tun safiyar jiya" Wai da irin dabarar nan Emzee sai ya yiwa yayarsa alama da ta tashi su ma su fita. Shiru bata gane rangwada kan da yake yi ba sai da yace "Adda taso muje muma Daada yaci abinci" Hannunsa da ya riko nata ta ture "kai kyaleni ka tafi idan kana so. Ni ban gaji da ganinsa ba." Matsowa ta sake yi jikin kafar Zayyan tana murmushi "Daada na chanja kama daga yadda ka sanni ko?" "Kin koma tamkar Innata" "Bani labarinta" Emzee sai ya shiga kada kai. Idan abin Addarsa ya motsa fa bata dogon tunani. Yanzu ace daga dawowarsa zai fara bata labari. Ita kuma neman abinda zai zaunar da ita wurinsa take yi kada ta tashi ta dawo ace ya koma inda ya fito. "Kin yiwa Hamma Awwab godiya ne? Dashi aka je dauko Daada fa naji Mama tana fada" An tuno mata da Hammanta sai ta tashi tana murmushi "Daada bari naje na dawo kafin nan kaci abincin" "Sai kun dawo Alheran" Wani abin ta tuno zata taambayeshi Emzee ya turata waje ta karfi ya rufe kofar. Ummi tana ajiye tray a gaban Mijinta taji gabanta ya fadi da aka rufe kofar ga kunya kamar wata sabuwar amarya. Dariya taji Zayyan yayi yana kallon kofar "ina kika samo min wadannan yaran Fillo? Nan fa dabara yayi mata don su bamu wuri" Sai da tayi murmushi yaji zuciyarsa tana kadawa da tasowar dadaddiyar soyayyarta tace "sakamakon tureni da Tureta yayi ne" ya sake yin dariya. Ta gama ajiye komai a gabansa zata fara zuba masa tea din domin ya gasa cikinsa ya riko hannunta bai zaunar da ita ko ina ba sai cinyarsa. Kunya matsananciya ta kama ta yayi mata wani irin riko da yaji tana neman tashi. Rungume tayi ya dora kansa a tsakiyar kirjinta. A hankali taji hawayensa yana jika mata gaban riga. Tallabo shi tayi ta sake rike shi itama nata hawayen yana sauka a kansa da ya cire hularsa. Sunyi kusan minti biyar a haka sai ajiyar zuciya kawai da take yi. Da taji yana neman dago kansa ne ta sassauta rikon "ga tea ka fara sha sai na zuba maka tuwo" Bai bata damar tashi ba sai lebbanta da ya shiga zanawa da karamin yatsansa ya soma magana a hankali "ban taba dena sonki ba Mairama, ban manta ki ba da kyautatawarki gareni. Idan kunci yayi min yawa sai na cika zuciyata da ranar da na fara kamaki kin saci mirinda" Murmushi tayi mai hade da hawaye shi kuwa ya cigaba da abinda yake yi "a duk lokacin da zan ganmu cikin wannan yanayin nasan mafarki ne wanda nake kwadayin cikarsa idan mun hadu a aljannah. Ashe zan sake ganinki matata. Ashe da rabon na sake samun kaina cikin farincikin zama miji a gareki..." hannu yasa yayo kasa da kanta daidai fuskarsa "ban sani ba ko na manta ko zan iya tunawa" "Me?" Ta tambayeshi gabanta yana lugude wai yau ita ce tare da Zayyan. "Wannan" ya karasa fada da hade lebenshi da nata. Lumshe idanu kawai suka yi kowannensu hawayen farincikin cikar buri yana saukowa daga idonsa suka sake rungume juna tightly. ********** Gidan Mami suka tafi saboda Emzee ya hango shigar bakon da suka zo da su Awwab din Mama yasan manyan nasu can suka je. Ilai kuwa sun taru can dinne Excellency ya gabatar musu da Chibuzor wanda ya fada musu sanadin haduwarsu da Zayyan. Wannan ake kira al'ajabi su Major sun koka sun murmusa sun dara duk a lokaci guda. Yayin da matansu suke dakin Mama su ma suna nasu mamakin. A gidan Mami suma a falo aka baje hirar murna ta kaure sun saka Awwab a gaba sai ya fada musu yaya akayi. "I am exhausted ku bari ayi komai a tsanake" Sallamar Radhiya yaji ya dago idanunsa da suka soma ja saboda muguwar gajiya da yunwa. Jin kansa yake kamar yana yawo a iska babu kuzari ko kadan. Emzee ne a gaba ko da ya shigo kai tsaye yaje ya rungume shi. "Allah Ya baka abinda kake so duniya da lahira Hamma. Thank you" "Kada kayi min kuka dai bani da karfin rarrashinka" Awwab ya zolaye shi. Yana sake kallon Radhiya sai ga nata hawayen kamar famfo ya tashi da sauri. Wani irin sonsa take ji ta kuma rasa da wace kalma zatayi amfani domin ya gane girman farincikin da ya saka ta a ciki. Kofa ya nuna mata dama ko zama batayi ba ta fita yana take mata baya suna jin shakiyancin Ibrahim da Raji wai love is in the air. Wurin tsayuwa yake nema inda zasu samu su kadaice babu yayi gajeren tsaki. Da sunyi aure fa shikenan duk inda yaso zai kaita. Yanzu anbi an cika ko ina an hana mutane sakewa. Ta kula da yadda yake ta kalle kalle tayi murmushi. "Hammana" Dama ya lafiyar kura. Ya gaji tilis wannan kira da tayi masa yasa zuciya da gangar jikinsa duka amsawa. "Nagod..." "Shhhhh kada ma ki fara. Idan kina da wani abin cewa dai ki fada" Idanunta fal kwalla tace "ni me zan ce Hamma" "Ni ina da abin fada Alheran." Da wata irin siga mai shiga rai yake kara hargitsa ta da muryarsa "I am not a soldier kuma bani da zuciyar da zan taba zama. Kuma ni ba likita bane, bana jurar ganin jini....But I love you so much kin hana min nutsuwa tun daga ranar da na fara ganinki" Kifta ido kawai tayi hawayenta ya sauko "nima haka Hammana" Ya ce "wayo ko?" Sunkuyar da kanta tayi tana murmushi "ina fata kin shirya aurena yanzu?" Ba shiri ta rufe fuskarta da gefen mayafi tana neman komawa gidan Mami. Marairaicewa yayi sosai ya koma kalar tausayi ya shagwabe mata yadda take yi ita ma "Come ooon na gaji fa. I need a wife, a friend....uhummm.... I need you." Murmushi take yi sosai ta kasa dagowa ta kalle shi ma. Ya duka saitin fuskarta yana neman hada ido da ita tana kaucewa "kin gani ba, ba don kin mayar dani gwauron dole ba da yanzu I have Alheran to hug when I am happy or sad. My Schatzi to kiss when love is in the air right?" Gabadaya ta rikice masa ta ma kasa gudun ta barshi shi kadai yake ta zuba hirarsa. "Kinsan me? I am so tired ga yunwa. Mu koma ciki?" Tausayinsa taji kana ganinsa kasan a gajiye yake sosai kuwa. "Muje na zuba maka" "Baki bani amsa ba fa. Na dage ina ta debo zance duk don na burgeki" Ya bata dariya ta gama kayarta sannan tace "I am all yours Hammana kai nake jira tuntuni" Amsar tayi masa dadi suka shiga falon tare. Babu kowa su Zahra sun shige dakin Mami su Ibrahim suna dakin Awwab. Zama yayi akan doguwar kujera ta wuce kitchen zuba masa abinci. Akan tray ta hado komai ta dawo sai dai me...Awwab ya mike abinsa wani nannauyan bacci yayi awon gaba dashi abin tausayi. Kallonsa tayi tana jin soyayyarsa tana dada zama sabuwa a zuciyarta. *********** A kasa Mairama ta zauna Zayyan yana jingine da kujera ta saka plate din abincin a tsakaninsu sannan ta tashi. "Ina zaki?" "Hannu zan wanke" ta amsa tana sunkuyar da kai saboda tunanin abinda yayi mata mintuna kadan da suka wuce. Tasowa yayi shima yace zai wanke nasa hannun. "Yi zamanka ina zuwa" Bata dade ba ta dawo yayi zaton ruwa zata kawo masa a roba na wanke hannu sai gani yayi ta zauna ta debo tuwon ta kawo bakinsa. Yau kam bashi da karfin zuciya ko kadan. Yau daya dai a Zayyan mijin Mairama yake wanda ya kwashi dimbin shekaru yana muradin sake ganinta ko da daga nesa ne. Hannun nata ya kama ya karasa dashi bakinsa. "Ashe haka tuwo yake da dadi muka rinka cewa bama so da muna yara" taji yace ta soma dariya ya fara bin yatsunta daya bayan daya yana sudewa. Fillo sarkin kunya sai ta kasa kara diban wani ta bashi. Ya sanya hannu ya dago kanta idanunta a rufe "alfarma nake nema Fillo" "Babu alfarma a tsakaninmu kaima ka sani" "Yau daya don Allah ki tattaro duka kunyar nan ko Alheran ce ki bawa ajiya. Mairama kadai nake bukata in nuna mata yadda shekaru ashirin da biyu suka galabaitar da Sojanta" 💕[11/2, 7:11 AM] 46💕 🏽 A haka ta gama bashi abincin yaci mai yawa. Yaushe rabonsa da tuwo ko abinci mai dadi? Miya tasha nama da bushasshen kifi yaci son ransa duk loma yana binta da addu'a da kalmomi masu nuni da kewarta da yayi. Harararsa tayi cikin wasa "kasan dai ba'a son magana ana cin abinci ko" "Gani nake yi idan nayi shiru kamar zaki bace na dena ganinki" ya bata amsa kai tsaye yana kallon idanunta da suka cicciko da kwalla. Hannunsa ta kama ta rike gam da hannun hagunta ta cigaba da bashi da daman. "Babu inda zani Sojana" Murmushi suka yiwa juna basuyi aune ba ya cinye leda daya madaidaiciya harda karin rabi na tuwon. Nama ma ba kadan ta bashi ba sai da yaji cikinsa yayi masa nauyi don kansa yace ya isa yana dariya. "Kada na kasa tashi daga wurin nan fa Fillo. Ina zaune kina ta zuba abinci a tumbin da yunwa ta cinye shi." "Inda kake horon yunwa suke yi maka? Dubi yadda ka rame sosai ko da dai ba kiba gareka ba amma yanzu ana ganinka za'a gane rama ce ba siranta ba" tayi maganar yayin da ta soma hade kan kwanukan zata kai kitchen. Da wata irin murya mai sanyi Zayyan yace "Mairama...ki kira min su Major muyi magana kafin na saka hakarkarina a makwanci." "Ka huta don Allah" "Yadda kuke matse da son jin me ya sameni nima haka na damu da son jin yadda kuka rayu ke da 'ya'yana da aminai na. Kirjina yana son amayar muku da nauyin da yayi ta dako ko zanji sauki" Wani irin tausayinsa take ji tana gama kai kwanukan ta wanko hannunta ta dawo ta kira Mami ta sanar da ita. Su Major so suka yi ya huta ko zuwa gobe ne amma yasan shi dai bazai iya hakurin nan baiji me ya sameta ba. Har wannan lokaci Baban Arifah yana gidan tare suka dawo falon Zayyan yace a kira masa duka yaran domin su ma sun cancanci sanin ina mahaifinsu ya shiga tsahon lokacin nan. Falon yayi tsit Awwab ne kawai babu. Radhiya dama tana dawowa ta sake komawa gabansa yana daga kan kujera tana kasa. Zayyan ya dube su daya bayan daya ya jinjina kai domin yasan wannan labari yanzu ya fara bada shi har sai duk wanda ya kamata ya sani ya sani. Sojansa ya koma rikakken namiji ma'abocin cikar zati kafin ya fara magana. "Kwanaki kadan bayan rabuwarmu da Baban Arifah zuwa wuraren karfe daya da rabi na jiya sunana 3810 mazaunin gidan yari da ake yiwa zargin dan tawaye a Liberia" Major da Baba Hadir sun ji kadan daga labarin daga wurin Baban Arifah amma sauran matan musamman Ummi da Alheran sun dimauce matuka. Daga lokacin da ya rabu dasu Hadir kawo ga haduwa da rabuwarsa da Baban Arifah da zamansa a wannan prison din ya sanar dasu mahimman abubuwan da suka same shi. Wahalhalun zaman kurkuku da tsananin begen komowa gida garesu. Kuka duka matan suke yi wurjanjan. Ummi saboda tsananin kaduwa tsigar jikinta har tashi take yi ta kasa zaman falon ta tashi tayi ciki sai sautin rufe kofar daki aka ji. Murmushi yayi yana kallon kofar da ta bi "banda abin Fillo komai ba ya wuce ba" Jikkuna sunyi sanyi. Girma, kima da darajar wannan bawan Allah ta ninku a cikin idanun duk wanda yake zaune a wurin. Ga su Daddy dadin ciwon abun duka su ukun fa a garin ceton rayuwarsu ne ya fadawa wannan kaddara mai radadi da sosa zuciya. Idanuwa sunyi kuka ba babba ba yaro shiyasa Mami ta cewa yaran dukkansu su tashi tunda sauran labarin ba bakonsu bane. A sanyaye suka fice zuwa gidan Mama ita kuma da Maman suka shiga wurin Ummi. Dama kuma tun zuwan su Zayyan din bayan anyi zaman gabatar da juna sallah suka yi shine Daddy ya jagoranci addu'a da suka yi. Emzee da Ibrahim gidan Mami suka wuce su. Da kyar bayan fitarsu Major yace "Zayyan ka ga rayuwa ni bani da wani bakin magana ko baka hakuri. Nauyi da girmanka nake kara gani ina jin inama ban biyo motar da taje camp dinku ba ranar. Da bazan biku wurin ba kai kuma babu dalilin da zai sa ka koma daukoni har wannan abu ya faru. Nine silar komai Zayyan ka yafeni" ya kare muryarsa tana rawa sosai. Idanun Zayyan sai suka kada suka yi jazur "ashe ni din ba kaninka bane kamar yadda nayi zato. Matsayin da muka baka ni da Hadir ba shi ka bamu ba" Sai ga hawaye ya saukowa Major da sauri yace "a'a Zayyan ba haka bane. I feel so guilty" "Saboda kaninka yayi rayuwar da ko da babu kai ita Allah Ya zaba masa? Hadir kace wani abu mana ka barni inata babatu ni daya" Wani mashahurin shiru yaji ya ratsa falon ya kalli Hadir ya kallesu duka a dan tsorace yace "kada kuce min wannan mutum-mutumi ne ba Hadir dan uwana ba" Hadir din ne ya fara dariya kafin sauran su biye masa da kyar ya iya cewa "Zayyyyyan ko" yana kada masa yatsa. Abokin nasa bai chanja hali ba. Suna cikin damuwa sai da ya saka su dariyar dole. Tashi yayi yaje yana dan dukan kafadar Hadir din a hankali "tun zuwana banjin kayi min magana ba dole na tambaya." Baban Arifah Excellency yace "ka zauna Mustapha zaiyi maka duka bayanin da ya dace" Haka ya koma ya zauna yana sauraron Major wanda ya fara da labarin tasa rayuwar sannan ya gangaro dawowarsu Nigeria da sake haduwa da Hadir. Jikin Zayyan wata tsuma yake yi da tashin hankali da yaji rayuwar da suka yi. Wane irin ciwo ne PTSD yake ayyanawa a ransa da ya nemi haukata Major mutum mai dauriya da karfin zuciya? Yanzu Hadir dinsa ne yayi shekaru baya iya motsa komai nasa kuma baya magana...kai rayuwa shine mutane suke kwallafa rai da neman haram bayan idan Allah Yaso sai Ya dauke maka komai Ya barka da ranka. Hadir mutuwar zaune fa yayi kuma aka raba shi da nasa iyalin alhalin yana cikinsu. Sai yaji yafi tausayin aminin nasa akan tasa rayuwar. Bayan ya gama jin komai ya kalle shi " To gaskiya shawarar da zan baka shine ko ka bude baki ka fara magana ko kuma kaf tarihin 'yan matanka wadanda zan iya tunawa da wanda ban tuna ba in dora nawa zan kaiwa Zainab mu koma gefe ni da Fillo musha kallo" Zayyan yace a yayin da yake ta kore kwalla da yatsansa. Dariya Baba Hadir yayi ya taso suka sake rungume juna. Excellency yaji suna kara burge shi "ina zaune ana nuna min wariya. Ai shikenan ba fushi zanyi ba bare na barku. Nema kuke ku nuna min ku ukun kunfi shakuwa ni dan karo ne" Major ya kwashe da dariya saboda yanayin muryar da Excellency din yayi magana da ita ta ban tausayi. "Dama ka dena damuwa nima ana nuna min amma ya na iya they are my Ladies" Aka sake yin dariya musamman da Baban Arifah yace shima dole zumuncin nan ayi dashi mai karfi. Kuma da yake shine babba don har Major ya girma a shekaru yace "na dauki matsayin babban yaya mai fada a ji. Idan kuma aka ki ji to fa na iya displine" Zayyan yana dariya yace "Ka tuna min da 'yan gidanmu Yaya Babba. Ina ta tunaninsu wallahi. Ko yaya Maikudi don yafi kowa baudadden hali a gidan" Dariyar da suke yi yaji dif ta dauke har ya soma zargin ko rasuwa akayi a gidan nasu. "Maikudi ya rasu ne? Ku fada min dama nasa rai da ba kowa zan samu a raye ba" Major ya sake kallon Excellency "to Yaya Babba ai sai kayi masa bayani mu dai babu ruwanmu ko Hadir" Excellency ya dan dake "wato zamewa zaku yi? Kada ku manta ku kuka fara naku ma harda duka. Ni me nayi Allah na tuba banda dan tsare shi kuma ba ya fito ba last month" "A fada yadda zan gane ni dai" Major ne ya soma bashi labarin yadda ta kasance da Mairama bayan an tabbatar da rasuwarsa a wancan lokaci. Maikudi ya handame abinda ya bar musu kuma don karfin hali yayi ta musu kazafin mutuwa ya rabasu da masu taimaka musu. Iyakar kulewa da bakinciki Zayyan ya kwasa ga tashin hankali da suka ce masa a makance suka dawo suka sami matarsa. Ashar yake nema da zai turawa Maikudi sai dai takaicinsa daya bai ma san wanda ake yayi ba yanzu. "Kiyayyar da yake min har ta kai ya cutar min da iyali irin haka?" Yace a raunane. "Kuma meye dalilinsa na yi maka karya kaima" yayiwa Baban Arifah tambayar. "Barni da karamin dan iska, da yaci uban duka cewa yayi fa wai dan firit ya ganni ya zata buzu ne." Shi ya bada amsa da seriousness amma dariya suka saka ganin yadda yake kosasshen dan siyasa. Ya kuwa hade rai saboda dariyar da suke yi masa. Su Mami suna ta bawa Ummi baki a daki su kuma a falo sun cigaba da tattaunawa. *********** Kiran sallar la'asar da aka soma daga masallacin wani gida a nan kusa da estate din inda suke zuwa jam'i shine ya farkar da Awwab da yake baccin wahala a falon Mami. Yunwa yake ji kamar yaci babu, idanunsa suka sauka akan plate din da Radhiya ta rufe akan centre table bayan yayi bacci. Daukowa yayi ko kuskure baki bai iya tashi yayi ba ya shiga ci da sauri. Ko rabi bai ci ba sai amai kamar zai fitar da kayan cikinsa. Ibrahim da Emzee kakarinsa suka ji daga toilet din da yake cikin falon suka fito. Emzee ya tafi zai taimaka masa shi kuma Ibrahim ya tafi gidan Mama dauko mukullin motarta idan abin zuwa asibiti ne su tafi. Yanayin yadda ya shiga falon da sauri shi ya tada hankalin Radhiya tana gyara hijabin jikinta tayi alwala. "Ibrahim ya?" Shima gwanin rudewa ne yana ta bincike a falon yace "Hamma ke amai ban san me ya same shi ba" "Amai?" Radhiya tace a tsorace tana fita da sauri. Da shigarta gidan Mami ta hadu da Emzee a falo yana gyara wurin amma bata ga Awwab din ba. "Adda fita ki koma gidan Mama" Emzee ya umarceta saboda baya so Awwab din ya leko ta ga yadda ya jigata lokaci guda. "Don Allah Emzee ka barni na gamshi minti daya kawai" kuka yazo mata. "Kina so su Mami su zo su ganki a nan ne ace kin biyo saurayi?" "A'a" "To ki koma idan ya dawo falo da kaina zan kirawoki kinji" ya koma lallabata saboda yadda ya kula ta shiga wani yanayi. "To...toh...don Allah kada ka manta" A sanyaye ta fita ta koma ta tada sallah. Ibrahim kuma yaje bangaren Ummi lokacin su Daddy sun taso zasu je suyi sallah sai Excellency ya wuce a bar Zayyan haka sai gobe kuma. Da ya fada musu halin da ya baro Awwab mukullin mota ne bai gani ba zai kaishi asibiti Zayyan ya dakatar dashi. "Yarona ya bawa kanshi wahala yaki cin komai tun jiya" "Awwab din da bashi da juriyar yunwa?" Cewar Major. "Ku bashi abu mai zafi ya sha sai yayi kamar rabin awa sai yaci abinci. Amma banda ci da sauri ko da yawa sosai. Nima da naci na shekara ashirin da biyu gashi da kyar nake tafiya" Murmushi Ibrahim yayi yana jin Zayyan ya burge shi. Gidan ya koma lokacin su Zahra suna can ya fada musu a hada masa tea. Ita ta hada masa lipton kawai da yaji kayan kamshi da sugar daidai aka kai masa. Wanka kawai yayi da sallah ya sha ya sake kwantawa kansa na juyawa. Bai ga ta ina zai taba iya zama soja ba. Su da suke zama a bakin tituna domin tsaro ga mutane ko su yanki daji ko wuraren tarzoma ayi ta fafatawa babu ci babu sha na tsayin awanni. Radhiya na idar da sallah Ibrahim ya fada mata me Daada yace game da Awwab din. Ya zauna a kan kujera yana cewa "amma fa da gani yana jin jiki...cikinsa a dame sosai abin tausayi. Gaskiya yana bukatar kulawa. Naga kin fimu damuwa ko har an daidaita ne ban sani ba" "Allah Ya kaimu yaji sauki sai ka maimaita masa" Emzee yace daga bayansa "Adda ki dafa masa wani abincin mana tunda na gidan ya saka shi amai" Da sauri ta bar wurin ta koma kitchen din Ummi. Sai da ta tafi Emzee yace da Ibrahim "kana da problem fa, ka ga yadda ka karasa tayar mata da hankali da abinda kake cewa" Shi bai hango me yayi ba da gaske yace "daga fada mata gaskiya? Kai baka ga alamun yana jin jikin ba?" "Kai baka iya sakaya zance bane" "Kamar wani mace ayi ta luguiguita magana saboda wahalar da kai" "Anya Ibrahim zaka iya soyayya kuwa? Irin janyo hankalin yarinya da dadadan kalamai duk zero kake" Emzee yace da mamaki don Ibrahim kai tsaye yake abu yasha a jikin Mama. "Magana mai dadi ta wuce ina sonki kina sona mu hade kai kawai a daura aure a wuce wurin? Kakale kakalen soyayya yasa na kasa samun wadda zata burgeni fa" "Baka hadu da shagwababbiya bane sunfi tsayawa a rai" "Allah Ya tsareni a rinka tale baki ana karya wuya kamar mara lafiya. Malamin jinya ne ni?" Emzee yana dariya Zayyana ta banko kofar daki ta fito ashe tana jinsu. Tsaki taja da karfi yadda duka zasu ji ta wuce a fusace. Maganar Ibrahim ta sani sarai da ita yake ba wani ba. Duk da tana shiri da su duka kuma bata da abokan hira idan suna gidan sai su amma fa tafi jituwa da Emzee. A da bata ganewa idan Ibrahim ya fadi magana akan yanayinta amma yanzu an kile anje bodin an hadu da 'yan mata. Ba wannan Zayyan bace mai komai Daddy, ita ma yanzu ta san me take yi. "Ka ga ka taba min kanwa." "Da nayi me? Ai banyi komai ba sai na sami wannan bakin na dalle inji wa take yiwa tsaki ni da kai" Emzee ya mike yana daga hannuwa "my friend da kai fa take. Ba dama tayi magana ka rinka cewa ana tale baki. Mutane irinka gidansu babu wani armashi komai a rinka yi kamar yaki. Irin dan tattalin nan da rarrashi ni ban ga alamun zaka iya ba" Ibrahim kallon tausayi yayi masa don shi soyayya bacin lokaci ya dauketa musamman da ya dukufa karatun nan baji ba gani. "Chege Emzee anya kai a NDA dinnan soja kaje zama ko kuwa dai idan kayi graduating buzu zamu shimfida maka a kofar gida ka koma mai bada lakanin mallaka da inganta kauna" Cakumo shi Emzee yayi ya matse a tsakanin hannu da cikinsa yana cewa Allah Ya kawo shi neman shawara ya ga yadda zai rama. *********** Sai da Radhiya tayi kusan minti biyar tana tunani kafin ta yanke shawarar me zata dafawa Awwab me sauki da zai ji dadinsa. Fridge ta bude ta fito da mince meat ta juye a karamar non-stick pot sannan ta hada albasa, tumatir uku da attaruhu biyu kanana tayi blending tare da tafarnuwa karama. Juyesu tayi a wani pan ta saki wuta nan da nan ruwan ya kafe. Sai ta dora mince meat din shima batare da ta saka ruwa ba na jikinsa ya bushe ya soma sauya kala sai ta zuba soyayyan mai a kai. Ta yanka albasa babba ta juye a ciki tare da wancan kayan miya ta zuba gishiri da kayan kamshi ta barsu suna suyowa a hankali. Sai da ta ga sauce din nata ya fara haduwa ta kara maggi da curry sannan ta dafa couscous wanda ta sakawa butter da dan gishiri a ruwan dahuwar. Ruwa ne kadan ake sakawa ayi komai cikin sauri kada ya cabe ko yayi tuwo. Yayi kyau sosai a ido ta kwashe ta zuba a karamin flask. Sauce din shi kuma ta zuba a wani bowl ta hada masa komai da plate da cokali ta bawa Zayyana dake zaune tana kunkunin maganar Ibrahim ta kaiwa Awwab. Fauziyya ta rinka mita saboda abincin dan kadan Radhiya tayi gashi ransu ya mugun biyawa. Da yake hankalinta yana wurin Hammanta ko a jikinta sai cewa tayi idan suna so su jira Hamma ya warke tayi musu. "Ke wallahi lallaba dangin miji akeyi a zamanin nan" Fauziyya tace tana maka mata harara don sosai tasa rai zata ci. "Nima dangin mijin ce sai hakuri Adda babu yadda zakiyi dani" "Don Allah ki taimaka min mana Radhiya idan banci ba bana jin bacci zai iya daukana yau" ta koma kwantar da kai. Zahra ta bita da kallon tuhuma "anya Fauziyya kalau kike kuwa? Jiya ma fa kinyi mana daga an soya kwai da mince meat kika cinye fiye da rabin wanda aka ajiye a dinning. To ko dan mince meat kika dauko" "Kada kiyi min fata har yau ina tuna kalar kukan da nayi ina nakuda. A bar zancen na yafe" Radhiya ta sami na tsokana daga baya ta tausaya mata ta kawo sauran sauce din amma babu cous cous duka ta juye masa ta bata. Zayyana ce ta zuba masa a plate ta mika masa. "Gashi inji Adda Radhiya" Karba yayi tun kafin ya fara ci cikinsa yana dada rarakewa da yunwa. Yanzu kam a hankali ya rinka ci sai abincin yayi masa dadi sosai. Yana gamawa ya kira wayarta kuwa. "Hammana ya jikin?" Yaji muryarta ta shige shi a nutse 'yan salihancin na kusa. "Better. Nag...." "Hey! Ka manta babu godiya ne" tayi saurin dakatar dashi. A kasalance yace "To me zance na nuna miki naji dadi?" "Babu komai ni dai kawai ka warke" "Love you Schatzi" "Me too Hammana" ta kashe wayar da sauri kamar yana gabanta. Kalmar nauyi take yi mata bata jin zata iya fada. Daga masallaci Excellency ya wuce Chibuzor yana mota tare da wani dreba su ka yi ta masa godiya. Su Major ma suka ce to yanzu dai zasu bar Zayyan ya huta ya wuce ciki. "Ango" yaji Baba Hadir yace da sigar tsokana a kokarinsa na magana. "Malam ka bude baki kayi tsokanar da gaske naji. Ba kyaleka zanyi ba sai naji ina fada kana fada" "Kaga wuce wurin matarka. Idan kaso ma magrib da isha kayi naka jam'in da ita" Major yace yana nuna masa kofa. Shi da Baba Hadir kowa ya tafi nasa gidan. Shima sai ya tafi yana murmushi. Daga falo ya soma jin wani irin kamshi mai shiga rai da bai taba sani ko jin makamancinsa ba. Turaren wuta ne dan gaske irin wanda su Mammee suke aiko mata dashi ta saka a ko ina. Kofar da ya ga ta shiga lokacin da take kuka ya bude. Nan ya sameta akan abin sallah tana addu'a ya zauna a kasa gefenta ta kammala sannan ya tashi tsaye. "Yanzu me zanyi?" "Ka kwanta ko baka yi bacci ba nasan jikinka yana bukatar kwanciyar" Da yake yamma ce sanyin da aka fara ya karu sosai shiyasa ta kashe AC sai fanka kawai. Kayan jikinsa ta kalla tasan bazai ji dadin kwanciya dasu ba. Kamar yasan me take tunani ya cire rigar ya ajiye akan kujera daya dake dakin. Da farko kunya taji sai dai tana ganin yadda ya koma bata san lokacin da wani irin kuka yazo mata ba. "Sojana kaine haka?" Ta bi wuyansa da kirji tana shafawa. Ya masifar ramewa fiye da yadda take tsammani dazu da yake cikin riga. Rigar yayi saurin dauka "bari na rufe kasusuwan nan kada su firgita min mata" sai ya ga ta kama rigar ta mayar ta ajiye ta rungume shi tana jin wani iri a zuciyarta. Wace irin rayuwa Zayyan yayi ne. Ta sani har abada idan ba samun kanta tayi a irin wannan yanayin ba to bata isa ta fahimci ainihin radadin da yake ji a ransa yake ta kokarin dannewa da fara'ar dole ba. Sojoji nawa ne a irin rayuwar sun rabu da iyalansu babu ranar sake haduwa. Nawa ne matan suka sake aure suka sake sabuwar rayuwa ashe mazan nasu suna da rai. Yanzu da tayi aure fa? Da Allah Ya jarabceta da son waninsa fa kuma ya dawo full of hope na ganin iyalinsa. Shikenan duk wannan farincikin sai ya koma ciki ya dawo matarsa ta zama ta wani kila ma da zuri'a a tsakani. Wayyo bayin Allah. Allah Sarki sojojin kasata. Kuka mai tsanani ta sake fashewa dashi yana shafa mata baya ta dago kanta a hankali "yanzu da nayi aure fa Zayyan? Da shikenan ni da kai..." Bai barta ta karasa maganar ba domin kuwa shima wannan tunani yana damunsa kuma Ya san wata kyauta ce kawai daga Allah da yanzu labari ya sha bamban. A take ya soma nuna mata wata irin zazzafar kauna mai tsayawa a rai, ruhi da gangar jiki. Soyayya bata tsufa sai dai ma'abotanta su tsufa. A wannan rana abinda suka kwana suna tunawa junansu kenan. ********** WATAN DA YA GABATA Malamijo ne ya coge a jikin bango yana ta kamshin turare dan d'uri. Sanye yake da manyan kaya babbar rigar nan kamar a nade shi dukkansa a ciki. Ga jar dara wasu bangarorin sun dan cinye ta koke. To amma dai ita ce ta fi dama dama cikin hulunan nasa. Kafarsa kuwa cover shoe ne na maza mai dan tudu ta kasa da tsukakken baki ya coko gaba. Wata mata ce ta fito ta kofar gidan da yake tsaye a gefe taci kwalliya foundation tayi kuka. Kallo daya kacal zaka gane irin matan nan ne da ake kira da masu kirar coca cola. Murmushi ta saki da ta ganshi shima ya maida mata jikinsa har rawa yake ya ga mace irin wadda yake so. Amintaccen yaronsa Talle da yake taya shi nemo 'yan mata ne ya tallata masa 'yar makotansu sakin wawa kyakkyawar mace son kowa kin wanda ya rasa. Sai gashi kwalliya ta biya kudin sabulu. Matar tayi ta ko ina ga ta gwanar kwarkwasa bata sha wahalar tafiya da imanin Malamijo ba. Da zai tafi kyautar dubu biyar yayi mata a ziyara ta farko. Yana zuwa gida dakinsa ya fada hankali a tashe. Ga mace har mace fa ya samo amma babu guri a gidansa, mata hudu ne a gidan. To yanzu wa zai sallama? Yadikko dai yana da yakinin duk ranar da ya sallameta 'ya'yansa kaf sai sun masa rashin mutumci irin wanda bai taba tunani ba. Banda Mairama da ta dage yanzu wurin ganin ta hada kan kannen nata babu wata shakuwa a tsakaninsu. Akwai nutsatsu akwai fitinannu duka ya tara amma tarayyarsu daya shine girmama Yadikko da Hajjo da itama tayi nisan kwana a gidan. Atine tsohon ciki gareta, Na'e kuma ko wata uku bata cika ba. Idan ya saketa yanzu ya cuci kansa tunda bai gama more kudin da ya kashe mata na aure ba. Ranar Malamijo kasa baccin kirki yayi tunani ya addabe shi. Bayan kwana biyu Atine ta sauka aka sami 'yan biyu mata. Da murna Hajjo ta tare shi da wannan zance ya hade rai. "Don bala'i tun ana daidai din kuma yanzu abin ya koma bibbiyu? Wai ni bazaku barni na sha iska bane? Mata kowa tazo bata da aiki sai haihuwa. Mtswww" Hajjo tasan halin mijin nasu sarai kuma dayake da ita aka je asibitin ta ga irin wahalar da Atinen ta sha sosai. "Idan ka gama tsakin sai ka kawo kudin da za'a siyo abubuwan karin jini ayi mata girki mai kyau. Kuma dai wannan karon a daure a bamu na yin kauri. Yarinyar nan taji jiki" Abin da bai taka kara ya karya ba dama neman rigimar yake ido rufe da daya daga cikin matansa don sosai Hajiyayye ta gama tafiya da imaninsa da wani salon soyayya da take gwada masa. Ji yake kamar bai taba aure ba. Ya karkace kai ya kankance idanu "Rashin kunya zaki yi min Hajjo? To sai ki kwata tunda da uban mutum muka tara ki yiwa kishiya girkin bikin jiki" Ranta ya sosu da zagin da yayi mata "Nagode madallah sai dai ka sani uban nawa da bai ajiye ko dan marakin sa ba duniya bata yi masa shaidar auri saki ba." "Wuyan wata yayi kauri. To sai ki tattara ki koma gidan wanda baya auri saki. Ali mai auri saki kema yayi miki saki daya" Da farko kunnenta har nema yayi ya toshe saboda abu ne da ta sakankance bazai taba faruwa ba. Shiyasa ma ta saki jiki ma ta saki jiki kuma ta dauki salon Yadikko na ganin sun rungumi duka yaran da babu uwayensu musamman masu kananun shekaru. Barta da fada da rashin barin ta kwana amma duka matan Malamijo bai taba auren wadda take sonsa soyayya ta gaske ba zaman hakuri ba irin na Yadikko kamarta ba. Kuntata musu da yake yi yasa da wahala soyayyar ta fito ana kokarin ci a koshi. "Me kace Malamijo?" Ta fada a razane. Shima kuma sai jikinsa ya dan so rissina "nace a tattara a tafi na sauwake miki. Idan akwai nama a gidan tsoho sai kije kuyi ta ci" Duk wani abu da take tunanin fada masa domin ragewa kanta bakinciki sai ta ga yayi kadan. Zuciyarta tana zafi ta shige dakinta. Mayafi kawai ta dauka ta fita daga gidan batare da ta leka dakin Na'e ba tunda Yadikko ma tana asibiti wurin maijego. Kafin ta karasa bakin titi sai kuka ya kufce matan. Da kyar take ganin gabanta haka ta tafi gidan iyayenta a cikin gari. Malamijo kuwa tunda ta fita yaji duk ya shiga damuwa sai dai wayar Hajiyayye a lokacin ta mantar dashi komai sai gashi a washegari ya tura wakilai gidansu. Abin mamaki basu bar gidan ba sai da suka bada sadaki don iyayenta sun ce basu ga dalilin jan lokaci ba. Yadikko tayi kukan wannan wulakanci da ya yiwa Hajjo taje ta fadawa abokinsa da suka yi hannun riga wato Mal Kallamu. Ko kadan baiji dadi ba amma yasan Malamijo baya jin shawara. Duk da haka yaje gidan basu kwashe da dadi ba kuwa. Abin takaici cikin 'yan matan nam hudu da yayiwa aure lokacin da idanun Ummi suka bude biyu an sakosu. Sauran kuwa zaman wulakanci da kaskanci suke a nasu gidajen. Sun auri mazan da basu san darajarsu ba ko kadan. Kina magana kuma a goranta miki cewa babanki ma yafi haka. Daga nan dai Malamijo ya shiga gyaran gida amarya zata tare. Yadikko hakurinta ya kare ta kudurta a ranta cewa Atine na yin arba'in zata bar gidan. Yarinya ce karama marainiya. Babu wata mace tsayayyiya da ta gani daga danginta da zasu bata kulawa ita da 'yan biyun nata. Ana sauran kwana biyar ne amarya ta tare Mairama taje kafin ta wuce Abuja. Yadikko sai ta kasa fada mata an saki Hajjo tunda tasan sun shaku daga baya. Kuma ma dai tana gudun ta fada ta hanata nata niyar barin gidan. Ita dinma ba zama take ba tana ta zagayen dangi amma bata leka Salame ba a niyarta sai ta dawo. Washegarin tafiyarta amarya ta tare. Malamijo ana ta zumudi yayi aski an gyara ko ina. Da kullin kazarsa ya shiga dakin amarya da zummar kiranta zuwa turakarsa sai ya samu bata ciki sai wasu yara dugwi dugwi da yabi ya lissafa su shida cif kwance wasu akan gadon da shi ya biya aka yi mata kayan daki. Wasu kuma an yi musu shimfida a kasa. Juyawa yayi zai fita nemanta yaci karo da wani yaro dan kimanin shekaru sha uku. Bangaje Malamijo yayi ya haye kan doguwar kujerar dakin da babu kowa a kai ya kwanta. Abin ya daure masa kai ya tafi dakinsa zai ajiye ledar da hannunsa ya fita neman ba'asi sai ya sami Hajiyayye zaune akan katifarsa da ya sauya saboda zuwan amarya ya saka maigida kar ka taka. "Sannu da zuwa Angona" tace tana make murya. "Sannunmu dai" ya daure ya amsa kafin kuma ya soma fada "su waye a dakinki?" "Dakina kuma? Mtsw anya da mutane a dakin kuwa? Ni dai da zan fito ban bar kowa ba sai yaran namu" Idanu ya zaro "yaranku ke da wa? Sun kai goma fa inajin" "Bakwai ne ba yawa. Biyu ne kawai babansu daya. Sauran..." "Kowa da nasa?" Ya tambaya hankali a tashe. Murmushi tayi masa tana tasowa gabansa tana rangwada jiki na juyawa. "Daren yau namu ne ni da kai ka bar batun yara zamuyi maganarsu gobe" Ledar ta karba ta bude kamshi ya doki hancinta. Kaji ne uku dakwale sun gasu an yanka musu albasa, kabeji da tumatir. Yawunta ya tsinke bata ankara ba ya tsiyayo ta gefen baki akan idanun Malamijo. Haka ya tsaya kamar gunki ta kamo hannunsa ta zaunar dashi jiki na bari zata ci nama. Biyu ta raba naman ta kwashe daya a wata ledar ta ture gefe. "Wannan yara sa samu su lamusa da safe. Idan ban basu ba gobe bani da zaman lafiya" Tashi yayi kawai yana tunanin ko bulala zai samo ya tafka mata. Don yana sonta sai a ha'ince shi. Ance sakin wawa baifi a ce tana da yara biyu ba. Kuma don jaraba sai a kawosu su tare a gidan tare. Hannunta da tayi rabon naman tabi ta lashe tas yana neman abin duka bata sani ba ta tashi itama. "Cin nama irin wannan yafi dadi idan mutum ya rage kayan jikinsa yadda ana gamawa sai a fadawa angwanci ko Malamijo nawa na kaina" ta shiga kifta masa idanu. "Zaki ci kwal ubanki ne" yace a zuci ya kama kofar dakin ya fita. Wurin ajiyar itace yaje ya sami wata sanda ya dauko wata sanda ya dawo ya jingine ta a kofar dakin ya kutsa ciki sai ya hadu da wata dattijuwa a zaune da daurin kirji ta saka ledar naman a tsakanin kafafunta tana ta tauna kashi. "Ke kuma daga ina" yace yana huci. "Maigida lafiyarka kuwa?" Murya dai ta Hajiyayye ce amma wannan ai tafi kama da dattijuwa. Sosai ya shiga kallonta yau babu foundation fuskar ta nuna da kyau. Da gani a kalla tayi arba'in da biyar ko ma fin haka. Kayanta da jibge a kasa ya kalla ya kuma kallonta. "Ke tashi tsaye" ta kuwa mike tana sunne kai wai ita kunya. "Ya na ganki a bushe kamar ni? Ina abubuwan jikin naki?" "Au" ta juya ido "kayan da nake ciko dasu kake nufi? Gasu can. Wai naga bacci zamuyi ne nace bari na cire nasha iska" "Wai tsaya, kece dai Hajiyayye da muka yi magana yanzun nan kika ce min yaranki bakwai? "Kai dai ka damu da son sanin yaran nan naka. To zauna muna ci ina fada maka. Su goma sha daya ne amma biyu babansu daya nace ma ko..." "In kin isa Allah shi tsinan. Kin kuwa san ko ni wanene da zaki cuceni haka? Kalleki fa babu body babu alamar body sai tumulin 'ya'ya. To ki tashi tun muna shaida juna kije ki tashesu ku bar min gidana" Bata nuna masa ranta ya baci ba tana cin naman da ya soma kasa tace "ka dai yi hakuri mu wayi gari sai su koma gidanmu. Idan na tashesu cikin dare yanzun da wahala suke boye maitarsu. Idan naman kazar bai ishesu ba sai ka ga cikin mutanen gidan nan ana ciwo ya kama wane. Kaga bazan so ba" Baki na rawa duka makaman yakin nasa suka bace yace "kina nufin wai...wai...wai ku din...kina dai nufin" "Mayu ba. Nayi zaton ma Kawuna ya fada maka tun lokacin da ka tura wakilanka. Kada ka damu indai zasu ci nama su koshi wallahi babu mai sani a gidan nan. Idan ba haka ba....toh...don shi babban da na taho dashi ma cewa yake wai ya ga cinyoyinka kamar..." A tsorace ya rike cinyoyin nasa ita kuwa ta ci naman nan duka ta cinye. Tun daga ranar kwanaki shida kenan kullum babban danta wanda ba ma a gidan yake ba zai je gonar Mamamijo ya debo kaji ko zabi kamar biyar su gyare shi da 'yan uwansa a tsakar gidan ayi dabge a ci sauran na gani. Malamijo bala'in tsoronsu yake ji ya kuma kasa fadawa kowa dom yanzu tsorata shi take yi har cikin dare duk da karyar maita tayi. Ya kara ramewa ya tsotse babu mamora a jikin. Hajiyayye banda nama sai tatike shi take da karyar maita yana bata kudi. Su Yadikko nasu ido ne babu mai cewa komai an barshi da sababbin iyalinsa. ********** Kwana biyu da dawowar Zayyan sun buga soyayya shi da Mairama ko farkon aurensu albarka. Gaishe su kawai yaran ke zuwa yi babu mai zama a bangaren. Su Radhiya ma basa kwana sun koma tsakanin gidan Mama da Mami. A haka ance musu wai su barshi ne ya huta. Yau suke sa ran kiran 'yan uwa a waya a sanar dasu idan ya dawo daga headquarter. Zasu karasa hada duk abinda ya dace ne domin ya zamana komai anyi shi officially. Awwab yaji sauki kuma nan da kwana biyu yake son komawa ya karasa abinda zaiyi ya dawo kafin hutun ya kare a aura masa Alheran. Raji da Zahra su ma zasu tafi Osun wurin dangin iyayensa. Daga can su je Katsina sannan su koma Germany. Arifah da mamanta sunzo jiya yau kuma tace akwai fa zuwansu park ita bata hakura ba su shirya zata zo su tafi. A gidan kuwa tayi laasar washegari suna yin sallah suka shirya zasu tafi. Awwab ya dauki Raji a gaban mota sai ,Zayyana da Radhiya a baya. Ibrahim da Emzee a motar Mama sai su Fauziyya a motar Arifah. Wani sabon park ta kaisu na dan wane da wane. Ba tsada bace da shigarsa sai dai masu zuwa da irin abubuwan da ake saidawa kaji pure water guda daya naira ashirin ya sa ba kowa ke iya zuwa ba. Hakan ya kare shi daga zama matattarar 'yan kwaya kowa ka gani yana kokarin nuna shi din ya isa. Wurin ya kawatu da flawoyi kwantacciyar ciyawa da mutum zai iya zama a kai ko babu shimfidar komai. Ga wani abu kamar korama ruwa yana wucewa da gudu. Akwai manyan bishiyu masu kara masa ni'ima da daddadar inuwa. Suna fitowa Emzee da Ibrahim ne suka dauko carpets da za'a shimfida. Raji ya dauko cooler din da aka zuba robobin ruwa da gwangwanayen lemuka cikin kankara. Zayyana da Radhiya kwandunan abinci shi kuma Awwab ya nufi wurin masu gasa nama Arifah ta biyo shi. "Captain yaushe ne komawar taka?" "Jibi. Akwai sako ne?" "Not really.."tace tana dan murmushi. Mayar mata yayi yana jinjina kai. "Akwai wata a kasa kenan. Haba kanwata kada ki boye min komai" Radhiya ya gani ta nufosu fuskarta babu walwala. Dama tun a gida ya kula kamar ma bata son fitowar. Shi kuma dama ce yake gani saboda baya samun chance din zama da ita suyi hira. Idan ba'a kirata ba to tana wani aiki. Tayi kyau sosai cikin pakistan da ta saka. Rigar baka da aikin zare pink sai pink din wando mai fadi da pink din mayafin da ta yafa. "So cute" ya furta a hankali gabadaya hankalinsa ya koma gareta. "Muna komawa gida zan bada shawarar ayi ayi bikin nan naku kafin a nemi 'yar mutane a rasa" Arifah tace tana dariya. "Da kin kyauta. Yanzu dai zaki fada min me kike son fada ko we talk some other time? Schatzi akwai kishi yanzu haka sai nayi lallashi" "Ahhh to bari na gudu kada ta hanani yayanta" Wurin wasu kujeru da aka baza a karkashin bishiyon Radhiya ta koma ta zauna takaici ya isheta da kishi. Awwab na jin me Arifah tace ya gama karbae ledojin naman yace "wanne? Emzee fa kaninta ne" A kunyace tace "ba shi ba...how much do you know about Yousuf? Yana kirana kuma dai nima I like him" Da farinciki yace "in sha Allahu baki da matsala kanwata. Maybe maganarki yace yana son muyi" Amma wannan hadi yayi masa sosai. Tare suka taho inda Radhiya take Arifah ta karbi ledojin don bata da girman kai shi kuma ya zauna a kujerar dake kallonta. "Schatzi, kishi?" Tsuke baki tayi taki yi masa magana ya tashi yaje ya dauko musu maltina guda daya ya dawo. Bai ce komai ba ya bude ya sha ya tura mata. Sai da ta dan murguda baki wannan dimple din mai bashi sha'awa ya motsa ta dauka ta sha itama ta tura masa. Haka suka yi har ta kare. "Zaki kara?" Ta noke kafada. Haushin nata da biyu ne dama. Ga dariyar da yake yiwa Arifah ga tafiyarsa jibi duk ya dagula mata lissafi. Tun bai tafi ba ta soma jin kewarsa. Sati uku yace zaiyi mafi karanci ko yayi wata guda. Duka duka yaushe suka daidaita yake tunanin sake tafiya ya barta. Yatsa taji ya kada a kusa da fuskarta ta dago daga tunanin da take yi tana kallonsa. "Indai Arifah kike yiwa wannan fushin ki dena zancen Yousuf muke yi. It seems sun daidaita" Duk da tana kokarin boyewa ya kula da dadin da hakan yayi mata amma sai ta sake dinke fuska. "Me kuma nayi? Kinga tafiya ce a gabana bana son wannan fushin" Kwallah ya gani ta ciko idon ya sosa mata inda yake kaikaiyi. "Ya Allah" yace ya soma damuwa "Alheran ba kya son na tafi ne?" Kifa kanta tayi akan teburin gabanta bayan tace eh. "Kada ki bari hawayen nan ya fito" "Me yasa?" "Zaki sani rarrashin da bai kamata nayi ba with a hug and maybe a..." Dagowa tayi da sauri "na dena don Allah. Sai ta ga yana kallon fuskarta shine ta taba idonta taji danshi "kadan ne ya digo Hammana kuma ba ni na fito dashi ba" Tasowa yayi daga wurin zamansa yana zagayawa gabanta a hankali "ya na iya tunda ya fito sai na rarrashe ki....come here" Ba shiri ta mike itama tana ja da bayan "Allah na dena fa...ka tsaya a inda kake" Bai dakata ba ya cigaba da matsowa "ga wani nan ma yana zuba. Schatzi tana bukatar rarrashi irin wanda ni kadai zanyi mata ko" Ga kunya tana ji ga zancen yayi mata girma sauri ta kara ta na neman ina sauran suke "ba hawaye bane ruwa ne" Idanunsa har wani ciki suka yi yace "kin fara karya ne? Ina kika ga ruwan?" "Uhmn, uhmm yawu ne kaga" ta tabo idon ta nuna masa. Cak ya tsaya ya kwabe fuska "ashe baki dena kazanta ba" Dariya ta koma yi "zaka taka danyen..." "Stop Alheran, bana son kazantar nan taki" Ta kuwa cukule tana jindadin yadda ta dawo ita yake gudu "kalli mana ka gani danyen...." "Schatzi!" "Oui ma Chérie" ta amsa innocently kamar bata san me take yi masa ba. "Ko ki bari...." "Ko kayi me?" "Kada ki kureni ki ga me zanyi din fa" ya gargadeta da hannu yana dawowa kusa da ita suka soma jerawa suna gangarawa hanyar inda sauran suke. "To nayi shiru." "Better. Call me that name again. Dama na gaji da Hamman nan. Su Zayyana su fada kema ki fada babu bambanci" "Chérie" tace da wata irin siga mai shiga zuci. "Meaning?" "Daidai da Schatzi amma french version" Tsayawa yayi a gabanta ya hanata cigaba da tafiya "idan na dawo bana son ko sati muyi ba'a daura aurenmu ba. So tun yanzu ina fada miki zan sanar da su Baba. Idan kinso ana tambayarki ki sake cewa baki shirya ba" Dariya ya bata tace masa ko gobe yake so ta shirya. "Da kin raina kanki kuwa" Nutsuwa tayi a ladabce tace "Me yasa? Dukana zaka yi?" Sai da tasa shi dariya "Matsoraciya ina kika baro 'Yar Soja nasan da ita ce cewa zata yi bismillah " " 'Yar Sojan lafiya bayan ta kare min ina nan ina son dreba" Yana juyowa suka hada ido ta gudu duk kiran da yake mata kunya ta hanata tsayawa. Bata sake bari sun zauna su kadai ba saboda kunyarsa da ta rinka ji. Da ana daukar hotuna kuwa fafur taki yarda ayi musu su biyu. ********** Rama 'yar asali ba bogi ba Malamijo ya sake yi gabadaya ya sake karewa sai kasusuwa sai kayi zaton mayun gidansa sun fara lasarsa ne. Gidan gonarsa yaje za'ayi lissafin abincin dabbobin da kuma ware wadanda za'a kai Enugu karshen sati. Yana zuwa babban yaronsa Talle ya soma cewa "Yallabai an fitar da shanun da ka turo a dauka. Gaskiya kayi dabara da kace a rage wasu saboda nan din ya soma matsarsu basa walawa sosai" A take ya soma zufa duk da sanyin gari "wadanne shanu kenan?" "Wanda ka turo dan wajen amaryarka mai zuwa daukan kaji ya dauka mana. An bashi ashirin da uku yanzu saboda motocin sunyi kadan zai dawo a cike hamsin din" Jiri ne kawai ya soma dibar Malamijo saboda tashin hankali jikinsa yana rawa yace "ni ne zan turo a kwashe shanu? Da can a ina suke ban ce a raba ba sai yau?" "Ba dai karya yayi min ba yaron nan? Kusan awa guda da tafiyarsa" Kuka Mamamijo yasa bare da ya soma dubawa a gigice ya fahimci manya manyan bijiman sa aka kwashe "da su taba shanun nan ba gara su lasheni ba ita da yaranta" Talle dai lallashi yake yi Malamijo ya kama hanyar gida fakam fakam yana zubar da hawaye kamar yaro. Daga tarewarta sunci kaji yafi hamsin. Sau biyu ana daukar tumaki duk yayi shiru don tace masa magana na fita ko ita bata cinyeshi ba yaranta zasu ci. Dakinta yaranta ne a ciki ita kuma ta tare a dakinsa sauran matan basu da girki. Sai dai kowacce ta dora abinda ya samu suna kallo ana wadaka da nama kullum. Babur ya tare ya hau don yayi saurin zuwa gida. Yana zuwa gidan bata dakinsa ya tafi nata. A can yaji tana waya tana kyakyata dariya "Talle baka da kyau. Kasan shawararka ta maita tayi sosai. Tsohon banza yana son ransa da na kada idanu sai kaga yana tsuma. A sayar da shanun nan ko dubu hamsin hamsin ne tunda kace manya ne kowa ya dau rabonsa" Wani gululun bakinciki ne ya turnuke shi yadda Hajiyayye tayi masa wasa da hankali. Yanzu yana fito da maganar nan magauta sai su sami abin dariya. Ta ina zai samu ya gasa musu gyada a hannu kafin ya damkawa hukuma? Shawara daya ce tazo masa ga bacin rai ya dauki waya ya kira Mairama. A lokacin tana ta koyawa Zayyan yadda ake tura sako a waya yana ta mamakin fasaha da kimiyar nasara sai ga wayar Malamijo. A ladabce ta amsa ga tsoron ko lafiya saboda shi dai baya kira sai dai a kira shi. Ko gaisuwarta bai amsa ba ya soma bambami. "Yanzu Mairama kin kyauta min kenan? Yarinyar nan 'Yar soja ance tazo hutu amma ni ban ganta ba har yau. Naka naka ne Mairama a rinka zumunci." "Malamijo kayi hakuri dama satin nan zasu zo da Karami sai wani dalili ya gifta amma suna tafe wallahi" "To ni dai idan da hali su taho gobe ko jibi. Idan ma kudin mai ne babu zan biya. Ina ta shelar akwai jikata a Faransa abokai sunki yarda. Shi kuwa Zayyanu kice ya taho da kayan sojojinsa idan da bindiga ma ya dauko ko ta katako ce." Jikinta ne ya bata ba lafiya "Malamijo me ya faru ne?" Kamar ya fada mata amma zuciyarsa na zargin tana cikin masu murna. Duk wanda yaji me ya same shi cewa zaiyi Allah Ya kara. Radhiya kuwa yasan ko zata yi dariya sai ta rama masa su Hajiyayye bazasu tafi haka nan ba. Zayyanu karami kuma ai soja ne dole ya tsaya masa ko baya so tunda hukuma dai anyita ne domin kare al'umma eheee. Tana ajiye wayar ta kalli Zayyan da 'yar damuwa a fuskarta "ina jin fa an tabo min uba, akwai abinda ke damun Malamijo" Dagowa yayi daga kan cinyarta da yayi matashi "tun baki tabbatar ba kin soma hade rai" "Sai naji duk na matsu nima na ganni a Sumailan. Idan wasu ne suka taba shi ba yarda zanyi ba, ina son tsohona" "Mairama wai ni wa Alheran ta gado ne? Tawa ce ta fito fili amma kema fa ba jin magana kike ba" Dariya tayi sosai kafin suka yanke shawarar tafiya Sumaila jibi su ajiye yaran su wuce Sakkwato. Daga can kuma suyi Nijar in sun dawo su tsaya a rugar Barkindo kafin su dawo Abuja. Zuwansa headquarter dazu an kare komai amma duba da cewa dole ya bukaci lokaci da iyalinsa shiyasa aka bashi zuwa farkon sabuwar shekara wanda daya ga wata ake son yin taron karrama shi. Idan an gama zaiyi wata uku yana daukar training da courses domin ayi updating dinsa tunda Nigeriar da ya dawo ba ita ya bari ba a 1994. Akan wannan shawarar suka tsaya bayan magariba lokacin su Radhiya sun dawo ya shiga wurin Baba Hadir. Nan ya sami Awwab zaune a kasa a gabansa yana rokon shi dai yana dawowa don Allah ayi aurensu da Radhiya kafin ta koma. Ya kara da cewa ya bada cigiya jiya a cikin estate din block C akwai gida. A dan littafinsa Baba Hadir ya rubuta masa cewa zai yi magana da ita da kuma su Daddy. "Ni dai Baba da ka kyaleta wallahi tsoronta nake kada a maimaita irin na da. Kawai ka yanke hukunci shikenan" "Kada ka bada maza mana Awwab ya haka kake tsoron matarka" cewar Zayyan yana dariya. Awwab sai ya tashi ya fice yana mai jin kunya. Hadir ne ya rinka masa bayani a rubuce na abinda ya taba faruwa da kuma bukatar yaron har yanzu. Sai da Zayyan ya gama karantawa tsaf sai ya bata rai "nifa na baro A B C D din a Liberia kayi min bayani kawai." "Zayyan" Hadir yace yana dariya. "Kaga yara dai naku ne bani da ta cewa akan komai nasu nima dan gayya ne. Fatana Allah Yasa wannan karon babu wata matsala da za'a samu daga Katsinan" "Baka ji haushi ba?" Baba Hadir ya rubuta masa. "Ko kadan dan uwa. Major Mustapha da iyalinsa sunfi karfin haka a wurinmu kaima ka sani. Ya kula min da iyali sannan ya kula min da kai. Me zan nema kuma? Maganar yara wannan mukaddari ne idan akwai rabo sai kaga anyi" "Zayyan" Baba Hadir ya kira sunanshi kawai don jindadin halin abokin nasa. Dan daure fuska Zayyan yayi "kada ka karar min da suna. Rinka hadawa da wata kalmar don naji dadi" "Zayyan...fitina" yace yana dariya [11/2, 7:24 AM]🏽 ]🏽 : 48..💕 "Kinci albarkacin 'yarki bazan biye miki ba" Maman Danmama tace tana sakin labulen. Bata bar wurin ba Halifa yayi sallama. Muryarsa kamar a kan Salame akayi recording tuni ta gano ko waye tace ya shigo. Sai da ta fita ta harari Maman Danmama irin abin nan na danta yazo sannan tace ya shigo ciki. Kannen nasa ma an sabar musu idan sun ganshi sun ga kudi ko abincin kirki shiyasa suna ganinsa suka fara murna zasu rungume shi ya dakatar dasu. Kazamai ne na ajin karshe shi kuma tsaftarsa har taso tayi yawa. Zama ma kasawa yayi dakin wari da zarnin fitsari kawai yake yi. Rahima da kanta ke duke tana sharar kwalla ta dan dago da murmushi don tasan sunan ko da suke dadewa basu hadu ba. "Yaya Halifa barka da zuwa" Wata muguwar tsawa Salame ta daka mata "tashi dan ubanki kwadayayiya. Wuce ki tafi gidanku ai kin dubani mun gaisa ko." Zabura tayi ta mike a gigice saboda yadda ta razana da tsawar tayi hanyar kofa Halifa ya fincikota saboda gefen fuskarta kawai ya gani ya gane kanwarsa ce. "Rahima" ya furta a hankali yana kallon jajayen idanunta. Yarinyar da kadan ta fi rabinsa. 'Yar karama ce wahalar rayuwa ta tsotseta. "Cikani" tace wasu hawayen masu zafi na sauko mata ta kwace hannunta ta fita. Ta sani Ummansu bata kaunarta amma yadda take nuna bambanci kirikiri yana kona mata rai. Mahaifinta talaka ne futuk amma yana kaunarta tamkar rai. Amaryarsa da ta fara son azabtar da ita dashi da babarsa suka tashi tsaye akan ko ta rungumeta kamar 'ya ko ta koma inda ta fito. Kudin sana'arta da Salame take sakawa ido har nawa ne? Zuwan karshe gabadaya ta tattara mata kudin ta bayar. Wannan karon kuma a kofar gida taji wani makocinsu yana yiwa babanta tijara akan ya ranta masa kudin da ya biya mata WAEC da zata rubuta a farkon sabuwar shekara bai biya ba. Tilas da fito da kudin ta bashi ya bawa mutumin ba don yaso ba. Abin ko kwana uku ba'ayi ba kuma babu wanda ta yiwa lalle bayan nan bare ta sami na zuwa dubiyar. Yanzu abin takaici zani daga akwati Salame ta dauko za ta shimfidawa Halifa saboda babansa yana da kudi. Ta soma tafiya kenan Halifa ya risketa ashe ya biyota "Rahima tsaya mana" Cak ta tsaya amma bata ce masa komai ba. Hannunta ya kama ya dora mata bandir din naira dari bibbiyu sababbi "kiyi hakuri da halin Umma. Ki rike wannan zan zo gidan naku muyi magana kinji ko" "Nagode" sai dai kudin mika masa tayi yaki karba sai kawai ta ajiye akan wani bulo da yake gefen hanyar irin wanda ake zama a kai tayi gaba abinta tana goge hawaye. Ko kadan Halifa baiji dadi ba. Sai ya tuna da Radhiya tace shine babba ya kamata ya hade kan kannensa. Idan suka tafi a haka tabbas Salame zata ginasu da kiyayyar juna ne. Kana ganin Rahima kasan tana bukatar taimako amma zuciya irin tata ta sanya bazata kwantar da kai tana roko ba bare aji dadin goranta mata. Idan ruwa kadai babanta zai iya bata tasha in sha Allahu zata yi hakuri dashi bazata gaza ba. Da yake ana ji dashi ko fadan bin Rahima da yayi bata masa ba sai kudurin ko nawa ya bata sai tasa ta kawo mata. "Zauna mana mu gaisa ka tsaya" "Sauri nake yi Umma. Dama munzo da baki ne gidan Malamijo shine nace ko zaki zo ku gaisa" Fuskarta ta nuna bata ji dadi ba "can kuma ka fara zuwa?" "Ko shiga banyi ba na taho nan" "Su waye bakin?" "Su Gwaggo Mairama ne..." So tayi ta kwada masa mari sai dai kuma kada ta toshewa kanta kofar ihsani dan abinda zai bata ya fasa. "Mairaman zanje in gaisar saboda ka raina uwarka? Me ya kaika wurinta har kake cewa tare kuka zo?" Shi fa irin wadannan abubuwan ke kara nesanta shi da ita. "Umma tare muka zo daga Abuja kuma ba ita kadai bace" Tabe baki tayi "wato ka fara shege mata kawai saboda ance tana wani karatun banza a Kano kuma suna zuwa Abuja ko. To bari kaji in fada maka duka kwarewa ne a maula ita da 'ya'yan suke zubar da mutumcinsu a gaban masu kudi. Ni nafi tunanin aikatau take yi" "Umma ni zan tafi idan bazaki je ba. Na rasa me tayi miki ba kya gajiya da aibata ta. Ga wannan" ya mika mata kudi a cikin envelop da ya riko dominta. "To muje bari na dauko mayafi" tace a sanyaye bata kaunar batawa yaron nan rai. Iyaka idan taje ta yanka mata kashedi ta dena bibiyar danta ba tare suka haifeshi ba. Ba wata tafiyar kirki suka yi ba suka iso kofar gidan Salame tana ta hura hanci ita mai da. Sauran kuwa a gida ta barsu har wadda ta yaye idan ta sami abinci ta tafi musu dashi. Emzee da Ibrahim suna bakin mota suna sauko da kaya suka iso. "Drama ta barka Halifa" Emzee yace yana dariya. "Ko me akayi a dawo dashi farko gaskiya" Salame ta kallesu ta watsar Emzee sau biyu yana cewa Gwaggo Salame ina wuni tayi kamar bata ji ba. Sai yake ya yiwa Ibrahim shima bata amsa shi ba yace wai kila don tana sauri ne bata ji su ba. Ta kai bakin kofa su kuma suna fitowa. Ummi da Daada zasu yiwa rakiya da zasu tafi yanzu. Sai kuma dreban gidan su Halifa shima zai tafi idan sun tashi tafiya Halifa zai kira shi yazo ya tafi dasu. Gaban Salame wani irin bugu yayi da ta ga Mairama tayi wani irin kyau ta kara haske. Kayan jikinta a hasashen Salame sai kace wata matar gwamna. Wannan 'yar ta ta mai kama da aljanu itama ka kalleta sai ka kara ga wasu 'yan matan Zayyana da Hibba su ma kowacce ta hadu karahe. Bayan wani ta gani kusa da Malamijo suna magana ta wuce su Mairama a fusace za ta shiga cikin gidan. "Salame babu gaisuwa? Ko ba ita bace?" Zayyan yace albarkacin Halifa da ya tabo shi yana cewa ga Ummansa. Ba ta iya juyowa ba sai tsuma da take yi tun daga tsakar kanta har tafin kafa. Tasan muryar nan da irin tasirin da ta jima tana yi mata a duk lokacin da taji ta. Sannu a hankali ta juyo idanunta suka sauka akan Zayyan Muhammad Tureta mutumin da har yau babu wani namiji da ya kaishi daraja da kima a idanunta. Takowa take yi jiki a mace zuwa gabansa ta ma manta da kowa da komai sai tashin tsumin kaunar da take masa. Idanunta suna kwararar da hawaye ta kusa isa gareshi "Zayyan dama kana raye?" Malamijo gani yayi tana neman wuce gona da iri yasha gabanta "sai ki ka ga mijin kanwarki ko? Ashe tsahon shekarun nan yana daure a gidan yari" "Gidan yari? Allah sai Ya saka mana. Ni dama jikina yana bani baka barmu ba Zayyan" tace tana kuka sosai. "Zai saka mana kam ni da iyalina. Mairama matso ku gaisa mu tafi" Zayyan yace fuskarsa babu digon fara'a ko kadan. Ji wannan zubar da mutumci da take neman yi a gaba danta, mahaifi da kanwarta kuma matarsa. Ita Mairama dama tsayawa tayi ta ga iya gudun ruwanta saboda yadda ta kula kamar bata cikin hayyacinta. Da ace bata san tana son mijin nata ba sai tayi tsammanin tsabar kaduwa ce kawai. "Adda Salame yaya gida da yara? Da Halifa bai taso ki ba ma zamu tsaya a gidan naki ai su gaisa da maigidan naki" Firgigit ta tuna wai tana da aure. Amma Allah Ya isa Alh Indararo. Wallahi tayar masa da hankali kawai zata yi ya sauwake mata ta huta. Sakin fuska tayi don dole suka gaisa da Mairama ta rakata har bakin mota. Ta bangaren da Zayyan yake zaune a baya ta tsaya yayi saurin danna abin rufe window ya dage glass din. Bata bata rai ba ta dawo bangaren Mairama ta leko da kanta. "Hmm nace bari nayi miki karambani. Kun dai tambayi malamai game da matsayin auren naku ko. Kada aje ana haramtaccen zama. Idan babu auren gara a san me ake ciki tun wuri" Da Mairama tana zagi da sai ta hado mai kyau ta zubawa Salame. Wannan jaraba har ina. Daga sake haduwa dashi take kokarin dawo da maitarta a fili. "Kinsan ba sakina yayi ba kuma ban sake aure ba. Saboda haka auren mu yana nan har yanzu" "Mu tafi mana" Zayyan yace da dreban rai a dan bace tun bayan dawowarsa. Ba don ta gaji da kallonsa ba ta koma gefe aka ja motar tana tsaye tana daga hannu "bye bye, bye bye" take ta fadi tana murmushi. Hannun Mairama ya rike yana kallon fuskarta "meye na tsayawa yi mata dogon bayani bayan kinsan akan hanya muke?" Murmushi tayi ya karawa fuskarta kyau "gani nayi gara nayi mata bayani tun wuri kada tayi tunanin akwai wata kofa da za ta iya samu ta shiga gidanka" Bude baki yayi ya kalleta "kada kice min ta fada miki" "Bata ji komai ba ta sanar dani kuma shine dalilin mutuwar aurenta kamar yadda Alh Salisu ya fada min jiya da kana waya da Baban Arifah lokacin da yazo. Cewa yayi nayi hankali da ita mai hali baya fasa halinsa kuma gashi na gani" "Mairama ina so ki sani wallahi ban taba cin amanarki ba akan Salame" Kanta ta dora akan kafadarsa ta rufe ido "kada zancenta ya bata mana farincikinmu" Alamun saka zip yayi a baki yana dariya suka cigaba da hirarsu cikin shauki har suka isa Kano. Gidan da ya gina da guminsa da kuma gadon mahaifiyarsa ya shiga yana tuna baya. Saboda hazo ya fara kura amma da gani an kashe masa kudi wurin gyara da kayan alatu. Mairama ya janyo ya dora kansa a kafadarta yana tsaye a bayanta yace "kin tuna zuwanmu gidan nan na farko?" Sai da taji kunya Allah Yasa baya ganin fuskarta "ban tuna komai ba" "Da gaske? Ni kuwa kamar a kaina aka ajiye ranakun da Mairama ta rinka nunawa Zayyan soyayya irin wadda nake sa ran a maimaita. Jikina yana bani a nan kika samo Zayyan fa" "Ni dai ka kyaleni gyaran gida zanyi" tace a kunyace "Muje na tayaki ai muna da lokaci. Sai jibi zamu tafi Sakkwato in je mu hadu da Maikudi" Ajiyar zuciya tayi tana hango wannan haduwa bazata yiwa Maikudi kyau ba ko kadan. ********** Ranar da daddare bayan Yadikko ta dawo ne Radhiya taji komai game da amaryar Malamijo a wurinta. Taji zafin sakin Hajjo ita ma tayi ta bawa Yadikko baki akan kada ta tafi wa zasu gani su ji dadi. Shima Malamijon kuma sai ya fada mata abubuwan da Hajiyayyen tayi masa. "Malamijo ai kowa maye ne sai dai idan baiso nunawa ba. Ka rubuta mata takardarta tun dare gobe zaka bata kuma wallahi Hajjo kadai na yarda ka dawo da ita" "Ba ma sai kin fada ba 'Yar soja ikon Allah. Na ma gama aure yanzu sai dai ku" "Wai ni su waye ma suke yi maka waliyai ne a aure auren Malamijo?" "Kaniyarki mai ido a tsakar ka" yace yana laluben takalmi zai biyota dashi ta gudu. 11/2, 7:24 AM] 🏽 🏽 : 47..💕 'Ya'yan nasu sun hadu a falon Ummi kowa na bawa Daada labarin kansa musamman game da karatu shi kuma yana rike da Daada Karami. Radhiya ta kalli yaron ya kurawa babanta ido tayi murmushi tana tambayar Mami da suke shigowa tare da Mama suna neman wucewa dakin Ummi wai yaushe zasu yi taron sunansa ne. Mama ce ta bata amsa "babu wani taro fa Radhiya tunda babansa ya dawo me kuma zai bukata? Masu tahowa dai zasu zo amma barka kawai" "Yaya zaki yi mana haka babu shawara Zainab?" Cewar Mami tana nuna mata rashin jindadi. "Ni da dana zata yi min karfa karfa to wallahi ban yarda ba" inji Ummi tana goyon bayan Mami. Zayyan ya daga hannu kamar dan makaranta "idan kun bani dama in raba gardama?" "Mun baka" Mama tace da sauri tana neman tsira. Da Baba Hadir suka yi shawarar soke taron kawai kwanaki sun kara ja kuma ma dai dawowar Zayyan ita ce abu mafin dadi garesu. Kallon iyalan nasu yayi yana jin tamkar Allah Ya bashi fiye da abinda yake nema a duniya. Major da Hadir harda Baban Arifah da ya sadaukar da rayuwarsa dominsu batare da tunanin ko kadan zasu saka masa ba gashi sun rike masa iyali da gaskiya. Idan ya biyewa zuciyarsa kuka zai yi musu daga su har matan kwarai da suke aure wadanda suka karfafa musu gwiwa wajen dabbaka zumunci a bayan idonsa. Shi ba butulu bane da zai manta Mami Hassana wadda mijinta Major da Ummi suka bashi labarin cewa aikatau tayi a Germany domin ciyar da iyalinta amma a cikin abinda take samu Major ya rinka cire wani abu kafin ya fara aiki yana aikowa matarsa Mairama. Babu wanda baiyi masa ba amma Allah Ya sani yana jin girman Mami sosai a zuciyarsa. Daga ita har Mama Zainab sun wuce matan abokai a gareshi sai dai ya kira su 'yan uwa. Sun burge shi matuka yadda suka tsayawa juna a matsayinsu na matan sojoji suke kokarin rufawa juna asiri. Ba don a gidan iyayensa an bar kari tun ran tubani ba ai da kamata yayi ace ya dawo ya sami matarsa a tsakiyar matan su Badaru. Abin takaici shine sun tashi babu wannan shakuwar tsakaninsa da 'yan uwansa maza da mata. Jume tun kuruciya ta koya musu tsanarsa a matsayin dan kishiya. Sai dai yaji dadi da Mairama ta fada masa yanzu kam idan ka cire Maikudi tsakaninsu da sauran musamman 'ya'ya da jikokin Mal Aminu abokin babansa sai dai hamdala. Ita ma a nata bangaren rashin shakuwa da 'yan uwanta da kuma rashin tsayuwar uba akan 'ya'yansa ya sake bata lamura. Da ace zumuncin nasu mai karfi ne ya tabbatar ko a daji iyalinsa suke bazasu wahala ba. Duka rayuwar Mairama bayan tafiyarsa ai a cikin gidan mahaifinta tayi kafin ta koma Rugar Barkindo amma rashin wannan zumuncin ya sa ita da wadda bata tare da ahalinta kusan daya. "Daada" Radhiya ta dan taba shi saboda nisa da ya soma yi a tunani. Murmushi yayi a lokacin Awwab, Daddy da Baba Hadir suka shigo su ma yace "indai na isa to na soke taron sunan" "Kai da danka Daada waye zai hanaka abinda kake so" Mama tace tana murmushi. Sauran kuwa da gaske sunyi mamaki harda Ummi kuwa. Sai dai abinda yace ya sanya su wani irin farinciki a take. "A iya sanina Zayyan kaima ba'ayi taron sunanka ba ko" ya kalli Emzee da suke zaune kusa da juna shi da Ibrahim tamkar tagwaye. Dariya yayi yana zaro idanu "Daada ba dai cewa zaka yi a nade ni a shawl a koma baya ba" Ai kuwa falon ya kaure da dariyar yadda yayi har ya tashi zai bar musu falon da Ibrahim yace "irin jaririn samudawan nan kawai zaka koma". "Dawo ka zauna in karasa...Zayyanatun Daada kema ba'ayi miki suna ba" Zayyana sai ta rasa inda zata saka kanta don dadi Zayyan ya fasa mata kai yace ita tashi ce. Ibrahim ya dan kalleta yadda take dariya ta tashi ta koma kusa da Zayyan ta zauna tana narkewa "Daada ba'ayi min ba, ko kayan barka fa bana jin an kawo" "Kiji tsoron Allah" Mami tace tana dariya. "Ai kuwa duk wanda bai kawo ba muna binsa bashi. Su Ummi da Mama kowa ta kwance bakin jaka" Anata dariya ta hada ido da Ibrahim wanda ya kasa gane mata tun ranar da yayi maganar tale baki. Abin ya dame shi sosai ya kasa fadawa Emzee. Yanzu suna hada ido yayi murmushi ita kuwa ta murguda masa baki ta kawar da kai, babu wanda ya kula sai shi. Zayyan ya dago Daada Karami "kaima bakon duniya nazo na tare hanya ba'ayi maka taro an kawo kayan barka ba. Saboda haka in sha Allahu za'ayi taro na musamman idan komai ya natsa na Zayyan, Zayyan, Zayyanatu da Zayyan." Hayaniyar murnar da suka cika falon da ita ba arziki Mami tace su tashi su fita. Zayyan ya yafito Awwab da hannu. Tun shigowarsa dama baiyi magana ba sai ma dukufa da yayi yiwa abokin aikinsa text akan abinda zasu yi idan ya koma. "Idan an gama suna sai mu fara shirin bikin dana. Kunyi min komai daidai amma an bar min yaro ba aure. To mu dai yarinya ko 'yar waye tunda yana so idan ta kama na sato ta ne zanyi na kawo maka kaji ko" Idanu suka koma kansu shi da Radhiya lokacin suna rige rigen arcewa daga falon. Shi hanyar waje yayi ita kuma tayi kitchen. Su Major ma sai da suka yi dariya. "Kunga kama kai, yanzu don Allah waye yaji na ambaci suna?" Da dariya suka fita harda ta kitchen ita ce karshen tafiya. Major yace masa ya fara tara jikoki ya kamata ya rage chalikanci. "Idan na dena so kake su rinka guduna? Kuma dai shekarata nawa ina danne Zayyan Tureta ta karfin tsiya. Yanzu kuwa lokaci yayi da zai fito yayi kara'i" "Aiki ya sameki kanwata kiyi a hankali kada mu fara ganinsa da kitso da dankunne irin na matasan zamani" Baba Hadir ya rubuta ya mikawa Mama ta bata. Zayyan yana ganin tana dariya yace sai ya gani. Daga nan dai hirarsu ce da bata karewa suka dasa. Sai sakon text Alh Salisu ya yiwa Baba Hadir zai zo suyi sallama gobe zasu koma Kano da yaran. Ya kara da dan korafin wai ko basu hakura bane yana ta sa ran zuwansu gidansa ko su ko yaransu amma shiru. Baba Hadir sai yaji babu dadi ya mikawa Daddy wayar. Kiransa Daddy yayi bayan sun gaisa yace "Hadir yana mai baka hakurin rashin zuwan nasa. Wani abu ne ya taso amma idan babu takura kuma kana da lokaci kafin ka tafi goben me zai hana ka shigo ka ga uzurin nasa?" "To Allah Ya nuna mana Yasa lafiya. A gaida yaran don Allah" Da haka suka yi sallama. Matan na daki suna tsokanar Ummi amarya babu lalle babu gyaran gashi ta ce laifinsu ne. Mama tace ba don jego ba da idan ta fara gyarata sai sun biya mata Hajji da Umra. "Ni dai naga ranar da zaki girma Zainabu. Ina jin halinku ne Sakkwatawan nan. Daga ke har Zayyan sai ku sa cikin mutum ciwo da ban dariya." "Cewa zakiyi suyi abu su daure fuska ki rantse ba daga bakinsu magana ta fito ba" Ummi ta fada da dariya. "Baki ji ba wai zai satowa Awwab Radhiya ya kai masa ita. Uban amarya zai saki layi." Kowacce ka gani tana cikin walwala da annashuwa suna jindadin zama da juna sai fatan Allah Ya kade shaidanu Ya kara hada kawunansu. ********** Tun dawowar Zayyan yau ce rana ta farko da su ka kebe su kwadai da 'ya'yansu a bangaren Ummi. Ba kowa ne da wannan tunanin ba kuwa sai Mama Zainab. Bayan sun fita ta tura musu Radhiya da Emzee da sunan su je ko babansu yana son hira dasu. Babu wani boye boye tace ya kamata su bashi lokaci yaji matsaloli da cigaban rayuwarsu kamar yadda kowane uba yake yi. Radhiya taji kunya sosai ganin da su Zahra a wurin. Amma sai ta kula babu wadda abin ya dama sai ma goyon baya da su ka baiwa Mama aka korasu yau su kwana a gidansu. Ummi da Radhiya ne suka yi girki yayin da Zayyan yake sake jin daukakar da Emzee yake samu a NDA tun shekararsa ta farko. Ya yaba kwarai da dan nasa yana jinjinawa a ransa wannan wai magajinsa ne wanda bai barshi ta ko ina ba...suna da aiki. A kasa Radhiya ta ajiye musu abincin Zayyan yace ta dauko babban plate yau a kwano daya zasu ci ya ga girman lomar kowa. Da dariya aka soma ci sai gashi su hudun sun buge da zubar hawaye lokacin da ya kallesu daya bayan daya yace "ko yanzu mutuwa ta riskeni zan tafi ina mai farinciki da cika godiyata ga Allah." Ummi ce ta fara hawaye sai Radhiya ta kama harda shessheka. Emzee ma duk dauriyarsa sai da yayi "don Allah ni dai a dena kukan nan abincin da dadi amma zaku sa ya fita daga raina" Dundu Ummi ta kai masa "acicin kawai" "Zancen gaskiya Ummi. Ba abin nayi fuska na gama ci sannan nayi nawa kukan ba na rasa me tayani" "Ashe haka kake Zayyan? Shiyasa Malamijo yace yana nemanka kaje da bindiga ko ta katako ce" "Nemana kuma Daada?" Ummi ta amshe da fada musu sakonsa na dazu "sai ku shirya zamu tafi tare. Zamu barku a can mu wuce Sakkwato daga can muje Nijar" Radhiya ta rike baki "Ummi wai ni din da gaske yace ko dai kin fada ne kawai don kada nace baya sona" "Kaniyarki" ta kai mata duka Zayyan ya tare yana cewa babu mai taba masa uwa. "Da gaske nake Daada, cewa fa yake yi idan yaji muryata gabansa faduwa yake yi" ta turo baki da takaici. "Gonarsa take zuwa tace wai dabba ta kasa tasa a yanka. Ka kuma sanshi da dabbobinsa sarai" Ummi tace tana murmushi. "Amma anya lafiya kuwa yake nemanmu?" Emzee yaji abin ya daure masa kai. Malamijo fa ko waya baya kiran kowa sai dai a kira shi. Kowa da tunaninsa amma sunfi kawowa da gaske akwai matsala. Ko ma dai meye jibi da wurwuri zasu bar Abuja. Gara suyi su dawo da wuri Radhiya ta fara aikinta. Zayyan yaji dadin wannan program da zata yi yace idan tana bukatar bayani game da halin da sojojin suke riskar kawunansu a filin daga a shirye yake. Basu ankara ba suna wannan hira sai gani suka yi daya da rabi na dare. Dole aka tashi ba don sun so ba saboda hirar tayi musu dadi. Suna jindadin yadda iyayensu ke zolayar juna. Ummi tace mijinta dan saurayi ne wanda ya tafi yanzu an kawo mata wanda ya fara furfura. Zayyan yace "ko kiyi shiru ko na tona miki asiri su san cewa a wurin bin kwalaben mutane a gidan biki kina shanye ragowar mirinda muka hadu" "Bonono rufe kofa da barawo...ai ka gama tonawa" Emzee da Radhiya dariya harda hawaye. A zahiri idan kewarsa ta ishi Mairama tana bawa yaranta wannan labari amma yadda ya fada yana kwatanta yadda tayi da ya kamata dole suyi dariya. It was a time well spent a tsakaninsu. ********** "Ikon Allah jama'a dama Zayyan yana da dan uwa da suke mugun kama banda wadda na gani a wurin Zayyan karami?" Alh Salisu yayi magana a lokacin da suke shiga gidan Baba Hadir shi da yaransa ya kasa dauke ido daga kallon Zayyan din. "Nine dai Salisu ba kama bace" Gabansa yaji yayi wata irin faduwa ya shiga kallonsu yana jira wani yace wasa suke yi amma shiru kake ji. Radhiya ce tayi dabarar kiran su Halifa da kannensa su ka bita wurin Ummi. Zayyan tasowa yayi ya kama hannun Alh Salisu wanda jikinsa ya fara rawa sai kuma ya soma hawaye "kai din ne don Allah? Hadir Zayyan nake gani. La ilaha illallahu....Zayyan dai nake gani." "Nine Salisu Allah Ya dawo dani" Mamaki da al'ajabi ne ya kama shi sosai da aka yi masa bayanin dawowar Zayyan. Wannan al'amari da daure kai yake. "Gashi a hanya muke ina da taro gobe da sassafe na 'yan kasuwa. Don Allah ku tsaya a gidana idan kun shigo goben." Ita ce abinda ya fada musu karshe lokacin da suka gama hira ya tashi. Aka tura kiran yaran sai ga Halifa tare da Emzee yace a tafi a barshi zasu taho gobe in sha Allahu shima yana son zuwa Sumailan. Alh Salisu yace babu matsala a turo 'yan matan. Kusan minti goma suna jiransu suka taho da Zayyana za'a rokawa Hibbah itama ta kwana. Yayi dariya "Kuna tsareni da ido na isa na hana ne" Kananan ma sai suka hau rigima saboda kaunarsu dasu Jawad da Femi. "A'a kuma kada abin yayi yawa. Ku wuce muje su ma zasu taho gobe" "Ka kyalesu mana nan da can duka gida ne. Dama su Alheran zamu ajiye a Sumaila mu Kanon zamu kwana sai a kawo su gida" Alh Salisu yaji dadi da Zayyan bai nuna fushinsa ba da ya fada masa laifinsa na rashin kula masa da iyali. Dreban motar yaran ya roka arzikin ya koma can gidan nasa ya kwana gobe sai yazo su tafi shi kuma ya shiga mota suka tafi. Ga alamu Halifa ya damu kwarai da Radhiya komai ya kira ta ko ya sakota a ciki. Yanzu ma hira suke yi take tambayarsa yaushe rabonsa da zuwa wurin Malamijo yace ya dade sosai. "Gaskiya kazo muje ka ganshi. Kila ma har Gwaggo Salame ba ka zuwa gidanta ko?" Ta dan dage gira. "Bazan miki karya ba ita ma bana zuwa yadda ya dace da ya ziyarci mahaifiyarsa. Gidan nata ne ko hadiyar yawu bana iyawa ga yaran nan nata ko sunayensu ban rike ba sai azabar roko" Dan bata rai tayi "ba cikinku daya ba Halifa, ko zaka so ace wani bare suke roko? Wai kuwa ina dayar nan bana rike sunanta" "Rahima? Tana can nasu gidan" yace da rashin damuwa. "Ni kuwa da zaka gyara zumuncinku da ka burgeni. Dube ku duk bamu saba da juna ba haka su Ummi ma. Ita da Gwaggo Salame ban san yaushe suka hadu karshe ba" "Ke Ummanmu ko gidan Malamijo bata zuwa in fada miki." Yanayin zumuncin nasu baiyi mata dadi ba. Shi kuma da yake babba a nasu gidan sai taji ya kamata ta bashi shawarar gyara tsakaninsa da kannensa. Ko ba komai yana cikin rufin asiri zai kyautu ya rinka dan taimaka musu. Sunyi nisa suna tattaunawa Awwab ya shigo yaci karo dasu suna dariya hira tayi dadi. Tuni fuskarsa ta chanja ya koma ya kira wayarta. Tana dauka fito kawai yace ta tashi. A bakin mota ta ganshi ya jingina bayansa ya harde kafafunsa da hannuwa a kirgi. "Sannu da hira" yace fuska babu fara'a. "Hira kuma?" "Ba ita kike yi ba na taso ki" Duka girarta biyu ta rinka dagewa tana wani juya masa ido da dariya "Chèri kishi kake yi? Oh my, my , my sai naji na koma wata sarauniya" Sakin baki yayi ya kalleta kafin ya girgiza kai "mutum ma baza'a barshi ya nuna bacin ransa ba" Kashe masa ido tayi tace "no chance baby" Wani irin kallo ya bita dashi ta tsure "kasan Allah subutar baki ne ba baby zan ce ba" "Ah kawai kice kin girma. Daga fara saka min sunaye nan gaba ni din zaki dauke" Kamar tayi masa kuka ta sake cewa fitowa yayi kawai. "Saboda shine a ranki ko? Kinji me Daada yace dai ki fara hada kayanki" Dagewa tayi bisa subutar baki ne shi kuma yayo ta zolayarta sai gashi sun koma hirarsu mai dadi. "Please ni dai bana son yadda yaron nan yake shige miki. Nasan dan uwanki ne bazan rabaku amma ni dai a kula kinji ko. Ina kishinki sosai Schatzi" "In sha Allah Cheri amma nima fa kada kaje kana yiwa 'yan matan jirgin nan masu dan skirt dariya wallahi. If not za ka ganni a mafarki muna fada" "Naji...kuma banda zuwa rugar Barkindo ki rinka zuwa hira wurin Dr Zakari. Nasanki da likitoci ba sauki" Dariya ya bata sosai. Ita sai yanzu ta gane ashe lab attendant ne ba likita ba "ka doke kowa fa ni sai dreba ko ba abin hawa" Sunyi ta hira kamar kada su rabu don washegari karfe bakwai zai bar gida. Da safe da wuri ta tashi don suyi sallama duk da wayar da suka dade suna yi cikin dare don ma ya dage sai ta kwanta. Bayan tafiyarsa ba jimawa su Zahra su ma suka dauki hanya ita da Raji sai kuma tawagar su Ummi. Gidan sai yayiwa su Mami shiru don ma Fauziyya tana nan amma Ibrahim da Zayyana duk sun bisu. Shi Ibrahim zasu yi kwanaki kadan da Emzee a Sumaila su dawo Kano gidan nasa kakannin. *********** Tun dare Malamijo yake ya da habaici a cikin gidansa wanda Hajiyayye bata fahimta ba. "Gobe iwar haka watan tatse rashin mutumcin wasu zai tsaya." Hajiyayye tana sakace hakori zazzaro masa idanu "me kenan kake nufi" "Zancen zuci ne ya fito fili. Ko an hana magana ne ban sani ba?" "Kayi abarka. A dai kula ne kada yawan surutun ya tasar min yara kasan halinsu. Yanzu duk naman da suka ci sai kaji suna neman kari" Dauriya kawai yake a kai gobe amma yana cikin tashin hankalin rashin sanin ina shanunsa. Yau tun asuba yake gonar. Tsagerin yaron nata da yaje daukan wasu sai ya kasa saboda ganin idonsa da wasu bakin fuskoki dole ya tafi. "Allah Ya hada fuskokinku da sarkin mayu dai amaryata" Malamijo yace harda hade hannuwa irin na mai addu"a. Cikin Hajiyayye kuwa ya cure wuri guda a take kamar zata yi zawo "wannan wane irin mugun fata ne Malamijo?" "Ban gane mugun fata ba. Yanzu kamar ni kinsan dadin da zanji duk ranar da na hadu da Mai Martaba Sarkin Kano Dan Lamido kuwa?" Rai a bace tace "to meye hadin sarkin Kano da sarkin mayu?" "Meye ne naga kin soma gumi? Namu sarkin shine sarkin Kano. Ke kuma naku Sarkin mayu. Yadda nake son ganin namu kuma nake kaunarki shine ne nake miki fatan haduwa da naku kema" "To ba amin ba...kaga ni kudi nake so kamar dubu dari karshen wata yaran nan namu kowanne ana yi masa yanka shi kadai saboda rage karfin maitar" Allah Yaso shi ba don abinda yaji da kunnuwansa ba da yanzu hankalinsa in yayi dubu ya tashi akan neman kudin. Amma yanzu sai cewa yayi tayi hakuri zai tanadar mata zuwa dare gobe. Saboda samun wuri harda yi masa tsaki tace "to a hanzarta" "To ranki ya dade" Matsawa tayi akan katifar tana nuna masa wuri "taho mu kwanta ni bacci nake ji" Hadiyar yawu yayi saboda sai yanzu da yake sansano tsira ya kara tabbatar da kazantarta da muguwar rama. Wa ya aike shi kwanciya kusa da ita karshe kasusuwan jikinta suje suyi masa sartse ko su soke shi. Karfe takwas na safe ya soma kiran Ummi wai yana fata yaran sun taho tace masa tare zasu zo da ita harda Halifan Salame. "In kin barni na ma manta da sunansa tunda uwarsa bata san mutumcina ba. Wannan yaro ina tsammani kamaninsa ma sun bace min. Kinga sai kun taho dai. A hanzarta do Allah" Ta gama tabbatarwa lallai babu lafiya gidan nasu. Sun kimtsa kowa ya fito suka yi sallama dasu Mami da Mama. Emzee da akace ya sako kayan makaranta sai ya sami irin shirt dinnan da ake yi da zane zanen khakin sojoji ya saka akan bakin wando. Radhiya kuma atampa ta saka da mayafi tayi kyau sosai. Umminta kuma wani lace ne dan ubansu mai tsada da kyau ta saka green da orange ta dora orange din mayafi da farin gilashinta tayi kyau sosai Zayyan ji yayi kamar a dage tafiyar ko na awa guda ne ya samu ya yaba mata yadda ya dace. Dadinsa ma mota guda Daddy ya bashi da dreba daga shi sai ita. Motar gidansu Halifa kuma mai wuri uku ce yaran suka duru a ciki. Abinka da tafiyar sammako da kuma rashin tsaye tsaye a hanya karfe hudu suna cikin garin Sumaila. Shekarun baya ne suka rinka dawowa Zayyan. Zuwansa garin nan na karshe lokacin da Mairama tazo yawon arba'in din Alheran ne. Yanzu gashi Alheran dinsa aure yake shirin yi mata. Bacci ko na minti biyar bai iya yu ba sai kalle kallen chanjin da aka samu. Kafin su karasa gidan Malamijo motar da su Radhiya suke ciki ta tsaya daga bakin wata kwana. Halifa ne ya sauka ya taho wurin motar su Ummi ya leka ta taga. "Gwaggo Mairama nace bari naje wurin Umma na fada mata kunzo tazo ku gaisa kafin ku wuce Kanon" Zayyan bai manta da wace Salame a baya ba kuma har yanzu ba wai yana dokin ganinta bane. Ya kula Halifa yaro ne mai nutsuwa daga jiya da suka kwana gashi uwa uba da ga Alh Salisu. Jiyan da Mairama taso sanar dashi cewa sun rabu da baban Halifa saboda kada yayi masa maganarta sharewa kawai yayi. "Ta san da zuwan naka ne?" Ummi ta tambayeshi. "Bata da waya amma nasan zata zo ko don ta tayamu murnar dawowar Daada" ya kare da murmushi. Suna kallo ya gangara daga baya sai ka rantse wani babban Alhaji ne. Girman jikinsa da irin shaddodi da yadikan da yake sakawa suke kara masa cika ido. Malamijo yau ko kofar gida bai leke ba yana jiraj zuwan bakinsa. Abinci biyu akeyi yanzu a gidan nasa. Nasu Yadikko daban na amarya da iyalinta daban. Kunya tasa bai iya fadawa Yadikko zuwan bakin da bai ma san suna da yawa ba kuma. Ita ranta ya dade Hajiyayye kuma babu dalilin da zaisa ya fada mata. Dirin mota yaji yana kashingide a tsakar gida daga shi sai dogon wando da 'yar shara duk sanyin nan ba ji yake sosai ba ya tashi da sauri kai baka ce tsoho bane mai shekarunsa sam baya jin jikinsa. Silifas dinsa ya saka yana washe bakin nan Hajiyayye ta fito daga kitchen da katuwar cooler shakare da farar shinkafa 'yar gomnati ta dafawa 'ya'ya zasu zo su ci banza. "Ina kuma zaka je kake wannan saurin? Ga abinci ka jira in dan tsakura maka ladan ganin ido ko" Bai ma jira masu tare masan sun shigo ba ya dora hannuwa a kugu ya daure fuska "a cikin gidan nawa kike zancen tsakura min abinci? Ashe baki da mutumci ban sani ba. To ki jira in dawo ciki zaki ga yadda zanyi dake mutuniyar banza" Ta tsorata sosai amma sai ta dake kada tayi saurin nunawa "ni Hajiyayye kake yiwa wannan magana? Ko magagin baccin da ka soma ne bai sakeka ba?" Kallon banza yayi mata harda su juya idanu yau take sallah fa a wurinsa ya fita a gaggauce. Kiris ya rage ya saki fitsari da ya ga 'ya'yan Hajiyayye ne ashe a akori kura manyan mazan su uku katti dasu tamkar ba daga cikinta suka fito ba. Dirowa suka yi daga bayan motar suka cewa dreban yaje gidan gonar ya jirasu. Zasu ci abinci ne su zo a dauko shanu ko hudu ne idan motar zata dauka. Idanun Malamijo sai suka kawo ruwa ya fara kokawa da kwalla. Samarin suka sauko kai cikin gidan suna muzurai su a dole mayu 'ya'yan mayya. Tsabar wulakanci basu duba tsufansa ba suka ringa bangazar kafadarsa suka shige cikin gidan. Jiki a sanyaye ya juya zai koma sai ga wasu galla gallan motoci guda biyu sun doso gidan. Ihu ne kawai baiyi ba don tsananin murna ya koma daga soron ya tsaya yana jiransu. Jin kansa yake daidai da kowane maye da yake cikin gidansa. Emzee da Ibrahim ne suka fara shigowa ya tarbesu cikin nishadi. Sai 'yan mata Hibbah da Zayyana sannan Radhiya ta biyo bayansu. "Malamijo nawa" tace tana murmushin da ta saba idan zata yi masa tsiya. "Yanzu ace kin zo kasar 'Yar soja bazan ganki ba sai nayi cigiya? Ina Mairaman take? Duniya Mairama duk tafi sona kaf 'ya'yan babu mai girmama maganar Malamijo kamar ta." Yayi maganar batare da korafin Radhiya kada tayi masa wani abu ba daidai ba a cikin gidan. "Uhmm Malamijo tare fa muke da..." Emzee ya soma fada masa saboda yana tunanin gara ya sani kada abin yazo masa a bazata. Hannu ya yarfe gefe yana kallon Mairama da wani mutum yasha yadi na maza mai masifar kyau da tsada cikin wanda Baban Arifah yasa aka dinka masa. "Ko ma waye su zo ku hadu ku ci uban 'yan iskan gidan nan" "Su wa kenan?" Radhiya tace da doki sai dai Malamijo baya ma jinta ko kadan. Mutuwar tsaye yayi hannunsa a kahon zuci yana farfar da idanu bakinsa ya kasa hada kalmar Zayyan da yake son ambata. Zayyan na karasowa da murmushinsa ya mika hannu ya riko hannun daman Malamijo. Ai hannuwansu na haduwa Malamijo yayi sharaf a sume ya fado masa a jiki. Dama sun sani dole ya tsorata. Emzee ya rugu zai daga shi Zayyan yace ya wuce su gyara inda zai kwantar dashi ya ciccibe shi shi kadai tamkar ya dauki yaro karami. To abu ne babu body babu alamar body. Dama ya lafiyar kura...tuntuni babu jikin Hajiyayye mayya tazo ta karasa gawar da ba tata ba. Tsakar gidan babu kowa sai gayyar su Hajiyayye rashin wadatar dakin yasa ta dawo dasu nan duk da ma dai akwai sanyi garin. Banda cooler din shinkafa a gefe ga ta miyar da ta wadatu da nama na tinkiyar da suka dauko jiya ga salad da su tumatir yau din bushasha za'ayi saboda jiya sun tarki sa'a. Shanun da suka dauka suna ajiye a gidan Talle ranar kasuwar dabbobi zasu kai a kwashi naira. Da sauri Emzee ya shigo sabuwar tabarmar da ta shimfida yaran nata sun soma zama ya murtuke fuska duk da bai sansu ba "kai ku tashi" "Yaro kai kuma daga ina?" Babban cikin nasu ya tambaya yana masa kallon raini. Ido kawai Emzee ya watsa masa yaja baya da sauri. Tsabar training sai budewa kwanjinsa yake yi musamman daga kirji, hannuwa suna murdewa irin na kakkarfan namiji. Rigar jikinsa ma kusan ta kama shi ita ta karasa tona asirin yanayin jikin nasa. Wanda ya rage akan tabarmar mai bin babban ya kalla yayi masa alamar ya tashi. "In naki fa?" Emzee bai sake tunani ba ya ja tabarmar ya kifar dashi a wurin ya koma gefen dakin Malamijo ya shimfide masa ita sannan ya shiga ya dauko masa filo. Radhiya dakin Yadikko tayi da sauri ta same shi a rufe da karamin kwado sai ta je na Hajjo. Nan ta tarar da komai ba yadda ta sani ba sai karajin Hajiyayye daga bayanta. "Ke daga ina kuke ne kike leka min daki?" Da mamaki tace "dakinki? Ina Hajjon kuma?" Daidai nan Zayyan ya shigo da Malamijo a hannu ya kwantar dashi a inda Emzee ya nuna masa Ummi tana take masa baya hankali a tashe. "Ku su waye ne?" Hajiyayye ta matso inda suke ta kalli Malamijo ta watsar. Cikin salama Ummi tace mata "ni 'yarsa ce wadannan kuma yarana ne da babansu" Tsaki taja duk da suturun jikinsu sunyi mata kwarjini amma bata so raini ya shiga tsakaninta dasu. Yadda uban yake tsoronta to kowa ma fa yaji tsoro kada a kawo mata wargi ba dauka zata yi ba. "Me ya same Malamijon?" Tace a dakile wanda tuni ran kowa ya sosu. "Tsorata yayi ya suma" Ummi ta bata amsa. "uhmmm" ta tabe baki "bana son hayaniya kamar yadda shi uban naku ya sani a kiyaye" Hayaniyar da take yi ce tasa mutanen cikin gidan suka fara lekowa ganin da wa take yi. Na'e ce kawai da wasu cikin yaran. Yadikko sun tafi asibiti da Atine guda cikin jariran babu lafiya ko ta kan Malamijo bata bi ba da zasu tafi. Ita yanzu burinta kawai Atine tayi arba'in yaran su kara kwari itama ta tafi. Shekaru sama da arba'in tana zaune tamkar sharar gidansa ta kula masa da yara ya bude baki ya fada mata magana son ransa. Kannen Mairama da suke zawarci su biyu da sauran kannensu duk sunyi zuru zuru amma ganinta sai gasu sun fara sakin fuska suna yi musu barka da zuwa. Hajiyayye ta wani daka musu tsawa saboda tsaurin ido "ba cewa nayi idan yaran nan sun zo cin abinci kowa ya zauna a daki ba? Ko shi Malamijon bai nanata muku ba kafin shigowarsu?" Mayunwatan yaran kananun suka matso suna jira ta zuba musu ta kalli tabarmarta "ku shiga dakinsa akwai tabarma a bani tawa zan ciyar da yaranmu" Zayyan da Mairama sun tsaya ne kawai kallon wannan mata mai zubin mahaukata tana ta bada umarni a gidan. Daurewa tayi ta tambayi wata kanwarta matsayinta a gidan. "Amaryar Malamijo ce" "Amarya kuma?" A iya saninta babu sauran wuri a gidan nasu to wa ya saka. Sai gashi kafin ta tambaya ma ta bata amsa da cewa Hajjo ya saki "Malamijo Hajjo?" Tace kamar tayi kuka. Kanenta da suke karatu a Kano gidanta su Laila duka lokacin da suka zo kafin ta wuce Abuja tasa sun tafi hutu wurin iyayensu mata. Ta san da tuni ta sami labari a wurinsu. Babu wanda yayi motsi da Hajiyayye tace su dauke Malamijo daga kan tabarmarta ta doki cinya tana sababi wai zai farfado ya sameta ne sai ya yiwa bakin nan bayanin matsayinta. Abin takaicin ya ishi Zayyan zaiyi magana Ummi ta dakatar dashi ta nuna masa Radhiya da take bin matar da wani irin kallon raini "Baki ga suma yayi bane kike zancen a baki tabarma ku ci abinci?" "Yarinya kada kice zaki yiwa Hajiyayye rashin kunya wallahi sai na farfasa miki jiki yanzun nan a wuce wurin" babban yace a kule yunwa na cin hanjinsa an tsaya ana bata musu lokaci. Ko kadan daga uwar har yaran basu da da'a. Sai da ya gama Radhiya ta tafi gaban kulolin da ta kula suna yiwa kallon mutumci ta bude da ta ga miya ce nama ya kusan cika ta. "Wa ya baki izinin taba min abinci? Ke idan Malamijo ya farka zan iya sawa ya hanaku sake zuwa gidan nan" Emzee da Ibrahim Radhiya ta nunawa kulolin da hannu tamkar ba da ita ake magana ba "bros ga fa abinda ya kawomu Sumaila kuzo mu fara aiki" Tamkar masu jira suka je zasu dauki kulolin nan yaran Hajiyayye suka yi kukan kura tamkar mayun gaske. Duk abinda suke yi Malamijo ya farfado ya ma dan bude ido da ya ga abu ya soma kankama ya runtse kayansa ya cigaba da kwanciya. Ummi da Daada wuri suka samu suka zauna saboda abin kunya ne ace suna da su Emzee su rinka saka baki suna magana da yara irin na Hajiyayye. Ummi tana da yakinin indai da yaranta a wurin bata da matsala don ko da Radhiya kadai ta barsu ta ishesu. Wurin ke neman kacamewa Radhiya ta kira Zayyana ta nuna mata kula daya tace ta zauna a kai itama ta zauna akan daya ta dora kafa daya kan daya. Tsagerun Hajiyayye suna son tashinsu amma yadda take kada kafa ga wasu maza a tsaye a gefe wato Emzee da Ibrahim kowa ya tamke fuska duk sai suka sha jinin jikinsu. Malamijo da yaji abin baiyi masa ba ya dan kyallo ido daya yace "Zayyan" Uba da da ne suka amsa a tare. Wai shi Malamijo a tunaninsa ko dai Hajiyayye mayar gaske ce take son tsorata shi da fatalwar surukinsa zai daure ai ba'a san Fulani da tsoro ba ya dauke kai kamar bai ganshi ba ya cigaba da cewa Emzee "ina rundunar sauran sojojin da kace zaku zo tare?" Ba yaran ba Hajiyayye ma sai da cikinta ya bada sauti "soja kuma" Emzee ya sake mazewa sai lokacin ta kula da kayan jikinsa ma. Hankalinta yayi mummunan tashi kuwa a tsorace ta cewa manyan su fita zata san abinyi. Su ma da sauri suka fita din kada rundunar sojojin su iso. Tana kallo Radhiya ta kira yaran gidan suka debo kwanaku yau ko biki ake a gidan sai haka. Abincin nan tas ta rabe musu harda kwakkwafe kular bata bar ko kwayar shinkafa ba. Zayyan kallonta yayi ya saki murmushi kawai tana kara burge shi. Haka yake kaifi daya kuma haka yake son 'ya'yansa. Kada su cuci kowa kuma kada su bari a cuce su. Bayan ta gama ta tura kular wurin wanke wanke ta dawo kusa da Malamijo ta zauna. Hajiyayye ta rasa me ya kamata ta yi saboda bacin ran da take ciki. Wannan wane irin mutane ne suka shigo gidan da yake karkashin mulkinta suna neman chaza mata kai. Kwafa tayi ta bar wurin ta tafi daki zugar yaranta suna biye da ita ana kukan nama. Malamijo sai lokacin ya bude ido yana murmushi a hankali yadda babu mai ji sai na kusa dashi yace "Alakakai gayyar mayu daga nan ma sai gidan tsoho" Radhiya tace masa "fadi da karfi mana taji Malamijo a haka bazata san kana yi ba" "Barni da ita a hakan ma kun more min su. Bana so taji ne ta dawo" "Barka da yamma Malamijo" Zayyan yace bayan yaran sun gama dariyar kalaman Malamijo. Jikinsa ne yayi wani mugun sanyi kamar an sare masa gwiwa ya juya ya tabbatar Zayyan din ne dai yake gani kawai sai ya koma ya kwanta ya rufe idanu. "Mairama kirawo matar nan tazo ta tsallake ni." "Tsallakewa kamar wata mayya" "Yo ba mayyar bace? Aure ne na kaddara na kwasowa kaina. Yanzu don bala'i ko yaya na kalli bangaren arewa maso gabashin inda kike zaune sai in rinka gane gane" Ibrahim da Emzee ne suka fara dariya Ummi ta hararesu. Zayyan da ya gane dashi ake dole ya rike tashi dariyar a gaban suruki. "Kamar me da me kake gani?" Radhiya ta tambayeshi tana danne dariyarta. Fuskarsa sai tayi kalar tausayi ya kalli Ummi yana girgiza kai "ina tsoron fada in saka babarku kuka". Kasa daurewa yayi da ya kyalla ido ya kuma ganin Zayyan a zaune " 'Yar soja mai kamar mahaifinku matar nan tana son yi min cune. Dadin abin ma dai tsakanina dashi sai alheri har muka rabu muna mutunta juna" Dariyar kowa a take ta fito fili Zayyan ya matso ya sake kama hannuwan.Malamijo da yake shirin sandare masa saboda tsoro "nine dai Zayyan ban mutu ba" "Minal hubsi wal haba isi....tuf, tuf" ya mike tsaye jiki na tsuma amma a dole dauriya zaiyi yana tofe tofe "kakana malami ne har ya mutu kuma sunansa naci har wata fatal..." Ummi gani tayi abin ya soma yawa baban nata yasa yara suna dariya ta tashi ta riko hannunsa suka zauna kusa da Zayyan. "Malamijo Allah Yayi da ransa ashe rufe shi akayi a kurkuku a can kasar da suka je yaki." "Ki bari dan Manzo" "Taba shi kaji wallahi shine" Ali gadanga Malamijo ikon Allah sai kuka yana shasshafa jikin Zayyan. "Allah Qadiran Ala Mayyasha'u. Zayyanu kana nan dama?" Zaman jajantawa akayi ya kira Na'e da bata sanshi ba a wurinta yake jin Yadikko ta fita. Sun dan taba hira aka tafi yin sallah Mairama ta fada masa Kano zasu wuce a bar masa yaran. Bai fada mata komai game da Hajiyayye ba sai iya wanda idonta ya gani. Dan sauran mutumcinsa yaji yana son karewa a idanunta. Idan sun tafi zai fadawa su Radhiya ko da ja a kasa su fitar masa da ita da yaranta. Kuma a nemo masa shanunsa kafin jininsa ya karasa hawa. ********** Kyakyawar matashiya ce irin wadda ake kira black beauty durkushe a gaban Salame tana sauraron fadan da take yi mata tana share kwalla da kasan hijabinta. Salame ta zama tamkar wata almajira a yankwane duk ta tsufa fiye da shekarunta hakora sun soma yin wani layin kore kore daga sama ta kankance idanu tana surfa mata masifa har wani yawu ne yake kumfa kumfa daga gefen bakin. "Banza jinin matsiyata. Dangin ubanki kaf basu da farcen susa sai kwala kwalan idanu kamar mujiya. Yanzu Rahima banda baki daukeni a bakin komai ba in aika miki cewa bani da lafiya amma kizo min gida hannu na dukan cinya" Muryarta har ta dashe saboda kuka a tsakar dakin da ko arzikin leda babu ga kannenta 'ya'yan Alh Indararo sai murguda mata baki suke yi da masu gwalo tace "Umma wall..." Hannu ta kai ta mangareta "rufe min baki zaki fara sakin karya yadda ubanki yake yi. Kina sana'ar yin kunshi amma 'yar kazar nan ko ki dan kullo kudin ki bani domin saka albarka ya gagara. Kinfi ganewa ki bawa matsiyacin babanki ya ciyar da matarsa da 'ya'ya ni da na tsugunna na haifeki ko oho" Maman Danmama ce ta dago yagaggen labulen dakin ta leko "ke kuwa Salame ki bar yarinyar nan haka mana. Tun shigowarta kin sakata a gaba da bala'i kamar baki san ciwon haihuwarta ba" Cike da masifa ta dago "ki dai zuba ruwa a kasa ki sha kawai saboda farinciki. To dai duk tsiya tafi Danmama da yake karen mota a tasha" 💕[11/2, 7:24 AM 49 💕 🏽Radhiya bata kwanta ba sai da ta gama tsara yadda za ta yi da Hajiyayye gobe. Ba'a taba mata kaka a kwana lafiya. Yadda ta rabe mata abinci bata sami ko loma daya ba haka da daren ma dan kadan ta ce Na'e ta zuba musu ita da yaran. Bakinciki yasa Hajiyayye ta kasa komai saboda sau uku tana kokarin zuwa dakin Malamijo sai ta tarar da Ibrahim da Emzee a kofar dakin kamar suna gadinsa. Bayan kowa yaci abincin safe ne Radhiya ta fito tsakar gida tana tambayar waye mai girki yau. Yadikko ta kama kunnenta ta rike. "Na fada miki babu mai girki a gidan nan sai amaryar kakanki. Na'e ma da tayi tuwon dare jiya kawaici tayi miki bata ce komai ba" Hajiyayyen rabewa tayi a jikin kofar dakinta tana jinsu tayi murmushi. Ashe dai Yadikko tasan matsayinta. Idan suka yi kuskuren biyewa wannan yarinyar za ta barsu da jidali ne idan ta tafi don duk wanda ya shiga gonarta sai ya gane kurensa. "Tunda babu mai girkin dole ni zanyi kenan da kaina. Bari na leka Malamijo ya bada shanu uku ma sun isa da za'ayi yanka" "Yanka kuma? Radhiya idan kika zo gidan nan bakya zama kiyi ta mana jaye jaye. Nama kuma kema kin sani ba'a kawowa gidan nan har kike kiran yanka." Bata ankara ba sai ga Malamijo ya fito yau dai sanyi ya saka shi saka kayan kirki ya rufe kasusuwan jikinsa. Daure fuska yayi yana hararar Yadikko. "Kinji nace bazan bada shanun bane da zaki yanke min hukunci? 'Yar Soja guda nawa kuke bukata?" "Uku tace" inji Emzee da suka gama sanin me take da niyar yi. "Amma shanu uku 'Yar Soja waye zai taya ku aikin naman? Yayi yawa. In baku daya dai yau kowa yaci" Murmushin mugunta tayi da Ibrahim yayi mata alama cewa fa Hajiyayye ta leko daga dakinta tana sauraronsu. Haka take so taji ko wani nata yaji a kai mata rahoto. "Kada ka damu naman nan ba mune zamu ci ba. Wadanda za'ayiwa yankan kuma danye suke so" Idanu Malamijo ya zaro "Hajiyayye zaki yiwa yanka?" Sai da ta kula kowa ita yake sauraro ta dare kan turmi ta zauna "Bakina dai da zasu zo. Jiya da na ga yadda gidan nan ya koma shine na kira Sarkin mayun Faransa...can inda nake karatu. Dayake muna mutumci da 'ya'yansa sai ya daukeni kamar 'yar cikinsa. To shine nayi masa maganarka na cewa ka auro mayya. Yayi ta mamaki tunda yasan ni ba mayyar bace. Shine fa yau da sassafe ya kirani wai ya kai maganar can ofishin majalisar dinkin duniya akan harkar mayu sun ce zasu turo wakilai azo ayi bincike ke" Idanun Malamijo tuni suka raina fata ya hau rawar jiki "ni nace kiyi zancena da wasu ne? Haba Radhiya ashe baki da hankali ban sani ba. Mayun Najeriya basu cinyeni ba sai na Faransa" Yadikko tana ji tasan sharrin Radhiya ne amma yadda idanun Malamijo suka kada suka yi ja sai ta kyale ko banza ta rinka tunawa tana dariya. Cikinsu Ibrahim ne ya iya daure dariyarsa yace "Turawan mayu inajin kince basa cin mutane sai mayu 'yan uwansu ko" "Eh mana, matsalar dai bincike zasu zo yi. Wai ashe daga last year aka haramtawa duk wanda ba maye ba auren maye saboda gudun rigingimu da suke tasowa." Ta yi kamar ta rage murya za ta yi rada bayan ta san sarai kowa yana ji "yace zasu kama duka mayun gidannan ne a tafi dasu. Hukuncin take dokar shine kisa ta hanyar babbakaraisin din mayun a baiwa oganninsu su ci da bredi" Tsuuuu zawo ya nemi saukowa daga jikin Hajiyayye cikinta na murdawa tana matse shi da kyar saboda tsabar kaduwa. Babban yaron da tazo dashi gidan ashe shima yaji ko takalmi bai saka ba ya fito daga dakin nata a guje Radhiya tana a kamo shi. Dayake ba niyar kama shi da gaske suka yi ba da gangan suka bari ya gudu. Ragowar yaran nata ta kalla tace kowa ya tashi tana uban gumi kamar wadda tayi tsere. Muryar Radhiya taji tana magana da yaren da bata ganewa. Wayar karya ta gama da French ta juya ta kalli Halifa da yake jindadin wannan drama yayi ta dariya kamar cikinsa zai kulle "ka rufe kofar nan. Yanzu suka kirani wai ashe sun ga fitar daya kuma sauran ma sun gama shiri yace idan wani ya sake fita daga gidannan harda mu za'a ci da bredin" Hajiyayye da gudu ta saki mayafinta hankalinta gabadaya ya tashi. Ta ma rasa da me zata ji. Talle da yaki daukar wayarta tun safe taji ya ake ciki game da shannun ko kuwa wakilan majalisar mayu da za'a turo su kama ta. Acinyeki da bredi wata zuciyar ta tuna mata. Harda guntun hawaye sai da tayi bata ankara ba kafin ta daure ta fito inda suke. "Uhmm nace Malamijo yau me za'a dafa da rana ne? Naga ana ta hira shine baku kirawoni ba" wai ita nan za ta bagarar kamar bata san me suke yi ba. Daga nan ta samu ta arce. Ofishin 'yan sanda zata je ta shigar da kara kafin turawan mayun su iso azo a fitar mata da yaranta. To shima ba wai yana cikin hayyacinsa bane duk ya gama tsorata ya fara danasanin kiran Radhiya. Yarinyar nan da ya gama sanin halinta me ya kaishi kiranta da kansa. Wayarta ce tayi kara a lokacin taken wakar Celine Dion ta film din Titanic wanda ta sanyawa Awwab. A wurinta wakar bata tsufa sai ma nishadin da take saka ta idan ta tuna masoyinta. Idanun Malamijo da na Hajiyayye basu da na biyun kwatance a lokacin. Tsoro ne karara ya bayyana ita kuwa tana dauka da turance tace masa "Chèri please follow my lead i'll explain everything later. Say something in German" (ka biyewa duk yadda kaji nayi, zanyi maka bayani daga baya. Ka yi magana da yaren Jamus) Yana cikin office dinsu a lokacin ya kirata. Abinda tace kawai ya isa ya saka shi gane cewa akwai abinda take yi. Alheran dinsa bata ji, sai dai kuma idan ta canja daga yadda take ta tashi daga yarinyar da ya fara so daga haduwar farko kenan. Fitinanniyar dai ita ce tashi mai sanya shi nishadi a kowane lokaci. Speaker ta sanya kowa na ji ya rinka yi mata kalaman soyayyar da yasan cewa ba fahimta take yi ba ita ma. "Amaryar Malamijo kin dai ji me yace. Wai ku jeru a daki ke da yaran naki yanzu zasu shigo. Idan anyi binciken sun ware mayu a cikinku sai su saki sauran" "Inji uban wa akace mu mayu ne? Garin nan waye bai san gidan iyayena ba? Malamijo kace wani abu mana" ta fada a raunane hawaye na zuba. "Ince me? Na auro mayya tayi sanadin da majalisar dinkin duniya ta mayu zata zo gidana" ya ce gumi na karyo masa. Gidan gabadaya yayi masa zafi dari bisa dari ya yarda da zancen Radhiya. Wayar ta dan kara a bakinta "ranka ya dade ko za ka danyi mata hausa ta fahimta. Mayyar da ta auri kakan nawa ce ta fito" ta kalle su "shine wakilinsu da yake kula da hausawan mayu" "Bata wayar" Awwab yace dariya na ciwo shi. Wace mai tsautsayin ce wannan ta shiga tarkon Alheran? Ai Hajiyayye na jin haka ta zube a kasa ta fashe da kuka. Tsoro yayi mata yawa zawon ya fara tsartuwa daga ma'ajiyarsa saboda tsoro. Muryar Awwab dama irin wannan deep voice din ce mai tahowa daga kirji. Mata da yawa suna fadawa soyayyarsa a kanta yayin da take razana marasa gaskiya irin Hajiyayye. "Kayi min rai ranka ya dade aradun Allah karya nake ni ba mayya bace. Mutum ce kamar kowa kuma indai aurene ko bai sakeni ba ni na saki kaina yanzu zan tafi ba sai kun zo ba" Dariya yake neman yi Radhiya tace da sauri "ranka ya dade bari na tayaku binciken kafin ku iso zan tabbatar da gaskiyarta" kashe wayar tayi ta ga kowa ya fara ja da baya saboda zawon Hajiyayye. Wari ya isheta amma haka ta daure bata matsa ba. "Me kike cewa?" "Nace ba, aurena da Malamijo wallahi duk shiri ne tsakanina da Talle. Rabonmu kawai muka zo yaga mu tafi amma bani da alaka da mayu. Kuyi hakuri yarana akwai marayu a ciki. Waye zai kula dasu?" "Tunda har kun iya kulla cuta ki shirya ko ba'a kamaku an cinye ba zaki shiga prison. Kurkuku nake nufi" Emzee yace yana cin magani. Rarrafawa tayi wurin Malamijo wanda hankalinsa ya kwanta da ya gano me Radhiya ta shirya. Dage hanci yayi ga wari ya dame shi "ki kwashe yaranki kada ki koma min cikin dakin Hajjo. Daga nan ki tsaya ki kirawo su. Sannan shanuna...." Tana kuka tuni ta mike tana gyara zani babu kyan gani tace "suna gidan Talle" "Me kike jira ne baki fita ba sun kusa isowa" Radhiya ta dada tsorata ta. Yaran ta kira suka fito a gurguje kan kace meye wannan sun fita Malamijo yana daga murya yana sanar da ita saki uku yayi mata. Suna fita gidan ya kaure da hayaniya da murna. Malamijo tsananin farinciki yace "kowa ya shaida wallahi na bawa 'Yar Soja kyautar tunkiya, akwai wata mai ciki ta zama taki" "Ahhh nifa gaskiya tayi min kadan" tace tana tura masa baki. Baiyi fushi ba ya saki fuska "to me kike so Alherin babanta" "Alheran ne fa ba Alheri ba" "To ni dai sammakal...me kike so? Kai ku fito kowa yayi shaida zan yiwa babbar jika ta kyautar bajinta" "Ni dai kada ka kasa fa" "Ke! Dube ni nan da kyau Ali Gidado nake. Ciki lafiya baka lafiya. Da kudina a jikina" Kowa ya fito harda maijego Atine. Hassana da Usainanta suna bayan Zayyana da Hibbah da suke jindadin daukar yaran. Radhiya ta dan hadiyi yawu kafin tace "Malamijo za ka dawo da Hajjo ko?" "Kamar da kasa yarinya. Ai da shike Allah Ya taimakemu dole mata suke idda kinga bata gama ba har yanzu da damar kome tsakaninmu" "To dama so nake tunda ka yarda za ka min abinda nake so su duka matan nan ka hada da Nene Marka da kai kanka Hajji me zuwa ayi daku" Yawu mai daci ne ya tokare masa a wuya da yaji me tace. Dan murmushin nasa ya bace bat. Hajji har mutum shida kamar tana son talauta shi. Bai bata amsa ba yace Emzee su zo su tafi gidan Talle a fito masa da shanunsa. Radhiya tace to a bata tinkiyar mara ciki a yanka. "Indai nama ne muje gonar sha Allah an dena miya lami a gidan Malamijo amma ki sake shawara akan batun zuwa hajji. Idan ba kaina zan sayar ba dame zan biya kudin" *********** Safiyar laraba washegarin tahowarsu daga Abuja jiki a sanyaye Ummi ta ajiye wayarta tana matsar kwalla a boye. Ashe Daada yana kula da ita. Fita tazo yi daga dakin saboda kukan da ya taho mata ya yi saurin tare hanyar. "Haba Fillo me zaki boye min? Waye ya rasu kike kuka kuma baki son na sani?" Kukan gabadaya ya taho mata yana rarrashinta sannan da kyar ta fada masa cewa matar Badaru ce ta kirata wai yau sadakar uku na rasuwar Mal. Aminu abokin mahaifinsa mai matsayin uba a gareshi wanda yake ta dokin zuwa ya gani. Jikinsa ne ya saki ya zauna ya dafe kai. "Sojana kayi hakuri" tace wata kwallar na taruwa a idonta. "Waye ya isa yaja da ikon Allah? Zamu iya tafiya a yau ko kin gaji?" Da sauri ta tashi "muje yau din." Ba wasu kaya suka baza ba, abinci ma siya sukayi jiya da yau din shiyasa cikin abinda bai kai minti shabiyar ba sun gama kimtsawa dreban kawai suke jira yaje siyan mai. A hanyarsu ta zuwa Sakkwaton babu wata hira. Zayyan yaci burin zaman hira da Mal. Aminu Allah bai nufa ba. Sun isa da sauran haske Ummi ta rinka kwatantawa dreban Daddy din da ya kawosu. Zayyan ganin garin yayi kamar ba Sakkwaton da ya sani ba. Kamar sauran wuraren da ya gani nan ma an sami chanji na fasalin abubuwa da cigaban rayuwa. Karuwar tituna da gine gine yasa bai gane lungun gidan nasu ba. Har yanzu dai mota bata shiga amma duk da haka wurin ya sauya. Sun fara tafiya Ummi ta dan dakatar dashi da suka karya kwanar gidan Mal. Aminu maimakon su mike hanyar gidan nasa iyayen. "Ko za ka jira na fara zuwa na sanar dasu kada ganinka ya tsorata mutane da yawa." Bai musa mata ba don yasan gaskiya ta fada. Ita kadai ta karasa kofar gidan daga gefe an saka rumfa inda maza suke nasu zaman makokin. Kan ta a kasa taji an kira sunanta "Maman Radhiya kece da yamman nan?" Rayyanu ne yayan Zayyan wanda yake bi. Gefe ta dan matsa yazo ya sameta suka gaisa. "Kinje gidan babu kowa ko? Da yake yau za'a rufe zaman makokin duka muna nan" Ta'aziyya ta fara yi masa kafin cikin nutsuwa ta sanar dashi dawowar Zayyan a takaice. Ikon Allah kawai ya rinka ambata kafin yace ta shiga ciki zai taho dashi. Tana kallonsa ya duka yana yiwa Badaru rada kafin ta karasa shiga gidan. A tare suka nufi hanyar da ta baro da sauri kamar zai tafi kafin su karasa. Dan uwa dan uwane komai lalacewarsa. Lokacin da yake tare dasu a shekarun da suka gabata kiyayya, kyara, hassada da bakinciki ne kadai abinda yake gani a idanun 'yan uwan nasa. Yanzu kuwa kafin su karasa gaban juna daga shi har su hawayen farinciki suke zubdawa. Dayake dreban Daddy yana da labarin yadda akayi zaton Zayyan ya rasu da dawowarsa baiyi mamaki ba da ya ga magidanta irinsu rungume da juna suna hawaye. Hakuri ya rinka basu amma sai da kyar suka iya mallakar kawunansu don ma a waje suke. "Muje Jume ta ganka Zayyan." Badaru ya ja hannunsa kamar ya kama yaro. A ciki kuma bayan yin gaisuwa ga Gwaggo Ladi da 'ya'yanta mata dake wurin Ummi ta matsa kusa da su Mubaraka da matan su Badaru ta fada musu dawowar Zayyan. Matan mazan na alhini yayunsa mata suna kuka. Jume ta zaga bayi sai Gwaggo Ladi suka fadawa. Hankula suka tattara suka koma kofar gida sai suka fara tunanin ko dai su koma nasu gidan ne tunda nan gidan gaisuwa ne ga matan mutane a zazzaune. "Ku barni na ganshi kafin ku tafi. Allah bai kaddari haduwarsa da babansa ba ku bari na gane masa Zayyanu" cewar Gwaggo Ladi. Sallamar babban dan Mal. Aminu da kannensa maza dasu Badaru ita ta sanya matan kuka da ganin Zayyan da yake tsakiyarsu. Idonsa a kan Gwaggo Ladi tana dago masa hannu ya taho gareta. Girma ya kamata sosai tafiya tana wahalar da ita. A gabanta ya durkusa gidan ya koma tamkar yanzu akayi mutuwar. Daga inda Jume take bayan ta fito daga bandakin take jiyo koke koke. A tsaye suke ita da wata jikarta ta wurin 'yarta mace ta saka ta kiran Maikudi a waya. Kare masa tanadi tayi rai a bace har anyi uku bai zo ba. Yana gidan ma aka aiko da rasuwar yaki fita wai ciwon jiki yake yi. Ya riga ya sakawa ransa cewa Mal. Aminu makiyinsa ne bai ga dalilin zuwa jana'iza ko gaisuwa ba. Sai da ta gama fadan ta ajiye wayar ta tako itama din kafafun sai a hankali. Kamar ance ta kalli gaban Gwaggo Ladi sai ganin mutum tayi a durkushe gabanta 'yan uwansa sun kusa rufe shi. Gaba na faduwa da rawar murya tace "wa nake gani kar Mal. Muhammadu?" Kama yayi mata sosai da mijinta matar Rayyanu ta kamo hannunta a hankali ta zaunar a gefen Gwaggo Ladi. Zayyan ya matso yana murmushi da 'yar kwallarsa. "Jume Zayyanu ne ya dawo" Idanunta ta shafa harda gogewa da zaninta tayi murmushi mai ciwo "ko dai nima na mutu ne?" Sai ta sake tsinkewa jama'a zukata aka cigaba da kuka. "Jume ni din ne dai Zayyanu ba mutuwa nayi ba" "Nagode Allah da bakina zan rokeka gafara" tace tana wani irin kuka da take tuna bakar izayar da ta rinka gana masa tun kuruciya. Maikudi da ya gagareta har yanzu waye silar lalacewarsa idan ba ita ba. Basu barta ta cigaba da magana ba suka tattara duka iyalin gidan Marigayi Muhammadu Tureta suka tafi nasu gidan. Murna a wurin 'yan uwansa da 'ya'yansu da suka sanshi a matsayin baban su Radhiya ba kadan ba. "Me zan dafa maka Zayyanu? Ban yarda ka ci abincin kowa ba sai girkina. Kai ku hura min wutar icce ni ba son girkin risho nake ba" Zaunar da ita Zayyan yayi yana dariyar yadda ta tashi hankalinta "ki zauna nayi ta kallonki Jume" "Har me zaka kalla a jikin matar da taci zalinka ta kasa rike amanar maraya" Mairamu da kowa ma hawaye suke yi na tausayinsu. Ga su Badaru da suka san yadda rayuwar gidan nasu ta kasance tun da su ma sai rokonsa gafara suke yi. "Bana jindadin yadda kuke yi min. Jume ke uwa ce a gareni mai cikakken iko akan danta. Da dadi da babu dadi kinci kashina kinci fitsarina. Wahalar da nasha ta kuruciya ita ta samar da Zayyan din da yake gabanki mai hakuri da juriya" ya juya ga 'yan uwansa "idan kuna biye mata za ku tabbatar min da cewa ni din dan uba ne kawai baku daukeni kaninku ba" Kalamansa sunyiwa Jume dadi haka ma yayunsa. Tashi tayi da sauri tayi hanyar bangaren Maikudi. Yadda baije gidan gaisuwa ba haka ya hana matarsa da 'ya'ya suna zaune kowa rai a bace amma basu da yadda zasuyi dashi. Matarsa har tafi jindadin lokacin da aka tsareshi su ka sakata suka wataya son rai a gidan. Yana daga uwar dakinsa a kwance ya bararraje matarsa tana yi masa tausa. Daga bakin kofa take ta kwala masa kira ya taso a fusace. "Jume ya haka zaki zo min har kofar daki. Wannan ai rashin tunani ne, waye yake zuwa kofar dakin mai aure. Gaisuwa ce dai nace bazanje ba ko ana dole ne inji" "Ba wanan ya kawoni ba Maikudi kazo ga dan uwanka ya dawo" Da yana da kudi bai ga dalilin da zaisa shi zaman gidan nan ba. Ya tsani ya farka ya ga kowa cikinsu saboda babu mai kaunarsa. Haka ya karaci zamansa da shan wahala a rufe sai sun bushi iska suke lekawa. Zayyan da sauran suna jiyo yadda yake daga mata murya shiyasa ya tashi yabi bayanta. "Ko ma waye dan uwan bai san inda nake bane da bazai karaso ya gaisheni ba sai kin taso da kanki? Wato gani matsiyaci nine zan fito gaida irin mutanen da kuke yiwa maula ke da su Badaru....." Numfashinsa ne ya nemi daukewa a lokacin da Zayyan ya bullo tsakar gidansa inda ya tsare kofa ya hana Jume wucewa sai ma kukan bakinciki da take yi. Zayyan yana shigowa bai tsaya ko ina ba sai a gabansa ya cire hannu ya kwada masa mari. Bude baki yayi yana neman hada kalma ko daya ce ya fada Zayyan ya kara masa wani. Marinsa ya rinka yi hagu da dama kumatunsa ya dauki radadi kamar garwashin wuta a take. Idanunsa a rufe suke da takaicin halin Maikudi. Banda bakincikin da yake ji na muguntar da ya yiwa iyalinsa kuma shine ya kara masa da rashin da'ar da yake yiwa Jume. Mahaifiyar da duk abinda tayi a baya mai kyau ko akasinsa tayi ne domin farincikin 'ya'yanta. Shi fa babu abinda zai dorar game da uwa sai labari. Wane irin farinciki zaiyi da za'a bashi damar kasancewa da tasa uwar ko da na rana daya ne. Shi wanda ya sami damar yana takewa ta hanyar cusa mata bacin rai. Marin karshe da ya kai masa sai da bakinsa ya fashe. Mairama na ganin haka ta kama hannunsa "ya isa haka Sojana ban sanka da fushi ba, kamata mu koma dakinta" Rungumo Jume yayi a jikinsa suka bar wurin bayan wani mugun kallo da ya yiwa Maikudin. Sawu na daukewa Maikudi ya kwalla kara yana riko matarsa ta zaro idanu a tsorace kada ya huce a kanta "kin ga abinda na gani yanzu? Kema kin ga fatalwar Zayyan?" "Ni banga kowa ba" tace cikin halin ko in kula sai ma murnar marin da ya sha da take ganin rama mata akayi. Kansa yaji yayi nauyi yasa hannu ya shafi jinin bakinsa ya tabbatar fa gaske an mare shi din ya fito zuwa dakin Jume. A zaune ya ga Zayyan din yana bata baki akan tayi hakuri da abinda Maikudi yayi mata. Buguzum buguzum haka ya shiga dakin babu sallama ya sa hannu a kafadar Zayyan don ya tabbatar cewa mutum ne da gaske. Yadda idanun Zayyan din suka yi lokacin da ya dago kansa ya sa Maikudi yin baya da sauri jikinsa na bari. "Baka mutu ba?" "Ba haka kaso ba ko? Yadda ka tsara shine na mutu matata ta haifi da ba rai ita da 'yata suyi hatsari su mutu su ma kaci dukiyar da zata zame maka wuta ranar lahira" Da borin kunyarsa ya kalli Mairama "sannu munaf...." "MAIKUDI!!!" Zayyan ya daka masa tsawar da hatta Mairama sai da ta razana. Da dan allinsa ya nuna shi yana kada masa shi a gaban fuska "ko da wasa kada ka sake yunkurin yiwa matata magana balle kuma ka hadata da kalamai na batanci. Kai ba ita da Jume ba wani ma a gidan idan ya sake kuka da kai wallahi sai kayi mamakina. Abu na karshe daga yau har na bar gidannan kada ka bari ko inuwarka ce na sake ganin gilmawarta a gabana. Get out" "Ni da gidan ubana kai ka isa kayi min turanci. Ba tsoronka nake ji ba" yace daga bakin kofa yana sauri kada Zayyan din ya biyo shi. Babu wanda ya sake saka shi a lissafi. Jume duk yadda yaso hanata da kanta tayi masa tuwon alkama da miyar karkashi akan wutar murhu. Zaman hira kuwa an raba dare ne ana bashi labarin abubuwan da suka faru bayan tafiyarsa shima kuma ya fada musu nasa. ********** Numfarfashi kawai Malamijo yake saki yana daga kwance a dakinsa ko zama baya iyawa sai an tada shi. Ga mutane cikin 'ya'yansa da jikoki ana ta yi masa sannu. Sallamar Nene Marka tare da Radhiya su ka shigo dakin. Ba arziki ya tashi yana nuna Radhiya. Ba don kada a raina shi ba kuka zaiyi ko yaji sassauci a ransa "Wai da gaske so kike ki karasa ni ne? Dame kike so naji? Shanuna, shanuna shegen yaron nan Talle ya gudu dasu sannan kin kawo Marka wato tazo in biya musu kudin Hajji da yawun bakina ko" Murmushi Radhiya tayi har ranta tana tausayinsa tace "duba ka tazo yi...ku taso mu basu wuri ko" Tace da su Emzee. Murmushi yayi yayar tasa ta fara daukan haske ta gane inda ya kamata ta rinka tashi musamman idan manya ne zasuyi magana. Nene Marka ma ta kalli bayanta har ta saki labulen da suka gama fita tayi dan murmushi. Radhiya fa tana da hankali idan aka tabota ne kawai bata da dadi. Daure fuska tayi lokaci guda tana kallon yayanta. "Ali" tace da kaushin murya. "Alin ma kai tsaye Marka, wato tunda na soma talaucewa an sace min shanu ga kaji ance suna murar tsuntsaye shine dan girman da kike bani ya kau. Kada ki manta dai sunan Malam ne kakanmu ehe. Idan kin kirani Ali kamar kin kira sunan Malam ne babu kara" "Kaga dakata min ba wannan ya kawoni ba. Zumunci nazo yi zan duba ka nayi maka nasiha ta karshe don babu lallai na cigaba da hakurin zuwa gidanka" Jikinsa ne yayi sanyi kuma. Gidansu ita kadai ce mai hakurin zumunci dashi sauran har wadanda ya hada uwa dasu sai abu ya kure suke zuwa. Ita kuwa 'yan dakinsu har gori suke yi mata wai tasa kwadayin abin hannunsa a rai shiyasa take like masa. Gashi dai shine babba amma sai aci a cinye a gidajen sauran babu shi babu 'ya'yansa saboda kawai kada ace yayi gudunmawa. "Yanzu kuma me nayi?" "Meye ma baka yi ba? Dubi yadda ka koma sai mokadewa kake yi kamar ragowar yunwa. Ni dinnan da bana takama da komai sai dan rufin asirin da Allah Ya yiwa mijina, ba da ba jika na fika kyaun gani da cika ido" "Ku mata dama banda ci me kuka iya?" Gyara zama tayi bata sake magana ba har yarinyar da ta kawo mata ruwa ta fita sannan ta cigaba "Malamijo wallahi ka guji haduwarka da Allah akan yadda kake rayuwa" "To, tohhh zaki fara ko. Idan kina abu sai kace kin saki nono ne Hajjo ta kama. Kuyi ta zakulowa mutane laifuka kawai don a rubuta min zunubi to dai kowa mugun fatanta a kanta zai kare" Girgiza kai tayi cike da takaici "kaga irin halin naka...ni ka saurareni don banzo da shirin kwana ba." Sassauta murya tayi ta kafe shi da ido don yasan zancen nata babu wasa a ciki. "Malamijo ina tsammanin ko rantsuwa zanyi babu kaffara a kaina cewa duk garin nan babu mai arzikinka. Tunda Baffanmu ya raba mana shanu tun yana raye ba'a shekara biyu ba naka suka ninka abinda ya bamu. Ni ko wuka aka saka min a wuya bana ce ga abinda na tsinana da nawa ba. Amma kai kam ka sami albarkar kiwo. Nafi shekara arba'in a gidan miji ban taba batan wata ba sai gashi kai da kayi naka bayan ni yanzu a lissafina mutum talatin da daya ne naka masu rai banda biyar da suka rasu da masu bari" "Hakkun" ya gyada kai maganar ta soma samun shigarsa. "Wadannan 'ya'ya amanar Allah ne kuma kai dai kaci wannan amana. Ko kadan baka rikesu yadda musulunci ya tanada ba. Rashin wadatasu da abincin kirki ba shi yafi damuna ba kamar sakaci da zumuncinsu. Yawansu na banza ne saboda babu wanda ya damu da dan uwansa. Ka ga duk iskancin Salame....." "Kyale wannan mara mutumcin ko ni kaza ta fini mutumci a idanunta" "Kaga matsalar ai kayi ta aibatasu. Salame ko tana da mugun hali da sa hannunka a kara lalacewarta. Duk yadda duniya take wasan gare gare da ita a gidan miji bai sa tayi hankali ba har yau. Yadda ka banzatar dasu haka ta fita harkar Halifa da Rahima. Albarkacin kudin uban Halifa yanzu take jansa. Amma Rahima fa?" Langabe kai yayi "ko a waje muka hadu bazan shaidata ba wannan" "Shikenan so kake idan kasa ta rufe idanunka sun gama zumunci kenan sai a lahira idan an hadu a filin hisabi?" "Kai Markajo ni dai fadi me kike so nayi duk kinbi kin tsorata ni. Kina kallo ba lafiya gareni ba." "Ka hada kan zuri'arka. Kafin ka bar duniya ka dinke barakar dake tsakaninsu. Banda Mairama da Ayuba babu wanda yake nuna damuwarsa a kanka. Abu na biyu yau ka gani da kaki sharar masallaci ai kayi ta kasuwa. Wata can da bata da gadonka ta kwaso iyalinta suka tagayyara ka sai jikoki suka kwaceka. Da gidan nan a hade yake wadancan zaratan samain yaran naka ba ubanta zasu ci ba ta koma inda ta fito daren da ta tare. Wai ma shin auren bai isheka ba. Kayi lukuta, siririya, fara da baka, mai kyau da mummuna. Babu kalar da baka taba ajiyewa ba amma kaine har yau aure kake" Jikin Malamijo yayi mugun sanyi domin kuwa ya soma ganin ishara. Marka ce kadai ya tabbatar zata fada masa gaskiya batare da sanya son zuciya ba. Ko Radhiya sai da ta hado da cewa a kai wasu hajji sai kace zuwa Zaria ne abin. "Nagode Marka kuma sha Allahu kafin ki tafi zaki ga sauyi. Taron hadin kai zanyi a gidan nan Mairama tana dawowa daga Nijar" Sai yanzu tayi murmushi "ya dai kamata, ai Radhiya ta fada min dawowar baban nasu da alkawarin zasu zo min." Hirar zumunci suka yi sosai tana ta bashi shawarwari. Rokonta yayi ta taimaka taje masa bikon Hajjo kafin ya shawo kan Yadikko. "Wani hanzari ba gudu ba Malamijo" Nene Marka tace kafin ta tashi "ka kira Salame kayi mata jan ido irin na uba mahaifi wanda ya isa da gidansa . Ita ce fa babba a gidan nan" "Ina jin fa kanta ya kwance wannan. Jiya ta bani mamaki wai sai gata. Nayi zaton dubiya tazo yarinyar nan sai cewa tayi wai tayi magana da wani Malami suna tantamar ingancin auren Mairama da Zayyan. Wai yace mata shekara hudun farko da basa tare matsayin saki daya ne, ta biyi kuma saki biyu ta uku saki uku. A takaice dai wai na rabasu a barshi ya nemi wata itama ta sami daidai ita. Ni dai kaina daurewa yayi sosai nace Salame ko ta fara hauka ne" Nene Marka bata taba niyar fallasa maganar son da Salame take yiwa Zayyan ba amma jin wannan magana ranta in yayi dubu to ya baci. Da za ta ga Salame yanzu wallahi sai ta mareta. Nan take ta warwarewa Malamijo wannan batu da kuma kakkarfan zargin da take na cewa ita ta makanta kanwarta Mairama tsahon shekaru goma saboda ta auri Alh Indararo. A kidime ya tashi zaune sosai "Kin gane min 'yar jakar uba" "Shiyasa nace ka hade min kan yaran nan" Kan Emzee wata irin sarawa yayi da jin wannan mummunan labari. Kawunsa Ayuba ne yazo da abokansa malamai shine ya turo shi yi musu iso wurin Malamijo kafin ya gama yiwa tagwayen kannensa addu'a. Kai tsaye Emzee ya shiga dakin cikin bacin ran da bai taba yin makamancinsa ba. Jijiyoyin kansa sun tashi idanu sunyi ja. "Nene" yace da wani irin yanayi mai ciwo. Hankalinta da na Malamijo a tashe ta dafa shi "Zayyan don Allah ka bar maganar nan inda ka ji ta. Zancen makarantar kuma zargi ne kawai" "Tunda kika fadawa Malamijo nasan ya wuce zargi." Yace a fusace. "Kwantar da hankalinka Zayyanu. Ni dai na haifi Salame ina mai tabbatar maka babu wani iskancin da zata zo dashi da ban ga wanda ya fishi ba. Zan bi diddgin maganar da kaina. Kai dai ka rufa min asiri kada yayarka taji zancen nan mu duka mu shiga uku. Ka fita hakuri da nutsuwa ka bari muyi komai cikin lumana" Malamijo ya sami kansa da lallaba Emzee. Ficewa kawai yayi daga dakin a hanya yaci karo da Halifa. Wani mummunan kallo ya maka masa Nene tana biye dashi tace da Halifan allurar soja ce ta motsa saboda Malamijo yayi masa fada. Da yake ba bakon zafi bane sai ya yarda harda tausayawa Emzee din. Dakin da suka kwana ya shiga ya rinka naushin bango ko zai ragewa kansa fushi. Da ya bar maganar a cikinsa gara ace bai ji ba. Kai dama ace Radhiya ce taji ta gwadawa Salame me ake nufi da uwa. Wai saboda wani can Alh Indararo shine ta makanta musu uwa. Kuma karin abin haushi wai Daada dinsu take so. "Wallahi sai dai ki mutu amma yafi karfinki" "Kai da wa?" Yaji Ibrahim yace daga bayansa. Kasa amsawa yayi sai kwanciya da yayi yana ta juya zancen. Abin ya dame shi matuka ya dena walwala ya matsawa Ibrahim suka tafi Kano gidan kakaninsa. Halifa da Hibbah su ma zasu tafi amma kememe Emzee yaki yarda su hada tafiyar saboda baya ko son ganin Halifa. Washegarin tafiyar tasu yaje yace da Malamijo ya basu kudin mota. Dubu goma ya bashi duk da yasan kudin yayi yawa amma gara ya tafi ko hankalinsa ya kwanta. Kullum da zulumin kada Radhiya ta gane yake kwana. Ta shiga damuwa sosai akan yadda kanin nata ya koma sai matsawa Malamijo take yi akan ya tambaye shi ko ta sanar da iyayensu. ********** Kwanan su Zayyan uku a Sakkwato sai birnin Agadez a kasar Nijar. Da kwatance suka isa unguwar inda gidan Alh Ghoumar da Alh Sidi suke makotaka da juna. Mammee suna Niamey da mijinta tunda dan siyasa ne. Kowa yayi mamakin zuwan Mairama ita kadai tace banda yaran ta tahi lokacin da ta kira kwaya domin a kwatanta musu hanya. Tante Nasara sai da ta kira Radhiya da Emzee taji muryoyinsu ta tabbatar kowa lafiya kafin isowarsu gidan. Murnarsu kuwa bayan sun ga Zayyan bazata misaltu ba. Masu kuka na yi masu suma suna yi. Dangin Innar Zayyan sun sake nuna bajintarsu da kwarewa wurin rikon zumunci da murnar dawowarshi. Mammee tayi kuka tayi fadan me yasa basu sanar da ita ba sai da suka iso gashi kowa ya rigata ganinsa. Kwanansu biyar 'yan uwa suna faman kokarin kyautata masa da nuna masa cewa shi din dan dangi ne. Tamkar kada ya baro kasar sai dai dole ya koma saboda litinin zaiyi reporting a headquarter ana nemansa. [11/2, 7:24 AM]🏽 ]🏽 : ***********50💕 Tsattsaye suke maza da mata a kofar dakin a aibitin likitoci suna ciki suna aikin kokarin ceto rayuwar yarinyar da ke ciki. Daga can gefe Hussaina ce take kuka wiwi jikinta duk jini tana sambatun kada autarta ta mutu. Duk cikin yaranta kowa ya shaidi yadda take masifar son auta Hany. Yarinya ce kyakkyawa mai mugun shiga rai. Bata da hayaniya ga kokari a makaranta. Hussaina duk inda ake hirar yara tamkar sauran shidan babu su zancen bai wuce Hany tayi kaza ko Hany tace kaza. "Kiyi shiru mana Hussaina mu samu su fito aji halin da take ciki" Ummansu tayi mata tsawa. Alh Baba da akayi komai a kan idonsa ya biyo su asibitin shima hakuri yake bawa Hussainar hankalinsa a mugun tashe. Saboda soyayya yarinya ta sanya reza ta tsinke jijiyoyin hannunta wai gara ta mutu da a rabata da wanda take so. Wannan wane irin zamani ne rikirkitacce haka. Lokaci ya shude kafin likitan ya fito yace anyi nasarar tsayar da jinin amma fa wanda ta zubar da yawa ana bukatar a kara mata ko leda daya ne zuwa biyu. Hannu na rawa Hussaina ta kira Nura. Blood group dinsa daya da Hany tace maza maza yazo a debi jininsa. "Kawai ki nemi wani" taji ya bata amsa ga alama ma cikin maye yake don a datse maganar ke fita. "Nura ni kake fadawa haka? Kanwarka fa nace" "Tare fa aka gwadamu kuma kema irin naki ne ki bata mana" ya kashe wayarsa ya fada gado rigijib. Kwance a kasa Ghazalatu ce rike da cikinta bayan yayi mata mugun duka. Da rarrafe ta soma tafiya domin ta bar dakin sai ta gano ashe jini ne yake naso a duk inda ta bi ga azababben ciwon ciki ya murdeta. Lallabawa tayi zuwa dakinta ta kira Mummy Gambo ta fashe mata da kuka. "Sai da nace bazan dawo ba Mummy gashi nan zai kasheni" Hannu ta kai ta tabo Daddy Haroun ta saka wayar a speaker hankalinta a tashe saboda yadda take jin muryar Ghazalatun. "Me ya sameki?" "Mummy dukana yayi ga jini yana bin kafata kuma cikina...cikina..." Kashe wayar tayi da sauri ta kira Hussaina wadda take kwance ana diban nata jinin. A zatonta Nura ne shiyasa ta matsawa Ummansu ta bata wayar sai dai tana karawa a kunne ta jiyo masifar Gambo hatta Umman tana ji. "Hussaina ki rubuta ki ajiye sai nasa an daure Nura in ga uban me kuke takama dashi. Yarinyata ba jaka bace da zai rinka dora mata hannu duk lokacin da ta raya masa. Dama kuma na fadawa Alh Baba idan ya kuma dukanta ya daki aurensa" Muryarta ta zama weak sosai tace "Gambo muna asibiti da Hany ki bari..." "Bazan bar komai ba. Ki tura a dauko min yarinya a kaita asibiti tace jini yana bin kafarta" Yunkurin tashi tayi Umma tace ta kwanta ta fita ta sanar da Alh Baba wanda ya hana a fadawa mijin Hussaina da Baban biyu komai sai yadda ta kaya. Dan tsohon sai ya kara shiga firgici ba yadda ya iya haka ya kira Baban Biyu ya sanar dashi. Yana gida a zatonsa Umma tana gidan Alh Baban ne ashe kuma suna asibiti. Kanin su Mami ya nema Allah Yasa ya dawo gida dayake bashi da nisa daga gidan iyayen nasa yazo suka fara tafiya gidan Nura. Bugun duniya Kawu Mas'ud yayi a dan karamin gate din gidan ba'a bude ba. Ya shiga kiran Ghazalatu tana can bata san inda kanta yake ba sai da Baban Biyu yace ya zai kira wasu cikin 'yan uwa su taru a balle kofar sai ga Nura cikin maye ya bude gate din. "Wane dan...." Naushi yaji ya sauka a bakinsa da hanci zaiyi magana hasken fitilu ya nuna masa fuskar kakansa da kuma kanin babarsa wanda ya sauke masa naushin kafin ya bangaje shi ya shiga ciki. Kofa biyu ya bude yana leke ya sami dakin da Ghazalatu take kwance a kasa. Da sauri ya ciccibota don ma wahala ta sake zugeta bata da nauyi ya fito ya sakata a bayan mota. Nura yana tsaye ya yi ribas suka bar wurin bai iya motsi ba. Asibitin da aka kwantar da Hany suka kaita tunda nan Alh Baba yace su samesu. Ana zuwa Ghazalatu tayi bari na 'yan biyu. Umma kuka ta zauna tana yi sosai kamar yadda Hussaina duniya tayi mata zafi. "Kinji dadi Hussaina, ga ribar shiga tsakanin Gambo da Hassana kin gani zahiri ko. Itama Gambon da shegiyar kafiya da kin jin magana zata zo ta ga nata sakamakon na dora son zuciya akan komai." "Umma kada kice haka" Hussaina tace a raunane. "Matsa min ni na wuce" Umma ta fita tana share hawaye. A wajen inda motar Kawu Mas'ud take ta sami Alh Baba da Baban Biyu. Ranta yana kuna yau ta manta da surukuta da girman Alh Baba ta soma magana. "Kun tuna lokacin da Awwab da iyayensa suke rokon a barshi ya auri Ghazalatu da daya yarinyar abokin Mustapha ko? Ku ka kekashe kasa kuka nuna naku, naku ne dan kowa bai isa ba. To yau gashi Hannatu tana son yaron da iyayensa sun rantse sai dai ya auri 'yar uwarsa kuma su danginsu basu zama da kishiya" "Fatima!" Baban Biyu ya daga murya da niyar yi mata fada. Kukanta ne ya tsananta tace "Ko me zaka ce sai dai ka jira na gama fadin nawa. Saboda wannan akidar ta auren dangi da ba farilla ba kun raba min kan 'ya'yana. Dukansu yanzu daga masu goyon bayan Hassana sai 'yan bayan Gambo. Hussaina kam dama ita ta sayawa kanta koma me ya sami nata yaran saboda kofar da kuka bude musu tun farko. Ni dai baku yi min adalci ba wallahi". Bayan motar ta bude ta shige "kaini gida Mas'ud" ta umarci dan nata. Alh Baba da Baban Biyu aka rasa me cewa komai. Yanzu yake bawa kaninsa labarin abinda ya kaisu da zuwa asibiti. Hussaina ta damu da halin da Hany ta shiga saboda dangin saurayin nata sunki yarda ayi auren shine ta tsefe ido ta tafi gidan Alh Baba tana rokon ya sanya baki tunda kakan yaron abokinsa ne. Fadan da ya soma yi mata ne akan soyayyar ya sake jagula komai ta fita ta yanka hannunta. A take Hussaina ta kira mahaifiyarta tana kuka shine ta taho gidan suka wuce asibitin tare. "Yanzu ita Hussaina ba kwari gareta ba ga jinyar mutum biyu. Na rasa yadda zanyi da rigimar nan. Nura bashi da hankali dole muyi wani abu" "Ko baka ce ba wannan wajibi ne. Tunda Fatima ta ajiye kawaicin tayi magana kasan an kure hakurinta." Umma na zuwa gida ta kira Mami ta fada mata abinda ke faruwa tana kuka. Hankalin Mami a tashe ta sanar da Daddy. Suna haka Daddy Haroun ya kira shi wai Gambo babu lafiya jininta ya hau suna asibiti. Mami ta leka daki wurin Fauziyya, ita kadai ta rage a gidan ta fada mata zasu fita zuwa asibiti. Daren ranar basuyi kwanan kwanciyar hankali ba. Mummy Gambo ta tayar da hankalinta saboda bata san halin da Ghazalatu take ciki ba. Can kuma Hussaina da daya daga cikin 'ya'yan Alh Baba mata ne zasu kwana da Hany da Ghazalatu. Garin Allah na wayewa sai haramar tafiya Katsina. Mami bazata bisu ba saboda Fauziyya dake fama da laulayi ga yaro sannan mijinta baya gari. Daddy ne yayi musu kara suka tafi tare. Al'amura dai basuyi dadi ba haduwar Hussaina da Gambo tamkar ba ciki daya suka fito ba. Sai da Umma tayi kuka sannan kowacce ta shiga hankalinta. 'Ya'yan dai da suke yi dominsu sune yau suka hadasu fada. Umma kuwa tace hakkin Hassana ne ya kamasu. Shekara uku sun dauki gaba ta babu gaira babu dalili akan abinda idan kowa ya ajiye son zuciya zasu daidaita shi cikin lumana. Gabadayansu sun fahimci kuskuren abinda suka yiwa Mami akan auren Awwab tunda kowacce ta gani a kwaryarta. Ita Hussaina yanzu 'yarta ce a matsayin Radhiya na da kuma dangin mijin masu bala'in kudi ne saboda haka ana yi musu kallon masu kwadayi. Mummy Gambo da take ganin 'yarta tafi karfin zama da kishiya ta kare a gidan mashayi mai duka. Banda bari sai tayi jinyar jikinta da ya doku. Daddy Haroun ma dai cewa yayi a raba auren saboda ko waya Nura baiyi ba bare yazo dubiya. Bayan dogon zama da mayar da maganganu Alh Baba yace da mijin Hussaina ya umarci dansa da sauwakewa Ghazalatu kafin sauran zumuncin iyayensu ya karasa lalacewa. Sai dai Nura ya kafe bazai saketa ba. Hakuri yayi ta badawa akan cewa yana sonta kuma bazai kuma shan kayan maye ba. Mummy Gambo ta tafi da ita Abuja suna jira idan ya gama haukan a cewarsu zai kawo takardar. *********** Rugar Barkindo da Gaya wurin Nene da su Ummi ke da niyar zuwa sai waya suka yi musu suna bada hakuri da zarar ya gama da wurin aiki zasu zo. Innawuro tace babu komai dama yanzu ai zama bai ganshi ba. Radhiya suka tsaya dauka kawai Emzee da Ibrahim aka ce su biyo motar haya saboda motar tayi musu kadan. Kafin su tafi Malamijo yace da Ummi idan ta sami sarari ta dawo zasu yi taro na 'yan uwa. Abin yayi mata dadi kuwa sosai yadda baban nata ya sauya. Hajjo ce dai take wahalar dashi yanzu taki yarda ta koma sai yawon ban hakuri yake yi. Gidan kajinsa ko ashirin ba'a samu ba duka sun mace da cutar murar tsuntsaye. Ayuba ne ya kwantar masa da hankali akan cewa yaci sa'a ba shi kanshi aka dauke ba saboda kin fitar da hakkin Allah na zakka. Duk lokacin da yayi masa magana a shekarun baya Malamijo sai yasa a kamo kaji uku ko biyu yace ayi miya zakka ce ya fitar. *********** Abin farinciki da murna ashe kiran da aka yiwa Zayyan kira ne na alkhairi. An tabbatar masa da sabon mukaminsa na Major General sannan kuma gwamnatin tarayya tare da hadin gwiwar Nigerian Army su ka yi masa kyaututtuka na bajinta. Da farko dai an bashi dankareren gida a unguwar Maitama nan cikin Abuja da masu gadi kananan sojoji. Gida na gani na fada ginin zamani wanda bai taba tsammanin akwai irinsa ba bare ace zai mallake shi. Sai kuma motoci guda uku banda daya da take mazaunin official car tare da drebansa. Basu tsaya a nan ba aka hada masa da cheque wanda ganinsa ya sanya shi fitar da hawaye a matsayin compensation. Ina zai kai wannan kudin yake ta tunani. Ranar shi da iyalinsa sun ga soyayya daga wurin 'yan uwa da abokan arziki. Daddy da Baba Hadir sunfi kowa murna babu kyashi babu hassada. Zayyan ya cancanci fiye da wannan ma. Taron karramawa kamar yadda aka yi masa bayani tun farko za'a yishi ne daya ga watan junairun sabuwar shekara abinda bai kai watanni biyu ba. Shi kuma nasa taron da kudurin da yake dashi na wannan ranar sai washegari biyu ga wata. A cikin satin su Ummi suka yi parking din dan abinda ba'a rasa ba domin sabon gidan babu abinda babu cikin manyan kayan bukata na gida. Abinda baiyi musu ba ko babu sai su canja. Ranar Juma'a suka tashi Ummi tayi kuka tamkar bazata sake ganin Mami da Mama ba. Suna yi tana yi mazansu na bada hakuri. "Meye abin kuka bayan ko minti ashirin bana jin zakuyi a hanya kafin ku ga juna" cewar Daddy. Mami tace "Mun saba fa tafiyar kafa ce kullum muna tare" "To ai sai kuyi hakuri kowa ta koyi zaman kula da mijinta ku dena yawo" Ummi da Mama kunya ta kamasu saboda shi ba mai yawan surutu bane. A haka dai suka tare Baba Hadir ya baiwa Zayyan shawarar cewa ana iya yiwa Ummi tranafer ta karasa karatunta a Nile ko Baze University da suke a nan tunda babu amfanin ace tana karatu a Kano shi yana Abuja. "Ko zaka kara aure ne?" Ya tsokane shi. "Yi hakuri kada taji yau ta hanani tuwon dare" "Kafin a koma hutu sai mu nemi bayanin yadda ake yin transfer din" Littafin da ya rubuta masa Zayyan ya kalla ya dan bata rai "wai da gaske haka zamu rinka hira Hadir bazaka kokarta kana magana ba?" "Wwwahhalla" Baba Hadir ya bashi amsa. "Duk da haka ka daure don Allah. Idan ba bude baki kayi muna zantawa ba gani zan rinka yi kamar ban hadu da Hadir ba har yau" Alkawari yayi masa cewa zai cigaba da kokari. Cikin motocin da aka bawa Zayyan wadda tafi kyan ya bawa Ummi aka hadata da dreba. Daya kuma ya bawa Ibrahim mukullin "kai da dan uwanka. Nasan ba gari daya kuke karatu ba saboda haka tana nan sai kunzo hutu babu mai tafiya da mota makaranta" A hakan ma sun gode matuka iyayensu suka tayasu murna. Da yake gidan bene ne babba akwai dakuna shiyasa guda biyu da suke kusa da juna a kasa aka bawa Ibrahim din daya Emzee daya. Radhiya tana murnar zata gyara daya a sama Ummi tace kada ma ta batawa kanta lokaci aurar da ita zasuyi daki na Zayyana ne. Mama ta bata rai "ya haka ne kun kwashe yaran duka?" "Wadda taji haushi ta sake haihuwa" Ummi tace tana satar kallon Mami. "Cigaba da yi min fata kizo ku haihu rana daya da Radhiya muga tsiya" Ai gaban Ummi sai da ya fadi tana ta cewa ba amin ba Mama da Mami suna dariya wai sun ga honeymoon din kamar bazai kare bane sai ta sauka. Kunya sosai taji kuwa ta ja bakinta ta tsuke. Duk wani shiri da ya kamata ayi domin fara aikin da ya dawo da Radhiya Baban Arifah ne kan gaba. Abinda take shirin yi ya kayatar dashi matuka inda ya dauko mata hayar kwararren cameraman aka hadata dashi. Arifah kuma ta zabi zuwa a matsayin wadda zata yi co-ordinating komai saboda ya tafi bisa tsari tamkar shirin film ba kara zube ba. Da connection din Excellency ya samu aka nemo masa wasu cikin makotansu Zayyan wadanda mazansu suka rasu a Liberia dasu zata fara. Yau litinin suka gama shiri zasu tafi Kwara state can karamar hukuma Moro. Suna airport kafin jirgin ya sauka Radhiya ta matsa gefe suna hira da Awwab. Rigima take yi masa tun jiya wai ya dawo. "Schatzi saura kadan fa na gama. Ko baccin kirki bana yi saboda saurin da nake yi na dawo wurinki." "Ya za ka dena bacci sosai salon kaje kayi mistake a kara maka kwanaki ko" "Ya Allah, yanzu yaya kike so ayi?" "Ka rinka bacci, cin abinci akan lokaci da tunanin ina nan ina kuka saboda ba ka nan" Tamkar yasa hannu ya daukota ta cikin wayar haka yake ji "Do you miss me that much?" "Every second Hammana" ta amsa masa da murmushi. "Ki kula min da kanki okay, banda kula likitoci kuma." Dariya tayi mai sauti yana jinta har ransa "yanzu ko asibiti idan ba dole ba ai bazani ba saboda ta kare min" Shima dariyar ta bashi. Yana so yaji tace ta kare mata dinnan cikin shagwaba "I love you Alheran" Kalmar da har yau take yi mata wuyar maida masa a kunnensa kenan. Nauyi take ji sosai sai dai ta kare da me too. Tun yana korafi har ya hakura. "Chèri ka turo min hotonka amma yanzu zaka dauka please kafin mu tashi" "Ba yadda na iya dake" yace sannan ya katse kiran. Shi ba ma'abocin daukar kansa a hoto bane sai dole yanzu ma abokin aikinsa ya bawa ya dauke shi ya tura mata. Bayan kamar minti biyar ta turo masa wani. Daukar kanta tayi tayi kyau sosai dimple dinnan ya fito ta hada da nasa a photo college wani frame mai kyau. Akan hotonsa ta rubuta Alheran Schatzi a nata kuma Awwab Chèri. Sun tafi zasuyi boarding ta sake kiransa. "Ka saka shi wallpaper dinka. Idan ka dawo zan duba. Yanzu zamu shiga kayi mana addu'a. Yaya Arifah tana gaisheka" "Whoa, ki dan tsaya mana in amsa kowanne kafi ki cigaba" "To ai yanzu zamu tashi" "Allah Ya tsare Yasa kiyi ki gama a sa'a kuma Ya sa mana albarka a ciki. Ki gaishe da Arifah" "Amin" tayi ta cewa har aka bada umarnin a kashe waya tana masa hira sannan ta kashe. Arifah ta kalleta tana murmushi "ba fa zaki rigani aure ba duk wannan lovey dovey din naku sai na riga" "Nima zan fi so babban yayan nawa kada yazo bikina yana gwauro" Dariya suka yi tare kafin su dora hirar Yousuf da Awwab. Magana dai tsakaninsa da Arifah ta kankama don yace ta fada a gida zai zo wurinta amma da maganar aure so gara a sani tun wuri. Tante ma sai da ta kira Radhiya ta dan yi mata tambayoyi game da Arifan sun gamsu ana jiran komawarsa Nigeria su karasa daidaitawa. Jirgi na sauka da suka fito motoci biyu na jiransu daga gidan gwamnatin Kwara. Gwamnan mutumin Baban Arifah ne kuma ya fada masa dalilin zuwan nasu. A cikin gidansa aka tanadar musu masauki. Bayan sunyi wanka sunci abinci aka kaisu suka gaishe shi sannan suka kama hanyar Moro inda Radhiya zata yi hira da Maman Dolapo matar da ta fara yi mata wanka ranar da aka haifeta. 💕******51**💕 Ummi da Emzee suna magana akan tafiyar Radhiya Daada ya shigo falon yake fada musu wayar da yayi da Alh Salisu yanzu. Kamar wasa ya ce Halifa ya bashi labarin program din nata shi kuma cikin hira ya fadawa matarsa. Shine take cewa abin zaifi kyau idan suka sami wanda zaiyi directing daukar komai. A yadda tace masa ya kamata aikin yayi kyau a haka ne zai burge masu kallo kuma a sami damar isar da sakon yadda ya dace. "Yanzu yaya kake ganin zamuyi gashi tace suna hanyar garinsu Maman Dolapo" Ummi tace bayan ta nuna gamsuwarta akan shawarar da matar Alh Salisu ta bayar. "Kya tambayi kaza hanyar rafi Fillo. Ni ba don ma kada nayi karya ba da nace muku meye hadin director da daukar video. Naga su Directors ma'aikatan office ne" Emzee da ya kwana biyu baya fara'a sai gashi yana dariya "Daada kamar masu harkar film din Hausa yake nufi" "Ina na sansu, ni dai so nake aikin nata yayi fice yadda take so ace 'yar Zayyan ce nima ina so ince nine baban Alheran. Tunda an bata kudin aikin su ma zasu so ganin abu mai kyau. Zan kirata yanzu su koma kai kuma na baka daga yau zuwa gobe ka nemo min wanda zai yi mana directing din" "Yes Sir" Emzee ya tashi ya kame tare da sarawa mahaifinsa ya fita. Gidan Mama yaje wurin Ibrahim ashe Ibrahim din fushi yake yi dashi bai ma sani ba. "Ka huce daga kumburin da ka ke yi ne kazo nema na?" Shiru Emzee yayi kafin ya dan shafa keyarsa "kayi hakuri mana Ibrahim. Tun a Kano nace maka babu komai" "Ai shikenan fita zanyi ni ka gaida gida Mama na ciki. Idan kuma kwana zaka yi sai na dawo" sa kai Ibrahim yayi zai fita fuskarsa a daure. Ba haka Emzee yaso ba. Tun daga Sumaila yake cikin kuncin maganar da yaji daga bakin Nene Marka shine har suka gama kwanakinsu a Kano baya sakin fuska. Sai da ta kai Ibrahim ya fara zargin ko Kanon ne baya son zuwa a dole ya shiga kirkirar murmushi. Dayake da wuya ransa ya baci shiyasa wannan karon ya kasa mallakar kansa. Makantar shekara goma da Umminsa tayi bazai taba mantawa ba. "Surbajo tsaya don Allah" ya kamo Ibrahim kagin ya fita daga dakin. Shi kuma ya sake hade rai "gidan nawa kakannin ne baka son zuwa shine...." "Haba kai kuwa wallahi ba haka bane" Emzee yace hankali a tashe baya son ya batawa dan uwansa. "To yane?" Hannunsa yaja ya zaunar dashi a gefensa "Zauna mana". Da gaske Ibrahim baiji dadi ba shiyasa ma ya wayance ya baro gidan bayan an gama murnar tashin nasu. Shine abokin Emzee na farko wanda har yau bashi da kamarsa. Abokan sirrin juna ne wadanda suke kokarin koyi da iyayensu. Duba da wannan da kuma gudun wancan zargi da ya darsu a zuciyar Ibrahim din ya sa Emzee fada masa abinda yaji. Baki Ibrahim ya rike yana mamakin wannan labari "tab, inama dai Radhiya ce taji wallahi da anyita ta kare. Yanzu kai bazan so ka soma fadawa su Ummi ba rigima ce kawai za'ayi gashi Nene tace bata tabbatar ba" "Amma da gaske fa wai Daada take so yana auren kanwarta." Tsaki yayi ransa yana kara baci "seriously man abin nan ya dameni fa" "Ai dole amma zancen gaskiya shawarar da zan baka kada ka bari yayi affecting alakarka da Halifa. Ni sai yanzu na gane yadda ka rinka shareshi kafin mu bar Sumaila" "Kuma kasan Allah bana jin dadin yadda nake masa. Kawai ji nake idan ina kula shi naci amanar su Ummi" "Tunda Malamijo yace zaiyi bincike ka bari yayi. Shine fa babansu nasan ko don abinda ya faru da majalisar dinkin duniya ta mayu bazai bari irin haka na faruwa a gidansa ba" Dariya sosai Emzee ya rinka yi suka mayar da hirar kan shirun da gidan yake yi saboda rashin Radhiya. Kofar dakin suka ji an kwankwasa sai muryar Zayyana tana tambayar ko Emzee ne a ciki. Tare suka fito da Ibrahim suka zauna tana tsaye da Daada karami a hannu Emzee ya karbe shi. "Zan wuce dakin Mama naji kamar muryarka Ya Emzee. Yaushe kazo?" "Ban dade ba ko Mama bata san ina gidan ba. Ya su Mami...zan ma dai shigo ai" Shi kadai take kallo ta dauke ido daga saitin Ibrahim tace "DK na kawowa Mama ya tashi daga bacci bari na mika shi na koma girki nake yi" "DK kuma?" Ibrahim yayi saurin cafewa "ta dage a rinka kiransa DK wai Daada Karami saboda a bambanta shi da Daada. Sai nake ga hakan yafi ko?" Tabe baki tayi ta wani juya idanu irin na 'yan mata masu tasawa suna jin kansu ta murguda baki "uhumm Ya Emzee sai ka shigo kaji akwai story" wucewa tayi ta kai DK wurin Mama tazo ta sake cewa Emzee sai ya shigo sannan ta fita. Rufe kofarta yayi daidai da dariyar Emzee harda rike ciki. Ibrahim ya bata rai kuwa "me kake yiwa dariya?" "Babu komai wani labari na tuna" yana kokarin danne dariyarsa saboda yadda damuwa ta mamaye fuskar Ibrahim sosai. Kamar mai shirin kuka yace "Kaga ka dena dariyar nan muyi magana sosai. Ka lura da abinda Zayyana tayi min ko? I can't remember the last time da tayi min magana ko ta amsa min." Wata muguwar dariyar Emzee ya kuma yi sai da Mama ta fito. Gaisuwar ma da kyar yake mata yana kallon Ibrahim dariya na cinsa. "Sojoji fa baku da kirki idan kunso mugunta. Yanzu wannan dariyar ta mene?" Mama ta tambayeshi don tasan ba abu bane da ya saba. "Mama ki sa mana albarka kawai" Kai ta girgiza ta koma ciki kawai. Ibrahim kuwa tashi yayi zai bar wurin Emzee ya riko shi. "Dawo mana muyi magana dan uwa" "Kana wannan dariyar kamar sabon kamu" "Ba dole inyi ba ina kallon fadan masoya" Duka hannu bibbiyu Ibrahim yake kai masa "ni da Zayyana? Amma ka cuceni ma. Kai baka ga yadda take murguda min baki bane?" "Ibrahim wai kana nufin baka san kana son Zayyana ba?" Ita ce tambayar da Emzee yayi masa da ta shige shi ba zato ba tsammani. "Matsalarka kenan ko yaya ka sami chance sai zancen soyayya. To ni dai kada kaje kayi min sharri bance ba" "Naga ka damu ne saboda ta dena kula ka. Kana magana kamar kayi kuka duk dan tale bakin nan kaima sai da kayi min yanzu" Ya fuskanci kamar tsokanarsa Emzee yake yi kawai ya tashi "meye laifina don na damu? Kanwata ce fa. Ko gaba kake so muyi bayan kasan matsayin masu gaba a addini" Haba Emzee ya rike shima yana tashi "da gaskiyarka kuma fa. Bari naje dai naji nasan story din nata baya wuce tayi sabon saurayi. Zanyi mata fada kuma akan wannan halin da ta tsiri yi maka" Duka zancen dena shigar Ibrahim yayi daga lokacin da Emzee yace labarin saurayi zata bashi. Ransa har ya soma baci. "Yanzu hirar samari kake yi da karamar yarinya Emzee, gaskiya bai dace ba. Muje idan kai bazaka iya yi mata nasiha ta dena kula samari ba ni zan iya." "Ta dena kula kowa sai kai ba" Emzee yace a hankali yadda bazai ji ba. Bangaren Mami suka je. Jawad yana ta wasansa a falo shi kadai sai motsin Zayyana a kitchen. Saboda tana tsammanin shigowarsu tunda ta dawo daga kai DK bata cire hijabin jikinta ba dan madaidaici iya kugu saboda saukin aiki da kare jikinta. Wannan tarbiyar Mami ce kaf dinsu har Radhiya ta koya musu zama da mayafi ko hijabi a kusa saboda samarin dake gidajen uku. Idan daya muharraminki ne to fa sauran biyun ba haka bane. Yana daga cikin kuskurenmu a fake da 'yan uwantakar da aure zai iya shiga tsakani 'yan mata suyi ta saka kaya su matse jiki iyaye na kiran wanta ne ko kanwarsa. Bayan zamanin yanzu ko muharraman ba kowace shiga ce ake iya bayyana a gabansu da ita ba saboda yadda shaidan yayi tasiri a kwakwalenmu. Lekowa tayi ta amsa sallamarsu sannan tace tana zuwa. Kwashe abincin ta yi ta fito tana sanar dasu yanzu Mami da Fauziyya suka tafi asibiti. Jikin Fauziyya babu dadi tayi ta amai tun safe ko tashi bata iyawa. Da dukkan gaskiyarsa Ibrahim yace "Wane irin ciwo ne yake damunta haka kullum sai ace bata da lafiya" don duk laulayin da ake cewa tana yi yayi zaton ana nufin ita mutum ce mai yawan rashin lafiya. Zayyana sai ta sake biris dashi ta tambayi Emzee ko zai ci abinci yace ya koshi labari yazo ji. Shagwabe fuska tayi Ibrahim yaji wani azababben bacin rai da bai san dalilinsa ko daga ina yake ba ya dirar masa a zuciya. A gaban Emzee take wannan kwabe fuskar...to me take so yayi mata? Maganarta ya tsinkayo tana cewa "Hibbah ta takura min Ya Emzee wai zata fadawa Alhajinsu ya hadamu a kaimu Dubai karatu. Ita bata ma gama ba amma take nacin kada na karbi admission din Baze. Yanzu idan taje ta fada akayiwa Daddy magana fada zaiyi min nasan" ta kare maganar muryarta na rauni. "Ki fada mata ba kya so kawai na kula tana da rawar kai." Emzee yace bayan gajeren tunani. "Na fada fa har kusan fada muka yi taki yarda. Jiya da mukayi magana da Ya Halifa..." A fusace Ibrahim ya harareta bai ma san yana daga murya ba yace "Halifa kuma? Me ya hadaki waya da Halifa?" Idanunta ne suka yi kwal-kwal za tayi kuka ta kara narkewa za ta kai kararsa wurin Emzee. "Ya Emzee ka ...." "Emzee pls bamu wuri yarinyar nan is trying my patience" Ibrahim yace yana hade girar sama da kasa. "Anzo wurin" Emzee yace da shakiyanci ya dauki Jawad yayi waje abinsa. Tsilli Zayyana tayi da idanu a tsorace saboda babu alamun wasa ko kadan a fuskar Ibrahim. "Zayyana" ya kira sunanta rai a bace. Wai har waya take da Halifa shi yana zaune hoto. A hankali ta dago idanunta suka sauka acikin nasa. Nasa sun kankance da kishi ita kuma nata sai girma da suka kara cike da hawaye. Fuskarta so cute bakin nan ta gama shirin kyabe masa shi da yayi mata magana mara dadi ta saki kuka. Kamar wanda aka sokawa kibiya haka idanun Zayyana da fuskarta suka shiga zuciyar Ibrahim. Abin da bai yarda shi yake ji ba game da ita ya yunkuro masa gabaki daya. Fadan da ya so yi mata ya makale a makoshi sai samun kansa yayi da narke fuska irin nata. "You look beautiful" yace da taushin murya idanunsa a kanta. Tsigar jikinta ce taji ta tashi ba shiri ta tashi a guje za ta bar falon ya sake cewa. "Zayyana me yasa kika dena yi min magana?" "Ba kaine ba" tace fuskar nan a shagwabe. Da sauri yace "Na dena" "Me din?" "Ko ma meye please kada ki sake yi min irin haka" Murmushi tayi da ya sake tafiya da sauran kuzarin Ibrahim ta shige daki ta barshi yana ta sakin murmushi shi kadai. Da dan gudu ya koma gida ya sami Mama da Emzee suna hira. Wani tsalle ya daka ya mikawa Emzee hannu suka tafa. "An kashe boss kenan" Emzee yace yana dariya. Kafadarsa Ibrahim ya daka yana nuna masa Mama. Girgiza kai tayi abinta tana murmushi tasan ko ma meye da kansa zai dawo ya fada mata don baya iya boye mata komai. Ba don kada tayi azarbabi ba ma sai tace yayi mata kama da sabon shigar soyayya. Da kyar Ibrahim ya nutsu suka yi maganar daraktan da ya dace su nema. An sha buge bugen waya da abokan Ibrahim na Kano kafin Allah Yasa suka sami nambar wani Nafi'u Bigman. Shi Bigman ba'a ma gama sanin sunansa cikin daraktocin ba amma akwai kokari da himma duk da bako ne a harkar. Rashin suna da yayi yasa bashi da ayyuka a gabansa har ya amsa gayyatar gaggawa da aka tura masa. Bai yarda aikin gaske bane sai da Zayyan yayi magana dashi yaji muryar babba. Emzee yayi masa sauran bayani aka bukaci ya tafi Kwara jibi sannan aka bashi nambar wayar Radhiya. Karamin aiki ne ya koma babba domin tana gama yi masa bayani yaji gabadaya ta kwadaita masa son aikin. Email dinsa ya tura musu a take Arifah ta tura masa sauran bayani da kuma tsarin kalmomin tambaya na hira da Radhiya zata rinka yi musu. Kusan kwana yayi yana bincike mai zurfi akan harkar rayuwar sojoji da irin matsalolin da suke fuskanta na yau da gobe. Gari na wayewa ya nemi Assistant dinsa suka tafi Kwara. Shi da ba kowan kowa ba sai gashi a gidan gwamnati ana karrama shi. Takarkar contarct wadda Ibrahim ya tsara aka tura musu suka yi printing a take Bigman yasa hannu Radhiya ma ta saka sai Arifah da Assistant dinsa a matsayin shaidu. Gyare gyare suka kawowa aikin ta fannin yanayin presentation da dialogue (maganar da zasu rinka yi idan camera na kansu). Karin bayani yayi musu cewa ba shirin film bane amma ko documentaries ana tsari sosai kafin ayisu idan ba haka ba zai zama kara zube karshe a kasa isar da sako sai asarar lokaci da kudi. Wannan abu ya yiwa Radhiya da Arifah dadi. Sun dauki lokaci a wani falo da aka basu suka gama gyara komai washegari sai wurin Maman Dolapo. Motar da aka basu bus ce wadda camera man ya sako kayan aikinsa suka taho tare da dan gari wanda yake musu rakiya da kwatancen da aka basu. Layin da suka shiga a cabalbake yake da ruwa kamar tsakiyar kasuwa. Tambaya ya rinka yi har aka kaisu gaban wani gida mai karamar kofa da shago a jikinsa. Babbar mace ce zaune a kan benci a kofar shagon da aka zubawa provision irisu kayan shayi da lemo. Ganin mutane cikin shigar alfarma ta fito da sauri tana dariya ciniki yazo. Da pidgin English tace musu. "Una welcome, wetin u wan buy?" (Sannunku da zuwa. Me zaku saya?) Zuciyar Radhiya ta bata wannan ce Maman Dolapo din haka kawai sai taji kwalla ta taho mata. Shagon fa babu wani abin arziki a ciki duk kankantarsa ko rabi bai cika ba. "Mama Dolapo?" "Yes, yes" tace a dan tsorace don bata ganesu ba kada ace 'ya'yanta sunyi laifi ne. Hoton da Ummi ta bata ta ciro daga jaka ta mika mata "kin gane wannan da kuka zauna a Sokoto Mairama." Hoton ranar sunanta ne da akayi da su Ummi da yawancin matan da suke makotaka dasu. Namiji daya ne a cikinsu Awwab yana manne da Mama saboda a hannunta Radhiya take ya dora nasa hannun ya tallefota ta kasa. A take Maman Dolapo ta saki kuka tana tuno shekaru masu yawa da suka gabata. Idanu ta zubawa Radhiya kafin cike da rashin yarda tace "kene yarinya wannan ko?" Ta nuna Mairama. Kai Radhiya ta gyada da mamakin yadda matar tayi saurin ganeta. Ji tayi ta tattarota gabadaya ta rungume tana ihun murna. Makota kuwa da masu shaguna aka taro a kofar gidan tana kuka tana dariya tace 'yarta ce tazo daga Sokoto. Cikin gidan ta ja su ta rasa inda zata saka kanta don murna. Nan ta tura aka kira Dolapo daga garejin da yake aikin makanike da sauran yaranta. Duka bayanin Radhiya ta gane ga kukan da taci na jin dawowar Zayyan daga prison. Canja kaya taje tayi aka hada yaran duka sannan aka fara shirin daukar kashi na farko na shirin Military Voice. Ana dora camera akan Radhiya a kofar gidan inda zata gabatar da gidan waye suka zo jikinta ya fara bari. Anyi ya kai sau biyar sai tayi kamar zata daure sai murya ta fara rawa. Arifah ta gaji ta kira Awwab. "Matarka fa zabuwa ce ta kasa yin abinda ya kawota sai rawar jiki take yiwa mutane" "Bani ita" Yaso ace tare suka zo Allah bai nufa ba. "Schatzi" ya kira sunanta a hankali. Hawaye ne ya digo mata ba shiri "Hammana" "Mw kike tsoro hmm? Ashe baki damu da rayuwar da families din sojoji suke yi ba." "Na damu mana" "Then do your best my baby..go on and make soldiers proud" Wani irin dadi da karfin gwiwa taji gami da kunya tace masa "kayi ta min addu'a har mu gama na sake kiranka" "Alwala ma zanyi yanzu kinji. Jeki kada ki bata musu lokaci" Rigar da ta dora akan kayanta mai karamin hannu da tambarin makarantarsu ta gefen dama a gaba kuma an rubuta AZM Tureta. Gyara tsayuwarta tayi ta gabatar da kanta da kyakkyawan murmushi. "Alheran welcomes you to the Military Voice" Daga nan tsarin Darakta Bigman da kalaman da Arifah ta rubuta ta rinka bi har suka shiga cikin gidan inda Mama Dolapo take zaune a tsakiyar 'ya'yanta guda shida. Ta amsa tambayoyi game da sunayensu, aikin mijinta da shekarar da ya rasu. Sai kuma irin yadda suka rayu da wahalhalun da ta jurewa domin 'ya'yanta. "A iya zaman da kuka yi da mijinki ko zaki iya fada mana wane abu ne yafi tsaya miki a rai game da aikinsa na soja" Kwalla Mama Dolapo ta share tana murmushi mai ciwo tana magana da pidgin dai wanda a wurin tacewa zasu rubuta abinda take fada da turanci mai kyau a kasa saboda mutane su fahimta "kinsan kowane maaikaci yana fita yaje wurin harkokinsa ya dawo gida ga iyalansa. Idan tafiya ce zai ce kwana kaza zanyi na dawo. Amma mu indai miji yace zashi aiki fieldwork to fa dake matar dashi sai kun ga juna kawai musamman wurin rikici ne. Mafiya yawan lokuta duk inda sojoji suka je kai taimako na tsaro indai wata mushkila ta taso da za'aji rauni ko rasa rai da wuya idan ba cikinsu bane. Mu muna gida muna jiran tsammani bayan ko su a junansu sun sani kila fa idan na tafi nine bazan dawo ba ko abokin aikina wane. Babban tashin hankali shine kiga wasu sun fara dawowa baki da cikakken bayani game da naki mijin. Kullum kina cikin shiri kiyi wanka kiyi girki ki gyara gida kina sa rai yau ne, gobe ne, jibi ne zai dawo gareki. Idan da rabo ya dawo idan babu kuma sai dai sakon mutuwarsa" ta karashe da wani irin matsanancin kuka. Cameraman din sai da ya kawar da fuskarsa ya goge ido. Haka Darakta Bigman, Assistant dinsa, Arifa da Radhiya kowa ya zubar da kwalla. "Kin taba nadamar auren Soja" "Ko kadan, bana fushi da aikin mijina don nasan ba kowa bane jarumi kamarsa. Damuwata bata wuce yadda rayuwa ta koma mana ba bayan ransa. Mata da yawa da muka rasa mazajenmu ance za'a bamu wani abu to amma lokacin wai babu kudi. Shekaru ashirin da biyu kenan tun ina zuwa Sokoto har na hakura na dena." Radhiya tace "abu na karshe, kina da wani sako da kike son mikawa ga gwamnatin kasar nan?" "Ina dashi....KU DUBE MU 'yan Nigeria!....a kullum kwanan duniya ana mutuwa kuma muma din mazajenmu kwanakinsu ne suka kare. Sai dai abin dubawa shine umarnin kasarsu da son kare rayuwar miliyoyin jama'ar cikinta ya kaisu ga rasa rayukansu, su bar iyalai babu gata. Ku tuna da marayu da zawarawan da sojoji suke bari, ku tuna da su kansu sojojin domin damu dasu babu abinda za'a biyamu ya maye mana gurbin kewar da muke kwana mu tashi da ita idan suna bakin aiki. Abu daya kawai nake so shine kasarmu ta dena mantawa damu da sadaukarwar mazajenmu. Bakunan al'umma su rinka yi musu addu'a a duk inda suke domin su sake samun kwarin gwiwar yin aikinsu." "Maman Dolapo mungode" "Mune da godiya" Ana dauke camerar daga kansu Radhiya taje ta rungume Maman Dolapo tana hawaye. Wai a haka ma don matar ta sakaya wasu abubuwan ne. Kafin su tafi envelop ta dauko a cikin jakarta. Sakon Ummi ne a ciki na dubu hamsin ta mikawa Maman Dolapo da kuma katin da aka buga da wuri na walimar da suka shirya ta dawowar Zayyan domin ta bawa matan wadanda suka zauna tare. Dubu dari dama Ummi ta ware musu ita da Christie saboda idan ka cire su Mami bata da tamkarsu kuma a zamansu na barrack din. Washegari gidan wani soja mai konanniyar fuska suka je. Duka duka bai fi shekaru talatin da biyu ba. Nasa labarin ma ya tabasu inda yace an tura shi aiki ne cikin garuruwan da ake yawan rikici. Wataninsa bakwai ya dawo gida bayan wata biyar da dawowar tasa matarsa ta haihu. To ba shiba kusan kowa ya tabbatar jariri ba nasa ba. Mata da ta ga an ganota tace laifinsa ne baya bata kulawar da ta dace. Tun aurensu sau nawa ya taba yin wata guda tare da ita. Yayi bakincikin abinda tayi masa iyayensa suka raba auren ya sake tafiya aiki. A can kuma wuta ta kama a wani ginin maaikata bayan rikici ya balle suka je kai dauki. Nan ya kone sosai da kyar aka samu ya rayu amma rabin jikinsa da fuska sun kone. Aikin da yake ji dashi dole ya hakura sannan shekara biyar kenan duk inda ya nema ya rasa saboda munin halittarsa. Babu wanda yake tunawa da cewa mutum shida ya tseratar daga gobarar nan kafin zuwan motar kwana-kwana. Lokuta da dama ji yake inama ya mutu ya huta da kyamar da al'umma suke nuna masa. A tsukin kwanaki goma su Radhiya sunyi yawo a garuruwan Nigeria lungu da sako suna hira da sojoji ko iyalansu. Kuka kam ba'a cewa komai. Darakta Bigman ya ga wani salon rayuwa da basu taba sanin akwai ba. A irin yawon sun hadu da matan da suka yi sa'ar samun wani abu na kyautatawa daga daga dangi ko abokai ko kuma cikin abinda ake bawa mazajensu daga wurin aikin. Sai dai da yawansu babu abinda yake daga musu hankali kamar kewar mazansu na bakin aiki ko wadanda suka rasu. Abin da ban tausayi matuka. Masu nakasar dole a dalilin rashin wata gaba da suka yi a bakin aiki su ma tasu rayuwar yana cikin garari. Da dama cikinsu kuma sai su kasa rungumar wani aikin saboda tsaro suka sani shi su ka fi iyawa. Tafiya ce irin wadda ake kira mabudin ilimi suka yi. Wuri na karshe da suka je shine garin Onitsha (Onicha) wurin Christie. A wata makarantar kwana ta 'yan mata suka sameta inda take aiki a matsayin malamar Geography. Christie tayi kukan sake ganin Radhiya sai da ta hadasu a waya da Ummi kamar yadda ta hadasu da Maman Dolapo. Ta amsa tambayoyin da Radhiya tayi mata inda take tambayarta yadda ta sami kanta a aikin koyarwa. Sa'arta daya sai da ta hada NCE dinta sannan tayi aure. Bayan labarin mutuwar mijinta ta koma gida ashe tana da ciki. Da Radhiya da camera man suka bita cikin gidanta da tace su shigo. Kofar wani daki ta bude yarinya budurwa na kwance tana bacci ga kafafunta a lankwashe. "Rebecca sunanta. Kashinta bashi da kwari bata tafiya ga matsalar kwakwalwa. Saboda ita ban sake aure ba ga rashin kudi da kyar na sami wannan aikin na koyarwa. Matsalar farko da na fara samu shine rashin mai kula min da tunda bani da kudin da zan biya mai raino. Wurin aikin suka ce na dena zuwa da ita a bayana lokacin tana da shekara goma na fara. Nasan wasu zasu daukeni mara imani amma bani da yadda zanyi. A gida nake kulleta naje aiki na dawo in tarar tayi kashi da fitsari. Ko ta mirgina inda zata iya jin ciwo daga baya na soma daureta idan zan fita shima da kaina naga rashin dacewarsa. Shine fa nake takura mata na hanata baccin dare har ta saba sai da safe tayi har naje na dawo. Albashina dashi muke cin abinci da sayan magungunanta duk sati. Rayuwarta akwai tsada sosai shiyasa na kasa daukar mai aiki har yanzu" Dole mai imani ya zubar da hawaye idan ya ga rayuwar Christie da 'yarta. Itama dubu hamsin Radhiya ta bata inji Ummi da katin gayyata. An sha wahala amma ana fatan bukata ta biya. Tare suka koma Abuja harda Darakta Bigman saboda zai duba video din gabadaya bayan an gama editing. Arifah da Radhiya kamar kada su rabu ance sabo turken wawa. Gashi dai suna gari daya amma saba su kwana daki daya suyi komai tare. Kafin ayi bacci kuwa kowacce zata raba lokaci da masoyinta idan an kare su koma hirar samarin nasu suna dariya. Kwanaki bakwai ya rage mutan Nijar su zo kawo gaisuwar Arifah. Yousuf kuwa jiransu yake yi su dawo dama ya taho domin kara gina kansa a zuciyarta. Kowacce ta shiga motar da mahaifinta ya turo daukarta. Cameraman da Bigman motar su Arifah suka bi za'a saukesu a hanya sai jibi idan sun kammala aikin hadawa zasu je gidan Major General Zayyan. A guje Radhiya ta shiga gida ta kwakume Ummi tana murna. Itama Ummin tayi kewarta sosai gidan kamar ba shi ba. Zayyan da taya bera bari kuwa dagata yayi yayi juyi da ita ai kuwa yasha nishi. Ummi ta rinka dariya. Abinci taci sosai Zayyan yana ta tausayinta wai ta fada tana gamawa tace bacci zata je tayi sai jibi da safe a tasheta. "Ana la'asar zaki ji bugu idan baki tashi ba" cewar Ummi "A tasheni sallah amma banda cin abinci. Na gaji sosai Ummi" Tana sauke hakarkatinta akan gadon sai bacci kamar an jibge kayan wanki. Da kyar take tashi tayi sallah ta koma. Bayan isha ne Daada yace Ummi ko kunu ne ta dama mata baya so ta kwana da yunwa. "Sai kace wata jaririya..idan taji yunwa zata fito ne" "Ni dai ki dama don Allah. Baki ga yadda tayi zuru zuru ba kin kuma san meye a gabanta. Ni bazan kai 'yata gidan miji a bushe ba azo ana mata gori" "Oh ni Mairama, waye zaiyi mata gorin?" "Awwab mana. Yanzu tana murmurewa a gidansa zai ce kamar ba ita ya dauko a bushe ba." Tafa hannuwa ta shiga yi tana dariya "Wannan uban amarya mun ga ta kanmu." Lallabata ya koma yi saboda da gaske yake dan wuya ya gani ta fara yi saboda rashin hutu "taimaka kinji 'yar albarka Mairama baiwar Allah" Ba yadda ta iya haka taje ta dama kunun gyada ta tafi dakin. Wata irin kwanciya Radhiya tayi a wargaje tsabar ta tara gajiya a jikinta. Ummi kuwa ta sakar mata duka a cinya ashe Zayyan ya gani "A'a Wallah ki bari fa. Daga cewa ki bata kunu sai cin zali" "Dubi yadda ta kwanta fa" Murza idanu Radhiya take yi ta tashi tana tura baki "Ummi me nayi?" tace cikin magagi. Zayyan karasa shigowa yayi ya zauna a gefen gadon kusa da ita "tashi kisha kinji Innata kada ki kwana da yunwa" "Na koshi" tace da kyar idanunta na rufewa. Allah Sarki ji yayi bazai iya bari ba yana tausayin 'yar tasa. Da tare dashi suka girma Allah kadai Yasan irin yadda zai shagwaba kayarsa. Gyara zama yayi ya dora kanta a kafadarsa idanunta a rufe "rinka bude bakinki kinji Alheran sai Ummi ta baki" Baki Ummi ta wangale ta ma rasa me zata ce masa. Wannan sangarta har ina. Shi kuwa kiss ya hura mata wai ta rufe bakin ko ya matso. Daure fuska tayi tana nuna masa Radhiya dake zaune kanta a kafadarsa ido a rufe. "To ki bata ko yanzu..." "Naji, naji. Ke bude baki ko na kwara miki kowa ya huta" Da rarrashi Zayyan ya samu take bude bakin Ummi na bata yana shafa mata baya har ta shanye. Ta bude na karshen Ummi tace "ai sai ki rufe bakin ya kare" Zamewa ta soma yi zata kwanta Zayyan yace ta dan yi hakuri ko yaya cikinta ya sassauta. A daddafe tayi minti biyar sannan ya gyara mata kwanciya ya kashe fitilar dakin sannan ya rufe kofa yana dariya shi kadai. "Kalau kuwa Sojana" "Lafiya kalau...yau dai mafarkina ya tabbata. Kin tuna na taba ce miki ina son komai na Alheran ayi dani. Ko wanka kike kyuyar yi mata ni zanyi saboda bana son missing komai na rayuwarta tun kafin cikin Zayyan. Na rasa abubuwa da dama amma kafin ta koma hannun Awwab sai dai ku rufe ido" "Sojana ba fa babyn da ka tafi ka bari bace. Kaima duk ka wani tsufa shine zaku yi mana kara'i" "Ba don kada abin nawa yayi yawa ba har goyata sai nayi" "To ni a goyani mana" suka ji Emzee yace yana hawowa saman saboda bai ga kowa kasa ba. "Karasa min shi zaka yi?" Ummi tace suka sa dariya. "Yau daya dai nima inyi shagwaba irinta Adda" Emzee ya zagaya bayan babansa ya sako hannuwansa suka zagaye wuyan baban. "Anya Zayyan ba zamu jira idan matarka ta haihu nayi goyon ba..na jika ne kamar buhun siminti" Zayyan yace yana riko hannuwan nasa da suke wurin wuyansa. Ummi ta yi gaba kuwa "Ah to ku bari na tafi don kada ma na dorar" Emzee zai sake shi kenan ashe Zayyan shammatarsa yayi sai ji yayi ya raba kafafunsa da kasa ya zagaye falon dashi. Kunya sosai ta kama Emzee sai gashi zai gudu daga falon Zayyan ya janyoshi ya rungume. "Allah Yayi muku albarka" "Amin Daada" ya amsa da 'yar kwallarsa. Kasa yayi da gudu Zayyan ya kife akan kujera. "Fillo yau fa sai kinyi min tausa" "Kai da kake jin goyo nima bari nazo na hau" Wani kallo yayi mata kasa-kasa ta tashi tayi gaba da sauri. Har yanzu tana jin kunyar mijin nata da baya rabo da tsokana kamar ba babba ba. *********** Kwana biyun nan Radhiya bata komai sai bacci. Ita bata san ma ashe basa samun hutu ba sai da ta dawo gida. A rana ta biyu sai ga Yousuf ya iso. Yayi wani fes dashi aka fara tsokanarsa ya kusa zama ango saboda yadda Babban Arifah ya matsu da tayi aure bai ga dalilin jira ba. To shima baban Yousuf din ya matsu nasa tilon dan yayi aure shiyasa tun a waya su ka gama daidaitawa da Excellency. Abu ne na manya kuma kowa yana ji da nasa. Da yamma Emzee ya kaishi gidansu Arifah yace to ya nemi mai dawo dashi don yasan yau din ta dabance a wurinsu. Shi kuwa gobe zai koma Kaduna makaranta yana da abubuwan yi. Yana komawa gida an kawo copy na farko na aikin su Radhiya. Sakawa akayi a falon Daada, Ummi, Bigman da Camera man da uwar gayya. Taken National Anthem aka fara kafin nuna mutane a garuruwa daban daban na kasar da muryar Radhiya tana bada takaitaccen uwa ma bada mama Nigeria uwar 'ya'ya da yawa. Daga nan fa aka shiga shirin sosai. Komai yayi tamkar kana kallon film da aka bata lokaci wurin kawata shi. Abin ya kayatar da Zayyan matuka. Mai camera dai Excellency ya sallame shi amma duk da haka Zayyan yayi ihsani sosai. Bigman kuwa cewa yayi rabin kudin zai karba saboda shi kiransa kawai da akayi ya bude masa ido da abubuwan da bai taba tunaninsu ba bare ya damu. Hasali ma dai bai dauki soja da wata daraja ba da ta wuce idan ya gansu suna checking a hanyoyi ya zagesu sama da kasa ya wuce abinsa. Alfarmar da yake roko shine idan wannan shiri zai cigaba don Allah yana son zama daraktansa kada su nemi wani. Inda baiyi musu ba sai a fada masa ya gyara shima yanzu yake wayewa da aikin. Su Ummi sunji dadi nan take Radhiya ta turawa Supervisor dinta sannan ta kara da doguwar wasika game da zato da suka yi mahaifinta soja ya rasu da dawowarsa. Cikin minti talatin matar ta kirata a waya ta tayata murna kuma ta yaba matuka da aikin na awa guda da aka yi a Nigeria. Sunyi mamakin saurinta tunda wata biyar aka bata. Basu san dan Nigeria da dagewa bane. *********** Bayan kwana biyu Radhiya tana ta rubutu ta saka computer a gaba tana hada report akan project dinta a daki. Sanye take da dogon wando da rigar sanyi tayi parking gashinta a tsakiya ba a nutse ba wani ya zazzaro ta gefe da bayan. Ummi ce ta shigo da plate din fruits da ta yanka ta mika mata. Fuskarta a sake take tace "Gashi 'yar gatan Daada kun maidani 'yar aiki ko" sai dai har ranta Alheran tana burgeta. Waye zaice yarinyar za ta nutsu haka har ta bawa karatu mahimmanci. "Ummina yi hakuri so nake na gama ne kafin jibin da zamu tafi Sumaila" "Wasa nake yi miki. Nima ina so inga kina kokari ai." Leka aikin tayi ta dan karanta wasu layuka ta koma ta zauna akan gado "kin kusa gamawa ne?" "Inzo?" Ta tambaya don tasan kila akwai abinda Ummin take son cewa. Kujerar gaban working table din ta juya zuwa bangaren Ummi tana fuskantarta. Murmushi Mairama tayi kafin ta soma magana a nutse "Alheran maganar aurenki da Awwab ce ta taso" Gabanta taji ya buga da ta tuna wancan karon yadda abubuwa suka kasance. Umminta ta kula sai ta kwantar mata da hankali. "Wancan karon na rabaku ne domin samar da maslaha. Yanzu kuwa sai inda karfina ya kare babu mai rabaki da Awwab sai Allah" Kunya ta kama Radhiya saboda Ummi bata saba yi mata magana haka ba. Dauke kai tayi kamar bata kula da 'yar ta ta ba ta cigaba da magana. "Nasara ta fada min cewa idan iyaye maza sun zo jibi akan maganar Arifah da Yousuf zasu roki alfarmar ayi auren karshen watan nan saboda basa son a ja lokaci kuma a ganinsu sauki nw tunda zasu zo taron baban naku dama. To shima maigidan nata ya fadawa Daada shine Daddy dinku ya yanke shawarar idan anyi finalizing maganar a haka to za'a daura auren Arifah ranar asabar ke kuma lahadi domin kawo sauki. Zai kama 27th da 28th December. Biki sai bayan sati biyu lokacin kinga an gama taron karrama Daada sannan munyi namu" Ai jikin Radhiya sai yayi sanyi da ta gama lissafi a kanta kwanakin basu fi sha wani abu ba. Nutsuwarta ta nema ta rasa duk ta wani firgice. Hawaye ta soma "Shikenan ni daga dawowar Daada sai aure" "Ki godewa Allah da yanzu haka za'a aurar dake mahaifinki yana kasa" Kuka ta fashe dashi sosai Ummi tace ko tayi shiru ko ta kira Awwab tace masa ya nemi wata ita ta fasa. Da saurinta ta dago kai sai taji kunya. "Ki kwantar da hankalinki na yarda da Awwab kuma kema kin sani zuri'ar su Mami sunfi karfin komai wurinmu. Sannan ki zama cikin shiri daga Sumaila wurin Innawuro zaki zauna sai ana kwana uku daurin aure tace gyara zata yi miki. Mun riga munje da Daada da kina can aiki" Tashi Radhiya tayi ta dare gadonta da tsalle "ni ko gadon ban mora ba Ummi zaku koreni" "Sai ki zauna morar gado sarkin shirme" Bayan kwana biyu suka tafi Sumaila ita da Ummi taron da Malamijo ya shirya. Emzee ya riga ya koma makaranta bazai fito ba sai gab da taron da za'ayi. Washegarin zuwansu sauran 'ya'yansa kowa ya gama zuwa. Su Habu da Bature sun ajiye iyali shima Ayuba saura watanni kadan bikinsa. Tun dare aka fara soye soyen nama da kayan miya kai kace biki ne za'ayi washegari. Yara da manya abin ya zame musu sabo amma kowa murna yake yi. Shadaya na safe washegari kowa da kowa ya hallara a katuwar tsakar gidan da aka saka mata rumfa da tabarmi. Kujera daya ce a tsakiya Malamijo ya hakimce abinsa bayan an bude taro da addu'a yace kowa ya tashi ya gabatar da kansa masu 'ya'ya kana gama fadin naka yaranka su fadi nasu. Salame ce ta fara tashi tana ta hura hanci tasha leshi mai kyau amma fa ita daban shima daban. Yadda ta matsawa Halifa lamba cewa tayi idan ya bari aka ganta a wulakance to kansa ya wulakanta. Cikin shagunan mahaifinsa yaje ya siyo mata mai kyau kuwa bai tsaya kanta ba ya siyowa duka yaranta sannan ya bawa Hibbah na Rahima yace ta kai dinki amma kada ya kai girmanta. Har kofar gida ya kai mata sai taji dadin zuwan nasa fiye da kayan. Ciki ta kaishi wurin kakarta ta kasa boye farincikinta tana ta cewa ga yayanta na Kano. Babanta ya saya mata mayafi mai kyau daidai aljihunsa da ya dace da kayan sai gata tayi wani irin kyau kakarta tayi ta wasa ta kafin ta fito. Da ta iso gidan a cike daya daga cikin kannenta ta gani ta tambayesu ina Ummansu yarinyar a tsiwace tace mata ta duba mana ko ta bata ajiya ne. Ajiyar zuciya tayi ta rinka dubawa ta ganota a can gefe taki sakarwa 'yan uwanta jiki. Yawan mutane yasa ta zauna a kusa da wata mai kama da larabawa sai wani irin kamshi take yi tayi kyau cikin jar atampa super. Radhiya ta dukufa yiwa Awwab text bata kula da ita ba sai ta taji Salame tana fadin sunanta ta ajiye wayar a cinyarta ta koma saurarenta. "Sunana Salame kamar yadda kuka sani kuma mijina Alhaji ne don ya sauke farali tun kafin wasu su fara rike naira" Rahima cusa kanta tayi a cinyarta saboda kunya Halifa yaji kamar yayi tsuntsu ya bar wurin. "Babban dana ma da babansa duka alhazawan ne yayi karatu a kasar Misira ne ko ...." neman Halifa ta rinka yi da ido ya dukar da kai. "Zauna haka Salame bari yaran suyi da kansu za'afi gane juna" Hajjo ta dakatar da ita. Malamijo ya samu ta dawo bayan ta gama fushin yanzu sannu a hankali yake binta. "Halifa sunana a Kano muke da zama" Salame tayi caraf ta amshe "waye zai ganeka a haka? Ka fada musu sunan babanka Alh Salisun kwari wanda kowa yake gani a talabijin" Duk da ita ta haifeshi ko kadan baiji dadi ba dama ga kadaicin rashin zuwan Emzee saboda makaranta. Yana zama Rahima ta mike a kunyace. Ita bata san mutanen gidan sosai ba Radhiya kuwa ta bita da kallo. "Sunana Rahima Usman" ta kara da sunan mahaifinta a zatonta haka ya kamata tayi tunda taji an yiwa Halifa fada. "Kin manta baki ce musu me buga iska a titin...." "SALAME!!!" Malamijo yayi mata wata irin tsawa da shi kanshi baya jin ya taba daga murya irin haka. Wata irin dabi'a ya karance ta da ita yanzun nan. 'Ya'yan da ta haifa da masu kudi sune mutane Rahima kuma bata da amfani. Da girmanta ta janyo wa kanta zubewar mutumci a gaban kannenta da 'ya'ya. Ummi sai tayi saurin mikewa domin katse shirun da ya ratsa wurin ana ta kallon Salame. "Sunana Mairama daga Adda Salame sai ni" Harda masu ihun murna cikin kannen saboda tuni ta fara janyosu a jiki tun bayan yadda ta sake ganin rigimar Mami da kannenta. Kallo na bakinciki da hassada Salame take wurga mata. Mairama dai atampa ta saka super itama amma duka wurin babu wanda ya kama kamar kyaun da suka yi ita da Radhiya. Fatar jiki ta nuna hutu da jindadi gami da kwanciyar hankali. Radhiya ta tashi ta fadi sunanta itama sannan tace akwai kaninta yana makaranta bai sami zuwa ba. A sanyaye take magana saboda hawayen da take gani Rahima na zubarwa a boye. Komawa tayi ta zauna ta kama hannun Rahiman guda daya ta rike amma bata ce mata komai ba sai ma matsawa da tayi jikinta ta saka daya hannunta ta dan rungumota a jiki. Sai da tayi mai isarta a hankali nutsuwa ta rinka zuwar mata ta dago jajayen idanu ta kalli Radhiya. "Abu ne ya fada min a ido fa kada ki zata kuka nayi" "Mai karya" Radhiya tace tana kada kai. "Ai dai baki ji na rantse ba" Murmushi suka yi wa juna Radhiya taji kanwarta ta ta shiga ranta yayin da take tunanin hanyar da zata bi ta kartawa Gwaggo Salame rashin m ko dan kadan ne taji idan da dadi gwasale mutum a bainar jama'a. 💕 [11/2, 7:24 AM]🏽: 52..💕 Sai da kowa ya gabatar da kansa aka kare akan jarirai Hassana da Usaina. Malamijo ya gyara babbar rigarsa yana kallonsu wai gabadaya tsatsonsa ne wannan. Bai taba tsayawa ya duba wannan babbar baiwa da Allah Yayi masa ta 'ya'ya ba. Kafin yanzu kallon nauyi da matsala kawai yake yi musu yana ganin matan da yake aura basa kyauta masa kowacce tana zuwa sai ciki. Babu wanda bai tara ba cikinsu da nagari da shakiyai. Akwai nutsatstsu ga kuma fitinannu. Biyu ma dai cikinsu kauraye ne 'yan chau-chau. Malamijo ya kusa shekara bai sasu a idanunsa ba kuma bai damu ba saboda sunfi zama a gidan kakaninsu na wurin uwa tunda babarsu daya. A can suka koma kaurayen saboda 'yan uwan babar tasu irin mafarautan nan ne masu yawo da karnuka. Ba'a tsaya nan ba duka dai cikin yaran nasa akwai rikakken dan jagaliyar siyasa wanda yayi suna akan rashin mutumci indai aka taba 'yan jama'iyyarsu. Ga dreban adaidaita sahu da karamin dan sanda mai mukamin kofur. Ga Mal Ayuba mafi rikon addinin cikinsu. Akwai mai sayar da kayan fruits a wheelbaro a cikin Kano. Bature shi da yake yayi NCE koyarwa yake yi, Habu kuma yana sayar da kayan masarufi. 'Ya'yan dai sai son barka kowa da inda yafi kauri. A bangaren matan ma dai babu wata mai ilimin da ya wuce secondary sai Mairama da ta koma lokaci daya da 'ya'yanta. Da yawansu basu gama makaranta ba. Na gidan mijin kalilan ne ga zaurawa biyu. Akwai uku marasa jin magana daya saurayinta dan daba, biyun kuwa samari ke daukar nauyinsu. Ba dai yawon ta zubar suke yi ba amma ana kanwar ta zubar din kai na hayaki suna jinsu daidai da kowa. Abinda Mal Ali Gidado Malamijon Sumaila bai saba ba kuma bai taba tunanin zaiyi ba ne yayi masa bazata. Hawaye ne masu zafi yake fitarwa saboda tun bayan wata nasiha mai nauyi da Ayuba ya cire kunyar mahaifinsa yayi masa jikinsa ya mutu murus. Duk wata guntuwar hayaniya sai ta dauke wurin yayi shiru. Mairama da bata hada son Malamijo da komai duk halinsa kuwa sai kuka. Salame ta kalleta shekeke ta tabe baki "sabon salo" Gyaran murya Malamijo yayi ya gama karya zukatan matansa musamman masoyiya Hajjo da Nene wadda yace dole tazo 'ya'ya nata ne itama "abinda zan fada muku ba yawa ne dashi ba, don Allah ku yafewa min" Yaran nasa ma sai gashi daidai da daidai matan nan suna yarfe kwalla da wannan kalami nasa. "Babu wani abu da nayi muku wanda zan bugi kirji dashi a gaban Allah game da rike amanarku. Haka Ayuba yace min jiya ko ba haka ba...Aradun Allah kasa bacci nayi duk ya tsoratani" Wasu na dariya wasu na murmushi saboda yadda yake maganar bai dauketa da wasa ba. "Nayi alkawari zan gyara sha Allahu kafin na mutu zanyi kokarin gyara laifina." Radhiya don ta rage musu nauyin da ya saka musu a zuci ta dauko zancen da tasan baya so "dama ana cewa siituna aw saba'una tafiya tayi nisa" "Don kaniyarki shekarata hamsin da bakwai watan azumin tsofaffi zanyi da takwas" yace fuska a tamke don yaki jinin zancen mutuwa. Gabadaya wurin ya kaure da dariya da mugun tsakin da Salame take saki. Sarai Malamijo yaji kuma ya kudiri niyar saitawa 'yar tasa zama. Nasihar hadin kai ya dora musu da ita sai gashi sannu a hankali wadanda basu magana a da ko dai don rashin jituwa ko don rashin sabo da juna hira ta fara barkewa a tsakaninsu. Abinda Malamijo bai sani ba shine gabadaya 'ya'yan nasa ba kin junansu suke yi ba rashin tsayuwar uba a rayuwarsu ita ce babbar nakasun da suke fama da ita. Yau gashi zaune dasu babu hantara babu zagi kowa ransa wasai. Yadikko ganin haka tace me zai hana suna cin abinci yaran na zuwa gareshi yaji me kowa yake yi kuma ya bincike matsalolinsu. Abin yayi masa dadi matan cikinsu masu kuruciya suka tashi aka zubo abinci ga nama shar dasu. Hayaniya kuwa sai da Radhiya ta kira Emzee tace tana ta tausayinsa saboda yayi missing. Sun dan taba hira ta ajiye wayar. Rahima ta kalleta a kunyace saboda ganin kanta take wata muguwar local akan Radhiyan tace "shine kanin naki da kika ce yana makaranta?" "Eh bari ki ga hotonsa saboda kada ku hadu baku san juna ba" tace tana binciko mata hotonsa a wayarta. Wanda yake sanye da khakinsa yayi wani kyau ta nuna mata. Shiru Rahima tayi tana kare masa kallo lokaci guda taji wata irin kunya saboda wani kallon kasa-kasa da Radhiya take yi mata "kema sojoji suna burgeki ko?" "Uhm ni dai tsoronsu nake ji" "Kice dai irin halin Fulanin zaki yi na tsoron duk mai uniform" Dariya suka yi tare wata yarinya da bata fi shekara goma ba ta kawo musu tray shakare da shinkafa dafaduka taji kayan lambu tayi kyau. Karamar uwa ce dai tunda 'yar Malamijo ce suka karba su hudu da wasu matan kusan sa'annin Rahima duka 'ya'yan gidan suka fara ci. Radhiya duka burgesu take yi kana ganinta kaga wayayyiyar 'yar boko ga gayu amma da ta shiga cikinsu ajiye komai take yi ta koma daidai dasu kamar yadda Umminta take yi. Abinci suka fara ci sauran matan suna yiwa Rahima korafin tana cikin garin amma bata son zuwa gidan duk ba'a saba da ita ba. Murmushi tayi kanta a kasa ita kowa ma kunyarsa take ji "Zan rinka zuwa yanzu sai kun koreni" Daga sama suka ji muryar Salame babu wanda ya kula da zuwanta sai hannunta da ta kama kunnen Rahima dashi da karfi "gani nazo tunda ke baki da hankalin idan kin shigo ki zo ki nemi uwarki ki gaisheta" Kunnen zugi yake kamar zai tsinke ta soma hawaye idanu sun fara dawowa kansu anata bata hakuri ta wani hade rai ita me 'ya. "Umma kiyi hakuri a makare nazo kuma bana son tsallake mutane na ga kinyi nisa" "Tunda an samo abinda babu a gidan tsoho ai dole kice nayi nisa. Maza kici ki tashi ki koma" "Umma!" Halifa yace a zafafe yana tahowa wurin ransa yayi mugun baci. Kafin ya iso Mairama ta fizgo hannun Salame wadda bata sassauta rikon kunnen Rahiman ba sai da ta saki wata wahalalliyar kara. "Ke wuce da ita dakin Yadikko ina zuwa" ta umarci Radhiya kafin ta finciki hannun Salame zuwa bangaren samarin gidan daga can gefe. Kwace hannunta Salame tayi tana furzar da yawu da hura hanci. Maganar da zata yi ce ta makale saboda ido da suka hada da Mairama. Borin kunya duk ya kama ta tace "ni kike yiwa wannan kallon Mairama?" "Nayi miki Adda ko zaki dauki mataki ne?". Bata ce komai ba ran Mairama a sama don zuciyarta wani irin tafasar bacin rai take yi saboda abinda Salame take yi. Ta gama kunyata kanta cikin kannenta sannan tazo ta matsantawa yarinya. "Hantara ko kadan bata da dadi ya kamata ace ke da kika girma a gidan nan ki fi kowa dorarwa amma shine tun dazu kin saka yarinya a gaba kuma a cikin mutane. Ko me tayi miki ki bari ku kebe mana. Su wadanda kike fifitawar ai ba finta suka yi ba tunda yadda kika haifesu itama haihuwarta kika yi" Cinya Salame ta buga "dadin abin dai baki isa ki fada min dadin haihuwarta ta ba bare kice ina cusgunawa 'yar wani. Ban shiga sabgar iyalinki ba kema ki tsame hannunki akan nawa. Halifa ma da kike wani jansa a jiki wallahi na hana daga yau a kyale min kayana" "Nan kuma baki isa ba. Idan kinsa karfi kin shiga tsakanin zumuncinmu bazan yarda da na 'ya'ya ba." "Mairama" tace da sigar warning tana kada yatsa "kada ki kaini bango" "Allah Ya ganar dake don ban ga amfanin magana dake ba" Mairama tace tana juyawa. Yadikko suka gani a gefensu "ke da nake yiwa kallon mai hankalin kuma ashe biye mata kika yi zakuyi rigima Mairama? Wai me ya sameku ne ku da kowa yasan kanku a hade yake kamar tagwaye" Tsaki Salame ta buga tayi gaba tana harare harare. Yadikko da take matsayin uwa a garesu a gidan abin yayi mata zafi sai Mairama ke bata hakuri. A can dakin da Radhiya ta kai Rahima kuwa yarinyar kuka take yi sosai abin tausayi. Radhiya taji wani irin haushin Gwaggon tasu ya dada shigarta. Maganar da Rahima tayi mata ne ya sake karyar mata da zuciya ita da Halifa da ya biyo su dakin. "Me na yiwa Umma ta tsaneni? Don Allah ku tayani bata hakuri" Kwalla ce ta taru a idanun Halifa ya fice daga dakin don babu yadda za'ayi ya fada mata abinda ya fahimta wato talaucin mahaifinta yasa take kinta. Dreban da ya kawo shi ya kira dama ya zaga cikin gari ne yace yazo su tafi an gama taron. Babu wanda ya yiwa sallama yayi tafiyarsa yana ji inama inama....don dai kawai uwa uwace babu yadda mutum zaiyi da ita. Radhiya rarrashin Rahima tayi ta yi tace mata idan babanta zai yarda tazo su koma Abuja tare. "Baffa baya son kwadayi Adda Radhiya" tace tana dan murmushi. "Zuwa gidana sunansa zumunci ba kwadayi ba kinji ko." Ummi tace tana shiga dakin da murmushi saboda yadda take jin son Rahima a zuciyarta. Hannunta ta kama ta mikar da ita "Tashi in hadaku da Habu ya biki gidan ya tambayeshi idan yaso kya dawo bayan bikin Addar taku" Baki ta bude da murmushi "Adda aure zakiyi?" Ganin idon Ummi yasa Radhiya jin kunya ta fita daga dakin. Ita kuwa zaunar da Rahima ta sake yi tana mata nasiha akan hakuri da mahaifiyarta. "Gwaggo na ga ku ma duk kun tsaneta kuma a gidan nata ma Alhajin kullum idan yana nan naje fada suke yi. Bata son kowa sai su Ya Halifa kuma itama ba'a sonta" Wani iri Ummi taji zuciyarta tayi nauyi. Wane da ne zai so ya ga kamar ba'a son iyayensa? To Salame haka kawai hassada da kyashi yasa ta bata da kowa nata kuma rainin da tayiwa baban Rahima yasa bata son 'yarsa bayan saboda soyayya ko auren fari baiyi ba ya aureta tana bazawara. "Ba tsanarta muka yi ba...kinga ki cire komai a ranki zamu daidaita kanmu babu ruwanku. Ke da 'yan uwanki zumuncinku nake so yayi karfi" Idan ba kakarta ba zata rantse bata taba doguwar magana da wata mace mai matsayin uwa ba a gareta sai yau. Ashe salihancin nan duka rashin samun wuri ne don samun fuska da ta gani wurin kanwar mahaifiyarta yasa ta saki jiki ta rinka fada mata matsalolinta da tambayoyi kala kala sai ga Ummi tana dariya sosai saboda sosai take ganin zallar kuruciya tare da Rahima. Irin abinnan ne dai wai ita kada a raina talaucinsu shine sai tayi ta daure fuska. Salame a zatonta ta tafi sai ganinta tayi da Mairama sunyi wajen inda mazan suke tana magana da Habu. To su din ma kowa yaji takaicin yadda ta rinka yiwa Rahiman shiyasa ba musu shi da Bature suka tasata a gaba har gidansu suka roki arzikin a barta tabi kanwar mahaifiyarta saboda suna son a farfado da zumumcin da aka saki a baya. Kakarta Iya abin yayi mata dadi don tasan Rahiman tana bukatar dangin uwa. Babanta kuwa da farko ki yayi sai daga baya ya rinka kashedin don Allah a cewa Mairama amana kada su wulakanta masa 'ya kuma a dawo da ita kwana uku bayan an gama bikin zaiyi daidai da kwana biyu kafin a koma 3rd term lokacin da zata koma makaranta suyi jarabawar fita. Da zasu tafi kowanne ya samo dan canjinsa ya bata ta shige da murna Iya tace maza ta debo kayanta masu kyan ta wanke. Duk bidirin nan Salame bata sani ba. Kuma tafiyar tasu washegari ne don da dreba aka hadosu. Tafiyarsu Rugar Barkindo ma Zayyan ya nace suyi kwana biyu kacal har Radhiyan su dawo saboda gaskiya shi an cuce shi ace sai ana baifi kwana biyu daurin aure ba Alheran dinsa zata dawo gida. Har yaushe suka gama hirar yaushe gamo. Sosai ya rufe idanunsa yace idan Mairama bazata iya fadawa Innawuro ba shi zai fada ai ba rashin kunya yayi ba kawai yana bukatar lokaci ne da 'yarsa kafin ta koma karkashin wani. "Son 'ya'yanka yayi yawa Sojana" Ummi tace tana dariya. "Kada ki ga laifina kinfi kowa sanin ni dasu muna bukatar juna" "Ni kuma ba'a bukata ta ko?" "Ke kuma matsayinki ai ba irin nasu bane. Idan kin dawo sai in kara jaddada miki cewa Tureta na Fillo ne ita daya" Hirarsu suke yi gwanin sha'awa bayan sun gama ta koma wurin Malamijo suna zancen bikin Radhiya da ya gabato. Don Zayyan ya fada mata washegari Rayyan da Badaru zasu je Abuja saboda zuwan iyayen Awwab wadanda Daddy Haroun zai yiwa jagora neman auren Alheran Radhiya. *********** Karfe goma na dare bayan Radhiya ta gama shirin bacci ta dauko wayarta ta ga missed calls din Awwab rututu. Turo baki tayi ta kira shi ya soma mita kuwa saboda rashin daukar wayarsa da ta tsiri yi. Ya damu sosai ya kwantar da murya a hankali yace "Me yake faruwa ne Schatzi? Nayi laifi?" "Hammana yaushe zaka dawo ne" yaji tace kamar za ta yi masa kuka. Yadda yake missing dinta ma baya jin ta kama kafarsa amma da yake ita ce mai bakin rigimar sam ta hana shi sakat. "I am trying to finish up da wuri na taho." "To" kawai tace ya dafe kai don ya sani ranta a bace yake da dadewarsa. Komai na Alheran burgeshi yake yi zuciyarsa tana kara aminta da soyayyar dake tsakaninsu cikin wani yanayi yana jan kowace kalma yace "Do you love me that much?" Kunya taji ta kalli gefenta da Rahima take kwance da sauran 'yan matan babu mai bacci sai kawai ta suri hijan ta fice. Shiru yaji bata yi magana ba sai da taje wurin dan tudun nan na soron gidan ta zauna. "Kasan ina nake yanzu?" Yadda ta iya yi masa shagwaba haka ya koyi yi mata shima "Baki bani amsata ba ni" "I do" Shiru suka yi kowannensu na begen dan uwansa. Shi yayi ta maza ya tambayeta ina take din. "A soron gidan Malamijo" Ai kuwa duk abinda yayi a soron nan ya tuna. Zamansu na cin abinci da suka rinka kama-kama da cokali daya sai kuma ranar da ya fara bata ragowar alawar bakinsa ta shanye sauran kadan din ya karba ya karasa. Kewarta sosai ta kama shi ya riga ya sabar mata da yasha ko yaci abu ya rage mata. Sau tari yanzu yana kai abu bakinsa ita ce take fado masa ya rinka tunani kenan. "Kin tuna min da memories masu dadi a wurin na kara missing dinki fiye da yadda nayi few seconds back. Bari na fada miki su daya bayan daya" Ita kadai take ta sakin murmushi yana fada mata din. Sai kuma ya koma rigimar wai ta kalli tsabar idonsa tace bata son aure. Wannan rigima taki wucewa a wurin Awwab sai dai idan bai tuna ba. Zancen gidan da zasu zauna ya yi mata idan bata da matsala dashi dazu iyayen nasu maza sun fada masa za'ayi musu gyara a bamgaren Ummi na da kenan zasu zauna kusa da Mami da Mama. Idan ta gama makaranta gabadaya sai ya nemi wani saboda bashi da ra'ayin zamansu a Germany duk da can yake aiki. Tunda aikin ba na zama bane babu amfanin ya ajiyeta can. Duk lokacin da yake off duty zai dawo Nigeria. Yana so ta cigaba da Military Voice ne amma babu inda zai fiye masa sama da ace tana yiwa kasar haihuwarta wannan aikin. Kare hirar tasu yayi da cewa ta turo masa sizes na duk abinda tasan cewa da size ake saya. "Kamar me da me?" "Seriously Schatzi? Nayi zaton zaki gane ba sai munzo muna jin kunya ni dake ba. Ai dai kinsan nasan size din takalminki" "Kunya kuma? Banda takalmin akwai wani abu ne da za'aji kunyarsa?" Tace batare da ta kawo komai a ranta ba. "Eh to kamar b...." Ihu ta saka masa ta ma manta dare ne da kuma inda take "zan yi maka text sai anjima" "Silly girl....call me kafin ku tafi goben kuma ina jiran size din b..." Kit yaji ta kashe wayar yana imagining din yadda take yi da fuska saboda kunya. Washegari suka wuce Rugar Barkindo harda Rahima. Tunda take bata taba fita daga Sumaila ba shiyasa ta kasa boye farincikinta. Ko me ta tambaya Ummi da Radhiya basa gajiyawa wurin bata amsa. Nan da nan ta zama lively kamar ba yarinyar nan mai boye kunci a zuciyarta ba. A irin shekarunta na tashen 'yan matanci babu abinda take bukata kamar uwa da zata sakata a hanya ko da ba ita ta tsuguna ta haifeta ba. Jin kanta take yi wata daban itama kamar kowa. Ummi har wani dokin isarsu Abuja take yi domin ta hadata da Zayyana kawance. Sakon Zayyan na a koma masa da 'yarsa ya riski Innawuro a take Ardo yace baiga laifinsa ba domin da ya girma dasu bazai fadi haka ba. Amma tabbas bayan aikin da ta tafi tana yawon garuruwa kuma ta dawo ana shirin aure ta sake nisa dashi bai kamata ba. Innawuro bata ji haushi ba sai ma dadin cewa mijin Mairama tabbas dan halak ne ya dawo da dakon son 'yarta kuma yana kokarin samun kyakkyawar fahimta da 'ya'yansa. Sai dai bata so yadda bata samu ta gyara 'yarta Mairama ba a lokacin nata auren jikar ma ta rasa. Su ma suna da hanyoyinsu na gyara amarya na gargajiya wanda bata so Radhiyanta ta rasa. Da suka yi kwana biyunsu suka zaga 'yan uwa ta hada kayanta ta bisu tunda su Ardo zasu je wannan babban taro na dawowarsa ga daurin aure sa dawo tare. Kafin su isa Ummi tayi waya a kai mata Zayyana gida ta taho mata da kanwa. Mami sai ta nemi Ibrahim tunda bai koma ba sai farkon February. Kadaici ne ya dame shi saboda rashin Emzee kullum baya gida kamar yaci kafar kare. A hanya suna tafiya tayi shiru kamar ba ita ba. Tun ranar nan da yayi mata magana akan dena kula shi da tayi bata yarda su hadu su kadai sai ta gudu. Kunyarsa take ji sosai kamar wani surukinta. Gidan Mama ma ta dena sakewa saboda tsoron kada ya rutsata. Gefen titi ya samu kusa da masu fruits. A tunaninta wani abu zai saya amma kowa yazo tambayarsa me za'a kawo sai yace babu komai. Wurin minti shabiyar Zayyana ta gaji da dukar da kan nata ta dago a hankali tace "washh" saboda kagewar da yayi. "Da baki dago ba nan zamuyi ta zama" yace yana tayar da motar. "Me yasa" ta tambaye shi murya kasa tana faman shafa wuyanta. Maimakon ya amsa sai cewa yayi "Rinka juya shi hagu da dama zaifi saurin sakewa" A hankali ta dago kai su ka hada ido. Wata irin faduwar gaba taji tamkar yau ta fara ganin Ibrahim din ba shiri ta kawar da kanta. Bai sake mata magana ba sai da ya rage tafiyar tasu saura kadan. "Zayyanatu" Babu inda bai amsa kiran nan ba a jikinta sai bakinta da ta kasa motsawa. "Nasan kinji abinda naji yanzu kafin ki koma kallon titi haka ne?" Baiyi tsammanin jin amsarta ba ya cigaba da kallon gabansa "my feelings are true idan na sami karbuwa ina fatan kare rayuwata Zayyana Mustapha tana tale min baki idan tana jin shagwaba. Abu daya ne bana so....dena yi min magana da kike yi" Cusa kanta tayi kawai a tsakanin cinyoyinta gabanta na tsananta bugu ba ita ta sake dagowa ba har aka bude gate din gidan suka shiga. A raunane Ibrahim ya dakatar da ita da zata fita "please Zayyana kice wani abu". Saboda yadda yake jinta a ransa idan taki amincewa bai san ina zai saka kansa ba. A guje ta fice batare da tayi magana ba. Tana shiga gidan tayi sama da gudu dakin Radhiya ta kankameta tana murna. Lokacin ko awa daya basuyi da isowa ba Rahima tana wanka. "Kalau kike kuwa?" Dariya tayi "Ras ras Adda" yau anya ma zata iya bacci kuwa take kissimawa a ranta. Gani take kamar ba gaske ba. Wai sai da yayi maganar take ji a ranta tamkar ta shekara da soyayyarsa sai yanzu ta farga. Wayarta ce tayi kara ta kasa dauka da ta ga shine sai rawa da jikinta yake yi ta saka a silent ta fice daga dakin zuwa wurin Ummi. A can tayi zamanta daga baya suka sauka kasa tare Ummi na son dora girki kafin Daada ya dawo tunda bata da mai aiki yanzu dai suke neman ko da mai shara ce ita zata cigaba da girkinta. Ibrahim suka tarar a falon ya kunna tv amma hankalinsa baya wurin. Kamar ta koma Ummi ta gama amsa gaisuwarta ta turata kitchen ta samo masa abin sha. Tana tafiya Radhiya da Rahima suka sauko daidai fitowarta daga kitchen Radhiya tana dariyar shakiyanci ta mika mata wayarta. "Gashi nan kin barta a daki wani Khaleel yana ta kira" Da sauri ta karbe tayi sama sauran kadan ta fadi Ummi ta bita da kallon tuhuma. Ibrahim ne ya hade rai ya cika yayi fam wato tana da wani Khaleel shine taki amsa masa dazu. Ummi ce tace ya hau sama dakinta su gaisa da Innuwuro don tace ita da saukowa sai da safe saboda ba ta kaunar hawa bene. Saman ya hau ya sami Zayyana a falo tana ta kai kawo da waya a hannu. Karbe wayar yayi ran nan a bace ya ga akwai lock ya mika mata. "Bude min" Budewar tayi ya sake karba da sauri ya nemo sunan Khaleel din ya kira a fusace yana jira a dauka ya fara fada sai wayarsa ta soma ringing. Guntun tsaki yayi saboda Khaleel din yaki dauka ga wayarsa ta dame shi da ruri. "Ana yi maka waya" Zayyana tace tana kallonsa a kunyace "Babu ruwanki....shi Khaleel din baya daukar waya ne?" "Nima ban sani ba" Kira yayi na uku can ba'a dauka ba tasa wayar kuma anki hakura. Yana zaro ta daga aljihu Zayyana ta karbe da sauri ta daga tasa a kunne idanunta a kansa. "Ya Khaleel ya akayi ne?" Kallonta yayi ya ciro wayarta dake kunnensa ya tabbatar muryarta ce a ciki yaji. Wani kayataccen murmushi ya saki idonsa yana yawo tsakanin wayar da fuskarta. "Ni Ibrahim Khaleel din?" "Bani wayata ni" ta shagwabe masa. Biye mata yayi batare da ya sani ba shima tasa fuskar yanayin yadda tayi...tale bakin nan da baya so. "Kin tayar min da hankali Zayyana. Its not fair sauran kadan zuciyata ta tsaya" Dariya take a hankali tana sadda kai shi kuwa tamkar ya hadiyeta ya fada tsundum baya fatan fitowa. Wayar ya mika mata da yaji kamar ana hawowa saman ya motsa bakinsa kadan "nagode" Dakin Ummin da yake a bude ya tafi wurin Innawuro ita koma ta koma kasa inda Radhiya ta hadata da Rahima. Kafin dare su biyun sun dinke tamkar sun jima da sanin juna. Sai wurin tara Zayyan ya dawo. Sallamarsa kawai Radhiya taji ta tashi a guje kamar yarinya taje ta rungume shi suka sa dariya. Rahima ya kalla da ta gaishe shi a ladabce tare da Zayyana. Ya saki fuska "Rahima ko? Yaya mutanen gida?" "Lafiya kalau, mun sameku lafiya?" "Alhamdulillah" ya amsa mata sannan ya bi bayan Ummi ya hau sama. *********** A kwanakin da suka gabata Innawuro ta dage wurin wanke jikarta da ruwan lalle mai kyau wanda babu wani hadi cikinsa sai zallan garin da take jikawa ta hada mata da ruwan turare wanda matar Baffa Gide ta hada mata da wasu itatuwa. Ranar da zata nuna mata yadda zata yi sai ga Radhiya ta fito daga toilet a guje fuska sharbe da hawaye tana cewa ita bazata yi wanka dashi ba. Innawuro ta rasa yadda zata yi da ita saboda kukan gaske take sai ta Ummi ta shiga tsakani. Tana faman hawaye da jan hanci daure da tawul tace "Ummi so take kawai jikina yayi faci faci da jan lalle a ce min dodo ranar bikin. Kinga fa haka ta taba yi min aski yanzu kuma ruwan lalle...ja take so na koma?" Zayyan yana jiyo su don ranar asabar ce babu inda yaje hankalinsa yayi dakin kunyar Innawuro ta hana shi shiga amma da tuni ya fito da 'yarsa. Ummi tun tana fada sai ta koma lallabata karshe dai ita tayi wanka da ruwan tace ta jira ta gani ko nata jikin zaiyi ja. Ai kuwa ta jira sai gashi Umminta ta fito jikinta yana wani irin santsi ga kamshi mai dadi. Washegari da kanta tace Innawuro ta hada mata tace taki suka gama dramarsu sannan aka fara gyaran jikin jika. Rigima ta biyu tana wannan baccin nata kamar wadda aka saukewa buhun siminti Innawuro ta daura mata lalle dungulmi har kusan rabin kafa. Kafa daya akayi ta farka a gigice zata cire Innawuro tasa Zayyana da Rahima suka danneta. Babu abinda Radhiya bata ce zata yi musu ba idan ta tashi ko a jikinsu sai da aka gama Innawuro tayi mata jan ido sosai. "Wallahi idan kika cire sai na saba miki. Wannan lallen dumama miki jiki zaiyi ana miki gata kina shirme" Hawaye ne ya digo mata "to sai ki min tsohuwa ta fada kwata ina laifin ma kice a siyo salatif ayi na gayu" Dun jgure mata kai Innawuro tayi "nasan damuwar taki bata wuce kada azo na biki wannan bai fita ba ko. To kisha kuruminki kina da akalla kwana ashirin dole zai fita kuma bayi miki zanyi a hannu ba" Baki ta zumburo "kuma safa zan rinka sakawa kullum" "Da kuwa kin burgeni domin so nake ki rabu da taka wannan tayil din naku duk ba gata bane a jikin mace sanyi na ratsa ta" Ta dai kwana da lalle amma da safe Rahima da Zayyana sai da tasa suka gudu daga gidan suka koma gidan Mami don cewa tayi balotelli zata yi musu. Tun suna dariya sai gata da almakashi tuni Zayyana ta tsure saboda ta tuna da. Akan lallen Awwab kansa yasha mita kamar shi ya kulla mata sai hakuri yake bata. Shima suna ta nasu shirin da Yousuf saboda ba wasu abokan kirki garesu ba. Awwab idan ka cire mazajen kannensa da Yousuf din a yanzu da suka yi muguwar shakuwa bashi da abokai a Nigeria sai na wurin aiki. Shiyasa kayan da zai yi amfani dasu na daurin aure iyayensa ya barwa ragama. Baba Hadir kaninsa ya turawa kudi da wasu kayan Awwab din domin ayi masa daidai jikinsa. A bangaren mata kuwa Mama tuni ta warke don bata zama. Duk abinda za'ayi ita ce gaba Mami da Ummi 'yan kallo. Siyayya suke yi sosai zuwan Mama Kano sau biyu. Zayyan dai ya saki bakin aljihu ne hankali kwance wannan arziki da Allah Yayi masa na ganin auren 'yarsa ba karamin abu bane. Duk wani abu da ake bukata na auren 'yar gata ya yiwa Alheran. Ana haka sai ga dankareren gado da setin kujeru 'yan Italy masu dan karen kyau da tsada Alh Mousa mahaifin Yousuf wato mijin Tante Nasara ya aiko dasu banda kudi masu yawa da ya tura ta account dinta yace kada ta tambayi Zayyan komai idan tana bukatar kari ta neme shi. 💕[11/2, 7:24 AM] : 53. 💕 Ita da Arifah suma nasu shirin suka fara inda da sahalewar angwayen nasu suka amince a hada dinner a Abuja bayan kowacce anyi mata nata bikin na gida. Arifah a Jos za'ayi wasu events din bikin 'yar gwamna guda daya tilo ita kuma Radhiya sai da aka yi ta tunanin inda yafi dacewa karshe Mama tace ayi a Abuja amma yini a Sakkwato za'ayi kamar yadda za'ayiwa Arifah a Jos. Ranar kai amarya kowacce a daukota daga garin mahaifinta washegari suyi dinner dinsu. Daga nan kuma tsugunne bata kare ba domin Tante tana can Nijar da sauran 'yan uwa ana shirin bikin 'ya'yanta Yousuf da Radhiya saboda haka ana wannan dinner din can zasu wuce ayi sabon biki sannan amaren su tare. Dama kuma Tante din ta riga ta sanar dasu Ummi kada a dauko wata mai gyaran jiki zata taho da kawarta tun suna 'yan mata idan sun zo taron Zayyan zata barta a nan. Arifah daga Nijar zasu wuce France shi kuma Awwab ya riga yasa an fara nemawa Radhiya visar Germany can zai tafi da ita suyi sati biyu su dawo Nigeria. Tun yanzu kowa jiki ya fara fada masa saboda shirye shirye. Ana ta kai dinkunan biki na amarya , 'yan uwanta da iyaye. Zahra da Raji sun dawo daga Katsina sai hutu ya kara daga wurin aiki amma fa idan ya koma shekarar kaf bashi da hutu. Fauziyya itama sauki ya samu sun koma Katsina sai daurin auren Bilal zai taho da ita. SANNU SANNU BATA HANA ZUWA Saura kwana uku daurin auren Arifah hakan na nufi kwanaki hudu ya rage na Radhiya amma har yanzu Awwab bai dawo ba sai bata hakuri yake yi al'amura sun zo ba yadda yayi zato ba. Radhiya tun tana daurewa sai da tayi masa kuka da daddare akan bata fatan a daura auren baya nan. Hakuri ya bata domin wani training aka saka yake jagoranta. Ainihi bashi bane da tuni ma ya dawo gida sai matar wanda zaiyi ta haihu sati biyar kafin ainihin lokacin haihuwarta. Abu yazo da tangarda dole ya dauki hutu. Gashi daga shi sai Awwab ne suka yi wannan course din a Ukraine. Tunda sunsan aure zaiyi shine aka daga masa kafa zai taho ana gobe daurin auren Yousuf. Ga abu ya dame shi ga fushin Alheran dinsa sannan Mami da Daddy sun kira shi a lokuta mabambanta kowanne baisan dayan ya kira ba suna jaddada masa idan ya bari aka daura aure babu shi zai ga fushinsu. Ya gama shirinsa tsaf ranar da zai taho ana gobe daurin auren su Arifah yayi ta kiran Radhiya taki dauka tana ta kunkuni. Text yayi mata mai dauke da dadadan kalamai ya sanar da ita yana hanya zai sauka shadayan dare. Bata yi masa reply ba sai sai kowa ya ga sauyi da walwalarta da ta karu. Tante ta fadawa ya taho tace to maza ta tanadar masa abinci a kai gidan Mami. Yousuf da suka zo da sauran mutanen Nijar shi acan yayi masauki dakin Awwab tare da Raji. Gidan Major General Zayyan kuwa babu masaka tsinke saboda 'yan uwansa na Nijar iyaye su Alh Sidi da Alh Ghoumar. Alh Mousa dai da mijin Mammee da sauran tawagarsu hotel aka kama musu. 'Yan uwa ne aka taru ko ta ina. Emzee ma ya da safe ya iso sai dai gidan Mama ya wuce kai tsaye ga mamakinsa Halifa ma ya riga shi zuwa suna tare da Ibrahim. Sakin fuska yayi kamar babu komai a ransa ya rungumi dan uwansa sai dai har ransa yana jin babu dadi da kuma hangen me zai faru idan gaskiya tayi halinta. Sai bayan magariba Radhiya ta dora girkin da Tante tace tayiwa Awwab Emzee da Ibrahim suka zo dauka. Farar shinkafa ta dafa masa tayi shar da ita sai dai baifi minti biyu ya rage ta kwashe ba ta juye mata alayyahu madaidaici a ciki. Gyareshi tayi amma bata yayyanka ba a haka tayi amfani dashi bayan ta cire shi. Ba kuma tsigar nan ta ganye kawai ba, ta hada ne harda itacen inda yayi karfi da yawa kadai take yankewa. Yau dai tayi kamar na mutum biyar ne tunda tasan su Yousuf na gidan. Miyar kuwa farfesun kaza ne da ta barshi ya danyi kauri an yanka dankali amma da girmansa a ciki da caras shima da dan girma sai koren wake. Rahima, Zayyana da Hibbah suna makale wurin koyon girki tayi ta gama. Sai da ta dibar musu suka sama mata lafiya. Ibrahim ne ya fara zuwa kitchen din yace Zayyana tazo ta bashi labarin Khaleel. Radhiya da bata gano komai ba tace "ashe dai zatona ya zama gaske da nake tunanin ko saurayinta ne kusan kullum sai ya kirata sai ta gudu don kada muji me ake cewa" Kashewa Zayyana ido yayi da take ta jin kunya Hibbah da Rahima sun san komai shiru kawai suke yi "zan binciko mana shi Adda Amarya muna zuwa" Bai yarda ya fita ba sai da ya sakata a gaba. Rahima ce take ta yiwa Radhiya tambayoyi suna tsaye ita da Hibbah ita kuma tana wanke kwanukan da ta bata Emzee ya shigo. Bata ganshi ba sai alama ya yiwa Rahima da suyi shiru. Ido ya rufe mata ta baya sai dai jini baya buya tuni ta gano rabin jikinta ne Zayyan dan Zayyan. Rungume juna suka yi tana ihun murna don har ta fitar da ran zai zo saboda tasan tsananin makarantarsu. Ya wani kara budewa ya kereta tsaho sosai yana mata dariya ya dan duku kansa "ashe nayi missing dinki Addata yau gaskiya kwanan hira zamuyi kafin Hamma ya daukeki, na fasa bin Ibrahim ma" "Ka manta ko an daura ina gida har sati biyu?" "Eh to idan ya bani damar hirar kenan. Muje dakina kiga wani abu" Suna juyawa Hibba tace "Ya Emzee ina wuni" "Lafiya kalau mai tale baki number two" Dariya tayi za ta fita taji Rahima tayi mata wani irin riko tabi bayanta da sauri. Radhiya tayi saurin cewa Emzee ga Rahima tana dakatar da ita su gaisa. Haba Rahima idanu tuni sun raina fata ashe tunda ya shigo ta tabbatar shine sojan taji cikinta ya kulle saboda girmansa da ta gani. Sai yanzu ya kula da ita a zatonsa 'yar uwar Hibbah ce ko wata dai cikin bakin biki ya saki fuska zai amsa gaisuwar da tayi masa a tsorace suka hada ido. Wani irin yanayi ne da bai taba zato ko tsammani ba ya fizge shi a take a lokacin ya fadada murmushinsa gareta yanayin idanunta tamkar wani maganadisu ya zame masa. "Kinyi kama da matsorata, yaya sunanki?" Ya tambayeta a kasalance. Yawu ta hadiya tace "Rahima" "Rahima zaki zama kawar soja?" ya sami kansa da cewa babu wani tunani. Duka Radhiya ta kai masa a baya ganin idanun Rahiman sun kara girma duk ta firgice "kada ka tsorata min kanwa dama har yanzu bata sakewa idan Daada ya shigo." Tana ganin Radhiya ta dauke masa hankali ta fita da sauri ta riga Hibbah zuwa daki. Sai da ta rufe kofa ta soma sauke numfashi da sauri da sauri. Tunda take bata taba ji ko ganin wani abu da ya kwashe mata nutsuwa kamar wannan bawan Allah ba. Danganta abin tayi da tsoron sojoji da take yi ta kai hannunta kirji tana jin yadda zuciyarta ke bugawa. A kasa kuwa kafin su bar kitchen din Ibrahim ya shigo yana kiran Emzee dreban da zai dauko Awwab motar ta lalace a hanya Raji kuma da yake gida bai san gari ba shine Ummi tace suje su dauko shi. Shi dai Emzee so yayi ya zauna a kira masa yarinyar nan mai idanu bai gaji da kallonta ba. Da abincin da Radhiya tayi a motar suka je dauko shi. Ibrahim kasa hakuri yayi sai da yace masa yayi jiki saboda aikin nasa yafi yawa a zaune gashi babu inda yake zuwa daga gidan da ake basu kamar hostel idan baka da ra'ayin kama wani ko kana da naka sai office din nasu. Murmushi kawai yake yi yana jin kewar Radhiya amma dare yayi ana neman shabiyu gashi jirgin safe zasu bi zuwa Jos saboda karfe biyu ne auren kuma suna tare da ango. Wanka kawai yayi da sallah yaci abincin nan sosai tare dasu Raji suka kwanta a gajiye bayan ya tura mata text din godiya tunda taki daukar wayar tasa. Ya dena damuwa don ya ma fi son haduwarsu ta gaba da amsa sunan matar Awwab. Da safe kuwa ba a nutse suke ba anata shiri. Duka kayan da zasu saka na daurin auren a jaka suka saka su. Suka wuce airport mota mota sai Jos. Karfe biyu da 'yan mintuna bayan sallar azahar Major General Zayyan Tureta ya karbi sadakin Arifah daga hannun kanin Alh Mousa naira dubu dari da dalleliyar mota. Nan da nan jama'a suka shaida auren Yousuf da Arifa abinda wata uku da suka wuce ko sanin juna basuyi ba bare suyi tunanin wannan rana. His Excellency the Executive Governor of Plateau state Rtd Col. Nasiruddeen Aliyu ya tara jama'a sosai 'yan siyasa manya a wannan taro mai dumbin tarihi. Ansha hotuna a ranar biyar na yamma suka sake dagewa sai Birnin Shehu. Ga gajiya an dauko ga wata za'a sake dauka gobe. Hotel da wani guest inn Zayyan yasa yayunsa kama dakuna da dama saboda yayi mamakin jama'ar da suka zo wannan aure. Da wuri ya biya kudin masaukin saboda haka basu sami wata matsala ba. Mutanen Katsina gayya guda sai kayi mamaki kamar ba su bane masu cewa dole Awwab ya auri 'yar uwarsa don duka kakanin Awwab sunzo su ukun. Malamijo da 'ya'yansa maza kananun ne kadai babu amma ya dauko kowa ga kannensa suma motoci suka ciko da mijin Nene. Ga jama'a guda daga Nijar wadanda suka halarci auren Yousuf jiya. Daga Rugar Barkindo Ardo, Baffa Gide, Baffa Habubakari da su Zakari kusan kowa yazo shaida auren 'yar soja. Mutanen Tureta da su Alh Salisu da duk wanda ya kamata sun zo. Chibuzor dashi aka daura na Arifah kuma yau ma yana tare da babansa Zayyan shima zai shaida. Karfe goma na safe aka saka saboda masu komawa a ranar su iya tafiya. Kusan ma dai kowa juyawa zaiyi suna sa ran da an daura anci abinci a fara tafiya. Zuwa lokacin Zayyan ya ciko sosai don Mairamansa ba da wasa ta tasarma fito da mijin nata ba. A babban masallacin juma'ar unguwarsu da yake bakin titi za'a daura auren. Wata hadaddiyar mota ce ta tsaya a harabar masallacin sojoji suka yi dafifin kare shugabansu. Mutum uku ne suka fito daga motar wata shadda suka saka iri daya ruwan zuma mai dan karen tsada. Dinkinsu da komai hatta hula da takalmi basu bambanta ba. Suna fitowa aka fara daukarsu a hotuna tun kafin su karasa ciki. Uban gayya ne Major General Zayyanun dan mutan Sakkwato yana ta murmushi kamar shine angon. Har yau da yake shirin aurar da 'ya bai dena tafiya da hankulan mata ba. Daga gabansa rike da wata sanda mai kyau domin samun balance din jiki Daddy Rtd Major Mustapha ne mutumin Katsinan Dikko kunya gareku ba tsoro ba. Kamilin mutum msi tafiyar da komai cikin tsari da haiba. A bangaren damansa kuwa aminin kwarai ne wanda abotarsu ta zame musu 'yan uwantaka Rtd Lt Hadir gaisuwarsa daban take jinjina ga dan mutan Kanon Dabo mai dutsen Dala da Gwauron dutse, Kano ko da me kazo an fika. Hadir Murtala abokin da Zayyan Tureta wadanda sukayi zamani a matsayin zaratan jaruman samari kyawawa. Su ukun nan tarihin rayuwarsu abin duba ne domin kada duniya ta manta da soyayyarsu da sadaukarwa domin kasarsu domin abotarsu. Taku suke maza 'yan uwansu na waigensu domin sun isa a dube su din. Cikin masallacin suka shige ana ta gaisawa da 'yan uwa da abokan arziki. Daga waje mintuna kadan bayan shigewarsu wata motar ta iso Awwab ya fito rike da waya a hannunsa yana sanye da shadda fara kal wadda aka yiwa aiki da zare ruwan toka msi duhu. Hula da takalminsa kalarsu daya da zaren sai agogo da links din hannun rigar duka silver masu kyau. Saboda kurewar lokaci ranar da zai taho yayi aski saisaye aka yi masa wani irin gyaran fuska da ya fito da gajeren kwata miliyon dinsa. Matashi ne ajin farko mai tattare da nutsuwa da kamala. Kallo daya za ka yi masa kasan cewa yau din ta dabance a wurinsa ranar aurensa da Alheran dinsa. A gefensa angon jiya ne Yousuf bayansu kuma Emzee da Ibrahim sanye da wani ubansun yadi da Mama ta dinka musu. Su dinma kamar iyayensu daga sama wato hula har takalmi babu ta inda su ka bambanta komai. A tare dasu Halifa ne shima ya fito fiye da zato. A cikin masallacin kuwa wakilan ango da amarya aka nema Hadir da Zayyan su ka matso gaban limanin suka zauna a kusa dashi. Yadda yake a tsarin musulunci haka aka gabatar da komai inda Hadir waliyin amarya ya karbi sadakinta naira dubu dari daga hannun Zayyan waliyin ango. Addu'a aka yi aka shafa Captain Muhammad Awwab Mustapha ya zama mijin Alheran Radhiya Zayyan Tureta. Hamdala ya rinka yi babu tsayawa a lokacin da yaji kammaluwar komai Schatzi dinsa ta zama tasa halak malak. Hotuna ake ta yi da gaishe gaishe na 'yan uwa da abokan iyayensu. Malamijo da tawagarsa kadai sun isa gayya. Gidansu Zayyan aka wuce ya sakarwa 'yan uwansa da matansu Badaru ragamar girkin da za'a ciyar da mutane kafin su tafi. Da farko Mairama yaso su zo su kwana a garin domin yin abincin ita kuma tace dama ce ta nuna musu yana kaunarsu kuma ya yarda dasu. Ai kuwa basu bashi kunya ba domin kowa yaci ya sha anyi abu cikin girma. Kuma sai da Baban Arifah ya samu yazo shima duk da mutanen da ya baro a gida. Maikudi ne dai idan akwai namijin mujiya to shi ne a wannan taron. Yana ta rakubewa a gefe Zayyan sai ya dauke kansa kawai. Daga baya ya ga bai da amfani nunawa duniya akwai baraka tsakaninsu shiyasa ya koma sako shi cikin al'amuran. Da yace Maikudi kuwa sai ka ganshi da mugun sauri ya taho. Ba su suka sami saukin kebewa daga mutane ba sai lokacin da ya idar da sallar la'asar. Yana zaune da 'yar cikinsa ya ajiye babbar rigar da hula can gefe. Bayan doguwar addu'a ya dauko wayarsa ya turawa Radhiya text din da yake ta son yi tun bayan an daura auren. (Ina hukuncin matar da bata daukar wayar mijinta? Ki fada mata Awwab ya zama na Alheran kuma ta shirya karbar punishment dinta na share shi). Hira suke yi da Fauziyya da Zahra rabi suna tsokanarta rabi kuma shawarwari ne suke bata tunda yanzu itama girma yazo. Ita dai jiki yayi sanyi kamar ba ita ba. Wani abin tayi dariya wani kuwa sai dai taji kunya idan sun fada amma ta kasa magana. Duk da ba bikin bane ya taso amma gidan ya rude don ma anyi sa'ar kawowa Ummi masu aiki biyu 'yar dattijuwa da kuma mai sauran kuruciya. Sakon Awwab ta karanta suka ga murmushin nata ya koma na daban. Fauziyya ta dago wuya zata leka wayar "Ango ya miko gausuwa kenan...mu gani me yace" Janyota Zahra tayi "ina ruwanki, idan kin matsu kiji me yace nemi naki mijin tunda suna tare kema yayi miki text din. Radhiya tashi ki koma daki kiyi magana da mijinki kinji" Kasa mikewa tayi Fauziyya ta cigaba da zolayarta sai da Zahra tayi da gaske don ta kula jikin kanwar tasu mai sabon mukamin matar yaya yayi mugun sanyi. Tana tafiya Fauziyya ta tallabe kanta da hannu biyu. "Jikin ta kanwa yayi la'asar fa Sis. Duk surutunta kinga fa bakin ya mutu. Allah sarki irin matsoratan amaren nan za'ayi" "Tausayinta kike ji ko tsokana?" "Tausayin dai...hmmm kazo kayi ciki ka rasa inda za ka tsoma ranka kaji dadi" Tuntsirewa da dariya Zahra tayi ta gano Fauziyya laulayi ne yasa ta a gaba shine za ta saka mutane itama. Bayan Radhiya ta koma dakin babu kowa. Gefen da tayi sallah ta kalla ta tuna nasihar da Mama tayi mata a wurin bayan ta umarceta da tayi nafila ta godewa Allah bayan an daura auren. Wata irin soyayyar Awwab take ji tana kara shigarta sosai ta lumshe idanu ta kwanta sannan ta kira shi. Sautin numfashinsa ne ya sanar da ita ya dauka amma yaki yi mata magana shima nata hawa da saukar numfashin kadai yake sauraro wanda ya kara masa gudun bugawar zuciyarsa. Ita ta fara kartse shirun nasu ta hanyar gaishe shi da tattausar murya "Hammana ina wuni" Da kyar ya iya hada kuzarin amsawa yana jin kamar yau ya fara son ta "Matsoraciya yaya kike?" "Tsoron me nake yi?" "Daga kinji nace zaki karbi punishment shine kika dawo daga strike din yi min magana mana" Kamar yana gabanta ta tura baki "to ba kaine ba" Katseta yayi don yasan fushin har yanzu na menene "Ko ba ni zan aureki ba kinsan bazan yi missing aurenki ba bare kuma Alheran din ta Awwab ce" Kunya taji sosai yayi murmushi ganin yau ita ce babu baki "wai ni tun yanzu ina bakin naki ya koma ne? Anya zamu shirya da wannan amaryar kuwa wata bebeya nan da ita" Ibrahim ne yayi masa alama da hannu motocin da zasu kwashesu sun iso. Ba yadda ya iya sallama yayi mata yace tayi musu addu'a gasu nan fitowa zasu taho. Kafin su iso anyi abinci sosai jiran isowarsu kawai akeyi. Kowa yaci ya koshi kuwa sai son barka aure ya yi albarka sai fatan zaman lafiya ga sababbin ma'auratan. A gajiye su ka dawo ana sallar isha kowa sai bacci. Angwayen biyu, Raji da Bilal suna gidan Mami. Ibrahim da Emzee kuwa gidan Mama. Daya ga wata ta matso babu lokacin zama babban taron da ake ta jira ne Allah Ya kawo shi. A haka ma da ba su ne suka shirya ba basu da zama balle kuma na washegarin da yake nasu. Dadin abin ma kuma domin tallata shirin Radhiya Baban Arifah ya samu yace a saka wani bangare nashi a wurin taron tunda shugaban kasa zai je. Ita kuma sai ta gaggauta sanar da Supervisor dinta domin ta nema mata izini. Kwana biyu a tsakani matar ta fada mata cewa su uku an wakiltasu zuwa su gani sannan su tayata murnar dawowar mahaifinta. Ranar kwanan murna tayi sai gashi ana gobe taron sun iso. Duk wannan lokacin angon nata yayi wuyar gani suyi nan suyi can saboda ganin sun kammala komai bisa tsari yadda suke so. Malamijo da kansa ya hada mutum biyar cikin masu zuwa taron daga gidansa a yara sai kuma Yadikko da Hajjo. Shatar mota yayi musu ana shirin tafiya sai ga Salame niki niki da kaya ita da yaranta wai itama zata je. Ba wani abu bane ya tunzurota kuwa sai labarin da ta samu na cewa Rahima ashe ta bi Mairama. Zuwa zata yi har gidan taci mutumcin yarinyar tunda tana son nunawa makiyanta cewa bata isa ba. Abu na biyu kuma so take taje ta ganewa idanunta wace irin rayuwa Mairama da Zayyan suke yi da akaje daurin auren 'yarsu a Sakkwato aka dawo ana zuzuta taron da angon da Radhiya ta dace da shi. Malamijo bai hanata zuwa ba amma da karamar 'yarta kadai ya yarda taje sauran ya turasu cikin gidansa. Tunda aka shigo garin Abuja bakin Salame yaki rufuwa tana ta kalle kalle. A tasha dreban ya tsaya aka tura wani dreban daga gidan yaje ya taho dasu. Nan fa cikin Salame ya duri ruwa ganin sojoji da bindiga tun daga bakin gate din wani irin katon gida mai kyau. Jikinta yayi sanyi kalau ba ta fatan ace wannan ne gidan Mairama. Bata gama tunanin ba kuwa aka wangale gate din gidan. Wani bacin rai taji ya tuko ta da fa yanzu gidan nan nata ne ba don bakincikin da Mairama tayi mata ba. Suna shiga Ummi da kanta ta fito tarbarsu da murnarta tare da Rahima wadda tun safe da tace mata Malamijo yace da Salame za'a taho jikinta yayi sanyi. Ummi tana kula da duk motsin yarinyar kuzarinta ya ragu sai kayi mata magana bata ji ba saboda zulumi. Ashe kuwa ba a banza ba don suna saukowa daga mota da ta tafi da murnarta saboda tana son Umman nata taje ta durkusa har kasa tana gaisheta. Kusan hambareta Salame tayi kafin ta dangwara mata yarinyar da ta kai shekara uku tana wani irin wari. "Ki wuce da ita ki gyara mata jiki tayi kashi sannan ki bata abinci " Jiki na rawa Rahima ta karbi yarinyar da kafarta da komai amma dole ta dauketa ta wuce Ummi ta shiga ciki. Itama Ummin ba ta niyar koyawa Rahima rashin kunya dole ta bi umarnin mahaifiyarta. Sakin fuska tayi tana musu maraba. Salame tana ta wani basarwa ita bata ga abin burgewa ba har suka shiga ciki. Tun daga katon falon zaka san gida ne na wanda ya isa duniya take damawa dashi. Dakunan da zasu zauna ta nuna musu da kanta su Radhiya suka zo gaishesu ita da Zayyana da Hibbah wadda tayiwa gidansu kaura duk da cewa Maman tasu tana gari. Duj inda 'yan mata suka hadu sunfi jindadin kasancewa tare musamman idan tasu tazo daya. Rahima wanka ta shiga yiwa kanwarta Khadi yarinyar tana ta yi mata rashin kunya "Ki dena tabani" "Kin kona ni" "Sai na fadawa Umma" "Ni ki bani sabulun da kaina dan wanke" Radhiya tuni ta hasala ta fada bandakin tace Rahima ta fita ta karbo mata kaya. Wani irin kallo ta yiwa Khadi yarinya ta bare baki za tayi kuka ta daure fuska "kina yi min kuka zan cillaki ta taga kowa ya huta mara kunyar kawai" Yadda bata ga alamun wasa a fuskar Radhiya ba sai ta hadiya kukan dama na samun wuri ne tayi mata wanka kamar tayi amai ace yarinya kamar wannan tana kashi a wando ga wani kai a daddage babu gyara anyi kitson roba da yawa sun warware. Zuge sauran tayi ta zuba mata shampoo akan ta soma kukan sai ta fadawa Umma saboda bata yarda a taba mata kai ko Salamen sai tayi ta lallabata tunda tana ji da ita. Radhiya bata sake bi ta kan rarrashi ba sai da ta wanke kan nan tayi mata wankan. A kasa kuma Rahima dakin da suke taje a gaban Salame ta durkusa tace a bata kayan Khadi. "Kin wanke wadancan ko kuwa ni zaki kawowa na wanke?" "Yanzu zan wanke Umma" Hajjo tuni ta fara zuwa wuya a kufule tace "Salame idan kinsan zuwa kikayi ki tsangwami yarinyar nan ina mai tabbatar miki yanzu zan kira Malamijo a mayar dake gida. Shashancin banza da hofi kai. Rahima ga jakarta can bude ki dauka" Ummi tana wurin ita abin na Salame yanzu tausayi ne take bata saboda ta hana kanta sakewa ta hana wasu. Rahima da ta duba kayan ashe na babbar Salame ta dauko garin haushin an hanata zuwa da dukkansu. Rigunan sunyi girma haka dai ta dauki wata riga zata saka mata ga pants din duk na babbar. A kanta Salame ta huce haushin rashin dauko kayan daidai tana ta yi mata fada saboda bata san yadda zata yi ba. Ummi ta kada kai "Rahima anjima bayan magariba kizo na aikeki dasu Zayyana" "To Ummi" tace a sanyaye ta fita. Tana cikin hawa benen Emzee na saukowa a gurguje yake tafiya suka kusa karo tayi saurin matsawa gefe. Idanun nan nata ne suka sauka a kan fuskarsa wadda a take murmushi ya maye gurbin bacin ran da ya sauko dashi saboda ganin Salame da yayi a cikin tawagar 'yan Sumaila. "Kawar Soja daga ina?" "Ni dai ba kawarka bace" Murmushi yayi ya nade hannuwansa a kirgi ya tsare hanyar wucewarta "nima ba kawancen kawai nake so ba harda...." Da sauri ta dago gabanta na faduwa "harda me?" Kansa ya dukar daidai fuskarta "harda idanun Rahima...zan samu?" Rikicewa tayi ta samu ya dan matsa ta kwasa a guje yana ta cewa tayi a hankali kada ta fadi. Sai da ya ga ta bace masa ya dan rankwashi kansa "Muhammad Zayyan kalau kake kuwa?" Ya tambayi kansa don ya rasa yadda akayi idan ya ganta daga bugun zuciya sai kasa controlling kansa da bakinsa da yake yi. Kai ya girgiza ya sauka ya dauki mota ya fita. Bayan magariba kuwa Ummi ta bawa Zayyana dubu ashirin da biyar tunda ita ce babba tace dreba na jiransu su siyowa Khadi kayan sawa kuma kada su manta da takalmi, pants da brush. Sahad ya kaisu suka kwaso kayan da ya dace. Rahima tana da wata dubu daya cikin kudin da Ummi ta basu rannan suka siyo kayan kwalliya ta sayawa Khadi packet din ribbons na dari shida za ta yi mata kitso sai ta saka mata. Gida suka wuce da murnarta bayan sun nunawa Ummi tasa musu albarka ta wuce ta kaiwa Salame. Ba karamin dadi Salame taji ba don bata da komai sai dari uku amma dayake ta saka hassada da kyashi a zuci sai ta kyabe baki. "Ki fada mata ina komawa gida zan turo mata kudinta don nafi karfin cin arzikinta yanzu ma don na manto jakar ne kuma a ciki kudina yake" Tashi Rahima tayi zata fita Salamen ta kuma kiranta "ina kuma zaki je? dawo nan ki kwanta kusa dani" To ai ko numfashin kirki bazata iya ba bare bacci a gabanta a tsorace take sosai Yadikko ta kama hannunta ta kaita bakin kofa ta ce ta wuce wurin yayarta Radhiya ta rufo kofar. Tana dawowa tasa hannu ta dauke Salame da wani gigitaccen mari. A kidime ta dago kai ga kannenta don ma Khadi tayi bacci. Hajjo tace tayi mata daidai. Rai a bace sosai Yadikko ta nunata da yatsa "ba ni na haifeki ba Salame amma ina tsammanin rikon da nayi miki ya bani matsayin uwar da ta isa dake. Nayi miki rantsuwa daga yau har mu tafi idan kika sake yin wani abu domin cusgunawa Mairama ko Rahima sau naci mutumcinki la'ada waje. Mutuminyar banza wadda bakinciki ya yiwa tsatsa a zuci." "Shiyasa taki gaba taki baya babu wani cigaba a rayuwarki" Hajjo ta kara da nata. Sunyi mata tatas don sai da tayi hawaye Yadikko ta kyaleta tana jin zafin wannan mummunar halayya ta Salame yarinyar da a da can tafi kowa shiru shiru a gidansu ashe macijin sari ka noke ce. Da rana Ummi ta bawa Yadikko katinsu na shiga wurin taron haka ma ta baiwa Tante wanda zata bawa nasu mutanen. To dayake dama da yawansu sun zo ne akan ainihin na gidan ba wannan ba da gwamnati ko muce sojoji suka shirya ba sai ba'a sami rikici ba. Katin ba yawa garesu ba kuma dai bazasu so suje su bawa kansu kunya ba. An gama hada masu tafiya su Mami suna gidan Emzee tun safe da yasa kafa ya fita basu sake ganinsa ba. Kafin sallar magariba sai ga Arifah da Mom dinta da gudu suka rungume juma ita da kanwarta Radhiya. Matar Alh Salisu itama ta iso aka fara shirin fita domin karfe takwas za'a fara taron. Sai da Ummi ta shirya mijinta bayan kyakkyawar kulawar da ya samu tamkar kada ya tashi saboda yadda yake jin matar tasa a rai. Sababbin kayansa da suka dace da mukaminsa ta taimaka masa ya saka ta saka masa sabuwar farar safa da bakin takalminsa tafiyayye cover shoe. Ya sake gyara fuska sai wani annuri yake fitarwa. Sai da ta kammala dashi sannan ta fita itama ta shirya don tare zasu tafi. Lace ne ta saka army green da digon gold a jiki. Mai kwalliya Mama ta dauko amma aka ce tayi mata matured kwalliya ba mai cika fuska ba kamar karamar yarinya. Tayi kyau matuka ta fito a Mairama Fillon Zayyan babu wata makusa sai hassadar makiya. Mayafinta gold ne sai takalmi heel da wata karamar dinner pause itama gold ga farin gilashinta ya sake fito da kyakkyawar fuskarta, hannuwa da kafafu sun sha jan lalle mai kyau da tasa 'yarta Rahima tayi mata. Matan manya ne suka fito ita da Mami, Mama, Tante, Mom din Arifah da Matar Alh Salisu. Fita suka yi kowacce ta shiga motar mijinta abin gwanin ban sha'awa sojoji na mara musu baya. Mutum biyu aka kara daga Nijar sai kuma Mubaraka yayar Zayyan da matar Badaru. Yadikko kuma ta bawa Salame, Ayuba da Bature kati don Laila ita dama tuni Ummi ta bata nata tana tare dasu Radhiya ana ta shiri. Kowa ya gama nasa shirin suka fito Radhiya ta saka wata abaya mai masifar kyau da daukar ido ja da bakaken stones. Covershoe mai madauri ta saka baki sai purse da ta saka wayarta da hoda. Duka dama abayar suka zabi sakawa sai dai kowa tata daban. Ummi ta fito da 'yarya Rahima don itama ta saya mata wata baka mai duwatsu pink. Idan kaga matan sai ka juya ka kara babu wadda bata yi kyau ba. Jawad da Femi a gida aka barsu saboda taron babu yara suka fito aka shiga motocin da suke jiransu. Mazan ma ba'a barsu a baya ba sun hade duka cikin suits kamshi na dukan kamshi su ma suna gamawa sai Nicon Hilton inda za'ayi taron a wani babban dakin taro da yake cikin hotel din. Decoration din wurin komai green ne da white an kawata shi fiye da zato ga ma'aikata a tsaye suna jira a shigo su nunawa kowa seat dinsa saboda akwai number a jiki. Awwab da Yousuf a matse suke da ganin amarensu abin takaici number din seat dinsu ya nesanta su da juna. Radhiya wata faduwar gaba taji da suka hada ido yana zaune kusa da Yousuf rike da waya a hannu. Ya hade cikin three piece armani suit khaki color da coffee coloured necktie ga brown din cover shoe. Daga inda yake a zaune ya daga wayarsa ya dauketa a hoto ta sadda kanta kasa a kunyace su Zahra suna mata dariya. Bayan an zazzauna kamar minti goma MC KDM sunan mai gabatar da taron wanda baya zuwa kowane irin taro dama sai na manya yace kowa ya tashi shugaban kasa zai shigo da first lady. Wurin zamansu daban aka zauna bayan national anthem da akayi. Ummi duk ta damu ina Karami sai da Zayyan yace ta kwantar da hankalinta dan nata yana nan za ta ganshi. An shiga taro ka in da na in hankula suka karkata suka koma ga MC da abubuwan da ake gabatarwa. Salame kallo daya ta yiwa Zayyan bata kara ba domin zuciyarta sai da tayi barazanar ballo mata kirji kuma abin takaici ga Alh Salisu a gefe sai taji duk ta muzanta a cikin mutane saboda kayan da ta saka na taron gidan Malamijo ne ganin kanta tayi wata koma baya a cikinsu. Duhu hall din yayi a take hasken screen da za'a gabatar da tarihin Zayyan ya mamaye wurin. An fara da nuna hotunansa yana matakin farko a soja sai dariyar manyan baki kake ji kadan kadan saboda daga hoton kadai zaka iya gane cewa Zayyan Tureta ba karamin fitinanne bane. A hankali aka zo kan aurensa duka ana nunawa ne KDM yana bayani. An tsayar da hoton akan shi da Daddy da Baba Hadir ranar tafiyarsu Liberia. Daga nan ya cigaba da narrating rayuwar da Zayyan yayi sai da gwamnoni biyu suka zubar da hawaye musamman da aka zo video din fitowarsa daga motar da ta kaishi Nigerian Embassy lokacin da ya hadu da Excellency da Awwab. Su Ummi sai hawaye yasa hannu ya rike nata a hankali tace "I love you Sojana" "I love you too Fillo" ya maida mata iya jin kunnenta. An kare video din da wani hotonsa ne shi da Ummi, Radhiya da Emzee a falon gidansa bayan sun koma. Fitilu aka kunna mutane sai sharbar hawayen jin labarin al'ajabi na wannan soja. MC yace kowa ya shirya domin ganin wasan da sojoji suka shirya domin murnar dawowar jan gwarzo jarumin jarumai. Wata murya suka ji inda mai ita yake commanding Cadets 'yan uwansa da kowa ya shiga layi. Tsit hall din yayi kamar ruwa ya cinyesu lokacin da aka saka wani kida irin na band din sojoji sai gasu nan sun fito mutum arba'in cikon na arba'in da dayan shine commander din wannan parade din wato Cadet Muhammad Zayyan Tureta. Sun sha training ba na wasa ba daga shi har sauran shiyasa babu kuskure ko na motsi daga garesu. Bindiga ce a hannunsu duk da ba harbi zasu yi ba suka yi wani wasa da ita da ya burge kowa a wurin. Komai nasu tare kidan yana chanjawa da umarnin Emzee. Karshe mutane suka ga wadanda suka gama parade din sun matsa Emzee ya sake bada umarni sai ga wasu suna fitowa cikin tsari suka shiga sahu suka yi wani layi layi sai da suka durkusa kowa ya gane sun rubuta Nigeria ne ai kuwa mutane a tare suka karanta "NIGERIA" Wasu suka fito a bayansu suma suka dunkule a kasa aka sake karantawa. "WELCOMES" Sai na karshen suma cikin gwaninta suka yi nasu layin tare da durkusawa. "ZAYYAN" Habawa sai wuri ya kaure da tafi da murna KDM yace "Da wannan nake gabatar muku da tauraron wannan rana Major General Zayyan Muhammad Tureta" Chanja kida akayi yazo ya haye stage din bayan ya yiwa dansa abim sonsa Emzee kallo daya tak yana tsaye ya kame sauran suna nan inda suke. KDM yace ko yana da abin fada ga dimbin 'yan Nigeria da suke wurin da masu kallo live a gida. "Thank you Nigeria you have given me 22years worth of love in a single night. Long live Nigeria, God bless my country" Wani hawayen Mairaman Zayyan ta fitar batare da ta sani ba. A nan tsaye aka barshi shugaban kasa ya taso zai bashi award. Hularsa ya cire ya mika masa hannu sai da Mr President ya bawa kowa mamaki domin bai karbi hannun ba sai rungumar Zayyan da yayi sannan ya karbi award din daga hannun Chief of Army Staff ya mika masa. Rahima babu inda take kallo sai Emzee da yake tsaye har lokacin a kame babu gajiyawa taji wata irin azababbiyar soyayyarsa tayi mata kamun in ba kai babu rayuwa. It was a moment da bazata taba mantawa ba a rayuwarta har abada. Bayan Zayyan ya zauna ne su Emzee sun koma mazauninsu Chief of army staff din da kansa ya gabatar da shirin Military Voice yace suna alfahari da wannan yunkuri na sanar da duniya sadaukarwar da sojoji da iyalansu suke yi. Sannan gashi sun sake ganin inda yake bukatar a duba domin tallafi ga wadanda suke cikin mawuyacin hali. Sake yin duhu wurin yayi sai ga Radhiya tana gabatar da shirin sannan aka nuna bangarori daban daban a ciki wanda ya janyo zubar hawayen mutane da dama a wurin. Iyayenta da mijinta were so proud haka ma 'yan uwa. MC KDM sai cewa yayi Radhiya ta fito tace wani abu game da shirin nan Ita da Arifah suma nasu shirin suka fara inda da sahalewar angwayen nasu suka amince a hada dinner a Abuja bayan kowacce anyi mata nata bikin na gida. Arifah a Jos za'ayi wasu events din bikin 'yar gwamna guda daya tilo ita kuma Radhiya sai da aka yi ta tunanin inda yafi dacewa karshe Mama tace ayi a Abuja amma yini a Sakkwato za'ayi kamar yadda za'ayiwa Arifah a Jos. Ranar kai amarya kowacce a daukota daga garin mahaifinta washegari suyi dinner dinsu. Daga nan kuma tsugunne bata kare ba domin Tante tana can Nijar da sauran 'yan uwa ana shirin bikin 'ya'yanta Yousuf da Radhiya saboda haka ana wannan dinner din can zasu wuce ayi sabon biki sannan amaren su tare. Dama kuma Tante din ta riga ta sanar dasu Ummi kada a dauko wata mai gyaran jiki zata taho da kawarta tun suna 'yan mata idan sun zo taron Zayyan zata barta a nan. Arifah daga Nijar zasu wuce France shi kuma Awwab ya riga yasa an fara nemawa Radhiya visar Germany can zai tafi da ita suyi sati biyu su dawo Nigeria. Tun yanzu kowa jiki ya fara fada masa saboda shirye shirye. Ana ta kai dinkunan biki na amarya , 'yan uwanta da iyaye. Zahra da Raji sun dawo daga Katsina sai hutu ya kara daga wurin aiki amma fa idan ya koma shekarar kaf bashi da hutu. Fauziyya itama sauki ya samu sun koma Katsina sai daurin auren Bilal zai taho da ita. SANNU SANNU BATA HANA ZUWA Saura kwana uku daurin auren Arifah hakan na nufi kwanaki hudu ya rage na Radhiya amma har yanzu Awwab bai dawo ba sai bata hakuri yake yi al'amura sun zo ba yadda yayi zato ba. Radhiya tun tana daurewa sai da tayi masa kuka da daddare akan bata fatan a daura auren baya nan. Hakuri ya bata domin wani training aka saka yake jagoranta. Ainihi bashi bane da tuni ma ya dawo gida sai matar wanda zaiyi ta haihu sati biyar kafin ainihin lokacin haihuwarta. Abu yazo da tangarda dole ya dauki hutu. Gashi daga shi sai Awwab ne suka yi wannan course din a Ukraine. Tunda sunsan aure zaiyi shine aka daga masa kafa zai taho ana gobe daurin auren Yousuf. Ga abu ya dame shi ga fushin Alheran dinsa sannan Mami da Daddy sun kira shi a lokuta mabambanta kowanne baisan dayan ya kira ba suna jaddada masa idan ya bari aka daura aure babu shi zai ga fushinsu. Ya gama shirinsa tsaf ranar da zai taho ana gobe daurin auren su Arifah yayi ta kiran Radhiya taki dauka tana ta kunkuni. Text yayi mata mai dauke da dadadan kalamai ya sanar da ita yana hanya zai sauka shadayan dare. Bata yi masa reply ba sai sai kowa ya ga sauyi da walwalarta da ta karu. Tante ta fadawa ya taho tace to maza ta tanadar masa abinci a kai gidan Mami. Yousuf da suka zo da sauran mutanen Nijar shi acan yayi masauki dakin Awwab tare da Raji. Gidan Major General Zayyan kuwa babu masaka tsinke saboda 'yan uwansa na Nijar iyaye su Alh Sidi da Alh Ghoumar. Alh Mousa dai da mijin Mammee da sauran tawagarsu hotel aka kama musu. 'Yan uwa ne aka taru ko ta ina. Emzee ma ya da safe ya iso sai dai gidan Mama ya wuce kai tsaye ga mamakinsa Halifa ma ya riga shi zuwa suna tare da Ibrahim. Sakin fuska yayi kamar babu komai a ransa ya rungumi dan uwansa sai dai har ransa yana jin babu dadi da kuma hangen me zai faru idan gaskiya tayi halinta. Sai bayan magariba Radhiya ta dora girkin da Tante tace tayiwa Awwab Emzee da Ibrahim suka zo dauka. Farar shinkafa ta dafa masa tayi shar da ita sai dai baifi minti biyu ya rage ta kwashe ba ta juye mata alayyahu madaidaici a ciki. Gyareshi tayi amma bata yayyanka ba a haka tayi amfani dashi bayan ta cire shi. Ba kuma tsigar nan ta ganye kawai ba, ta hada ne harda itacen inda yayi karfi da yawa kadai take yankewa. Yau dai tayi kamar na mutum biyar ne tunda tasan su Yousuf na gidan. Miyar kuwa farfesun kaza ne da ta barshi ya danyi kauri an yanka dankali amma da girmansa a ciki da caras shima da dan girma sai koren wake. Rahima, Zayyana da Hibbah suna makale wurin koyon girki tayi ta gama. Sai da ta dibar musu suka sama mata lafiya. Ibrahim ne ya fara zuwa kitchen din yace Zayyana tazo ta bashi labarin Khaleel. Radhiya da bata gano komai ba tace "ashe dai zatona ya zama gaske da nake tunanin ko saurayinta ne kusan kullum sai ya kirata sai ta gudu don kada muji me ake cewa" Kashewa Zayyana ido yayi da take ta jin kunya Hibbah da Rahima sun san komai shiru kawai suke yi "zan binciko mana shi Adda Amarya muna zuwa" Bai yarda ya fita ba sai da ya sakata a gaba. Rahima ce take ta yiwa Radhiya tambayoyi suna tsaye ita da Hibbah ita kuma tana wanke kwanukan da ta bata Emzee ya shigo. Bata ganshi ba sai alama ya yiwa Rahima da suyi shiru. Ido ya rufe mata ta baya sai dai jini baya buya tuni ta gano rabin jikinta ne Zayyan dan Zayyan. Rungume juna suka yi tana ihun murna don har ta fitar da ran zai zo saboda tasan tsananin makarantarsu. Ya wani kara budewa ya kereta tsaho sosai yana mata dariya ya dan duku kansa "ashe nayi missing dinki Addata yau gaskiya kwanan hira zamuyi kafin Hamma ya daukeki, na fasa bin Ibrahim ma" "Ka manta ko an daura ina gida har sati biyu?" "Eh to idan ya bani damar hirar kenan. Muje dakina kiga wani abu" Suna juyawa Hibba tace "Ya Emzee ina wuni" "Lafiya kalau mai tale baki number two" Dariya tayi za ta fita taji Rahima tayi mata wani irin riko tabi bayanta da sauri. Radhiya tayi saurin cewa Emzee ga Rahima tana dakatar da ita su gaisa. Haba Rahima idanu tuni sun raina fata ashe tunda ya shigo ta tabbatar shine sojan taji cikinta ya kulle saboda girmansa da ta gani. Sai yanzu ya kula da ita a zatonsa 'yar uwar Hibbah ce ko wata dai cikin bakin biki ya saki fuska zai amsa gaisuwar da tayi masa a tsorace suka hada ido. Wani irin yanayi ne da bai taba zato ko tsammani ba ya fizge shi a take a lokacin ya fadada murmushinsa gareta yanayin idanunta tamkar wani maganadisu ya zame masa. "Kinyi kama da matsorata, yaya sunanki?" Ya tambayeta a kasalance. Yawu ta hadiya tace "Rahima" "Rahima zaki zama kawar soja?" ya sami kansa da cewa babu wani tunani. Duka Radhiya ta kai masa a baya ganin idanun Rahiman sun kara girma duk ta firgice "kada ka tsorata min kanwa dama har yanzu bata sakewa idan Daada ya shigo." Tana ganin Radhiya ta dauke masa hankali ta fita da sauri ta riga Hibbah zuwa daki. Sai da ta rufe kofa ta soma sauke numfashi da sauri da sauri. Tunda take bata taba ji ko ganin wani abu da ya kwashe mata nutsuwa kamar wannan bawan Allah ba. Danganta abin tayi da tsoron sojoji da take yi ta kai hannunta kirji tana jin yadda zuciyarta ke bugawa. A kasa kuwa kafin su bar kitchen din Ibrahim ya shigo yana kiran Emzee dreban da zai dauko Awwab motar ta lalace a hanya Raji kuma da yake gida bai san gari ba shine Ummi tace suje su dauko shi. Shi dai Emzee so yayi ya zauna a kira masa yarinyar nan mai idanu bai gaji da kallonta ba. Da abincin da Radhiya tayi a motar suka je dauko shi. Ibrahim kasa hakuri yayi sai da yace masa yayi jiki saboda aikin nasa yafi yawa a zaune gashi babu inda yake zuwa daga gidan da ake basu kamar hostel idan baka da ra'ayin kama wani ko kana da naka sai office din nasu. Murmushi kawai yake yi yana jin kewar Radhiya amma dare yayi ana neman shabiyu gashi jirgin safe zasu bi zuwa Jos saboda karfe biyu ne auren kuma suna tare da ango. Wanka kawai yayi da sallah yaci abincin nan sosai tare dasu Raji suka kwanta a gajiye bayan ya tura mata text din godiya tunda taki daukar wayar tasa. Ya dena damuwa don ya ma fi son haduwarsu ta gaba da amsa sunan matar Awwab. Da safe kuwa ba a nutse suke ba anata shiri. Duka kayan da zasu saka na daurin auren a jaka suka saka su. Suka wuce airport mota mota sai Jos. Karfe biyu da 'yan mintuna bayan sallar azahar Major General Zayyan Tureta ya karbi sadakin Arifah daga hannun kanin Alh Mousa naira dubu dari da dalleliyar mota. Nan da nan jama'a suka shaida auren Yousuf da Arifa abinda wata uku da suka wuce ko sanin juna basuyi ba bare suyi tunanin wannan rana. His Excellency the Executive Governor of Plateau state Rtd Col. Nasiruddeen Aliyu ya tara jama'a sosai 'yan siyasa manya a wannan taro mai dumbin tarihi. Ansha hotuna a ranar biyar na yamma suka sake dagewa sai Birnin Shehu. Ga gajiya an dauko ga wata za'a sake dauka gobe. Hotel da wani guest inn Zayyan yasa yayunsa kama dakuna da dama saboda yayi mamakin jama'ar da suka zo wannan aure. Da wuri ya biya kudin masaukin saboda haka basu sami wata matsala ba. Mutanen Katsina gayya guda sai kayi mamaki kamar ba su bane masu cewa dole Awwab ya auri 'yar uwarsa don duka kakanin Awwab sunzo su ukun. Malamijo da 'ya'yansa maza kananun ne kadai babu amma ya dauko kowa ga kannensa suma motoci suka ciko da mijin Nene. Ga jama'a guda daga Nijar wadanda suka halarci auren Yousuf jiya. Daga Rugar Barkindo Ardo, Baffa Gide, Baffa Habubakari da su Zakari kusan kowa yazo shaida auren 'yar soja. Mutanen Tureta da su Alh Salisu da duk wanda ya kamata sun zo. Chibuzor dashi aka daura na Arifah kuma yau ma yana tare da babansa Zayyan shima zai shaida. Karfe goma na safe aka saka saboda masu komawa a ranar su iya tafiya. Kusan ma dai kowa juyawa zaiyi suna sa ran da an daura anci abinci a fara tafiya. Zuwa lokacin Zayyan ya ciko sosai don Mairamansa ba da wasa ta tasarma fito da mijin nata ba. A babban masallacin juma'ar unguwarsu da yake bakin titi za'a daura auren. Wata hadaddiyar mota ce ta tsaya a harabar masallacin sojoji suka yi dafifin kare shugabansu. Mutum uku ne suka fito daga motar wata shadda suka saka iri daya ruwan zuma mai dan karen tsada. Dinkinsu da komai hatta hula da takalmi basu bambanta ba. Suna fitowa aka fara daukarsu a hotuna tun kafin su karasa ciki. Uban gayya ne Major General Zayyanun dan mutan Sakkwato yana ta murmushi kamar shine angon. Har yau da yake shirin aurar da 'ya bai dena tafiya da hankulan mata ba. Daga gabansa rike da wata sanda mai kyau domin samun balance din jiki Daddy Rtd Major Mustapha ne mutumin Katsinan Dikko kunya gareku ba tsoro ba. Kamilin mutum msi tafiyar da komai cikin tsari da haiba. A bangaren damansa kuwa aminin kwarai ne wanda abotarsu ta zame musu 'yan uwantaka Rtd Lt Hadir gaisuwarsa daban take jinjina ga dan mutan Kanon Dabo mai dutsen Dala da Gwauron dutse, Kano ko da me kazo an fika. Hadir Murtala abokin da Zayyan Tureta wadanda sukayi zamani a matsayin zaratan jaruman samari kyawawa. Su ukun nan tarihin rayuwarsu abin duba ne domin kada duniya ta manta da soyayyarsu da sadaukarwa domin kasarsu domin abotarsu. Taku suke maza 'yan uwansu na waigensu domin sun isa a dube su din. Cikin masallacin suka shige ana ta gaisawa da 'yan uwa da abokan arziki. Daga waje mintuna kadan bayan shigewarsu wata motar ta iso Awwab ya fito rike da waya a hannunsa yana sanye da shadda fara kal wadda aka yiwa aiki da zare ruwan toka msi duhu. Hula da takalminsa kalarsu daya da zaren sai agogo da links din hannun rigar duka silver masu kyau. Saboda kurewar lokaci ranar da zai taho yayi aski saisaye aka yi masa wani irin gyaran fuska da ya fito da gajeren kwata miliyon dinsa. Matashi ne ajin farko mai tattare da nutsuwa da kamala. Kallo daya za ka yi masa kasan cewa yau din ta dabance a wurinsa ranar aurensa da Alheran dinsa. A gefensa angon jiya ne Yousuf bayansu kuma Emzee da Ibrahim sanye da wani ubansun yadi da Mama ta dinka musu. Su dinma kamar iyayensu daga sama wato hula har takalmi babu ta inda su ka bambanta komai. A tare dasu Halifa ne shima ya fito fiye da zato. A cikin masallacin kuwa wakilan ango da amarya aka nema Hadir da Zayyan su ka matso gaban limanin suka zauna a kusa dashi. Yadda yake a tsarin musulunci haka aka gabatar da komai inda Hadir waliyin amarya ya karbi sadakinta naira dubu dari daga hannun Zayyan waliyin ango. Addu'a aka yi aka shafa Captain Muhammad Awwab Mustapha ya zama mijin Alheran Radhiya Zayyan Tureta. Hamdala ya rinka yi babu tsayawa a lokacin da yaji kammaluwar komai Schatzi dinsa ta zama tasa halak malak. Hotuna ake ta yi da gaishe gaishe na 'yan uwa da abokan iyayensu. Malamijo da tawagarsa kadai sun isa gayya. Gidansu Zayyan aka wuce ya sakarwa 'yan uwansa da matansu Badaru ragamar girkin da za'a ciyar da mutane kafin su tafi. Da farko Mairama yaso su zo su kwana a garin domin yin abincin ita kuma tace dama ce ta nuna musu yana kaunarsu kuma ya yarda dasu. Ai kuwa basu bashi kunya ba domin kowa yaci ya sha anyi abu cikin girma. Kuma sai da Baban Arifah ya samu yazo shima duk da mutanen da ya baro a gida. Maikudi ne dai idan akwai namijin mujiya to shi ne a wannan taron. Yana ta rakubewa a gefe Zayyan sai ya dauke kansa kawai. Daga baya ya ga bai da amfani nunawa duniya akwai baraka tsakaninsu shiyasa ya koma sako shi cikin al'amuran. Da yace Maikudi kuwa sai ka ganshi da mugun sauri ya taho. Ba su suka sami saukin kebewa daga mutane ba sai lokacin da ya idar da sallar la'asar. Yana zaune da 'yar cikinsa ya ajiye babbar rigar da hula can gefe. Bayan doguwar addu'a ya dauko wayarsa ya turawa Radhiya text din da yake ta son yi tun bayan an daura auren. (Ina hukuncin matar da bata daukar wayar mijinta? Ki fada mata Awwab ya zama na Alheran kuma ta shirya karbar punishment dinta na share shi). Hira suke yi da Fauziyya da Zahra rabi suna tsokanarta rabi kuma shawarwari ne suke bata tunda yanzu itama girma yazo. Ita dai jiki yayi sanyi kamar ba ita ba. Wani abin tayi dariya wani kuwa sai dai taji kunya idan sun fada amma ta kasa magana. Duk da ba bikin bane ya taso amma gidan ya rude don ma anyi sa'ar kawowa Ummi masu aiki biyu 'yar dattijuwa da kuma mai sauran kuruciya. Sakon Awwab ta karanta suka ga murmushin nata ya koma na daban. Fauziyya ta dago wuya zata leka wayar "Ango ya miko gausuwa kenan...mu gani me yace" Janyota Zahra tayi "ina ruwanki, idan kin matsu kiji me yace nemi naki mijin tunda suna tare kema yayi miki text din. Radhiya tashi ki koma daki kiyi magana da mijinki kinji" Kasa mikewa tayi Fauziyya ta cigaba da zolayarta sai da Zahra tayi da gaske don ta kula jikin kanwar tasu mai sabon mukamin matar yaya yayi mugun sanyi. Tana tafiya Fauziyya ta tallabe kanta da hannu biyu. "Jikin ta kanwa yayi la'asar fa Sis. Duk surutunta kinga fa bakin ya mutu. Allah sarki irin matsoratan amaren nan za'ayi" "Tausayinta kike ji ko tsokana?" "Tausayin dai...hmmm kazo kayi ciki ka rasa inda za ka tsoma ranka kaji dadi" Tuntsirewa da dariya Zahra tayi ta gano Fauziyya laulayi ne yasa ta a gaba shine za ta saka mutane itama. Bayan Radhiya ta koma dakin babu kowa. Gefen da tayi sallah ta kalla ta tuna nasihar da Mama tayi mata a wurin bayan ta umarceta da tayi nafila ta godewa Allah bayan an daura auren. Wata irin soyayyar Awwab take ji tana kara shigarta sosai ta lumshe idanu ta kwanta sannan ta kira shi. Sautin numfashinsa ne ya sanar da ita ya dauka amma yaki yi mata magana shima nata hawa da saukar numfashin kadai yake sauraro wanda ya kara masa gudun bugawar zuciyarsa. Ita ta fara kartse shirun nasu ta hanyar gaishe shi da tattausar murya "Hammana ina wuni" Da kyar ya iya hada kuzarin amsawa yana jin kamar yau ya fara son ta "Matsoraciya yaya kike?" "Tsoron me nake yi?" "Daga kinji nace zaki karbi punishment shine kika dawo daga strike din yi min magana mana" Kamar yana gabanta ta tura baki "to ba kaine ba" Katseta yayi don yasan fushin har yanzu na menene "Ko ba ni zan aureki ba kinsan bazan yi missing aurenki ba bare kuma Alheran din ta Awwab ce" Kunya taji sosai yayi murmushi ganin yau ita ce babu baki "wai ni tun yanzu ina bakin naki ya koma ne? Anya zamu shirya da wannan amaryar kuwa wata bebeya nan da ita" Ibrahim ne yayi masa alama da hannu motocin da zasu kwashesu sun iso. Ba yadda ya iya sallama yayi mata yace tayi musu addu'a gasu nan fitowa zasu taho. Kafin su iso anyi abinci sosai jiran isowarsu kawai akeyi. Kowa yaci ya koshi kuwa sai son barka aure ya yi albarka sai fatan zaman lafiya ga sababbin ma'auratan. A gajiye su ka dawo ana sallar isha kowa sai bacci. Angwayen biyu, Raji da Bilal suna gidan Mami. Ibrahim da Emzee kuwa gidan Mama. Daya ga wata ta matso babu lokacin zama babban taron da ake ta jira ne Allah Ya kawo shi. A haka ma da ba su ne suka shirya ba basu da zama balle kuma na washegarin da yake nasu. Dadin abin ma kuma domin tallata shirin Radhiya Baban Arifah ya samu yace a saka wani bangare nashi a wurin taron tunda shugaban kasa zai je. Ita kuma sai ta gaggauta sanar da Supervisor dinta domin ta nema mata izini. Kwana biyu a tsakani matar ta fada mata cewa su uku an wakiltasu zuwa su gani sannan su tayata murnar dawowar mahaifinta. Ranar kwanan murna tayi sai gashi ana gobe taron sun iso. Duk wannan lokacin angon nata yayi wuyar gani suyi nan suyi can saboda ganin sun kammala komai bisa tsari yadda suke so. Malamijo da kansa ya hada mutum biyar cikin masu zuwa taron daga gidansa a yara sai kuma Yadikko da Hajjo. Shatar mota yayi musu ana shirin tafiya sai ga Salame niki niki da kaya ita da yaranta wai itama zata je. Ba wani abu bane ya tunzurota kuwa sai labarin da ta samu na cewa Rahima ashe ta bi Mairama. Zuwa zata yi har gidan taci mutumcin yarinyar tunda tana son nunawa makiyanta cewa bata isa ba. Abu na biyu kuma so take taje ta ganewa idanunta wace irin rayuwa Mairama da Zayyan suke yi da akaje daurin auren 'yarsu a Sakkwato aka dawo ana zuzuta taron da angon da Radhiya ta dace da shi. Malamijo bai hanata zuwa ba amma da karamar 'yarta kadai ya yarda taje sauran ya turasu cikin gidansa. Tunda aka shigo garin Abuja bakin Salame yaki rufuwa tana ta kalle kalle. A tasha dreban ya tsaya aka tura wani dreban daga gidan yaje ya taho dasu. Nan fa cikin Salame ya duri ruwa ganin sojoji da bindiga tun daga bakin gate din wani irin katon gida mai kyau. Jikinta yayi sanyi kalau ba ta fatan ace wannan ne gidan Mairama. Bata gama tunanin ba kuwa aka wangale gate din gidan. Wani bacin rai taji ya tuko ta da fa yanzu gidan nan nata ne ba don bakincikin da Mairama tayi mata ba. Suna shiga Ummi da kanta ta fito tarbarsu da murnarta tare da Rahima wadda tun safe da tace mata Malamijo yace da Salame za'a taho jikinta yayi sanyi. Ummi tana kula da duk motsin yarinyar kuzarinta ya ragu sai kayi mata magana bata ji ba saboda zulumi. Ashe kuwa ba a banza ba don suna saukowa daga mota da ta tafi da murnarta saboda tana son Umman nata taje ta durkusa har kasa tana gaisheta. Kusan hambareta Salame tayi kafin ta dangwara mata yarinyar da ta kai shekara uku tana wani irin wari. "Ki wuce da ita ki gyara mata jiki tayi kashi sannan ki bata abinci " Jiki na rawa Rahima ta karbi yarinyar da kafarta da komai amma dole ta dauketa ta wuce Ummi ta shiga ciki. Itama Ummin ba ta niyar koyawa Rahima rashin kunya dole ta bi umarnin mahaifiyarta. Sakin fuska tayi tana musu maraba. Salame tana ta wani basarwa ita bata ga abin burgewa ba har suka shiga ciki. Tun daga katon falon zaka san gida ne na wanda ya isa duniya take damawa dashi. Dakunan da zasu zauna ta nuna musu da kanta su Radhiya suka zo gaishesu ita da Zayyana da Hibbah wadda tayiwa gidansu kaura duk da cewa Maman tasu tana gari. Duj inda 'yan mata suka hadu sunfi jindadin kasancewa tare musamman idan tasu tazo daya. Rahima wanka ta shiga yiwa kanwarta Khadi yarinyar tana ta yi mata rashin kunya "Ki dena tabani" "Kin kona ni" "Sai na fadawa Umma" "Ni ki bani sabulun da kaina dan wanke" Radhiya tuni ta hasala ta fada bandakin tace Rahima ta fita ta karbo mata kaya. Wani irin kallo ta yiwa Khadi yarinya ta bare baki za tayi kuka ta daure fuska "kina yi min kuka zan cillaki ta taga kowa ya huta mara kunyar kawai" Yadda bata ga alamun wasa a fuskar Radhiya ba sai ta hadiya kukan dama na samun wuri ne tayi mata wanka kamar tayi amai ace yarinya kamar wannan tana kashi a wando ga wani kai a daddage babu gyara anyi kitson roba da yawa sun warware. Zuge sauran tayi ta zuba mata shampoo akan ta soma kukan sai ta fadawa Umma saboda bata yarda a taba mata kai ko Salamen sai tayi ta lallabata tunda tana ji da ita. Radhiya bata sake bi ta kan rarrashi ba sai da ta wanke kan nan tayi mata wankan. A kasa kuma Rahima dakin da suke taje a gaban Salame ta durkusa tace a bata kayan Khadi. "Kin wanke wadancan ko kuwa ni zaki kawowa na wanke?" "Yanzu zan wanke Umma" Hajjo tuni ta fara zuwa wuya a kufule tace "Salame idan kinsan zuwa kikayi ki tsangwami yarinyar nan ina mai tabbatar miki yanzu zan kira Malamijo a mayar dake gida. Shashancin banza da hofi kai. Rahima ga jakarta can bude ki dauka" Ummi tana wurin ita abin na Salame yanzu tausayi ne take bata saboda ta hana kanta sakewa ta hana wasu. Rahima da ta duba kayan ashe na babbar Salame ta dauko garin haushin an hanata zuwa da dukkansu. Rigunan sunyi girma haka dai ta dauki wata riga zata saka mata ga pants din duk na babbar. A kanta Salame ta huce haushin rashin dauko kayan daidai tana ta yi mata fada saboda bata san yadda zata yi ba. Ummi ta kada kai "Rahima anjima bayan magariba kizo na aikeki dasu Zayyana" "To Ummi" tace a sanyaye ta fita. Tana cikin hawa benen Emzee na saukowa a gurguje yake tafiya suka kusa karo tayi saurin matsawa gefe. Idanun nan nata ne suka sauka a kan fuskarsa wadda a take murmushi ya maye gurbin bacin ran da ya sauko dashi saboda ganin Salame da yayi a cikin tawagar 'yan Sumaila. "Kawar Soja daga ina?" "Ni dai ba kawarka bace" Murmushi yayi ya nade hannuwansa a kirgi ya tsare hanyar wucewarta "nima ba kawancen kawai nake so ba harda...." Da sauri ta dago gabanta na faduwa "harda me?" Kansa ya dukar daidai fuskarta "harda idanun Rahima...zan samu?" Rikicewa tayi ta samu ya dan matsa ta kwasa a guje yana ta cewa tayi a hankali kada ta fadi. Sai da ya ga ta bace masa ya dan rankwashi kansa "Muhammad Zayyan kalau kake kuwa?" Ya tambayi kansa don ya rasa yadda akayi idan ya ganta daga bugun zuciya sai kasa controlling kansa da bakinsa da yake yi. Kai ya girgiza ya sauka ya dauki mota ya fita. Bayan magariba kuwa Ummi ta bawa Zayyana dubu ashirin da biyar tunda ita ce babba tace dreba na jiransu su siyowa Khadi kayan sawa kuma kada su manta da takalmi, pants da brush. Sahad ya kaisu suka kwaso kayan da ya dace. Rahima tana da wata dubu daya cikin kudin da Ummi ta basu rannan suka siyo kayan kwalliya ta sayawa Khadi packet din ribbons na dari shida za ta yi mata kitso sai ta saka mata. Gida suka wuce da murnarta bayan sun nunawa Ummi tasa musu albarka ta wuce ta kaiwa Salame. Ba karamin dadi Salame taji ba don bata da komai sai dari uku amma dayake ta saka hassada da kyashi a zuci sai ta kyabe baki. "Ki fada mata ina komawa gida zan turo mata kudinta don nafi karfin cin arzikinta yanzu ma don na manto jakar ne kuma a ciki kudina yake" Tashi Rahima tayi zata fita Salamen ta kuma kiranta "ina kuma zaki je? dawo nan ki kwanta kusa dani" To ai ko numfashin kirki bazata iya ba bare bacci a gabanta a tsorace take sosai Yadikko ta kama hannunta ta kaita bakin kofa ta ce ta wuce wurin yayarta Radhiya ta rufo kofar. Tana dawowa tasa hannu ta dauke Salame da wani gigitaccen mari. A kidime ta dago kai ga kannenta don ma Khadi tayi bacci. Hajjo tace tayi mata daidai. Rai a bace sosai Yadikko ta nunata da yatsa "ba ni na haifeki ba Salame amma ina tsammanin rikon da nayi miki ya bani matsayin uwar da ta isa dake. Nayi miki rantsuwa daga yau har mu tafi idan kika sake yin wani abu domin cusgunawa Mairama ko Rahima sau naci mutumcinki la'ada waje. Mutuminyar banza wadda bakinciki ya yiwa tsatsa a zuci." "Shiyasa taki gaba taki baya babu wani cigaba a rayuwarki" Hajjo ta kara da nata. Sunyi mata tatas don sai da tayi hawaye Yadikko ta kyaleta tana jin zafin wannan mummunar halayya ta Salame yarinyar da a da can tafi kowa shiru shiru a gidansu ashe macijin sari ka noke ce. Da rana Ummi ta bawa Yadikko katinsu na shiga wurin taron haka ma ta baiwa Tante wanda zata bawa nasu mutanen. To dayake dama da yawansu sun zo ne akan ainihin na gidan ba wannan ba da gwamnati ko muce sojoji suka shirya ba sai ba'a sami rikici ba. Katin ba yawa garesu ba kuma dai bazasu so suje su bawa kansu kunya ba. An gama hada masu tafiya su Mami suna gidan Emzee tun safe da yasa kafa ya fita basu sake ganinsa ba. Kafin sallar magariba sai ga Arifah da Mom dinta da gudu suka rungume juma ita da kanwarta Radhiya. Matar Alh Salisu itama ta iso aka fara shirin fita domin karfe takwas za'a fara taron. Sai da Ummi ta shirya mijinta bayan kyakkyawar kulawar da ya samu tamkar kada ya tashi saboda yadda yake jin matar tasa a rai. Sababbin kayansa da suka dace da mukaminsa ta taimaka masa ya saka ta saka masa sabuwar farar safa da bakin takalminsa tafiyayye cover shoe. Ya sake gyara fuska sai wani annuri yake fitarwa. Sai da ta kammala dashi sannan ta fita itama ta shirya don tare zasu tafi. Lace ne ta saka army green da digon gold a jiki. Mai kwalliya Mama ta dauko amma aka ce tayi mata matured kwalliya ba mai cika fuska ba kamar karamar yarinya. Tayi kyau matuka ta fito a Mairama Fillon Zayyan babu wata makusa sai hassadar makiya. Mayafinta gold ne sai takalmi heel da wata karamar dinner pause itama gold ga farin gilashinta ya sake fito da kyakkyawar fuskarta, hannuwa da kafafu sun sha jan lalle mai kyau da tasa 'yarta Rahima tayi mata. Matan manya ne suka fito ita da Mami, Mama, Tante, Mom din Arifah da Matar Alh Salisu. Fita suka yi kowacce ta shiga motar mijinta abin gwanin ban sha'awa sojoji na mara musu baya. Mutum biyu aka kara daga Nijar sai kuma Mubaraka yayar Zayyan da matar Badaru. Yadikko kuma ta bawa Salame, Ayuba da Bature kati don Laila ita dama tuni Ummi ta bata nata tana tare dasu Radhiya ana ta shiri. Kowa ya gama nasa shirin suka fito Radhiya ta saka wata abaya mai masifar kyau da daukar ido ja da bakaken stones. Covershoe mai madauri ta saka baki sai purse da ta saka wayarta da hoda. Duka dama abayar suka zabi sakawa sai dai kowa tata daban. Ummi ta fito da 'yarya Rahima don itama ta saya mata wata baka mai duwatsu pink. Idan kaga matan sai ka juya ka kara babu wadda bata yi kyau ba. Jawad da Femi a gida aka barsu saboda taron babu yara suka fito aka shiga motocin da suke jiransu. Mazan ma ba'a barsu a baya ba sun hade duka cikin suits kamshi na dukan kamshi su ma suna gamawa sai Nicon Hilton inda za'ayi taron a wani babban dakin taro da yake cikin hotel din. Decoration din wurin komai green ne da white an kawata shi fiye da zato ga ma'aikata a tsaye suna jira a shigo su nunawa kowa seat dinsa saboda akwai number a jiki. Awwab da Yousuf a matse suke da ganin amarensu abin takaici number din seat dinsu ya nesanta su da juna. Radhiya wata faduwar gaba taji da suka hada ido yana zaune kusa da Yousuf rike da waya a hannu. Ya hade cikin three piece armani suit khaki color da coffee coloured necktie ga brown din cover shoe. Daga inda yake a zaune ya daga wayarsa ya dauketa a hoto ta sadda kanta kasa a kunyace su Zahra suna mata dariya. Bayan an zazzauna kamar minti goma MC KDM sunan mai gabatar da taron wanda baya zuwa kowane irin taro dama sai na manya yace kowa ya tashi shugaban kasa zai shigo da first lady. Wurin zamansu daban aka zauna bayan national anthem da akayi. Ummi duk ta damu ina Karami sai da Zayyan yace ta kwantar da hankalinta dan nata yana nan za ta ganshi. An shiga taro ka in da na in hankula suka karkata suka koma ga MC da abubuwan da ake gabatarwa. Salame kallo daya ta yiwa Zayyan bata kara ba domin zuciyarta sai da tayi barazanar ballo mata kirji kuma abin takaici ga Alh Salisu a gefe sai taji duk ta muzanta a cikin mutane saboda kayan da ta saka na taron gidan Malamijo ne ganin kanta tayi wata koma baya a cikinsu. Duhu hall din yayi a take hasken screen da za'a gabatar da tarihin Zayyan ya mamaye wurin. An fara da nuna hotunansa yana matakin farko a soja sai dariyar manyan baki kake ji kadan kadan saboda daga hoton kadai zaka iya gane cewa Zayyan Tureta ba karamin fitinanne bane. A hankali aka zo kan aurensa duka ana nunawa ne KDM yana bayani. An tsayar da hoton akan shi da Daddy da Baba Hadir ranar tafiyarsu Liberia. Daga nan ya cigaba da narrating rayuwar da Zayyan yayi sai da gwamnoni biyu suka zubar da hawaye musamman da aka zo video din fitowarsa daga motar da ta kaishi Nigerian Embassy lokacin da ya hadu da Excellency da Awwab. Su Ummi sai hawaye yasa hannu ya rike nata a hankali tace "I love you Sojana" "I love you too Fillo" ya maida mata iya jin kunnenta. An kare video din da wani hotonsa ne shi da Ummi, Radhiya da Emzee a falon gidansa bayan sun koma. Fitilu aka kunna mutane sai sharbar hawayen jin labarin al'ajabi na wannan soja. MC yace kowa ya shirya domin ganin wasan da sojoji suka shirya domin murnar dawowar jan gwarzo jarumin jarumai. Wata murya suka ji inda mai ita yake commanding Cadets 'yan uwansa da kowa ya shiga layi. Tsit hall din yayi kamar ruwa ya cinyesu lokacin da aka saka wani kida irin na band din sojoji sai gasu nan sun fito mutum arba'in cikon na arba'in da dayan shine commander din wannan parade din wato Cadet Muhammad Zayyan Tureta. Sun sha training ba na wasa ba daga shi har sauran shiyasa babu kuskure ko na motsi daga garesu. Bindiga ce a hannunsu duk da ba harbi zasu yi ba suka yi wani wasa da ita da ya burge kowa a wurin. Komai nasu tare kidan yana chanjawa da umarnin Emzee. Karshe mutane suka ga wadanda suka gama parade din sun matsa Emzee ya sake bada umarni sai ga wasu suna fitowa cikin tsari suka shiga sahu suka yi wani layi layi sai da suka durkusa kowa ya gane sun rubuta Nigeria ne ai kuwa mutane a tare suka karanta "NIGERIA" Wasu suka fito a bayansu suma suka dunkule a kasa aka sake karantawa. "WELCOMES" Sai na karshen suma cikin gwaninta suka yi nasu layin tare da durkusawa. "ZAYYAN" Habawa sai wuri ya kaure da tafi da murna KDM yace "Da wannan nake gabatar muku da tauraron wannan rana Major General Zayyan Muhammad Tureta" Chanja kida akayi yazo ya haye stage din bayan ya yiwa dansa abim sonsa Emzee kallo daya tak yana tsaye ya kame sauran suna nan inda suke. KDM yace ko yana da abin fada ga dimbin 'yan Nigeria da suke wurin da masu kallo live a gida. "Thank you Nigeria you have given me 22years worth of love in a single night. Long live Nigeria, God bless my country" Wani hawayen Mairaman Zayyan ta fitar batare da ta sani ba. A nan tsaye aka barshi shugaban kasa ya taso zai bashi award. Hularsa ya cire ya mika masa hannu sai da Mr President ya bawa kowa mamaki domin bai karbi hannun ba sai rungumar Zayyan da yayi sannan ya karbi award din daga hannun Chief of Army Staff ya mika masa. Rahima babu inda take kallo sai Emzee da yake tsaye har lokacin a kame babu gajiyawa taji wata irin azababbiyar soyayyarsa tayi mata kamun in ba kai babu rayuwa. It was a moment da bazata taba mantawa ba a rayuwarta har abada. Bayan Zayyan ya zauna ne su Emzee sun koma mazauninsu Chief of army staff din da kansa ya gabatar da shirin Military Voice yace suna alfahari da wannan yunkuri na sanar da duniya sadaukarwar da sojoji da iyalansu suke yi. Sannan gashi sun sake ganin inda yake bukatar a duba domin tallafi ga wadanda suke cikin mawuyacin hali. Sake yin duhu wurin yayi sai ga Radhiya tana gabatar da shirin sannan aka nuna bangarori daban daban a ciki wanda ya janyo zubar hawayen mutane da dama a wurin. Iyayenta da mijinta were so proud haka ma 'yan uwa. MC KDM sai cewa yayi Radhiya ta fito tace wani abu game da shirin nan nata. Dif tayi kamar ruwa ya cinyeta ta kasa motsi.. Dif tayi kamar ruwa ya cinyeta ta kasa motsi. 💕[11/2, 7:24 AM] 👸🏽MAMIN SADIQ 👸🏽: 54.💕 Sake kiranta akayi taji cikinta yayi wata irin murdawa. Ina ita ina yin magana kuma wai gaban wadannan mutane harda shugaban kasa, gwamnoni, sanatoci da 'yan majalisu. Kan Awwab taji a daidai kunnenta saboda kamshin turarensa ta gane shine cikin rada yace. "Get up baby" taji tsigar jikinta ta tashi. A sanyaye ta mike ya rike hannunta suna tafiya cikin burgewa ana daukarsu hotuna sai da ya kaita bakin steps din da zata hau ya tsaya yace mata "go on zan jira ki". Har ta haye yana jin taushi da dumin hannunta a cikin tafin hannunsa. Tsayuwa ta gyara ta kalli iyayenta taji wani kwarin gwiwa ta soma magana a nutse. Ta yabawa sojoji akan rayuwar da ba kowa yake da zuciyar yinta ba ta kara da rokon a dube su domin sun cancanci kulawar al'ummar da suke yiwa bauta. "Soja shi kadai ne yake mayar da kowane dan kasarsa dan uwansa a lokacin tashin hankali. Kowa zaiyi kokarin ceton nasa amma soja zai tsaya ya kai ceto ga wanda kila har ya gama taimakon ko kwakkwaran kallo bazai sami damar yi masa ba bare ace akwai wata alaka. Soja babu ruwansa da bambancin al'ada ko addini. Yare daya yake fahimta shine SAVE, HELP AND PROTECT EVERYONE." Daada ta kalla tace "Ina rokon afuwar babban bakonmu domin zan saci kalmominsa long live Nigeria, God bless my country" Haka aka rinka tafawa Radhiya sai da tazo step din karshe Awwab ya mika mata hannu ta rike ya kaita har gaban seat dinta sannan ya koma ya zauna. Taro ya burge matuka Zayyan ya sami alkhairi fiye da zato da tsammani. Supervisor din Radhiya tazo ta rungumeta su ma sunji dadi domin kuwa a take wani da minister of information ya tura musu ya bukaci su cigaba da bata duk wani training da zai taimaka mata domin su tababbatar da bunkasar wannan shiri. Sun fito tafiya Arifah tayi gefe ashe mukullin motarta zata karba da tasa dreba ya kawo mata. Yousuf yazo ya shige ya zauna bayan ya radawa Awwab cewa gida kawai zai rakata sai ya dawo. "Kuma an fada maka zan yarda da wannan zancen ne" yace yana dariya. Yousuf ya rage murya yana dariya shima "ni dai ko yaya sai na tabbatarwa Arifah ni mijinta ne yau...kada ka rufe min kofa rakiya ce kawai zanyi" Kusan kowa ya fito ana ta shiga mota. Awwab na kallon Radhiya ta shige motar da suka zo. Wadda ya tuko ya shiga kai tsaye gidan Daada yabi bayansu Bilal yana tambayarsa ina zasu je kuma yace "rakiya zanyi na dawo". Daga bakin gate ya cillawa Bilal key din motar yace shima kada a rufe masa kofa sai ya dawo. Raji dariya kamar me sun dago angwayen hakurinsu ya kare ne. To su din ma ciki suka shige kowanne ya kira matarsa. Tana hawa bene a gajiye taji wayar Awwab saboda kidansa daban ne. Da sauri ta dauka ga kuma kunyarsa da take ji. "Kina ina?" "Yanzu muka shigo gida" "Yunwa nake ji Schatzi" taji yace harda marairaicewa. "Ka karasa gida ne?" "Na biyo matata ta bani" Saukowa tayi da sauri tana fita suna karo ya riko hannunta ya ja ta gefe sai da ya gama dube dubensa ya turata wani karamin falo wanda kujeru ne kadai a ciki sai tutar Nigeria a tsaye. Faduwa gabanta yayi da ya tura kofar da kafarsa ya rinka taku a hankali zuwa gabanta. Kasa dago kai tayi sai dai ba shiri ta daga din sakamakon daukan da Awwab yayi mata. Dagota yayi ta hanyar saka hannuwa daga kasanta yayi sama da ita dole ta saka hannuwanta ta riko wuyansa domin kada ta fadi. Idanunsu cikin na juna ya soma juyi da ita yana dariya itama sai da tayi saboda yadda yake yi mata. "Nice to meet you Mrs Awwab" yace lokacin da ya direta a gabansa. Kunyar ce ta motsa saboda yadda ya tsareta da idanu ta kasa magana sai ma juyawa da taso yi ta fita. Hannunta kawai ya janyo ta fado jikinsa ya rungumeta sosai. A tare suke sauke numfashi da ajiyar zuciya yau burinsu ya cika. Kanta yana kirjinsa ya saka hannuwa a bayanta ita kuma nata suna ta wurin cikinsa ya soma magana cikin wani irin salo da shaukin soyayya. "Alheran don Allah kada mu taba bari fushi ko wata zugar mutane su shiga tsakaninmu. Nasan ni dake are not perfect but we complete each other. Kece zabin Awwab tun kin baby har ranar da zai dena numfashi in sha Allah" Kalamansa sun kara masa matsayi da kima a idanunta. Batare da ta dago kanta ba ta yi magana don tsokana "har lokacin da aka yi min aski?" Murmushi yayi "tashinki daga baccin nan da kallon da kika yi min shine lokacin da Awwab ya fara yiwa Alheran soyayyar da yake fatan ta kare a aure" Murmushin da tayi ne ya janyo shigewar dimple dinta ciki sosai. Abinda Awwab ya dade yana jiran damar yi sai ji tayi ya dora lips dinsa a wurin yayi kissing dinta. Kunya har sai da taji cikinta yana wata irin yamutsewa shi kuwa bai tsaya ba sai pin din da tayi rolling dashi yabi ya zaresu ya zame mayafin. Kansa ya kai gaban goshinta yana shafa gashinta da yake kulle cikin ribbon tayi packing dinsa a tsakiyar kanta ya kuma bata wani kiss din. Da wata irin murya yace "rufe idanunki" Ki tayi sai dai suna hada ido ta runtse nata da sauri saboda bata da kuzarin cigaba da kallon idanunsa. Tana ji yana dan motsi amma bata bude ba taji ya saka hannu ya zame mata ribbon ya cusa yatsunsa cikin gashinta ya sake matso da ita. Bakinsa ya hade da nata a nutse ya jefa mata sweet din bakinsa irin wadda suka taba sha a soron Malamijo. Bata san lokacin da ta bude idanuwanta ba saboda ta gane dandanon alawar. A haka suka sha ta kusa rabi sannan ya bar mata a bakinta ya sake janyota jikinsa. "Ina jindadi idan muna sharing abu...nafi son ko me naci babyna ma taci. I hope daga yau haka zamu koma yi...it is better than daya ya ragewa daya" Duk da bakon yanayin da take ji sai da ta tsokane shi "harda abinci ko?" "Ewww ke fa kazama ce" yana bata fuska da tunanin a tauna abinci daga baki. Dariya tasa "kaga tuwo zaiyi dadi...." "Fita, fita ki tafi dirty girl" yace yana nuna mata kofa tare da dora mata mayafinta a ka. Turjewa tayi "nama fa?" "Out" ya kuma cewa yana bata fuska ya dago hannu ya biyota ta kara gaba da sauri. Tana bude kofar ya janyota ya rungumeta ta baya kansa na kafadarta "babu abinda zai fito daga bakinki na kyamace shi Schatzi. Idan kin ga dama har kunu musha a haka" Ita ya bari da bata fuska "shhhh please Hammana dena fada" "Ko kosai shima zaiyi dadi" Yatsunta tasa ta toshe kunnuwanta ya sake matseta "juyo kiji last one din" Kafada ta noke ya juyo da ita da kansa "I love yo baby" A hankali ta dago kai ta kalle shi idanunta sun kara girma da haske tace "I love you Chèri" tare da shammatarsa ta fice da sauri. 💕[11/2, 7:24 AM] 55💕 . A bangaren Yousuf da Arifah kwatancen hanya ta rinka yi masa a kunyace har su ka iso titin da zai sada su da gidan inda daga nan ya gane hanya. Ciki ya shiga tunda masu gadin sun gane motarta kuma tana ciki. Duk ta daburce saboda auren nasu yazo da wuri basu gama sabo sosai dashi ba. Ya san da hakan shima shiyasa yake kokarin dinki duk wata kofa kafin su fara rayuwar auren sosai. "A love yanzu yaya zaki yi dani?" Fasa bude kofar tayi ta waigo kadan "me ya faru?" "Kin taho dani gashi bansan hanyar komawa ba kuma bani da ko cent a jikina da zan nemi taxi. Ga dare..." yace da wani irin yanayin da zaisa a tausaya masa. "Kaine fa kace zaka rakoni in karbi motar. Yanzu yaya kake so ayi?" Kwantar da kansa yayi baya ya jingina da kujerar yana kallonta "Nima ki rakani" "Yanzu su Mom zasu dawo ace ina naje?" Bude bangaren shi ta ga zaiyi cikin yanayin ko in kula yace "tunda haka ne muje kawai na kwana a dakinki kinga gobe sai mu shirya daga nan mu tafi zaifi sauki" Idanu ta zaro tana kada hannu "wasa kake yi amma" "Gadon naki karami ne? To ba sai ki kwanta a kasa ba ni ki bani gadon tunda nine bako" Dariya ya bata ma yadda yake maganar tace "rufa min asiri...ko za ka kira Yayana yazo ya daukeka?" "Ni bazan shiga rayuwar kanwata in hanata samun kulawa daga mijinta ba" "Hmm Y love rigima kake ji naga alama" "Ko daya" yace yana kamo hannunta ya rike yana murza yatsun. "To ka dauki motar ka tafi da ita" "In bata a hanya gobe ace ba'a ganni ba...naki" "Bari na nemi dreba ya mayar da kai" Bata rai yayi "bana so" "Ya zamuyi to?" Tace tana tura baki don tsoronta daya kada iyayenta su dawo a gansu sai ace bata da kunya musamman Mom dinta. Bata san yaya akayi ba ya janyota rabin jikinta a cinyarsa ya rungumeta sosai yana shakar kamshin jikinta mai dadi. Kansa yana gefen wuyanta sai numfashinsa kawai take ji yace. "Mhmmm mon amour" yana jin kamar su kwana a haka "...inata baki haske, inata baki haske kinki ganewa." Yadda hausar tasa ke fita da abinda yace ne ya sakata dariyar dole "kana ta bani haske..." "Eh mana amma baki gane ba....kowane ango yana tare da matarsa ni tawa tana nuna min halin hausawan Nigeria" "Ban dau haske bane" tace a hankali tana kokarin zamewa sai gashi tar an hasko wata torchlight mai mugun haske sosai cikin motar ta barin da yake. Arifah gabadaya ta gigice don kunya ta fasa guduwa sai ma kara kankame shi da tayi a kunyace bata son ko waye a tsaye ya ganta a haka. Yusouf kuwa ko a jikinsa sai ma sauke glass da yayi rabi har lokacin tana cikin jiikinsa. Security din yace da pidgin english "na Madam i dey find I never see her comot from the car" Ko kalma daya bai fahimta ba sai ma kullewa da kansa yayi yace "pardon?" Sai kuma kawai ya dan taba kafadarta "Ba fa na jin yaren nan ki kore shi kafin nayi masa ido daya na ganin matata" Yadda yake bata rai ma abin dariya ne. Haka ta daure ta dago kanta kadan "Oga Sunday I dey come" "No wahala" mutumin yace tunda ya tabbatar tana nan ya juya abinsa. Kokarin tashi daga jikinsa ta soma yi "Y love bari na hadaka da driver please" Sake riketa yayi ta kasa motsawa "ke kuwa ki dau haske mana A love, biyoki nayi fa don mu taya juna murnar aure" Duk wasu dabarunsa ta gama ganewa. Ko Radhiya kanwarta ai tasan ta wuce ayi mata wannan wayon bare ita. Wace murnar aure zata yi a kofar gida. Hannunta ta mika masa na dama ya riko da nasa ta dan daga hannun sama da kasa tana jinjinawa "congratulations on your...." "Rike kayarki tunda baki daukar haske ga abinda nake nufi" yace yana kai mata wani irin kiss da ya hanata motsawa. Dirin motocin da suka ji daga waje ne ya tayar musu da hankali su duka ta tashi daga jikinsa da sauri. "Yanzu ya zamuyi?" Tashin hankali karara a fuskarsa yace "nima ban sani ba, ba gidanku bane" A tsorace take amma dole tayi dariya don ya fita rikicewa. Shiyasa yaso ta dau haske tun dazu ya samu ya gudu saboda Yousuf mutum ne mai kunya sosai. Ko lokacin da yaso Radhiya wannan kunyar ita tayi ta cutarsa ya kasa fada da wuri ashe rabon Arifah Nasiruddeen ne. Saurin kiran Awwab yayi yace yazo ya dauke shi su tafi. *********** Bayan fitar Radhiya daga falon da sauri ya biyo bayanta amma bai ga alamunta ba. Da gudu ta shiga cikin gidan tana ji kamar za'a gane me tayi. Awwab zai kirata kenan don shi bai ki yau ya kwana a gidan ba Yousuf ya kira. "Ni gaskiya bazan zo ba rakiyar taka tayi kadan ni kuma yanzu na fara" yace masa yana dariya. Yousuf ya kalli motocin su Baban Arifa "Kada muyi haka mana Awwab ni da na baka kanwata ya kamata ka kyautata min" "Ni ba kanwar na baka ba" Daga murya Yousuf yayi amma kana ji kasan kawai damuwa ce "kada kasa na dage bikin nan sai ta gama ècole" "Daidai kenan, sai ayi bikin da baby dinmu mu shiga gida mu uku ko hudu" bai san me ya dami Yousuf din ba amma dadin tsokanarsa yake ji yana dariya lokacin da Raji da Bilal suka fito kowa da murmushi saman fuskokinsu. "A love kiyi masa magana" Yousuf yace da Arifa kamar yayi kuka. Tana karbar wayar ta soma magiya don tana iya hango kallon da Mom dinta take sakar mata bayan ta fito daga mota. Yousuf sai ji yayi wani gumi na neman saukar masa duk sanyin garin. Tare da Arifah suka matsa wurinsu suna musu barka da dawowa. "Yousuf ba dai sawa tayi ka kawota ba ka biye mata kai kuma?" Cewar Mom tana musu kallon daidai. Awwab na jin muryarta da hannu yayiwa su Raji alama suka shige mota yaja suna dariya yau sun sami abin tsokanarsa. Rakiyar yau bata yi ba sai dai ko gobe a sake. Yousuf yace da Mom "na ga ta karbi motar ne ga dare. Su Awwab nake jira zamu tafi suna hanya" "To babu damuwa bari na wuce" Excellency da mutanensa yayi gefe suna magana yana yiwa ango da amarya murmushi yace su shiga ciki kafin Awwab din ya karaso. A ransa kuwa dariyar yadda Mom sarkin takura ta ritsa su yake yi. Tunda anyi aure ba shikenan ba, ko don tayi sa'a ba sai da safe ya dawo mata da 'yarta ba. A cikin gidan ma kamar yana kan kaya hankalinsa bai kwanta ba saboda hawa da saukar da Mom ta rinka yi sai da Awwab ya kira shi. Da sauri ya fita daga gidan yana sauke ajiyar zuciya. Kai daren ranar kamar yayi ihu saboda yadda su Awwab suka saka shi a gaba da tsokana. Mami tana jiyo hayaniya daga dakin Awwab inda suke kwana kamar wasu yara. "Irin haka basarwa ake yi Yousuf" Awwab yace yana mike bayansa akan gado saboda gajiya. "Zan rama duk kuyi ku gama. Kuma matsa min na kwanta yau nan nake so." Ture Awwab yayi tsakiya dariya ta hana shi tabuka komai har Yousuf din ya kwanta a wurin mutum biyu don da gangan ya bude hannuwa wai baya son takura. ********** Fauziyya da Zahra sun riga Radhiya shiga daki. Rahima da Zayyana wani dakin suke kwana a kasa yanzu saboda yayyensu dake saman a dakin Radhiya ga yara biyu. Yadda take sauke numfashi Zahra ta tambayeta ko gudu tayi ta gyada kai. "To dai mutum ya girma guje guje ba naki bane amaryarmu" Zahran tace mata. "Kyaleta fa tayi abinta nan da sati biyu ko da kudi nasan da wuya ta iya daga kafa" "Me zaisa Adda Fauzi?" Radhiya tace da iyaka gaskiyarta. Zahra tace "Kyale wannan yayar taki kin santa sarai da tsokana" Tawul ta dauko za ta cire kayanta ta shiga wanka Fauziyya ta fara yi mata kallon mara gaskiya saboda a takure take wanda ba halin ta bane. "Amaryar Hamma kada kice min janbakin nan ya goge...gaskiya ina jin ba mai kyan kika saya ba. Ni fa shiyasa abu designer bai dameni ba, ance baya fita da wuri sai an goge shi amma ke lips dinki kamar baki shafa komai ba. Kalli ki gani" ta juya tana nunawa Zahra da tsokana. Radhiya ta rasa yadda zata yi sauran abinda basu gane ba ma sun gane don ba karamar kunya taji ba, shikenan Hammanta ya janyo mata. Turo baki tayi kamar za ta yi musu kuka "to ba...ba...uhmmm tissue na saka na goge" Fauziyya ta saki fuska "ohhh irin makeup remover dinnan ko? Please nima bani nagoge don ni sanyi nake ji bazan iya wanka ba" "Fauziyya ki kiyayeni ko in kira Ya Bilal yazo ya kwashe mana ke kowa ya huta. Mutum yana fama da kansa amma baki baya shiru" cewar Zahra amma daga ita har Fauziyyan dariyar tsokana suke yiwa Radhiya. Yau mai balotelli an dinke mata baki. Cikin dariya Fauziyya tace "wai ma in tambayeki, makeup remover din baya goge fuska iyakarsa baki kawai?" Sai yanzu Radhiya ta fahimci ina suka dosa da wannan tambayar da dariyar. Aka yiwa wani ma ta rama bare an shiga gonarta. 'Yar dariya tayi tana sunkuyar da kai tace "sauran yana bakin Hammana shi ya goge min" Idanu Fauziyya ta zaro Zahra kuwa dariya harda rike ciki. Suna son juna idan an hado kamar kar a rabu saboda irin wannan dramar. "Kika bashi ya shanye?" Fauziyya tace fuskarta kadai sai tasa mutum dariya. Radhiya ta gimtse dariyarta ta zauna kan gado ta dora kafa daya kan daya tana daukar wayarta. Sunan da ta saka masa Mon Chèri (my sweetheart) ta nemo tana nunawa Fauziyya "In kira shi ki tabbatar?" "Zahra ki fadawa su Mama tun wuri kada gobe labari ya wuce goge lipstick a bashi matarsa" "Ba tambayata kika yi ba Adda Fauzinmu" tace da shakiyanci. "Ah to matambayi baya bata gashi nan an dora ki akan hanya yadda zaki gane" cewar Zahra har lokacin dariya take yi sosai ita da Radhiya. Katse dariyar suka yi a dole da suka ji ance "Schatzi" daga cikin wayar hannunta. Su duka ukun suka kalli wayar harda ita da ta kira bata sani ba kafin suka fice daga dakin a guje suna dariya sai ka rantse yara ne masu kananun shekaru. Awwab da yaji shiru sai ya kashe wayar yana tunanin kila bata san ta kira ba saboda dare yayi. Da suka koma dakin ma suna kallon juna sai su kwashe da dariya Fauziyya na cewa dadin abin itama an goge mata nata janbakin yau da tayi kwanan tausayin kanta. Komai nasu abin sha'awa musamman wannan hadin kan da ya samo asali daga jajircewar iyayensu. ********** Washegari wuraren shadaya na safe a can gefe guda na katon falon gidan Zahra ce da kannen nata Fauziyya da Radhiya Rahima tana yi musu lalle iya yatsun hannu kawai banda kafa. Su na cikin yi Mami da Mama suka shigo Zayyana da tun daren jiya aka yi mata nata ta tashi da sauri tayi bakin kofa za ta karbi DK ta ga baya hannun Mama ko Mami. Baki ta tura tana leka waje "Mama ina DK?" Mami ta daure fuska tace "Meye haka babu gaisuwa ni matsa ki ban wuri yana wurin Ibrahim a mota" Murmushi tayi kafin ta matsa tana gaishesu. Mama tace taje ta karbo shi kunya take tana ganin idan ta fita kowa zai gane meye tsakaninsu. Ganin Hibbah ta taso zata karbo shi yasa ta fita da sauri. Hibbah tayi dan murmushi suna hada ido da Rahima. Fauziyya ta hararesu "gulmammu ko dai ku fasa mana kwan nan ko yau na danneku a daki ayi muku balotelli ko ya kike gani babbar yaya" ta kalli Radhiya. Dariyarsu kadai ta isa tona asiri amma Zahra tace "ku bari ta dawo mu sakata a daki ta fada ko yau ayi taro tana gida" Hibbah da Rahima dai sai dariya Fauziyya tace su din ma duk sai ta binciko nasu tunda Radhiya ta kauce su ne next. Wata irin tafiya Zayyana ta rinka yi kamar bazata isa wurin motar ba saboda irin kallon da Ibrahim yake yi mata. Tana zuwa ya fito da DK a hannu yana murmushi. "Kawo shi" tace tana mika hannu. Kara makale shi yayi a jikinsa yana harararta "dama ba wurina kika zo ba?" "Ni kanina nazo dauka" Wani irin kallo ya bita dashi "Ya kina ganina amma ta wannan yaron kike yi. Tun wuri ki sani bazan yarda da wasan kanin miji ba." Kamar gaske ya hade rai ita kuwa dariya ma take yi "Ka jira a haifi kanin mijin wannan dai twin dina ne ko ba ka ji sunansa ba...Zayyan da Zayyanatu" tayi masa gwalo. Bata fuska Ibrahim yayi ya tale baki yadda take yi ta cigaba da dariya. Muryar kuka ya soma yi mata "idan ba kin janyo na rage masa matsayi ba tunda haka ne. Tun farko ni me yasa ba'a saka min Zayyan din ba shi a saka masa Ibrahim?" "Saboda shi Zayyan kanina ne, shi kuma Ya Khaleel...." juya idanu tayi bata karasa ba ta kama hanya za ta gudu. Ibrahim kamar wanda aka dora a gajimare yake yawo don dadi ya biyota ya mika mata shi. Tana karbarsa ta kai hancinta jikin nasa tana gogawa tare da yi masa murmushi "baby DK dinaaaa" Jingina Ibrahim yayi da bango yana kallonta da jin sabuwar soyayya na dibansa "yaro kaji dadinka ko yaushe ni kuma zan sami arzikin ayi min haka wa ya sani" Kai ta dago ya kashe mata ido bata iya cewa komai ba saboda kunyar da ta ji ta shige ciki ta barshi a tsaye yana ta murmushi. Emzee ne ya shigo ta karamin gate da ledar mangaro masu kyau wanda ya sauka daga motar ya tsallaka siyowa da suna hanya kafin su shiga kwanar gidan. Yana karasowa motoci uku suka shigo manyan mata wayayyu suka rinka fitowa daga ciki. Mom Arifah kadai suka gane suka gaisa da ita da sauran matan tace Emzee ya kaisu wurin Mairama. Yana gaba sauran duka suna bayansa da ita suka shigo. Su Radhiya suka gaishesu sannan Zayyana ta hau sama ta fadawa su Ummi. Gayyar lallen ce ta tashi dama sun saka wata leda a wurin basu bata ko ina ba suka tafi daki. Dukkaninsu matan manya ne su takwas. Biyu matan gwamnoni, uku matan sanatoci, karamar ministan ilimi sai matar ministan ilimin wai sun zo sake yiwa Mairama murna ne zasu koma garuruwansa. Duka Mom Arifah ce ta gayyato su. Abubuwan ci da sha aka kawo musu Salame tana daga daki take jin muryoyin manya don su Yadikko bayan gidan suka tafi wurin aikin nama kafin isowar su Mama da Mami da zasu hadu ayi abinci da Tante. Ko da wasa bata hangi kanta tana taya aikin komai ba a gidan banda kwanan bakinciki da tayi jiya saboda yadda ganin Alh Salisu ya kara tada mata hankali shi da matarsa. Fitowa tayi tana hura hanci Mairama kuwa tace musu ga yayarta tana nunata. A mutumce suke gaisawa da ita sai ta saki fuska ta samu ta zauna a kujerar da tafi kusa da Mom Arifah tana ta wangale baki. Hannun Ummi da Mom Arifah ta gani ta yaba "gaskiya ina son lallen nan Mairama yaya zamuyi? A ina mai yi take? Yayi kyau sosai" Dadi Ummu taji " 'yata ce tayi min sunanta Rahima" Matar gwamnan Abia kasa hakuri tayi tana shafa hannun tare da kallon kafar gwanin sha'awa "ni dai a kirawo ta idan tana kusa tayi min inje dashi gida yarana su gani...nawa ake biyanta don basira irin wannan nasan da tsada" Salame an dade ba'a shiga aji ba amma dai tana fahimta kan bai gama toshewa ba. Ji tayi jikinta ya soma rawa taji kudi hankalinta a tashe 'yarta zata yiwa matar gwamna lalle. Sauran ma kowa tace tana so saboda yadda zanen ya fito radau sannan kalar tayi maroon sosai. Bude baki tayi za ta ce ko dari uku ne ma su kawo sai Ummi ta riga ta. "Ku da 'yarku ko nawa ne ma kuka bata sai dai muyi godiya" Mugun kallo Salame ta watsa mata sai dai babu wanda a kula a zuci tace "shegiya 'yar bakin ciki" "No, no please Ummin Alheran ki fada a biya don nima zanyi. Muna da yawa bare ace alakoro ne" Mom Arifah tace suna dariya. "Yanzu kuke magana" Salame ta sake cewa a ranta. Ummi dama ko kadan bata da niyar manyan matan nan suci bulus. Ta dai fadi haka ne don kada a ga kamar bata da kara. Amma wannan ai kofa ce da Rahima zata samu. Aunawa tayi ta ga a garin Abuja suke inda komai kudi ne. "N2000 take yin hannu da kafa" Wata Dr. Lara 'yar lukuta da ita karamar ministan ilimi tace "kirawota ta fara yi mana ko a gama da wuri tunda kuna da aiki a gabanku" Matar gwamnan Abia kuwa jakarta ta balle ta dauko bandir din dubu daya ta mikawa Ummi "take this hundred k sister Maryam for the eight of us." Baki Ummi ta bude zata yi godiya Mama ta rigata a gayance don kada a rainasu "Thank you Madam" Hannun Salame har wani kaikayi yake yi burinta Mairama ta miko mata tunda duniya ta shaida ita ta dau cikin Rahima ta haifeta ta shayar. Saboda haka tafi kowa hakki akan dukiyar 'yarta. Gilmawar Emzee Mami ta gani yana dauke da plate da ya bawa mai aikinsu ta yanka masa mangwaron zasu sha shi da Ibrahim tace ya kirawo Rahima. Zuciyarsa har wani dan tsallen murna tayi ya hau sama ya kwankwasa musu kofa. Radhiya ce ta amsa ya dan daga murya don kofar a rufe take. "Turo min Rahima ana kiranta" Kululu haka cikin Rahima ya kada da taji muryar Emzee. Hannunta kasa rike ledar lallen nata tayi sosai saura yatsa daya ta gama yiwa kanwarta Khadi ta tashi bayan ta lallaba ta gama. Hijabinta ta gyara ta bude kofar yana tsaye ya jingina da bango yana shan mangwaron da fork. Mika mata yayi ta girgiza kai cike da kunya. Kofar fita daga falon ta nufa yana tsaye har lokacin a inda ta ganshi da ta fito. "Kawar soja" Dakatawa tayi amma bata juyo ba har ya iso inda take ya tsaya a gefenta. A hankali yace "abinda muka yi jiya bai yi kyau ba ko?" Sai lokacin ta kalle shi da idanuwan da suke narke masa zuciya cikin sanyinta tace "yayi kyau sosai" "Amma kika kasa fada min?" Yace kamar yana fushi. "Kayi hakuri Ya Emzee" ta kira shi yadda taji Zayyana na fada. "Kowa fa ya fada ke kadai ce banji kince komai ba" "Kayi hakuri yayi kyau" "Sosai?" Yace excitedly "Sosai sosai" Murmushin fuskarsa ya dauke "kai duk da haka ban hakura ba. Yau idan an shirya za'a tafi idan baki ganni ba a wurin kada ki shiga motar kowa I will come for you" Idanunta ta zare tana kallonsa ya nuna mata kasa da ake jiranta suma jin Mama na cewa ya fada mata ta taho da kayan lallenta. "Idan baki jirani ba zamu dena kawancen nan so please ki jira ko bana nan zan dawo" Kallonsa tayi ta dauke kai ya dan sake matsowa ya rage murya "Rahima please do this for me" Bai jira amsarta ba ya sauka ita kuma ta koma ta dauko kayan lallen ta sauka gabanta na wata irin faduwa tana jin kamar rayuwarta bazata taba dadi ba idan babu shi a cikinta. Sai dai kuma tunanin yafi karfinta ta kowace fuska yana karyar mata da gwiwa. Jikinta ne yayi sanyi da Ummi ta nuna mata su wa za ta yiwa. Da wane hannun za ta taba wadannan matan masu kwarjini haka. Da kyar ta iya cewa bari ta kwaba wani saura kadan wancan. Yawun bakinta har bushewa yayi tana tsoron kada taje tayi musu mistake. Ummi ta lura da ita sai ta tashi tabi bayanta zuwa kitchen din da ta shiga da ledar kayan lallen. Salame ma sai ta bisu da sauri kafin Mairama taje ta bata dubu biyar ta murkushe sauran ta cinye ita kadai. A fusace take tazo shiga maganarsu ta dakatar da ita. "Ummi kingansu kuwa? Ni dai tsoro nake ji" Ummi ta tayata dibo ruwa tana tsiyaya mata a robar da ta zuba lallen da kayan hadi "na fiki tsorata in fada miki wai nice da matan gwamnoni a gidana" Rahima tayi murmushi "kema da kanki?" "Ahh tabdi to ni na taba ganinsu ne?" Murmushi ta sake yi sai kuma damuwa ta bayyana "kada hannuna ya rinka rawa" Kafadunta Ummi ta dafa "Rahima! So nake kasuwa ta bude miki ace matan manyan nan kike yiwa kunshi kina jina. Ki ajiye tsoro ki tuna cewa neman halak kike yi zaki taimaki Baffanki ko?" "Eh" "To ki nutsu yanzu haka dubu dari aka baki amma zan ajiye sai zaki koma gida na baki" "Dubu dari Ummi?" Rahima tace mamaki ya isheta ta rungume Ummin tana murna "in bawa Baffana da ke da Umma sai mu raba sauran da kannena" "Kut..." Salame tace tana yunkurin shiga kitchen din. "Banda ni ki bawa Baffanki da Addata su sa miki albarka kinji Rahima. Allah Yasa budi ne zai zo miki da hakan." Kasa boye murnarta tayi ta kuma rungume Ummi "Ummi nagode...dama kece Ummana da naji dadi" Dammm zuciyar Salame ta buga taji wani irin abu ya tokare mata wuya. Ka haifi da ya rinka fatan dama wata ta haifeshi...kenan fa Rahima bata sonta ko? "Kada na sake jin magana makamanciyar wannan kina jina. Ko me Adda Salame za ta yi miki kiyi hakuri domin duk duniya ba ka da masoyi sama da mahaifiyarka. Allah Yana fushi da mai sabawa iyaye" Hawaye ne ya ciko idanun Rahima ta fashe da wani irin kuka "Ummi bata sona" Da sauri Mairama ta sake rungumeta ko damuwa da lallen da ta cambala mata a jikin riga bata yi "tana sonki Rahima, nima kuma ina sonki. Baki san kece autar Ummi ba...Karami da kike gani dan karo ne kece autar" Murmushi Rahima tayi saboda Emzee da Ummi ta ambata. "Ko ke fa...wanke fuskar muje mu caski naira" Da gudu gudu Salame ta bar wurin kafin su fito ta nufi dakinsu. Abin da ya zame mata sabo a rayuwarta tayi wato kuka akan yadda Rahima ta dauketa. Yanzu ashe abinda take yi mata ya isa ya sanya Rahima jin inama ba ita ce mahaifiyarta ba? Hawaye sosai take yi zuciyarta ta kuntata. Tabbas ta cutar da 'yarta saboda wani dalili mara tushe wato rashin arzikin mahaifinta. Zama tayi a dakin tana ta tunane tunanen abubuwan da ta rinka yiwa mata. Sai kuma shaidan ya tuna mata da kudin da aka bada na kunshi. Kamar an tsikareta ta tashi tayi sama saboda bata ga Ummi a falon ba. Gara ta samu ta daidaita da 'yarta yadda ko arzikin yazo tare zasu ci abinsu. Banka kai tayi cikin dakin kai tsaye ta sameta tana nade gift da wrapping paper. Kallon banzan da ta saba tayi mata sannan ta rike kugu ta mika mata hannu. "Bani kudin" Sai da Ummi ta bawa iska ajiyarta na cikakken minti daya ta karasa abinda take yi kafin ta dago kai "kin bani ajiyar kudi ne Adda?" "Kada ki raina min hankali Mairama ina kokarin muyi komai cikin lumana tunda gidan da mutane. Kudin da aka bawa 'yata ta cikina Rahima na kunshi dubu dari nake magana a kai" Ummi ko ci kanki bata ce mata ba ta tashi ta dauko kudin a cikin wani kit ta mika mata. "Wato da har kinyi musu mazauni a cikin kayanki saboda bakar mugunta" "Adda Salame..." "Sunana kenan. Idan kinso kice Salamen kai tsaye ba damuwa zanyi ba" "Kudi kika zo karba kuma na baki saboda haka ki fice min daga daki kafin ranmu yafi haka baci" Ummi tace a haka ma kokarin danne zuciyarta take yi sosai akan halin yayarta da yadda take yiwa Rahima. "Oho dai, da fa bamu san asali bane sai ayi mana burga. Kunje kuna ta kwantar da kai a gaban mutane saboda ace kuna da kudi" Kashingida Ummi tayi akan gado ta nuna mata kofa "sauka kije ga irinsu can kema ki kwantar da kan ko za'a dace" Gani tayi da gaske bazata biye mata ga bakar magana ta yaba mata sai ta sauka kawai tana kunkuni. Rahima na ganinta da envelop din kudin taji wani irin kunci a zuciyarta don tayi imani da wuya ko kwandala ta bata a ciki wanda zata bawa Baffanta da Iya. Hawaye ke neman subuce mata taji sallamar Emzee. Matan wurin ke ta yabon abinda su ka yi jiya ana cewa iyayensu sunji dadi shi da yayarsa kowa da baiwarsa. Duk zancen da akeyi Rahima yake kallo da take duke tana yiwa wata lalle a kafarta. Kin kallonsa tayi saboda a haka ma da kyar take yi jikinta ke rawa. Yadda take motsa hannuwanta yayi ta kallo har ta gama yiwa matar ta soma na wata sannan ya tafi. ********** Karfe uku da rabi Awwab, Raji, Yousuf da Bilal suka fito daga gidan Mami kowa sanye da fararen kaya masu ado da koren zare da hula koriya. Saidai kowa dinkinsa daban ne amma shigar kenan kore da fari. Awwab nasa kayan wani lallausan yadi ne fari kal mai kyau anyi masa riga iya gwiwa sai hannu dogo ya saka links masu wani stone green. Aljihun gaban rigar rabin yadin da aka yi shi fari ne daya rabin kuma green sai yayi kamar triangle. Maballan rigar har wuya su ma duka green dinne sai wani siririn ado na green din zare daga gefe saya. Hular kansa da tasha kari hadin zare green da fari ce dai. Kafarsa farin takalmi cover shoe sai silver agogon dior. Kamshi yake fitarwa mai dadi shi kadai yake murmushi yana tsaye a gefen mota ya zura hannu daya a aljihun wandonsa yana danna waya. Text ya turawa amaryarsa cewa zasu dauko Arifah su biya su dauketa sannan su wuce. (Ni kunyar ganinka nake yi) ta rubuta masa. (Ni kuwa kwana nayi mafarkinki...can't wait to see you baby) Hoton fuskar kunya ta tura masa na whatsapp shine yake murmushi. "Mintuna kadan ya rage ka ganta kake wannan murmushin kai kadai" Bilal yace yana bude gaban motarsa. "Bazaka gane bane dan uwa....I love her to the moon and back" yayi maganar yana lumshe idanu. "Yau da bani da Fauziyya da ka saka ni neman aure amma yanzu sai dai nayi maka dariya don duk abinka sai ka jira anyi biki zamu bari ka dauketa" "Kayi hankali kada ku ja mu bar abin fada har jikoki" "Me kenan?" Yousuf yace yana bude motar da zasu tafi shi da Awwab. "Bari dai nayi shiru wadannan mazajen kannena ne kada su raina ni" Sai da suka gama barkwancin Raji da Bilal suka shiga mota daya Awwab da Yousuf guda daya. Su Awwab gidan Excellency suka wuce ko shiga basu yi ga Yousuf ya kira Arifah. A shirye take ta fito daidau gate inda suka yi parking. Shaddarta fara ce itama sai paint work green da stones daga wuya har kasa amma ba'a cika adon ba. Ashoke aka yi mata dauri dashi mai hawa-hawa tayi matukar kyau fuska tasha make up. Ga mayafinta green ta yafa a wuyanta. Yousuf gabadaya ya rikice ya fita ya bude mata kofar baya tana zama Awwab ya fito ya karbe key din motar. "Ina hauka ne zan bari ka tuka ni idanunka suna bayan mota? Shiga kawai muje kada kayiwa matata asara" Arifah dai kunya take ji murmushi kawai tayi tana gaisheshi. Yousuf dama jira yake yana shiga ya rungumota yana mata rada a kunne wai jiya basu gama taya juna murna ba. Da hannu ta rinka nuna masa saitin Awwab dake tuki. "Wannan yafi kowa fitina ki kyale shi kawai" Shiru yayi bai ce komai ba albarkacin Arifah da yake ganin mutumcinta sosai. Suna zuwa gidan an shimfida katuwar darduma wadda su Daada suka yi jam'in sallar la'asar. Su biyu suka tada tasu Arifah ta shige ciki. Yau ma Mairama da kanta ta shirya Zayyan kamar kullum ya saka shadda army green dinkin tazarce. Dayake tsayi gareshi ba karamin kyau yayi ba. Sai da ta tabbatar ya gama fitowa ta rinka masa wankan turare sannan ta dauko nata kayan. Itama farar shadda ce riga da zani amma dinkin Nijar anyi mata aikin green din zare ga mayafinta to-match. Ankon kenan dama su fito a 'yan Nigeria sak banda masu taro wato Major General Zayyan, Muhammad Zayyan (Emzee), Zayyanatu Mustapha da Zayyan Hadir. Nasu kayan iri daya ne army green shadda. Suna fitowa daga dakin Radhiya ta fito da ashokenta a hannu tayi wata kwana da ribas ta dawo kawai sai ta daga tsalle ta dane Daada. "Anya banyi garajen aurar dake ba, Fillo yarinyar nan bata girma ba fa" Ummi sai dariya "kunfi kusa soja da 'yarsa." "Ni dai ku tsaya nayi muku hoto" tace tana gyara musu tsayuwa "wayyo ni Daada da Ummina sunyi kyau" Dariya ta basu ta matsa baya zata dauka da wayarta Zayyan ya rungumo Mairama a jikinsa. Ita kunya Radhiya kuma ta kanne ido daya wai a zuwan bata gani ba. Sunyi bala'in kyau ta rinka daukarsu Zayyan yana biye mata suna yi a tsaye ko a zaune. Muryar Arifah da ta jiyo ne ta bar wurin da sauri taje ta karasa shiri. Hudu da ashirin kowa ya sauko sai fararen kaya kake gani da koren mayafi ko hula. Zayyana gown dinta aikin da farin zare aka hada shiyasa ta saka farin mayafi bayan anyi mata daurin yayi wanda dukkansu matan shi suka yi mai hawa-hawa da dankwalin kayan. Mutane ke ta fitowa babu wanda ya lura Rahima bata fito ba. Ita kadai take kokonto idan Emzee yaki dawowa ta kade. To amma babbar matsalarta yanzu bai wuce bayanta da yake ciwo saboda dukawa ba don yau ta aikatu. Irin kayan Arifah sak hatta takalmi da jaka Radhiya ta saka rigar tasu mai high neck. Basu saka sarka ba sai wasu doyayen dankunne green and white masu tsada da daukar ido. Ta kware da tafiya da heel bata jin wahalarsa ko kadan tana taku daidai ta iso gaban motar. Zagayawa yayi ya bude mata daya gefen gaban yana tsaye zata shiga wani ni'imtaccen kamshi na shigarsa ta ko ina ya rike mata hannu. Kallonsa tayi sau daya ta dauke kanta. "You look sweet baby" "Ka fini yin kyau Hammana" tace tana murmushi. Hannu kawai yasa ya janyota ta fito ya sake matso da ita jikinsa sosai yayi musu selfie. "Akwai bil adama a bayan mota" cewar Yousuf bayan ya sami chance din kaiwa Arifah kiss a kan hancinta tana rufe idanu. Dariya Awwab yayi wai yanzu damarsa ce sun gama nasu bai ce komai ba. Zama Radhiya tayi ya gyara mata rigarta ya rufe kofar sannan ya ja suka tafi kana leka motar taurarin soyayya sun mata kawanya. Wani katafaren events hall suka nufa inda suke iya ganin taron motoci sun cike wurin parking din ciki an fara layi a gefen titi. Suna shiga Emzee yana fita bayan ya karbi mukullin motarsu daga hannun Ibrahim da su suka ajiye su Laila da Zayyana. "Ina kuma zaka je kasan yanzu su Daada zasu iso a fara" "Yanzu zan dawo Rahima zan dauko please kace bazan dade ba idan an nemeni" "Emzee kodai-kodai?" Ibrahim yace yana daga gira. Cike da shauki Emzee yace "fadi ka kara bros yarinyar nan ta cuceni...ko shiryawa banyi ba kawai na nemi zuciyata na rasa ashe ita ta dauka. Da tayi warning dina kasan kai zan fara sanarwa" Duka Ibrahim ya kai masa a baya yana kyakyata dariya "shege malamin soyayya ya fada ruwa....tabdi amma har ta bani tausayi ta kwaso Emzee chewing gum" "Me ka mayar dani?" "Irin mazan da idan suna son mace zasu iya sadaukar da komai nasu domin kyautata mata mana" "To kai din ba shi bane?" Bangaren da Zayyana take Ibrahim ya kallo "I can die for her man" "I feel you bros nima haka nake ji. Ina bukatar time da ita ne domin in san ko wacece. Na dai fi tunanin tana da alaka da gidansu Halifa maybe cousin dinsu ce tunda ina ganinta da Hibbah." Gaban Ibrahim ne ya fadi ya soma tunanin yaya akayi Emzee bai san wace Rahima ba. Tunawa yayi da yadda ya tsani Gwaggo Salame yaji jikinsa yayi sanyi. Bai taba ganin Emzee so cheerful ba irin yanzu, gaskiya bazai iya rushe masa wannan sabon farincikin ba. Zai bari ya gano da kansa kila sanadiyar shiryawar iyayensu kenan. "Na tafi" yaji Emzee yace. A gurguje ya tada motar ya koma gida. Minti goma ya kaishi saboda babu nisa da gidansu. Sai yanzu ya tuna bashi da nambar wayarta to ta yaya zai kirata. Idan kuma ta tafi wurin bata jira shi ba fa. Tambayoyin da yake ta yiwa kansa kenan sai ga mai aikinsu 'yar budurwar ta fito itama a shirye fes da ita. "Yauwa don Allah kirawo min Rahima a dakin Adda Radhiya." "Kowa ya tafi fa muma Ummi tace yanzu dreba zai dawo daukarmu shine na fito dubawa da ka shigo" Gwiwarsa ce tayi sanyi ya koma motar sai ya sake dawowa zuciyarsa na fada masa Rahima na jiransa "daure ki duba min nasan tana nan" Ba musu ta shiga gidan. Dakin kasa da suke ta shiga tayi sa'ar ganin Rahima a shirye cikin nata kayan kamar kowa Ummi ta dinka mata sai dai ita dasu Zahra dankwalin kayan suka saka. Arifah da Radhiya ne kawai masu ashoke manyan amare. Mayafinta daidai da ita har ka ta lulluba shi yadda ta saba tayi kyau sosai. "Karami ke kiranki a waje" Da faduwar gaba ta tashi tana tunanin karfin halinta na zama don yace ta zauna. Sai dai bata jin akwai ranar da za ta yi fatan yi masa musu saboda babban matsayin da ya kwata ta karfin tsiya a zuciyarta don itama bata shirya ba. Kayansa hatta hula sak na mahaifinsa yana tsaye a bakin kofa ta fito. Ido suka hada ya sakar mata murmushi ta janyo mayafin ta rufe rabin fuskarta. "Hey kada ki cuceni ki hanani ganin fuskarki yau ba kawance" Langabe kai tayi suna tafiya wurin motar "sai me?" "Muhammad da Rahima" Sake rufe fuska tayi komai nata yana burge shi matuka ya dora hannunsa a saitin zuciyarsa "my God, she is so adorable" Sun kusa kaiwa motar yaji an kwala masa kira daga cikin gidan "kai Karami ku jirani wannan dreban da za'a turo ban ga ranar zuwansa ba" Ba kowa bace illa Salame ta taho buguzum cikin wata kodaddiyar shadda wadda take yiwa kallon mai kyau har yanzu tana goye da Khadi kamar wata jaririya. Gaban Rahima ya fadi zuciyar Emzee kuma tamkar ta fito ta baki saboda bacin rai har ta iso bakin motar ta bude gaba ta shige kwam abinta. 💕[11/2, 7:46 AM]: 56. 💕 Dan duka kanta tayi tana lekensa ta sake daga murya "kai shigo mu tafi mana" ta kuma lekawa ta daya bangaren "kema shiga kin yiwa mutane wani kikam" Emzee alama ya yiwa Rahima da ta tsaya don bai ga dalilin daukarta da makiyar Ummi a mota daya ba. Sannan abu na biyu baya son a matsayinta na yayar Ummi tayi abin zubar da mutumci a gaban Rahimansa. Khadi da ke kan cinyar Salame kuma duk maganar da take kusan akan fuskarta tayi sai sa hannu tayi ta toshe hanci babu kunya tana yiwa babarta wani irin kallon haushi "hmmm Umma hmmm wali-wali a bacinci" Da sauri Emzee ya fitar da kansa kafin ya shaka yayin da Salame ta dage ta zabgawa Khadi duka a gadon baya ta fashe da kuka. Rahima ta tafi da sauri ta bude kofar ta daukota Emzee ya yiwa Salame wani disgusting look. Gaban motar ya riga ya fara wani abu sama-sama mara dadin ji ga hakoranta masu kore daga samansu. Sannan abin haushi dubi yadda ta daki karamar yarinya haka. Kayan jikinta kuwa ya rasa abib fada. Shi dai ya tabbatar Ummi ta sasu sayen kaya ready made na mutan Sumaila shi da Ibrahim da Laila suka je. Haushin abinda Ummin ta yi mata dazu shine yasa taki saka kayan wai tafi karfinsu. Khadi 'yar banza ta tasha hannu ba musu ta gudu wurin yayarta ta lafe tana kuka. Jikin Rahima na rawa dreban ya dawo. Ajiyar zuciya Emzee yayi yana kallota ta saman motar. A hankali yayi mata magana yana kallon yadda ta rikice sosai "ki bisu zan taho yanzu okay" Kai ta gyada da sauri ta tafi daya motar tana tsoron kada Salame tayi mata wata maganar ko tace su koma gida. Ita kuma zuciya a baka saboda bacin rai yau rashin m din na Khadi akanta ya kare a gaban wannan yaron na Mairama. Muryarsa taji ya gama goga hannuwansa da juna. "Lets get going Gwaggo" Dauke kai tayi yana ganin dreban yayi waje kawai ya cire hularsa da riga daga shi sai wando da vest. Bayan motar ya ajiye rigarsa da kyau ya dora hular a kanta don kada ta fado ya shiga ya zauna ya daura belt. Salame ta kalle shi tana tunanin dalilinsa na tube riga bata gama sannin me ake ciki ba ya fizgi motar a guje ya fita da ribas sai da cikinta ya kada. Wata irin cin taya yayi da burki yayi kwana tamkar mai shirin zuwa Sumaila a awa guda daga Abuja ya kwashi motar ya hau titi. Gudu yake na karshen rashin hankali sai dai kaji qeeeyyyyy quuuuu....yaci taya ko ya taka burki sai motar tayi kamar za ta hantsila. Salame tana kallon yadda ya murtuke fuska kuma jikinsa baya motsawa amma ita sai dai tayi gaba yif ta dawo baya yif jikinta yana ta mazari. "Kai dan ubanka tafi a hankali ko ka saukeni" Idan motar za ta amsa to Emzee ya amsa. Salame sai da ta kai ta daga hannu za ta doke shi yayi mata wani razanannen kallo tare da taka burkin gaggawa sai ga kanta ya tafi saura kiris ta doki glass. Hannunsa yasa ya tareta don ba jini yake son fitar mata ba. Burinsa ko ta halin kaka ya fanshi wani abu na makantar Ummi na shakara goma. Tsanar Salame ke kara ruri a zuciyarsa zai bincika ya tabbatar da sa hannunta. Idan akwai ko su Ummi basu sani ba da shi da Addarsa sai sun yi mata abinda zata ji rayuwarta tayi kunci. Yanzu haka ranar zuwa Sakkwato biki suke jira shi da Radhiya su barwa Maikudi abinda bazai manta ba. Ba wani abu bane kuma yafi taba zukatansu sai wulakancin da ya yiwa Umminsu ga wahalar haihuwa ga radadin mutuwar miji da taji. Kowa ya sani a Nigeria biyu ga watan junairu ana tsaka da sanyi ne amma banda Salame matar Haji Indararo. Gumi take kashirban tana yiwa Emzee tofin Allah tsine. Lokacin da suka isa wurin yayi sa'ar ganin wata motar na fita yasan zai sami wurin parking. Katinsa ya nuna aka wangale gate ya shiga Salame tana ta numfarfashi. Yana tsayawa ta kama kofa zata fita taji a datse. Ashe harda hawayen wahala tayi bata sani ba cikin fada tace "shegen yaro mai kama da ifiritu bude min" Emzee a soja yake baka ganin wani abu wai shi sani ko sabo a tattare dashi sai murmushin mugunta "kinfi kowa sanin cewar ina da uba mijin kanwarki....ko ince mutumin da kike so?" Ya yi mata wani kallon gefe. Jikin Salame ya bugu saboda tukin da ya yi amma abinda yafi daga mata hankali bai wuce maganar da yayi ba. A ina yaji? Mairama ce ta fada masa ko waye? Karfin hali tayi ta daure fuska. "Rashin kunyar taka har ta kai haka Karami? Irin tarbiyar da Mairama take baku kenan ashe, kun tashi ba ku ganin girman kowa" Juyowa Emzee yayi ya mata wani kallo mai firgitarwa kamaninsa sun sauya gabadaya...soja mazan fama. "Kada ki kuma ambaton sunan Ummina domin tunda take bata taba nakasa dabba ba bare mutum" "Innalillahi wa inna ilaihi rajiun" Salame ta fada a tsorace jikinta yana tsuma baki na rawa "me...me kake nufi? Sharri za ka yi min kace ni na makanta ta?" Sai da kansa ya sara a lokacin domin dama bugun cikinta yayi ya bata tsoro domin jin gaskiyar lamari kuma yaji abinda yake so kafin ma ya tambaya. Duk da yana zargin tabbas ita ce amma yanzu da ya tabbatar sai da abin ya girgiza shi matuka. Ba ya kaunar Salame ko na digon sakan saboda bata cancanci a sota ba. Umminsa tana makance tsayin shekaru Salame tana gidan miji tana ciki da haihuwa taci me kyau tasha me kyau lokacin gwamnatinta na ci a zuciyar Alh Indararo. "Kuruciya tasa ban fahimci me kika yi ba shiyasa ban tona miki asiri ba tun lokacin da kika saka mata...." yace don ya kara tunzurata yana bude dash board. Sabon gumi na yake tsattsafo mata jin sirrin boye da ko da kanta bata zancen a zuci yau Emzee ya bankado shi. Harda sanyi ta rinka ji yana ratsata ya cigaba da lalubensa kamar ba ta cikin motar. Hakoranta sai sarkewa suke yi don tsoro tace "to yanzu kuma uban me kake lalube bayan ka gama yi min sharrin" "Bindiga" Idanunta kamar zasu fado karshen tsoro ta kai sannan ga uwa uba wani mahaukacin zawo da ya matsota saboda tsoro. "An...an. fada. Maka idan...idan ka kasheni. Mairama zata yi murna ne?" Bude pin din motar yayi "kin zata harbinki zanyi? Allah Ya kiyaye ba'ayi min wannan tarbiyar ba" Budewa tayi da sauri ya leka da kansa ta inda ta tashi "uhmm nace ba....nagode da kika tabbatar min da zargina akan waye ya makanta min uwa" Salame sai bude baki tayi tana masa kallon tsananin mamaki shi kuwa ya zura hannu ya janyo kofar ya rufe ta bangaren da take sannan ya kifa kai akan sitiyari yana kokarin mayarda hawayen bakincikin da suke neman zuwar masa. Dago kai yayi ya nemi wayarsa sai ya ga har lokacin tana tsaye. Da kallo daya ya karasa razana ta ta wuce ciki wurin da ake ta karbar baki za'a fara abinda ya tara jama'a. Yau ranar farinciki ce dole ya saita kansa. Ibrahim ya kira bugu daya ya dauka. "Bro turo min Rahima" yace da wata iron murya can kasa. "Bangane ba. Ba tare kuke ba?" Zai sake magana ya hangota tare da Zayyana zasu zauna "kana ina ne na ganta" Kwatanta masa inda yayi parking Emzee yayi Ibrahim yaje inda suke ya fadawa Zayyana ita kuma ta fada mata. Tana tashi bayan ta ajiye Khadi akan kujerarta ta hango Salame amma da ta ga hankalinta baya gareta sai ta wuce ta tafi. Ya gama saka rigarsa kenan yana gyara zaman hular a kansa ta bullo. Shagala Emzee yayi da yadda Rahima take tafiya cikin nutsuwa. Yanayin da ya shiga mai wuyar fassara soyayyarta ta mamaye masa kowane lungu da sako na zuciyarsa. Duk kunya ta isheta saboda yadda ya kafeta da ido har ta karaso. "Mu zauna a nan ko mu shiga ciki?" Yace yana fatan ta amince su zauna. "Za'a nemeka ai" "Okay muje" sun fara tafiya ya ga dacewar ya bata hakuri akan abinda yayar mahaifiyarsa tayi musu "Rahima kiyi hakuri akan abinda ya faru dazu. Na saka ki zaman jirana kuma bani na kawoki ba" Ita da tasan mahaifiyarta ce tayi sai tayi saurin cewa "ni ya kamata na baka hakuri" "Akan me? For being a good girl me jin maganarrr.....maganar wa dinki kika ji?" Ya zuba mata idanu. Murmushi tayi kanta a kasa "Ya Emzee?" "Nope" tsayuwa yayi ya hanata tafiya "Rahima wane matsayi kika bani?" Kasa magana tayi tambayar tayi mata nauyi duk da amsarta tana jin tamkar ta amayo masa ita ne ko za ta sami saukin wannan soyayya da tayi mata mugun kamu. Kamar yayi mata kuka saboda taki magana "gobe zan koma Kaduna da sassafe. Please Rahima ki fada min ni waye a gareki kafin na tafi....idan ba haka ba retire zanyi tun kafin na fara aikin na dawo ga filin yaki nan in your beautiful eyes muyi ta fafatawa." Zuwa yanzu ko fuskarta baya iya gani ta shige cikin mayafin ta rufe kanta gabadaya sai murmushi kawai take yi. Da kyar ta iya cewa "ni wa dinka ce to?" "My heart..." yace da sauri "ke fa?" Babu wanda zai wuce ya gansu baiyi musu kallo na biyu ba. Kana ganinsu ka ga masoyan da suka mutu akan juna kuma suka dace sosai da juna. Emzee fari ne kamar yayarsa ga kyau ga jikin matashin soja. Rahima kuwa baka ce fatarta tafi kama da wankan tawarda don da kadan Zayyana ta fita haske. Kyakkyawa ce sosai tafi Halifa da sauran 'ya'yan Salame nesa ba kusa ba sai dai su nuna mata haske. Round shaped eyes dinta sunfi komai daukar hankali akan fuskarta. Kamaninta sosai da kakarta Iya shiyasa take ji da ita. "Kinyi shiru Rahiman Muhammad" Sautin loudspeaker suka ji za'a bude taron da addu'a Rahima ta daure tace "to me kake so nace Muhammadun Rahima?" Murmushinsa dariyar farinciki ya koma yana kallonta da adoration "kince komai....realy? Kin yarda Muhammadun Rahima ne ni? Daga ni fa babu kari" Dariya tayi ta cikin mayafin tana gyada kai. Zuciyar Emzee ta cika da soyayyar kanwarsa da bai san suna da alaka ba ko kadan. Da sauri sauri suka karasa hall din za ta wuce bangaren mata ya bi bayanta da sauri yana maida numfashi tamkar wanda yayi tsere taji yace "Ina sonki Rahiman Muhammad" Juyowa tayi suka hada ido kowa da kayataccen murmushi a saman fuskarsa sannan suka nemi wurin zama. ********** Taro ya soma kankama bayan addu'o'i da mika godiya ga Allah mai gabatarwa Ibrahim Hadir ya gabatar da manyan baki na musamman. Ba kowa bane illa manyan aminai 'yan uwa ga Zayyan kowa da matarsa. Excellency baban Arifah, Major Daddy, Baba Hadir sai kuma Tante da mijinta mahaifin Yousuf. Wadannan mutane kowannensu ya taka muhimmiyar rawa a rayuwar iyalin Zayyan shiyasa idan suna ganin ya kyautata musu wurin ceton rayuwarsu ya kan ce babu kyautatawa mafi tsada da daraja sai wadda za kayi a bayan idon mutum idan ya mutu. Wannan kyautatawar kayi ta ne ba don ganin ido ba bare kasa ran a saka maka. A gefe guda ga duka 'yan uwan Zayyan mata uku da maza biyu domin Maikudi bazai taba iya zuwa ba duk da Zayyan ya bukaci hakan. To da wane ido zai kalli su Mairama, Daddy da har yau bai manta kalar bacin ran da ya gani a idanunsa ba, da uban gayya Zayyan wanda ya mare shi. Ya kure Zayyan iyakar kurewa kuma ya tabbatar abinda yayi musu bazai taba gogewa a zukatansu ba. Son zuciya da kwadayi ya mayar dashi mujiya a cikin ahalinsa. Yana ji yana gani sai dai yayi ta dari dari dasu domin tsanarsa da yake gani a idanunsu. Captain Onomza shima yazo ga jama'ar Rugar Barkindo, na gidan Malamijo da abokan arziki. Sannan mutumin da Zayyan ya dauka da matukar mahimmanci a rayuwarsa wato Chibuzor da matarsa da 'yarsu su ma kayan jikinsu irin na wadanda su ka yi ankon fari da green din. Sai kuma Maman Dolapo da Christie ma sun zo kafin shigowar Emzee suka share hawayensu dasu Mama. Ga Alh Salisu da nasa iyalin abin sai son barka. Ibrahim ne yake magana da turanci da hausa domin kowa ya fahimta ya sanar da cewa akwai gajeren wasa da abokan Emzee zasu gabatar mai taken A Soldier's Dream (Burin Soja). Drama ce mai kayatarwa wadda ta janyo wurin yayi shiru aka zuba musu idanu daga kan stage. Sojoji ne rataye da bindiga da 'yan jakunkunansu sunyi shirin tafiya filin daga. Gefe guda matansu da iyayensu suna ta kuka da yara. Idan ka ga yadda suke gabatar da dramar da matukar ban tausayi. Sun rabu da iyali suna ta kuka sannan sunje yakin an kashe da yawansu. Nan ma wurin dawowarsu mata da yawa suka rinka suma duk wadda ta ga babu mijinta. Mutane kuwa sai share hawaye domin an shigar dasu cikin rayuwar da basu santa ba kuma a da babu wanda yake damuwa da sanin nata. Da dramar ta kare Radhiya ma duk yadda ta ga abubuwa a Military Voice lokacin da suke dauka sai da tayi wani kukan. Bayan an gama tafa musu Ibrahim ya bukaci wadanda ake taro dominsu su hadu wuri daya. Zayyana dauke da DK wanda kayansa harda hula babu bambanci da na Daada da Emzee anyi masa komai dan karami daidai da jikinsa suka je wurin Daada. Wani envelop da Ummi tayi wrapping mai dan tudu Zayyan ya daga hannun DK da yake jikin Zayyan ya dora masa a kirjinsa. "This is for you my son" Su Daddy suna kallo babu wanda yasan menene a ciki. Wani ya sake daukowa ya fi wancan girma da dan nauyi ya mikawa Zayyana. "Kallabi tsakanin rawuna Zayyanatun Zayyan ga naki" Sai da ta rissina tace "Allah Ya kara budi Daada Ya saka da alkhairi" "Amin" su Excellency suka ce suna murmushi. Wani dan karami sosai Zayyan ya mikawa Emzee "Soja dan sojoji kaima ga naka" Godiya yayi sosai shima aka fara daukarsu a hotuna sannan kamar hadin baki aka shiga miko musu gifts kowa da abinda yake badawa. Family picture aka tashi dauka aka hada iyalan Zayyan, Daddy, Baba Hadir, Excellency duka wasu a tsaye wasu a durkushe. Zayyan ya dan gama waigensa ya hango Chibuzor ya kira shi da hannu shi da matarsa. "Sir this is a family picture" yace yana sake ja da baya. "You are my family Chibuzor" Zayyan yace yana yi masa murmushi tare da nuna masa inda zasu tsaya kusa da sauran yaran nasu. Chibuzor bai taba tunanin karamcin Zayyan ya kai haka ba. Yana da masaniyar yadda addini da yare ke kawo tawayar kyakkyawar alaka a tsakanin 'yan Nigeria amma ga wani babban soja masoyi ga mutane da dama ya rungumi kowa hannu bibbiyu. An gama hotuna aka fara cin abinci wanda yake serve yourself anyi shi a wadace kowa yaci ya koshi. Duk wannan abu da akeyi Salame tana rakube ko motsin kirki bata son yi saboda ko yaya ta ga giftawar Emzee sai cikinta ya duri ruwa. Yanzu idan ya bude baki a wurin nan ko kafin ta koma Sumaila ta kade har ganyenta don bata san me zasu yi mata ba. Ana yiwa Zayyan kallon mai kirki amma tana da yakinin cewa ba karamin mataki zai dauka akanta ba. Kallon kowa take yi daidai ana ta shagali wannan na hira da wannan, wancan da waccan amma babu wanda ya rabeta...abin bakinciki shine harda 'ya'yan cikinta. Idan Rahima ta gudu saboda yadda take takura mata meye dalilin Halifa da Khadi? Shi dai bai tsaneta ba amma baya kaunar halayenta ko kadan. Khadi kuma yarinya ce da ta goge a rashin kunya amma yau fushin nata saboda ta doketa ne. Salame sai ta ji ta very, very lonely abin ya tabata fiye da zato da tsammani. Kamar ance ta daga kai su ka hada ido da Mairama. Tun dazu da take gaisawa da mutane hankalinta yake kan Addarta. Yadda ta zauna ita kadai a table din mutum takwas an wareta kamar babu ita a wurin itama sai taji babu dadi. Fushin da take yi na kudin Rahima da ta karba dazu ya gushe. Murmushi tayi da su ka hada ido a karo na biyu sannan da hannu ta nuna mata inda ake dibar abinci. Wai don kada a rainata sai ta dauke kai ta juya mata keya. Ashe Mama na kallonsu ta tuntsire da dariya. "Oh ni Zainabu Abu inama ina da 'yar uwa mace muma mu hau sama mu fado." "Haka ma zaki ce?" Mami tace tana murmushi. "Abin naku ne kamar hadin baki. Kina yi dasu Gambo gefe daya ga Salame suna bugawa da Mairama" Ummi ta sake kallon Salame "babu abu mara dadi kamar ace kai da 'yan uwanka bakwa jituwa. Yawanci kuma duk sai ki ga hassada ta fi komai ruguza mana zumunci" "Ni zan fada muku haka don ina da tabbacin Hussaina da tayi ta ingiza rikicinmu da Gambo ba wani abu bane ya tunzuruta sai ganin wai muna da kudi mun wareta" Mami tace tana tuno bacin ranta. "Amma dai dan Adam babu godiyar Allah. Sai ki ga muyi ta takurawa kanmu domin mu kyautata musu amma basa gani" cewar Mama Mami ta mike "Yo ina kudin yake banda dai ana yiwa rogo kallon kitse. Kunga ni mijina bai ci komai ba yau tun safe kuma na ga mazajenku sun saka shi a gaba da hira ku taimaka kuyi musu signal ko su tashi ko na zuba masa shi kadai" Ummi da Mama suka sa dariya Mama tace "yayi matar Major Allah Ya bar mana ke. Ana kwasar jikokin ma ashe a gefe ana ta dabbaka kauna" Dariya Zainab ta basu suka mike tare kowacce ta zubawa mijinta abinda tasan yana so. Ummi na kai wa Daada nasa ta koma ta zuba fried sphagetti da wani sauce din naman sa da albasa, attaruhu da koren tattasai an yanka su manya manya, naman kuma dogo a tsaye ta hada da potato salad ta tafi mazaunin Salame. Ajiye mata tayi ta zauna a daya daga cikin kujerun. "Meye wannan za ki wani turo min abinci" ta sha kunu Ummi ma daure fuska tayi ta ja plate din "idan ba kya so sai na dauke" Da sauri Salame ta janye yawunta ya gama tsinkewa "barshi dai....kada kiyi zaton zanci da dadin rai ne don dai kawai ba kyau wulakanta abinci ne. Kuma ga bakinku ana kallonmu kada na kunyata uwar gayya Mairama matar Zayyan mai kudi" Ummi gimtse dariya kawai tayi tana ganin yadda idanun Salame suke walainiya akan plate din. "Bari na baki wuri kici" Wani iri Salame taji bata so ta tashi amma bazata nuna ba "haka kika iya dama naki bola wasu can bare sun fimu matsayi." "In zauna kenan kike nufi?" Ummi tace a ranta kuwa dariya ce fal take dannewa. Baki fal da taliya da nama Salame tace "In kin so tunda ai ba sai kin nunawa duniya bama shiri ba" A zuci Ummi tace "da baki girmeni ba da nace baki da kunya ma...kina so kina kaiwa kasuwa" A can kujerun karshe daga bari daya Yousuf ne da Awwab suke hira duk yawanci akan bikinsu ne da shirin da su ka tanadar masa. Dinner din da zasuyi basa bukatar taimakon iyaye da kudinsu suke son yi gasu duka babu wanda ya waye da harkar biki a Nigeria. "Ka bari idan mun koma gida muyi maganar da Bilal tunda shi dan gari ne" inji Yousuf "To shikenan. Yanzu dai shawara nake nema. Ina tunanin sayen mota amma kuma Alheran da zan barwa idan na tafi aiki itama ba zama zata yi ba." "Kawai ka barshi sai ta gama ta dawo nan din kunyi settling sai ka saya idan ba haka ba wa zaku barwa? Tunda akwai motocin nan a gida kawai ka bari" Arifah su ka gani ta nufosu da plates biyu Yousuf yayi saurin tashi ya karbo suka koma wani table din yana yiwa Awwab gwalo wai ga inda ake kula da miji. Arifah kunya taji ta kai masa duka a hannu ya rike hannun yana kallonta kamar su bar wurin nan ya samu damar nuna mata soyayya. "Ehemm da mutum a nan dai...albarkacin kanwata bari na baku wuri" Tashi yayi ya fara tafiya Radhiya ta kira shi kamar tasan ita zai nema. Tambayarsa tayi ina yake ya fada mata sai gata da plate guda daya da robar maltina. "I am starving Hammana" "Me yasa kike zama da yunwa" yace yana gyara mata kujera ta zauna. "To ba kaine nake ta nema ba muci" tace tare da turo baki. Bakin yake kallo yana lumshe idanu "kici abincin ni kuma ki bani bakin cin abinci yunwarsa nake ji" Kunya Radhiya taji har ta rasa inda zata sa kanta. Awwab kuwa yadda take yi ga dimple dinta yana ta shigewa ya burgeshi sai da yasa hannunsa a wurin. "I love this...." kanta ta sunkuyar yasa hannu ya rike kunnuwansa "sorry baby ina takura miki ko? Lets eat amma kinsan bazan ci na bakinki ba ko" ya kashe mata ido. Bata fuska tayi "Ewwwww ka zama kazami dai" "Kinga laifina an aura min ke" Hannuwa ta nade a kirji tana cika tana batsewa yana mata dariya. Kawu Zakari ta hango ai kuwa ta daga masa hannu tana dariya za ta rama. "Kawu Zakari tun dazu nake ta nemanka" Fuskar Awwab ba shiri ta sauya ya bata rai kamar wanda aka yiwa duka. Yau dai ya ga wannan Kawu Zakarin. Dan kyakkyawan bafillatani ya karaso ya mikawa Awwab hannu. Radhiya sai sakin murmushi take sai da ta ga Awwab ya koma abin tausayi ta dena jansa da hira. "Me yasa baka zo Antyn tamu ba ne?" "Tayi nauyi bana so ta wahala" Ba kunya Awwab ya saki fuska "ashe kayi aure" "Eh muna da yaro daya ma ga na biyu a hanya" Kawu Zakari yayi murmushi. "Kai Madallah wannan abu yayi kyau Allah Ya bar kowa da masoyinsa" Awwab yayi maganar farinciki ya mamaye fuskarsa abin dariya. Radhiya tana dariya harda hawaye don yanayin relief din da ta gani akan fuskar Awwab kamar wanda aka yiwa bushara. Kawu Zakari yayi murmushi "mijinki yana da barwanci Radhiya. Ana kirana bari na baku wuri" Sai da ya tafi Awwab ya kalleta "to dai kinji yana da aure matarsa tana shirin haihuwa ta biyu" "Dadin abin nima ina da auren nan and God knows I love my husband" Wani irin kallo yayi mata sai kuma kunyar abinda yayi ta kama shi ya cire hularsa ya rufe fuska tana jin muryarsa sai ka rantse kuka zaiyi "did I just make a fool of myself a gaban crush dinki Alheran?" "Eh mana" itama ta yi kamar kukan zata yi. Hular ya cire ya ajiye a gefe yana murmushi "laifinki ne Schatzi yanzu duk inda na ganshi sai na tuna da wai likita kike so" "Hamma Awwab" ta kira shi bata so ko kadan ya rinka tunanin akwai wani kafinsa ko bayansa don babu. Hannuwanta ya kamo ya rike "na'am" "Kai na fara so kuma kai kadai zan so har abada in sha Allah" tace da wani irin yanayi. Zuciyar Awwab ta sake yi mata wani babban masaukin "Alheran ki sassautawa zuciyata kada sonki yayi mata illa" Bata sake magana ba ta nuna masa abincin. Spoon biyu ta sako amma yaki yarda sai dai suci da daya duk da tana kunya ga iyayensu ko ina amma haka ya tilasta mata suka ci babu magana sai kallo mai cike da ma'anoni. DJ ya soma nasa aikin ana sako wakoki wuri ya kaure sai rawa wurin masu jini a jika. Ana soma wakar Nura M Inuwa ta amarya 'yar amana jikin Radhiya ya fara mazari tana hango 'yan mata musamman na Nijar 'yan uwansu ga Zahra can da Raji ana ta nishadi ta mike tsaye. "Ina zuwa?" Awwab yace jikinsa na bashi rawa zata yi. Wurin rawar ta kalla da ka tayi masa alama. Maltina ya cigaba da sha hankali kwance "zauna Schatzi please" "Hamma manaa" ta langabe kai. "Allah bazaki je kiyi rawa a wurin nan ba" Idanu ta zaro "harda rantsuwa?" "Kinga ya dace?" Juyawa tayi ta hango Yousuf yana cewa Arifah wai zaiyi rawa tazo tayi masa video. Kuka take shirin yi tace "Ka gani fa kowa yana yi" "Mu ba kowa bane. Sunana Awwab sunki Alheran...don't tell me you expect me to seat here and watch you dance a gaban mutane" "To...to..." kasa karasawa tayi sai dai ya sani ran ta ya baci. Dauke kai yayi ta gama kunkunin ta yana tunanin ma harda hawaye amma yaki bari ta tashi saboda indai akan tayi rawa gaban mutane ne ya yarda tayi ta fushin ya rarrasheta daga baya. Tana ji tana gani wakar ta kare aka sako wata Awwab ya tashi dama magrib ta gabato "ki jirani a nan zanje na shigo da mota ciki na kiraki mu tafi" Shan kunu ta sake yi harda kawar da kai gefe ya sunkuyo da kansa wurin kunnenta "you still look sweet" ya yafi. Murmushi tayi duk da ba wai ta hakura bane. To filin rawa ma Zayyana na hada ido da Ibrahim yana zaune da robar ruwa a hannunsa ya sha kunu yana mata nuni da ta fita da hannu. Kafada ta noke ya kuma hade girar sama da kasa dole ta fita tazo wucewa ta gefensa ta murguda masa baki. "Naji dai, rawa ce ban yarda ba" taji yace yana murmushi. Rahima dama bata shiga ba don bata iya ba tayi zamanta sai jakunkunan su Hibbah da Zayyana da su ka bar mata. Karamar wayarta kirar samsung sabuwa mai torchlight ce a hannunta tana game din snake jikinta ya bata kallonta ake yi ta baya. Juyawa tayi a hankali ta ga Emzee yana murmushi. Kujera yaja a kusa da ita ya juyata ya ware dogayen kafafunsa ya zauna ta yadda gabansa ne ke fuskantar bayan kujerar ya dora hannuwa a samanta kansa akan hannuwan. "Kinsan saurin da na rinka yi kuwa da naje raka abokai na?" "Meya faru?" "Kawai waka na jiyo nace Allah Yasa kada Rahiman Muhammad tayi rawa if not tear gas zan saki a wurin nan bayan na kai su Daada gida" "Meye tear gas kuma?" Yadda tayi tambayar kadai yasa shi shagala da kallonta kafin ya yi mata bayani. Kanta a kasa take dariya da yace shi fa kishi gareshi "samarinki nawa ki kawo numbers dinsu yanzu duk na kirasu na fada musu anyi miki miji" "Goma ne ba yawa kasan ba wani farin jini gareni ba" Rahima tayi dariya saboda kafin ta kai karshe ya kusa tuntsirewa daga kan kujera. Gyara zamansa yayi yace yana bata fuska "Kasheni ki huta" Shiru yaji tayi ya kira sunanta bata amsa ba. Tashi yayi ya dawo gabanta ya tsuguna yana leken fuskarta. Hawaye ya gani suna gudu akan fuskar da yake matukar so yaji hankalinsa ya tashi. Ya san iyakarsa ba don haka ba da ya rungumeta ya rarrasheta. "Rahiman Muhammad?" "Uhmm" tace da muryar kuka. "Na bata miki rai ne?" Gyada kai tayi "eh" Zuciyarsa yaji tayi masa nauyi "Ya Salaam me nayi miki?" "Cewa kayi fa na kasheka" ta fashe da kuka sosai. "Oh my God...am sorry kinji wasa nake yi" Soyayyar da suke yiwa juna ba ta wasa bace. Kowa na damuwa da damuwar dan uwansa. Hankalinsa ya tashi da kukanta ita kuma bata kaunar wani abu ya gifta tsakaninsu musamman mutuwa a yanzu da take jin ta samu farinciki irin wanda bata taba tunanin akwai ba. Irin matar da yake mafarkin samu mai shagwaba ya gani a tattare da Rahima saboda yadda take yi da fuska da muryarta "To ka dena cewa in kasheka" "Na dena...ban karawa" Wayar hannunta ya karba ya saka numbarsa yayi dialling layinsa yana cewa "in chanja miki waya?" "A'a wannan ma sabuwa ce. Sai mun gama WAEC za'a bani wata" tace da murmushi tana tuna abinda Ummi tace mata ranar da ta bata wannan din. "Ajinki nawa? No shekarunki nawa kada ace ina koyawa yarinya soyayya fa" Emzee yace yana dariya. "Ajina hudu a primary kuma shekarata 13" Kallonta yayi yasa yatsansa a baki ya ciza "da gaske? 13 amma kika iya kallon soyayya? Wannan idan kika 20 na zama sorry" Rahima sai dariya take irin wadda bai taba gani tayi ba hankalinta a kwance "kuma babana yace kada na kula kowa sai nayi 25" "Ba damuwa nima ba kulaki zanyi ba aurenki kawai zanyi sai ki karasa primary din a gidana" ya amsa mata don ya fuskanci tsokanarsa kuma take yi. Kalmar aure da ya sako ita ta kashe mata baki. Ya samu ta fada masa ainihin shekarunta wato sha shida da ajinta a makaranta. A take yayi mata alkawarin yana yin POP zai fadawa Daada a nema masa aurenta. Ko da wasa Rahima bata kawo cewa Emzee bai san ko ita wacece ba. Dadin hira ya saka shi mantawa da yi mata wannan tambayar tunda ta tabbatar masa da cewa tana nan a gidan sai bayan bikin Radhiya. ********** Wayar ta kalla tana ringing tasan Awwab ne ta kuma tura baki kamar yana wurin sannan ta dauka "fito mu tafi" kawai yace. Tafiyar kurame suka yi zuwa gidan ashe an fara komawa saboda iyayensu maza sun ce a gida za'ayi magriba babu wanda za'a bari a wurin taron. Yasan Yousuf da Arifah zasu tafi yau ma zaiyi rakiya shiyasa bai neme shi ba. Suna zuwa gida sai nishadinsa yake fushinta kamar baya damunsa ya fito ya zagaya ya bude mata itama ta fito. Hannunta ya kama kai tsaye ya wuce falon da su ka je jiya da ita. Wayarsa ya dauko ya bude wakar yar amana ta youtube sannan ya kama mayafinta ya cire ya ajiye akan kujera. "Kinsan wahalar da nasha kafin na sami wakar nan a youtube kuwa? Ni bana gane me suke cewa da kyar naji ance 'yar amana shine na nemo miki" idanunsa ya dora a kanta yana ganin yadda tayi kyau sosai kamar wata 'yar tsana "baby ga 'yar amana ki tashi muyi rawa" Shan kunun ne ya kare ta soma dariya da Awwab yayi playing wakar. "Wai da gaske nemo min kayi Chèri?" "Anything to see your smile Schatzi" ya janyota jikinsa yana shafa gefen fuskarta. Tsigar jikinta ke tashi ta soma rawar jiki ya rungumeta tsam a jikinsa. "Calm down ba yau zan baki tsoron ba ai. Rawa zamuyi kuma bazan bari ki fita a falon nan ba sai kinyi" Sai yanzu take jin kunya sosai "Hammana na tuba kayi hakuri" "Baby I want to see you dance...ba wai don na hanaki ba dazu wannan bazan taba yarda dashi ba amma between us harda kafi rawa zamu rinka yi a gidanmu" "To ai dai nan ba gidanmu bane kayi hakuri" tace ido wiki wiki tana nadamar yi masa gardama don ya hanata rawa. "Tunda ance sai anyi biki zaki tare kowa sai ya rufe ido kawai a barni duk inda kike muna tare" "Naji amma na fasa banda rawa...kunyarka nake ji" Fuskar tausayi yayi "Inje gida inyi kuka?" "A'a" Kashe wakar yayi ya kunna wata ta cikin wayarsa da yake yawan kunnawa idan yana tunaninta lokacin da suka yi fada mai suna You and I. Kidanta cikin taushi yake tashi babu hayaniya ko kadan sai kalmomi masu tasiri a zuciya. Takalmanta ya fara cire mata matsu tsini shima ya cire nasa sai safa. Wani irin riko Awwab yayi mata ya duko da kansa ya hade goshinsu. Hannuwansa na kugunta nata a kafadarsa sun zagaye wuyansa a hankali yace "hau kan kafafuna" Runtse idanunta tayi ta dora kafa daya a hankali tana jira taji ko zaice tayi nauyi ko ta cire sai taji yace "dora dayar" A tsaye take amma akan kafafun mijinta sannu a hankali yake bin kalaman wakar yana fada a saitin kunnenta yayin da yake tafiya a nutse suna takun rawa amma shi yake yin duka motsin. A haka suka kwashe kusan minti hudu bai nuna gajiya ba yana rike da ita suna musayar numfashi har wakar ta kare. "Duk lokacin da kike son yin rawa baby zan tayaki, a gaban wasu ne kawai ban yarda ba saboda ina kishinki. Da sonki na girma a zuciyata kina tunanin akwai ranar da zanso bata miki rai da gangan?" Girgiza kai tayi a hankali kalamansa na shigarta sosai kawai ta rungumeshi tana masa kukan da ake kira na kissa batare da tasan ma'anarsa ba. Idan an barta bata san dalilin hawayen nata ba idan ka cire tsantsar soyayyar Captain Muhammad Awwab Mustapha. Habarta ya dago suna kallon juna ta kasa tsayar da hawayenta. "Kukan na meye?" "I. Love. You Chèri" Kamar jira yake ta fada ya soma kissing dinta sosai. Karatu suka ji alaman an kusa kiran sallah ya dawo dasu duniyar da suke ya shafi gefen fuskarta "Da nasan hanaki rawa ne zai sa naji da kanki kin fada min wadannan kalmomin da na dade da cewa ban yarda da rawa ba" Duka ta kaiwa kirjinsa ya saketa ta dauki takalminta ta saka sannan ta bude jakarta ta fito da janbaki za ta kara sakawa. "Ana kiran sallah za ki sake kwalliya?" Kunya taji tayi saurin mayarwa sai da ya matsa mata tace "Jiya Adda Fauzy cewa tayi wai an shanye min janbaki" "Mata. Mata sai a barku...an fada min kuna zuwa ma ganin tafiyar amare washegarin da aka kaisu ko" yace yana tsareta da ido. Ba karamin rikicewa tayi ba kuwa don babu karya ko ita sun gama JS3 da akayi bikin wata 'yar ajinsu kawayensu suka ce wai azo aje gulma. Da ita aka je din amma babu abinda chanjin tafiyar kawar tasu ya sa mata a rai sai tunanin ko duka mijin yayi mata. A lokacin ta yiwa kanta alkawarin idan tayi aure miji ya kawo mata wargi sai dai su daku don ba kyalewa zata yi yaci zalinta ba. Murmushi ne ya subuce mata da ta tuna lokacin da sharrin kuruciya. Hannuwansa duka ya dora a ka "Na shiga uku kin taba zuwa kenan nima za'a zo mana" Da sauri ta rinka cewa bata je ba yana cewa sai ta fada masa gaskiya. Nan aka fara kiran sallah ya fita kamar ya tafi da ita. Ciki ta wuce ana ta layin alwala a waje mazan ma suna nasu. Gidan sai bayan isha ya dan daidaita inda Daada da su Daddy da iyalansu suka zauna a falonsa suna hira. Mama ce tace ita dai sai ta bude gift din DK daga bangaren da matan suke zaune yaran nasu suka soma murna suna jira a bude. Mami ce ta farke abin suka ga takardu ne a ninke. Ta bude ta karanta tana wani irin murmushi ta mikawa Mama. Ita kam hawaye ne ya zubo mata na farinciki Baba Hadir na kallonsu yace "Zainab?" Da alamar tambaya yaji me ya faru. Ibrahim ta bawa takardun yaje ya mika masa falon yayi shiru sai da ya karanta ya kalli Zayyan. "Yayi. Yawa" ya daure yace shima muryarsa na nuni da taba masa zuciya da abin yayi. "Babu ruwanka da kyautar uba da da kuyi mana addu'a Allah Yasa yaci gajiyarsa." Amin kowa yace ana mamakin Zayyan ya mallakawa Zayyan Hadir gidansa na Kano. Wannan ya biyo bayan dogon nazarinsu shi da Ummi sun san cewa duka sunfi Hadir karfi yanzu kuma Daddy yana da gidan kansa a Katsina. Mama ta karbi na Zayyana ta bude a take su ka bude baki da mamaki. "Zayyan meye haka ne?" Daddy yace yana kallon dankareren saitin gwal din da ya mallakawa Zayyana. Dankunne, sarka hade da zube da manyan abin hannu guda biyu iri daya biyu iri daya na kudi har dubu dari biyar. "Kada ku shiga tsakanina da 'ya'yana ba ku na bawa ba" Mami ta share kwalla tana jinjinawa zumunci irin na Zayyan da matarsa mai goya masa baya. Gift na karshe na Emzee mukullin mota ne sabuwa fil. Zayyan yace "waccan sai ta zama ta Ibrahim shi kadai. Allah Yayi muku albarka 'ya'yana" Saidai ayi ta cewa amin domin babu sauran godiya a tsakanin wadannan iyalin. Kaya Zayyan ya chanja zuwa farare irin na Daddy da Baba Hadir ga matansu kayansu iri daya suka zauna akan 3 sitter mazan a tsaye kowa a bayan matarsa aka dauki hoton tarihi na iyali uku masoyan juna.Dan duka kanta tayi tana lekensa ta sake daga murya "kai shigo mu tafi mana" ta kuma lekawa ta daya bangaren "kema shiga kin yiwa mutane wani kikam" Emzee alama ya yiwa Rahima da ta tsaya don bai ga dalilin daukarta da makiyar Ummi a mota daya ba. Sannan abu na biyu baya son a matsayinta na yayar Ummi tayi abin zubar da mutumci a gaban Rahimansa. Khadi da ke kan cinyar Salame kuma duk maganar da take kusan akan fuskarta tayi sai sa hannu tayi ta toshe hanci babu kunya tana yiwa babarta wani irin kallon haushi "hmmm Umma hmmm wali-wali a bacinci" Da sauri Emzee ya fitar da kansa kafin ya shaka yayin da Salame ta dage ta zabgawa Khadi duka a gadon baya ta fashe da kuka. Rahima ta tafi da sauri ta bude kofar ta daukota Emzee ya yiwa Salame wani disgusting look. Gaban motar ya riga ya fara wani abu sama-sama mara dadin ji ga hakoranta masu kore daga samansu. Sannan abin haushi dubi yadda ta daki karamar yarinya haka. Kayan jikinta kuwa ya rasa abib fada. Shi dai ya tabbatar Ummi ta sasu sayen kaya ready made na mutan Sumaila shi da Ibrahim da Laila suka je. Haushin abinda Ummin ta yi mata dazu shine yasa taki saka kayan wai tafi karfinsu. Khadi 'yar banza ta tasha hannu ba musu ta gudu wurin yayarta ta lafe tana kuka. Jikin Rahima na rawa dreban ya dawo. Ajiyar zuciya Emzee yayi yana kallota ta saman motar. A hankali yayi mata magana yana kallon yadda ta rikice sosai "ki bisu zan taho yanzu okay" Kai ta gyada da sauri ta tafi daya motar tana tsoron kada Salame tayi mata wata maganar ko tace su koma gida. Ita kuma zuciya a baka saboda bacin rai yau rashin m din na Khadi akanta ya kare a gaban wannan yaron na Mairama. Muryarsa taji ya gama goga hannuwansa da juna. "Lets get going Gwaggo" Dauke kai tayi yana ganin dreban yayi waje kawai ya cire hularsa da riga daga shi sai wando da vest. Bayan motar ya ajiye rigarsa da kyau ya dora hular a kanta don kada ta fado ya shiga ya zauna ya daura belt. Salame ta kalle shi tana tunanin dalilinsa na tube riga bata gama sannin me ake ciki ba ya fizgi motar a guje ya fita da ribas sai da cikinta ya kada. Wata irin cin taya yayi da burki yayi kwana tamkar mai shirin zuwa Sumaila a awa guda daga Abuja ya kwashi motar ya hau titi. Gudu yake na karshen rashin hankali sai dai kaji qeeeyyyyy quuuuu....yaci taya ko ya taka burki sai motar tayi kamar za ta hantsila. Salame tana kallon yadda ya murtuke fuska kuma jikinsa baya motsawa amma ita sai dai tayi gaba yif ta dawo baya yif jikinta yana ta mazari. "Kai dan ubanka tafi a hankali ko ka saukeni" Idan motar za ta amsa to Emzee ya amsa. Salame sai da ta kai ta daga hannu za ta doke shi yayi mata wani razanannen kallo tare da taka burkin gaggawa sai ga kanta ya tafi saura kiris ta doki glass. Hannunsa yasa ya tareta don ba jini yake son fitar mata ba. Burinsa ko ta halin kaka ya fanshi wani abu na makantar Ummi na shakara goma. Tsanar Salame ke kara ruri a zuciyarsa zai bincika ya tabbatar da sa hannunta. Idan akwai ko su Ummi basu sani ba da shi da Addarsa sai sun yi mata abinda zata ji rayuwarta tayi kunci. Yanzu haka ranar zuwa Sakkwato biki suke jira shi da Radhiya su barwa Maikudi abinda bazai manta ba. Ba wani abu bane kuma yafi taba zukatansu sai wulakancin da ya yiwa Umminsu ga wahalar haihuwa ga radadin mutuwar miji da taji. Kowa ya sani a Nigeria biyu ga watan junairu ana tsaka da sanyi ne amma banda Salame matar Haji Indararo. Gumi take kashirban tana yiwa Emzee tofin Allah tsine. Lokacin da suka isa wurin yayi sa'ar ganin wata motar na fita yasan zai sami wurin parking. Katinsa ya nuna aka wangale gate ya shiga Salame tana ta numfarfashi. Yana tsayawa ta kama kofa zata fita taji a datse. Ashe harda hawayen wahala tayi bata sani ba cikin fada tace "shegen yaro mai kama da ifiritu bude min" Emzee a soja yake baka ganin wani abu wai shi sani ko sabo a tattare dashi sai murmushin mugunta "kinfi kowa sanin cewar ina da uba mijin kanwarki....ko ince mutumin da kike so?" Ya yi mata wani kallon gefe. Jikin Salame ya bugu saboda tukin da ya yi amma abinda yafi daga mata hankali bai wuce maganar da yayi ba. A ina yaji? Mairama ce ta fada masa ko waye? Karfin hali tayi ta daure fuska. "Rashin kunyar taka har ta kai haka Karami? Irin tarbiyar da Mairama take baku kenan ashe, kun tashi ba ku ganin girman kowa" Juyowa Emzee yayi ya mata wani kallo mai firgitarwa kamaninsa sun sauya gabadaya...soja mazan fama. "Kada ki kuma ambaton sunan Ummina domin tunda take bata taba nakasa dabba ba bare mutum" "Innalillahi wa inna ilaihi rajiun" Salame ta fada a tsorace jikinta yana tsuma baki na rawa "me...me kake nufi? Sharri za ka yi min kace ni na makanta ta?" Sai da kansa ya sara a lokacin domin dama bugun cikinta yayi ya bata tsoro domin jin gaskiyar lamari kuma yaji abinda yake so kafin ma ya tambaya. Duk da yana zargin tabbas ita ce amma yanzu da ya tabbatar sai da abin ya girgiza shi matuka. Ba ya kaunar Salame ko na digon sakan saboda bata cancanci a sota ba. Umminsa tana makance tsayin shekaru Salame tana gidan miji tana ciki da haihuwa taci me kyau tasha me kyau lokacin gwamnatinta na ci a zuciyar Alh Indararo. "Kuruciya tasa ban fahimci me kika yi ba shiyasa ban tona miki asiri ba tun lokacin da kika saka mata...." yace don ya kara tunzurata yana bude dash board. Sabon gumi na yake tsattsafo mata jin sirrin boye da ko da kanta bata zancen a zuci yau Emzee ya bankado shi. Harda sanyi ta rinka ji yana ratsata ya cigaba da lalubensa kamar ba ta cikin motar. Hakoranta sai sarkewa suke yi don tsoro tace "to yanzu kuma uban me kake lalube bayan ka gama yi min sharrin" "Bindiga" Idanunta kamar zasu fado karshen tsoro ta kai sannan ga uwa uba wani mahaukacin zawo da ya matsota saboda tsoro. "An...an. fada. Maka idan...idan ka kasheni. Mairama zata yi murna ne?" Bude pin din motar yayi "kin zata harbinki zanyi? Allah Ya kiyaye ba'ayi min wannan tarbiyar ba" Budewa tayi da sauri ya leka da kansa ta inda ta tashi "uhmm nace ba....nagode da kika tabbatar min da zargina akan waye ya makanta min uwa" Salame sai bude baki tayi tana masa kallon tsananin mamaki shi kuwa ya zura hannu ya janyo kofar ya rufe ta bangaren da take sannan ya kifa kai akan sitiyari yana kokarin mayarda hawayen bakincikin da suke neman zuwar masa. Dago kai yayi ya nemi wayarsa sai ya ga har lokacin tana tsaye. Da kallo daya ya karasa razana ta ta wuce ciki wurin da ake ta karbar baki za'a fara abinda ya tara jama'a. Yau ranar farinciki ce dole ya saita kansa. Ibrahim ya kira bugu daya ya dauka. "Bro turo min Rahima" yace da wata iron murya can kasa. "Bangane ba. Ba tare kuke ba?" Zai sake magana ya hangota tare da Zayyana zasu zauna "kana ina ne na ganta" Kwatanta masa inda yayi parking Emzee yayi Ibrahim yaje inda suke ya fadawa Zayyana ita kuma ta fada mata. Tana tashi bayan ta ajiye Khadi akan kujerarta ta hango Salame amma da ta ga hankalinta baya gareta sai ta wuce ta tafi. Ya gama saka rigarsa kenan yana gyara zaman hular a kansa ta bullo. Shagala Emzee yayi da yadda Rahima take tafiya cikin nutsuwa. Yanayin da ya shiga mai wuyar fassara soyayyarta ta mamaye masa kowane lungu da sako na zuciyarsa. Duk kunya ta isheta saboda yadda ya kafeta da ido har ta karaso. "Mu zauna a nan ko mu shiga ciki?" Yace yana fatan ta amince su zauna. "Za'a nemeka ai" "Okay muje" sun fara tafiya ya ga dacewar ya bata hakuri akan abinda yayar mahaifiyarsa tayi musu "Rahima kiyi hakuri akan abinda ya faru dazu. Na saka ki zaman jirana kuma bani na kawoki ba" Ita da tasan mahaifiyarta ce tayi sai tayi saurin cewa "ni ya kamata na baka hakuri" "Akan me? For being a good girl me jin maganarrr.....maganar wa dinki kika ji?" Ya zuba mata idanu. Murmushi tayi kanta a kasa "Ya Emzee?" "Nope" tsayuwa yayi ya hanata tafiya "Rahima wane matsayi kika bani?" Kasa magana tayi tambayar tayi mata nauyi duk da amsarta tana jin tamkar ta amayo masa ita ne ko za ta sami saukin wannan soyayya da tayi mata mugun kamu. Kamar yayi mata kuka saboda taki magana "gobe zan koma Kaduna da sassafe. Please Rahima ki fada min ni waye a gareki kafin na tafi....idan ba haka ba retire zanyi tun kafin na fara aikin na dawo ga filin yaki nan in your beautiful eyes muyi ta fafatawa." Zuwa yanzu ko fuskarta baya iya gani ta shige cikin mayafin ta rufe kanta gabadaya sai murmushi kawai take yi. Da kyar ta iya cewa "ni wa dinka ce to?" "My heart..." yace da sauri "ke fa?" Babu wanda zai wuce ya gansu baiyi musu kallo na biyu ba. Kana ganinsu ka ga masoyan da suka mutu akan juna kuma suka dace sosai da juna. Emzee fari ne kamar yayarsa ga kyau ga jikin matashin soja. Rahima kuwa baka ce fatarta tafi kama da wankan tawarda don da kadan Zayyana ta fita haske. Kyakkyawa ce sosai tafi Halifa da sauran 'ya'yan Salame nesa ba kusa ba sai dai su nuna mata haske. Round shaped eyes dinta sunfi komai daukar hankali akan fuskarta. Kamaninta sosai da kakarta Iya shiyasa take ji da ita. "Kinyi shiru Rahiman Muhammad" Sautin loudspeaker suka ji za'a bude taron da addu'a Rahima ta daure tace "to me kake so nace Muhammadun Rahima?" Murmushinsa dariyar farinciki ya koma yana kallonta da adoration "kince komai....realy? Kin yarda Muhammadun Rahima ne ni? Daga ni fa babu kari" Dariya tayi ta cikin mayafin tana gyada kai. Zuciyar Emzee ta cika da soyayyar kanwarsa da bai san suna da alaka ba ko kadan. Da sauri sauri suka karasa hall din za ta wuce bangaren mata ya bi bayanta da sauri yana maida numfashi tamkar wanda yayi tsere taji yace "Ina sonki Rahiman Muhammad" Juyowa tayi suka hada ido kowa da kayataccen murmushi a saman fuskarsa sannan suka nemi wurin zama. ********** Taro ya soma kankama bayan addu'o'i da mika godiya ga Allah mai gabatarwa Ibrahim Hadir ya gabatar da manyan baki na musamman. Ba kowa bane illa manyan aminai 'yan uwa ga Zayyan kowa da matarsa. Excellency baban Arifah, Major Daddy, Baba Hadir sai kuma Tante da mijinta mahaifin Yousuf. Wadannan mutane kowannensu ya taka muhimmiyar rawa a rayuwar iyalin Zayyan shiyasa idan suna ganin ya kyautata musu wurin ceton rayuwarsu ya kan ce babu kyautatawa mafi tsada da daraja sai wadda za kayi a bayan idon mutum idan ya mutu. Wannan kyautatawar kayi ta ne ba don ganin ido ba bare kasa ran a saka maka. A gefe guda ga duka 'yan uwan Zayyan mata uku da maza biyu domin Maikudi bazai taba iya zuwa ba duk da Zayyan ya bukaci hakan. To da wane ido zai kalli su Mairama, Daddy da har yau bai manta kalar bacin ran da ya gani a idanunsa ba, da uban gayya Zayyan wanda ya mare shi. Ya kure Zayyan iyakar kurewa kuma ya tabbatar abinda yayi musu bazai taba gogewa a zukatansu ba. Son zuciya da kwadayi ya mayar dashi mujiya a cikin ahalinsa. Yana ji yana gani sai dai yayi ta dari dari dasu domin tsanarsa da yake gani a idanunsu. Captain Onomza shima yazo ga jama'ar Rugar Barkindo, na gidan Malamijo da abokan arziki. Sannan mutumin da Zayyan ya dauka da matukar mahimmanci a rayuwarsa wato Chibuzor da matarsa da 'yarsu su ma kayan jikinsu irin na wadanda su ka yi ankon fari da green din. Sai kuma Maman Dolapo da Christie ma sun zo kafin shigowar Emzee suka share hawayensu dasu Mama. Ga Alh Salisu da nasa iyalin abin sai son barka. Ibrahim ne yake magana da turanci da hausa domin kowa ya fahimta ya sanar da cewa akwai gajeren wasa da abokan Emzee zasu gabatar mai taken A Soldier's Dream (Burin Soja). Drama ce mai kayatarwa wadda ta janyo wurin yayi shiru aka zuba musu idanu daga kan stage. Sojoji ne rataye da bindiga da 'yan jakunkunansu sunyi shirin tafiya filin daga. Gefe guda matansu da iyayensu suna ta kuka da yara. Idan ka ga yadda suke gabatar da dramar da matukar ban tausayi. Sun rabu da iyali suna ta kuka sannan sunje yakin an kashe da yawansu. Nan ma wurin dawowarsu mata da yawa suka rinka suma duk wadda ta ga babu mijinta. Mutane kuwa sai share hawaye domin an shigar dasu cikin rayuwar da basu santa ba kuma a da babu wanda yake damuwa da sanin nata. Da dramar ta kare Radhiya ma duk yadda ta ga abubuwa a Military Voice lokacin da suke dauka sai da tayi wani kukan. Bayan an gama tafa musu Ibrahim ya bukaci wadanda ake taro dominsu su hadu wuri daya. Zayyana dauke da DK wanda kayansa harda hula babu bambanci da na Daada da Emzee anyi masa komai dan karami daidai da jikinsa suka je wurin Daada. Wani envelop da Ummi tayi wrapping mai dan tudu Zayyan ya daga hannun DK da yake jikin Zayyan ya dora masa a kirjinsa. "This is for you my son" Su Daddy suna kallo babu wanda yasan menene a ciki. Wani ya sake daukowa ya fi wancan girma da dan nauyi ya mikawa Zayyana. "Kallabi tsakanin rawuna Zayyanatun Zayyan ga naki" Sai da ta rissina tace "Allah Ya kara budi Daada Ya saka da alkhairi" "Amin" su Excellency suka ce suna murmushi. Wani dan karami sosai Zayyan ya mikawa Emzee "Soja dan sojoji kaima ga naka" Godiya yayi sosai shima aka fara daukarsu a hotuna sannan kamar hadin baki aka shiga miko musu gifts kowa da abinda yake badawa. Family picture aka tashi dauka aka hada iyalan Zayyan, Daddy, Baba Hadir, Excellency duka wasu a tsaye wasu a durkushe. Zayyan ya dan gama waigensa ya hango Chibuzor ya kira shi da hannu shi da matarsa. "Sir this is a family picture" yace yana sake ja da baya. "You are my family Chibuzor" Zayyan yace yana yi masa murmushi tare da nuna masa inda zasu tsaya kusa da sauran yaran nasu. Chibuzor bai taba tunanin karamcin Zayyan ya kai haka ba. Yana da masaniyar yadda addini da yare ke kawo tawayar kyakkyawar alaka a tsakanin 'yan Nigeria amma ga wani babban soja masoyi ga mutane da dama ya rungumi kowa hannu bibbiyu. An gama hotuna aka fara cin abinci wanda yake serve yourself anyi shi a wadace kowa yaci ya koshi. Duk wannan abu da akeyi Salame tana rakube ko motsin kirki bata son yi saboda ko yaya ta ga giftawar Emzee sai cikinta ya duri ruwa. Yanzu idan ya bude baki a wurin nan ko kafin ta koma Sumaila ta kade har ganyenta don bata san me zasu yi mata ba. Ana yiwa Zayyan kallon mai kirki amma tana da yakinin cewa ba karamin mataki zai dauka akanta ba. Kallon kowa take yi daidai ana ta shagali wannan na hira da wannan, wancan da waccan amma babu wanda ya rabeta...abin bakinciki shine harda 'ya'yan cikinta. Idan Rahima ta gudu saboda yadda take takura mata meye dalilin Halifa da Khadi? Shi dai bai tsaneta ba amma baya kaunar halayenta ko kadan. Khadi kuma yarinya ce da ta goge a rashin kunya amma yau fushin nata saboda ta doketa ne. Salame sai ta ji ta very, very lonely abin ya tabata fiye da zato da tsammani. Kamar ance ta daga kai su ka hada ido da Mairama. Tun dazu da take gaisawa da mutane hankalinta yake kan Addarta. Yadda ta zauna ita kadai a table din mutum takwas an wareta kamar babu ita a wurin itama sai taji babu dadi. Fushin da take yi na kudin Rahima da ta karba dazu ya gushe. Murmushi tayi da su ka hada ido a karo na biyu sannan da hannu ta nuna mata inda ake dibar abinci. Wai don kada a rainata sai ta dauke kai ta juya mata keya. Ashe Mama na kallonsu ta tuntsire da dariya. "Oh ni Zainabu Abu inama ina da 'yar uwa mace muma mu hau sama mu fado." "Haka ma zaki ce?" Mami tace tana murmushi. "Abin naku ne kamar hadin baki. Kina yi dasu Gambo gefe daya ga Salame suna bugawa da Mairama" Ummi ta sake kallon Salame "babu abu mara dadi kamar ace kai da 'yan uwanka bakwa jituwa. Yawanci kuma duk sai ki ga hassada ta fi komai ruguza mana zumunci" "Ni zan fada muku haka don ina da tabbacin Hussaina da tayi ta ingiza rikicinmu da Gambo ba wani abu bane ya tunzuruta sai ganin wai muna da kudi mun wareta" Mami tace tana tuno bacin ranta. "Amma dai dan Adam babu godiyar Allah. Sai ki ga muyi ta takurawa kanmu domin mu kyautata musu amma basa gani" cewar Mama Mami ta mike "Yo ina kudin yake banda dai ana yiwa rogo kallon kitse. Kunga ni mijina bai ci komai ba yau tun safe kuma na ga mazajenku sun saka shi a gaba da hira ku taimaka kuyi musu signal ko su tashi ko na zuba masa shi kadai" Ummi da Mama suka sa dariya Mama tace "yayi matar Major Allah Ya bar mana ke. Ana kwasar jikokin ma ashe a gefe ana ta dabbaka kauna" Dariya Zainab ta basu suka mike tare kowacce ta zubawa mijinta abinda tasan yana so. Ummi na kai wa Daada nasa ta koma ta zuba fried sphagetti da wani sauce din naman sa da albasa, attaruhu da koren tattasai an yanka su manya manya, naman kuma dogo a tsaye ta hada da potato salad ta tafi mazaunin Salame. Ajiye mata tayi ta zauna a daya daga cikin kujerun. "Meye wannan za ki wani turo min abinci" ta sha kunu Ummi ma daure fuska tayi ta ja plate din "idan ba kya so sai na dauke" Da sauri Salame ta janye yawunta ya gama tsinkewa "barshi dai....kada kiyi zaton zanci da dadin rai ne don dai kawai ba kyau wulakanta abinci ne. Kuma ga bakinku ana kallonmu kada na kunyata uwar gayya Mairama matar Zayyan mai kudi" Ummi gimtse dariya kawai tayi tana ganin yadda idanun Salame suke walainiya akan plate din. "Bari na baki wuri kici" Wani iri Salame taji bata so ta tashi amma bazata nuna ba "haka kika iya dama naki bola wasu can bare sun fimu matsayi." "In zauna kenan kike nufi?" Ummi tace a ranta kuwa dariya ce fal take dannewa. Baki fal da taliya da nama Salame tace "In kin so tunda ai ba sai kin nunawa duniya bama shiri ba" A zuci Ummi tace "da baki girmeni ba da nace baki da kunya ma...kina so kina kaiwa kasuwa" A can kujerun karshe daga bari daya Yousuf ne da Awwab suke hira duk yawanci akan bikinsu ne da shirin da su ka tanadar masa. Dinner din da zasuyi basa bukatar taimakon iyaye da kudinsu suke son yi gasu duka babu wanda ya waye da harkar biki a Nigeria. "Ka bari idan mun koma gida muyi maganar da Bilal tunda shi dan gari ne" inji Yousuf "To shikenan. Yanzu dai shawara nake nema. Ina tunanin sayen mota amma kuma Alheran da zan barwa idan na tafi aiki itama ba zama zata yi ba." "Kawai ka barshi sai ta gama ta dawo nan din kunyi settling sai ka saya idan ba haka ba wa zaku barwa? Tunda akwai motocin nan a gida kawai ka bari" Arifah su ka gani ta nufosu da plates biyu Yousuf yayi saurin tashi ya karbo suka koma wani table din yana yiwa Awwab gwalo wai ga inda ake kula da miji. Arifah kunya taji ta kai masa duka a hannu ya rike hannun yana kallonta kamar su bar wurin nan ya samu damar nuna mata soyayya. "Ehemm da mutum a nan dai...albarkacin kanwata bari na baku wuri" Tashi yayi ya fara tafiya Radhiya ta kira shi kamar tasan ita zai nema. Tambayarsa tayi ina yake ya fada mata sai gata da plate guda daya da robar maltina. "I am starving Hammana" "Me yasa kike zama da yunwa" yace yana gyara mata kujera ta zauna. "To ba kaine nake ta nema ba muci" tace tare da turo baki. Bakin yake kallo yana lumshe idanu "kici abincin ni kuma ki bani bakin cin abinci yunwarsa nake ji" Kunya Radhiya taji har ta rasa inda zata sa kanta. Awwab kuwa yadda take yi ga dimple dinta yana ta shigewa ya burgeshi sai da yasa hannunsa a wurin. "I love this...." kanta ta sunkuyar yasa hannu ya rike kunnuwansa "sorry baby ina takura miki ko? Lets eat amma kinsan bazan ci na bakinki ba ko" ya kashe mata ido. Bata fuska tayi "Ewwwww ka zama kazami dai" "Kinga laifina an aura min ke" Hannuwa ta nade a kirji tana cika tana batsewa yana mata dariya. Kawu Zakari ta hango ai kuwa ta daga masa hannu tana dariya za ta rama. "Kawu Zakari tun dazu nake ta nemanka" Fuskar Awwab ba shiri ta sauya ya bata rai kamar wanda aka yiwa duka. Yau dai ya ga wannan Kawu Zakarin. Dan kyakkyawan bafillatani ya karaso ya mikawa Awwab hannu. Radhiya sai sakin murmushi take sai da ta ga Awwab ya koma abin tausayi ta dena jansa da hira. "Me yasa baka zo Antyn tamu ba ne?" "Tayi nauyi bana so ta wahala" Ba kunya Awwab ya saki fuska "ashe kayi aure" "Eh muna da yaro daya ma ga na biyu a hanya" Kawu Zakari yayi murmushi. "Kai Madallah wannan abu yayi kyau Allah Ya bar kowa da masoyinsa" Awwab yayi maganar farinciki ya mamaye fuskarsa abin dariya. Radhiya tana dariya harda hawaye don yanayin relief din da ta gani akan fuskar Awwab kamar wanda aka yiwa bushara. Kawu Zakari yayi murmushi "mijinki yana da barwanci Radhiya. Ana kirana bari na baku wuri" Sai da ya tafi Awwab ya kalleta "to dai kinji yana da aure matarsa tana shirin haihuwa ta biyu" "Dadin abin nima ina da auren nan and God knows I love my husband" Wani irin kallo yayi mata sai kuma kunyar abinda yayi ta kama shi ya cire hularsa ya rufe fuska tana jin muryarsa sai ka rantse kuka zaiyi "did I just make a fool of myself a gaban crush dinki Alheran?" "Eh mana" itama ta yi kamar kukan zata yi. Hular ya cire ya ajiye a gefe yana murmushi "laifinki ne Schatzi yanzu duk inda na ganshi sai na tuna da wai likita kike so" "Hamma Awwab" ta kira shi bata so ko kadan ya rinka tunanin akwai wani kafinsa ko bayansa don babu. Hannuwanta ya kamo ya rike "na'am" "Kai na fara so kuma kai kadai zan so har abada in sha Allah" tace da wani irin yanayi. Zuciyar Awwab ta sake yi mata wani babban masaukin "Alheran ki sassautawa zuciyata kada sonki yayi mata illa" Bata sake magana ba ta nuna masa abincin. Spoon biyu ta sako amma yaki yarda sai dai suci da daya duk da tana kunya ga iyayensu ko ina amma haka ya tilasta mata suka ci babu magana sai kallo mai cike da ma'anoni. DJ ya soma nasa aikin ana sako wakoki wuri ya kaure sai rawa wurin masu jini a jika. Ana soma wakar Nura M Inuwa ta amarya 'yar amana jikin Radhiya ya fara mazari tana hango 'yan mata musamman na Nijar 'yan uwansu ga Zahra can da Raji ana ta nishadi ta mike tsaye. "Ina zuwa?" Awwab yace jikinsa na bashi rawa zata yi. Wurin rawar ta kalla da ka tayi masa alama. Maltina ya cigaba da sha hankali kwance "zauna Schatzi please" "Hamma manaa" ta langabe kai. "Allah bazaki je kiyi rawa a wurin nan ba" Idanu ta zaro "harda rantsuwa?" "Kinga ya dace?" Juyawa tayi ta hango Yousuf yana cewa Arifah wai zaiyi rawa tazo tayi masa video. Kuka take shirin yi tace "Ka gani fa kowa yana yi" "Mu ba kowa bane. Sunana Awwab sunki Alheran...don't tell me you expect me to seat here and watch you dance a gaban mutane" "To...to..." kasa karasawa tayi sai dai ya sani ran ta ya baci. Dauke kai yayi ta gama kunkunin ta yana tunanin ma harda hawaye amma yaki bari ta tashi saboda indai akan tayi rawa gaban mutane ne ya yarda tayi ta fushin ya rarrasheta daga baya. Tana ji tana gani wakar ta kare aka sako wata Awwab ya tashi dama magrib ta gabato "ki jirani a nan zanje na shigo da mota ciki na kiraki mu tafi" Shan kunu ta sake yi harda kawar da kai gefe ya sunkuyo da kansa wurin kunnenta "you still look sweet" ya yafi. Murmushi tayi duk da ba wai ta hakura bane. To filin rawa ma Zayyana na hada ido da Ibrahim yana zaune da robar ruwa a hannunsa ya sha kunu yana mata nuni da ta fita da hannu. Kafada ta noke ya kuma hade girar sama da kasa dole ta fita tazo wucewa ta gefensa ta murguda masa baki. "Naji dai, rawa ce ban yarda ba" taji yace yana murmushi. Rahima dama bata shiga ba don bata iya ba tayi zamanta sai jakunkunan su Hibbah da Zayyana da su ka bar mata. Karamar wayarta kirar samsung sabuwa mai torchlight ce a hannunta tana game din snake jikinta ya bata kallonta ake yi ta baya. Juyawa tayi a hankali ta ga Emzee yana murmushi. Kujera yaja a kusa da ita ya juyata ya ware dogayen kafafunsa ya zauna ta yadda gabansa ne ke fuskantar bayan kujerar ya dora hannuwa a samanta kansa akan hannuwan. "Kinsan saurin da na rinka yi kuwa da naje raka abokai na?" "Meya faru?" "Kawai waka na jiyo nace Allah Yasa kada Rahiman Muhammad tayi rawa if not tear gas zan saki a wurin nan bayan na kai su Daada gida" "Meye tear gas kuma?" Yadda tayi tambayar kadai yasa shi shagala da kallonta kafin ya yi mata bayani. Kanta a kasa take dariya da yace shi fa kishi gareshi "samarinki nawa ki kawo numbers dinsu yanzu duk na kirasu na fada musu anyi miki miji" "Goma ne ba yawa kasan ba wani farin jini gareni ba" Rahima tayi dariya saboda kafin ta kai karshe ya kusa tuntsirewa daga kan kujera. Gyara zamansa yayi yace yana bata fuska "Kasheni ki huta" Shiru yaji tayi ya kira sunanta bata amsa ba. Tashi yayi ya dawo gabanta ya tsuguna yana leken fuskarta. Hawaye ya gani suna gudu akan fuskar da yake matukar so yaji hankalinsa ya tashi. Ya san iyakarsa ba don haka ba da ya rungumeta ya rarrasheta. "Rahiman Muhammad?" "Uhmm" tace da muryar kuka. "Na bata miki rai ne?" Gyada kai tayi "eh" Zuciyarsa yaji tayi masa nauyi "Ya Salaam me nayi miki?" "Cewa kayi fa na kasheka" ta fashe da kuka sosai. "Oh my God...am sorry kinji wasa nake yi" Soyayyar da suke yiwa juna ba ta wasa bace. Kowa na damuwa da damuwar dan uwansa. Hankalinsa ya tashi da kukanta ita kuma bata kaunar wani abu ya gifta tsakaninsu musamman mutuwa a yanzu da take jin ta samu farinciki irin wanda bata taba tunanin akwai ba. Irin matar da yake mafarkin samu mai shagwaba ya gani a tattare da Rahima saboda yadda take yi da fuska da muryarta "To ka dena cewa in kasheka" "Na dena...ban karawa" Wayar hannunta ya karba ya saka numbarsa yayi dialling layinsa yana cewa "in chanja miki waya?" "A'a wannan ma sabuwa ce. Sai mun gama WAEC za'a bani wata" tace da murmushi tana tuna abinda Ummi tace mata ranar da ta bata wannan din. "Ajinki nawa? No shekarunki nawa kada ace ina koyawa yarinya soyayya fa" Emzee yace yana dariya. "Ajina hudu a primary kuma shekarata 13" Kallonta yayi yasa yatsansa a baki ya ciza "da gaske? 13 amma kika iya kallon soyayya? Wannan idan kika 20 na zama sorry" Rahima sai dariya take irin wadda bai taba gani tayi ba hankalinta a kwance "kuma babana yace kada na kula kowa sai nayi 25" "Ba damuwa nima ba kulaki zanyi ba aurenki kawai zanyi sai ki karasa primary din a gidana" ya amsa mata don ya fuskanci tsokanarsa kuma take yi. Kalmar aure da ya sako ita ta kashe mata baki. Ya samu ta fada masa ainihin shekarunta wato sha shida da ajinta a makaranta. A take yayi mata alkawarin yana yin POP zai fadawa Daada a nema masa aurenta. Ko da wasa Rahima bata kawo cewa Emzee bai san ko ita wacece ba. Dadin hira ya saka shi mantawa da yi mata wannan tambayar tunda ta tabbatar masa da cewa tana nan a gidan sai bayan bikin Radhiya. ********** Wayar ta kalla tana ringing tasan Awwab ne ta kuma tura baki kamar yana wurin sannan ta dauka "fito mu tafi" kawai yace. Tafiyar kurame suka yi zuwa gidan ashe an fara komawa saboda iyayensu maza sun ce a gida za'ayi magriba babu wanda za'a bari a wurin taron. Yasan Yousuf da Arifah zasu tafi yau ma zaiyi rakiya shiyasa bai neme shi ba. Suna zuwa gida sai nishadinsa yake fushinta kamar baya damunsa ya fito ya zagaya ya bude mata itama ta fito. Hannunta ya kama kai tsaye ya wuce falon da su ka je jiya da ita. Wayarsa ya dauko ya bude wakar yar amana ta youtube sannan ya kama mayafinta ya cire ya ajiye akan kujera. "Kinsan wahalar da nasha kafin na sami wakar nan a youtube kuwa? Ni bana gane me suke cewa da kyar naji ance 'yar amana shine na nemo miki" idanunsa ya dora a kanta yana ganin yadda tayi kyau sosai kamar wata 'yar tsana "baby ga 'yar amana ki tashi muyi rawa" Shan kunun ne ya kare ta soma dariya da Awwab yayi playing wakar. "Wai da gaske nemo min kayi Chèri?" "Anything to see your smile Schatzi" ya janyota jikinsa yana shafa gefen fuskarta. Tsigar jikinta ke tashi ta soma rawar jiki ya rungumeta tsam a jikinsa. "Calm down ba yau zan baki tsoron ba ai. Rawa zamuyi kuma bazan bari ki fita a falon nan ba sai kinyi" Sai yanzu take jin kunya sosai "Hammana na tuba kayi hakuri" "Baby I want to see you dance...ba wai don na hanaki ba dazu wannan bazan taba yarda dashi ba amma between us harda kafi rawa zamu rinka yi a gidanmu" "To ai dai nan ba gidanmu bane kayi hakuri" tace ido wiki wiki tana nadamar yi masa gardama don ya hanata rawa. "Tunda ance sai anyi biki zaki tare kowa sai ya rufe ido kawai a barni duk inda kike muna tare" "Naji amma na fasa banda rawa...kunyarka nake ji" Fuskar tausayi yayi "Inje gida inyi kuka?" "A'a" Kashe wakar yayi ya kunna wata ta cikin wayarsa da yake yawan kunnawa idan yana tunaninta lokacin da suka yi fada mai suna You and I. Kidanta cikin taushi yake tashi babu hayaniya ko kadan sai kalmomi masu tasiri a zuciya. Takalmanta ya fara cire mata matsu tsini shima ya cire nasa sai safa. Wani irin riko Awwab yayi mata ya duko da kansa ya hade goshinsu. Hannuwansa na kugunta nata a kafadarsa sun zagaye wuyansa a hankali yace "hau kan kafafuna" Runtse idanunta tayi ta dora kafa daya a hankali tana jira taji ko zaice tayi nauyi ko ta cire sai taji yace "dora dayar" A tsaye take amma akan kafafun mijinta sannu a hankali yake bin kalaman wakar yana fada a saitin kunnenta yayin da yake tafiya a nutse suna takun rawa amma shi yake yin duka motsin. A haka suka kwashe kusan minti hudu bai nuna gajiya ba yana rike da ita suna musayar numfashi har wakar ta kare. "Duk lokacin da kike son yin rawa baby zan tayaki, a gaban wasu ne kawai ban yarda ba saboda ina kishinki. Da sonki na girma a zuciyata kina tunanin akwai ranar da zanso bata miki rai da gangan?" Girgiza kai tayi a hankali kalamansa na shigarta sosai kawai ta rungumeshi tana masa kukan da ake kira na kissa batare da tasan ma'anarsa ba. Idan an barta bata san dalilin hawayen nata ba idan ka cire tsantsar soyayyar Captain Muhammad Awwab Mustapha. Habarta ya dago suna kallon juna ta kasa tsayar da hawayenta. "Kukan na meye?" "I. Love. You Chèri" Kamar jira yake ta fada ya soma kissing dinta sosai. Karatu suka ji alaman an kusa kiran sallah ya dawo dasu duniyar da suke ya shafi gefen fuskarta "Da nasan hanaki rawa ne zai sa naji da kanki kin fada min wadannan kalmomin da na dade da cewa ban yarda da rawa ba" Duka ta kaiwa kirjinsa ya saketa ta dauki takalminta ta saka sannan ta bude jakarta ta fito da janbaki za ta kara sakawa. "Ana kiran sallah za ki sake kwalliya?" Kunya taji tayi saurin mayarwa sai da ya matsa mata tace "Jiya Adda Fauzy cewa tayi wai an shanye min janbaki" "Mata. Mata sai a barku...an fada min kuna zuwa ma ganin tafiyar amare washegarin da aka kaisu ko" yace yana tsareta da ido. Ba karamin rikicewa tayi ba kuwa don babu karya ko ita sun gama JS3 da akayi bikin wata 'yar ajinsu kawayensu suka ce wai azo aje gulma. Da ita aka je din amma babu abinda chanjin tafiyar kawar tasu ya sa mata a rai sai tunanin ko duka mijin yayi mata. A lokacin ta yiwa kanta alkawarin idan tayi aure miji ya kawo mata wargi sai dai su daku don ba kyalewa zata yi yaci zalinta ba. Murmushi ne ya subuce mata da ta tuna lokacin da sharrin kuruciya. Hannuwansa duka ya dora a ka "Na shiga uku kin taba zuwa kenan nima za'a zo mana" Da sauri ta rinka cewa bata je ba yana cewa sai ta fada masa gaskiya. Nan aka fara kiran sallah ya fita kamar ya tafi da ita. Ciki ta wuce ana ta layin alwala a waje mazan ma suna nasu. Gidan sai bayan isha ya dan daidaita inda Daada da su Daddy da iyalansu suka zauna a falonsa suna hira. Mama ce tace ita dai sai ta bude gift din DK daga bangaren da matan suke zaune yaran nasu suka soma murna suna jira a bude. Mami ce ta farke abin suka ga takardu ne a ninke. Ta bude ta karanta tana wani irin murmushi ta mikawa Mama. Ita kam hawaye ne ya zubo mata na farinciki Baba Hadir na kallonsu yace "Zainab?" Da alamar tambaya yaji me ya faru. Ibrahim ta bawa takardun yaje ya mika masa falon yayi shiru sai da ya karanta ya kalli Zayyan. "Yayi. Yawa" ya daure yace shima muryarsa na nuni da taba masa zuciya da abin yayi. "Babu ruwanka da kyautar uba da da kuyi mana addu'a Allah Yasa yaci gajiyarsa." Amin kowa yace ana mamakin Zayyan ya mallakawa Zayyan Hadir gidansa na Kano. Wannan ya biyo bayan dogon nazarinsu shi da Ummi sun san cewa duka sunfi Hadir karfi yanzu kuma Daddy yana da gidan kansa a Katsina. Mama ta karbi na Zayyana ta bude a take su ka bude baki da mamaki. "Zayyan meye haka ne?" Daddy yace yana kallon dankareren saitin gwal din da ya mallakawa Zayyana. Dankunne, sarka hade da zube da manyan abin hannu guda biyu iri daya biyu iri daya na kudi har dubu dari biyar. "Kada ku shiga tsakanina da 'ya'yana ba ku na bawa ba" Mami ta share kwalla tana jinjinawa zumunci irin na Zayyan da matarsa mai goya masa baya. Gift na karshe na Emzee mukullin mota ne sabuwa fil. Zayyan yace "waccan sai ta zama ta Ibrahim shi kadai. Allah Yayi muku albarka 'ya'yana" Saidai ayi ta cewa amin domin babu sauran godiya a tsakanin wadannan iyalin. Kaya Zayyan ya chanja zuwa farare irin na Daddy da Baba Hadir ga matansu kayansu iri daya suka zauna akan 3 sitter mazan a tsaye kowa a bayan matarsa aka dauki hoton tarihi na iyali uku masoyan juna. [11/2, 7:46 AM]🏽 ]🏽 : 57. 💕 Washegari kafin a kira assalatu Emzee ya gama shirinsa. Ana kiran sallah yayi tare da Daada a nan wurin masu gadi sannan yace zai tafi. "Ba ka ci komai ba Zayyan, Umminka bazata ji dadi ba" Agogonsa ya kalla "Daada so nake kafin 9 ina cikin NDA in sha Allah" Addu'a da fatan alkhairi Zayyan ya yiwa dansa suna jiran karasowar Ibrahim ya kaishi tasha saboda ba a gidan ya kwana ba. Kan wasu kujeru masu kyau daga gefen kofa suka zauna suna hira irin ta uba da da gwanin ban sha'awa. Ummi ce ta fito sanye da hijabi akan doguwar rigar baccinta da ta daura zani ta ciki da tray yana ta turiri ta taho inda suke. "Inata saurin kada ka tafi ba ka ci komai ba. Ungo kuma ban yarda ka rage ba" Indomie ce guda biyu da daffafen kwai biyu sai kofin orange juice mai sanyi. Tasan halinsa baya shan abu mai zafi da safe sai dare. "Wayyo Ummi kinsan bana iya cin abinci da sassafe" yace yana kallon Daada yana neman agaji. Daure fuska tayi "baka isa ba kuwa, ina fitowa kitchen na hadu da Rahima a falo ina jin ma ruwa ta fito sha idonta alamun bacci bai isheta ba amma ta karbi girkin tayi kuma kace na mayar" Karba yayi da sauri bai gama jin me take cewa ba ya soma ci yana murmushi. Rankwashi ta sakar masa tana zaune akan kujerar da Zayyan ya tashi ya koma bayanta ya tsaya. Kuma ya hana Emzee tashi ya dauko masa wata. Ya kusa cinyewa suna ta masa tsiyar dama da yunwar Ibrahim ya shigo. Kafin yayi parking Zayyan ya duku kansa tsakanin Ummi da Emzee. "Jama'a wai ni yaushe zaku koya min mota ne? Da kunya fa ace Zayyan Tureta bai iya dan murza sitiyarin nan da kowa keyi ba" Me kuwa zasu yi banda dariya shi kuwa ya cukule yana cewa a motar Emzee zai koya yadda zaiji dadin bubbugeta kuma bazai ba da kudin gyara ba. Ibrahim yana karasowa bayan ya gaishesu ya karbe fork din hannun Emzee wai zaici. Emzee ya damke hannun ya hana shi. "Yanzu ko loma daya bazan samu ba?" A daidai kunnensa Emzee yace "Idan ka dawo Zayyana ta dafa maka" Yana jin haka ya gane wace ta dafa ya tasa Emzee a gaba karshe a tsaye ya karasa ci yana ta juya baya Daada da Ummi suna cewa da mai kwadayi da mai rowa. Cikin sauri sauri su ka bar gidan Ibrahim ya ajiye shi ya dawo. A hanya ya turawa Rahima text yana godiya da girkin da tayi masa da rokon kada ta bar gidan sai ya dawo. A ranar ne kuma Aishatou kawar Tante ta iso za ta fara gyaran amarya Alheran Radhiya. Tante Nasara tace mata ta tabbata ta fito mata da 'yarta ta yadda ko ita kanta Radhiyan idan ta kalli mudubi sai tace bata gane kanta ba. Sai da Ummi taci dariya tace to ayi mata wankan inji mana daga nan. Ba bata lokaci suna gama baccin gajiyarsu da kwana biyu aka fara gyara ciki da waje. Baki kuma kowa ya kama gabansa su Salame duka sun koma Sumaila na Nijar da Sakkwato suma sun tafi. ********** Wayar gaggawa Daddy ya samu daga Katsina da daddare Alh Baba yana son ganinsa tare da iyalinsa. An tabbatar masa kowa yana lafiya sai shi Alhajin ne ma da yake ta fama da ciwon suga. Washegari kuwa ya hada kan iyalinsa su ka tafi. Dama kuma a ranar Bilal yaso tafiya da Fauziyya idan an fara bikin sai ta dawo. Awwab sallamarsa da Radhiya da ga nesa-nesa akayi. Tun ranar da akayi taron nan da suna waya yace mata akwai sauran rawar da za ta yi masa. Wani mugun kida kamar zai tsaga mata waya ya tura mata yace tun wuri ta koya suna sake haduwa zata yi masa. Shikenan take gudunsa duk da yayi ta magiyar cewa wasa yake yi. Ana fara gyaran jiki Aishatou tace shima mijin sai ana masa rowar ganinta domin a haka ne idan sun hadu zai fi ganin kyaun da tayi. Haka yayi ta korafinsa da mita ya hakura tunda ya fuskanci da gaske maigyaran jikin da Tante Nasara suke. Zamu hadu kawai yake cewa Radhiya don sai ya fanshe wannan punishment din na babu gaira babu dalili an hana shi ganin matarsa. Mota uku su ka yi ranar da zasu tafi. Daddy da Mami a motarsa dreba na jansu. Sai Awwab da ya dauko Zahra, Raji da Zayyana. Mota ta uku kuwa Fauziyya ce da Bilal ana tuki ana shan soyayya wai kara'i take yi saboda laulayi ya sa ka ta a gaba kwana biyu yanzu kuwa anyi lafiya. Wani masallaci su ka tsaya sallah irin na matafiya kafin su shiga Kaduna Zayyana ta tsaya sakawa Jawad takalminsa su Daddy Haroun su ka shigo wurin. Mummy Gambo, Ghazalatu da kanwarta suna shiga masallacin su ka ga su Mami suna sallah. Su din ma sallar suka yi an idar sai yiwa juna kallon kallo saboda abinda ake cewa ta ciki na ciki. Ko kadan sun kasa sakewa da juna ayi hira yadda aka saba. Ba su Mamin ba, ba kuma ga yaran nasu ba. Nama da lemuka Awwab ya siyo ya kira Zayyana tazo ta karbar musu. Ghazalatu na can gefe da kanwarta Fauziyya ta fara yunkurin jawosu jiki. "Kuzo muci abinci" "Mun koshi" Ghazalatu tace a kunyace saboda nauyinsu da take ji idan ta tuna duk abinda ya faru saboda ita ne. Basu sake cewa komai ba amma cin abincin baya yi musu dadi saboda ga 'yan uwansu a gefe. Su kuma saboda sunce sun koshi babu damar zuwa su sayi wani. Mummy Gambo sai ta rasa yadda za ta yiwa Mami magana saboda kunyar kowa yanzu yasan bayan sun gama yi mata tijara ga yadda auren ya kare. Mami kuwa sai ta yi kamar bata lura da yadda ta takura ba ita da yaran tana cin abincinta hankali a kwance. A zuci tausayin Gambo take ji sai dai dole ne ta nuna mata kuskurenta. Can da abin ya ishi Mummy Gambo gashi Daddy Haroun ya tsaya suna magana da Daddy wadda duka akan yanayin sabanin iyalansu ne ta dan matso kadan kusa da Mami. "Ina ta zuba ido ko zaki gayyacemu taron da kuka yi na dawowar uhmmm baban yarinyar nan amaryar Awwab sai muka ji shiru" "Banyi zaton zaki so zuwa bane" Mami tace kai tsaye. Mummy Gambo dama neman kofar magana kawai take yi amma ba ta zargin yayarta don ba ta gayyacesu ba "Mami...hmmm...Mami kiyi hakuri akan duka abubuwan da suka faru" Zahra na jin haka ba ta jira Mami tayi magana ba yace duka su tashi su bar wurin don ta san maganar ta manya ce. Ghazalatu har ta soma hawaye. Mami ta kalli kanwarta tana tuna irin batancin da suka yi mata har gida. "Ki bar maganar nan mu karasa Katsina nan ba muhallinta bane" "Naji amma kice kin hakura don Allah" Mummy Gambo ta fada a raunane tana kara tsanar abubuwan da tayi. "Na yafe amma a bar zancen haka." Gaba Mami tayi da sauri don kada ta soma hawaye a wurin suka tafi kowa ya shiga mota. A jere suke tafiya har Katsina gidan Alh Baba. Anyi abinci sosai na tarbar bakin gidajen guda biyu. Sai da su ka yi sallar la'asar aka ci abinci sannan Alh Baba ya kira kannensa, Ummansu Mami sai kuma Mami, Hussaina da Gambo kowacce da mijinta da kuma 'ya'yan da abin ya shafa wato Awwab, Ghazalatu da Nura. Ba tare da bata lokaci ba Alh Baba ya soma magana. "Maman Biyu gani da 'ya'yanki da kowa a wurin nan kamar yadda nayi miki alkawari zanyi kokarin yi musu sulhu." Kallonsu yayi daya bayan daya "Hassana, Hussaina da ke Gambo mun taba zama daku shekara uku da suka wuce akan auren Muhammad da Ghazalatu. A wancan lokacin nawa idon ne ya fara rufewa da son ganin kamar yadda da yawa cikin 'ya'yanmu su ka auri juna su ma jikokin suyi haka. A zatona zumunci zan karawa karfi ashe ruguza shi nake yi. Kuma sai akayi rashin sa'a zumuncin na 'ya'yan mutum daya na bata. Maman Biyu kiyi hakuri" Mami da kannenta kowa sai sharar kwalla yake yi saboda ganin Ummansu tana kuka. Tayi bakin kokarinta ta shiryasu abu ya faskara shiyasa ta kawowa Alh Baba kukanta kuma bata ji nauyin fada masa gaskiya ba kai tsaye ta dora masa laifin bata zumuncin 'ya'yanta. Alh Baba ya koma ga su Awwab "Muhammad da kai zan fara. Kai da kanwarka kun hada kai bisa rashin sanin mahaifinka har ya nema maka wani auren. Tabbas ka fini gaskiya a lokacin da ka nemi hada mata biyu domin fitar da mahaifinka kunya." A hankali Awwab ya daga kai ya kalli Alhajin ya mayar da kansa kasa yana saurarensa lokacin da ya koma kan Nura yayi masa kaca-kaca akan irin tozarcin da ya yiwa Ghazalatu. "Wannan abu duk mun sanya son kai a ciki karshe bamu ji dadi ba. Gambo kin biyewa 'yarki tace bata son kishiya...." Awwab na jin zancen ya koma kan iyaye ya kalli Nura da yake tsananin jin haushi da Ghazalatu wadda tamkar a zare allura babu wata soyayya da ta rage masa a zuciya game da ita sai ta 'yan uwantaka da tausayin halin da ta fada a gidan miji. "Ku tashi mu fita" "Ban gama ba dreban sama ku koma ku zauna" cewar Alh Baba. "Alhaji zamu dawo tunda na ga maganar yanzu ba tamu bace" karamar tsawa ya dakawa Nura dama ya girme shi "kai tashi mana" Da sauri ya mike su ka fita su ukun. Alh Baba da sauran kakanin sun yabawa Mami wurin tarbiyantar da 'ya'yanta gashi har yasan su tashi saboda iyayensu za'ayiwa fada. Fada, nasiha da jan kunne sosai Alh Baba ya yiwa su Mami musamman Hussaina da ya dorawa alhakin ingiza wutar rikici tsakanin Mami da Gambo. "Abinda akayi ta rigimar dominsa gashi sai da ya faru..." Baba Karami yake cewa dasu "munje mun karbawa Muhammad auren yarinyar nan Radhiya. Ku kuma da kuke ta tada jijiyar wuya gashi gayyar ta watse. Kunyiwa yaranku auren huce haushi sun kare da hadaku fada da juna" Hussaina tafi kowa jin kunya ga ishrar da take gani a wurin Hany har yanzu bata da lafiya dangin saurayin kuma sunki amincewa. "Nasan hakkinku ne yake bibiyata Hassana da Gambo ku yafe min don Allah" Ummansu ma kukan take yi a dole su ka rinka cewa sun yafewa juna. Iyayensu albarka suka saka musu sannan aka sake kiran su Awwab. Baban Biyu yace yana bukatar daidaituwar zumuncinsu ko me zaije ya dawo tsakanin iyaye daga yau bai yarda su juyawa juna baya ba. Sun tashi zukata wasai. Daddy ne yayi saura da iyayensa yake fada musu irin alkhairin da Zayyan yayi masa da duk wanda ya rabe shi. "Banda ceto rayuwarmu da yayi kudin da gwamnatin tarayya ta bashi a matsayin diyyar wahalar da yasha wallahi yake ta bin mutane da alheri. Nasan ana cewa ka haifi mutum baka haifi halinshi ba amma ina kyautata zato akan cewa Radhiya a cikin namu dangin alkhairi ce. Ban taba kin Awwab da Ghazalatu ba. Duk abinda nayi nayi shi ne domin kulawa da bayan wanda ya sadaukar da rayuwarsa dominmu. Nasan gabadaya rigimar nan ta samo asali ne akan auren da na nema masa saboda haka ina mai rokonku da ku yafe min" Kowa yace ya yafe duk da ba laifi yayi ba. Hasali ma yayi abin yabawa ne sosai saboda bai kasance mai manta alkhairi ba. A hankali hira ta barke a tsakanin 'yan uwan inda su Zahra sosai suke jin zafin Nura da abinda ya yiwa Ghazalatu. Ana haka ta hango Awwab a kan kujera can gefe a cikin falon yayi nesa dasu. Murmushi tayi ta karasa inda yake wata sabuwar wutar sonsa tana ruri a zuciyarta. Chatting yake da Radhiya yana ta murmushi ta zo ta zauna a kujerar gefensa. "Ango kasha kamshi" tace tana rausayar da kai da murmushi. Hankalinsa na kan wayar yana yiwa Radhiya reply yace "Kamshi sai mata" Murya ta karyar alamun kuka take shirin yi "kaji irin zaman da muka yi da Nura ko?" Wayar yasa a aljihu ya maida hankali gareta "naji Ghazalatu sai dai ince kiyi hakuri komai mukaddari ne." Gwauron numfashi ta sauke tana tararrabin abinda za ta fada. Hannu ta ga ya mayar zai dauko wayar tayi saurin cewa "Yanzu shikenan tsakaninmu Ya Awwab?" Karo na biyu ya kuma mayar da wayar "ban fahimceki ba" Sunkuyar da kai tayi kafin ta bashi amsa "nasan cewa ban kyauta ba amma kayi hakuri idan da hali zan jiraka" Ya fara gane me take son cewa sai dai baya son zumuncin da ake kokarin fardadowa dashi ya kuma sake sumewa a dalilinsa "Ghazalatu mun riga mun wuce wannan matakin. I am happily married matata ko tarewa bata yi ba so please kada ma mu komawa abinda ya wuce" Hawaye ne ya zubo mata "yanzu baka tausayin halin da na shiga? Ban taba cireka daga zuciyata ba kuma a shirye nake na zauna da kai ko a ta biyun ne" Ransa yaji ya soma baci amma baya son janyo hankalin kowa garesu "Allah zai baki wanda ya fini amma bani da niyar mata biyu yanzu" Wani irin murmushi tayi "wato nice baka so wancan lokacin shiyasa har ka iya amincewa wata kuma ka fada da bakinka kana sonta ba wai don Daddy Mustapha ya nema maka aurenta ba" "Wai ni Ghazalatu Nura ya sakeki ne kike min wannan zancen?" Da murnarta ta amsa "ya hakura yayi min saki daya" "Idan dai ba lissafina ya baci ba ina tunanin har yanzu kina cikin kwanakin iddah ko" "Nasan da wannan amma bazai hana na fada maka abinda yake raina ba" Neman abinda zai fada mata yake yi wayar Radhiya ta shigo. Yana dauka ta soma kukan shagwaba wai baiyi mata reply ba. Dama hirar tafiya honeymoon suke yi ya bata zabin kasashe uku yace ta zabi daya shine ta tura masa inda take so bai duba ba. Hakuri ya soma bata Ghazalatu sai ta daga murya tana cewa wai yace gata zasu gaisa. Gudun kada ta zargi wani abu tunda ta riga taji muryar mace a wurin yace mata ga Ghazalatu zasu gaisa. Mika mata wayar yayi ta koma kan kujera ta zauna tana magana a gayance kamar bata so "amaryarmu ko ince uwargida sarautar mata yaya shirye shiryen biki?" Zuciyar Radhiya har ta fara tafasa da kishi musamman saboda yanayin yadda Ghazalatu ke fitar da harufa daki daki tana wani yauki. "Lafiya kalau" ta daure tace. "To ga amanar Yayana nan dai ki kula mana dashi sosai...idan kina bukatar shawarwari game da hanyoyin sace zuciyarsa ki karbi numberta a wurinsa." Wata shu'umar dariya tayi "kinsan na karance shi kamar tafin hannuna" "Abinda ba'a sani ba ake karantawa, ni da Hammana kuwa warin takalmi ne komai namu iri daya....how do I put it?" Radhiya tace muryarta na fita cikin nutsuwa. Dariya tayi a hankali saboda samo kalmar da ta dace ta fada "Alheran is the female version of Awwab...amma duk da haka nagode da tayin da kika yi min" Awwab tsabar mamakin abinda Ghazalatu tace kasa yi mata magana yayi sai jinjina kai yake da halin mata. Kallonsa tayi ta saki murmushi duk da ranta in yayi dubu ya baci da amaar Radhiya amma ai ba'a fara komai ba ma "Ga angon namu.....Yayana sauran maganar tamu fa?" Fizgar wayarsa yayi ransa a hade ta sake maimaita tambayar da dan karfi yace zasu karasa daga baya. Da sauri ya saka wayar a kunne yana cewa hello Radhiya ta katse kiran. Yasan za'a rina sai dai yana sake kira yaji ta kashe wayar gabadaya. *********** Ko sati ba'ayi ba da taji Mami tana fadawa su Ummi matsalar gidan Ghazalatu da mutuwar auren shine daga zuwansa Katsina yau zasu tada tsohuwar soyayya. Allah Ya bada sa'a tace a zuci ranta yana kuna tayi jifa da wayar ta kifa kai tana kuka. Kamar wasa ta kwashe yafi awa guda tana zubar da hawaye. A haka Rahima tazo ta sameta sai dai bata ga fuskar ba tayi zaton bacci kawai take yi. Awwab tun yana daukar abin wasa har ya fuskanci fushin nata na gaske ne. Bai san sau nawa yana gwada wayarta ba amma duk kira a kashe. Gashi layi daya gareta bare ya nemi wani. A ranar su biyun da kyar suka yi bacci saboda tunani. Asubar fari yana dawowa daga masallaci ya sake gwadawa nan ma shiru har bayan azahar. Bashi da kwanciyar hankali lokacin kana kallonsa za ka gane akwai abinda ke damunsa. Mami tana ta yi masa magana akan cewa su Umma da sauran matan kakanin sun ce lallai idan an dauko Radhiya daga Sakkwato nan Katsina za'a kawota ayi budar kai kafin su wuce Nijar. Sama-sama yake jin muryar Zahra tana cewa gaskiya tana tausayin Radhiyan saboda zasu sha yawo. Wayarsa a hannu yana yi mata text bai amsa ba Mami ta kira shi da dan karfi "wai meye yake damunka ne ana magana ka kasa amsawa? Ka ji abinda nake fada ma kuwa?" Saurin kallonta yayi "Mami naji, gajiya ce dai kowa sai yayi a tanadi maganin ciwon jiki kawai" Murmushi tayi tana cigaba da fadawa Zahra ta rubuta abubuwan bukata na walimar da za suyi ranar budar kan "tunda wahalar saboda ku ne ai kai ya dace ka siyo mana maganin" Murmushi kawai yayi ya tashi kamar jira suke Mami da Zahra su ka tambayi juna me yake damunsa ne. Kasa hakuri yayi ya kira Ummi saboda ba karamin kewar Radhiya yake yi ba ga damuwa tunda yasan fushi take yi dashi. Lokutan da ya sami damar kasancewa da ita kadai idan ya tuna sai yaji kamar ya budi ido ya ganshi tare da ita. Sun gaisa da Ummi lafiya kalau yadda su ka saba ya rasa da yadda zai nemi Radhiya. Ita da kanta ta fuskanci me yake damunsa. "Awwab kaima ka kira kanwarka baka samu ko?" Da sauri yace "eh" Murmushi tayi "Jiya Karami sai da ya kirani na hadasu, dazu ma ya sake cewa na bata su gaisa wai ya kirata shiru kuma bata kira shi ba. Ban san me yake damunta ba sai aikin kwanciya...." Rahima ta bawa wayar ta kai mata. Har ta mika hannu tana tambayarta ko Emzee ne Rahima tace ba shi bane. Tunda taji haka tasan ko waye sai cewa tayi ta mayarwa da Ummi wayarta yanzu za ta kunna tata ta kira shi. Awwab yana jin duk abinda tace kamar yayi ihu saboda yadda ya matsu ta amsa masa taki. Fitar Rahiman ke da wuya ta sake fashewa da wani kukan ko abinci ta kasa ci sai tunanin yana can suna soyayya da Ghazalatu. Zuwa dare jikinta yayi mugun zafi da ciwon kai saboda ita dama ba mutum bace mai sa abu a rai. Wannan karon da tayi shiru sai yake neman yi mata illa. Ummi ta gaji da wannan zaman daki da tsura da ga jiya zuwa yau take tambayar Aishatou mai gyaran jiki ko ta ga wani chanji game da ita. "Shiru shirun da take yi ne ke damuna dai Ummin Radhiya. Kuma kamar kuka tayi ma shiyasa jiya da yau aikin namu bamu dade ba. Ina jin fargabar aure ce ta fara taba ta. Kinsan fa ance aure yakin mata" Ummi ta soma dariya "yakin matan zamaninmu ko, yanzu budurwa ko ita ce ta hudu banda rawar kai me su ka sani" Hira suke abinsu akan bambancin matan da da na yanzu Mami ta kira suke zancen walimar da dole yanzu sai tayi a Katsina. Ummi ma tace dalilin da yasa ta kira dazu kenan Malamijo yace kafin su fara bikinsu a kawo masa jikarsa suyi nasu taron tunda ya kula wannan bikin ba na zama bane yawo za'ayi ta yi. "Yaran nan zasu wahala musamman Radhiya da take mace ko dai mu matso da bikin kada mu cure komai cikin sati guda muzo ana 'ya kwance uwa kwance" inji Mami. "Ke da 'yarki ne zaku kwanta ni kam garau zaku ganni don ko suyar albasa bazan tayaku dashi ba" Ummi ta bata amsa da dariya. "Kyale wannan 'yar rabona da ita tun jiya" Sai yanzu Ummi ta fara damuwa "Mami bari na dubo yarinyar nan. Jiya da yau a daki ta wuni muna cewa ko fargabar aure ne amma dai bari na duba" tace tana hawa sama zuwa dakin Radhiya. Bata ajiye wayar ba ta shiga ta same kwance a kasa ta rike kai da hannu biyu. Da sauri ta durkusa a gabanta tana dora hannu a kan goshinta da yayi zafi ga idanu a kumbure anci kuka an gode Allah. "Ke me ya sameki?" Ummi tace a tsorace tana ajiye wayar a gefe. Tayar da ita tayi ta koma kan gado. "Kaina zai tsage Ummi" tace a wahale. Mami na jinsu hankalinta ya tashi ta soma kwalawa Awwab kira ta ma manta suna Katsina ne Radhiya na Abuja. Tare da Daddy su ka shigo daga waje ta fada musu me taji Radhiya na fada. Sosai hankalin Awwab yayi matukar tashi ya kasa zaune ya kasa tsaye. Ummi aka sake kira tace musu zazzabi ne da ciwon kai amma ta bata magani. Idan bata ji sauki ba zuwa wayewar gari sai suje asibiti. Zayyan a dakin Radhiya ya zauna har wurin dayan dare bayan ya lallabata taci abinci da kyar. Maganar Ghazalatu keyi mata yawo a ka wai tasan Awwab kamar tafin hannunta kuma a gabansa amma bata ji yace komai ba. Ita bata taba sanin kishi ba sai akansa. Irin son da take masa ya saka mata wani irin kishi da take jin yafi karfinta. Idan yace zai auri kanwarsa ba hanawa zata yi ba amma ita ta yarda dari bisa dari da kazantar da baka gani ba tsaftace. Duk abinda zasuyi ayi a bayan idonta ba sai an nuna mata anayi ba. To itama Ghazalatun amsar da Radhiya ta bata tana nan tana ci mata rai. A daddafe Awwab ya kai asuba kafin takwas yayi wanka ya shiga cikin gidan saboda kofar dakinsa ta waje take. Yayi sa'ar ganin Zahra ta fito da Femi ya fada mata Abuja zai tafi ta fadawa su Mami idan sun tashi. Muryar Mami yaji tana tambayar shi jikin Radhiya ne yayi zafi ya juya yana sunne kai. Murmushi tayi "bazan hanaka zuwa duba matarka ba kuma hakan da kayi zai farantawa Umminku sosai" Dakatar dashi tayi tace ya jira ta fadawa Daddy. Sai da yayi wanka ya fito shima dadi yaji da Awwab din yayi tunanin komawa saboda Radhiya. "Akwai sauran kayan da Fauziyya za ta kawo ka fito min da akwatunan sai su jera anjima a kai gidan Alh Baba" Mami tace masa. Kayan lefe ne kusan komai ya hado abinsa da zai dawo amma Mami sai da ta bada kudi aka karo mata atampa, leshi da shadda daga kantin kwari a Kano. Shine take so ya fito da akwatunan da ya siyo sai a jera da sauran kayan a kaiwa kakanni su gani. Sai ranar dauko amarya zasu tafi da kayan Sakkwato. Hana shi tafiya Mami tayi sai da Fauziyya tazo wurin tara da rabi wai idan bai gani yanzu ba babu lallai ya gani. Shi dai kamar yace ba gidansa za'a dawo da su ba yayi shiru dai. Kaya sunyi kyau komai goma goma Mami ta kara sai da ta tashi ya janyo Zahra gefe saboda ta fi Fauziyya nutsuwa. Kitchen suka koma saboda Fauziyya da ta damu sai anyi da ita. Rasa yadda zaiyi da rigimar Radhiya yasa shi neman shawarar kanwarsa. Baiyi mamaki ba da Fauziyya ta shigo kamar an korota kafin Zahra tayi magana ita ta soma "wallahi Hamma baka kyauta ba. Baiwar Allah kila ma abinda ya haddasa mata zazzabin kenan" tace cike da jimami. "Yanzu waye ya sa dake?" Zahra ta harareta "kaga Hamma sai kayi a hankali don naga take taken Ghazalatu. Ita kuma Radhiya kaje ka bata hakuri kafin tayi maka balotelli" Dariya yayi yana tuna kan Radhiya na da sai kuma ya tuno laushi da tsahon gashinta yanzu yayi murmushi. Fita daga kitchen din Fauziyya take yi jin ance balotelli tace "ba wani balotelli fa indai za'a shanye janbaki tuni zasu daidaita" Ba don rannan ya matsa Radhiya akan dalilin sake kwalliya ana kiran sallah ba da bazai san me Fauziyya take nufi ba. Baki ya rike ita kuwa hankali ya tashi da ta fuskanci ya gane me take nufi ta dora hannu a ka tana salati. Zahra ta rinka kyakyata dariya Awwab ya fice yana cewa irinsu ne masu zuwa gulma gidan amarya. "Idan na ga kafarki a kofar gidana nan da wata uku ma sai na karyata don nasan me ya kawoki" Ta daure fuska "ai dai gaskiya na fada" Bakin mota suka raka shi batare da ya sake neman wayar Radhiya ba ya dauki hanya. Karfe uku yana cikin garin Abuja saboda ko mai bai tsaya sha ba yayi full tank a Katsina. Gidansu ya fara zuwa amma wurin Mama ya shiga. Bata nan sai Baba Hadir shi kadai wai Ummi tazo sun koma can gidan tare. Abinci suka ci tare da sallah sannan ya je yayi wanka ya tafi ganin Radhiya. Kananan kaya ya saka bakin jeans da bakar shirt mai maballai da collar ya dora rigar sanyi mai v-neck cream ta saman wuyan ya lankwasa kwalar shirt din ciki. Ba karamin kyau yayi ba yana ta kamshi ya shige mota. Yana shiga ya tarar da motar Ibrahim dama Baba Hadir ya fada masa can suka tafi duba Radhiya. Ummi da Mama sunyi mamakin ganinsa sosai ya sunkuyar da kai da Mama ta shiga tsokanarsa wai amarya tayi kira. Murmushi kawai yake yi Ummi ta tura mai aikinsu kiran Radhiya tasa Rahima kawo masa abinci. Bata yarda ba da yace a koshe yake sai da ya tabbatar musu a gidan Mama yaci. Mai aikin ce ta dawo tace wai bacci Radhiya take yi. Ba dai haka yaso ba kuma fuskarsa ta nuna. Mama ta nuna masa dakin da take ciki a kasa inda suke gyaran jiki. Yau ba'ayi ba amma saboda rashin kwarin jiki can ta shiga bayan an matsa mata ta sauko dazu. "Shiga tana ciki ka samu ka tursasata cin abinci me yiwuwa kai taji maganarka" Ummi ta kalla ganin ko motsi baiyi ba "muje sama mu karasa don naga alama dan naki ba tashi zaiyi ba" Awwab kunya Ummi kunya. Sai da su ka shige sannan ya tashi da sauri ya tafi dakin da aka nuna masa. Kwankwasawa yayi tana kwance da waya a hannu r muryar Hammanta amma kishi ya hanata kunna waya ta kira. Tura kofar yayi a hankali yaji tace "Rahima karo min bargo a sama dakin nan akwai sanyi sosai" "Gani ki yafa" Muryarsa ce tazo mata a bazata ta dago kai ta tabbatar shi din ne yana tsaye da ga bakin kofa sai kawai ta ja bargo ta rufe har kanta. Murmushi Awwab yayi ya zauna a gefen gado sannan a hankali ya zura hannunsa ciki ya kamo nata tana ta kokarin kwacewa ya rike. "Idan baki nutsu ba zanyi miki rawar 'yar amana" Dena motsin tayi yana jiyo sautin dariyarta a hankali yayin da take jin dumin hannunsa yana ratsa ta. Shiru su ka yi duka su biyun na dan lokaci sai daga baya ya soma magana. Hakuri ya bata tare da bayanin ya akayi ma taji shi tare da Ghazalatu a lokacin. "Ko kinfi so ace mun dena zumunci da 'yan uwana?" Tana cikin bargon ta girgiza kai yace yana dariya "ashe ma zakiyi saurin hakura duk kika tayar min da hankali" Gefen fuskarta kadan ta bude amma bata iya kallon idanunsa ba tace "ba hakura nayi ba ka tashi kayi min rawar" "Sai dai muyi tare" yace yana kashe mata ido. Sake rufa tayi ya kwanto a jikinta tuni ta fara rawar jiki kuwa "ko ki bude in ganki tunda dubiya nazo ko na shigo ta nan" yace yana dan matsa hannunta da ya rike ta kasan bargon. Ja taji yayi ta bude kanta da sauri. A kunyace ta ture bargon tana sanye da dogon skirt baki sai rigar sanyi da ta kamata mai high neck. "Give me a hug" yace yana ware hannuwansa. Bata motsa ba sai kai da ta sunkuyar yace "now please" da wata irin murya. Ji yake kamar ya janyo kwanakin nan su kare da wuri ace an gama biki kowa ya huta. Ba yadda ta iya ta dan matso kadan shi kuwa ya janyota jikinsa ya rungume yana shafa kanta. "I love you Schatzi ki dena kokwonto akan hakan. Bazan taba yin abu don na bata miki rai ina sane ba" Dama can bata gama kukanta ba sai yanzu ta sami damar yi masa yana ta rarrashi. "Ni dai ko za ka yi min kishiya bazan zauna gida daya da ita ba" Kanta ya dago yana murmushi "saboda me?" Shagwabe masa tayi "Ni dai kawai bana so" Goshinta ya yiwa kiss ta runtse idanu yace "saboda kina tunanin zanyi mata wannan?" Ya koma kumatunta hagu da dama "da wannan?" Sai kan hancinta "da wannan ma?" "Ni dai ban ce ba" "Ni nace baby...I miss you so much" yace yana kallon fuskarta idonta a rufe ya soma zana mata lips da karamin yatsansa "yau baki sa janbaki bane?" Tamkar ta nutse a cikin gadon ta kawar da fuskarta "bani da lafiya fa" Idanunsa a kanta yace "Ni kuma na taho all the way from Katsina shan janbaki ne fa" Ciwo dama ya riga ya warke tunda ya iso da sauri ta tashi yana kiranta wai ko vaseline ne ta shafa ta bashi ya shanye ta gudu tana dariya. Bata sake bari sun kebe su kadai ba sai da zai tafi gida tayi masa sallama yana ta korafin bai sha janbaki ba tana dariya. Kafin dare ta ware tas sai karadi da dariyarta da ta cika mutane dashi. Zayyan yana ganin chanjin da ta samu kuma an fada masa Awwab yazo yayi dariya wai dama can ciwon soyayya ne. "To saura ka fada a gabansu" Ummi tace fuska a daure don kada ya saka ta dariya. Alamun zip ya yiwa bakinsa sannan ya tashi yana nade hannun rigar baccinsa "bari na gani ko ina da sauran karfi" Mairama bata ankara ba ya dagata ya dire akan gado. Tana tashi ya danneta yana dariya "kwanta bitar karatunmu zamuyi muma" ********** Yau litinin ya sati na gaba ya kamata a fara biki gidan gabadaya suka tafi Sumaila tare da Mama, Zayyan kuma ya tafi Sakkwato. Sun isa gidan na Malamijo ya cika da 'yan uwa da abokan arziki. Su Innawuro daga rugar Barkindo, Nene Marka da kishiyarta tare da 'ya'yab kishiyar da jikoki sai kuma 'yan uwan Malamijo da nasu iyalan. Ranar laraba zasu yi Kamu saboda da yawansu ba iya zuwa Abuja zasu yi ba. Emzee yana makaranta har lokacin sai wani satin zai taho. Sunyi waya da Rahima ta fada masa sun taho Sumaila sai dai har yau bai kawo komai ba. Sallah kawai Rahiman tayi ta fadawa Ummi zata je gida. Envelop Ummin ta mika mata "ga kudadenki na kunshi ki kaiwa Baffanki" Da tsananin mamaki Rahima take kallon Ummi saboda da idanunta ta ga Salame da aihinin wanda aka bata ranar da tayiwa bakin Mom Arifah. Sauran wanda tayi kuwa ba wani yawa gareshi ba to ta ina kudin yayi wannan kaurin. Kasa shiru tayi muryarta tana rawa tace "Ummi ba kin bawa Umma wancan kudin ba?" Mairama ranta taji ya baci a tunaninta Salame ce ta fadawa Rahima ta karbe kudin. So tayi ta rufa mata asiri shine ta sake hada mata dubu dari da sauran kudin da ta samu. "Wancan kyauta ce zanyi mata ranar babu kudi a hannuna shine na bata naki amma gashi na dawo miki dasu" Tasan Ummin ta fada ne kawai ba yarda tayi ba. Kuka ta fashe dashi tana kara son kanwar Ummanta da danta Emzee. Cike da farinciki ta tafi gidansu. Baffanta yana kofar gida suna hira da abokinsa ya hangota. Bakinsa kamar gonar auduga ya tashi ya shige ciki da saurinsa yabi bayanta. A dakin Iya suka yada zango suna ta sakin murmushi ta je ta nanikewa Iya a jiki. Sunji dadi sosai yadda tayi fes da ita ta kara cikowa tayi kyau. "Har kin gama hutun ne Rahima?" Iya take tambayarta tunda basuyi tsammanin dawowarta yanzu ba. Bayani tayi musu ta cewa Iya don Allah ranar laraba tazo yinin Adda Radhiya. Labarin kirkin su Ummi tayi ta basu da yadda kasuwar kunshi ta bude mata. Da ta basu kudin ba karamin mamaki Baffanta yayi ba. "Tare zamu je gidan Malamijon idan kin huta nayi mata godiya. Dubu dari harda sha uku a hannuna arzikin Rahimata" yace yana dariya. Ta tashi taje bangaren matar gidan suka gaisa ba yabo ba fallasa ta dawo Iya ta mika mata kudi a leda "ga wannan Rahima nasa Baffanki ya raba kudin ki kaiwa Salame itama tasa albarka. Dubu talatin ne, Baffanki ma ya dauki talatin sauran kuma zan fara yi miki siyayya kinga ko maburgi baki dashi kada aure yayi mana zuwan bazata" Ture kudin tayi kamar zatayi kuka tace "A'a Iya Baffa ya rike duka" "Kul na kara ji mahaifiya ba abar wasa bace. Maza dauki ki kai mata ki dawo sai kuje can din da Baffanki ko" Ba haka taso ba tunda zai zama Salame taci bulus harda kari amma bazata iya yiwa Iya musu ba. Daukar ledar tayi ta boye a cikin hijabinta ta kama hanyar gidan Alh Indararo. A gidan Malamijo Radhiya bata san Rahima ta fita ba sai daga baya Ummi ke fada mata inda taje. Ta taho mata da kaya akwati guda masu kyau wanda bata yi wani amfanin kirki dasu ba kuma bata so dama ta bata a cikin gidan sai kawai ta nemi yaro ya rakata gidansu. Suna fita suka hangota tayi hanyar gidan Salame shine ta bi bayanta. Da Rahima ta isa tsakar gidan kamar kaji sunyi dambe ko ina shinkafa ce tun wadda aka ci da rana da mai ta watse a wurin. Ga kwanuka a bakin kofofin dakuna wasu a tsakar wurin kadan ne aka ajiye a wurin wanke wanke. A mutumce ta gaishe da Maman Danmama tayi sallama a kofar dakin Salame. Daga ciki ta amsa mata irin na gatse dinnan "Su Hajiya Rahima ne...shigo mana" Gwiwa a sake ta shiga ta gaisheta. Bata amsa ba sai kunnenta da ta kama ta murde iya karfinta amma dauriya irinta Rahima bata yi yunkurin kwacewa ba sai hawaye da yake zuba kamar an bude famfo "dama jiranki nake yi ki dawo mai shegen kwadayi. Kin bi Mairama gidanta batare da neman izinina ba sannan da muka je akanki Hajjo da Yadikko ke yi min fada" "Umma kiyi hakuri" tace idanunta a runtse zafin murdar kunnen tana ratsata sosai. Salame bata raga mata ba saboda bakincikin yadda har take da bakin cewa dama Mairama ce ta haifeta. Rai a bace take fada "kinje kin sami duniya da bakinki kina cewa ni bana sonki ko? Akwai uwar da kika taba yi min ne da zan so ki? Banda kaddarar haihuwarki me zai kaini gidan fakirin mahaifinki ma. Sai ana magana kiyi ta zarowa mutane idanu" Maman Danmama tana jinsu amma bata shiga ba saboda ko taje bazai hana Salame abinda tayi niyya ba. Bacin rai sosai Rahima take ji wanda ba don Salame ce ta kawota duniya ba yau da tayi mata fitsara da rashin kunya irin wadda bata taba sani ko ji ba. Sauran yaran suna dakin suna dariya Salame ta cigaba ido a rufe "daga yau na sake jin kinbi Mairama gidanta sai na saba miki. Har wani arziki garesu da zaki je kamar almajira kina 'yar cikina ana baki kafa da hannu kina kunshi wai ke mai sana'a" Kasa magana tayi sai gunjin kuka. Babu abinda ke damun Salame sai frustration da tsantsar hassadar Mairama. Yanzu kowa ya bude baki a gidansu ita yake kira a yabeta a yabi 'ya'yanta. Rayuwa tayi mata ba daidai ba ace ita ce yau a kasan kanwarta wadda a da can baya take cin arzikinta. Ga Alh Indararo tayi haukan tayi hankalin duka a banza yaki sakinta. Halifa shima kuma ya koma jikin Mairaman shine itama da ubanta ba kowan kowa ba take neman bijere mata. "Ba dake nake ba?" Ta hayayyako mata sai ji kake tas ta dauketa da mari saboda taki amsawa. Hancin Rahima sai jini Salame niyarta ta sauke duka bacin ranta yau a jikinta ta kuma daga hannu don ko jinin bata kula dashi ba Radhiya ta damke shi ta watsar dashi gefe. Kusan tare suka shigo gidan da Rahima duka abinda suka yi taji. Zuciyarta har wani daci take yi ganin yadda ake yiwa Rahiman da take kamar kwai yanzu a wurin Ummi. Ashe shiyasa Ummin ta kara janta a jiki don ta maye mata gurbin uwa. Tayar da ita daga durkusun da tayi a gaban Salame taso yi amma taki tashi sai ma ture hannunta da take yi. "Ki barta ta kasheni....Umma ki kasheni ki huta indai hakan zai sanyaya miki zuciya ki dena tsanata" Zuciya a wuya Salame ta janyo wayar rediyo "kina zaton ina wasa dake ne Rahima? Kin tashi a nan ko sai naci ub...." Wayar ta sauke mata a jikinta ya sami fuskarta sannan ta sake dagawa a kufule sai ta sauka a gadon bayan Radhiya saboda saurin kare Rahima da tayi. A zabure Rahiman ta mike ta kawo hannu za ta riketa ta nuna mata kofa "ki fita ki tafi gidan Baffanki gani nan zuwa" "Adda ...." tace jikinta sai rawa yake yi kukan ma ya dauke mata. "Nace ki fita ko sai ranki ya baci" Radhiya tace cikin fada. Da sauri kuwa ta fita tana hawaye. Radhiya ta juyo tana yiwa Salame wani irin kallo da ya tsirga mata ciki. Idanu ne na Zayyanu Tureta take gani cikin tsananin bacin rai da zafin zuciya. Kujera Radhiya ta janyo ta zauna bayanta yana uban zugi saboda dukan ya shigeta sosai. Yaran ta kalla ta daka musu tsawa tace su fice kafin ta kirga uku. Ko biyu bata kai ba suka kama gabansu a guje ya rage daga ita sai Salame. A rayuwarta bata taba tsorata irin na yau ba. Gani take kamar an hada mata Zayyan da Mairama a jikin mutum guda ne. Boye tsoron tayi tace "zaki rama dukan ne?" "Zan so na rama Gwaggo Salame sai dai kinci arzikin Malamijo kuma dukanki zai janyo min fushin uwa. Yau ne na biyu da naga irin abinda kike yiwa Rahima saboda Baffanta talaka ne. Sai dai mijin naki na yanzu ma bana jin zai iya kwatarki daga hannun hukuma ko yaso" A tsorace ta nunata da yatsa "Ke ki kiyayeni bana son rashin kunya don ko uwar da ta haifeki tayi kadan" "Ki dena zagar min Ummina, bansan me tayi miki kika tsaneta ba amma inda ta kai bazaki taba zuwa rabinsa ba har abada da wannan algae (gansa kuka) din na bakinki" "Wato dai turoki tayi ki fada min magana saboda baku da tarbiya ko?" "Baki ga rashin tarbiyata ba amma yanzu zan nuna miki" Emzee ta kira ya dauka zai fara janta da hira tace ya saurareta "motar sojoji nawa zaka iya turowa a kama Gwaggo Salame batare da kowa ya sani ba" Cikin Salame yace tsuuuu da taji muryar Emzee kuma ana zancen motar sojoji. Ko tunanin cewa shi dalibi ne bata yi ba tsoronta kawai kada a kama ta. Abinda tace ya saka shi tunani "Adda kada kice min kema kin gano ita ta makanta Ummi" "What???" Radhiya tace jikinta na bari Salame kuwa sulalewa tayi a kasa saboda ba karamin tsoron hatsabibancin Radhiya take yi ba tuntuni. Yarinya ce kamar aljana bata da tsoro ko kadan. "Kuna tare ne?" Ya tambayeta saboda bai fahimci zancen ba. "Ina gidanta yanzu haka. Emzee kayi min bayani sosai" "Adda dalilin da yasa ta tsani Ummi saboda tana son Daada ne, sannan ita ta yiwa Ummi asiri don ta auri wannan Alhajin da take gidansa yanzu" Kuka yaji Radhiya ta fashe dashi jikinta yana wata irin rawa sanyi na ratsata. Tsorata Salame da taso yi akan Rahima sai ya koma bakincikin muguntar da ta yiwa mahaifiyarsu. "Makantar shekara goma Gwaggo Salame na rantse bazamu yafe miki ba" tace tana wani irin kuka. Maman Danbaba tana jin abinda ta fada ta garzaya ta kirawo Alh Indararo ashe yana cikin daki ya dawo da wuri. Jikin Salame na rawa ta mike da dafa bango "kizo ki fita daga gidan tunda abin naku ya koma sharri" tana rarraba idanu kada wani ya shigo. "Adda" Radhiya taji Emzee ya kirata "me ya kaiki gidanta ba dazu kuka iso ba?" "Rahima na biyo" ta amsa cikin kuka. Kansa ne ya daure sosai "Rahima kuma?" "Eh Emzee, don baka ga irin dukan da take yi mata ba" "Me ya hadata da Rahima kuma? Ko wacce kike nufi na kasa fahimta" yace jikinsa a sanyaye yana tsananta addu'a kada abinda yake zargin tana nufi ya tabbata. "Rahima dai mana" "Wadda nake gani tare da Zayyana?" Yace a tsorace. "Eh" ta soma gajiya da tambayoyin ga serious maganar da ya kamata suyi. Muryarsa taji kamar zaiyi kuka a raunane "Adda kina nufin Rahima 'yar Gwaggo Salame ce?" "Kanwar Halifa ba..." Wayarsa ce ta subuce daga hannunsa batare da ya sani ba yaji kansa yayi mugun sarawa. Hawaye sosai Muhammad Zayyan Tureta ya soma yi a garin yaya Rahima ta cuce shi haka? Meyasa bata taba fada masa ba? Shiryawa suka yi ita da babarta ko kuwa shima asirin aka yi masa tunda ta saba? Ko kuwa ta turota ne domin ta sake bakantawa mahaifiyarsa saboda tsanar da tayi mata? Duka wadannan tambayoyin basu rage daidai da cikin cokali na soyayyar da yake yiwa Rahima ba sai dai wani irin zafi da yake ji a zuciyarsa domin ko sonta zai kashe shi bazai taba auren irin Salame ba. "Why Rahima???" Ya durkushe a kasa yana kuka kamar karamin yaro. 💕[11/2, 7:54 AM] 58💕 🏽: *KUYI HAKURI DA RASHIN YAWANSA BANA JINDADI NE YAU. NAGODE* Idanun Salame sunyi zuru-zuru saboda asirinta da wadannan 'ya'yan na Mairama suka sani. Daga nan kuma bata san yaya za ta kare ba. Radhiya kashe wayarta tayi bayan ta gama magana da Emzee ta koma kallon Salame tana ta hawaye. "Me Ummi tayi miki Gwaggo? Mata nawa ne suka taba son wani Allah bai kaddari zamansu tare ba kuma suka hakura?" Matsowa ta rinka yi inda Salame ke tsaye gumi na karyo mata. Wannan shi ake cewa kada Allah Ya kaimu ranar da za'a tsare mutum ana masa tambaya akan laifukan da ya binne. Ya Allah Ka rabamu da hisabi irin wannan da za'a tono komai da komai da muka taba aikatawa a rayuwarmu domin WALLAHI da matukar wahala mu haye. Kuka Radhiya take yi amma muryarta kowa naji a cikin gidan saboda karshe ranta ya kai kuloluwar baci "Kinsan tsananin da yake tattare da makanta kuwa? A lokacin Ummi ta rayu ba miji ga marayu sannan babu wadatar abincin da zata ci ta ciyar da yaranta. Gwaggo kina kallo sai da ta sayar da duk wani abu da ta mallaka muka dena karatu saboda neman magani." Kukanta ya kara tsanami ta matse kirjinta "sau nawa....sau nawa ina rokon Ummi ta barni nayi bara ko talla saboda bama koshi da abincin gidan Malamijo tana hanawa. Ba don Allah Ya dube mu su Innawuro sun zo ba kina jin da watarana bazata amince ba ko don kada yunwa tayi mana lahani. Sai Allah Ya sakawa Ummi Gwaggo" ta kare da fashewa da wani irin kuka. Rabonta da kuka sosai irin haka tun ranar da Ummi tace kada ta amsa cewar tana son Awwab. Yau ga abinda yafi rabuwa da Awwab kaji ko ka ga mutumin da baya kaunar mahaifiyarka kuma yake neman ganin bayanta. Jiki na rawa ga tsoro amma Salame bata so ta nunawa Radhiya sai cewa tayi "idan kin gama sharrin sai ki fita ki tafi in kuma zaki rama mata ne to na fara jin didif a jikina sai na san cewa kin haifu" Kallon da Radhiya tayi mata da jajayen idanunta kallo ne mai firgitarwa da nuna kwarewa wurin fitina da sanin yadda zaka rama abu cikin ruwan sanyi. "Ummi tayi mana tarbiya wadda ni ko Emzee bazamu taba watsa mata kasa a ido ba in sha Allah. Gwaggo Salame ke ba sa'ar yi na bace domin kin girmi mahaifiyata ma...amma.... zan hadaki da wanda yafi cancanta ya hukunta ki" tana kaiwa nan ta daga waya ta soma kiran mahaifinta Zayyan Tureta. Duk wannan abu da suke yi Alh Indararo da Maman Danmama suna kofar dakin sai dai su basu kula da tsayuwarsu ba sannan shima yana so ya gama gane kan zancen kafin ya afkawa Salame. A can hostel dinsu kuma Emzee bayan ya gama nasa kukan shima babu wanda yake so da burin saukewa nauyin zuciyarsa sai mahaifinsa. A take shima ya soma kiran wayar Zayyan din. ********** Yana zaune a dakin Jume kan tabarma yana cin abincin da ta dafa masa da kanta suna hira. Abin mamakin da ya gani bai wuce sabon fenti ba ciki da wajen gidan ana ta gyare gyare wanda yawanci jikokin gidan samari keyi. "Wai ni wannan gyaran Jume waye zaiyi amarya ne?" Zayyan ya tambayeta yana dariya. " 'Yan uwanka ne suke son yin gyara saboda bikin Alheran mana. Ita ce fa jikar farko ta bangaren namiji a gidan nan ka ga kuwa mune da biki" Dadi yaji sosai "Allah Ya saka da alkhairi Jume nagode" Dan harararsa tayi "meye haka kamar wanda aka yiwa wani abu. Kai dai ka gama ci ga 'ya kayayyaki can da suka hadawa amarya." "Harda wata wahala kuma?" "Ashe ba 'yarsu bace indai abinda suka yi sunansa wahala" Saurin bata hakuri yayi ya gama cin abincin sannan ya mika mata wata leda mai kauri. Budewa yayi ya dauko kullin kudi guda uku kowanne dubu dari biyar biyar yace gashi nan ta bawa yayunsa Badaru, Rayyan da Maikudi. Sannan ya dauko kananun kullin su kuma dubu dari bibbiyu ne yace na matan ne su ma su uku. Wannan duk cikin kudin da aka bashi ne wanda yake ganin idan bai nemi lada ya raya zumunci dasu ba yayi asara kuma bai godewa Allah da ya dawo dashi gida lafiya ba. Jume sai kwalla tasa zani ta goge "Zayyanu da wane bakin zanyi maka godiya kuma in cigaba da rokon yafiya akan zaluncin da nayi maka?" Baya son tana yi masa haka domin uwa ya dauketa "kisa min albarka kawai Jume abar maganar. In Allah Ya yarda ke kuma hajjin wannan shekarar zamu je dake da Mairama" "Ayya...ayya Zayyanu...Allah Ya jikan Innarka da Malam. Na cutar da baiwar Allahn nan ashe nice da moriyar danta" tace tana kuka sosai. Cikin wanda ta ya fara bata na dubu dari biyar din ta dauko ta mika masa kuma tana sane saboda ta gano Maikudi ya taho dakin amma ya tsaya daga waje saboda ya hango Zayyan. "Wannan ka rike kayanka Zayyanu don wallahi ko kwabo bazan baiwa Maikudi ba." Da sauri Zayyan yake dubanta "haba Jume me yayi zafi haka?" "Komai ma. Zayyanu komai da komai yayi zafi daga lokacin da Maikudi ya danne dukiyar marayu sannan saboda bakin hali da tsantsar mugunta ya aika da sakon mutuwarsu har Nijar ya dakile masu tallafa musu" Maikudi yana daga waje yaji kamar ya rafka ihu. Shigowa yayi ya rakube a gefe ya durkusa amma ya kasa cewa Jume da kanin nasa komai. Ita kuwa kallon banza take masa saboda irin abubuwan da yayi da irin yadda itama ya rainata. "Saboda kaji ana zancen kudi shine ka taho ko? Ka gani..." tace tana dorawa Zayyan kudinsa "to na bashi kayansa ban kuma lamunce ya baka ba ko da a bayan idona ba. Yau ba don dawowar abokansa ba ina da yakinin haka za ka yi ta gina kanka da dukiyarsu batare da nadama ba" Zayyan kama bakinsa yayi tunda ita da danta sunfi kusa. Ba don zumunci domin Allah ake yinsa ba ko inuwar Maikudi bazai sake kallo ba. Mutumin da baiji tausayin matar da akace mijinta ya rasu ba ga danyen jego. Mutumin da yayi amfani da emotional sentiment din Mairama yasa ta hakura da takardun gidan mijinta akan wasikar da ya bar mata kafin ya tafi. Zumunci akwai dadi akwai wahala sai mutum ya daure ya kai zuciyarsa nesa. Wayarsa yaji tana vibrating ya dauko sai lokacin ya kula da missed call din Radhiya da na Emzee. Tashi yayi ya saka kudinsa a aljihu yace da Jume yana zuwa. Wurin dakin Innarsa yaje ya tsaya zai kirasu Maikudi ya biyo shi da sauri. Dukar da kai yayi saboda mugun kwarjinin da Zayyan yayi masa. "Yaya akayi?" Zayyan yace da dakakkiyar murya. Kamar wanda aka tsuma a cikin ruwa don kunya Maikudi ya dago kai yana hada hannuwa "Zayyan ka duba girman zumunci..." "Wannan ka biyo kenan Maikudi..." ya zura hannu ya dauko kudin ya mika masa "gashi na riga nayi niyya dama" Ja baya Maikudi yayi "ba kudinka nake so ba Zayyan. Nasan akwai kunya in kalli idanunka ko na iyalinka in roki gafara amma ku taimaka don Allah. Kawu Aminu yace dama akwai ranar da zanji kunya gashi ko shekara baiyi a kasa ba lokacin yazo" Zayyan yaji wayarsa ta sake vibrating kallo daya ya yiwa Maikudi yace " 'ya'yana suna bukata ta zamuyi magana anjima" Bai jira cewarsa ba ya daga wayar gabansa ya fadi saboda jin muryar Radhiya tana kuka. "Daada" tace lokaci guda tana kara sautin kukanta. Faduwar gaba yaji sosai da sauri ya rinka watsa mata tambayoyi "Alheran menene? Ina Umminku? Me ya faru?" Salame na jin ta ce Daada hankalinta ya sake tashi don Zayyan ne mutum na karshe da zata so yasan wannan abu. Jikinta ya hau bari musamman da idanunta su ka sauka akan Alhaji Indararo da Maman Danmama. Radhiya ko a jikinta sai ma kara kwantar da murya da tayi. "Ummi tana gidan Malamijo" "Ke kuma kina ina?" "Gidan Gwaggo Salame" ta fada tare da kara sautin kukan kamar lokacin ma dukanta ake yi. Cikin fada yace "Can nace kije ko nan mijinki ya tura ki?" "Kiji tsoron Allah Radhiya me nayi miki kike kara kuka haka" Salame tayi maganar tana komawa kalar tausayi sosai. Shi kuwa Zayyan kukan 'yarsa har kokon ransa yake jinsa. Lallabata ya koma yi don yaji me ya faru "Alheran dena kukan ko waye ya taba min ke ba kyalewa zanyi ba" Ba kunya ta sakarwa Salame murmushi sannan tasa speaker ta kure volume din wayar "Daada dukana tayi da wayar rediyo fatar bayana ta cire..." "Laaaaahhhh kuji min yarinya...ba Rahima nazo duka ba kika tare? Ni ina ruwana da 'ya'yan gidanku me zai kaini dukanku...." idanunta har sun fara tara kwalla saboda wani sauyin numfashi da take iya jiyowa na Zayyan ransa ya soma baci. "Wai don na gane ashe tana sonka kuma ita ta makanta Ummi don ta auri Alha...." Salame kasa hakuri tayi tasa hannu ta toshe bakin Radhiya saboda yadda Zayyan yace "ME???" da karfi. Alh Indararo yana jin haka shi kuma ya wawurota ji kake tas-tas ya tsittsinka mata mari. Zayyan da ya zata tasa 'yar ake duka a kidime ya kashe wayar ya kira Mairama. Baiwar Allah bata san me ake yi ba tana tare dasu Innawuro ana hira ta dauka. Abinda bata taba ji ba wato Zayyan ya daga mata murya taji a yau. Zai iya hakuri da komai banda taba masa 'ya'ya ba kuma wai don bashi da kara ba sai don yasan wacece Salame a da lokacin da bata ji kunyar kai masa kokon barar soyayya ba alhali yana neman kanwarta. Abu na biyu kuwa bai wuce shekarun da ya kwasa cike da tsananin kewar iyalinsa. Yanzu da ya sami dama ta biyu ba zaiyi wasa da ita yana ji yana gani 'ya'yansa suna zubar da hawaye ba. Bashi da uwa ba uba sai mata sai su. Baya fata amma ya sani ana chanja mata amma jininsa bazai iya taba chanja shi ba. "Kije gidan yayarki Salame ki dauko min Alheran sannan gobe zanzo na dauketa mu koma gida" Tashi tayi ta matsa daga cikin mutane hankali a tashe "Sojana ban fahimceka ba" "Nima ban fahimta ba Fillo.."yace cike da damuwa "Alheran ta kirani yanzu wai Salame tana dukanta da wayar rediyo...." Ko karshen zancen bata tsaya ji ba ta koma ciki da sauri danunta sun kada sunyi ja. Nanatawa take yi yau ko ita ko Salame...ta gaji da wannan halayya da take nuna mata. Rahima ma a yanzu ba bari zata yi ta tabata ba bare kuma Radhiyanta. Wani dauke kai da take yi akanta ba shine yake nufin bata son abarta ba. Bata hada son 'ya'yanta da komai sai dai sanin rayuwa da kyaun hali yasa bata sangartasu da soyayya ba. "Mairama ina zaki haka lokaci guda kin fita hayyacinki" cewar Yadikko tana tasowa ta riketa. "Gidan Salame zani Yadikko. Kuzo muje kuyi shaida ayi min tsakani da ita domin na rantse zan nuna mata duk abinda nake yi ba wai rashin sanin ciwon kai bane. Idan zumunci dani ne bata so a yau ni da kaina zansa wuka na datse shi uban kowa ma ya huta" Mama cire DK tayi da take shayarwa ta mikawa Laila ta dafa Mairama "kiyi hakuri ki fadi me tayi miki" Kowa ya ga Mairama yasan tana cikin bacin rai dama ga ta da zuciya. Hakurinta da yawan kau da kai shine yake sawa a ga kamar bata da fushi. "Babansu Karami ya kirani yanzu wai Salame tana dukan wannan yarinya da wayar rediyo" "Me kika ce?" Malamijo yace da sauri yana nufosu. Hayaniya yake ji har soro shine ya fito. Cikin kankanin lokaci Malamijo, Nene Marka, Yadikko da Hajjo su ka hadu da Mairama zasu tafi gidan Salame kowa ya kasa gane me yake faruwa. Mairama ta kira Radhiya amma tana dauka kuka kawai ta rinka yi bata ce komai ba. Zasu fita ta ga Mama Zainab a tsaye bata da niyar binsu. "Yanzun nan in fada miki ana dukan 'yarki amma ki tsaya a nan Zainab" cewar Mairama. Gani tayi abin ya shafi danginsu bai dace ta tura kai ba "Kuje ku dawo Ummin Awwab" Fushin nata kan Mama ya nemi komawa tana ta kumburi tace "kada kije din...kuma sai na fadawa Mami" fuuuu tayi gaba tana sababin da babu wanda ya santa dashi. Nene Marka tace "maza Zainabu dauko mayafinki wannan 'yar uwar taki bata iya fushi ba ko kadan" Duk da babu nisa motar Mairama suka shiga sabo mutane dreba ya ja su. ********** Bayan marin da Alh Indararo ya rinka saukewa Salame zuciyarsa a sama har yana haki ya nuna ta yatsa "naji komai kuma nasan komai. Sai yau na fahimci yaya akayi na aureki Salame" Radhiya gefe ta koma abinta bayanta na zugi tana jiran isowar su Ummi saboda Daada yace ta jira gasu nan zuwa. Kuka yaki zuwar wa Salame sai kumatunta duka biyun da ta rike zugi da radadi na shigarta. Cigaba yayi da fadansa sa'arsu daya babu yara a gidan kamar anyi shara. Dama na Salame ne masu zama su ma yau Radhiya tayi musu jan ido babu ko daya. "Lallai biri yayi kama da mutum. Salame ko ina shan giya me zai kaini aurenki bayan tun kina gidan Idris na sanki. Sau nawa nake bawa matana labarin yadda yake zuwa wurina neman bashi saboda ya auri hatsabibiyar mata mai bani-bani wadda ta raina shi. Kinsan talaka ne amma kike amfani da son da yake miki kika tatike shi. Ranar da zaki haifi Rahima ma idan baki sani ba ni na bashi aron mota aka kaiki asibiti. Sannan ragon suna da kika matsanta masa shima bashi ya nema a wurina sai da ya shekara uku ya iya hada min kudin ragon." "Alhaji me ya kawo wannan tone-tonen? Kada kace ka yarda da zancen yarinyar..." Mugun kallon da ya jefa mata yasa ta koma tayi lakwas "Salame kyan dan maciji asirinki ya tonu" ya nuna Maman Danmama "ga uwargidana nan ki tambayeta ko da Mairama ta makance nan nazo na fada musu matar da zan aura ta sami matsalar ido kuma tana da marayu. Idan ta tare duk wadda ta cutar da ita a bakin aurenta. Amma duk wannan abu lokaci guda naji zan iya rabuwa da kowa a kanki Salame. To albishirinki aikin boka yayi ci da kyau domin ke da gidan nan sai dai kiyi min takaba ko a fitar da gawarki. Kinzo kenan 'yar kundun uba" Wayar da ta gama dukan su Rahima da ita ya dauko daga kan kujera ya daga kawai ya shiga lafta mata. Saukar farko Salame ta zabura za tayi rawar 'yan bori. Ashe ba dadi ta sa matar da ya saki karshe sai da yayi mata dukan kawo wuka kawai saboda ta dakar mata 'ya. Dukan da yake mata ya soma firgita Radhiya da uwargidansa duk haushinta da suke ji Radhiya sai ta sami kanta da janyo Salame bayanta yayin da Maman Danmama ta rike hannun Alhajin yana ta kumfar baka yana masifa kamar ya ari baki. Numfarfashi Salame take saukewa su ka ji sallama daga waje wadda mai yinta ko ba'a fada ba yana cikin bacin rai ne da fushi. Ba'a dena sallamar ba cikin daga murya tare da dukan kofar gidan a fusace. Alh Indararo shima cikin bacin rai ya fita yaci karo da Idris rungume da 'yarsa Rahima idonta daya ya kumbura ga shatin waya yayi bororo a rabin fuskarta har wurin idon da samansa. Mutum mai hakuri ba sawa ba fitarwa irin Baffan Rahima yau shima an kure shi karshe ko gaisawa basuyi ba ya soma fada "Billahillazi huwar Rahmanu Alhaji ka gargadi matarka idan ba haka ba zan tube rigar mutumci in shiga har cikin gidan nan inci mutumcinta. Dubi wannan diban albarka da ta yiwa Rahima. Yau yarinyar nan ko zaman kishi suka yi da uwarta a yanzu da babu aure a tsakaninmu bata cancanci wannan abu ba bare kuma 'yar cikinta." Saukowa Alh Indararo yayi saboda yadda yarinyar ta bashi tausayi "dakata muyi magana Baban Rahima" "Wace irin dakatawa zanyi? Kullum da fargaba da komai ni ko Iya muke matsanta mata tazo gidannan saboda uwa uwace komai lalacewarta. Babu ranar da Rahima bazata dawo min gida da hawaye ba amma yau ka duba ka gani don Allah. Dubi yadda fuskarta ta koma daga zuwanta" Motar su Mairama ce ta tsaya suka firfito gabadayansu. Kafin su karaso Rahima ta kwasa a guje ta rungumeta tana kuka mai ban tausayi. Hajjo ce ta fara ganin fuskar ta dago kanta da sauri. Mairama ma ta gani a tsorace tace "meye wannan Rahima?" "Umma ce ta dakeni" Mairama cije lebenta kawai tayi ta damki hannun Rahima ko Alh Indararo da Baffan Rahiman bata tsaya yiwa kwakkwaran kallo ba ta shige cikin gidan tana cewa "SALAME kina ina?". ************************************ Cikin Salame kullewa yayi da ta ji muryar Mairama. Yau ko ba'a fada ba ta sani cewa kashinta ya bushe ta kure kanwarta ta. Radhiya kuwa da sauri ta iso bakin kofar dakin idanu sunyi ja sun kankance. Ummi na ganinta a haka taji hankalinta ya sake tashi yau 'yar kunyar ma babu ta janyota jikinta za ta dubata ta saki siririyar kara saboda bayanta da aka taba. Ai kuwa da sauri Ummi ta zaro idanu ta juya Radhiyan ta dage rigarta. Ga farar fata ga gyaran da take sha jiki yayi mugun laushi shiyasa wayar tayi mata wani dogon layi da yake tsartuwar jini daga tsakiya. Ruwan bala'i da masifa yau sun tarar wa Mairama ta kama hannun Radhiya ta hada da ba Rahima. "Kama kanwarki kuje Lucas yana mota ya kaiku MHC" Mama kallo daya ta yi a kofar dakin ta hango Salame kamar kaya jibge a kasa tayi saurin jan hannun Rahima saboda duk lalacewa baza su so ta ga mahaifiyarta a wannan halin ba. Da taimakonta suka kama Rahiman saboda ta fi Radhiya jin jiki suka fice. Itama bata son ayi a gabanta gara yau dai suyita ta kare a gaban mahaifinsu. Dama jiran fitarsu Ummi take yi tausayin Rahima ya dakatar da ita. Dakin ta banka kai ciki a fusace Salame ta mike da kyar. Cike da bacin rai da masifa Ummi tace "zuwa nayi mu saukewa juna iskokan dake kanmu Salame saboda na dade da fuskantar cewa kanki yana da matsala" Wai saboda karfin hali tana kallon kowa a tsaye ta kumburo baki "saboda na daki 'yar gwal shine kuka yo min taron dangi..." waje tayi sai ta tsaya turus gani ashe harda Malamijo da Nene, ga su Yadikko da Hajjo. A zatonta Mairama ce kadai da Baffan Rahima da ta gano tare da Alh Indararo shima tana jin ramawa tasa 'yar yazo yi. Bude baki tayi za ta sake yin magana Malamijo ya kai mata wani wawan marin da bazaka taba kawowa a ranka dan hannunsa zai iya ba. Hannu ne na tsohon kashi ya sake bata a kumatun hagu. Wasawasa sai da yayi mata yafi biyar wani tukukin bakinciki yasa ta kasa kuka. "Ke mahaukaciyar ina ce Salame? Na fuskanci burinki bakincikinki ya kaini lahira to amma baki isa ba. Ko Amiru da yake yawon jagaliya bai samin bakincikin da kike kunsa min ba" "Duk wannan abin akan Radhiya ne saboda ita kuna kaunar uwarta tunda babanta yana da kudi ko" "Rufewa mutane baki mutuniyar banza" cewar Nene tana jin kamar ta maketa. Jan bakinta tayi ta tsuke kowa a tsakar gidan ita yake yiwa kallon da take fassara shi da tsana. Mairama ta dubi iyayen nasu "Malamijo yau gani ga ka ga kuma babbar 'yarka. Ban san me nayi mata ba tsayin shekarun nan tun farkon aurenmu amma wallahi na gaji. Daga yau sai yau idan ta kuskura ta sake taba min yara zan dauki matakin da mu duka nan sai ran kowa in yayi dubu ya baci." Ta mayar da idanu ga Salame "Wai da nake ta taraki ki sani ba tsoro bane kawai ina yi ne da sa ran wata rana zaki ajiye makaman yakinki mu zauna lafiya. Amma tunda kince ba haka ba mu zuba nida ke shege ka fasa. Duk wani zafin rai da kike takama dashi kin kwana da sanin Mairama tana da dubunsa a ajiye" "Kinga malama ni dai ba da niya na taba Radhiya ba. Rahima zan daka ta tare wayar ta sauka a bayanta ko ba haka ba?" Ta tambayi iska tunda babu mai bata amsa jikinta yana kadawa kada a cigaba da maganar nan allura ta tono garma. Malamijo zaiyi magana Mairama ta riga shi "assha 'yar uwa, kada kiyi tunanin dukan Alheran kadai ya kawoni ko daya. Gobe kafin wannan lokacin zaki baiwa ubanta bayanin dalilin dukan masa 'ya, kuma kada ki manta matar aure ce ban san me zai faru ba idan mijinta ya ji. Wannan diban albarka da kike yiwa Rahima kadai ya isheni. Don ta ni kin dade baki yi min rashin mutumci ba. Ranar da duk na gaji na fyatoki ba ganuwa zakiyi ba" Dariyar Alh Indararo ce ta katse Mairama "wai ke nan duk masifar akan dukan da tayiwa Rahima ne dama? To ni tunda na auri Salame ban taba ganin yarinyar nan ta shigo gidan nan ta fita babu kwalla a idonta ba. Wannan kuma kadan ne cikin abubuwan da tayi miki" "Me kake nufi Alhaji? Wai me kika dauki Rahima ne Salame?" Baffan Rahima ya tambaye shi a zatonsa ta yiwa 'yar tasa abinda yafi wanda ya gani "yanzu ashe alkhairi zai iya zama sharri, sharrin ma ka rasa wanda zaka yiwa sai dan cikinka. Kudine dubu dari da 'yan kai Rahima ta kawo tace min a Habuja tayi lalle ta samu. Shine aka raba kudin ni talatin itama uwar aka ce ta kawo mata talatin sauran kuwa zamu fara yi mata tanadin aure. Shikenan daga zuwanta ta dawo min gida da fuska a kumbure" ya kare zuciyarsa a karye saboda shi ba ma'abocin fada bane. Mutum ne mai kyaun hali da matukar hakuri. Kaddararsa daya bata wuce soyayyar Salame da tayi masa mugun kamu ba ashe rabon haihuwa ne yasa ya aureta. Maganganunsa ba karamin shigar Salame tayi ba sai lokacin ta sake kallon ledar da Rahimar ta yar saboda marukan da ta sha. Kenan Mairama sake bawa Rahima wani kudin tayi a madadin wanda ta karbe? Wani abu taji yana neman danne mata zuciya sai dai bata yi nisa ba ta tsinkayi muryar Alh Indararo yana cewa "wanda bashi da kashin arziki ko a cikin rijiyar kudi zaka tsoma shi bazai taba yi ba. Nan ta dawo da kudi dubu dari tana yi mana burga wai 'yarta ta fara sana'a. Ci banza ci hofi bana jin akwai sauransu yanzu ma." Kallon banza Mairama ta watsa mata saboda da gani babu abin tsinta a jikin Salame bayan tsiya tsagwaronta. Juyawa tayi da zummar fita daga gidan Alh Indararo ya ga idan yayi shiru ai wasa ya kare bayan ko rabin tanadin da ya yiwa Salame na bakinciki bai idar ba. Fada sosai Malamijo da su Nene suke yiwa Salame shi kuwa yayi saurin tsayar da ita. "Mairama ince ko kina da masaniyar cewa duk wannan rashin hankalin da Salame take yi miki tana yi ne saboda son mijinki da take yi" Cak Mairama ta tsaya ta juyo a hankali ta koma gaban Salame ta rike hannayenta duka biyu ta soma yi mata fada tamkar 'yar cikinta "da gaske baki da hankali ne Adda? Ta yaya za'ayi ki bari duniya tasan cewa kina son mijin kanwarki? A lokacin da ake zaton babansu Karami ya rasu babu kunya kika dubi idanuna ina zaman kunci da zafin rabuwa kika fada min kinso shi na hakura ban taba daga zancen ba. Adda Salame a lokacin har tausayinki na ji saboda soyayya bata taba yiwa mutum uzuri sai nake ganin ba laifinki bane." Hawaye ne mai zafi ya ke fito mata saboda rashin sanin wace irin mutum yayarta ta zama "idan kika kuskura kika bari su Halifa suka san wannan abin nayi miki rantsuwa abinda ya rage na kimarki da darajar uwa a zukatansu sai ya tsiyaye ya bi rariya." Baki na rawa Salame ta iya hada kalmomin "sharri...sharri ne. Sharri yake min" Tsawa Malamijo ya daka mata "Ki rufe min baki shashashar banza wadda bata san ciwon kanta ba...ko kinsan ko sati biyu bamu rufa ba da nasa Halifa ya hadani da babansa kuma ya tabbatar min dalilinsa na sakinki kenan. Har yaushe zaki cigaba da karar da rayuwarki akan hangen ta wani" Mairama gani tayi idan ta cigaba da tsayuwa ba mamaki a kwashi Salame a baro saboda ji take yau da ita ce ta haifeta sai tayi mata dukan kawo wuka ko za'ayi sa'a kanta ya dawo daidai. Abinda Nene Marka take ta gudun fitowarsa Alh Indararo yace "ke kuwa wace irin zuciya gareki Mairama? Ta so mijinki kin sani baki dauki mataki ba sannan ta makanta ki tsahon shekaru shima duk taci bulus kenan? To idan ke kin hakura ni bazan yafe ha'incin da tayi min ba na asirin aurenta ba tare da son raina ba" Suman tsaye Mairama tayi jikinta yana bari kamar wadda aka kwara wa ruwan sanyi wani irin kallo take yiwa Salame ita kuwa sai girgiza kai take yi tana hawaye tare da yarfe hannuwa. Bata taba jin tsoron batawa wani mahaluki rai ba sai yau da take jin ta tsani kanta saboda sabanin kallon tsana ko fushi sai ta ga kallon tausayi sosai Mairama take yi mata. Idanu Mairama ta rufe hawaye suka zubo tasa bayan hannunta share sannan tayi murmushin kafi kuka ciwo. Muryarta tayi mugun sanyi ta dafa kafadar Salame tace "A kaina saboda ba kya kaunar ganin murmushi a saman fuskata kika yi shirka Adda? Shin Adda kina tunanin zaki iya rayuwar da nayi ne har kika zabi neman yadda zaki mayar da rayuwata taki? Kin taba tsawaita tunani kice Mairama shekararta ashirin da hudu da aure amma har yau bata taba zaman shekara uku tare da mijinta ba har girma ya soma zuwa garesu. Ban san kiyayyar da kike yi min ta kai haka ba amma ina rokonki da ta tsaya a kaina ni kadai kada ki kuma bari ta shafi 'ya'ya. Daga yau kuma nayi miki alkawarin idan har ba bisa lalura ba ko ke kika nema da kanki bazaki kara ganin fuskar Mairama ba bare ta sanya miki bacin rai." Tafiya ta soma yi cikin wani irin kunci mara misaltuwa su Malamijo suka bi bayanta tunda babu wani amfanin jan magana kuma. Bacin rai sosai Mairama take ji a wannan lokacin. Ita kam bata taba nufin kowa da sharri ba amma ga wadda tafi so duk duniya tun kafin tasan kanta tana neman ganin bayanta. Wanda zai makantaka ko na kwana guda ne ai babban makiyi ne bare wannan shekaru haka cikin kwanciyar hankali. Da sauri Salame cikin rashin sanin madafa ta bi bayansu ta sha gaban Mairama. Kuka ta ga kanwarta tana yi sosai fuskarta tayi ja. "Me kuma ya rage, raina kike nema?" Mairama tace da kaushin murya. Da sauri Salame ta girgiza kai "to bani hanya in wuce don ni da kike gani na haufu cikin uwa da uba bana amai na lashe. Tunda nace kin dena ganin fuskar da kika tsana to kin daina da gaske ba wasa ba" tace tana rabewa ta gefenta ta fita daga gidan. A kafa su ka tafi gida babu mai cewa wani uffan kowa da nasa tunani. Sun kusa kofar gidansu Malamijo ya yanke jiki ya fadi tunani yayi masa yawa saboda ko ba'a fada ba ya sani cewa shine musabbabin lalacewar duk wani bara gurbi ciki 'ya'yansa kamar yadda yasan cewa duk wanda ya shiryu a cikinsu daga Allah ne da taimakon Yadikko matar da bata haifi ko tsinke ba amma taci kashi da fitsarin kusan duka 'ya'yansa. Allah Yasa Baffan Rahima yana biye dasu saboda son ya ga halin da 'yarsa take ciki ya tafi da ita gida. Hankalinsu duk ya tashi musamman Mairama da take yiwa yau din kallon bakar rana ya ciccibe shi ya saba a kafada ya karasa dashi gidan. A kidime Mairama ta kira Radhiya ta turo musu Lucas tace ai sun kusa gida an duba su. Da sauri sauri suke shirin saka shi a mota ya farfado yace babu inda zashi. Hajjo tun tana lallaba shi har ta koma fada "so kake ka cuceni kawai. Cikin shekarar nan na dana zaman iddah yanzu kuma takaba kake son kakaba min don mugunta daga dawowata" Duk da yana jin jiki bai hana shi galla mata harara ba "ina jin har kin gama lissafin tumunin takaba to ta Allah ba taki ba. Ina nan garau ba mutuwa zanyi ba. Ke in bakiyi wasa ba fa Hajjo sai na kaiki zan taho daga baya" Cinya ta buga tana dariyar jindadin ya tashi amma duk da haka bata barshi haka ba "ashe da rabon ayi suna da kai" Sam ya manta a waje suke ya kalleta a tsorace yana hadiyar yawu da kyar "wace take da ciki kuma ni Ali wai ku baku da tausayi ne bazaku barni na huta ba" Radhiya, Rahima da Mama basu san lokacin da suka sa dariya ba Ummi ta tallewa Radhiya da Rahima keya tana murmushi suka shige cikin gidan. Manyan daki suka shiga suna cigaba da tattaunawa Mama da Ummi kuma su ka tafi dakin da aka basu. Radhiya ma da Rahima daki daya suka shiga nan Rahima tana hawaye ta soma cewa Addarta tayi hakuri da abinda Ummansu tayi mata. Daure fuska Radhiya tayi tana harararta da wasa "Rahima bana son kina sake tada wannan maganar. Nasan ko ma meye su Ummi sun gama daidaitawa a junansu babu ruwanki" Wani kukan ne ya taho mata ga idonta daya yana zugi kamar zai fado "Adda ni shikenan Umma bata sona, me nayi mata ta tsaneni?" Tausayi da kaunar kanwarta ya sake kamata ta zauna a kusa da ita ta rungumeta haushin Salame yana kara kamata. Allah Yasa kada Rahima taji sauran maganar game da Gwaggo Salame don tasan it will break her heart fiye da yanzu. A tausashe tace "Ummi tana sonki kinji kuma bazata sake bari ta dakeki ba" "Mu ga bayanki" Rahiman tace a kokarinta na nemo nutsuwa ta yafawa kanta a dole. Radhiya kwanciya tayi Rahima ta dage rigarta wurin yayi wani iri da yanzu ita za'a sake saukewa wannan bulala bayan wadda ta sauka a fuskarta. Maganin da aka basu tace za ta shafa mata Radhiyan tace ta bari suyi wanka sai su shafa. A dakin da su Ummi suke kuwa suna shiga ta haye gado ta kwanta tare da juyawa kofa baya. Kuka take yi sosai jikinta har wata irin karkarwa yake yi. Abin na Adda Salame har ya kai haka ashe. Ita kuwa banda auren Zayyan me kuma tayi ta konawa 'yar uwarta rai haka. Mama jikinta duk yayi sanyi a hankali ta zagaya gabanta ta zauna daga gefe. "Mairama" tace cikin sigar rarrashi. Sake juya mata baya tayi muryarta har tana sarkewa tace "ki barni inyi kuka Zainab, ashe a duniya akwai wanda zai tsaneni har ta kai ga yi min asiri na makance. Ina nan ina yiwa kaina kallon wadda bata shiga gonar kowa ba ashe na kure yayata kiyayar tayi tsamari" dago rinannun idanunta tayi suka hada ido tace "Allah kadai Yasan mutum nawa ne suka tsaneni" Hawaye Mama ta soma yi itama "mijinki yana sonki Mairama. Ni da Mami muna kaunarki kamar ciki daya muka fito kuma ga Malamijo da sauran mutanen gidan nan, banda su Radhiya rabin rai" ta dage mata gira. Murmushi Ummi tayi kamaninta da Radhiyan suka fito sosai "nagode Zainab Allah Ya kara mana zumunci. Inama Mami tana nan da nasan bazata gudu ta barni yadda kika yi ba dazu kawai ina cikin fada na juya neman support na ga wayam" Mama sai da tayi dariya sannan ta kira mata Mami. Tana dauka bayan sun gaisa take basu labarin yadda suka yi da Alh Baba wurin shiryasu ita da kannenta. "Nan ma fa fama muke ina jin shirin ne za'ayi idan an gama hawa saman" cewar Mama. Ummi cikin kuka take yi musu bayanin abubuwan da suka faru. Su duka ukun kuka suke yi musamman Mami da tayi nisa tana jin kamar tayi tsuntsuwa tazo ta wanke Salame irin wankin babban bargon nan. Zumuncin da yake tsakanin su uku abin burgewa ne da sha'awa domin kowacce da zuciya daya take son sauran. Bayan sun gama Mama tace "to saura Oga tun dazu wayarki ke haske nasan shine" Murmushi na musamman Ummi tayi ta mika hannu ta dauko wayar wanda yayi daidai da sake kiranta da Zayyan yayi. Tana dauka ko sallama bata yi masa ba ya kira sunanta a kagauce saboda yadda hankalinsa ya tashi. Jin muryarsa kadai ya sake tado mata abinda Salame tayi sai kawai ta fashe masa da kuka. Yi take yana sauraronta yayin da Mama ta dauke DK tayi waje don ta basu wuri. Sai da tayi mai isarta tayi shiru don kanta. Hakuri ya bata tare da kalmomi na kwantar da hankali sannan ya nemi jin ba'asi. "Ki kwantar da hankalinki gobe in sha Allahu jirgin safe zan biyo" "Sojana" yaji ta yi masa kiran da dole ya amsa. "Mairama Fillon Zayyan me kuma akayi?" Kukan yaji ta cigaba da yi "Don Allah ka fada min ni muguwa ce ko naso kaina ne da yawa da na aureka har ya janyo min kiyayyar Adda Salame?" Ta fada da wata irin murya abin tausayi. Kwafa yayi kawai yana jin kamar ya baro garin Sakkwato a lokacin saboda yazo ya nunawa Salame kurenta. "Ki bari inzo goben sai na baki amsar da ta dace. A haka babu abinda zaki fahimta" "To don Allah ka taho da wuri sosai, yau ina jin ko bacci bazan iya ba" "Saboda kewata ko saboda Salame ikon Allah?" Dariya ya bata "bani da sauran abinda zance mata na bar maka komai Daadan Alheran" ta kare cike da kunya. "Ki cire komai da kowa a ranki ki barni ni kadai yau dinnan bana son tunani ya dameki. Ina nan tare dake babu wanda zai taba min ke batare da na nuna masa mijinki yana sonki ba" Sannu a hankali ya mayar da akalar hirar ta soyayya inda yayi nasarar rabata da duk wata damuwa. ********** Hawaye kafewa yayi a idanun Salame tun bayan fitarsu Mairama ta koma ciki tana tafe kamar kwai ya fashe mata a ciki ta shige dakinta. Mayafi ta dauko ta fito Alh Indararo yayi wuf ya fito daga falonsa. "Ina zaki je?" Bata da wani kuzari bare tayi masa rashin kunya "ka yiwa Allah ka barni inje gidan Ta Madina" Baki ya rike saboda tsabar mamaki kamar wata mace "Ta Madina dai mahaifiyarki?" Kai ta gyada masa kai kace kadangaruwa ce. "To sai kin dawo yau nasan zata ce tayi gamo. Idan kin fita ki turo min 'ya'yana. Kuma Yasin kika kuskura isha ta riskeki a waje ko a ina ne har can zani na sabunta miki kamanni muguwa mai muguwar zuciya" Bata iya tankawa ba ta fita tayi sa'a kuwa jikin gidansu yaran suka shiga. Gida tace su koma sannan ta wuce gidan babarta a kafa tafiyar minti sha bakwai ta kaita. Da sallama ta shiga jama'ar gidan su ka rinka kallonta kamar an ga wata sabuwar halitta. Babu wanda ta kula ta kunna kai dakin Ta Madina ta sameta zaune akan tabarma tana gurza goro. Da mamaki ta dago tana kallonta kafin ta soma magana. "Iko sai Lillahi...Salame ke nake gani ko kuma gizo kike min. Tohhh ni dai ban kwana dake a raina ba bare ace saka ki nake a zuci har kika fara min gizo" Daga bakin kofar Salame ta zube saboda ganin uwa mai dadi ta shiga kuka tun daga kasan zuciyarta. Ta Madina kamar mai kallon film haka ta kare mata kallo ta gama kukan bata ce komai ba. Sai da ta fuskanci kamar tayi shiru ta tabe baki tace "alhaki kwikuyo ya biyoki kenan. Ina kyautata zaton wannan hawayen na Rahima ne ko hakkinta. Ko ma wanne ne a dakin nan nace miki da sannu zaki ganewa idanunki illar abinda kike matar Alhaji" Da kyar ta iya cewa "Ta Madina baki kika yi min gashi ya kamani" "Karya kike" ta nunata da yatsa a harzuke "ke idan nayi miki baki buzunki ma bazai ganu ba in fada miki." Kai ta sunkuyar tana ji Ta Madina ta cigaba da fada "wai ni Salame zaki nunawa kina auren maikudi ban isa dake ba. Nan inda kike zaune lokacin kika tsaya kina fada min maganganu saboda Rahima tazo ta roki in baki hakuri ki yafe mata ko ma menene tayi ki dena dukanta. Saboda kinci maiko kin tada kai kika kada baki kika ce mata idan ta kuma zuwa wurina baki yafe mata nononki da tasha ba. Ni...ni Salame kika yiwa wannan rashin arziki" Ta sani ita din mai laifi ce sosai a wurin mahaifiyarta. Idan bata ga ba daidai ba a dalilin kowa dole ne ta gani a dalilin Ta Madina. Muryarta ta ji tana ta koro bayani kamar yau akayi. "Yarinyar nan tayi kuka kamar me tun daga ranar idan tazo daga waje take kwada sallama na fita mu gaisa. Yau shekara biyu rabona da ita saboda kaninki Sa'adu rannan yayi fushi ya daukota a ka ya dire min ita yace idan kin isa kizo gabansa ki tabata. Da yake ta gaji halin kwarai wurin babanta a guje ta fita tana tuna kalmar rashin yafiya da kika jefa mata...shikenan ta dena zuwa" Ajiyar zuciya ta saki ta gurfanar da kai "Ta Madina ki yafe min amma yau abinda ke damuna yafi karfin Rahima" "Wa kuma kika tabo kuma?" Cikin kuka ta zayyane mata komai batare da ta boye wani abu ba. Bacin rai sosai take gani akan fuskar Ta Madina kafin ta nuna mata kofa "ga hanya nan idan kika sake shigo min gida nima ban yaf...." A guje Salame ta tashi "kada ki karasa zan tafi" "Baki ga komai ba ma indai bazaki dena wannan shashancin ba. Duk kinbi kin tsangwani kanki kin lalace kamar alayyahu yaji rana" Ta Madina ta daga murya yadda zata ji. Sai da ta tabbatar ta tafi kuma hankalinta ya tashi kawai sai ta kira wata jikarta 'yar kanin Salamen ta saka ta kiran Halifa a waya. Cewa tayi ya gaggauta zuwa Sumaila indau yana Kano yace to. Rahima ya kira tana dauka ta fashe masa da kuka sai ya kara jin hankalinsa ya tashi. Gashi ta kasa cewa komai. A ranar ya dauko hanya kai tsaye gidan Ta Madina yaje. Matsa mata yayi da tambaya ta kasa cewa komai kawai ya wuce gidan Alh Indararo gashi dare yayi. Alhajin da bai san ina Salame ta makale ba ya fyede masa biri har bindi....bai karasa bindin ba dai tunda kuwa iyaka abinda ya fada masa bayan dukan Rahima da 'yae uwarta wadda ya gano Radhiya ce daga kwatancen da yayi masa sai kuma baton makanta Mairama. Bai kai ga fada masa soyayyarta ga Zayyan ba Maman Danmama tayi saurin dakatar dashi. Halifa idanunsa kamar garwashi sai jijiyoyin kansa da suka tashi kamar zasu fasa fatar su fito. Cije lebensa na kasa yayi har yana jin dandanon gishiri yana magana da kyar yace "yanzu kowa ya sani?" "Ina maganar kowa Halifa, wannan zance fa yarinyar Mairaman ce ta kira waya wani yake fada mata muna ji mu kuma. Da su Malamijo suka zo kowa yaji mana." Hawaye Halifa ya soma abin tausayi "Rahima ma ta sani?" "Eh tohhh...lokacin da muke zancen dai bata gidan sun tafi asibiti amma ban sani ba wala Allah ko a can gidan an fada mata." Alh Indararo yace bayan guntun tunani. Jiki a sanyaye kamar wanda yasha duka ya kira Mairama. Tana ganin kiran hankalinta ya tashi. Kuka Halifa ya saka mata muryarsa tana rawa yake mata magana. "Ummi ki yafe mata ba don ita ba don Allah..." "Halifa kana ina?" "Gidanta" "Waye ya fada maka?" Tace tana taya shi kukan. "Yanzu zan zo gidan Malamijo amma don Allah don sonki da Annabi Ummi kada ki bari Rahima taji don bansan yadda zata dauki abin ba" Kwantar da murya tayi tace ya taho tana jiransa. Babu wanda ya san ya shigo ta kaishi dakin Malamijo inda ya sha kukansa kamar ba gobe Malamijo yana ta bashi baki. Ranar babu wanda yayi baccin kirki cikin manyan ba don komai ba kuwa sai tausayin Halifa da yadda ya dami kansa. Radhiya sai da ta ga Rahima ta kwanta ta soma nata kukan itama. Tana tausayin 'ya'yan Gwaggon tasu sannan a gefe daya ta tsaneta saboda wahalar da ta sanya Umminta fuskanta. Awwab ba karamar damuwa ya shiga ba da yayi ta kiranta babu amsa ashe ta yar da wayar a dakin Salame. Itama bata tuna ba sai daga baya sai dai bata son yaji muryarta a yadda take gashi kowa da tasa damuwar shiyasa ta kasa aron waya. Cikin bargon kuma Rahima ce ta boye kanta tayi kuka har sai da taji kanta yana neman rabewa biyu don ciwo. Bata san me Ummanta tayi ba amma yanzu ace mahaifiyar mutum tayi masa tsanar da sai wasu ne suke tare masa? Wace irin kiyayya take gwada mata da har ta kasa ko da sau daya yi mata kallo irin wanda take yiwa sauran 'ya'yanta? Da wannan tulin tambayoyin bacci a kwasheta. Gashi ta kira Emzee yafi sau ashirin sai dai wayar ta tsinke don kanta batare da ya dauka ba. ********* A bangaren Emzee wutar kiyayyar Rahima ke cin ransa kamar gobara yayin da ya kasa gane a wane matsayi ya barta a cikin zuciyarsa. Kunci da bacin ran da ya shiga a wannan dare bazai misaltu ba. Da abin ya ishe shi Daada ya kira ya rasa yadda zaiyi ya fada masa halin da zuciyarsa take ciki. Ya dai yi masa kuka abinda ya daurewa Zayyan kai sosai. Kallon jarumi mai dakakkiyar zuciya yake yiwa dan nasa ashe akwai abinda zai kawo hawaye a idon mazaje. "Ba kace dama an baka leave har zuwa bikin Alheran ba?" Ya tambaye shi bayan ya samu yayi shiru. "Eh Daada" "Gobe da sassafe ka sameni a Kano Janguza barrack wurin Captain Onomza zamu je Sumaila tare. Akwai jirgi karfe bakwai da rabi shi zan biyo in sha Allah" Suna gama wayar ya kira Captain Onomza ya sanar dashi yana bukatar mota guda ta sojoji. Allah Yasa da uniform dinsa a mota sai dai tunda ba da dreban zai tafi ba zai dauki jakar ne kawai. Akwai mutum uku da suke tare a daya motar masu bashi kariya duka dasu zai tafi Kano. Ziyarar tasa ba official visit bane amma ya kamata a tauna tsakuwa domin aya taji tsoro. Yau daya banda Mairama, Alheran da Zayyanunsa da yayi ta aikin rarrashi daga nan Allah kadai Yasan mutum nawa Salame ta sa zubar da hawaye. Ita mace ce mai rauni bazai dauki hukunci irin wanda aka yiwa Maikudi ba akanta amma tabbas zai nuna mata ta taba masa mutane mafiya suyowa a ransa. 💕 11/2, 8:04 AM]****** 59💕 Daddy ya fito daga daki ya tarar da Awwab yasa Mami a gaba kamar zaiyi kuka. Yana ganin mahaifinsa ya tashi da sauri "yauwa Daddy ka ga Mami ko" Girgiza kai tayi da guntun murmushi ta kalli maigidanta da yake yi mata kallon tuhuma tace "yana da hannu, waya da kuma kudin kiran waya amma haka kawai yazo ya tsattsareni da tambayoyi, to nima ban sani ba" Idanun Daddy suka koma kan Awwab jikinsa a sanyaye ga damuwa karara yace masa "wa kake so ta kira maka?" Mami ta riga shi cewa "zuwa yayi fa zaiyi min wayo...wai nayi waya da su Ummi nace eh, shine ya koma tambayar wai in sake kira inji kowa da kowa lafiya yake. Idan matarsa yake nema baya samu ya kira Ummin tashi da kansa mana" Murmushi Daddy yayi "kinci sa'a babansu Sakkwato yaje da da kaina zan kira ince a kaiwa 'yata mijinta yana nemanta" Kai Awwab ya sunkuyar yana jin kunyar mahaifin nasa. Da ya ga abin bazai kare ba Mami tana tsokanarsa ya tashi ya gudu amma zuciyarsa babu dadi ko kadan. A tunaninsa ko bata da chaji za ta ari waya ta kira shi musamman tunda tafiya su ka yi tasan cewa zai damu da jin lafiyarta. Tamkar an tsikare shi ya sake janyo wayarsa ya kira Zayyana shiru bata shiga sai ya nemi Zahra yace ta bata tace masa tayi bacci. Kai ya dan sosa ya kashe tare da kiran Emzee. Rai a jagule ya dauka duk da ganin nambar Awwab din amma baya cikin nutsuwa. Daga muryarsa kadai Awwab ya gane akwai abinda yake damunsa. Emzee da yake very jovial amma yanzu da kyar yake amsa masa. Tambayarsa nambar Rahima yayi tunda yasan duk rintsi suna tare da Alheran. "Bani da ita" yace a takaice yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa. Tun dazu ya goge numbar abin bakinciki da takaici shine lokacin da ya bude zaiyi deleting a take kwakwalwarsa ta haddaceta. Abin ya bawa Awwab mamaki yace "ka ji me nace kuwa? Numbar Rahima fa...Alheran nake nema tun suna hanya ban sake jinta ba" "Hamma bani da ita kuma ba kanwata bace idan kana so zan turo maka ta wasu a gidan ko ka kira ta Mama" Sai lokacin ya tuna da Mama aka tafi da tuni ya kira ta. Yanayin kanin nasa ne ya dame shi a tausashe yace "Emzee are you okay?" Zafi kirjinsa yake masa yana kara jin haushin wannan soyayya da yake yiwa Rahima. Dumin hawaye yaji a karo na barkatai yau yana zubar da hawaye. "No" "Want to talk about it?" Awwab yace a hankali saboda ya kwantar masa da hankali. Muryarsa gabadaya tayi breaking kana ji kasan kuka ne ake dannewa "Not yet Hamma kawai ka tayani da addu'a" "Shikenan amma zan jira zuwa lokacin da za ka iya fada min idan wanda zan baka shawara ne sai na baka. A problem shared is half solved" Ajiye wayar su ka yi bayan ya dan ja Emzee din da hira. Sam yaji hankalinsa ya kasa kwanciya ya yanke shawarar komawa wurin Mami ya kuma rokar arzikin ta kira Ummi shi dai burinsa ace kowa lafiya ko da baiyi magana da matarsa ba. Falon gidan ya nufa lokacin wurin takwas na dare. Tun kafin ya shiga yake jin murya kamar ta Ghazalatu da Mummy Gambo. Mamaki yake me suke a gidan a daren nan. Yana shiga Mummy Gambo ta soma dariya "ango kasha kamshi" A ladabce ya gaisheta yana tambayarta Daddy Haroun. Mami ya tambaya Daddy tace yana daki ya shiga. Tunda ya shigo Ghazalatu ta kasa sukuni sai aukin murmushi tana fari da idanu sai da Mummy ta zungereta "baki gaishe da yayanki ba" Ta turo baki "to ba shi bane kamar bai ganni ba" Wucewa yayi abinsa duk da yana jin Mami tana cewa me yasa zai share mata 'ya. A ransa yace "Mami kenan, kema dai kin fada ne kawai don kada ace baki damu ba" Mummy Gambo tace "jira kike yi ya fara gaisheki ko me da zaki ce kamar bai ganki ba? To ni dai bana son rashin kunya. Ku sulhunta ke da dan uwanki a cigaba da zumunci kamar da" Murmushi Mami tayi don kada ta gwasale kanwarta a kokarinta na son farfado da zumuncinsu "kyalesu Gambo sun fi kusa ai, tashi Ghazalatu ki shiga wurin Zahra nasan tana daki tunda har yanzu Bilal da Raji basu dawo ba" Tana tafiya Mami ta cewa Gambo gobe ta shirya su je gidan Hussaina. "Babu inda zani Mami ki barta kawai. Tunda ita ta gina min gadar zaren nan na rufta sai ta kare kalau" "Ba'a haka Gambo. Kada mu sake bari shaidan yayi galaba a kanmu. Ki duba sau nawa Umma tana kuka akan wannan sabanin. Indai ba so muke muma wata rana mu zubar da hawaye a dalilin faruwar irin haka ga namu 'ya'yan ba to mu bar komai ya wuce" A can dakin Daddy kuma waya suke da Zayyan ya fada masa yadda su ka yi da Mairama. "Ka bani shawara me ya kamata na yiwa matar nan. Idan banyi mata abinda za ta ji sosai ba komawa wurin boka ko wani tsibbu ba wahala zaiyi mata ba" "Na rasa yadda akayi zumunci ya lalace haka wallahi. A fito tsatso daya ko ma ciki daya amma ka ga mun rufe ido muna neman ganin bayan juna. Hassada tayi mana mummunan kamu ita ce tushen komai" cewar Daddy cike da takaici. "Akwai wanda zaiyi sama da abinda Maikudi yayi min kuwa? Banda kwashe komai ya kara da toshe hanyoyin da taimako zai iya samun Mairama...wani abin sai dai muyi kawai domin Allah ba don halin mutum ba" Daddy tunawa yayi da yadda Maikudi ya jigata a hannuwansu saboda ba karamin bakinciki suka ji ba da abubuwan da ya yiwa iyalin Zayyan sannan ya auna da makantar shekara goma "daga shi har ita yayar Mairaman babu gwara. Makanta ko ta wuni daya ce fa ba abin mantawa bane" Shawara Daddy ya bashi daidai da yadda yake ganin ko shine abinda zaiyi kenan. Yana dariya ya kara da cewa "ba don mun fara tara jikoki ba da mun kwashi 'yan kallo a garin Sumaila gobe." Zayyan ma dariya yayi yana jin Daddy na cewa Awwab ya zauna ya jira shi ya gama waya. "Ka fada masa abinda ya faru don nasan Alheran ba fada masa zata yi ba kuma hakkinsa ne ya sani." "To sarkin taya bera bari" "Zancen gaskiya fa kaga matarsa ce, don dai kawai mun biyewa mata ance sai anyi biki da tana gidansa babu mai shiga cikin case dinnan cikinmu duk wanda ya tabata da shi zasu gamu. Kace ya sameni a Kano kafin shabiyu goben kawai" "So kake ku hana matar mutane kwanciyar hankali ne kake ta tara mata gayya?" "Tsuntsun da yaja ruwa..." Zayyan yace yana shafa sajensa. Suna gama wayar kuwa Daddy ya fadawa Awwab saboda duk a zatonsu duka sosai Salame ta yiwa Radhiya tunda da ta kira Daada kuka take yi fiye da yadda dukan yake mata zafi. Ita kuwa tayi ne kawai don yazo ya a kawo karshen mulkin Gwaggo Salame. Ai kuwa Awwab ya shiga tashin hankali sosai bai iya bacci ba har garin Allah Ya waye yana tunanin wane irin duka ne aka yi mata. Ganin ba iya bacci zaiyi ba kawai karfe shida da rabi ya shirya cikin kananun kaya wandonsa chinos ruwan toka da polo shirt fara. Agogo yake daurawa lokacin da maganar Emzee ta fado masa da yace Rahima ba kanwarsa bace, ba mamaki dalilin faruwar wannan abu ne. Sai yaji ya kara tsorata da zumuncin yanzu. Kafin takwas yana hanya don shi bai dauki tuki a bakin komai ba. Shima Zayyan jirgin bakwai da rabi ya biyo yana ta jujjuya maganganunsu da Hadir da Major na daren jiya. Kafin ya sauka Captain Onomza ya turo mota aka dauke shi zuwa Janguza barrak. Tara da rabi Emzee ya iso su ka jira Awwab shi ma goma da 'yan kai yana barrack din don ma bai san hanya ba da kwatance ya karasa. Sun gama shirinsu motoci biyu cike da sojoji ta ukun Major General Zayyan Tureta ne da dreba da kuma escort dinsa da suke yawo tare sai kuma motar bayansu Emzee da Awwab. Kafin su bar barrack din ya kira Mairama inda ya bata umarnin ta tabbatar gidan nan babu yara kafin ya iso. "Ina nufin ko su Alheran bana son na tarar sannan kananun yaran gidan duka kowa ya fita." "An gama ranka ya dade" tace tana kirkirar murmushi. Kebewa tayi da su Yadikko ta fada musu su ka sanar da Malamijo. Nan yace su tattara duka yaran su tafi ainihin gidan iyayensa wanda yanzu sai 'yan uwa baya son kowa ya dawo saboda zasu yi taro na manya. Babu wanda ya kawo tangarda sai Halifa shima kuma hankalinsa ne a tashe saboda Salame da ba'a gani ba tun jiya Alh Indararo yana ta babatu. Ummi ta kira shi gefe ta kwantar masa da hankali sannan tace yaje gidan Ta Madina ya daukota. Gani tayi yana son yi mata tambaya ta dafa shi. "Kada ka damu Malamijo ya gano inda ta kwana tun jiya kuma yana son shi da Ta Madina suyi mata magana ne." Sai lokacin hankalinsa ya kwanta ya tafi. Bai dade ba ya kawo Ta Madina shima ya tafi inda su Radhiya suke. Yau dai bayanta yayi tsami a dan rankwafe take tafiya ita kuma Rahima sai dankwali tasa ta daure idonta saboda ko yaya ta motsa tana jin kamar kwayar idon fitowa zata yi. Ragowar shatin wayar kuwa yana nan kwance a fuskarta ba kyaun gani sai hijabi ta janyo ta rufe fuskarta sosai. Da Halifa ya shiga dakin da suke ya ganta kuka ta saka masa Radhiya sai ta fice kawai ta basu wuri. Itama kukan take yi tana tausaya musu. Babu dan da zai zo jin ana zagin iyayensa bare kuma a kai ga kowa yana jin haushinsu saboda wani abu da suke yi ba daidai ba. ********** Tunda tazo gidan Mal. Kallamu abokin Malamijo Salame banda aikin kuka babu abinda take yi. Ta rasa me yake yi mata dadi kowa ganin laifinta yake yi. Duk abinda tayi ba karya aka yi mata ba amma babu mai fahimtarta. Duk wata rayuwa da take so da buri Mairama ta haye kai ita take yi. Rahima kuma ba komai ke dawainiya da ita akan yarinyar ba sai neman inda za ta sauke damuwarta. Ta rasa farinciki komai ba ya yi mata dadi gashi iyaye da 'yan uwa sun juya mata baya. Fuskar Mairama ta tuna lokacin da ta ke yi mata alkawarin bazasu sake haduwa ba taji wani iri a ranta. Wai shin mene ne takamaiman abinda ya rabata da Mairama idan ka cire auren Zayyan wanda ita Mairaman bata da masaniyar tana son shi. Kan nata ya toshe ta kasa tunanin kirki kawai sai ji tayi ana bubbuga kofofin gidan da karfi maza suna hayaniya ana kiran sunanta. "Come out" taji wani ya doka kofa da karfi yana fada. Ciwon ciki ne haka siddan taji ya kamata da tsananin bukatar zagawa bayan gida saboda tsabar firgici da tsoro. Kofa kofa sojojin suke budewa suna hargaginsu idan sun so tsorata mutane. Mal. Kallamu da matarsa duk da Malamijo ya kira ya fada musu yanzu sojoji zasu zo fitar da Salame amma bai hana shi shiga tashin hankali ba. Murdaddun maza ne majiya karfi babu tsoro babu rissina suke ta kiran Salame cikin wata irin murya. Dakin ta kalla babu wurin buya gashi muryoyinsu da bugun kofar yana ta matsowa kurkusa. Jiki na kyarma ta tashi ta mikar da katifar dakin ta jinginata da bango sannan ta shige bayan ta buya a zuci tana cewa "sai nayi magana ace bani da hankali amma ta ina talauci yayi saboda Allah tashin hankali yazo wa mutum gida babu wurin buya. 'Yar kwabar nan ko gado da za'a iya shiga karkashi a labe duk babu" Gidaje biyu ne tsakanin Malamijo da aminin nasa kuma har can gidan ana jin abinda sojojin suke yi shiyasa mutane kowa ya shige gida baka jin wani motsin kirki tamkar babu mutane. Dattijuwar matar Mal. Kallamu da tsoro ya isheta bata ci nanin ba nanin za ta ci ta tayi saurin nuna musu kofar dakin da Salame ta kwana. Gyada kai babban cikinsu yayi su ka yi shiru gabadayansu na dan lokaci har sai da ta soma sauke ajiyar zuciya a zatonta sun tafi. "Allah Ya soni....amma bari na fito sai na nunawa Mairama har yanzu gaba nake da ita. Nice zasu turowa sojoji saboda........." Haske ta gani wal daidai da faduwar katifar a kasa. Saura kiris ta saki fitsari ganin sojoji da kafta kaftan takalma kai kace filin daga zasu je suna nuna mata hanyar kofa wani ya daka mata tsawa. "Get going my friend" Jiki na tsuma numfashinta sai ka rantse fita zaiyi saboda tsananin kidima ta fito ko takalmi babu sai mayafi tayi gaba suna biye da ita. Motocin da ta gani ne suka sa ta hadiyar wani yawu mai mugun daci sannan aka nuna mata kofar gidansu ta shiga a darare. Zayyan yana mota ya hango shigarta ya kada kai. Mace da kimarta da komai ta zabi wulakanta kanta kamar wata mara daraja. Babu abinda yake tunzura zuciyarsa kamar makantar masa da mata na shekara goma. Fitowa yayi daga motar sanye da kayansa na sojoji yayi matukar kyau sai dai fuskar nan babu alamun wasa ko kankani kai baka ce Zayyan bane. A hade take tamkar hadari mai shirin zubar da ruwa. Cikin wani irin taku da dogayen kafafunsa yake tafiya da sassarfa yaransa suna kamewa suna sara masa. Sai da ya sauke ajiyar zuciya da ya shiga soron gidan yana fatan bukata ta biya domin idan Salame ta sake gangancin taba masa iyali bayan zamansu na yau to ko Mairama bazata sami labarinta ba sai yasa an gama koya mata hankali. Wasu mutanen basa gane yaren laluma da bi a hankali. Magana tafi shigarsu da tasiri idan su ka ji an taba lafiyar jikinsu. Katuwar tsakar gidan gabadaya iyayensu ne. Malamijo, Yadikko da Hajjo sauran amaren nasa yace kowacce ta zauna a daki. Gefe ga Innawuro da Nene Marka sai Ta Madina. Mairama da Mama Zainab suna daki. Can daya barin kuma Alh Indararo ne da Baffan Rahima. Kusan tafiyar yaji Zayyan yayi da Salame tana labe a bayan kofa ta kasa karasa shiga tsakar gidan. Takun da taji daga bayanta da hadadden kamshi mai tafiya da hankalin duk wanda ya shaka su ne suka sa ta farga ta juya baya. Ai tana hada idanu dashi kallon da yayi mata sai ji tayi fitsarin da take makalewa yana diga. Zayyan kuma ya dauke kai kamar bai ganta ba ya taho fuuu shine ta shiga kamar wadda aka koro. Babu wanda cikinsa bai yamutsa ba da Zayyan ya shigo duk da cewar da yawansu sun sanshi amma babu wanda yayi masa wannan sanin ta fuskar sojoji. Escort dinsa na bayansa sauran suna waje ya nufi gaban Malamijo. Mal Ali Gidado sai ji yayi hantar cikinsa na kadawa kamar ba surikinsa bane. Yanzu yaron nan idan allurar sojansa ta tashi ya manta da matsayinsa a gareshi yace zai hada dashi a kulle ai ya shiga uku. Wani tunani ne ya darsu a zuciyarsa ya kara tsorata wato tunanin ko Mairama ta fada masa yadda baya ciyar da ita da yaranta sosai lokacin da ta dawo gidan. Dan sakin fuska yayi ya gaishe shi sannan yace ina Innar Salame. Ta Madina jiki na rawa taja jiki ta fara yin hanyar kofa za ta gudu Hajjo tace "ga ta can a bayanka...Ta Madina ana magana" Idanunta su ka soma kadawa ta dafe kirji "banda abinki Hajjo idan da kara ai Yadikko zaki nuna matsayin Innarta. Ni dai haihuwar Salame kawai nayi amma komai nata da tarbiyarta a hannun Yadikko suke. Yau ko wani abu tayi ba daidai ba tarbiyar Yadikko ce da Malamijo" Yadikko ta zaro idanu ganin kowa ita yake kallo "daga abin arziki kuma sai kice nice na haifeta. Irin wannan tunda ya nemi ainihin mahaifiyar nasan cewa akwai dalili." Shi dai Malamijo gumi ne ya cika masa tafin hannu ya kalli Salame ta firirice gabadayanta a ta manne da bango. Zayyan ya sake daure fuska yana kallonta sannan yace "Malamijo ina son ganinka da mahaifiyarta muyi magana" Kan kace kwabo su Hajjo da sauran kowa ya bace sun shige dakunansu. Alh Indararo ma da Baffan Rahima cewa suka yi zasu jira a soro su ka tafi. Ta Madina ba don taso ba aka bude musu wani dan daki suka shiga ita da Malamijo. Zayyan zai bi bayansu ya kalli Salame ya daka mata wata razananniyar tsawa da ta kadawa hatta Mairama da ke daki ciki "zaki zo ki shige ko sai...." Bai rufe baki ba ta shige dakin itama ta sami jikin bango ta kuma rabewa sannan Zayyan ya shigo ya zauna. "Salame" taji ya ambaci sunanta da wata irin kakkaurar murya. Jinin jikinta ya sake tsinkewa bakinta kamar ansa kwado ta kasa budewa ta amsa. Ta Madina kuwa ta kai mata duka "ke dallah bude baki ki amsa kina ji ana kiranki" "Barta dai so take ta nunawa sojoji iyakarsu" cewar Malamijo a hasale. Kai ta dago a hankali su ka hada ido da Zayyan sai ji tayi har abada bata fatan sake kallon wadannan idanuwan masu tsorata mutane su kada masa zuciya da hanta. Sunkuyar da kanta tayi tana kallon kasa. Gyara zamansa yayi ya dan rankwafo kansa "naji labarin duka abubuwan da kika yi tun daga tafiyata zuwa jiya da yamma." Gumi take yi sosai tsoro iyaka tana ji kuma tayi imanin idan sun nemi tafiya da ita babu mai hanasu. Yadda ake bada labarin rashin imanin sojoji itama yanzu haka zasu je su rinka azabtar da ita? Muryar Zayyan ce ta katse mata tunani. "A jiya da aka fada min abubuwan da kika yi babu abinda yazo raina sama da son kulleki a dena jin duriyarki har abada...." kallonta yayi na abinda baifi sakan goma ba ya kula hankalinta yana gareshi kamar yadda yake so "...sai dai kinci darajar haihuwa Salame. 'Ya'yanki daidai har bakwai idan na rufeki ko kadan banyi musu adalci ba musamman kananan. Yanzu ina so a gaban mahaifanki ki fada min me Mairama tayi miki wanda ya janyo faruwar wadannan abubuwa" Shiru tayi kamar ruwa ya cinyeta ya daga murya "ba dake nake ba?" Zabura tayi ta sake yin baya "uhmm, uhmmm" "Kin zama bebeya ne ko me?" Ya sake yi mata tsawa. "Uhmmm babu komai" tace da kyar iyayenta suna kallonta cike da haushi. "To ni bari na fada miki me ya hadaku. Shekaru ashirin da hudu da suka wuce nazo gidan nan tadi wurin kanwarki kika kawo min wasikar tayin soyayya, anyi haka ko ba'ayi ba?" "Anyi" tace da sauri. "A lokacin na amsa miki ko nayi wani abu da zai nuna miki cewa ni Zayyan ina da fuska biyu ta ha'inci in nemi kanwa in nemi yayarta?" Girgiza kai ta soma yi a hankali tana tuna yadda ya yayyaga wasikar ya watsar. "Salame nasan cewa soyayya babu ruwanta da dacewa ko akasin haka. Amma ance wai ana barin halal ko don kunya. Kanwarki wadda bata da zance sai naki kuma kema a yadda na fahimta wancan lokacin kina sonta ita ce kike son manemin aurenta. A tunani na ke mai iya hakuri ce ki bar mata ko da ina sonki balle tun farko ita na nema. A matsayinki na musulma tun lokacin ya kamata ki karbi kaddara ki rungumi kyautar da Allah Yayi miki ta Salisu. Ko kinsan cewa Zainab matar Hadir nine na fara nemanta? Ni na nemi kwatancen gidansu duk da ba wata muguwar soyayya naji ta kamani a lokacin haduwarmu ba amma kinsan indai saurayi ya nemi gidansu budurwa ko yaya ya ga abinda yake so ne. Amma abin mamaki ranar da Hadir yaje gidansu da zummar fada mata ni bazan samu damar cika alkawarin zuwa ba su ka kamu da son juna. Tun daga wannan ranar har rana irin ta yau ban taba sake yiwa Zainab kallon da ya wuce kanwata matar dan uwana ba." Malamijo da Ta Madina sai jinjina kai suke yi yayin da Salame tayi shiru kawai tana sauraron maganganunsa. "Ko da kina sona to ba da zuciya daya bane hasali ma nafi danganta abinda kika yi da hassadar kanwarki. Kun rayu kece 'yar gata saboda kina samun kulawar mahaifiya ita kuma babu uwa babu dangin uwa. A kullum Mairama ce a kasanki ki bata saura tayi miki godiya. Lokaci daya kinga abinda kike so shi kuma ya karkata gareta shikenan kika juya waccan soyayya da kike yi mata zuwa kiyayyar da hassada ta zama musabbabinta. Kin manta cewa kowane bawa da irin rayuwar da Allah Ya tsara masa. Wallahi Salame tunda kika ga baki aureni ba ki sani cewa bazaki taba iya rayuwar da Mairama tayi ba. Duka duka ba don rabon haihuwa ba zaman har na wata nawa muka yi a karkashin inuwa guda? Mun rabu da kuruciya batare da mun mori komai a zamantakewarmu ba mun sake haduwa farin gashi na wahala da zuwan shekaru ya zo gareni. Matata da na bari da kuruciya na dawo ta koma babbar mace. Kinsan yadda muke ji kasancewar shekarun da ya kamata mu zauna mu fuskanci juna sun kare bama tare. Duka duka Salame shekara nawa kuma ya rage mana da zamu sake maimaitawa a doron kasa? Na tafi na bar yarinya ko tafiya bata yi na dawo watanni kadan ga aurenta. Cikin da bansan meye a ciki ba na dawo na sami katon saurayi yana shirin zama soja. Salame zaki iya wannan rayuwar da Mairama tayi cikin kunci, kewa da makanta ga marayu a gabanta???" Damm taji zuciyarta ta buga sai ga hawaye daga sama yana sintiri akan kumatunta. Ta Madina ma kuka take yi Malamijo ya sake jin kunyar abinda yayi a baya. Kuncin da ya baro a baya ne ya tuna shi ma Zayyan din yasa yatsansa ya kore hawayen da ya taru a gefen idanunsa. "Labari yazo Zayyan ya mutu amma kika cigaba da nunawa Mairama kiyayya wadda har ta kaiki ga makanta ta. Abinda nake so ki gane Salame shine ba Mairama kika tsana ba kuma kiyayyarki ba gareta bane. KIYAYYAR SALAME GA SALAME TAKE. Rayuwarki ce gabadaya bata yi miki ba saboda kin ginata tun farko da hassada da bakinciki shiyasa komai baya burgeki sai abinda wani ya samu. Wanin ma wadda kika dauka kishiyarki baki son ta fiki da komai. Da ace kin kasance mai godiya ga Allah da karbar kaddara ina me tabbatar miki sai kin kwance zani kin baiwa Mairama kwance. Dubi irin dimbin arzikin tsohon mijinki yanzu. Ni fa banda kaddara babu wanda yayi tsammanin dawowata harda ni kaina. Dama kece babba a gidan nan amma da kin karbi rayuwarki ta farko da duk gidannan sai sunci arzikinki. Kin sake aure kin dauki karan tsana kin dorawa Rahima saboda ba auren bane a gabanki lokacin. Burinki ace kin yiwa Mairama zarra kuna zawarci ke kin rigata samun mijin aure saboda kin fita da komai. Nasan akwai kaddara da rabon haihuwa a kanki amma duk da haka yadda kike tafiyar da rayuwarki shine ya munanaki a gaban 'yan uwanki." Mayar da hankalinsa yayi ga Malamijo da Ta Madina "ga iyayenki nan kowa cikinsu fushi yake da ke. Duk wanda kika raba kin zalince shi musamman 'ya'yanki kin bar musu abin fada wanda nake fata zancen ya mutu a gidan nan. Ki gyara rayuwarki wannan shawara nake baki idan kuma kinki ji to na tabbata jikinki yana kaikayi ne na son a taba lafiyarsa mu kuma zamu taba" Shiru dakin yayi na wanu dan lokaci kafin Malamijo yayi gyaran murya ya soma magana "Zayyanu nasan Salame tayi ba daidai ba amma ina tuhumar kaina da zama silar komai. 'Ya'yana ban basu damar girma da iyayensu mata ba bare su samu ingantacciyar tarbiya. Babu wanda nasan damuwarsa a cikinsu hankalina yana kan dabbobina da yawan aure aure. Gashi an wayi gari ana ta sako min 'ya'yan bayan dogon jinkirin da suke samu kafin manema su fito. Nima ban rike Mairama da 'ya'yanta rikon da ya dace uba ya yiwa 'yarsa da take cikin halin bakincikin mutuwar miji ba ta yaya 'yar uwarta da ta bari shaidan yayi galaba a kanta zata yi. Ka yafe min do Allah do Annabi" Kunya ce ta kama Zayyan yace masa dama daga shi har Mairama basu rike shi a rai ba. "Ke kuma mutuniyar banza tashi zakiyi ki roki kowa gafara musamman Mairama da Rahima da kika rinka zalinta" cewar Ta Madina. A sanyaye Salame ta fara cewa su iyayenta su yafe mata zuciyarta tana ta harbawa ta ma kasa gane wane hali take ciki. Bayan sun ce sun yafe ta koma ga Zayyan shi kuwa kofa ya nuna mata "kije ki sasanta da kanwarki sannan yanzu zan tura su Rahima su dawo ki daidaita tsakaninki dasu. Wannan magana bana so su sani kwatakwata burina kawai ki rungumi 'ya'yanki ki basu tarbiya mai kyau musamman wannan yarinyar da kika zo min gida da ita sai kin tashi tsaye." Yace yana tuna irin rashin kunyar da yaji Khadi tana yiwa Rahima watarana a Abuja. Mikewa yayi zai fita ya dan dawo sai da gabanta ya doka "yauwa zanyi magana da shi baban Rahima yanzu sai dai ina son yi a gabanki so ki biyoni don ina sauri ne" "To" tace da azama tana bin bayansa. Suna zuwa soron su ka same su zaune akan tudun nan kowanne cikinsu ya mike da sauri. Zayyan hannu ya mika musu suka yi musabaha sannan ya kalli Baffan Rahima saboda kamanni da suka nuna shine baban nata. "Ni sunana Zayyan" yace dashi. "Idris nake" Baffan Rahima yayi masa murmushi. "Ni kuma Alhaji Indararo aka fi sanina dashi" cewar maigirma miji na Salame. "Mal Idris alfarma nake nemarwa kaima da iyalina Mairama" "Haba Yallabai ni kuwa har wace irin alfarma kake tunanin zan iya yi maka?" Zayyan ya kalli Salame sannan ya kuma kallonsa "Rahima nake so ka bamu idan babu takura. Dan zaman da mukayi da ita ta shiga ran kowa a gidan musamman ita Umminsu. Don Allah ka bamu ita kafin nan da Allah Ya kawo mata mijin aure ta sami soyayya da gatan da ta rasa na mahaifiya" Baffan Rahima bai san lokacin da murmushi mai hade da dariya suka kwace masa ba "Yallabai Rahiman tawa ita ce kuke so?" "Ta cancanci soyayyarmu kuma nayi maka alkawarin zamu riketa kamar 'yar cikinmu" "To Yallabai za ku rinka kawota in ganta ko?" Yace a raunane harda 'yar kwallarsa. "Wannan kuma dole ne" Zayyan yace yana dariya. Mal.Idris ya kamo hannunsa "na baka Rahima amana Yallabai duk da nasan bata baki nake yi ba sai na fada ba. Nagode nagode sosai" Juyawa Zayyan yayi ya tambayi Salame "kina da abin fada game da hakan?" Kada kai tayi a sanyaye. Alh Indararo ya murmusa "sannu da kokari Yallabai nima ina da yaran wallahi biyar ta haifa min duka mata. Bari na garzaya gidan na turo maka su sai ka zaba" Dariya Zayyan ya danne a ransa kuwa yana tunanin ko ganinsa bazasuyi ba. Su ai 'ya'yan so ne basu da matsala. Ra hima kuwa ya fuskanci abinda Mairama keso kenan amma ta kasa fada masa saboda gudun kada yaki amincewa saboda halin Salame. "Kina iya tafiya ki turo min matata idan kin shiga" Zayyan yace da Salame. Ciki ta koma jiki a sanyaye yawancin kowa ya fito sun cigaba da harkokinsu murya na rawa tace wane daki Mairama take. Da hannu Nene Marka ta nuna mata. "Dama kiranta yake yi maigidan" "To ni zanje in fada mata?" Cewar Nene. "A'a" tace da sauri sannan ta shiga dakin yau harda sallama. Mama ce ta amsa mata a fili Mairama kuwa a zuci ta amsa ta kawar da kanta gefe. "Ana kira" "Wa ake kira?" Mama ta tambayeta. "Ita" Salame ta amsa tana nuna inda Mairama ta juya mata baya. Murmushi tayi duk da bata ganin fuskarta amma muryar Salamen tayi laushi a zuci tace kadan ma kika gani. Dama tayi kwalliyarta tayi kyau ta yafa mayafi a kafada ta fita ko kallon inda Addarta take bata yi ba. Tana zuwa soron kamshin da yanzu mijin nata yafi amfani dashi ya doki hancinta ya mika mata hannu sai da ta waiga baya ta kuma kalli kofa ta girgiza kai. "Za'a iya shigowa fa" "Fillo rowa zaki min?" Murmushi tayi ta taho gareshi ya rungumeta tsam yana jin wata nutsuwa tana ratsa shi. A kunnenta ya ce "Fillo ashe an sami karuwa? Allah Ya raya mana" Gabanta ne yace das tsabar tsoro ta dago da sauri "rufa min asiri ni wallahi bani da komai" Dungure mata kai yayi "matsoraciya kawai....barkar samun Rahima nake miki" "Rahima kuma Sojana?" "Mun gama magana da babanta yanzu ta zama 'yar Zayyan da Fillo" Mairama bata san lokacin da ta kankame shi tana murna ba. Godiya take ta zuba masa cikin nutsuwa ya soma mayar da godiyar wani abu daban sai da taji kamar motsin ana tahowa tayi saurin matsawa gefe yana yi mata dariya. "Ni yau zan koma amma Abuja zan tafi please ku dawo waahegarin bikin nan bana son zama babu ku a kusa. Sannan na kashe case dinnan ki bata dama ta gyara kuskurenta" Dan jimm tayi kafin ta kada kai "shikenan, amma shine ka tsorata mutan gidannan da dakarunka ko" "Bukatata zata biya nasan in sha Allahu zata gyara. Da farko tafiya naso yi da ita amma kinga amfanin shawara Major da Hadir suka kwabeni da hukunci cikin zafin rai. Tabbas na yarda Salame mai laifi ce sosai wadda bata cancanci a raga mata ba ko kadan. Amma ta bakin Major yace ku mata idan aka nemi a ci ku da wuta sai ku sake botsarewa baku ki ayi kan mai uwa da wabi ba. Muna iya hukuntata ta dawo yadda ta taba zuwa wurin boka yanzu ma ta sake iyaka dai a sake kamata wadda bazata damu ba indai bukatarta zata biya. Ina ganin mu bata wannan damar idan ta sake baudewa kuma to zan hadata da masu ladabtar da ita in and out" Kwalla fal idon Mairama tace "nagode Sojana Allah Ya saka da alkhairi. Amma zaka jira yaran su dawo ko...idan ka tafi wannan yarinyar damuna zata yi ta hanani sukuni. Mutum ya girma sai sabuwar sangarta ke shigarta" Murmushi Zayyan yayi "dole na jira. Ya batun abincin mutanen nan?" Mairama tace masa an kusa saukewa. Waya ya dauko ya kira Emzee da suke tare da Awwab da yace su jira ko a gonar Malamijo ne sai ya kirasu. Mairama ce ta karba ta fada masa inda su Radhiya suke tace su daukosu su dawo gidan. Zamanta tayi suna ta hira da Zayyan a ciki kuma Salame ta shige tsohon dakinsu da Mairama zuciyarta sai zafi take ta rasa inda za ta saka ranta taji dadi. Duka fadin gidannan kowa baya sonta tayi bakinjinin da ita da kanta ta rakitowa kanta. *********** Mota bata karasawa kofar gidan saboda haka daga can nesa kadan Emzee yace Awwab yayi parking ya karasa a kafa. Ya shiga suna gaisa da mutane Radhiya da Rahima a tare suka ji muryarsa. Radhiya ce ta fara fitowa daga dakin da suke da sauri Emzee yayi kamo hannunta a dan birkice saboda fuskarta da ya gani tayi ja. "Adda ina da ina ne yake miki ciwo? Kun koma asibitin? Sun baki magani?" Murmushi tayi "kai Emzee irin wannan tambayoyi" "Da kyar na wayi gari inata tunanin ko yaya kika kwana. Zo mu tafi tare muke da Hamma" yace yana kallon Rahima dake tsaye a bayanta ta janyo hijabinta ya rufe mata fuska. Mamaki ya kama Radhiya duk da tasan cewa dama zai damu saboda rashin wayarsu jiya. Yau kuma tun safe take gwada tasa wayar a kashe ashe yana sane. Murmushi tayi dimple dinta ya shige ciki sosai ta kamo hannun Rahima tana ce masa itama fa akwai ciwon a jikinta. Tabe baki yayi "Allah Sarki" Wata irin fargaba taji a take ta dago kai ta kalle shi sai ta ga yayi gaba abinsa yana yiwa mutan gidan sallama kamar bai san da zamanta a wurin ba. Idanunta suka cicciko da kwala tana mamakin wannan abu. Yaki daukar wayarta tun jiya yau kuma ya ganta ya share. To ko dai yana fushi ne saboda Ummansu ta daki yayarsa ta tambayi kanta. Babu mai jinta bare ya bata amsa haka ta fito a sabule ta bi bayansu. Tun kafin ta karaso wurin motar Awwab ya fito ya dora hannu a jikin kofar bangaren da yake yana kallon yadda Radhiya take tafiya tana dan cije lebenta na kasa. Gashi wurin da mutane dole ya daure ta karaso. Gaba Emzee ya tafi zai shiga Awwab ya hade fuska cikin wasa yace "haba inlaw koma baya ka barni naji ya kwanan iyali" Murmushi Emzee yayi Radhiya na dariya idanunsu suna cikin na juna Rahima tayi murmushi ta shiga baya. Ga tsananin mamakinta wata muguwar harara Emzee ya doka mata yana ganin kawai da gangan tazo masa shiyasa taki fada masa wace babarta. "Hamma bari kawai zamu taho a kasa ga Halifa can na hango ya fito" "Wasa nake fa shigo mu tafi kada mu bar Daada da jiranmu" Ai baya jin yana kaunar zama inuwa daya da Rahima. Ayatul kursiyyu ya shiga karantawa yana son idan ma wani abu aka yi masa Allah Ya bashi lafiya. Ko da yaji, wannan soyayya da yake mata daga haduwarsu a ranar ko baccin kirki bai iya yi ba sai aikin tunaninta. "Ina biye daku dama babu nisa fa" yace kawai ya taka ya riski Halifa. Awwab ya ja motar tare da kamo hannun Radhiya ya rike gam. Ba magana suke yi ba sai dai kallon da suke yiwa juna kawai mai cike da shauki. Rahima bata kula da abinda yake faruwa a gaban ba saboda tashin hankalin da take ciki. Me ya sami Emzee kamar bai san ta ba. Suna zuwa gidan ta sauka daga motar ta shige ciki. Awwab ya dago hannu ya shafa fuskar Radhiya ta lumshe idanu. Jinginar da ita ya yi kokarin yi yana cewa "bayanki bazai sage ba kin zauna kinyi gaba Schatzi" Da sauri ta dago jin zai hada bayanta da kujerar tare da yin kara cikin wani irin sautin wahala "aashhh Chèri da zafi" Gabadaya Awwab ya rude "mu gani" yace yana shirin kwanto da ita jikinsa ta matsa da sauri tana rufe idanu. "Silly girl" ya ja hancinta "ashe ciwon ba na gaske bane tunda bai hanaki jin kunya ba" Kyabe fuska tayi kamar me shirin kuka "Hammana ina kayan dubiya?" "Bayan kin fada min kika yi sai a wurin Mami naji." "To kuma sai ka taho hannu na dukan cinya" Kai ya girgiza yana dariya "wata maganar idan kika yi sai ta tuna min wata yarinya da na hadu da ita shekara uku da suka wuce a falon Mama mai kwalkwalin kai" Shan kunu tayi tana kumbure kumbure "sai na fadawa Daada kana tsokanata" Dariya yake mata ta cukule fuska "baki san yadda hoton kan yarinyar ya zauna min bane a kaina" "Kaga bana so" "Idan baki so a bani janbaki na shanye ki gani idan zan sake tsokanarki" ya kare da lumshe idanu yana budesu a kanta. Kunya duk ta kamata shi kuwa kamar ya cusata a zuciyarsa kawai yake ji saboda yadda komai nata yake burge shi. Hira suke yi a nutse yana ta tsokanarta daga baya ya kare da bata shawarar a matsayinta na babba kada ta bari ko kadan su Rahima su ga wani chanji daga garesu. A irin wannan lokacin ne mutum yake kwasar lada domin ya rama sharri da alkhairi. Sosai take jindadin shawarar tasa kafin daga baya su gangara kan shirin dinner din da za ta daki Abuja nan da kwanaki. Halifa da Emzee basu dade ba suka isa gidan inda suka shiga dakin da iyayen nasu da kakanni suke. Emzee yana kallon Umminsa ya hango Rahima a jikinta Ummin kamar tayi kuka tana kallon fuskarta. "Ni dai ko asibiti zan kaita ne a Kano wannan idon yayi kwanciyar jini" tace tana juya fuskar Rahiman yadda su Innawuro zasu gani. Kirjin Emzee yayi wata irin dokawa saboda yadda fuskar Rahimansa ta koma...Rahimansu dai ya gyarawa kansa da sauri tare da saurin barin wurin. Yana tafe fuskar tana masa yawo a ka cike da tashin hankali. Ba zato yaji ance "Karami" Juyawa yayi yana kallon Salame tayi wani iri. Fuskar Rahima ya tuna yaji ransa ya baci amma albarkacin Ummi sai ya gaisheta. Kasa boye mamakinta tayi saboda tasan bata kyauta musu ba amma yaran suna da ladabi duk da fitinarsu da ake gani musamman Radhiya. "Uhmmm dama...nace...dama...uhmm" "In tafi ne?" "Cewa nayi ko za ka kira min su Radhiya da Halifa" "Radhiya ko Rahima?" "Radhiyan dai" kunyar ganin Rahima take ji sosai kuwa. Wayarta ya kira sannan ya tafi kiran Halifa wanda tun a hanya yake bashi hakuri yace kada ya damu magana ta gama wucewa. Radhiya da Halifa sunje sun sameta sai ta rasa abin fada sai da Halifa yace zai tafi ta iya hada kalmar hakuri ta baiwa Radhiya. Murmushi kawai tayi tace babu komai saboda yadda bata sakewa a gabanta. Bayan tafiyarta ne ta dan sassauta murya tace da Halifa "Me kanwarka take cewa game dani?" "Me zata ce kuwa Umma banda kuka" Shiru tayi na rashin sanin abin yi kafin daga baya tace "wai fuskarta ta kumbura?" Shi gabadaya ya kosa da tsayuwar ma "bari na kirawo miki ita ki gani" "Dawo Halifa" tace tana yafito shi da hannu bai tsaya ba sai da yaje kofar dakin da suke. "Rahima kizo inji Umma" Duk wanda yake wurin ya ga firgicin da ya bayyana a fuskarta ta kankame Mairama sosai har ta soma kwalla. "Tashi kije Rahima" Nene ta umarceta. Tamkar wadda kwai ya fashewa haka ta mike tana kallon Ummi ko zata ce mata ta zauna sai ta ga tayi mata alamar taje. A tsorace take sosai ta fito ta bi bayan Halifa. Tana zuwa daga nesa ta zube a kasa ta gaisheta. Salame ta amsa yau babu wannan hura hancin. "Dama jiranki nake yi mu tafi" A kidime tace "ina?" Murmushi Salame tayi wai nan ita gyara za ta yi "muje gidana kiyi min kunshi saboda Kamun gobe. Amma ki fara dauko kayan da zaki saka goben sai mu shiryo daga can" Abinka da rashin sabo Rahima sai jin abin tayi bambarakwai ta kasa cewa komai sai faduwar gaba. Halifa take kallo tana neman agaji. "Umma ita za ta yiwa Radhiya kunshi fa ko?" "Eh da su Anti Laila" ta ce cikin sauri. Salame ta fuskanci akwai tsoronta a tattare da Rahima to amma so take ta gyara ya kamata su bata dama. "Nima ina nan din zan jira ki sai ku fara da wuri saboda yau nice da girki." Ta murmusa hakoran nan masu gansa kuka suka bayyana "yau sai ki tayani muyi girkin tare" Qut...Rahima ta hadiyi yawu Halifa ya kalleta ya danne dariya saboda yasan karshen takura da tashin hankali tana cikinsa. Salame ta bar wurin batare da Rahiman ta amsa ba can kasan zuciyarta tana jin wani iri game da yadda idon yarinyar ya koma. Yarfe hannuwa Rahima ta shiga yi tana kallon Halifa "yaya zanyi?" Tausayinta yaji a ransa yana murnar shi namiji ne don gaskiya bai hango yadda zai iya kwana da ita ba da shine Rahima. Babu wata sakewa ko shakuwar uwa da 'ya kawai sai ku kwanta kusa da juna. Kiranta taji Radhiya tayi bayan tafiyar su Emzee suna wurin Ummi tace a kira wata mai lallen Rahima babu wanda zata yiwa saboda idonta. Radhiya dama a yatsu kawai zata yi saboda dai kada ace amarya ba kunshi. Gidan ya soma kaurewa da hayaniya Ummi ta fadawa Rahima ta tafi gidansu ta hado duk wani abu mai mahimmanci musamman takardun makaranta da ita zasu koma gabadaya. "Ummi gabadaya kika ce?" Ta kasa boye farincikinta. Tana son Mairama tsakani da Allah saboda a dangin mahaifiya babu inda ta ga soyayya da kulawa kamar a wurinta. Bayan la'asar kuwa ta sulale ta fice a soro ta hadu da Salame "yauwa dama ke nake jira muje" ta nuna mata kofa. A tsorace tace mata kaya zata debo a gida. Salame ko a jikinta tace idan ta dauko ta taho gidanta gobe sai suyi sammakon fitowa. Yau Rahima an shiga tsaka mai wuya. Yanzu idan ta rufeta da duka tana cikin bacci fa. "Naji ance jibi zaku wuce ne kinga zai kyautu mu kwana muna hira tunda zamu jima bamu hadu ba" Jiki a sanyaye tace to tayi hanyar gidansu. Baffanta da Iya basu ji dadin ganin yadda idonta yayi ba ta hada 'yan kayanta masu kyau ta fada masa inda zata kwana. Nan yayi tsalle ya dire yace ba dashi ba babu inda zata je. Iya ce tace ya kyaleta tunda babu mai rabata da mahaifiyata. Ba don taso ba haka taje gidan. Kanenta na binta da ido shekeke Salame ta daka musu tsawa tace bazasu gaishe da yayarsu ba. Rahima da yaran a tare suka firgice Salame ina ma ta kula sai fada take wai basu da tarbiyya basu san girman na gaba dasu ba. Murhu ta hada ta dawo ta kirata wai ta tayata tankade. Tare suka yi girkin tana ta dararewa saboda kada jikinta ya gaya mata. 💕 [11/2, 8:04 AM 60💕 : Tare suka yi girkin amma Rahima ce karfin aikin. Yaran gidan sai binta suke da kallo ita dai kanta na kasa har suka kammala. Baffanta ne ya kira Ummi ya sanar da ita inda zata kwana kada suji shiru. Addu'a ta rinka yi Allah Yasa kada wani abu mara dadi ya biyo baya. Lura Salame tayi da yadda Rahima take tsakurar abincinta. Tuwon masara ne da miyar karkashi sai tashin daddawa take yi ga sukunbiya an saka saboda ita. A cikin kwanon silva ta zubawa Rahima ta kwarara miyar a kai. Sai da ta gama lashe hannunta ta bi irin abin miyar nan da ya kan makale a tsakanin hakora da harshe tana sakato shi sai ji kake tana tsk-tskk da baki ta kora da ruwan rijiya sannan ta tabe baki. "Abincin namu bai kai na 'Yan Abuja dadi bane naga kina ta yafita kamar bakya so?" Kafin ta kai karshen maganarta Rahima ta zunduma wata katuwar loma wadda ta kasa hadiyewa saboda bata kaunar karkashi ko kadan. Da gudu taje bakin rariya ta zubar ta dawo tana jiran Salame ta soma fada sai taji tayi mata magana babu wannan fadan. "Ba kya cin tuwo ne?" "Miyar...miyar ce dama...dama karkashi ne....bana sha" "Yo maimakon ki fada nayi miki hadin mai da yaji sai ki cuci kanki? In kin fada min ai ba dukanki zanyi ba" tace da ita amma idan kaji yadda muryarta ke fita sai ka dan tsorata. Takaicin yadda yarinyar ke zabura duk motsinta ne yake damunta. Kwanon ta dauka ta mikawa sauran yaranta da gudu suka far masa dama sun cinye nasu ita kuma taje kitchen ta dibar mata wani cikin sauran da zasuyi dumame dashi da safe. Mai kwantirola ta yaryada mata da gishiri ta dauko yaji da rabin maggi a dakinta ta saka sannan ta bata. Ko kadan wannan hadi bai yiwa Rahima dadi ba saboda man danye ne sai karni ke tashi amma kyautatawar da mahaifiyarta ta gwada mata karon farko tun wayonta yasata yin kwalla ta janyo farantin ta cinye shi duka. Basu wani jima da gamawa ba Alh Indararo ya dawo gida Salame ta kai masa nasa abincin. Kayan jikinta tun na jiya ne babu zancen wanka a ajandarta duk kuwa da cewa da murhu tayi girki ga kauri ga datti. Tunda ta shiga banda harara da habaici babu abinda yake mata ya gama cin abincin yace ta fita kada ta sake zuwa turakarsa da sunan kwana sai idan da kansa ya nemeta. Abu na biyu kuma ya bata lokaci kankani ta san yadda zata yi su daidaita da Mairama a basu ko da mutum biyu ne cikin yaran shi ma a rage masa nauyi. Kallon raini ta bishi dashi "wannan shi ake kira karfin hali barawo da sallama." Hannu ya kawo da sauri zai sauke mata ta fita ba shiri yana ta fada kuma wai kashin tsiya gareta kada ya kuma ganin kafarta a dakin. Dama waye ya aiketa bayan jiya ya mata dukan nan jiki yayi tsami. Dakinta ta koma aka yiwa yara shimfida Khadi tana gado tace da Rahima. "Kwaba lallen kizo ki yayyaba min dashi zan kwana saboda ya kamu sosai" "Kada ya cabe ko ba mai ado kike so ba?" "Ado kai 'yan nan. Kada ki damu zan iya kwana dashi." Duk yadda idonta yake damunta bata nuna ba ta kwaba lallen nan ta zauna. Wayarta ta soka a gaban dankwalinta bayan ta kunna torchlight saboda rashin wuta sannan ta kamo kafar. Dandakuwa sunan wani abu. Ga datti da wani maiko maiko ga yalwataccen kaushi yabi ko ina a cikin kafar babu inda babu. Kamar ta ce mata ko zata wanke kafar amma babu fuska sai uwar hamma da Salamen take yi. Ba yadda ta iya haka tasa kasan zaninta ta goge kafar sosai sannan ta baje basira ta soma zane. Goma ta wuce ta gama Salame tace mata ta kwanta a daya gefen ya zamana Khadi na tsakiyarsu. Da kyar ta iya bacci saboda rashin sakewa da sabo. Asubar fari kuwa ta mike ciwon ido yayi sallama ya kara nauyi tana ruwa. Alwala ta dauro ta zo ta tashi Salame ta kwashe mata lallen ta goge hannuwan da kafafu sannan itama tayi alwalar. Tun a lokacin tana iya ganin yadda lallen nata ya fito radau yayi kyau musamman hannuwanta. A sannu sannu gurbin da ta danne Rahima a zuciyarta ya fara neman nuna kansa ga duniya. Sai take jin wani takaici da haushin kanta na kin sakarwa yarinyarta tun farko. Sunyi sallah Rahima ta gaisheta ta amsa tare da cewa ta bude idon da ta rufe mana. Ai kuwa tana ganin yadda ya kuma hadewa gabanta ya fadi. Hakuri ne tun jiya ta kasa bawa Rahima sai yanzu take sake ganin rashin hankalinta. Ruwan kunu taje ta dora da ya tafasa ta debi wani a bokiti tazo ta gasa mata wurin. Babu wani sauki da taji amma abubuwan kyautatawar da Ummanta ke yi mata kadai sun isheta farinciki. Kafin ta dawo daga dama kunun Rahima ta soma janyo kayayyakin da suke soke a lungu da sakon dakin babu wadatar isa ga zarni da wari duk ya hada. Gari guda ta hada wanki sannan ta soma shara Salame ta shigo. Tunda take dan cikinta bai taba yi mata shara ba. Na gabanta banda cin tsiya da fitsara basu san komai ba. Halifa namiji ne, macen da zata yi kuma ta dauki karan tsana ta dora mata. Bata ce mata komai ba Rahima ta aikatu sai wuraren shabiyu ta gama gyara dakin. Wankin kuwa Salame tace zata yi da kanta. "Lokaci na kurewa shirya ki tafi gidan Malamijo zan taho anjima ki bar min wankin" Wanka taje yi bandakin babu kanta sai kawai ta shafa ruwa a fuska da kafa ta fito sauran ta wanke musu bandakin. Da sauri ta shirya suka yi sallama ta fito. Sai yanzu ta saki ajiyar zuciya ta sami nutsuwa saboda duk a tsorace take. Da zuwanta gidan tayi sa'ar samun bandakin da babu kowa ta nemi ruwan zafi tayi wanka. Ido suntum ta shiga daki wurin Ummi hankalinta ya sake tashi. Abinci ta sa ta ci suka tafi asibiti a cikin garin. Sai bayan azahar suka dawo anyi mata allurai tasha magani ta kwanta bacci. Biki yayi biki gida ya cika da dangi abin farinciki harda wasu cikin mutanen Sakkwato banda na rugar Barkindo zuga guda. Anci an sha babu kwandalar Mairama ko ta mijinta. Malamijo ne yayi kusan komai sai kuma kannen Mairama su ma wasu katan din lemo, akwai wadda tayi zobo da ginger aka kulla a leda, cincin da meatpie kowa dai ya nuna da gaske sun gaji da zaman doya da manja zumuncin suke muradi ayi. Amarya Radhiya sanye take da leshi mai dan karen kyau ja da adon duwatsu anyi mata dinkin buba ta daura zamin a kai. Kafarta babu lalle sai yatsu kawai haka ma hannu amma tasha ado ba kadan ba. Sarkar beads aka yi mata shirin ya kayatar matuka tana tsakiyar fili ita da Mama da 'yan uwa ana kidan kwarya. Rawa take tana juyi karaf idanunta suka gano mata shigowar Gwaggonta Salame tana tafiya tana dafa bango saboda takalminta. To da yake Allah baiyi ta mutum mai riko ba indai anyi abu ya wuce to fa ya wuce kenan a wurinta sai dai dan abinda ba'a rasa ba. Shiyasa take kaifi daya babu munafurci ayi komai a wuce wurin. Tana takun rawar a girgiza 'yan mata da masu kidan suke yi taje ta riko kafadun Salame ta kawota tsakiyar fili. Ba laifi tayi kyau atampa ce a jikinta ta sako wani takalmi da bai tsufa ba tun na lefe saboda bata sakawa sosai yayi mata tudu. Yau kuwa dole a dama da ita kowa yasan cewa bata karewa Salame ba. Bata gama gyara tsayuwa ba Radhiya ta rinka juyi da ita ana girgiza jiki ana rawa. Salame tayi wuri wuri ta jigata 'yan uwa aka basu fili ba abin ta gudu ba ace bata son zumunci tafi kowa laifi. Wata kanwarsu ce ta leka dakin da Mairama take zaune da Rahima mai bacci tace mata ta leko tasha kallo. Daga bakin kofa ta hango rawar da suke tika harda su Hajjo amma Salame jikinta yafi na kiwa girgiza saboda Radhiya ta matsanta mata. Me Mairama zata yi kuwa banda dariyar yadda suke yi. Daidai lokacin Salame ta dago kai suka hada ido Mairama ta daure fuska kamar ba ita ke dariya ba ta shige dakin. Kwafa Salame tayi cike da takaici a zuci take ta babatu "jimin rashin mutumci fa, tana kallo 'yarta za ta ballani maimakon ta tsawatar shine ta koma daki, yanzu kayi magana a hadaka da sojoji saboda rashin gata" Wani kanin Mairama ne mai hoton yazo aka fara sannan fa Salame ta samu damar sabulewa. Malamijo ma yazo ansha hutuna yana rike da 'yan biyunsa. Kyautar saniya da sa ya yiwa Radhiya babbar jika yace amma a barsu a gonarsa ya cigaba da kiwata mata. Abu yayi kyau zukata sun haskaka da farinciki. Bayan isha ne Salame ta gama shirin tafiya ta shiga neman Rahima. Haka kawai take son su tafi tare jiya taji dadi har ranta ko da bata iya nunawa ba. Tana daki wurin Mairama tana faman lallabata taci abinci. Gobe da sassafe zasu tafi saboda a kaita asibiti. Yanayin idon ya soma bata tsoro. Daga jikin kofa Salame ta coge taki yiwa Mama da Ummi magana sai Rahiman ce tace mata "Umma inzo mu tafi ne?" Keyar Mairama kawai take gani amma jikinta ya bata gara ta hakura kafin wani abu ya biyo baya. Duk da haka ta ga yana da kyau ta tunawa kanwarta wace tayi ciki da goyon Rahima. "A'a yi zamanki Rahimata, gobe zan shigo da wuri kafin ku wuce mu karasa hirarmu ta dazu. Kayanki kuma zan bayar a kawo miki yanzun nan" Dariya ce ta ciwo Ummi wai Rahimata...to dama waye yace ba tata bace? Ita kadai ta nesanta kanta da yarinyar kuma zata fi kowa farinciki idan taja ta a jiki ta sami soyayyar uwa kamar kowa. Sake maimaita kalmar tayi sai dariya tana ta kokarin dannewa amma yadda Salamen tayi magana dole mutum ya dara. Mama na ganin haka ta tace Rahima ta kawo ruwa kwarewa tayi. Tana fita ta kalli Salame da ke tsaye har yanzu "dan bubbuga mata bayan mana Adda Salame kina tsaye tana tari" Idanu ta zaro kamar zasu fado tace "wa? Ni....shegiya inji dan daudu. Rufa min asiri ina tabata yanzu zaki ji dirin motocin sojoji ana kiran Salame" Kan kace kwabo ta fice abinta ko da Rahima ta dawo bata nan. Washegari sammako suka yi saboda yadda Ummi ta matsu suje asibiti kullum idon kara kumburi yake yi. Ta yiwa Malamijo zancen masu zuwa biki yace kada ta damu zai turo wasu Abujan wasu kuma su bisu Sakkwato har zuwa kai amarya Katsina sannan wasu daban suje Nijar. Hakan yayi mata kuwa sosai. A ranar Mami itama da nata gayyar suka wuce Abuja. Abinda ya bata mamaki bai wuce biyosu da Fauziyya da Bilal suka yi ba. A take ta nunawa Fauziyya bata son yawo ta bari har sai ana gobe Bilal yace shine yake son su tafi saboda akwai abinda zasu yi da Raji da angwayen. Bata matsa son jin ko meye ba suka kama hanya. ********** A Abuja azahar ta riskesu saboda sammakon da suka yi. Dan kwana biyun da babu Mairama Daada yaji jiki saboda har yau gani yake ko daya bisa dari na fanshe rashin matarsa baiyi ba. Yana falonsa na kasa suka iso Radhiya ta makalkale shi yana dariya. Ita kuma ta lura hakan na masa dadi sai yaji kamar bai rasa komai ba na rayuwar 'ya'yansa shiyasa take yi. Rahima na gefe tana murmushi ta gaisheshi ya sakar mata fuska fiye da yadda yake yi kwanakin baya da ta zo. "Auta bakya laifi wannan daurin har ido na meye?" Ummi ce tayi masa bayani Radhiya ta kwance ya ga idon ransa kuwa ya baci kamar ya ga Salame a gabansa ya saita mata fuska. Da kansa ya kira Emzee da ya bar gidan tun safe kuma saboda zuwan Rahiman ne yace yazo bayan la'asar ya kaisu asibiti. Bai ma san waye za'a kai ba amma dolensa ya amsa umarnin mahaifinsa. Karfe hudu da rabi ya iso Ummi ta sauko sanye da riga da zani da hijab ta tura mai aiki kiran Rahima. Tamke fuska yayi bayan sun gaisa tunda yaji sunanta. Doguwar rigar atampa ce a jikinta ta dora rigar sanyi mai zip ta gaba mai dan fadi tare da hijabi fashion wanda ya zarta kafadunta da kadan. Idonta kuwa hankici tasa ta dafe shi bata son haske na ratsa shi. "Ina wuni" tace da ta iso kusa da shi da Ummi. Waya ya shiga dannawa baji ba gani yana a'uziyya a zuci wai kada a sake makalo shi da wani nau'in siddabarun a cikin muryarta da take masa dadi har yau. "Baka ji ana gaisheka ne?" Ummi tace tana nufar kofa za ta fita. Sai da ya harari Rahima mamaki ya sake kamata sannan yace "na amsa Ummi baki ji bane" "Wai haka Rahima?" "Ummi ya amsa" tace tana murmushi. Emzee na ganin Ummi tayi waje ya dawo kusa da Rahima kamar gaske ya kuma daure fuska "babu kunya kike yi mata karya, ni nace ki rufa min asiri ne?" Jikinta ne ya soma rawa saura kadan ta fashe da kuka tace kasa yayi hakuri kawai ta wuce. Da ta karasa bakin motar ma baya ya bude duka bangare biyun yana cewa wai su shiga baya tare zasu fi jindadi. Ummi bata ce komai ba tayi zamanta yaji dadin hakan saboda don bai san karyar da zaiyi mata ba idan ta tambayeshi. Asibitin Samu Wadata su ka je inda suna zaune Ummi ta saka shi ya bada numbar katinsu aka dauko sannan suka yi zaman jiran a kira su. Basu jima ba kuwa aka kira Rahima da Ummi suka shiga wurin likitan. Bayan ya duba idon sosai yace musu wasu jijiyoyi ne suka toshe sakamakon jinin da ya daskare a ciki shi ya kawo kumburin idon. Magani ya rubuta mata na sha da digawa domin sace kumburin sannan zasu dawo bayan kwana biyar a auna lafiyar idon. ********** Kwana biyun bayan dawowarsu an cigaba da gyara Radhiya sosai. Mama ce da aikin hadata da kayayakinsu na Sakkwatawa da kuma na wata kawarta Maman Farida. Sai kuma takunkuminta na hana Awwab ganin amarya. Tun ranar da su ka dawo daga Sumaila ta fada masa da kanta. Manufarta bai wuce samun lokaci da kyau a gyare mata 'ya ba. Sannan kuma tasan cewa idan ba haka tayi musu ba haka zaiyi ta zuwa kullum yana bata show tunda yasan matarsa ce. Idan kuwa sai da komai ya kammala ne dole ya fi ganin tasirin aikin. Ba wani damuwa yayi sosai ba saboda shima bashi da isasshen lokaci. Tun safe suke kulle gidan Mami idan ta fita shi da Bilal, Yousuf, Raji, Emzee da Ibrahim sai wani mutum guda daya da yake zuwa sai dare ya tafi. Mama tayi juyin duniya Mami ta fada mata me suke yi taki su ma kuma kowa ya rufe bakinsa. Yau da yake neman alfarmar son ganin Radhiya lallabowa yayi yana mata magiya. Wasa yake yiwa DK da yake hannunsa yana mata magana. "Ko awa biyu bana jin zamuyi don muma abinda yake gabanmu akwai cin lokaci" "Na yarda amma da sharadin sai ka fada min me kuke yi kai da 'yan uwanka" Dariya yayi don kowa yasan tana binsu daidai suna zillewa ne. "Big surprise ne Mamanmu ni dai a taimaka kada zuciyar......" Da sauri tace "Ahhhh dena kiran zuciya yanzu zan kira na sanar da ita." "Allah Ya ja da ran Mama. Nagode" yace tare da ajiye DK a cikin wani abun kwanciyar yara yana murmushi. Bayan fitarsa ta kira Ummi ta fada mata gobe zai zo daukar Radhiya zasu je yin hotuna wanda za'ayi amfani dasu a wurin dinner din. A wurin Ummi Radhiya taji zancen ta kama yi masa mitar bai fada da wuri ba yanzu wane kaya zata saka yace ita kadai yake bukata goben komai is ready. "Hammana da ya ka shirya komai ban sani ba?" Tace cikin jindadi. Murmushi yayi mai sauti "ke dai ki shirya around 12 zan zo. Love you...sai munyi waya anjima ana jirana" Saroro tayi da wayar a hannu tana tunanin me yake dauke masa hankali ne yanzu bashi da lokacin hirar kirki. Da dare kuma ba wani jimawa suke ba yake kwanciya. Washegari kafin ya iso ta gama shiri tun daren jiya sunyi magana da Arifah itama Yousuf ya fada mata zasu je kuma kada ta tanadi kayan sakawa. Zahra ce ta yi mata light make up mai kyau fuskarta kamar ka dauke ka dasa ga wani irin kamshi mai rikita kwakwalwa da sanyaya ruhi. A kitchen ta yiwa Ummi sallama saboda yace bazai shigo ba sai sun dawo gudun bata lokaci. Awwab kasa dauke ido yayi daga kanta tun fitowarta har ta iso gaban motar inda yake tsaye rike da kofa ya bude mata. Murmushi tayi tana sunkuyar da kai haka kawai wani irin nauyinsa take ji. Tana shirin zama ya duko daidai kunnenta "you look sweet" Fadada murmushin tayi ta rufe fuska da tafukan hannayenta. Sai da ya zauna ta soma gaishe shi idanunsa a kanta kamar zai cinyeta. "Hammana ina wuni?" Tace da karamar murya tana jin faduwar gaba. "Lafiya kalau my baby." Yanzu ma murmushi kawai tayi kamar ba ita ba wani salihanci ne yayi mata dabaibayi yayin da kwanakin barin iyayenta da zama cikakkiyar matar Awwab suke gabatowa. Tayar da motar yayi ya kama hannunta ya rike yana magana a hankali amma idanunsa na kan titi. Cikin muryarsa mai tafiya da zukata wadda har yau idan Radhiya taji sai ta sanyata cikin wani irin yanayi na tsanananin son mai muryar yace "kinsan wani abu?" Kai ta girgiza ya cigaba da magana "yau inspecting dinki zanyi" Mantawa tayi da shiru shirun ta kwace hannunta da sauri tare da zare idanu, baki na rawa tace "me...me ne?" Kin kallonta yayi har yanzu saboda ya san sai ta saka shi dariyar da baiyi niyya ba "Inspection nace ko ban isa ba?" Da rawar murya tace "ka isa amma ni ban taba jin anyi bane" "To ke me kika sani game da aure dama. Kafin amarya ta tare ango yake yi domin tabbatar da cewa tana da tsafta." Katse shi tayi da sauri "Hammana wallahi ina wanka kullum kuma ba ma sau daya ba" "Dan kin fada da baki shikenan ni kuma sai na yarda?" Gabanta ke matsanancin faduwa ta kwantar da murya tace "Kasan dai bazan yi maka karya ba...ka tambaya kaji" Murmushi ya juya yayi mata sannan ya gyara muryarsa domin ta saki jiki yana dariyar yadda ta tsorata "na yarda dake Schatzi, kuma nima gaskiya da aka fada sai da naji kunya nace bazan iya ba...." Wani irin numfashi yaji ta sauke saboda samun relief ta gyara zama harda kwantar da kanta akan seat. Murnar da ta fara bata yi dogon zango ba taji yace "..to amma kwanakin nan duk kin chanja I really miss my Alheran." Wani abu taji har zuciyarta yana bin dukkan jikinta soyayyarsa tana karuwa a cikin ranta. Idanu ta lumshe lokacin da ya dan kalleta yana yin kwanar gidansu Arifah domin a nan zasu dauki hotunan. Akan Radhiya ya gaskata soyayya ya kuma san dadin kasancewa da masoyi. Rabuwarsu ta shekaru ukun nan kuwa shine lokaci mafi radadi a zuciyarsa. Dawo dashi tayi daga duniyar da yake neman tafiya ya barta ta hanyar cewa "Chèri nice fa har yanzu" Sun shiga gidan har yayi parking amma bai bude musu su fita ba ya zuba mata idanunsa "Gaskiya a'a shiyasa dole zanyi inspecting dinki na tabbarar ke din ce da gaske" Baki ta shiga turawa kamar karamar yarinyar ya kasa hakuri sai da ya saka yatsansa yana shafar dimple dinta a sanyaye yake cewa "tawa Alheran din bata ganina ta kasa magana...I miss wannan 'yar kauyen me yawan kuka da dariya akan Hammanta, Schatzi dina da muke ci daga plate daya da spoon daya, muke shan abu mu ragewa juna. I miss 'Yar soja saboda ni ita ce wadda na kamu da sonta lokacin da na fara hada ido da ita. Idan zaki dawo min da ita yanzu I promise you babu wani inspection da zanyi....atleast for now" ya kare da kashe mata ido. Kalamansa sun tsaya mata a rai taji kamar su dawwama a cikin wannan yanayin. Kallon da yake mata mai kashe jiki ne ta gaji dashi saboda yadda ta rasa sukuni gabadaya ta hura masa iskar bakinta daf da idonsa ya kifta idon tayi baya da sauri tana masa dariya. "Gaskiya ta kare maka sosai Hammana" "Na sani Alheran, daga ranar da na ganki da wannan kwal....." Saurin fita tayi daga motar don tasan me zai ce. Ita kuwa babu lokacin da ko tuna shi idan tayi sai taji matsananciyar kunya kamar farkon haduwarsu a falon Mama. Fuskarta da alamun bacci ga kai a aske. Bayanta ya biyo yana cewa ta saurare shi ita kuwa ta ki suna dariya wata mai aiki ta kaisu falon da Yousuf da Arifah suke baje kolin soyayya suna jiransu. Arifah rungume Radhiya tayi suna murna sannan ta ja hannunta zuwa dakinta inda wata mai kwalliya take jiransu. Jaka ce guda biyu iri daya sai dai kala da ta bambanta Arifah ta mika mata farar ita kuma ta dauki cream. "Ga kayan da zamu saka kuma an nanata min yadda suke a jere har kasa haka zamu rinka dauka" tace tana murmushin yadda suka yi da Yousuf kafin zuwan su Awwab. "Ina mamakin yaushe suka sayi kayan da dinki" cewar Radhiya. "Nima tambayar da nayi kenan. Amma wurin telan nan da muka kaiwa dinkin biki suka kai. Yanzu dai tashi mu shirya" "Muje na fara gashe da Mom tukunna" "Tun safe ta fita maybe ta dawo kafin mu gama" Kayan saman suka fara daukowa tare da fadawa mai kwalliyar kada tayi musu heavy make up. Atampa ce ja da zanen fulawa manya navy blue anyi musu riga da skirt fitted a cikin kayan akwai dan karamin kwalin fashion sarka da dankunne ja sai mayafansu kashka mai stones navy blue. Kowacce cikinsu ta kasa boye farincikinta suna murna kai kace yara ne. Duka kayan da mahadinsu na mayafi da sarka. Babu bata lokaci aka tsara musu kwalliya kowacce tayi kyau. Daurinsu ma iri daya ne mai hawa hawa su ka dora mayafan a kafadunsu. Ga mamakinsu Awwab da Yousuf suna sanye da blue jeans da red shirt mai dogon hannu. Radhiya dai hawaye take neman yi saboda yadda Awwab yayi surprising dinta yayi matukar burgeta da shiga rai. Mai hoto yace idan sun shirya shima fa ya shirya. Hotuna suka yi sosai kowanne couple sunyi su kadai sannan anyi musu tare. Kayansu na biyu shadda ce ta matan orange ta mazan kuma combination din orange da fari sun sha hula. Nan ma kamar wancan kowa yayi da matarsa sannan sunyi tare. Sai kaya na uku matan lace doguwar riga anyi aiki a gaban na mazan ma irinsa ne dinkin yarbawa harda hularsu. Wannan gudunmawar Raji ce mijin Zahra kayan sun amshi kowa aka yi hotuna ana zolayar juna. Kayan karshe abaya ce hadaddiyya kowa ya nemi kalar da matarsa tafi so amma design iri daya. Na Radhiya light green na Arifah light purple (lilac). Ango Awwab yasa yadi irin mai shara sharan nan light green amma babu hula shi kuma Yousuf lilac. Idan ka kansu kamar kada ka dauke ido. Sunyi matukar kyau aka karasa musu hotunan Yousuf ya nanatawa mai hoton zasu zo da daddare su nuna masa hotunan da su ka zaba da kuma jerin yadda suke son ayi musu slide show din. Ko a nan kawai amaren sun san mazansu sun karramasu sun nuna musu soyayya. A daki Arifah take fadawa Radhiya abinda Dad dinta yake yawan fada mata tun bayan da aka daura auren. "Akwai ranar da zaki ji wai me ya sameki ne kika rasa mijin aure sai wane saboda kawai ya bata miki rai. Shima watarana zaiji kamar ya rufeki da duka don takaicin wani abu da kika yi ba daidai ba. A irin wannan lokacin babu abinda ke rike igiyar aure kamar idan kuka tuna memorable moments din da kuka gina lokacin ganiyar soyayya. Saboda haka kowa ya sami dama yayi kokarin nunawa dayan cewa they are special" Radhiya ta jinjina kai tace "Sis to mu me zamuyi musu?" "Ki bari a gama biki yanzu dai sunyi mana one-zero." Wayar Awwab ta katsesu Radhiya tayi hanzarin mayar da kayan da tazo dasu ta dauki jakar kayanta ta sauka. Abinci aka gabatar musu wanda Arifah tasa aka shirya amma kunya ta hanasu ci. Plate Awwab ya samu ya zuba musu shi da Radhiya ya rike hannunta su ka koma wurin wasu kujera daga can gefe guda. Yousuf yace masa ya kyauta dama bashi da niyar barin Arifah ta tashi bata ci komai ba. Yadda suka saba kama-kama da spoon daya Awwab da Radhiya suka yi a haka aka ci abincin sannan suka tafi tare da Yousuf ya sauketa a gida. *********** Ana saura kwana biyu fara events din Jos wanda kowa zaije banda Radhiya ance itama amarya ce. Tayi magiyar har Awwab ta roka yace tayi hakuri ba yinsa bane amma idan ta shirya ya kama musu masauki shi da ita sai su tafi tare. Da jin haka tasan hakuri ya zame mata dole ta gama rigimarta da shagwaba ta sallama. Sai gashi Zayyana da Rahima suka ce mata zasu zauna da ita su ma sun fasa zuwa. Ummi kuwa tace basu isa ba ya zama dole a karrama iyalin Excellency. To karshe dai Fauziyya ce ta fake da laulayi ta zauna tunda kwana biyu ne zasu yi kuma dai ba son tafiyar take ba. An gama wannan shawarar washegari ya kama ranar da za'a mayar da Rahima asibiti. Ido ya sace kamar bashi ba amma kuma yana ta ruwa. Ummi ta shirya zasu tafi da Emzee da Ibrahim shiru bata sauko ba Emzee ya hau sama kiranta. A falon saman ya ganta zaune akan kujera ta dafe kai tare da runtse idanu. "Ummi..." yace a tsorace ganin tana ta runtse ido "baki da lafiya ne?" Hannunta ta dago masa tana son ya taimaka mata ta tashi "tun dazu nake jiran wani ya hawo, taimaka ka mayar dani daki jiri ke dibata sosai" Da taimakonsa ta karasa dakin da kyar kanta yana ta juyawa kuma ta kafe bazata bisu asibitin ba wai stress ne kawai da rashin zama. "Kaje ka kai min yarinyata a duba mata idon nan idan kun dawo sai ku karbo sakon nan da na fada maka wanda zamu tafi dashi Jos gobe" Ba haka yaso ba don har Daada ya kira a waya ya fada masa. Sanin halinta na kin asibiti yace su tafi da Rahiman ya kusa tasowa zai kaita da kansa. Yana saukowa ya nemi Ibrahim ya rasa. Can ya hango shi da Zayyana suna hira an nutse a cikin soyayya. Tsaki yaja tuni ya dawo daga rakiyar 'yan mata. Zayyana ya tura ta kira Rahima su tafi Ibrahim ya kyabe baki "Ni dai gaskiya babu inda zata je ka kira wayarta mana ko kaje ka kirata da kanka. Dawo ki zauna kinji" Emzee ya rike haba "ashe da gaske akwai ranar da zan ga kana tale baki? Kanwata kiyi a hankali kada ya fiki iyawa a kasa gane wace Zayyana waye Ibrahim" "Banda abinka ga Zayyanan ai" Ibrahim ya nuna kansa sannan ya nuna Zayyana yace "ga Ibrahim". Murmushi tayi tana jin kunya ta je kiran Rahima. Dama a shirye take gudun bacin rai daga Emzee yasa tayi zamanta sai Ummi ta sauko. Lokacin da ya fadawa Radhiya Ummin bata jindadi tana daki bata sani ba. Zayyana tace bazata bisu ba saboda anyi printing takardunta na admission da ta samu a Nile University akwai wuraren da zata cike Mami zata turo dreba a karba. Ibrahim kememe yaki bin Emzee da yaji haka. "Kuje ku dawo Zee-zee ina jiranka a nan" ya nuna inda yake zaune. Haushi ya kama shi kuwa saboda ganin yanzu su biyu ne kadai zasu shiga motar. Gaba tayi nufin shiga tunda su kadai ne yace "koma baya". Bayan ta zaga ta zauna abinta batare da tayi masa magana ba. Yana zama ya kula kamar mudubinsa a saitin fuskarta yake don duk motsinta yana gani maimakon ya hango titi. "Koma gefe" ya umarceta. Gefen ta koma ta rakube zuciyarta tana zafi. Ba komai yake damunta ba sai rashin sanin aihinin abinda tayi masa wanda ya bata masa rai har yake mata haka. A gaban mutane bama ya shiga shirginta sai ya zama dole. Idan su kadai ne kuma dalili ya janyo sai yayi mata magana to ba mai dadi yake yi ba. Ba karamin azabtuwa yake da yin hakan ba domin kuwa har yanzu ya kasa rabata da matsayin da ya bata na Rahiman Muhammad. Ga tausayinta da yake dawainiya dashi saboda ciwon idonta. Ko tari taki yi a motar ya kunna karatun Qur'ani kira'ar Mishary Rashid Al-Afasy cikin suratul Kahf. Da kadan da kadan yake jin tashin muryarta tana bin karatun a hankali sai ya sami kansa da rage volume batare da tayi la'akari ba. Idanunta a rufe sai dai lokaci lokaci tana sanya tissue ta goge ruwan da yake fitowa kamar hawaye daga dayan idon nata. Bakinta yake bi da kallo ta mudubi can cikin zuciyarsa yace "Rahima". Wani mugun horn yaji yayi saurin kallon gabansa tare da taka burki da karfi kadan ya rage ya dokawa motar gabansa. Rahima ta bude ido da sauri ya juyo suka hada ido sai harara yake maka mata. "Wato ta nan kika bullo kuma? Bari mu koma gida addu'a zan ce Ummi ta rinka yi min saboda na fuskanci abin naki da gaske ne." Bata fahimci me yake nufi ba shi kuwa bai fasa cewa zai tsananta addu'a ba wai tunda an biyo ta can asirinsu ya tono shine ake neman sake tafiyar da tunaninsa gashi daga kallonta ta mirror ya kusa yin accident. Idan ka ga yadda yake fadan abin dariya kuma ya kasa hakura da kallonta ta mirror din. Sun kusa isa asibitin yayi parking a gefen hanya saboda abin ya ishe shi yace ta dawo gaba. Ita dai bata da ta cewa sai fatan idan ma wata lalurar ya gamu da ita da ta janyo masa chanja halaye Allah Ya yaye masa. Yanzu ta dena jin haushinsa sam sai tausayi. A asibitin tare suka shiga wurin likitan. Tambayoyi yayi mata game da yadda take jin idon ya haska ya gama bincikensa sannan yace ta rufe idon mai lafiyar ta karanto masa ABCD da aka hargitsa daga can karshen wani office inda ake gwajin ido. Zuciyar Emzee ta tsinke kuka ne kawai baiyi ba jin Rahima guda biyar kadai ta iya fada daidai sauran kuwa sai dai ta kalli Q tace O ko ta kira K da E. Abin gwanin ban tausayi sai da mutum yayi mata haka sau uku ya tabbatar abinda yake zargi ne ya sami idon. Ita kuwa ganin yana maimatawa har cewa tayi dashi tana gani fa. Sai dai sakamakon toshewar da jijiyoyi suka yi da jini aikinsu yayi matukar rauni duk da cewa an magance toshewar kumburin ya warke gabadaya. Ko idon zai yi lafiya da wahala ta sake gani sosai dashi. Yatsunsa ya shiga nuna mata yana cewa ta fadi ko nawa ne. Nan Rahima ta rikice inda bata tantance biyu da uku. Hawaye sosai ta soma yi da likitan ya soma bayani. Duk yadda Emzee yake kokarin nesanta kansa da ita ba karamin tausayinta bane hake bin ko ina a jikinsa. Wasu magungunan ya rubuta mata sannan ya auna karfin idon yace zaiyi mata glass ne su dawo nan da kwana uku. "Babu yadda za'ayi mu samu gobe da safe saboda tafiya zamuyi a goben" cewar Emzee. "Zaku iya samu amma sai ka kara kudi. Kayi magana da cashier din idan ka fita" Nan suka gama komai ya biya kudi cikin wanda Ummi ta bashi. Maimakon su tafi gida wani babban shago ya wuce da ita ya sa salesgirl din tayata neman frame mai kyau. Wani round ta zaba ya dace da fuskarta babu dai me yiwa kowa magana ya biya kudin suka koma asibiti. A mota ya barta yace ya kai musu sannan suka tafi gida. Zayyan na komawa gida ya sami Mairamansa a kwance Radhiya ta bata tea taki sha wai bacci kawai take son yi ta rabu da ita. "Jeki abinki Alheran ajiye min tea din" yace da ita. Tana fita ya cire rigar khakinsa ya rage singlet da godon wando ya kwanta a kusa da ita tare da janyota jikinsa. "Fillo me yake damunki ne kwanakin nan na lura kamar baki da lafiya." "Stress ne Sojana kuma kaima kasan dole ne tunda kun dauko mana abinda yafi karfinmu." Dariya yayi yana shafa kwantaccen gashin kanta da yake nadewa da kansa saboda laushi. Dinner ce angwaye suka tsara abarsu Baban Arifah yazo ya chanja komai. Abokansa 'yan siyasa da manyan mutane wasu ba zuwa Jos zasuyi ba shine suke ganin kawai gara ayi wata a Abujan. Sai kuma bangaren sojoji da suke yiwa Zayyan kallon wani celebrity suma kowa yana son zuwa bikin 'yarsa. Excellency yace bai ga amfanin ayi taro gutsi-gutsi ba alhalin mutane daya ne zasu zo. Kuma dama bikin ya rabu kashi kashi ayi ta tara gajiya da barnar kudi. Hakan da yayi ya kara masa kima a idanun su Baba Hadir da Daddy domin ya nuna yasan zafin nema ba kamar yadda yake a wurin 'yan siyasarmu ba ayi sati ana biki ana barin kudi. Shiyasa su Mama kullum suna tafe ana ta shiri domin suyi taron da zai kayatar ya fitar da mazajensu kunya. A cikin kunneta Zayyan yace "ni kuwa sai nake ganin kamar na tureki ne Fillo" Da saurinta ta tashi zaune "rufa min asiri da abin kunya Sojana. Muna bikin 'ya ka tureni da wane ido zan kalli mutane." "Kin fiye tsoro kamar ba matar soja ba. Ina ruwanki da mutane. Iyaka ki goya namu ta goya nasu ba shikenan ba" "Ni dai ka dena wannan fatan" tace tana sake narke masa. "Yanzu ma na fara, kinsan irin farincikin da zanyi kuwa idan gaske ne? Hmmm Fillo kiyi fatan Allah Ya amsa domin ki ganewa idanunki babban matsayin da zaki kara takawa a zuciyata" "Kana nufin akwai inda ba ni bace dama?" "Ko daya, sai dai zan kara mata fadi ne domin a haka kinyi mata yawa" yace yana kara rungumeta tare da addu'ar cikar burinsa. A nata bangaren itama hasashen cikin take yi amma kunyar kasancewarsa take. Ina zata boye kanta ace tayi ciki bayan ta aurar da 'ya. Ga tarin fargabar yadda Zainab ta haihu. Sai dare ta iya saukowa Emzee yayi musu bayanin abinda likita yace. Mairama taji babu dadi sosai. Wata kiyayya ta banza da Salame ta dorawa kanta ta janyo ta makanta 'yarta da bata yi mata laifin komai ba. Kuka sosai Rahima take yi Zayyan yace kowa ya fita ya barsu da ita. Daga shi sai ita da Ummi ya rinka yi mata nasiha akan hakuri da karbar kaddara. A nutse yake janta karshe ya nemi jin me take son karantawa idan ta gama makaranta tace Nursing take so. Murmushi yayi yana yabawa zabinta sai dai wani hanzari ba gudu ba shine makarantar da aka sama mata sun ce sai sunyi mata gwaji kafin ta shiga SS3. Idan bata sami result irin wanda suke bukata ba sai ta maimaita ajin. "Daada repeting fa kenan a wayance" tace a sanyaye da guntun hawayenta. Ummi tayi dariya "kin ganni fa tare muke tafiya da yayyenki Ibrahim da Karami. Yanzu nan da sati biyu zan koma makaranta ina level 4 suna level 4" Murmushi tayi kafin tace "Nasan ma sai sunyi min ko don English da Maths" Kwantar mata da hankali Daada ya cigaba da yi yace ko me ya faru kada ta damu. Ummi kuma tace za'a daukar mata lesson teacher a gida. Bayan ta koma wurin Radhiya wayar Malamijo Ummi ta kira ta fada masa. Fada yayi kamar ya ari baki karshe yace "Mairama kinga hakkinki ko" Hawaye ta soma yi "Malamijo ka dena fadin haka kaddararmu ce daga ni har Rahiman" "Ai ko ban fada ba hakan ne. Salame ko kadan bata da hankali. A da bata damu da Rahima ba yanzu kuma hakkin yarinyar nan bibiyarta yake duk inda ta zauna bata da zance sai Rahima kamar wata sabon kamu. Tayi ta nunawa mutane kafarta wai ita tayi mata lalle..." Dariya ce ta nemi kwacewa Mairama tace "Kayi hakuri ba da niyar bata maka rai na fada ba" Albarka ya rinka saka mata yace ba da ita yake fushin ba yana dai jira ya gani ko wannan dalilin zai sa Salame ta dawo hayyacinta sosai. A yadda ya tsara Na'e da wasu ne cikin yaran zasu zo Abujan. Yadikko taje Sakkwato ita kuma Hajjo taje Nijar. Maman 'yan biyu dai banda ita a wannan yawon yaranta kananu ne ga zaman mota. ********** Bikin kwana biyu suka halarta a Jos tare da su Tante Nasara da wasu daga Nijar da suka taho tare. Kudi dai yayi kuka to amma ba abin mamaki bane duba da cewa biki ne na 'ya daya tilo ga gwamnar jihar tasu. Gabadaya aka dunguma suka koma Abuja wasu a mota wasu a jirgi. A hanya Ummi ta rinka amai kamar zata fitar da kayan cikinta don sosai ta galabaita. Mama tana sannu tana murmushi wanda ya janyo Ummi kai kararta wurin Mami. Hakuri Mami ta bata tana gargadin Mama da ido saboda birkici musu da Ummin tayi. Zuwa yanzu ta gama tabbatarwa ciki ne duk da bata je asibiti ba hankalinta duk ya tashi ina za ta kai abin kunya a cewarta. Da su ka isa gidan Daada su duka ukun suka sauka a nan ana lallaba patient. 'Ya'yan nasu basu san me yake damunta ba sai hawa suke ana mata sannu. Sai da ya rage su hudu a dakin da Tante Nasara sannan Mama ta kasa hakuri ta soma tambayarta. Doki ne ya isheta tana dariya "Ummin Awwab anya baki harbu ba?" Ummi ta gama aika mata sakon harara kamar ido zai fado "kin manta bindigeni akayi" Su duka ukun suka sa dariya ta sake hade rai lokacin da Tante tace "abar zancen wasa matar Yaya kamar fa ciki ne dake" "Wannan ya wuce kama Nasara barka da zuwan Daada ne yake sakata amai. Sai dai muce Allah Ya inganta" cewar Mami. "Wallahi...wallahi...." ta soma cewa sai kuma kuka sosai tana yi harda sheshsheka tace "ina zan kai wannan abin kunya don Allah. Ciki kamar wata yarinya?" Mama ta galla mata harara "Allah Ya bamu hakuri" tana dauko DK da yake kwance akan gadon "kai taho kaji dan soyayya in yayeka in samo maka kani ko kanwa." Fuska jajur Ummi take nunata da hannu ga hawaye yaki tsayawa "Ya isheki Zainab wannan ba abin wasa bane." "Ni bansan ma me zan ce miki ba. Ki wayi gari bayan shekaru da dama da cikin Zayyan a jikinki abinda nasan ko a mafarki baki hangowa shine kike kuka? Mairama kyauta irin wannan ai sai sadaka da kyautata ibada. Uhmm Mami ga kanwarki nan bari na nemi Emzee ya kaini gida kada ta bata min rai" ta mike za ta fita Tante ta rikota tana cewa. "Allah Ya shiryeku kuna abu kamar yara" Mami ta sauke taguminta da tayi tana kallonsu suna aikin hararar juna "ni tunda nake ma na taba ganin matan da suka gagara girma kamar wadannan." Mama tace "baki jinta ne da wani shirme wai kunya...wannan ba shine babbar shaidar Zayyan ya dawo da soyayyar Mairama ba" Duk yadda jikin Ummi yake a mace bai hanata jifan Mama da pillow ba itama tana dariyar "Allah Ya shiryeki Zainab" "Amin Ya shiryemu mu duka." Ta koma tana kallon Mami "saura ke fa ya kamata mu ga shaidar cewa har yau kina qalbin Major" "Allah Ya tsareni da wannan abin kunya" tayi saurin cewa. Ummi tace "ooooohhh da shine kuke yi min fata saboda rashin tausayi. Ni na manta yadda ake raino" "Kin dai san yadda ake samun baby....." Tante ta hangame baki "Haka kike Zainab?" "Ta wuce nan Nasara ki kalleta kawai ki dauke kai" cewar Mami. Tsokanar juna suka cigaba da yi ana cewa Ummi ta tabbatar taje asibiti duk da dai ko yanzu sun fara kirgin watanni. Babu ruwansu 'ya'ya suna shagalinsu suma suna nasu. Washegari duk wasu masu zuwa daga wani garin sun gama isowa. Radhiya dasu Zahra da wuri suka tafi salon inda Arifah da wata cousin dinta suke jiransu. Gyaran hannu da kafa aka fara yi musu ga fatar jikinsu tana ta sheki anyi gyara har an gaji. Bayan sun gama aka zo wankin kai. Radhiya na bude gashinta Arifah ta rike baki ganin yadda kasansa yayi wani irin ja mai duhu. "Dye kika saka?" "Lalle ne" ta bata amsa kafin ta hau bayanin yadda ta kwana hudu tana kwana da lallen da take shafawa a a gashin kullum. Kimantawa tayi kamar daya bisa ukun gashin amma daga kasa take saka masa lallen shine yayi wannan kalar. Daga sama zuwa kafadunta baki yayin da kasan ya bada wata kala mai kyau. Ita da bata saka relaxer steaming da stretching aka yi mata ranar wuni guda a nan suka kwasheta. Yau Laraba ranar da ake jira tayi. Karfe takwas mai lalle tazo dama jiya an yiwa kowa amarya kadai ta rage. Zama na musamman suka yi aka gama ja sannan aka dora baki. Karfe biyar Mama tayo waya don itama gidanta da baki haka na Mami. Su Hussaina, Nura da Hany wadda ta soma jin sauki sun taho. Gidan Mami tayi masauki sauran suna gidan Mummy Gambo. A jikin katin an riga an rubuta tsarin events ciki harda zuwan baki daga bakwai da rabi tunda ana Magrib shida da rabi ne zuwa takwas da kwata lokacin da za'a rufe hall a fara event. Mutanenmu da son biki babu mai son a rufe shi a waje shiyasa duk mai zuwa shiri yake da gasken gaske. Wanka Radhiya ta silla tare da dauro alwalar magrib. Bayan ta shafa mai tayi sallah ta zura kaya don har ita Mama kira take akan idan suka bata lokaci zata saba musu ne. Riga da skirt ne na wani irin material pink da ya amsa sunansa. Rigar daidai da jikinta amma wuyan ya rufe mata baya sai daga gaba aka bude. Hannun dogo daga kasa an bude shi sosai. Shirt din ma sai daga kasan gwiwa aka saka net domin kara masa fadi. Kafin a fara kwalliya Emzee ya kwankwasa kofar dakin yana kiranta. Tana lekowa ya saki murmushi "my one and only Sis kinyi kyau" Itama murmushin tayi "kai Emzee ba ayi kwalliyar ba fa." "Duk da haka bani da ta biyunki" yace daidai fitowar Rahima ta kada kanta kawai don yanzu ta saba da halinsa. Dakin Daada ya nufa da Addarsa inda suka sami iyayensu suna jiransu. Baki yaran su ka saki suna kallon Ummi da Daada sunyi kyau kamar ranar tasu ce. Ummi lace ne baki a jikinta wanda ya amsa sunansa anyi masa wani irin adon cin baki da sky blue din zare da stones. Anyi mata kwalliya ta fito sosai tana haskawa abinka da mai yaron ciki. Mayafinta, takalmi da jaka duka sky blue ne, ga dankareriyar sarka da abin hannu. Daada kuma shaddarsa ce sky blue din aikin jikinta simple yet elegant. Yana sanye da hula zannabukar wadda ta dace da kayan. Ummi rike take da links tana kokarin balle masa a hannun rigar ta kasa. Shigowar Emzee shine ta bashi ya makala masa. Daada yace a rufewa Radhiya ido kyauta zai bata. Emzee ne mai wannan aikin sai da Daada ya bude wata hadaddiyar sarka shigen ta Ummi sannan aka bude mata idon. Tsabar murna kuka ta saka masa ta fada jikinsa. Emzee sai ya koma gefe yana daukarsu hoto gashinta ya kwanta a bayanta. Saka mata dankunnen da sarka iyayenta suka yi tana ta musu addu'a da godiya.Kusan minti goma suna kashe selfie a tsakaninsu sannan Radhiya ta tafi aka fara zuba mata kwalliya tayi kyau karshe. Wasu kayan Fauziyya ta daukar mata a wata karamar jaka da kayan gyara kwalliya saboda idan anyi rabin taron an riga an kama musu daki da zasu chanja kaya a cikin Sheraton Hotel inda za'ayi event din. Kowa ya gama shiri ana ta shiga mota masu tafiya da katinsu a hannu tunda card admit ne. Takwas da minti kadan Awwab ya shigo gidan ya bude wurin da wani irin kamshi mai ruda tunani da sanya shauki. Three piece tweed suit ce a jikinsa burgundy color da dark pink necktie da irin hankicin nan da ake leko dashi ta saman aljihun coat din. Yayi aski da gyaran fuska fuskarsa ta sake fitowa sosai. Yana shigowa daidai da Zayyana ta riko Radhiya saboda tsinin takalminta suna saukowa a hankali. Murmushi ya sakar mata ita ta mayar lokacin da zukatansu ke tsananta bugu ya karasa step na biyar inda suke tsaya ya mika mata hannu "shall we?" Kai ta gyada a hankali tana ta murmushi ya riketa suka sauka. Su Zahra na biye dasu mazansu na waje suka je suka shiga motocin da mazansu ke jiransu. Ankonsu lace ne cream da head golden kowacce ka kalla kara. Zayyana kai tsaye motar Ibrahim ta wuce shi da Emzee su ma suit din ce jikinsu grey amma basu saka necktie ba sai maballin saman da suka bari a bude. Ba shi ba ba Emzee sai ka rasa wanda yafi yin kyau. Rahima tana biye da ita da dan glass dinta kamar a dauketa a boye Emzee ya kasa dena kallonta. Ibrahim da baisan dawan garin ba yace bari su dauki mota daya kawai suka tafi a tasa. Matan na baya suna gaba suna taba hira amma Emzee da Rahima sai uhm da uhmm. Bakar Limousine ce ta dauki amare da angwayensu zuwa Sheraton Arifah da Radhiya suka zama bebayen karfi da yaji. Kayansu babu bambanci ko daya sai sarkarsu yayin da mazan su ma komai daya ne a jikinsu. Kofar hall din katuwar poster ce zaune a kasa gefen dama hoton Yousuf da Arifah wanda suka yi da shadda matan aka saka pin aka danne musu fafaren mayafansu ta tsakiyar daurin da suka sha. A bangaren hagu kuma Radhiya da Awwab sunyi tsayuwa iri daya. Matan na zaune akan kujera suna kallon fuskokin mazansu dake tsaye a gefensu sun dafa hannun kujerar. A tsakiyar hoton an rubuta sunayensu. Kafin shigarsu iyayen taro suka taho. Kayansu saka iri daya bakin lace na Ummi da sky blue irin shaddar Daada, Mami Caramel irin shaddar Daddy, Mama light yellow irin ta Baba Hadir, Tante Brown irin na Alh Moussa sai kuma na Mom light green irin na Excellency. Idan ka cire iyayen Yousuf sauran hudun zaratan maza ne da suka dandani me ake kira bautar kasa da jiki da lafiya tare da matansu jarumai wurin hakuri da juriya. Taku suke ana daukarau hoto a cikin kayataccen hall din har zuwa mazauninsu. Bayan sun zauna be aka kira angwaye da amare abin gwanin ban sha'awa da burgewa. Taro ne na manyan mutane komai cikin nutsuwa da hankali ake gabatar dashi. Bayan an bude shi da addu'a aka gabatar da takaitaccen tarihin angwayen da amarensu. Wani abin burgewa shine kiran Emzee da da MC Kdm yayi a matsayin babban abokin amarya saboda babu wanda yasan Alheran Radhiya Zayyan Tureta sama da shakikinta Muhammad Zayyan Tureta. Zahra ce ya bada tarihin Awwab sai kuma wani abokin Yousuf da kawar Arifah 'yar kanin babanta suka bada nasu. Can cikin taro akwai 'yan gidansu Zayyan da su Hussaina harda Mummy Gambo da yaranta. Ghazalatu ta shiga wani yanayi na tashin hankali ganin yadda Awwab ya fito yayi masifar kyau. Kallonsa take bata ko kiftawa saboda yadda take jinsa a ranta. Ana tsaka da taron ne su ka ji wani dummm sai wanda ya sanya Awwab da Yousuf tashi lokaci guda kuma hall din yayi duhu sai haske ya koma bakin kofar shigowa. Radhiya dai taji Awwab ya matse mata hannu kadan sannan a daidai kunnenta yace mata yana zuwa. Idanu fa sai suka koma bakin kofa bayan kamar minti daya da rabi sai ga Yousuf da Awwab sun bullo ta katuwar kofar shigowa. Dukkansu sun cire coat dinsu sai ta cikin mai maballai ta gaba wadda suka dora akan farar shirt din mai dogon hannu sannan sun cire necktie sun bude maballai biyu na gaban shirts dinsu. Sanye suke da homburg hats kalar wandunansu an dan turo ta gaba a karkace. Yousuf ne ya fara magana da mic a hannunsa daga can gefen amaren ta sama aka fara slide show inda hoton Arifah ya bayyana tana zaune cikin fulawoyi tana murmushi. Sannu a hankali yake takowa zuwa gareta yana magana cikin harshen turanci duk da dai faransanci yafi zama sosai a bakinsa. ("Thank you Arifah Nasiruddeen for being a part of life. Thank you for accepting me to be the man in your life. You are my Queen the most beautiful woman I have ever seen. To the special you I say I love you") Ba Arifah ba hatta Mom dinta sai da taji wata kwallar farinciki. Hannunta ya kamo zuwa tsakiyar filin idanunsu cikin na juna a lokacin da Awwab ya soma taku daidai zuwa wurin zaman Radhiya. ("Once upon a time an adorable Angel was born") hoton Radhiya ne ya bayyana ranar sunanta wanda aka daukesu tana hannun Awwab yana murmushi ya dan juyo da fuskarta yadda zata fito a camera ("You and I were always meant to be. I love you with all my heart...just so you know, it has always been Alheran Radhiya. The fearless 'Yar soja, my one and only") Wannan karon Ummi ce da hawayen ta sunkunyar da kai Daada ya matsa mata hannu yana cewa suyi kusu addu'ar fatan zaman lafiya. Awwab ma riko hannun matarsa yayi zuwa tsakiyar filin kusa da Arifah sannan ya yi mata murmushi shi da Yousuf suka ja baya. Kidan wakar da matasan wurin da dama suka sani ta Umar M Shareef JININ JIKINA ce ta karade wurin hasken wurin ta koma kan Awwab, Yousuf, Emzee, Ibrahim, Bilal da Raji duka sun ajiye coats dinsu kowa ya tsaya a inda ya dace suka fara takun wakar yayin da baitin farko ya cika wurin. (Da ganinki sai na kamu.. gashi kin zamo jinin jikinaaaa) Ba tare da kuskuren taku ko tangarda ba domin sun sha wahalar rehearsal da mai koyar da rawar da suka dauko suke miming wakar suna rawar da ko wadanda suka hau ta a film din bazasu nuna musu komai ba. Mamaki tukuru.a fuskar Radhiya da Arifah yayin da jama'a suke kallon wannan abin burgewa ana ta murmushi da dariyar farinciki. Can gefen slideshow ake yi na hotunam da suka dauka rannan kowa yana bin baiti ana nuna amaryarsa. Saboda basu taba zato da tsammani ba shiyasa mamakinsu da farinciki yayi musu yawa. Radhiya sai da taji kamar a wurin ta rungume Awwab ta kwana tana fada masa cewa shi kadai ne farincikinta a rayuwa. Sai da wakar ta kare a daidai imda suke rawa a tsugunne suna kada hannuwansu su ma su Awwab hakan suka yi wuri kuwa ya kaure da tafi kamar zasu tsaga hall din. Gashi duk yadda manyan nan suka so yin liki an saka wani abu kamar ribbon alamun babu wucewa. Suna gamawa fita suka yi haske ya mamaye wurin MC yace za'a fara cin abinci. Ana ta hayaniya da zancen yadda abu ya kayatar Fauziyya tazo ta ja amaren zuwa dakin da zasu canja kaya. Lace suka saka coffee color da gold head da sauran accessories aka gyara musu kwalliya. Ana tambayarsu yaya suka ji game da babban surprise din su Awwab sai murmushi an rasa me cewa wani abu. To su ce me bayan amgwayen sun gama musu komai. A wurin shiga suka hadu dasu Awwab da Radhiya na gaba su Arifah na bayansu. Wannan karon shadda suka saka golden babbar riga da hula. Sun shiga kafin su zauna aka canja waka zuwa ta Nura M Inuwa wato 'Yar amanar da Radhiya ke matukar so. Wannan karon kam iyayensu mata sai da suka fito Awwab da Yousuf basu bar komai na irin takun Zango da ya hau wakar ba suna faman baza babbar riga. Liki akeyi kamar ba'asan ciwon kudi ba Awwab ya makale matarsa a gefe ganin wurin babu masaka tsinke. Taron ya tashi sa misalin shadaya da rabi na dare anyi hotuna anci an sha rayuka sun faranta. Ghazalatu kamar ta hadiyi tabarya haka bakinciki ya tsaya ya tokare mata wuya. Tana ta bin Awwab da ido bata san ta ina ba sai jin Nura tayi a bayanta ya rungumota a waje da suka fito ana tafiya gida. A fusace ta juyo tace masa bata son wulakanci meye haka zai tabata. "Dazun nan na mayar dake Ghazy" yace yana shafa keya. Ashar ta dankaro masa saboda tsabar bacin rai. Tana hangen yadda zatayi ta sami Awwab shine don rashin mutumci ya mayar da ita. Ko sauraronta baiyi ba ya jefata a motar da yazo da ita yace mata yau zasu fara angwanci. Wuri ya watse saura mutane kadan Awwab ya karbi mota a wurin drebansu wadda yada ya kawo masa ya budewa Radhiya. Yau duk ya kashe mata baki da abubuwan mamaki. Babbar rigar ya cire da hula ya dora mata akan cinya kamshin turarensa ya mamaye hancinta ya shiga mazaunin dreba ya tada mota. Shiru ta kasa magana sai murmushi ya kalleta yace "tunanin me kike yi Schatzi?" Kafin ta bada amsa ya zame mata gwaggwaronta da ya zauna das a kanta ta ja mayafin da ta ce a saka mata a jakar kayan ta rufe kanta. "Ke nake sauraro?" Ido ta runtse ta soma magana a hankali "Hammana bani da wani buri da ya wuce faranta maka. Abinda kayi min tun farkon haduwarmu har zuwa yau bazan taba mantawa ba. I love you with all i've got. Alheran is never complete without Awwab. Nagode, nagode, nagode" ta daga hannunta mai zoben da ya saka mata ta sumbata. Hannunta kawai ya kamo ya rike a haka ya kaisu gida suna kallon juna suyi murmushi. Ita kuwa harda sunkuyar da kai. Kusan kowa ya dawo ga motoci nan birjik a ciki ya samu wuri yayi parking. Rigarsa da hular ya dauke daga cinyarta ya jefa baya inda ya cilla mata gwaggwaro sannan ya juyo da jikinsa yana fuskantarta ya jinginar da kansa gefe. "Baby" taji yace a hankali sai da tsigar jikinta ta tashi. "Uhmm" "Na gaji sosai" "Ai dole ka gasa jiki ko ka kasa tashi gobe" ta fada gabanta na faduwa. Hannunsa ya mika mata duk lokacin yana kallonta tana jin idanuwansa a jikinta ta dukar da kai tana wasa da yatsunta da suka sha lalle. Sai da ta sake jin sabuwar faduwar gaba ta mika masa hannun damanta. Tayi zaton rikewa kawai zaiyi ashe hanya ya nema ya janyota gabadaya jikinsa tana kan cinyarsa. Rungumeta yayi sosai yana sauke numfashi ta soma mutsu mutsun son tashi. "Kinga" yace yana jan wani dan compartment a gaban motar tayi arba da mukullai "na gidanmu ne, ko dai ki nutsu ko na juya kan motar a biyoki da kayanki gobe" Da sauri tace "Kai Hammana" "I am serious baby na gaji sosai...mun kusa wata da aure da yanzu kin fara amai da tashin zuciya...." Salati ta soma yi kunya kamar ta nutse a wurin "ni dai babu ruwana" "Da nawa ni kam please ki bani janbakin nan na goge miki ko kuma mu tafi gidan" A tsorace tace "idan wani ya ganmu fa?" "Baki ji nace janbaki zan goge ba...haka zamu fada musu ai" ya sake yi mata wani irin riko. "Wannan fa wayo ne" "Ki bari nayi miki wayon mana" ya kyabe fuska shi a dole zaiyi mata shagwaba. Dariyar da ta soma yi ya datse da bakinsa tun tana jin tsoro har ta biye masa suka manta a cikin gidan Daada suke. 💕[11/2, 8:22 AM] 61💕🏽 Da kyar ta samu ya kyaleta ta fito daga motar ko ido ta kasa hadawa dashi. Shi kuwa ko a jikinsa sai ma murmushi da yake ta yi yana rike da hannunta. Kashe mata ido yayi yace "yau ba zaki kara shafa wani ba don kada a gane?" Motar ta nuna masa "shiga ka tafi ni dai" Dariya yayi mata sannan ya dora hannunsa akan kirji ya ce "Kora ta kike yi? You are breaking my heart Schatzi, nayi zaton yau babu mai rabani dake" "Ba korarka nake yi ba amma yanzu ina shiga ciki kunyar su Adda Zahra zanji. Sun san fa mun taho tun dazu amma kawai sai su ga na dade ban shigo ba?" "Kin ma bani tausayi, idan kika tare Alheran na rinka baki kunyar nan kenan. Yadda nake so matata ta rinka kulawa dani haka nima zan rinka yi miki" ya janyota jikinsa ya zagaye kwankwasonta da hannuwansa. Kunya sosai take ji gasu a waje kuma a gidan da yake da mutane tasan ko yaushe wani zai iya fitowa. Kukan shagwaba ta soma yi masa yace to ta shige ya rakata zuwa falo. Sun kusa shiga ta fara cewa ya juya ya tafi ita bata son su Fauziyya su ganshi. Kai ya girgiza yana janyota ta hanyar dora hannunsa a kafadarta suna jerawa "indai Zahra da Fauziyya ne ina tabbatar miki kowacce tana wurin mijinta yau babu mai kwana a nan. Femi da Jawad suna wurin Zayyana da Rahima" Baki Radhiya ta rike "a ina zasu kwana?" Hancinta yaja a hankali ya juyo da ita gabansa ya rage tsayi tare da hada nasa hancin da nata yana magana a hankali "su na inda muka baro yayyen naki kowacce tasan abinda ya kamata. Wannan tsallen da muka sha sai da tausa..." kwantar da murya yayi mai kashe mata jiki "Allah Sarki Awwab tasa matar kunyar mutane tasa ko tunanin ciwon jikin da zai kwana yana y batayi ba. Dani da na biya sadaki da Ibrahim da Emzee babu maraba" Hannuwanta ta ware kawai ta shige jikinsa ta kankame shi. Yau dinnan ya gama mata komai da performance dinsu. Hawaye take yi na tsabar son Awwab da kuma rashin son bata masa rai "Hammana kada kayi fushi dani" "Kin wuce haka a wurina baby. Bazanyi fushi ba amma sai an rama min." Kai ta gyada da murmushinta "na yarda" "Ranar da aka kawoki fa..." yace yana shafa fuskarta. "Na amince" ta bashi amsa a dake. "Baby kada fa ki chanja shawara ba kyaleki zanyi ba" yace da warning voice yana dariya. Juya masa idanu ta shiga yi tana jijjiga kai "meye a cikin tausa da ba zan iya ba Chèri? Allah Ya kaimu" Karamin yatsansa ya dago ya hada da nata "pinky swear?" yace yadda yara suke yi. "Sealed and stamped" ta kuma bashi amsa da kwarin gwiwa duk da har kasan zuciyarta tasan kawai fada take yi. Tun yanzu ma kunyarsa take ji ga faduwar gaba idan su na su kadai bare kuma ace daga ita sai shi a gida. "Yanzu zan tafi da kwarina..." sake kissing dinta yayi ya rakata har cikin falon da babu kowa sannan ya juya ya tafi yana mitar wannan kwanaki da ake ta cinye masa na kasancewa da matarsa. Zancen zuci yake yi yana tuki "Allah Ya kaimu dai ki haifa min baby girl. Idan ta girma ana daura aure zan bawa mijinta su tafi don ni dai kam wannan tsarin bazan yarda a sake yiwa kowa ba". ********** Yamutsa fuska Zayyan ya kula Mairama tana yi tun da suka dawo tayi wanka ta gama shirin bacci ta kasa kwanciya. Kwalbar turaren hannunsa ya ajiye ya dawo kusa da ita akan wata kujerar cushion mai laushi sosai guda daya da take dakin. "Fillo yaya ne?" "Warin panadol dakin nan yake yi kuma na duba ban ga inda magani ya zube ba" "Panadol kuma? Bana jin komai sai kamshin turaren wutar da kika saka" Hancinta ta matse ta hanyar sake yamutsa fuska "yanzu baka jin kamar panadol ya rube?" Zayyan bai san lokacin da ya kwashe da dariya ba harda buga kafa "rubabban panadol ne dai kin tabbata ba nine na tube din ba ko?" "Eh tayani dubawa ba wasa nake ba" ta tashi tana kokarin dukawa ya dawo da ita kusa dashi. "Nace miki na tureki kinki yarda. Tunda kika kin taba jin panadol ya rube?" Kunya taji tana murmushi "wurin dinner dinma fa haka ya rinka yi" "Fillo wata nawa ne ki dena ja min rai" yace yana kallon saitin cikinta. Wata irin kunya ta rufeta wai ita ke da ciki. Dazu da safe Mama ta kaita asibitin an tabbatar mata wata biyu ne. Da yatsu tayi masa alama Zayyan harda hawaye "kinga ikon Allah da yadda Yake gwada karfin mulkinSa ga wanda Yaso a lokacin da Yaso. Ina sonki Mairama Allah Yayi miki albarka Yasa ki zama matata har aljanna" "Amin Sojana...ba ka jiye min haihuwq ga 'ya a gidan miji" "Itama ta haihu nan da wata tara nake fata. Arziki ne ni dai nagode" "Nima ai nagode" "To muje mu kwana kafin na fara jin rubewar panadol din nima" yaja hannunta suka kwanta kamar kodayaushe aka bude sabon babin tsohowar soyayyar da kullum suke aikin sabunta ta. Da safe da yawa cikin bakin sun tafi musamman na Kano. Na Sakkwato kuwa sun jira su koma tare the next day. Zahra da Fauziyya ko keyarsa babu sai a ranar tafiyar. Awwab yazo yayiwa Radhiya sallama tare da saka mata kudi a jakarta ko za ta bukaci wani abu saboda shi da su Mami Katsina zasu wuce. Ummi, Mama da Tante ne zasu Sakkwaton. Can ma gagarumin taro aka hadawa 'yar Zayyan don sunyi bajinta sosai 'yan uwansa. Anyi komai an gama lafiya. A ranar 'yan daukar amarya suka zo da ga Katsina da akwatunan lefensu guda takwas da kit. Awwab yayi kokari matuka abu kadan ne ba shi ya saka ba. Duk wannan bidiri da akeyi Ghazalatu suna can wani karamin hotel da Nura yana angwancewa. Tayi kuka tayi bala'in ta koma rarrashi duk ya toshe kunmuwansa. Cewa yayi sai ranar da za'a kai amarya Katsina zasu koma lokacin an gama share gidansu domin can zasu wuce. Tana kuka ta kira Mummy Gambo wadda tace mata umarnin Alh Baba ne tayi hakuri ta zauna gidan mijinta da kansa yayi alkawarin idan Nura ya sake tabata zai dauki mummunan mataki a kansa. Ba sa son da kuruciyarta a fara kirga mata aure. Ba haka taso ba amma dolenta ta hakura ko don gudun kada jiki yayi tsami. Cikin wata hadaddiyar laffaya Mama ta shirya Radhiya aka fara shirin tafiya Katsina da matar Awwab. Ummi dai ba binsu zata yi ba daga nan Zayyan zai zo su wuce Nijar. Har yanzu bata bari kowa ya gane tana da ciki. Dauriya take sosai shiyasa Mama tayi ta kawo mata abin da zai sassauta mata tashin zuciya a boye. An fito tafiya da amarya idanunta a bushe saboda har yanzu ita fa bata ganin an kaita kenan tunda tasan zasu je Nijar sannan a koma Abuja. Abinda ta sakawa ranta kawai wani bikin zasu je a Katsina. An fito tafiya bakwai da mintuna Jume da Gwaggo Ladi sunyi mata nasiha zasu tafi da iyayenta mata yayyen Zayyan da matan su Badaru ga wasu cikin cousins dinta sai su Yadikko masu komawa Sumaila yayin da Hajjo da wasu yau din zasu tafi Katsina. Takalmin Radhiya me madauri ne ta durkusa tana daurawa wata tsohuwa tayi zaton kuka take yi tace " 'yar nan sai hakuri ki dena kuka haka kowace mace haka aka yi mata kema da sannu zaki saba" Dagowa Radhiya tayi innocently tace "Iya ba kuka nake ba takalmina nake daurawa" (wadda ta tsargu da ita nake.....) Ummi na gefensu tsabar kunyar da taji bata san lokacin da ta durma mata wani uban dundu ba sai da ta kuma durkusawa cikin fada tace "kuka kike mana, ba na hanaki karya ba shine zaki kalli idanun Iya kice mata ba kuka kike ba" Iya wadda ta kasance 'yar uwar Mal. Muhammadu ta kalli idanun Radhiya sosai "ai kuwa kamar ba kukan take ba Mairama" "Kuka nake mana Iya baki gani bane kawai...ni ku rikeni na fasa tafiya" Radhiya ta soma yi musu hargowa ana rikota tana komawa ta rungume Ummi. Tsabar takaici ta rasa me zata yiwa yarinyar nan ta huce. Wannan runguma a bainan nasi salon ace basu da kunya. Fada Ummi ta soma yi mata matar Rayyanu tace "haba Mairama ki rike yarinyar nan taji dumin uwa mana sai ki hauta da fada kamar baki san ciwon rabuwa da gida ba" Mama ta gimtse dariya tace "kinsan wani idan abu yayi masa yawa kukan ma kasawa yake...tun da muka tashi asuba take sharar kwalla" Ummi kamar ta hadiyi zuciya da Jume ta fito ga mutane suna ta cewa wai sun basu tausayi wannan uwa da 'ya akwai shakuwa sosai a tsakaninsu. Duk yadda take jin kunyar 'yar fari kuma a gidan surukai Sakkwatawan nan babu ruwansu suke cewa ta shiga daki ta kwantarwa da 'yarta hankali. Suna shiga Ummi ta juyo a fusace Radhiya ta kwashe da dariya sannan ta nutsu tace "Ummi Allah Ya kara miki lafiya wallahi bani da kamarki duk duniya" Hawaye ne ya saukowa Ummi ba shiri ta kai mata rankwashi ta goce. Da kanta ta rungumo Radhiyan tana murmushi zuciyarta na sake cika da farinciki "Allah Yayi miki albarka Ya baku zaman lafiya. Banda kiriniya kinga dai aure ba abin wasa bane kuma kin girma" Tana makale a jikin mahaifiyarta take amsa mata. Gudun kada a leko ta tasata a gaba suka fito aka sakata a mota. Canter guda aka cika shake sosai da kayan gara gari guda kamar masu shirin bude kanti. Gidan Alh Baba aka kaita inda duka kakanin da matayensu suke zaune suna jiransu. Yau dai wanda baisan Alheran Radhiyan Awwab ba ya ganewa idanunsa. Wasu ma sai tausayin Awwab din ya kamasu yadda Alh Baba ya hana wannan auren da farko. Zukekiyar bafillatana mai jinin buzaye irin wannan har ita ake yiwa yanga. Motocin da suka kawota dama akwai na sojojin da suka biyosu domin kariya kowa yasan ta wuce ajin raini ita da danginta. Yarinya an kawota da gararta abin kwatance sai son barka. Zahra ce ta shigar da ita falon kanta a rufe ba ta iya dago kai ba amma jikinta ya bata Awwab yana ciki saboda wani fitinannen kamshin turaren da yake amfani dashi yanzu. A gefen kakarsu Maman Biyu aka zaunar da ita Alh Baba yace "dawo kusa da mijinki jikata" A sanyaye ta tashi Zahra ta ja ta kusa dashi ta zauna a darare ita kuma ta fita. Nasiha tsofaffin nan suka rinka yi musu baka jin komai sai sheshshekar kukan Radhiya da gaske fadan yana shigarta. Da yake ta baza laffayar a kasan inda ta zauna ta karkashi Awwab ya zura hannu ya kamo nata sai da ta zabura amma yaki saki yana matsawa a hankali. Kukan nata ne ya tsagaita Baba Karami yace a wuce da ita gida su samu su huta. Uwargidan Alh Baba ce ta fito da ita aka damkata hannun iyaye mata suka wuce gidan Daddy. Dangi ne ko ta ina ga su Hajjo ma sun iso. Ana neman uwar amarya Mama ta fito ta rike hannun Radhiya har dakin Mami suna tare da 'yan uwanta ana hira kamar wani abu bai hadasu ba. Bayan gaishe gaishe da tambayar hanya Mama ta kama hannuwan Radhiya dake zaune a kasa har yanzu bata bar kuka ba jikinta yayi sanyi ta dora a tafin hannun Mami na dama sannan ta kawo na hagun ta dora a kai ya zama na Radhiya ke tsakiya. Muryarta babu alamun wasa tace "Mami ga amanar 'yata...." Mami ta harareta "meye haka Zainab, Radhiya 'yata ce kada kiyi min haka" Girgiza kai Mama tayi harda 'yar kwallarta "Mami ki barni nima na aurar da 'ya yadda kowa yake yi. Alheran dai a tafukan hannunki ta fado duniya kece kika karbi haihuwarta. Ko da aure ko babu ke uwa ce ga tsatson Mairama da Zayyan. A madadin babansu Hadir ina mai baki amanarta. Kinsan halinta babu wani abu sabo a wurinki. Idan tayi kuskure kinfi kowa sanin ta yadda zaki tsawatar ki sakata a hanya. Na baki amana ne ba don bazaki iya ba sai don taji da kunnenta cewa yanzu da da ba daya bane. Da can 'yarki ce yanzu kuwa jininki ta koma. Ke kuma Radhiya daga yau kin girma saboda haka duk abinda na fada miki a gida ki fara aiki dashi domin ibada kika zo yi" Zantukan Mama Zainab ya taba Radhiya da Mami suka rungume juna suna kuka. Yadda suka yi ya taba matan dake dakin sosai suna kara girmama wannan kyakkyawan zumunci na mutanen nan. Mami da kanta ta kama kai Radhiya dakin da Fauziyya suke tana fita kuwa suka fara zolayarta sai dai babu bakin ramawa an kashe mata jiki gabadaya. Bayan sunyi sallar la'asar anci abinci Mama ta hada 'yan uwanta da wasu kannen Mairama suka fito suka zaga kofar baya bangaren Awwab da yake jikin gidan amma kofarsa daga barin hagu ake shiga. Da can dan karamin falo ne da daki sai toilet. Amma ana gab da daura auren Daddy ya fadada masa wurin aka kara girman falon sannan akayi kitchen. Sun saba kowa a garinsu yake zuwa sallah. To haka yake son ta kasance ga tilon dan nasa. Sai kuma ya ga gidan nasu babu yara Zayyana kanta ba dadewa za'a aurar da ita ya zama daga shi sai Mami. Shine yayi wannan gyaran yada idan anzo Awwab ba sai ya nemi wurin ajiye iyali ba ko kuma su rinka rabe rabe a cikin gidan. Lokacin da ya fadawa Baba Hadir yayi wannan gyaran alfarma Hadir din ya roke shi akan cewa kada ya bari Zayyan ya sani haka kuma matansu sun boyewa Mairama. Komai da ya kamata a saka a cikin gidan nan Baba Hadir da Mama Zainab ne suka yiwa 'yar tasu. Daki daya ne aka saka mata wani makeken royal bed mai kyau. Ba'a cika dakin da tarkace ba bayan kayan gadon sai wani irin show glass na gani da fada wanda yasha turarukan wuta na asalin da humra da wasu irin turaruka masu maiko. Labulayen dakin kansu abin kallo ne. Toilet din a cikin daki yake an chanza tiles, tray din wanda, toilet seat da sink gabadaya an zuba sababbi. Kayan cikinsa ma sun hadu kamar ba toilet ba anyi masa kyale kyalen zamani. Falon bai kai girman dakin ba shi kuma royal chairs ne aka saka 3 sitter da one sitter guda biyu saboda wurin kada ya cushe. Ga katuwar wall tv da duk aka hada kayan kallo akan wani kayataccen tv stand. Centre table dinta da kananunsa na gefen kujeru duka masu kyau sai wani chest of drawer a karshen falon an jera plates da tarkacen kayan kitchen. Ana shigowa falon kofar dakin ce a farko daga dama sai kofar kitchen tana kallonsa daga hagu. Idan ka shiga kamar kada ka fita, gashi dai karami amma komai cikin girma da wadata akayi shi. Zaman aikin karasa duk wani gyara da yayi saura su kayi. Emzee da Ibrahim ne a kitchen suka hada gas cooker da su fridge. Kafin isha bangaren amarya ya fito fes sai wani uban kamshi har bangaren Mami ana ji. Su Hajjo sunyi mamaki sosai ganin Mairama bata yi musu zancen akwai wani gidan a Katsina ba. Ba tayi kasa a gwiwa ba wurin nemanta inda ta ce musu bata da labari ko kadan itama. Zayyan ta fadawa yace shima bai sani ba. Sun tabbatar aikin su Mama ne wannan ta kirata kuwa ta ma kasa godiyar sai kuka tana cewa "Zainab Allah kada Ya taba bawa shaidan dama a kanmu. Kada Allah Ya bani ikon zama butulu a tsakaninki da Mami" "Amin amma ki bar magana irin haka kada kisani kuka zan kira anjima" katse wayar tayi ta share kwalla. Me zasu cewa iyalin Zayyan. Gidansa da ya gida da guminsa da gadon mahaifiyarsa dungurugum ya baiwa DK kuma ya sayawa Ibrahim mota. Da shi da Daddy basu taba nuna wata alama da Hadir zai ji cewa bai kaisu arziki ba. Sun dauki kawunansu abu guda basa hangen komai sai soyayyar da suke yiwa juna. Bayan sun koma ciki ne take fadawa Mami gobe ana gama budar kan bayan magariba sai a kai Radhiya. Mami ta girgiza kai "a'a fa Zainab abinda biki bai kare ba, ko me za'ayi sai mun gama da Nijar dinnan kowa ya huta lokaci guda" Mama ta kankance ido don bata da niyar chanza shawara "Mami kuji tsoron Allah, aure kwana nawa ana jawa yarona rai. Yo banda ma dai shi Awwab din anyi mai hakuri da tuni ba sai dai labari ya sha bamban ba. Kullum saka ido nake in ga tafiyar Radhiya ta sauya....." Da sauri Mami ta mike "ba dai tariya kike so gobe ba? To a kaita dakinta gobe ba sai kin fara barambarama ba" Shu'umar dariya Mama tayi "haka kawai don dai daga shi har ita ba wayis bane ta wannan fanin ga gabontar 'ya'yan fari da duk mun kwashi kunyarmu a hannu tun a Abuja" Yousuf tun daga wurin dinner ya zarce da Arifah Nicon ya karbe wayarta sai gobe zasu tafi Nijar. Mom dinta tayi ta korafi Excellency kuwa yace yaro yayi masa daidai. Su basu yi lissafin halin da yaran zasu shiga ba kawai sunyi tsari yadda yayi musu. Gidan tun safe aka tashi da aikace aikace saboda walima ce babba Mami ta shirya a farfajiyar gidan. 'Yan uwa na nesa da kusa sun taru. Daga shabiyu zuwa la'asar anyi kade-kade da raye-raye Rahima tun tana jin kunya da komawa baya har ta ware saboda Zayyana bata san bakunta ba. Duka kayan da Radhiya ke sakawa Mami ce ta tanada. Bayan la'asar atampa aka bata ta saka super exclusive dinkin sosai yayi mata kyau aka dora mata wata bakar alkyabba tasha ado sai sheki da daukar ido. Wurin zamanta daban an kawata shi ga kujeru a jere aka kira wata babbar malama tazo yin bayanai da nasiha game da zaman aure da hanyoyin samun kyakkyawan zama da miji. Radhiya jikin gabadaya yayi sanyi hawaye kawai take zubarwa don kalaman matar akwai shiga rai da tsoratarwa. Sai da magariba ta gabato sannan taron ya watse bayan addu'o'i daga bakin malamar. Ciki aka koma ana alwala da sallah. Radhiya ta fito daga toilet kenan Mama ta shiga dakin ta kirata. Dakin Mami ta kaita babu kowa a ciki ta bata wani abu a cikin kofi mai zaki da wani dandano da bata gane ba. "Maza shanye kuma kada a sake baki wani abu ki sha kada kizo cikinki yayi ciwo sun isa haka. Sannan ki zama cikin shiri idan anyi sallah zamu kaiki kyayi wanka a can don nan ko ina a cike yake" "Ina?" Tace a firgice murya na rawa. "Bangarenku mana" Wani abu taji ya tsirga mata a ciki ta daure tace "Mama wane bangaren kuma?" Daure fuska tayi ganin Radhiya ta firgice lokaci guda kafin ta tara mata mutane "ina kinsan cewa akwai dakin Awwab a gidannan" Idanu cike taf da hawaye tace "eh" "To nan aka gyara miki idan kunzo kinga babu ruwanku da takurawa Mami kuna da komai a can" cewar Mama tausayin Radhiyan ya soma kama ta. "Amma ba. Ance. Ance sai mun dawo daga Nijar ko Mama?" Tace da sigar roko. Kafadarta Mama ta dafa tace "Radhiya, aure kika yi ba kwana kika zo yi gidan Mami ba kema yanzu nan gidanki ne. Ina so ki cire tsoro kamar yadda kika ji nasihar malamar nan dazu kada ki bani kunya kinji ko 'yar albarka. Jeki kiyi sallar zan zo mu tafi, kuma banda kuka ki tabbatar kin daure takalminki da kyau dai.." ta kare da zolayarta. Kasa daurewa tayi tana sallah tana hawaye. Yanzu shikenan sai kowa ya kwana a cikin gidan ita kuma a kaita dakin Hamma Awwab? Da an fada mata da wuri da ta shirya zuciyarta amma wannan bazatan ya shammaceta da yawa. Sukuku haka tayi sallah ta idar harda su sharar hawaye. Kukanta yasa Rahima rasa walwala tazo ta rungumeta itama tana yi batare da taji dalilinsa ba. Zahra da Fauziyya ne suka shigo Zayyana ta kira su akan kukan su Radhiyan. Zahra tace "amaryar Hamma me ya faru?" Kara sautin kukan tayi "wai kaini za'ayi" Da ido Fauziyya ta yiwa Zayyana da Rahima alamun su fita sannan ta kwashe da dariya "wai, wai, wai....kice yau za'a kwana ana goge janbaki. Gara kisa 24hours shine baya fita da wuri" Zahra ma dai dariyar tayi Radhiya na kuka tace "sai na fadawa Hamma" "Tuba nake anti amarya. Tashi muje in baki karatu kinji kanwata yayata" A dakin Mami kuma Mama ta kira Awwab tace masa shima ya taho da shiri yanzu za'a kai amarya jiya sha'afa tayi bata fada masa ba. "Ina za'a kuma kaita Mama?" "Bangarenku mana mun karasa jeren tun jiya" Wata irin murna ta kama shi yace "Allah Mama?" Sai da tayi dariya tace "idan ma kayi nisa ni dai yanzu zan rakata kasanta da son shiga jama'a kada taji ka shiru ta dawo cikinmu" Takalmansa yake sakawa lokacin a gefen gidan Baban Biyu inda sukayi sallar magariba yace mata "gani nan Mama....Mama nagode sosai" ya cigaba da zuba mata godiya sannan ya ajiye wayar ya taso Bilal ya fada masa a ina zai siyo abubuwan da ango ke shiga gida dasu. ********** Tsokanar Radhiya Fauziyya take tun tana kuka ta dena wani abun ma sai sunyi dariya ita da Zahra. Sallamar Mama taji wadda ta tsinke mata zuciya ta tashi da sauri. "Taso mu tafi" "Wayyo Mama banyi sallama dasu Adda Zahra ba" tace a rikice. Mami taji wani irin tausayinta domin tana kusa da Maman. Duk bakin Radhiya da dakewar zuciya yau babu. Mama ta rungume hannu a kirgi "to ina nan yi musu sallamar" Rungumesu ta shiga yi sai ta basu tausayi bare ma Fauziyya kukan take tayata. Hannunta Mama ta janyo "muje kinji gobe da safe zan turo miki su ayi ta rungume- rungumen" Mayafi kawai ta yafa ta saka wasu flat shoes masu dan uban kyau suka fito. Wata kanwar Ummi ce ta dauko akwatinta wanda bata san da zamansa ba duk cikin aikin Mami ne wannan kayan da ta dinka mata kala goma. Kayan kwalliya da underware daga cikin wanda ta taho dasu ne aka dibar mata aka zuba. Suna fitowa bakin kofa Emzee na danno kai zai shigo. Ai yana ganin tana kuka ya fara tambaya hankali a tashe. Kanwarsu ta bangaren Badaru ce ta fada masa kaita za'ayi. Ya bata rai kuwa. "Yanzu Mama ana kai kowa a mota amma Adda a kafa" Hajjo ta kamo kunnensa "To sannu me taya bera bari ina zamu kaita da mota" "Ni gaskiya ban yarda ba Mama don Allah bari na kaita a mota" yace yana turo musu baki. Rahima murmushi kawai tayi ganin halayen Emzee mabambanta. Ta dai tabbatar baya hada kowa da yayarsa kuma baya boyewa ma. Iyaye na masa fada ya kama hannunta ya rike "da so nayi na zagaye gidannan sai biyar dake a mota sannan a kaiki amma tunda sun ki muje na rakaki Addata" Dariya ya basu ya fuske abinsa wai ai bata da kawaye shine dai babban abokin. Haka ya shige cikin mata abinsa har falonta aka wuce dakin da ita ana musu fatan alkhairi. Ko minti shabiyar basuyi ba suka tafi Mama tace mata tayi wanka akwai kaya a ciki ta nemi wanda bazai takurata ba ta saka. ********** Tana jiyo hayaniyar mutane sama-sama daga main house din tayi kuri tana tunani wai yau ita ce a gidan nan a matsayin matar aure-matar Awwab. Ita ma bata da masaniya akan za'a ware musu wuri a gidan nan shiyasa take ta mamaki. Kanta ta bude ta karewa dakin kallo a take ya shiga ranta komai ya burgeta matuka. Ta tashi a hankali ta leka toilet, falo da kitchen zuciyarta fes. Tunowa tayi da gargadin Mama akan tayi wanka ga turaruka da ta nuna mata na humra a showglass da kuma wasu a cikin akwatin da aka zuba mata kaya. Mikewa tayi ta cire kaya tayi sa'a akwai tawul biyu a bandakin kuma akwai heater ta bango a kunne. Wanka tayi kafin ta gama taji ana kiran isha ta dauro alwala ta fito. Jakar kayan kwalliyarta ta dauko ta jeresu akan dressing mirror sannan ta shafa mai. Gaban showglass din taje ta bude ta shafa humrar masu daddadan kamshi tazo ta shiga fesa body spray. Gashi dama jikinta yasha dukhani dama cikin kamshin take. Tana durkushe gaban akwatin neman kayan sawa daga ita sai tawul taji an murda kofar dakin za'a shigo. Gabanta ya fadi da sauri taje ta danne kofar tana cewa waye cikin rawar murya. Murmushi Awwab yayi saboda a haka ma ya iya gano hakikanin firgici da tsoro a muryarta. "Schatzi masallaci zanje, na ajiye aby a falo ne kada ki gani ya baki tsoro baki san wanda ya kawo ba" "To" "Ba zaki bude naga fuskarki ba kafin na tafi?" Shiru tayi tana kallon kanta yaushe ma zata yarda ta bude. "Sai na dawo matsoraciya" A hankali yaji tace "adawo lafiya" Kasa kunne tayo taji karar rufe kofar gidan sannan ta sauke ajiyar zuciya. A gurguje ta janyo wasu riga da skirt na wani yadi mai laushi ta gyara fuskarta da kwalliya madaidaiciya ta kuma fesa turare sannan ta saka wani zumbulelen hijab mai hannu har kasa shima ta bishi da turaren. Sallar isha tayi ta hada da shafa'i da wutiri. Bayan ta idar ta zauna addu'a akan sabuwar rayuwarta kafin ta shafa ta ake jin alamun an shigo sai dai yanzu kai tsaye ya bude kofar dakin ya tsaya yana kallonta a zaune kan abin sallah. Shafawa tayi ba don ta gama ba sai dai kawai kallon da yake mata yayi yawa kuma yaki magana. Yana ganin tayi yunkurin tashi yace ta zauna. Abin sallah ya dauko a inda ta dauki wanda take kai ya shimfida a gabanta. Ta san sallar me zasuyi bata bukatar karin bayani ya ja su suka yi nafilar godiya ga Allah. Addu'a sosai yayi musu tana cewa amin a hankali ta kasa daga ido ta kalle shi. Mikewarsa ne ya sanar da ita ya gama zai nade abin sallar ta karba da sauri amma har yanzu bata kallonsa. Shi burge shi take yi komai nata. Ta bayanta taji ya tsaya ya zuro hannayensa ya tayata ninke abin sallar. Faduwar gabanta ya sake tsananta lokacin da ya rungumeta a haka ya dora kansa a kadafarta yana mata magana a kunne. "Dama kin ajiye wannan shirun bani da niyar chanja abinda nayi niyya yau ko da zip zaki saka a bakin" "Hammana me kayi niyya?" tace jiki a mace. "Good ashe da bakinki...idan na fito daga wanka zan fada miki, abinda na sani dai shine...." ya juyo da ita suna fuskantar juna tayi saurin runtse idanu. Matso da fuskarsa yayi saitin ta sosai "muna da alkawarin massage idan kin manta zan tuna miki" [11/2, 8:28 AM] 👸🏽MAMIN SADIQ 👸🏽: Bai jira cewarta ba ya saketa ya kama rigarsa zai cire. Da sauri ta bar dakin ta rufe masa kofa tana haki ita dai yau ta shiga dari. Awwab kuwa dariya yayi ya wuce yayi wanka shima yayi duk wani abu da ya saba na shiri bacci. Tana zaune tsuru kamar wadda ta yiwa sarki karya ya bude kofar dakin ta dago kai da sauri suka hada ido. Kayan bacci ne a jikinsa na cotton riga mai gajeren hannu da dogon wando. Wannan kamshin da yake janta gareshi ta soma shaka ta lumshe ido a hankali. Kusa da ita ya zauna ya bude ledar kazar da take da zafi har yanzu sai kuma ya mike ya dauko robar maltina daya a fridge ya dawo. "Cire hijabin kici abinci" "Ni dashi zan ci" "To babu laifi shi ma bazai hana ango abinda yayi niyya ba" yace yana kashe mata ido. Turo baki tayi cikin shagwaba "ni wallahi tsoro kake bani Hammana. Me kayi niyya" Mischieviously yayi murmushi "nothing...ahhh bude baki" ya mika mata naman. Kasa karba tayi ta sunkuyar da kai. Ya kula dai yau da rigima a tare da ita sai ya dauko remote ya danna tunda an jona komai na tv din ya shiga neman channel din da zai bari a nilesat. MBC 2 ya kai ana wani film ya tambayeta ko tana son gani tace eh da sauri. "Zan barki ki gani amma da sharadin zaki cire wannan hijab din muci naman nan if not yanzu zamu shige daki..." Kafin ya kai karshe ta yiwa hijabin masauki akan wata kujerar yaji numfashinsa ya tsaya na yan dakiku saboda kyaun da tayi masa. Gashin ta ta kama ya zare ribon din ya zuba a bayanta da kafadu. Wannan lallen da tayi yasa kan yayi kyau sosai inda kalar ta fito ya zura yatsunsa a ciki yana rufe idanu. "I love this Alheran" ya janyota kusa dashi sosai yana yamutsa mata gashin. A gefen jikinsa ya rabata ya shiga bata naman yana ci shima. A haka suka koshi yace tayi zamanta ya kwashe komai zuwa kitchen. Sauran ya saka fridge ya wanko hannunsa ya dawo. Miko mata hannu yayi yana son ya taso ta kyabe fuska "ai ba'a gama film din ba" "Brush kawai zamuyi mu dawo" "To kaje ka fara yi kaine babba" Dariya ta bashi wai nan wayo zata yi masa ya wuce dakin yayi ya dawo "saura ke" "Kada ka kashe tv din Hammana yanzu film din ya fara kyau" tace tana tashi bayan bata fuskantar komai a ciki. Ko wuka za'a saka mata bata san me akeyi ba. "Zama zanyi na gane miki inda kika tashi" ya zauna ta tafi. Tana rufe kofa ya kashe tv din da fitila sannan ya shiga daki ya rufe kofa. Ai tana jin motsin shigowarsa jiki ya soma rawa ta gama brush din ta kasa fitowa. Sai da tayi minti biyar ta yanke shawarar ce masa ita fa kallo zata yi kawai. Da kwarin gwiwa ta fito yana waya cikin harshen jamus yaki kallonta. Zaune yake akan gado ya mike kafafunsa ya jingina da pillow. Kofar dakin taje ta murda taji a rufe. Ta sami wuri ta tsaya tana jiran ya gama. Sallamar mutumin yayi ya taso yana tahowa gabanta na kara faduwa. A tsakiyar dakin ya tsaya ya ware mata hannuwansa yana murmushi tare da yi mata nuni da ka. Babu yadda ta iya ta saki hannun kofar ta taka da sauri ta fada kan kirjinsa. Sun dauki kusan minti biyu a haka kowa da nasa tunanin da yake tattare da soyayyar dayan. Da yatsunsa ya dago kyakyawar fuskarta a tausashe yace "Babyna guduna kike yi kuma?" "Film din...." sai kuma tayi murmushi ta kasa karasawa. "Kema kin san baki da gaskiya gashi kinyi shiru. Muje ni inyi miki tausar tunda kin kasa cika alkawari" "Zanyi maka" "Fara saka kayan bacci" Akwatin nata ya bude babu ko daya na lefenta kuma suna Sakkwato za'a wuce dasu Abuja. Wardrobe ya bude inda ya zuba nasa kayan ya dauko mata t-shirt dinsa tana ta kamshi. "In saka miki?" Yace yana dariya don yasan bazata yarda ba. Harararsa tayi "da kayana zan kwanta" "Schatzi" yace hannuwansa na jindadin yamutsa mata gashi ya rasa dalili ita kuwa da kyar take iya bude idanu saboda yadda take ji. "Naam" ta amsa a raunane. "Saka riga ko Ango yayi abinda yayi niyya" Sakinta yayi ba don yaso ba tana ture turen baki ya fita daga dakin don ta shirya a tsanake. Cikin sauri take komai tana yi tana kallon kofa gashi key din ta waje yake. Rigar ko cinyarta bata gama rufewa ba. Tana fesa turare ya turo kofar jikinta ya soma rawa shi kuwa Awwab rufe kofar yayi ya jingina da bayanta tare da harde hannuwansa a kirji yana kallon Alheran a matsayin matarsa abar so da kaunarsa. Turaren da ta dauka ta ajiye jikinta yayi matukar sanyi tana kallon gadon tana son zuwa ta kwanta ta rufe jikinta amma bata son yin kwakkwaran motsi a gabansa. Tahowa yayi gabanta yasa hannu a waist dinta ya matso da ita jikinsa da dayan hannun kuma turaren da ta ajiye ya dauka ya feshe mata jiki dashi sannan ya saka hannuwansa duka ta bayanta ya dagota jikinsa ya soma juyi da ita a dakin tuni ta kankame shi tana dariya. "Please, please, pleeeeaaass ka ajiyeni" tace tana zagaye hannuwanta a wuyansa. "Sai na cire miki wannan tsoron da yake hanaki sakewa" "Zan sake....Chéri na sake ma.....Hammanaa" Ajiyeta yayi a hankali tana jin kamar har yanzu juyin suke yi ta kankameshi tana sauke numfashi. Hannuwansa ta sake ji ta bayanta ya tura yatsunsa cikin gashinta da ya mayar abin wasa yana magana can kasan makoshi "na yafe miki tausar nan fa" Zare jikinta take neman yi ta kasa saboda rikon da yayi mata a hankali tace "nagode" Dago kanta yayi yana bin bakinta da kallo idanu a lumshe "gani nayi ko da tausa ko babu bazai hanani abinda nayi niyya ba" Tsoron ya soma dawowa tace "Wai me kayi niyya ne?" Wani irin kallo mai kashe jiki yake binta dashi yace "Spending the whole night loving you my baby. Ki taimaka ki bani dama saboda ko kinki bazai hana Awwab abinda yayi niyya ba, bani da hakuri indai akan sonki ne Alheran" kasa yayi da kansa ya soma kissing dinta tamkar ranar ya fara samun wannan damar. Radhiya bata iya sake komai ba sai abinda Awwab ya koya mata. Kamar yadda yace ya nuna mata soyayyar da bazata taba hadata da komai ba a rayuwarta. Bacci kuwa sai can cikin dare ya rungumeta tsam a jikinsa ta soma yinsa a wahale tana ajiyar zuciya hawaye har cikin bacci yana jin digarsu a kirjinsa. "I am sorry my love" yace yana kara karfin rikon da yayi mata. "I love you so much" duk da yasan ta dade da soma bacci ba zata ji ba. Hannunsa na dama ya sarke da nata yana shafa kanta a zuciyarsa yana addu'ar Allah Ya basu zaman lafiya da albarka a zaman aurensu kuma Ya basu hakuri da juna. Soyayyar gudan jinin Tureta da ita ya girma yana rainon abarsa a zuci tun kafin su sake haduwa. Idan da akwai abinda yafi love at first sight kuwa to shi ya fada head over heels akanta. Ita ce duniyarsa, farincikinsa, cikar 💕* 63*💕 ************************************ Kiran assalatu na farko ya farkar da Awwab ya tashi da sauri yayi wanka saboda kada ya makara. A hankali yake komai saboda kada ya tasheta. Da ya gama ya sa dogon wando jeans ya dora rigar sanyi akan shirt din ciki don tun dare garin yake a lumshe ga iskar nan ta tsananin sanyin arewacin Nigeria da asuba. Zama yayi a gefen gadon yana shafa fuskar Radhiya a cikin duhun dakin sai haske kadan da yake fitowa daga toilet da ya bar fitila a kunne. Tashinta yayi yace asuba tayi. Sannu a hankali ta dago kan ta daga pillon ta bude nannauyan idanunta da fitowar hawaye. Yatsansa ya dora akan lebenta "Shhhh haba babyna kinyi bacci da kuka kin tashi dashi bai kamata ba. Idan bazaki iya tashi ba ki jirani na dawo daga masallaci" Hannunta na dama ta dunkule ta kai masa duka a kirjinsa tana kara narkewa cike da shagwaba da hawaye "bana bukata tunda ba ka sona" Awwab yayi murmushi tare da mikewa yana son tayar da ita sosai "zan baki amsa idan na dawo" Kunyarsa na tare da ita tayi saurin boye fuskarta cikin lallausan duvet din "Allah Ya tsare" "Amin Alheran" Yasa kai ya fita sannan ta tashi tana cije lebe don ma ya fita da ya ga raki da shagwaba mai lasisi. Duk abinta bata so ya dawo ya sameta a kwance saboda tana jin kunyarsa kada yace zai taimaka mata ba yarda zata yi ba. Shawarwarin Mama Zainab da Innawuro tsohuwar kakarta da tun farko ta fara gyara mata jiki da lalle tayi amfani dasu wurin cire son jiki ta gasa kanta da ruwan zafi sosai. Tunda akwai sanyin gari sai ta kara jindadin hakan. Bata bata lokaci sosai ba saboda gudun kada ya dawo ya sameta ta shafa mai mai kamshi da body spray sannan ta mayar da t-shirt dinsa da ya bata kafin su kwanta da dogon skirt dinta. Hijabinta ta dauko a falo tazo ta tayar da sallah tana faman runtse ido. Lokacin da Awwab ya fito a bakin gate ya hadu da Daddy. Kunya kamar ya nutse a wurin ya ji kamar ya koma saboda wani nauyin mahaifin nasa da yake ji. Samun kansa yayi da durkusawa har kasa yana tambayar Daddy din "an tashi lafiya? Yaya baki su ka kwana?" Sakin fuska yayi saboda ya fuskanci Awwab din a takure yake da kunya ya ce "Lafiya kalau Captain yaya kwanan diyata?" Kara masa kunyar yayi ya kasa amsawa sai kai da ya sunkuyar yana sosa keya. Daddy yayi murmushin manya yana musu addu'ar zaman lafiya. Da aka idar da sallah a masallacin ya so yayi saurin tafiya gida amma idon Daddy ya zaunar dashi. Tsohon sojan ba wuya ya gano bakin zaren shiyasa yayi kokarin katse wani makocinsu da yake neman jansa da hirar zaben da ya kusanto ya tashi su ka dawo. Gyangyadi Radhiya take yi akan abin sallah ta jingina bayanta da gadon ta ji ana rufe kofa. Cikin sauri ta cire hijabin ta hada da abin sallar ta ninke ta koma gadon ta rufa har ka. Sauran rufar ma a idon Awwab tayi saboda bude kofar dakin da yayi da sallama. A zuci ta amsa masa a zuwan bacci take yi. Yana kallon yadda take ta gyara kwanciya irin na masu baccin karya ya kyaleta sai da ya cire kayansa don yasan ba dadin kwanciya dasu zaiji ba ya saka jallabiya. Zagayawa yayi gefen gadon bangaren da fuskarta ke kallo ya durkusa. Da sauri da sauri take fitar da numfashi saboda tsabar kaduwa ga hawayen tausayin kanta tana yi. Hannun Awwab ta ji ya janye rufar da tayi ya bude fuskarta. Cikin gashinta da ya bazu akan pillow din ya sarke yatsunsa yana jin yadda ta soma rawar jiki. Idanunsa yake lumshewa yana budewa a kanta cike da kasala ya ce "Da kinyi soja yau da nayi musu dariya saboda kin basu kunya karshe. Abu kadan sai kuka jikinki yayi ta rawa." Bakinta ta turo "to ba kaine ba..." Ya karyar da kai idanunsa a kan bakinta "Saboda kin fini baki Schatzi, nima fa kukan nan ya kamata nayi tunda jiya aka kawoni" Dariyar da bata shiryawa bace ta kama ta. Yadda take dariyar ma baiki ya koma gareta ba saboda tamkar wanda aka sakawa magnet haka yake jin kansa. Sai dai yana tausayinta don yasan taji jiki...Allah Ya taimake shi an ware musu wuri ba a cikin gidan aka basu daki ba da an tafka abin kunya yadda ta rinka kiraye kirayen mutane. "Yaya jikin naki my amazing wife?" Juyawa take son yi daya barin saboda kunyar tambayar da yayi mata ya rike mata hannu yana girgiza kai. "Ko zaki juya ki bari na fada miki abinda nayi niyya kafin kiyi bacci jiya" kasa kunnuwa tayi saboda ko me Awwab zai fada mata abin so ne a gareta. Ba tun yau ba ya kware wajen fada mata kalmomin da kan sa ta kwana tana murmushi ita kadai. Idonsa sarke da juna suna aikawa juna sakonni da fahimtarsu sai su din ya soma magana da muryar nan mai tsuma zuciyar Alheran Radhiya. "Na karbi amanarki kuma na baki tawa. Matsayinki bana jin akwai wadda za ta taba samu a zuciyata. A kanki nasan mecece soyayya kuma nasan amfanin shakuwa. Baby kin faranta min rai sosai jiya duk da kin so cika min kunne da kuka...." murmushi tayi ta kawar da kanta shi kuwa tafin hannuwanta ya bi ya sumbata. Kafin ya cigaba da cewa, "You have my love" ta dago kai kadan ta dube shi. "You have my trust" ya matse hannunta yadda ba zata ji zafi ba. "And you have my respect" ya duka tare da kissing goshinta. Zai dago Radhiya ta zura duka hannuwanta ta rungumeshi a jikinta. Suna shakar kamshin jikin juna a haka ya dawo kusa da ita ya kwanta karatun nasu ya tattara ya koma na sababbin auren da suke matukar so da kaunar juna. Radhiya tayi dauriyar kin yi masa kuka amma ta kasa daga karshe. Kuka ne da tasan ba na wahala bane kawai harda wata irin soyayyar Awwab mara misaltuwa. Shi ma yana namiji yaya mamakin ganin yana tayata hawaye a lokacin da sabuwar soyayyarta take huda kowane bari na jikinsa tana sake samun mazauni. A take a wannan lokacin jikinsa yake fada masa cewa da wahala matuka wata mace ta sake samun gurbi irin na Alheran....son ta a jinin jikinsa yake. It has always been Radhiyan Hamma Awwab. Bacci suka koma irin wanda da wuya in sun taba yin irinsa mai tattare da nutsuwa da kwanciyar hankali. Basu san lokacin da Zayyana tazo wurin goma ba tayi ta doka sallama da breakfast dinsu har ta gaji. Kofar net da aka zagaye karamar barandar da ke gaban katuwar golden kofar gidansu mai kyau ta bude ta ajiye kwandon tunda a rufe komai yake da wani kyalle mai kyau. Komawa tayi ta fadawa Mama ita fa taji shiru. Shadaya saura wayar Awwab ta soma ruri ya dauka da sauri zai kashe saboda kada karar ta tasar masa Radhiya dake kwance akan faffadan kirjinsa. Sunan Mama ya gani babu damar kashewa kenan yayi kokarin zame jikinsa Radhiya ta kara cukwikuye shi tana zumburo baki. Murmushi ya saki ya kawar da gashinta daga kan fuskar yace "so adorable". Wani kiran ne ya sake shigowa still dai Mama ce ya danyi gyaran murya kafin yayi mata sallama sannan ya gaisheta. "Awwab kayi hakuri surukanka zasu wuce ne mutanen Sakkwato da Sumaila shine suke son yiwa Radhiya sallama. Sai na ga ya dace ka fara shigowa kayi musu bangajiya" "Mama ni kadai zan shigo?" Ya ce kamar zaiyi kuka don tsakaninsa da Allah kunya yake ji ya shiga gidan. "Ka nemi 'yan uwanka su Bilal kuyi sauri. Ina kanwar taka ina fata ta tashi ta shirya ba jimawa zasu shigo" Shirun da yayi da guntuwar in'ina ya fahimtar da Hajiya Mama komai. Murmushi tayi mai sauti Awwab ya rasa me zaiyi sai ya ga Radhiyan ma ta farka kawai shiru tayi tana kunyar tashi. "Bani ita Awwab" yaji Mama tace. Dora mata wayar yayi a kunne kafin ta soma magana Mama tace "saurareni da kyau Radhiya kin tuna me nace jiya ko?" "Uhmm" tace a hankali. "Tau, ki shiga ruwan zafi sosai kinga gobe akwai tafiya gabanmu idan ba so kike ayi ta zancenki ba ki gyara kanki. Zan shigo anjima idan bakiyi ba zan gane kuma kinsan sauran" Rufe kanta tayi ta mikawa Awwab wayarsa. Tana ji ya tashi ya shiga toilet bai dade ba ya fito ya yaye rufar da tayi sai da tayi masa ihun ganinsa da tawul kadai gashi ya cire mata abinda ta rufe kanta. "Muje muyi wanka" kawai yace ya sunkuceta yana cewa ashe buhun sumunti ce bai sani ba. Duk wani zille zille da taso yi bai barta ta fita ba a haka akayi wankan. Bayan sun gama ya hada mata ruwa mai zafi a robar da ta zauna dazu wadda saboda hakan Mama ta saka musu ita. "Kin sanni da kunne ina jin me Mama take fada" ya kashe mata ido ya fita ya barta da tulin kunya. Lokacin da ta fito ya gama saka kaya sai wannan kamshin nasa na musamman take ji. Shadda ce ya saka mara nauyi ga hularsa a gefe. "Ba don ina tsoron kaina ba kuma dai ana jirana da na tsaya shiryaki da kaina baby" yace lokacin da ya ajiye brush din da ya taje saisayayyen kansa. "Na yafe fita ka tafi" Kan gado ya fada sai lokacin ta kula ya chanja komai amma kunya ta hana tambayarsa ina ya ajiye wadanda ya cire. "Kunyar fita nake yi kada a gane" ya tashi yana tafiya a gefenta "tayani dubawa tafiyata bata chanza ba ko" Bubbuga kafa ta soma yi "Hammana bana so" "Ba fa dake nake ba, nima bana so a gane ne kinsan manyan nan..." Daga murya tayi cike da shagwaba ta ce "HAMMAAAA" Yana kyakyata dariya ya fita. Kwandon abincin ya gani ya dauko ya dora a kan centre table sannan daga inda yake ya fada mata ta tabbatar ta ci kafin ya dawo. Shiryawa tayi cikin wani hadadden lace tayi daurin da ya bayyana gashinta da tayi packing ta sako shi tsakiyar daurin sannan ta gaban ma ta ja dankwalin ya danyi baya. Fuskarta tasha kwalliya tayi kyau sosai. Sauri tayi ta gama saka awarwaron da ta dauko kalar kayan sannan ta fito falo ta dan karkade kura duk da babu. Turaren wuta ta saka a ko ina kamshi kuwa ya soma tashi kana tahowa bangaren za ka ji. Fridge ta bude babu komai na kayan abinci sai ruwa da lemo kala kala. Da yake ana sanyi tunda suka zo Katsinan sau daya aka dauke wuta shima bata dade ba aka dawo da ita. Abincin da aka kawo ta bude, doya ce da aka soya da kwai a flask daya sai bread da farfesun kaza ya ji kayan kamshi. Ga kayan tea da ruwan zafi a flask. Kitchen ta kai ta ajiye don bata jin za ta iya cin komai duk yunwar da take fama da ita kuwa sai Hammanta ya dawo. Awwab kuwa da gaske sai da Bilal yayi da gaske su ka shiga falon Mami inda iyaye da kakanni ke zaune. Ana ta tsokanarsa sai su Bilal ke ramawa shi kam baki ya mutu Schatzi kadai yake tunani. Da su ka gama fita suka yi zuwa wurin Radhiya an gama saka kayayyakinsu a motocin da zasu bi. Duk kunya ta isheta gashi babu su Rahima an barta ita kadai da manya kowa da abinda ya ke kara mata na nasiha. Kafin su fita Awwab ya dawo ya shiga daki sai gashi da envelop guda biyu. Daya ya bawa Hajjo dayan kuma ya baiwa Gwaggonta Mubaraka kowa su raba da abokan tafiyarsu. Shi kadai ya rakasu ta biyosu zuwa bakin kofar net din suna cewa ta koma ba sai ta fito ba. Tunda Awwab ya shigo suka ci abinci tare suke makale da juna sallah kadai ke fitar dashi. Shagwaba kala kala yana gani tana kuma burge shi sai nan nan yake da ita kamar kwai. A haka ma baya samun yadda yake so sosai saboda kunyarsa da tayi mata yawa. Abincin rana ma kawo musu akayi daga ciki wannan karon Rahima ce ta kawo Awwab ya karba. Su Zahra da Fauziyya suka kafa naci kamar bala'i sai sun je wurin Radhiya. Mama tace "gulmammu wace acikinku bata ga wannan daren ba eyye. Zaku je ganin kwaf ku gani ko ta sauya tafiya ko..." Mami sai da tayi dariya don ba karamar kunya suka ji ba har Fauziyyan kuwa. Zahra kamar ta kifa don sauri ta fice daga falon kafin a karasa barota. Mama kuwa sun kunnata bata iya yin shiru ba ta cigaba da sababi. Kafin magariba ragowar tawagar Malamijo sun iso gidan saboda tafiya Nijar da safe. Salame ce akan gaba ko zama bata yi ba wai sai ta ga dakin amarya. Sakin baki tayi tana kallon kayan kudi sai da Mama taje da kanta ta yo waje da ita wai da bandaki zata shiga ta rage mara tayi alwala ko tunanin cewa bandakin daya ne kuma a cikin dakin baccinsu bata yi ba. Sai da suka shiga ciki ne ta ga Halifa tare da Emzee da Ibrahim. Duka su ukun sun gaisheta babu yabo babu fallasa sai dai yanayin fuskar Emzee ya tsaya mata a rai fiye da zato da tsammaninta. Ganin Rahima ne ya mantar da ita komai abin mamaki ga ita kanta Rahiman Salame wani mugun tattali take yi mata kamar ta maidata ciki. Tunda Malamijo ya kirata yayi mata tas akan mutuwar idon Rahima tasha kuka kamar ba gobe. Ba komai ya tsaya mata a kahon zuciya ba irin yawaitar lokutan da Rahima ke durkusawa a gabanta tana rokon idan laifi tayi mata ta taimaka ta yafe mata. Yarinyar bata da matsala kuma bata santa ba. Burinta daya a duniya ta ga mahaifiyarta ta sakar mata fuska ta kaunaceta kamar kowa. Ita da ta iya zuwa wurin boka ta makanta Mairama da asiri yau an wayi gari 'yar cikinta ta gamu da lalurar da indai wani abu ya sake samun dayan idon mai lafiya to ta makance kenan fa. Tana ganin abubuwa amma ba ta iya rarrabesu. Ranar duk wani guntun rashin mutumci ma nemansa tayi ta rasa. Fatanta bai wuce ta kyautatawa Rahima ba ko ta yafe mata cikin sauki. Ga Halifa fuskarsa kullum a hade idan ya ganta musamman bayan matsalar idon kanwarsa. Baccin kirki kasawa tayi da ta duba hagu da dama sai kaji tana ina Rahimata? A bangaren su Ummi ranar su ma suka wuce Nijar da Daada. Duk wani boyonta kallo daya Mammee tayi mata ta ja ta uwar daki tana murmushi. "Mairama ciki gareki ko?" Tace da hausarta mara fita sosai. Ummi taji kunya sai sunkuyar da kai kasa take. Mammee kuwa tsabar murna ta fito tana shelantawa. Ummi ta rufe kanta a daki ta kasa fita saboda yadda 'yan uwa suke ta murnar wannan rantsatssen rabo. Zayyan yayi ta dariya yace maganinta kenan tunda ta damu a boye gashi anyi mata mai gabadaya. Cikin 'yan uwansa mata harda mai tambayarta wata nawa ne saboda a fara shiri. Ta ga gata muraran don ko cikin fari ne a jikinta karshen abinda zasuyi mata kenan. ********** Da daddare bayan sun gama dinner Radhiya tana wanke kayan da suka yi amfani dashi bata ji shigowar Awwab ba sai hannuwansa da suka bullo ta gefe da gefen cikinta ya riko plate din da take daurayewa suna yi tare. Jikinta tuni ya fara rawa saboda hatta soso sai ya sarke yatsunsu sun wanke abu tare dashi. Kiss taji a wuyanta ta kusa sakin glass cup din da suka gama daurayewa ya ce "hankali baby" "Ai kaine" "Ni sarkin laifi me kuma nayi" Tsuke bakinta tayi ya cigaba da abinda yake yi yana birkita mata lissafi. A daddafe aka gama ta rufe ido kawai ta kwanto da kanta kan kirjinsa sosai na dan lokaci sai kuma ta juyo suna kallon juna "Chèri muje na hada maka kayan tafiya gobe" "Kin hada naki ne?" "Suna cikin akwatin da Zayyana ta kawo min dazu da ta kawo abincin dare" Dakin su ka koma ya dauko wani akwati mai taya hudu daga kasa irin wanda duk nauyinsa mai ja baya ji saboda a tsaye yake rectangular. Na biyun karshen ya dauko ya nuna mata kayan da zaiyi amfani dasu ta fito dasu za ta zuba sai gani tayi ya zazzage nata kayan akan gado. "Hammana ya ka juye kayan ko basu shiryu bane?" A akwatin da take zuba nasa ya shiga jerawa "babu amfanin mu tafi da bags daban daban ne" "Idan ba masaukinmu daya ba fa?" Janyota yayi suka fada kan gadon yana zagaye fuskarta "nasa Yousuf ya kama mana hotel na kwana biyun da zamuyi" Ai sai ta kasa hadiyar yawu don fargaba "duk kowa yana nan sai mu tafi hotel?" "Yes...ta kare min Schatzi kema kin sani" ya cigaba da zana fuskarta da yatsansa "idan da nayi hakuri yanzu bazan iya ba...KEMA.KIN.SANI" ya fadesu dalla dalla kafin ya shiga nuna mata soyayyar da ko rabi rabin abinda ke ransa bai sauke mata ba. Kayan da basu karasa hadawa ba kenan su da akwati daya da himilin kayansu dake zube a gefe suka kwana a kan gadon. Tun asuba da suka yi wanka ta karasa hada musu kayan ta gyara dakin ta wanke toilet. Basu bar komai a waje ba bedsheet din ma cirewa tayi ta dinke ta turasu cikin ledar da yake ciki da kyar saboda gudun kura. Motoci harda wanda babu budget dasu mutane sun bi su Nijar ganin kwai da kwarkwata. Kamar kullum karamcin mutanen yana bawa Radhiya mamaki. Kudi ne dasu iyaye da kakanni amma akwai tarbiya da tsagwaron hadin kai a zuri'ar Alh Ghousman Agali. Gidan Alh Sidi Radhiya ta shiga saboda ance Umminta tana nan ta fada dakin da aka nuna mata da murnarta nan ta sami Emzee suna rigima da Mammee tana tura masa nonon rakumi ya damtse bakinsa yaki karba. Kan Ummi ta fada da murnarta Mammee ta sakarwa Emzee robar nonon ta tashi tana fada. "Alheran yaushe zaki girma ne ni Aghaisha" Turo baki tayi tana nanikar Ummin "me kuma nayi miki daga shigowata?" "Dagata kada ki kassara min jika, maimakon ki tayamu tattalinta sai ki tsaya shirme?" Ina kasa ta bude Mairama ta binne kanta. Emzee ya dago fuskarsa da nono ya watso masa ya kalleta sai wani nauyi ya bakunce shi ya dukar da kai. Radhiya kuwa ihun murna ta saki bilhakki ta sake rumgume Ummin tana murna. "Wayyo ni, wayyo Umminmu Allah Yasa mace zaki haifa me kama dani" tace tana dariya. Emzee ya kalli yadda take yi ya kalli Umminsu da kunyar da ta lullubeta sai ya tashi kawai yaja hannunta "Hamma Awwab yana kiranki muje na rakaki" Zame hannunta tayi "kai Emzee yaushe kuka hadu?" Ta juya zata kuma zama "Ummi wane watttttt" keyyyy haka Emzee yayi waje da ita yaja kofar ya rufe. Mammee tayi dariya tare da goge 'yar kwalla "sannu da kokari Mairama nasan irin halin Alheran. Haka yayata take kusan komai nata ta dauko. Zama da kishiya ne yasa tayi sanyi amma ko shi Mal. Muhammadu ai yayi fama da kiriniya tun farkon haduwarsu har auren." Murmushi Ummi tayi tana sauraron labarin uwarmijinta da bata taba gani ba sai a hoto. Wani falo Emzee ya kai Radhiya ya girgiza kai "ni da kin sani ni na fara fitowa yadda zan iya zaneki son rai. Sam baki kula da kunyar da Ummi take ji ba kike ta takurata da tambaya" "Ayya Emzee ban gani ba bari naje na bata hakuri" tace innocently. "Kin ji ki kuma, shiru ya kamata kiyi ki rinka taimaka mata idan tana son wani abu" Gyada kai tayi sai kuma ta hau murmushi "Amma kai baka yi murna bane? Ni fa na matsu naji ranar haihuwar" Hannunsa ya sakalo a kafadarta yana jinjina wautarta "Addata ta kaina ina tausayin Hamma nasan ya gamu da shiririta" "Kai dalla me ka sani, Hammana yana ji dani sosai don wallahi jiyama da dadd......" A gigice Emzee ya fara neman kofar fita daga falon yana cewa "na shiga uku don Allah kada ki fada" Ya kai bakin kofa tace "kai wank...." "Sai anjima" yace da sauri ya fita yana tunanin ko dai wanka za ta ce yayi mata tunda tace yana ji da ita. Tabe baki tayi da ya fita din tace "meye don na fada maka ya tayani wanke-wanke ba abin farincikinka bane ace mijin yayarka yana sonta" wani tunani ne ya darsu a zuciyarta bata san lokacin da ta kwashe da dariya ba harda rike ciki "shege Emzee ko dai yasan me akeyi ne...tabdi gara ya nemo mata mu kaishi." Ta nufi part din 'yan matan gidan inda su Zahra suke ta kuma ganin Emzee da tiyo yana wanke fuska ta zuci tace sumumu kasau wannan idan kayi aure matarka ta shiga dubu da soyayya. Cikin 'yan uwata ta shige tare dasu Fauziyya ana mata tsiya bakin ya kasa ramawa. Bayan isha Awwab ya kirata wai tazo su tafi ta rasa yadda zata yi. Can sai ga Tante Nasara ta kirata suka fita har wajen gate sannan ta daga waya ta kira Yousuf. Da faransanci tace masa, "Ga kanwarka nan ka kaiwa mijinta kafin Zainab ta cinyeni" Ya kwashe da dariya "Mam ina sonki wallah" "Da na kyaleka ka boye matarka ko? Zamu hadu a gida ne sai ka gaya min wanda ya baka shawarar satar amarya" ta ce tana dariya. Tare suke da Awwab a kofar gidan Alh Ghoumar ko minti biyu ba'ayi ba suka iso. Baya Awwab ya bude mata ta shiga ta gaishe da Yousuf tana tambayarsa Arifah yace wurinta zasu je. Wani katafaren hotel ne da yake cikin jerin manya a kasar baki daya suka shiga. Hawa na bakwai Yousuf ya bude mata wani daki bayan ya kira Arifah yace tare suke sannan suka juyo shi da Awwab zasu siyo musu abinci. Radhiya da Arifah suka rungume junansu suna murna. Arifah ke fada mata yadda daga Yousuf zai kaita gida ranar dinner suka kare a hotel. Radhiya tayi ta dariya suka koma hirar sabuwar rayuwarsu. Arifah ta girmi Radhiya sannan ta fita wayewa musamman ta wannan fanin. Shawarwari ta shiga bata yadda zata ajiye kunya ta bawa mijinta kulawar da ta dace. "Kinga ba mazauni bane idan ba kya kulawa dashi yanzun nan wata zata rabaki dashi" "Dena fada Sis" tace da rawar murya bata fatan ganin wannan rana. Ko zaiyi mata kishiya bata burin ace saboda gazawarta ne sai dai hali na rayuwa. Goma da rabi suka dawo Yousuf ya shigo yace mijinta na jiranta a waje. Tana fitowa ta fada jikinsa sai da yayi mamaki kuma ya nuna jindadinsa sosai ita kuwa sabon karatun Arifah ta dauka. "Miss me?" Yace yana mata jagora zuwa nasu dakin. "So much Hammana" "Love me?" "For as long as I live" tace tana kashe masa ido. Bude dakin yayi dama ya ajiye musu kayansu ya rungumeta "ki rinka sassauta min babyna wannan sabon salon naki zai hanani abin arziki" Zama yayi ta dare cinyarsa abinta tana magana cikin jan rai "wane abin arziki da za kayi?" "Uhmm wai da yau dai na bar amarya ta huta gajiya...to amma" Tana ganin abin zaiyi gaba ta tashi tana raba idanu "kayi hakuri Hammana ji nayi ance wai haka yana kara kauna" Guje-guje suke a dakin taki bari ya kamata yana cewa "kaunar zan nuna miki ai wadda ta karu" "Chèri bani da lafiya fa" "Harda karyar ciwo kike yi?" Ta girgiza kai tana shagwabe masa "a'a lafiyata kalau ni dai kayi hakuri" "Na hakura janbaki kawai zaki bani..." Daga inda take ta taho gareshi da saurinta ta hade bakinsu "ba kayi bayani bane tun dazu kasa ina wani tunanin" "Tunanin naki ma zai tabbata kema kin sani" ********** Washegari tun shabiyu suke tsakanin gidajen kawunan nasu ita da Arifah wadda aka kawo officially. Sai yamma aka yi wasan hawan rakuma a wani babban fili inda amare da angwaye kai harma su Ummi da Daada suka yi shigar gargajiya ta 'yan kabilar tamasheq. Yousuf da Awwab sun sha rawani buzaye sak. Radhiya da Arifah kuma nasu kayan harda sarkoki, abin hannu, na gashi da na hanci duk an makala musu sunyi kyau sosai. Kowacce amarya angonta ya taimaka mata ta hau rakumi su na rike da akalarsa an rufe rabin fuskar amaren suka zagaya wurin dasu ana ta daukar hoto. Salame tayi kallo ta ga abin mamaki a zuri'ar dangin mijin Mairaman da ta wulakanta. Kannen Halifa da matar Alh Salisu sun zo kai kace sun fita matsayi a wurin saboda yadda ta zubar da mutumcinta a baya. Ana tafawa amare da angwaye ance suyi tsere akan rakuman Emzee ya kalli Addarsa da mijinta ya zauna a bayanta ya rike linzamin rakumin da suke kai ya kalli Rahima da take kallonsu itama abin yana burgeta ya ce "nima in zo in samarwa kaina buzuwa ko ma hau rakumi da bikinmu" A can gefe take zaune mutane duk anyi gaba kallon tsere shine ya biyota don kawai ya bata haushi. Wani matashi kyakkyawan gaske cikin jikokin Alh Sidi ta nuna masa duk da zafin kalamanta tana murmushi "Ya Emzee to ko muma a hada namu bikin ne? Ka ga Aman yace muna komawa zai zo wurin Ummi" Hadari ma yafi fuskar Emzee kyan gani ya ce "yazo yayi mata me?" "Maganar aure ce don yace ba da wasa yake ba" ta yi masa wani dan banzan murmushi da ya daure masa zuciya. "Saboda an rasa mazajen aure a Nigeria daga zuwanki kwana daya a nan za ki ce kunyi maganar aure da wani" ya ce yana huci. Kwafa tayi a zuci tana jindadin ko ma fushin me yake da ita bai dena sonta ba "Abin ne yazo mana a bazata" "To bari kiji in fada miki indai Aman ne yana yana shaye-shaye ah to sai ki nemi wani" Hannuwanta ta rungume tana kallon saitin Aman din "sai inyi masa addu'a Ya Emzee yanzu ba'a gudun mutum don hali taimaka masa ake ya chanja" Bai san ya soma fada ba yace "inji uban wa? So kike ya rinka dukanki a gida? Ke wai da wane yare ma kuka magana bayan bai iya hausa ba" Rahima ta dake tayi murmushin da ya sake kawata fuskarta "ko babu yare mun fahimci juna...Ya Allah Ka bani...." Kishi tuni ya rufe masa idanu yace "Shut up, wallahi kika ce Ya baki Aman sai na tattakaki a wurin nan" Ranta ya soma suya saboda bacin rai "Sai na fada din...Allah Ka " Hannu ya daga zai mareta Mairama cikin bacin rai duk da bata san me ya hadasu ba amma ihunsa da daga hannunsa gareta ya matukar bata haushi. "Muhammad kana hauka ne?" Ta daka masa tsawa. Daga bayanta Salame ce ita kuma rashin ganin sanyin idaniyarta Rahima Idris Sumaila ne ya kawota wurin. Da sauri ta je ta kama hannun Rahiman wanda idonta ko gezau sai tarin ajiyar zuciya da take saukewa. Ummi ta damki hannun Emzee saboda bata taba ganinsa haka ba dayake filin a gefen gidan Alh Ghoumar ne tattaki kadan suka shiga gidan. Dakin uwargidansa ta wuce dashi suna zuwa ta rufe kofar ta juyo a fusace. "Karami baka taba yi min abinda ya sosa min rai kwatankwacin na yau ba saboda haka kafin nayi maka hukunci ka bude baki ka fada min me ya hadaka da Rahima har kake tunanin idan ka mareta zamu wanye lafiya" Salame lokacin tana rike da hannun Rahima ta kama hannun kofar za ta bude Rahima ta hanata tana girgiza kai. Itama ta gaji so take ta san me tayi masa. Wannan wahalar soyayya har ina kullum yana azabtar mata da zuciya. Ga mamakin Ummi sai kawai Emzee ya saka mata kuka ya dora kansa a kafadarta. Rahima na jin sautin kukansa itama ta fara nata yayin da jikin Salame yayi sanyi. Sai da yayi mai isarsa yana cije lebe yace "Ummi I love her so much, wallahi Ummi Rahima nake son aure kamar zanyi hauka saboda son da nake mata" Salame ta yiwa Rahima kallon tambaya wanda ita kuma taji furucinsa a bazata duba da yadda yake kyararta yanzu. Dariyar Ummin suka ji. Fuskarta tana nuni da zallar farinciki ta dora hannu akan fuskarsa "Allah sarki Zayyan Turetana ya girma, to waye ya fada maka ana dukan mace idan ana sonta? Ko tace bata son karamin sojan Mairama ne?" Takaici ya kama shi "Ummi yaya kike dariya this is not funny at all. Rahima fa nake nufi. Rahiman Gwaggo Salame wadda ta makantaki tsahon shekara goma" Innalillahi wa inna ilaihi raji'un Rahima da Salame suka fada a tare jikinsu na rawa. Salame bata son Rahima taji zancen nan da wuri sannan a yau a yanzu taji wata katuwar nadama ta lullubeta a gaban 'yar cikinta. Emzee ya soma ruwan hawaye "Ummi ni bansan 'yar Gwaggo Salame bace da bazan fara sonta ba, bakiji zuciyata ba Ummi ki rinka yi min addu'a Allah Ya yaye min. Ta yaya zan so 'yar wadda bata son mahaifiyata kullum burinta kiyi kuka" Mairama ma sai ta fashe da kuka Emzee ya rungume mahaifiyarsa yana jin dacin zuciya da rashin adalcinta na son Rahima. Hawaye na kwaranya a idanun Mairama tana share masa nasa ta ce "Karami idan kana son kanwarka nayi maka izini ka manta da komai ka nemi soyayyarta" "A'a" ya shiga girgiza kai. Kuka take sosai tace "Lallai ashe baka da wayo ban sani ba. Abinda Adda Salame tayi min ALKHAIRI NE babba a gareni. Yau da banyi wannan makantar ba maimakon murna Karami zan shiga rudani mara misaltuwa ne akan dawowar mahaifinku. Ko kasan cewa ko banyi auren soyayya ba dole zan nemi mijin aure saboda inganta rayuwarka da ta yayarka? Da yanzu ina da 'ya'ya da wani mutumin ba Zayyan Tureta ba fa Karami. Kana tsammanin duk wanda na aura ga zuri'a tsakaninmu zan iya barinshi kai tsaye saboda naku mahaifin ne? Kasan girman dake tattare da aure irin wannan kuwa. Ga mijin da nake so ya dawo amma wani yayi mana shamaki. Kila Allah Ya jarabceni da son sa fiye da babanku" Ta sake fashewa da kuka " nayi imani da yanzu mahaifinku yana cikin kuncin rayuwa duk da tarin arzikin da ya samu. Ciki ne dani Karami da ta ina kake tunanin Umminka zata sami wani rabon ta rabu da wani mijin da yara ta dawowa tsohon mijinta...ka duba girman wannan alkhairi da Allah Ya bamu ka gode Masa domin ni wannan kadai ya isheni dalilin da na yafewa Addata" Bai taba tunani makamancin wannan ba amma duk abinda ta fada masa gaskiya ne. Kukansu suka yi sosai sannan yace "duk da haka Ummina bazan iya ba. Ki yi min addu'a zan sami wata in kawo miki" Salame da Rahima sunji komai haka Radhiya wadda fitsari ya koro tun tsayuwar su Rahima a wurin take bayansu tana jin komai. Ganinta kawai suka yi ta wucesu ya bude kofar dakin ta shige tsakanin Ummi da Karami suna hawaye. Rahima kuwa da sauri ta matsa yadda babu mai hangosu daga cikin dakin ta shiga na kusa dashi da bata san ko na waye ba tana fitar da numfashi da kyar ta rike kirjinta tana dannawa. Salame ta gigice ta dafata "Rahimata yaya? Me ya sameki" A matukar raunane ta kalli Salamen idonta babu hawaye ta ce "Umma, don Allah nima ki soni kamar yadda Ummi ke son su Adda Radhiya. Wallahi Umma idan kika soni ko...uhmm nayi miki alkawarin zan zama 'ya tagari a wurinki ko banyi kudi ba zanyi miki biyayya." Magana take kamar zautacciya saboda tsananin tashin hankali ace mahaifiyarta, hasken rayuwarta, inuwar jindadinta ta aikata mummunan abu irin wannan. Salame sai hawayen mai cikea nadama sosai taji Rahiman ta kama hannunta "Umma nima kiyi min addu'a don wallahi ina son Ya Emzee...kinji kirjina Umma yana min zafi saboda na rabu da shi. Bazan iya zama da shi ba har abada saboda zaiyi ta kallonmu da laifin da muka yiwa Ummi" Kukan Salame ya dadu ta rungume Rahima sosai a jikinta "ba ke kika yi laifin ba nice nayi kuma zan je na nemi yafiyarta." "Duk abinda kika yi nima na dauka Umma. Shi baya gudun Ummi sai ni zan gujeki....Allah Ya kiyaye" Salame ta dago kan Rahima ta ce "kiyi kuka Rahimata kiji sanyi a ranki. Idan Mairama tace sai na kwanta na bata hakuri sannan zata yarda Karami ya aureki zanyi...Rahimata kiyi hakuri kullum kuka nake sakaki akan son zuciyata" Mikewa Rahima tayi harda karfin halin murmushi "ba kuka nake ba Umma kizo muje ana tsere mu cigaba da kallo" Kafin Salame ta ankara Rahima ta fita daga dakin ta durkushe a wurin ita kuwa tana kuka mai tsananin taba zuciya...waye ya aiketa kuma me ya rudeta ta rinka lalata rayuwarta da ta iyalinta da hannunta. ******** 💕64💕 *************************** Kasa zama Salame tayi ta tashi bin bayan Rahima sai ganin Mairama tayi tana dube dube. Ita take nema saboda Radhiya ta fada mata cewa sun ji komai. Daurewa tayi ta saki fuska ta nunawa Salamen kofar dakin tana so ta shiga su yi magana. Ita yanzu neman sulhu take yi saboda yadda damuwar Rahima ta zame mata kamar an ajiye mata dutsen dala a zuciya. Su na shiga kuwa ta juyo tana hada hannuwa ga idanunta sunyi ja sosai ta ce "Mairama nayi miki ba daidai ba nima na sani. Ba ke kadai ba duk wanda ya rabeni na cutar dashi na cuci kaina kuma, amma ki yiwa Allah da ManzonSa kada Rahimata ta biya bashin da ba ita taci ba" Mairama tana iya ganin gaskiyar maganganun Salame. Idan ma ba ta tuba bane don girman laifinta kallo daya za ka yi mata kasan cewa she is desperate, ta kai kololuwar bukatuwa da neman agaji a wurin wadda ta dade tana farautar farincikinta. "Adda Salame nan ba muhallin wannan maganae bane ki bari mu koma gida" ta ce mata tare da mikewa za ta fita. Da sauri Salame ta tashi ita ma "babu damuwa Abujan zan biki wallahi" Murmushi Mairama tayi ganin cikin lokaci kalilan Salame ta sauya. Za ta bude kofa kenan ta ga hannunta ta riko nata hannun da dan saurinta. "Tsaya dai mu yita da wajewa Mairama kinga a nan wurin...." ta fita ta tsaya daga kofar dakin inda suka tsaya dazu da Rahima "naji komai lokacin da kike fadawa Karami cewa kin yafe min. Kinga an rufe wannan shaftar kada sai mun tafi kice ba haka ba, ni kuma nasan naji da kunnuwana" Guntun tsaki Mairama tayi da dariya, mai hali baya fasa halinsa "tun kafin ki ce komai na riga na yafe miki Adda" Wani abu taji ya sauka daga makoshinta ta saki murmushi korayen hakoran nan su ka bayyana. A take zuciyar Mairama ta soma tashi ta danyu baya. Cikin sigar rainin wayo wadda za ta nuna Salame har kullum Salame ce sai ana mata uzuri ta ce "sai naji kuna zancen ciki kuma? Ina ke ina sake haihuwa an fara girma ga 'ya'ya suna tafiya gidan miji" Idan ta biye mata ba fa shiryawa zasuyi ba sai ma dai a karawa rigimar fetur. Amma ko yaya sai ta dan rama za ta ji dadi. "Soyayyar kenan Adda, ba dare ba rana kullum miji yana dokinka. Indau kuma batun auren Radhiya ne kada wannan ya dameki ni nan harda matar Karami sai mun kara haihuwa" tana fada a zuciyarta tana cewa (Allah Kada ka nuna min wannan bakar rana) Ta sake tabawa Salame inda yake mata kaikayi ta ce "zaki sha aiki kuwa don indai Rahimata ni ta biyo za ki kwatsa 'ya'ya kamar dabino. Za dai kiyi masa maganar ko? Ba yabon kai ba ni ban taba ganin 'ya mai ladabi da biyayyarta ba. Nake fada miki halin Sahabbai ta gado" Ran ta yana baci da maganganun farkon gashi na karshen suna bata dariya shiyasa kawai ta fita tana murmushi da rokawa 'yar uwarta shiriya. ********** Emzee dakin da suka yi masauki ya tafi ya kwanta yana ta juyi ya rasa shawarar da ya kamata ya dauka cikin dimbin shawarwarin da zuciyarsa take bashi akan Rahima. Bari dai su koma gida yayi magana da Daada. A haka gani yake soyayya bata yi masa adalci ba ta kaishi inda baya son zuwa kuma babu alamun za ta fiddo shi nan kusa. Radhiya kuwa da ta fito janyeta akayi za'a cigaba da hotuna jikinta duk babu kwari. Awwab ya kula da yadda tayi zuru-zuru kwalliyar ta goge saboda cabewar da tayi da hawaye sai ta goge kawai shiyasa ganinta haka ya shiga damuwa saboda bata da walwala. Samu yayi ya faki ido saboda yamma da tayi hankalin iyaye yayi nesa dasu ya fitar da ita daga wurin. Rawaninsa ya cire ya nemar musu taxi ko Yousuf bai nema ba suka koma hotel dinsu. A hanya bai ce mata komai ba sai da suka shiga dakinsu ya rage mata kayan jikinta da danginsu sarkoki da sauran kayan adon ya zaunar da ita a gefen gado sannan ya zauna a kasa a gabanta ya dora kafafunta akan cinyarsa yana matsawa a hankali. "Me ya sameki Alheran?" Dama kiris take jira kawai ta fashe masa da kuka. Hankalinsa a tashe ya tashi ya zauna a gefenta ya rungumeta tayi kukan ta gaji. Sai da ya lura numfashinta ya soma dawowa daidai ya sake tambayarta. Da kyar ta iya fada masa abinda ya riga yaji daga wurin Daada lokacin da suka je Sumaila bayan Salame ta daketa. Sai dai yayi matukar kaduwa game da dalilin makantar Ummi da kuma karshen bayanin Radhiyan wanda shine musabbabin kukanta a yanzu. "Hammana ka tuna lokacin da aka ce na hakura da kai saboda kada na bata zumunci?" Ya gyada kai yana tuna lokaci mai daci da ya shude a rayuwarsa. Ya azabtu da rashin cikar burinsa ya kuma ji haushin amincewarta a lokacin taki goya masa baya. Siririyar muryarta da ta dashe saboda kuka ce ta katse shi yaji ta ce, "It was so painful Chèri sai lokacin ma na fara sonka sosai. Yanzu yaya Emzee zai ji? Yana son Rahima ashe kuma yana gudunta saboda Ummi. Emzeee yana da sa abu a rai nasan da wahala yau ya iya bacci" Awwab sakin baki yayi yana kallon ikon Allah. Radhiya ta cigaba da fadin halin da kaninta zai shiga cike da tausayawa. Hade bakin nasa yayi ya ce "yanzu duk wannan hawayen na Emzee ne ba ma Ummi ba?" Tsakaninta da Allah tace "Ummi ai ta yafe nasu ya wuce. Emzee nake maka magana yanzu. He is so hurt yana ganin laifin Rahima a tunaninsa yaudararsa tayi taki fada masa wace mamanta" Jinjina kai ya rinka yi "indai zaki yiwa Emzee wannan kukan ni kuma me zaki yi min idan na kamu da son wata aka rabamu?" "Kace me?" Ta jefa masa tambayar idanunta sun wani kankance tana huci. Dariya ya soma yi mata "cewa nayi fa...ke dai banyi magana ba" "Ya dai fiye maka idan ba haka ba kuma yau babu bacci a dakin nan" ta juya masa keya. Kwanto ta yayi jikinsa "wasa nake yi miki Schatzi don ki saki ranki. Ina jindadi idan naga 'yan uwa suna son juna domin Allah. Keep it up my baby amma fa kada kowa ya kamo matsayina" Sunkuyar da kai tayi tana jin kunya "kowa matsayinsa daban...KAIMA.KA.SANI" "Wanne ne matsayin Awwab?" "The only man in my life" Rungume ta yayi suna shakar kamshin juna daga baya ya tasheta daga kan gadon "muyi wanka idan nayi sallar magrib zan koma wurinsa muyi magana man-to-man. Amma ki sani tun wuri sai na rankwashe shi. Haka kawai ya janyo min dan janbakin da naci burin gogewa idan mun dawo ya bi hawaye ya gudu" Da sauri ta tashi ba shiri ta koma ta zauna. Abu goma da ashirin ke damunta, dama jikin lallaba shi take ga kuma hawa rakumi da tayi dazu ta rinka jin kanta kamar akan kaya. Runtse idanu kawai take yi Awwab dama ya san matsalar yana mata sannu suka yi wanka ta gasa jiki sosai. Ana kiran magrib yace mata za'a kawo abinci takwas da rabi idan ta ci ta yi isha ta kwanta kafin ya dawo. Da kyar ta tsakuri abincin tana idar da sallah bacci mai nauyi ya kwasheta saboda irin gajiya da ciwon jikin da yayi mata rubdugu lokaci guda. Tare da su Daada Awwab yayi sallah ya nemi Ibrahim ya kira masa Emzee. Dawowa yayi yace yana kwance kamar bashi da lafiya kuma yaki bari ya fada a cikin gidan. "Kyale shi muje dakin" Ibrahim sauri yake yaje wurin Zayyana bai shiga dakin ba. Awwab na shiga ya same shi ya hada kai da gwiwa zaune a kasa. Kusa dashi yaje ya zauna yayi irin zaman da yayi suna zaune kusan minti biyar sannan Emzee yace "yaya zanyi Hamma?" Ya tabbatar dole zai ji daga bakin Radhiya kuma abinda ya kawo shi kenan. "Rahima tana sonka?" "A da ba! Ni yanzu ban ma san me ta daukeni ba" ya amsa cikin kunar rai. "Bana jin wannan yarinyar mai nutsuwa da hankali ga karancin shekaru za ta iya amince maka saboda wani mugun nufi. Emzee open your heart and listen to its voice. Me kake so?" Baiyi wani tunani ba yace "Rahima" "Shekarun baya dangina sun rabani da Radhiya a tunaninsu sunyi domin karfafa zumunci sai gashi ya lalace fiye da zato da tsammanin kowa. Idan kana tunanin za ka gujewa Rahima saboda zumunci ne you are making a grave mistake. Emzee aurenka da ita shine abinda zai fi komai saurin gyara abinda yake tsakanin Ummi da yayarta." Da sauri ya dago kai "Allah Hamma?" "Talking from experience" yace da murmushi "da ace tun wancan lokacin na auri Ghazalatu da Radhiya zumuncin iyayenmu da yafi karfi iyaka mata suyi kishi a junansu. Amma da hakan bata samu ba sai da akayi shekara uku su ukun suna jin haushin juna ana rigima mara tushe. Babu wanda nake fadawa amma I hate myself da na zama dalilin faruwar hakan so if you can avoid it please do so" A raunane Emzee yace "ina jin ni fa yanzu ta dena sona ta sami wani" Awwab ya ce "So da wahala yake komawa ki. Kai dai kada kayi wasa da damarka at the same time ka tuna cewa kaima yaro ne ko karatu baka karasa ba. Zanfi so ka gama karatun ka fito da karfinka ka yaki zuciyar Rahima har sai ta amince maka." "To yanzu dai in kyaleta?" "Da zancen soyayya kam ka rabu da ita ka gama karatu itama ta gama secondary. Amma try your best ka tabbatar ka mamaye rayuwarta..." Chuckling Emzee yayi yau fa yana daukar darasi sosai "how?" "Kada ka bari wasu mazan su sami dama. Keep her close, babu zancen soyayya amma ka bata kulawar da ko wani yazo a bayan idonka zata rufe ido ta kore shi batare da ka sani ba ma" Haba Emzee ya rike "Allah Sarki Addata, Hamma ka rinka yi mata a hankali kada son ka yayi mata yawa" Keyarsa Awwab ya talle yana dariya "kai kace ita, iya tace kai ni mai bada shawarar kuma baku damu dani ba" "Daga fadan gaskiya" ya turo baki. "Ladan kukan da ka saka min mata ne...bari na koma na barta ita kadai karshenta ta kasa....." Kofa Emzee ya bude masa da sauri "Allah Ya bamu alkhairi ba sai kace komai ba" ya kara da toshe kunnensa kada ya jiyowa kansa. Awwab ya fita yana dariya sosai ya ce masa "ni dai ka daure ko P.O.P ne kayi sai mu aurar da kai....ga Rahima 'yar karama da ita har ta bani tausayi" Kamar zaiyi kuka ya ce "wayyo Hamma ya na neman fassara ni" "Me kaji nace? Daga cewa 'yar karama to ba karamar bace?" Ya kuma yin dariya. "Wallahi zama da Adda ya fara nunawa a jikinka ni dai sai da safe" Emzee ya bata rai ya rakoshi waje. Tare da su Yousuf suka tafi. Yana zuwa shima kwanciya yayi yana rungume da Radhiyansa. Washegari akayi gagarumar dinner da daddare inda ma'auratan suka yi shigar buzaye su da iyayensu. Da safe kuwa kowa ya kama gabansa. Yousuf da Arifah Hawaii suka wuce honeymoon daga can kuma zasu tafi France inda gidansa yake kusa da na iyayensa. Su Awwab ma a ranar da suka koma washegari bakwai na safe suka tashi zuwa Athens babban birnin Greece zasuyi kwana goma kafin ya koma aiki. Duk wannan abu da akeyi babu wata alama ko kadan da Rahima ke nunawa ta damuwa sai dare yayi ta kwana tana kuka. Sabanin Halifa da yake namiji ita abin ya tsaya mata a rai fiye da kima. Da ciwo matuka ace mahaifiyarka ta cutar da wani, wanin ma kanwarta ta hanyar asiri har tayi shekaru goma babu ido. Ita nata daya ne yanzu baya bambance mata abubuwa amma yaya take ji bare wanda zai ga tsananin duhu na tsayin lokaci. Abu na biyu bai wuce mahaukacin so da tausayin Emzee da take yi ba. Ko kadan bata ganin laifinsa don ya kyamaceta. Uwa tafi karfin wasa. Ita ma bata guji Salame ba duk munin halinta ta yaya shi ba zai tsayawa tasa mahaifiyar ba..mace kamar Ummi mai kyauta da kyautatawa. Bayan dogon tunani da koke koke a boye ta yankewa kanta shawarar hakura dashi har abada. Emzee ba sa'an aurenta bane da kunya ta iya hada ido dashi bayan abinda Ummanta tayi musu. Sai yanzu ma take dada godiya ga Allah da ita ta samu a ido da wayar ba Radhiya ba. Da zasu barta ta koma Sumaila da tafi jindadi ma. A zahirin mu'amalarta da mutanen gidan duk karancin shekarunta ta iya daurewa ta nunawa Ummi bata da matsala. Har daki Ummin ta kirata akan maganar Emzee ta ce mata ko yana sonta bai taba fada ba. Shi kuma yana makaranta bare ya karyata. Satinsu guda da gama biki har an kai Rahima sabuwar makarantarsu anyi sa'a sun barta a SS3 amma Daada yasa an dauko mata lesson teacher wuni suke suna karatu saboda ta ci WAEC tunda bata yi rejistar NECO ba kuma an riga an makara. Ummi ma ta soma zuwa Baze tana kuma samun kulawa sosai daga maigida ran gida Zayyan Tureta. Cikinta mai laulayi ne shiyasa daga makaranta sai daki saboda rashin son kamshin gidan. A yau ana sauran kwanaki hudu su Radhiya su dawo Emzee yayi magana da Awwab wanda yace kada ya manta shawarar da ya bashi game da Rahima. Bayan sun gama hirarsu ne ya tura mata text. Zaune take tana kokarin solving din wani aiki da lesson teacher din ya bata a physics text din ya shigo. Duk a zatonta irin na layin wayan nan ne shiyasa zuciyarta tayi wani irin bugu da ta ga sunan Emzee. Jikinta wata irin rawa ya kama yi ta bude da sauri. (Kanwata kwana biyu boko ya boyeki. Ina fata babu wata matsala a sch din taku. All the best Rahima, Allah Ya bada sa'a. Yayanki) Ta karanta wannan gajeren text yafi sau shurin masaki. Dama malamin nata ya tafi aikin ta zauna yi sai kuma ta kasa fahimtar komai dole ta tashi ta shiga ciki. Wayarta a hannu lokaci lokaci sai ta duba ta kuma karantawa duk da tana kwabar zuciyarta da take jinya har yanzu. Da safe ma tana shirin tafiya makaranta wani text din ya kuma shigowa shima dai addu'a ce yake yi mata da fatan alkhairi. Baiwar Allah sai ta koma ruwa tsundum dan karfin halin nata ya guje mata. Haka dai akayi karatun ta dawo gida. Daga bakin kofa take jin muryar Salame tana cewa maiaikin nan gidan kanwarta ne ita bazata ci dan wake ba a dafa mata sabon abinci. "Banda ta raina ni ai tasan yau zan taho amma shine da zata tafi makarantar bata bar muku sallahun dafa min komai ba sai danwake? Ko ki dauke shi ko na yanko masa tsinuwa dashi da hannun da ya tsumbula shi a ruwan zafi" A kidime yarinyar tace "Ta fada mana zaki zo amma kinfi son danwake" "Da kenan! Amma Yasin bazan zo Abuja inci danwake ba kamar wadda iyaye suka cewa jeki kya gani" "Harda farfesun da salad din ma na kwashe?" Mai aikin ta tambaya a tsorace. Salame ba kunya ta karbe tray din "kece bakiyi bayani ba, cha nake mai da yaji zaku bani." Da gudu-gudu Rahima ta shigo ga takaici ga dariya ta fada jikinta. "Umma?" Salame ta washere baki kamar gonar auduga ta rungumota "Rahimata...." Allah Sarki zuciya na wuya sai kawai ta soma kuka tana kankame a jikin mahaifiya mai dadi ko da kuwa ta buzuzu ce. Da kyar Salame ta samu Alh Indararo ya barta ta taho sai da tayi karyar zuwa zata yi suyi magana akan yaran da za ta basu. Malamijo kuwa cewa yayi indai tasan rigima ce za ta kawota Abuja bai yafe mata ba idan ta je. Damuwa ce fal a zuciyarta akan Rahima. Ita kanta tana mamakin yadda ta damu da yarinyar sosai. Daga baya ta fahimci dama can tana son abarta wasu abubuwan ta saka a gaba kawai. Wannan kuka na Rahima ya tada mata hankali fiye da tunani ta kama hannunta zuwa dakin baki da yake kasa. "Rahima wani abin kika sake ji nayi?" Ta tambayeta a tsorace tana fata yanzu kuma ba labarin ta taba son Zayyan Tureta bane ya fito. Girgiza kai tayi hawayenta yana karuwa cikin rawar murya ta ce "Umma nace ki rinka yi min addu'a Allah Ya cire min Ya Emzee daga raina Umma ba kya yi...Umma ko sau daya kiyi min addu'a a rayuwata" ta durkushe a kasa tana matsanancin kuka. "Ina miki addu'a duk sallah Rahimata, idan ban miki ba wa zanyiwa bayan duk abinda naja miki" Salame ji tayi ta tsani kanta tana Allah wadai da son zuciya. Ita bata girbe da hannunta ba 'yar da take jin kunya ita ce take mata dakon wahala. A wannan lokacin Mairama ta nufo dakin saboda an sanar da ita zuwan Salame. Nan ta jiyo kukan Rahima ta bude kofar da sauri sai ta ga sabanin abinda ta zata wato tana dukanta rungumeta tayi. "To me yasa bana jin komai, kirjina kullum ciwo yake. Ki koma gida dani ina kunyar Ummi, ina kunyar Daada dasu Adda Radhiya" Fuska sharbe da hawaye Salame take shafa bayan Rahima "kiyi hakuri zan roki Mairama na santa da hakuri za ta duba lamarinki tunda tana sonki" Rahima sai girgiza kai take yi "a'a Umma bazan taba auren Ya Emzee ba ko...." "Ya isa haka Rahima zo ki fita" Mairama ta yi mata tsawa cikin bacin rai "ina zaune da ke ina bibiyar me ya sameki ni kin kasa fada min saboda ni baki daukeni uwa ba?" "Ba haka bane Ummi kiyi hakuri" tace tana dawowa kusa da ita tana wani irin kuka. Rungumeta Mairama tayi sannan ta ce "Karami ya taba cewa yana sonki?" Kai ta daga kawai jiki na rawa. Wannan wane irin so ne mai cin ruhi da ba za ta iya hakura kamar yadda take son yi ba. Cikin kulawa ta sassauta muryarta "indai ni na haifi Zayyan in sha Allahu sai kin amsa sunan matarsa tunda shi ya fara nemanki" "Ummi a'a" tace saboda sanin da tayi cewa yanzu baya sonta. Salame ta galla mata harara ga hawaye har yanzu "ke kaniyarki, ku ji min yarinya ana baki kina kin karba" Mairama murmushi tayi sannan ta ce "Kina so muyi fada ne?" "A'a" "To kada na sake jin zancen me ya hadani da Addata a bakinki ko na 'yan uwanki sai na saba muku. Babu ruwanku tare kuka ganmu. Karami kuma ki tattara shi ki zuba a kwandon shara ki fuskanci karatunki sai ya nemeki da kansa. Akwai wani namiji da ya isa ya ja wa RAHIMATA aji ne" ta kalli Salame da jin baki taji me zata ce. "Na fada miki Mairama ba dai hakuri ba ke dai barta da zuciya kamar kuturwa" cewar Salame tana fyace hanci da mayafinta. Rahima tayi murmushi ta ce "kai Umma" Mairama tayi 'yar dariya ta ce "Kin dai ga yadda nake hakuri da ita ku ma sai kuyi ta yi. Kiyi wanka ki ci abinci. Yau ranar zuwan malamin islamiyyar ne ko na lesson?" "Lesson ne" "Kici ki kwanta zan kira shi nace ya bari sai gobe....idan na sake ganin hawayenki akan wata damuwar da ba taki ba ni da ke ne" Fita Mairama tayi Salame ta bi bayanta da sassarfa. Kamar ba ta ji ta ba sai da ta shiga dakinta itama ta shigo kawai ta durkusa a gabanta tana kuka. Itama Mairaman kuka ta saka tana tsaye Salame na durkushe tana yinsa mai cin rai da zuciya abin tausayi. Lallai duniya mai yayi duniya juyi juyi yau ita Salame Ali ita ce durkushe a gaban Mairama Ali tana kuka irin wannan "Ki gafarceni Mairama wallahi ban kyauta ba, soyayya ba hauka bace ni ban san me yake damuna ba ko tunanin me nake har na rinka yi miki irin wannan diban albarka. Da gaskiyar mijinki hassada na dorawa zuciyata gashi ina nan jiya e-yau. Don Allah ko bayan raina Mairama ki aurawa Karama Rahima ko ta sami saukin cutarwar da nayi mata. Kinga ni ce da laifin amma ita ke da wahala banda haka ina ita ina wata soyayya mai zafi haka..." "Adda ki tashi ki zauna muyi magana" "Idan kinga na zauna to yafe min kika yi" "Ke fa kika ce mun wuce wannan matakin tun a Nijar" inji Mairama "Lokacin ma wasa ne nake yi mutum baya wasa da rokon gafara." Salame ta sake kwantar da kai. "Komai ya wuce a wurina, dama can ke kika jawo muna zaman zamanmu kika canja hali. Allah Ya kara mana hadin kai" Wani kallo mai cike da girmamawa da mutuntawa take yiwa kanwarta. Idan tana da sauran shakku na cewa Mairama tayi mata fintinkau a komai ya kau a yanzu. Za ta iya rantsewa cewa idan ita ce Mairama sai ta baro mata rashin mutumci kwando kwando kafin ta hakura. Halinsu ba daya ba haka nan zuciyarsu da bambanci. Kila shiyasa ita ta kare a kasa marainiyar wayonta ta haye ta barta. "Nagode, nagode, nagode...amma nace ba, maganar Karami da Rahimata za ki sanar da maigidan naki da wuri ko" Dariya ta baiwa Mairama "Adda Salame kenan maganar aure ai babu ita?" "Cewa zakiyi baki yafe min ba!" Salame ta saka sabon kuka. Zaunar da ita Mairama tayi don ta gaji da tsayuwar ta soma magana a nutse "Adda daga Karami har Rahima yara ne masu karancin shekaru. Shi yanzu yana ashirin da biyu da watanni ita ko sha bakwai bata rufa ba haka ne?" "Eh to amma auren wuri ba yafi ba ko don fitintinun zamani" "Nima zanfi son haka amma shi da yake namiji bai gama karatu ba. Ita ma bana so a yanke mata ba hanzari muke yi ba. Wannan soyayyar da suke yiwa juna wuta-wuta kamar yaki harda kuruciyar da take cinsu su duka da kuma isharar Allah akanmu ni da ke. Mu barsu su kammala, su kara nutsuwa su sake hankali sai mu ga abinda Allah zaiyi. Kada kiyi min mummunar fassara duk duniya babu matan da Karami zai kawo min a matsayin suruka nayi farinciki sama da Rahima ko Zayyana saboda su ne 'ya'yana. To Alhamdulillahi ba tare da wata dabara daga garemu ba sun daidaita kansu. Mu kara hakuri kadan wannan hayakin ya sauka hankali ya game jikinsu musamman shi namiji da ragamar gida za ta hau kansa" Kallonta Salame take cike da sha'awa tana murmushi "lallai boko ya ratsaki Mairama ji yadda kike fito da bayani mai ma'ana da kuma hangen nesa. Hakan yayi min wallahi dama burina ni dai in hada zuri'a dake duk tsiya ko albarkacin jikoki sai kin yafe min" ta kare da murmushi. Sai da Mairama ta dara don tasan tsokanarta take yi "zan yiwa Rahiman bayani da kaina ba rabasu zanyi ba amma a maida kai wurin karatu. Babban tashin hankalinta kuma kinsan akan yadda kike yi ma ta ne ina rokon arziki ki gyara ko zamu ji dadi" Dofana mazaunanta tayi a kusa da kanwarta sai ta ga bata kyareta ba sannan ta saki jiki "Mun riga mun shirya da ita fa...zancen gaskiya ma ina ganin laifinku a yadda na canza ke da Malamijo" "Da muka yi me?" "Tunda abin nan yake ta faruwa da kun sani kun karbo min taimako ko da na ruqiya ne don jikina yana bani me yiwuwa shafar jinnu ke damuna" Mairama ta kwashe da dariya "idan jinnu basu shafeki ba ai wannan annakiyar kazantar za ta shafeki. Adda ji hakoranki don Allah koraye babu kyaun gani. Na san da wuya idan Alh Indararo yana iya kusantar wannan bakin naki" Salame ta rike haba "su Mairama babu ranar girma, kada dai kice min kuna nan kun daddangwalar bakunan juna ke da mijinki" Dariyar da Mairama tayi ta jima rabonta da irinta "wai dangwalar baki...to naji ko ma me kike kiranshi ku ba kwa yi ne?" "Allah Ya agajeni ni ko magana yake min kaina baya matsowa kusa da bakinsa mai dan uban wari" "Wai Kura ce za ta ce da Kare maye, ke ma me zai kawo shi gaban naki. Ina ku ka baro brush da makilin?" "Tabbb..mu sami na kai wa bakin salati dai shine magana." Tashi tayi tana murza hannuwa "yanzu dai tunda hankalinki ya kwanata Salame ta dawo gareki a taimaka a bani abinci" "Au ni kadai ce hankalina ya kwanta? Shikenan jeki abinki kowa yayi ta kansa" "Daga wasa sai ki hade rai kamar zawo" Salame ta ce tana murmushi. Babu abinda zai faranta mata yanzu kuma sama da ganin ko yaya ita da Mairama sun fahimci juna. Wata dariyar Mairama tayi kawai tana cewa ta kula kazanta ta sami mazauni a tattare da yayarta. Abinci Salame taje taci ita kuma Mairama tayi wanka ta sauko kasan. Salame dai kasa sakin jiki tayi duk yadda ta so saboda wani girma da kwarjini da Mairama ta kara a idonta. Masu aiki take gani su na rawar jikin cika umarninta kuma ba wai don ita din ta kasance mai tsanantawa ba. Ko kadan, tsabar iya mu'amala da nuna musu cewa su da ita abu guda ne ya janyo hakan. Nasiha da jan kunnen da ta yiwa Rahima ya sake ninninka girmanta a idon Salame. Cikin hikima da sanin ya kamata take nuna mata ta ajiye komai tayi karatu. Ga mamakin Salame har ji tayi tana cewa, "Karami ba autan maza bane kada ki bari tun ba ku daidaita ba ya san cewa kina son shi haka. Kuma kada ki sakawa zuciyarki lallai sai shi, rayuwa bata da tabbas, kiyi kokarin inganta rayuwarki da ta iyayenki da kuruciyarki" Kunya sosai Rahima ta ji. Sai yanzu da maganganun Ummi ta soma rarrabe abubuwa ba kamar da ba da ta afkawa soyayya da ka babu wani ilimin sanin duniya. Ummi uwa ce ta gari kuma mace da ta san girman zumunci. Ba don zumuncin ba Allah kadai Ya san irin rayuwar da za tayi da 'ya'yanta. Mutane da dama sun taimaka mata albarkacin zumunci ba ta da dalilin kin kwatanta alkhairi bayan itama anyi mata. Da Zayyan ya dawo Salame har kasa ta durkusa ta gaishe shi ta kuma roki gafararsa wannan karon da zuciya daya take yi saboda duk abinda zai kawo hawaye a idanun Rahima gudunsa take. Kwananta biyu ta tattara ta koma da shatara ta arziki daga wurin Mairama. Rayuwa bata da tabbas, yadda ka dauketa haka za ta zo maka. Rayuwarsu ta cigaba da tafiya gidan Mami shiru da ga ita sai Zayyana su Fauziyya an koma Katsina, Zahra kuma rana daya ma su ka tashi da su Awwab sun koma Germany. Ibrahim yana Kano, Emzee a Kaduna kowa ya cigaba da harkokinsa. *********** Zaune suke a cikin jirgi kamar Radhiya za ta shige kirjinsa ta dora kan ta a kafadar Awwab, yatsun hannuwansu na sarke da juna yana yi mata rada a kunne tana dariya. Dago kai tayi tana tura baki "ka ga bana so" "Ni ina so baby, ina jira ki kirani bayan na koma ki tabbatar min kawai" Gabadaya zancen ma kunya yake bata so take a canja wani. Ta yaya zaiyi ta cewa wai yana jin tana da ciki zai fara siyayyar haihuwa tun yanzu. "Wane suna kike son mu saka kinsan tun yanzu zamu fara shawara" "Kai Hamma wai me yasa kake min haka ne. Ni wallahi kunyarka nake ji" Ido ya bude yana mata wani irin kallo "Really? Da gaske kunyata kike ji with all the......" "Shhhh" tayi saurin rufe masa baki da hannunta ya rinka cizon cikin hannun sai da ta dauke tana kai masa duka. "Ke ce da wani abu za ki hanani fadar gaskiya" "Ni dai mu bar zancen nan ko na canja seat" Alamun zip ya yiwa bakinsa ya koma ya narke mata jiki tana biye masa suna hirarsu ta masoya. Kwanaki goman da su kayi a Greece sun kafa tarihi a rayuwarsu domin kuwa sunyi su ne cikin kulawa da tsantsar kaunar juna. Kowa kokarin zarta dayan yake wurin kyautatawa ga shakuwarsu ta kara karfi kusan komai tare suke yi. Wani lokacin sai su cinye rabin dare suna hira kawai da bawa juna labarai. Yawo kuwa anyi kamar kafafu zasu tsinke. Shiru Radhiya ta ji Awwab ya dena magana ashe bacci ne ya kwashe shi. So da tausayinsa take ji saboda idan sun sauka a Abuja yau jibi da yamma zai tafi. Sabon da su ka yi da juna a kwanakin su tare yayi karfin da ba karamin ji zasuyi a jikinsu ba idan sun rabu. Gashi zaiyi a kalla sati uku ko hudu kafin ya sami kansa. Saboda tsarin aikin nasu mutum zaiyi aiki na wasu awanni ne masu yawa sannan ya sami break wani ya karba. Haka suke yi shiyasa su kan dauki kwanaki ko watanni batare da iyalansu ba. Kullum suna tare kamar cingam idan tayi nesa dashi bata san yadda zasu ji ba. Hannunsa ta kara damkewa a hankali itama bacci yayi gaba da ita. Sanarwar saukar jirgin cikin mintuna kalilan ne ya tashesu. Radhiya ta gyara fuskarta ta gyarawa Awwab wuyan rigarsa da ya lankwashe su ka jira saukar jirgin. Dreban Daddy ne yazo daukarsu tare da Zayyana da Rahima wadanda su ka kankame Radhiya suna murna. Anje shiga mota Awwab ya ja Radhiya gefe. "Schatzi ki rage tsallen nan kada ki taba lafiyar ajiyata" yayi maganar yana kallon saitin cikinta. Dariya ta yi "Na shiga dari Hammana idan ya zama gaske za ka barni na sakata na wala kuwa?" "Sosai ma, indai ba zai dami babyna ba" Gidan Mami su ka wuce Radhiya ta sami kanta da matsananciyar jin kunyarta kuwa. Mami ta taho da murnarta za ta rungumeta ta zube a kasa tana kwasar gaisuwa. "Kaniyarki Radhiya, surukar ki na can Maitama" tayi nuni da kofar gidan tana nufin Ummi "zo nan in gani idan ya kula min da ke yadda ya kamata" "Mami ni zaki fara dubawa ko tana kula dani" Awwab yace yana zama a hannun kujera. "Waye yake ta katon mutum kamar ka? Zayyana dauko musu mukullinsu aje a huta abincinku ma yana can" Duk wani nauyi ya kama Radhiya da kyar ta iya tashi bayan Mami ta matsa mata. Suna fita su ka shiga gidan Mama Radhiya ta dauki DK yaron sai girma yake karawa ga wayo. Da murna ta rungume Maman ita kuwa baki yaki rufuwa ganin 'ya'yan nata sunyi shar da su gwanin ban sha'awa. Abincin da ta dafa musu ita ma su Rahima sun kai musu nasu gidan. Awwab ne ya bude kofar yana rike da hannunta "finally we are home...shiga da kafar dama kuma kiyi addu'a" Umarninsa ta bi su ka shiga tare. Numfashinta ne ya tsaya a bakinta saboda irin dukiyar da mahaifinta ya narkar a falon kawai. Awwab ne ya ke janta sai da su ka shiga kitchen, store da dakunan gidan guda uku wanda daya da yafi kusa da kofa falo aka maidawa Awwab saboda baki maza. Wanka da salloli su ka gabatar sannan aka ci abinci. Ranar kafin tara sun kwanta jiki kamar anyi musu duka. Washegari ma kafin fa dora komai an kawo daga gidajen biyu shiyasa ba ta dafa komai ba. Gidan Mami da Mama suka je su kai musu tsarabarsu sannan su ka wuce gidan Ummi. Daada baki yaki rufuwa ya ga Alheran dinsa ta kara kyau ta ciko. "Awwab me kake bata ne?" Kunya ta kama Awwab ya sunkuyar da kai. Ummi tana ta jansa da hira sai ya kasa sakin jikinsa. Radhiya ta rinka masa dariya saboda itama sai da ya tsokaneta wai ta gama hada shi da jambaki ta kasa kallon Mami. Ya san dariyar ta meye shiyasa ya rinka harararta. Falon sama su ka koma ita da Ummi ta dame ta da tambayar wai don Allah Yaushe za ta haihu. "Wai ke ba kya jin kunya ne? Da girmanki kinyi aure mamanki za ta haihu kamata yayi ko maganar kika ji ki gudu" cewar Ummi Wata jaka mai kyau irin ta babies Radhiya ta daukowa tana cewa "Humm uhmm...da ga wannan ma ki haifo wani ina so ni dai" "Allah Ya tsareni ke dai kuje kuyi mun bar muku a haifa mu goya" Abinka da sarauniyar shirme budar bakin Radhiya sai cewa tayi "Kinsan Hamma yanzu kullum addu'a yake wai Allah yasa ina....." tunowa tayi da tabargazar da za ta tafka ta tashi da gudu "na shiga ukuna Ummi baki ji ba ko" Mairama dai dafe kai tayi sai da ta ji alamun ta sauka kasa tayi murmushi. Ance hali zanin dutse gara ta dena damun kanta da yawan damuwa idan tayi wani shirmen. Dadinta daya yadda Awwab yake sonta a hakan ta. Allah Ya kara musu zaman lafiya da fahimtar juna tace a zuci. Jakar ta dauka baka ce 'yar madaidaiciya mai kyau ta farke ledar da aka nadeta. Gefe ga aljihu hudu biyu a gaba da baya sai kuma wurin zura feeder da karamin flask. Da dan nauyinta ta bude sai da taji kwalla. Kaya ne a jere an ninke suna wani irin kamshi a sama da 'yar takarda ta rubuta (welcome to the world baby Tureta). Overall ce fara da farar hula na auduga masu bala'ain laushi. Sai vest da pant mai zebra stripes. Da wasu unisex kayan babies guda uku, tawul din wanka, shawl yellow shima mai laushi amma ba na sakar kulu ba. Sai feeder, siririn flask da kayan wanka harda baby perfume. Ummi ta rinka murmushi tana yiwa Radhiyanta da Emzee addu'a. Shima kullum idan ya kira sai yace Ummi jikinki babu matsala ko? Ba zai fito kai tsaye yace ciki bane wai shi kunya. Idan tace lafiya sai yace Allah Ya kaimu lafiya. Tana nan Daada ya sameta ta nuna masa. "To ai tunda ta saya in sha Allah da ita zamu je haihuwar" "Da kai za'a?" "In sha Allah" ya bata amsa. Tare su ka sauko yiwa Awwab sallama sun ce sun yafe masa zuwa gobe. Mami tayi musu tayin abinci da su ka koma amma Awwab ya rufe ido yace na Radhiya zai ci. Murmushi tayi "kinyi girkin ne Radhiya?" Kai a kasa tace "banyi ba Mami" "To kaji sai ku dauka a nan a daren nan za ka takurawa 'yata" "Haba Mami gobe fa zan tafi banci abincinta ba kuma" ya turo baki. Yayi sa'a Mama na gidan ta tare masa kafin Mamin ta tsige shi tace su tafi gida. Sai da su ja fita tace "Mami 'yan hana ruwa gudu" "Yanzu laifin me nayi?" "Shi girkin da mace za ta yiwa miji akwai sirrin dankon soyayya. Kyalesu taje ko karfe nawa ne ta dafa masa tunda yana so." Kitchen Radhiya ta shiga Awwab ya tafi yin wanka. Aikin nata ya dauki kusan awa guda da rabi har ya gama shiri ya shigo tace ya fita kada kamshin girki ya kama masa kaya. "Tayaki zanyi" "Nagode Hammana just wait for me a falo" Kallo ya zauna yi amma zaman duk ya isheshi saboda yau baya son abinda zai nesanta shi da ita. Tunanin yadda zaiyi managing rayuwarsa idan ya tafi ya addabe shi sai gata ta fito tara da arba'in da wani tray mai murfi silver. Murfin zurfi gareshi da fadi marikinsa a mulmule. Kan dinning table ta ajiye ta koma ta dauko banana and coconut shake da ta hada tun kafin ta fara komai yayi sanyi sosai. "Hammana na gama" tace tana fiddo plates. "Inzo inyi miki wanka sai mu ci?" Yace yana murmushi. "Na yafe please ka zo kaci kafin nayi wanka" Hannunsa ta kama ta ja masa kujera ya zauna sannan ta ce ya ci ta shige dakin. Murfin ya bude saboda kamshin da ya cika masa hanci. Kaza ta gasa tayi golden brown irin gashin larabawa ta zagayeta da hadin salad wanda ta kawata da kayan lambu daban daban ga chips a gefe daya. Rufewa yayi bazai iya ci ba bata nan. Wankan yau na daban ne komai has to be extra special yadda Hammanta zaiyi ta tunaninta idan ya koma. Mimi skirt ta saka da wata top mai hannu three quarter ta bata lokaci tayi kwalliya ta gyara gashinta sannan ta fito tana kwas kwas da wani heel shoe dinta. A tsakiyar falon Awwab ya tarota ta bata rai ganin bai ci ba. Kunnuwansa ya kama da hannu. "So nayi ka fara cin abincin sai nayi presenting maka sabuwar member ta Awwab crew" ta kashe masa ido. "Fully employed with all benefits baby...mu ci abincin nan kafin hankalina ya barshi gabadaya" Daga cin abinci aka kwana ana sallama da kyar ya samu tayi bacci saboda kuka. Kuma da kukan ta tashi ta kasa sakin rai karshe yace ba zata bishi airport ba tunda haka ne. Sai da ta ga da gaske yake idan bata yi shiru ba bazai yarda ta bishi ba ta goge hawayen amma kana ganinta kasan kukan take yi a boye. Da suka je yiwa su Mami da Mama sallama gabadaya tausayinta su ka rinka ji saboda fuskarta tayi ja alamun tayi kuka ta gode Allah. Ita da shi suna bayan mota sai dreba su ka tafi yana aikin rarrashi da kwantar mata da hankali. Da su ka dawo gidanta ta shige ta rushe da kuka ko abinci ta kasa ci a haka tayi bacci Zayyana tana dayan dakin za ta rinka tayata kwana. Sai bayan kwana biyu ta saki ranta Awwab yana shan rigima da koke koke a waya dai. Shima dauriya yake yi tare da karfafa mata gwiwa. Kwanansa takwas da tafiya Daddy ya gama yi mata shirin tafiya Nijar ta karasa aikinta. Katsina suka tafi tare da Mami aka bar Zayyana da Rahima gidan Ummi. Kwanansu biyu ya hadata da 'yar kanwarsa matashiya da su ke kusan sa'anni Na'ima saboda kada tayi tafiya daga ita sai dreba da daracta Bigman da cameraman. A can Nijar da connection din kakanni da iyaye aka samu aka hadata da wadanda ya dace cikin sauki tayi aikin sati biyu ta gama hada komai. Lokacin sati hudu ya rage mata ta koma France amma Awwab yace ko zai kara lokaci lallai ta jira shi yazo ya maidata. ********************************* ******************************** 🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚 A Katsina su ka sauka Mami da Daddy su na nan amma bangarensu take zama saboda nauyinsu da take ji ga rashin 'yan hira. Gidan Fauziyya take wuni ko ita tazo. Cikinta ya fito ga Jawad ya kara wayo. Sun zaga gidajen 'yan uwa saboda jan magana na Fauziyya ta kaita gidan Ghazalatu. Nura yana gida su ka zo ya rinka makalewa a jikin matarsa ba ta da damar motsi yana biye da ita. Duk haushi ya isheta wannan aure babu ranar rabuwa ta sake samun wani cikin. Ta kwantar da hankalinta amma rashin kunyarsa tana damunta. Duk wayewarta ta baya Nura kwararren dan duniya ne amma dai ya canja hali tunda yanzu da gaske son matarsa yake yi. Kadaran kadahan ta karbesu aka rabu lafiya. Emzee yana nan yana takurawa Rahima da text idan ta ga dama tayi masa takaitacciyar amsa guda daya tace lafiya. Wannan abu yana damunsa amma ya san shi da fita daga makarantar nan da kyar idan ba sai ya gama ba. Jan ajin nata wani burge shi yake yi ma amma yaki yarda ya kirata a waya. Cikin Ummi ma ya fito tana fama da karatu ga laulayi yaki sauki indai tana gida a kwance take. Yanzu an cigaba ta bangaren Salame tana yawan kiranta su gaisa. Kwana hudu kafin dawowar Awwab saura kuma sati Radhiya ta koma makaranta Mama ta sa a gyara mata 'ya. Gyaran jiki na musamman aka yi mata tana ta saka lalle a kasan gashinta saboda sanin da tayi yana son hakan. Tun dare take jin cikinta a daure da safe ma daurewa kawai tayi tana girki Zayyana tana shara yau bata da lecture. Suna cikin yin breakfast ta ji ciwon cikin ya karu da kyar ta iya tashi tsaye ta ce "Zayyana kirawo min Mami cikina..." Sai da ta taimaka mata ta kwanta akan doguwar kujera sannan ta fita da hanzari. Ko sallama bata yi ba ta fada gidan Daddy na tambayarta me ya sameta tace Adda Radhiya ke ciwon ciki. Cikin sauri Mami ta fito tana tunanin ko ciki ne da ita. Nishi take a wahale Mami ta taimaka mata ta tashi "Zayyana dauko mata hijab ko mayafi mu tafi asibiti" An gama saka mata hijabin jiri na kwasarta ta daga kafa Mami na rike da ita jini ya biyo kafafunta. Basu kula ba sai da ta daga daya kafar tare da zubewa a jikin Mami saboda wani matsanancin ciwo da bata taba jin irinsa ba da ya dirar mata lokaci guda da fitar gudan jini. Tana jin Mamin a rikice tana cewa Zayyana ta fadawa Mama da Daddy daga nan ciwo yaci karfinta jikinta ya saki. Asibitin da suke zuwa na Sami Wadata su ka je jinin yaki tsayawa har lokacin aka shigar da ita emergency. Sai bayan minti talatin aka gangarota zuwa wani dakin likitan yace saidai suyi hakuri bari tayi kuma saboda yadda take zubar da jini sai da suka yi mata wankin ciki. Mami harda hawayenta saboda tausayi Radhiya tayi fayau da ita. Mama ce ta sanar da Ummi itama hankalinta ya tashi ta fadawa Daada shi kam nasa yafi na kowa ma. A asibitin su ka wuni har ta tashi daga bacci. "Mami cikina zafi" tace tana runtse idanu. "Sannu kinji Radhiya zai dena in sha Allahu. Bari na hada miki tea ki sha" So take ta tambayesu me ya sameta amma ganin iyayenta maza sai taji jikinta yayi sanyi a hankali take share kwalla duk da bata san me ya faru ba. Ta riko hannun Zayyana ta ce "me ya sameni ne?" Zayyana sai ta fashe da kuka Mama ta fara fadan za ta daga mata hankali. A tausashe ta dafa kafadar Radhiyan ta soma magana. "Radhiya bari kika yi" Gabanta ne ya fadi ta tuna cewa kwanaki sun shude da tayi missing period dinta tunda Awwab ya tafi shine ta siyo PT strip take ajiyarsa sai ya dawo su duba tare. Ashe ma ba mai zama bane. Iyakar daurewa ko don kada ta bawa Umminta kunya ta tattaro tayi da abin ya ci tura kukan ya matsota sai ta juya musu baya. Kowa na ganin yadda jikinta yake rawa alamun tana kuka Mami tace su fita a barta ta ji saukin zuciyarta saboda cikin fari akwai shiga rai. Kukanta tayi mai isarta bayan sun fita. Ta saka rai da cikin sosai saboda yadda Awwab bashi da aiki sai kwadaita mata haihuwa da irin son da yake yi ya ga 'ya'yansu. A waje Daddy yace yaji shiru Awwab bai kira ba ga matarsa a kwance. Daada yace kada su fada masa tunda dai zai dawo nan kusa. Kuma bai kamata a tayar masa da hankali ba duba da yanayin aikinsa rayukan jama'a a wuyansa. Shadayan daren Nigeria Awwab yayi landing jirgi a Canada. Kamar kullum yana isa masaukinsu ya kira Daddy da Mami sannan Radhiya. Yayi ta waya shiru ta na shiga ba'a dauka an manta ta a gidan. Mami ce za ta kwana da ita kuma ta riga ta yi bacci sai ya nemi Zayyana taki dauka saboda bata san me za ta ce masa ba. Lokaci ya duba ya san dare yayi amma Radhiya ta rike schedule dinsa sosai na satin ta san lokacin tashin jirginsa da sauka wani zubin kafin ya kira ta neme shi. Komai dare a Nigeria sai ta jira shi duk fadan da zaiyi ba ta ji. Washegari da asuba yayi ta kira shiru ya kuma kiran Zayyana tace masa bacci take yi. Ya dai ji ne bai yarda ba . Mami ya kira da gari ya waye ya kusa tashi yace mata ya kasa samun Radhiya jikinsa na bashi babu lafiya kuma Zayyana na yi masa wasa da hankali. Hakuri ta bashi tace da kanta za ta kaiwa Radhiyan wayarta ce ta fadi. Shiru lokacin boarding yayi ya sake tashi back to Germany cike da damuwar da ake guje masa. Sai daren ranar aka kai mata wayar yana sauka ya kuma kira. Fada yayi niyar yi mata saboda ko faduwa wayarta tayi ya bar mata kudi da za ta iya sayen wata sannan ga wayoyinsu Mami. Amma yana jin weak voice dinta ya ajiye makaman yakin. Karyar mura tayi masa ya bi ta da toh ba don ya yarda ba. Da yamma ranar aka sallameta Mami ta hanata komawa nata gidan tana kulawa da ita sosai. Karamin wankan jego ta yi mata ta rinka gasa mata jiki ga abinci mai gina jiki ita da Mama su yi Ummi da Rahima sai dai su zo dubiya. Ranar da Awwab zai dawo taji karfin jikinta sosai tayi masa abinci. Naman sa ta yiwa yanka madaidaita ta tafasa da kayan kamshi su, citta, tafarnuwa, black pepper da albasa. Ruwan naman bayan ta tafasa shinkafa ta wanke ta juye shi ta karasa dafata da shi. Butter ta zuba a non-stick pan mai zurfi ta soya sausage da lawashi wanda ta yanka kananu juye shinkafar a kai batare da ta saka curry ba ta soyata. Naman shima soya shi tayi sannan ta hada attaruhu da albasa wadatacciya tayi grating ta soyasu da maggi da curry sannan ta hade da soyayyan naman. Sai kuma coleslaw da kunun aya. Gidan ya sha turaren wuta ga girkin amarya da sanyin AC Ba ta je airport din ba ta zauna kwalliya. Motar na tsayawa a gurguje taje ya gaishe da iyayensa da su Baba Hadir ya tashi Mama tana zolayarsa bai iya cewa komai ba sai dariya ya taho gida. Yana kama handle din kofar kafin ya murda ta riga shi. Kallon kallo su ka tsaya yiwa juna shi ya kara yi mata kyau da cika. Awwab na yi mata kallon fuskarta ta fada duk da kyaun da tayi mai fizgarsa. Rungumeta yayi tun a bakin kofa ya saki jakarsa yana kissing dinta cike da kewa. A hannu ya shige daki da ita sai da ta ga da gaske yake ta dakatar dashi saboda jininta da bai dauke ba. Bai damu ba ya rungumeta kawai a jikinsa yana fada mata yadda yayi kewarta. "Tashi kayi wanka kaci abinci Hammana" ta ja hancinsa. Wasa yake da gashinta ya dago ta su ka zauna "babu ko daya da zanyi sai kin fada min abinda ake boye min baby. Me ya sameki 4 days ago?" Babu hanyar guduwa ta sunkuyar da kai ta ce "Hammana miscarriage nayi" Jikinsa a take ya soma rawa ya janyota ya kankame "Schatzi dama kina da ciki?" Kuka ta saka a hankali "Ban tabbatar ba shine na siyo abin PT idan ka dawo mu duba" Ya dago fuskarta yana kallo "was it painful?" Ta gyada kai ya sake rungumeta yana bata hakuri da rashinsa a kusa lokaci irin wannan. Sabuwar jinya aka koma yi kamar yau abin ya faru ya hanata yin komai. Iya kwana ukun da suka yi kulawa yake bata sosai. Ranar juma'a da daddare su ka tashi zuwa France inda ya cinye hutunsa ita kuma tana zuwa makatanta amma da ta dawo sai yawo tare da su Arifa ko ita kadai da Awwab. Ranar da zai tafi kuka tayi da kyar Tante ta shawo kanta. ********** A hankali kwanaki ke tafiya cikin Ummi ya shiga watan haihuwa ga jarabawarsu ta karshe da suke yi. Lokacin Fauziyya ta kusa arba'in din Sahla jaririyarta. Zahra kuma cikinta yana wata biyar. Cikin ikon Allah sai bayan kwana takwas da gamawa ta tashi da nakuda. Allah Ya taimaketa yadda ta sha wahalar cikin sai haihuwar ta zo mata cikin sauki saboda ko minti talatin basuyi ba da zuwa asibiti aka fito musu da sankacecen saurayi kamar Radhiya tayi kakinsa har dimple din gefe dayan. Farincikin Zayyan Tureta a wannan rana ba zai fadu ba. Mairama ta sha addu'a sosai a wurinsa sai da tayi kuka. Ya kira Malamijo yace a yiwa shanu uku kudi a garkensa a yanka ayiwa mabukata sadaka. Mami ce ta yi mata wanka saboda a ganinta duk girman Mairama bata da wani cikakken experience game da haihuwa. Mama kuma ta sille jariri aka yi masa hoto ana turawa yayyensa da ke nesa. Radhiya ji tayi kamar tayi tsuntsuwa ta iso gida wurin baby da Ummi amma tana da sauran jarabawa daya sati mai zuwa. Ita da Tante da Arifah mai tsohon ciki suke zuwa siyayyar kayan baby saboda su Mammee sun ce ta hado kayan barka na gani da fada. Akwati biyar tayi manya manya uku na baby biyu na maijego. Emzee da Ibrahim su ma makaranta ta sarke musu wuya ana ta jarabawa. Su Fauziyya ke rokon alfarmar kada ayi suna babu su Ummi ta ce babu taron da zata yi. Mama da Mami su ka ce sai anyi. A zahiri Ummi bata son yi saboda rashin Radhiya da Emzee amma kunya ba zata bari ta fada ba. Ita dai burinta ace 'ya'yan da suka sha gwagwarmaya tare dasu za'ayi komai.a lokacin da Allah SWT Ya dube su. Shima uban gayyar mijin nata kasa fada masa tayi sai da hillata ya ganota. "Su Fillo wasa wasa kina da son 'ya'ya fa" yace yana dora jaririn a kafadarsa. Tayi dariya "Duk abuna na kai dan mutan Tureta ne?" "Ko kusa a bayana kike saboda haka ki rinka komawa gefe idan suna kusa ba ta ke nake yi ba" "Naji amma ka bani jaririna don kasan shi dai bana jin kunyarsa kamar sauran" Zama yayi kusa da ita ya ce "na rasa sunan da zan saka masa Fillo. Ga Major, Hadir da Baban Arifah cikinsu waye baiyi min halacci ba? Kinga ko da Hadir yake mai lalura nayi imanin da yana da hali kamarsu Mairama zai iya sadaukar da komai nasa domin iyalina." "Na sani Sojana ko dai na haifo wasu ne a cike sunayen" ta ce tana dariya. Ranar kwana hudu kenan da haihuwa nauyin 'yan uwan nasa rabin jiki yana damunsa ya rasa wa zaiyiwa takwara a cikinsu. Washegari da aka kawo Mami tare da Daddy da Baba Hadir su ka zo. Daddy ya mika hannu ya karbi kyakyawan jaririn daga hannun Zayyan ya mikawa Hadir. "Ni na yiwa Alheran yau kuma kaine da danka ka zaba masa suna don na rasa me yake damun abokinka sai wasa yake mana da hankali" Murmushi Baba Hadir yayi ya duka ya yiwa yaron addu'a sannan ya dago kai yace "Allah Ya raya mana NASURULLAH" Daddy yayi murmushi ya karbi yaron ya sumbace shi kumatun hagu da dama "hakika Allah mai kyauta da kari cikin nasarar da Ya bamu ne muka wayi gari mu ka ga wannan rana ace Zayyan ya dawo garemu har Allah Ya azurta shi da sake samun karuwa." Kwalla ce ta taru a gefen idon Zayyan ya sa hannu yana kade ta Daddy yace "me nake gani haka? Are you still a Lady?" Baba Hadir da Zayyan sai dariya yana cewa "wallahi namiji ne ranka ya dade" Excellency Nasiruddeen Aliyu wanda ya sake samun kujerar gwamnan Plateau a daren ranar ya sauka a Abuja ganin wannan dan baiwa da za'a iya cewa alkawarin Allah Ya cika domin haihuwarsa baiwa ce. Sunansa da na Nasrullah daya ne duka daga nasara sai dai bambanci kadan shiyasa yace shi aka karrama aka yiwa takwara saboda haka gagarumar kyauta yayi masa wadda ta tsorata iyayensa sai dai yace babu abinda zai yiwa jinin Zayyan ya fadi domin ko me ya zama a rayuwa sanadiyar zubar jini da hawayen Tureta ne. Kamar lokacin DK dan gidan Zayyan don babu abinda ya kware a fada irin Daada shima Nasrullah an dage taron sunansa sai yayyensa sun dawo nan da sati biyu ake sa ran kowa yana gida banda Zahra. Tante ta tafi Nijar da kwana biyu Radhiya ta koma gidan Yousuf jiran Awwab yazo zasu tafi Abuja. Kafin.ya iso yayi booking hotel online daga airport ya gudu da matarsa sai washegari su ka hadu dasu Arifah a wurin convocation din Radhiyan. Kyaututtukan da ta samu ba kadan ba musamman saboda shirin Military Voice. An yaba mata sosai basu bar makarantar ba sai da a gaban shugaban makarantar tasu da Awwab ma'aikatan Aljazeera su ka kawo contract na shekara hudu wanda su ka bata tayi Military Voice Africa (MVA). Da amincewarta kuma anyi alkawarin acknowledging dinta a matsayin wadda ta samar da shirin suka nemi izinin yin Military Voice Asia da Europe. Kudin da zasu biyata ba na wasa bane bukatarsu duka kasashen Africa guda 53 taje ta gana da sojojinsu da matansu su kuma zasu ware lokaci domin sanya shirin sau daya a sati. Yadda za'a rinka dauka da gabatarwa duk yana cikin contract din. Awwab baiyi gaban kansa ba ya kira Daddy da Daada suka bashi goyon baya sannan ya yarda ta amince aka saka sunansa a matsayin wakilinta. Kwana biyu su ka kara sai gida Nigeria da kwalinta na degree wanda ta fito da sakamako mai kyau. Iyaye da 'yan uwa an tayata murna. Da gudu ta shiga gida sai da ta dauki Nasrullah hankalinta ya kwanta. Kasa ta sauko dashi wurin Awwab ya rungumeta da babyn yana cewa Allah Ya nuna masa ranar da za ta haifa musu nasu. ********** Shirye shiryen zuwa P.O.P din Emzee suke yi Daada yace Ummi babu inda zata saboda Nasrullah baiyi kwari ba. Sai da ta ajiye kunya ta dangana da hadashi da Daddy ya barta taje. As expected Second Lieutenant Muhammad Zayyan Tureta ya fita da sakamako mafi kyau a wannan shekarar saboda kokari da kwazonsa musamman akan abinda ya shafi training dinsu. Ya sami lambar yabo kala kala iyayensa basu da abin cewa sai godiya ga Allah. A wannan rana Malamijo sai da yazo halartar taron sai dai ganin sojoji a kowace kusurwa rike da bindiga ya kada masa hanji. Tare su ka dunguma zuwa Abuja yau dai gashi a muhallin Mairama Daso. Yana rungume da karamin jikansa yana mai mika godiya ga Allah da Ya tsawaita kwanakinsa ya ga haduwar kan 'ya'yansa. Gida MashaAllah ya cika da 'yan uwa daga rugar Barkindo, Sakkwato, Nijar da Sumaila. Sunan da ba'ayi ba aka hade da murnar kammala karatun Radhiya, Emzee, uwar gayya Mairama da bakon duniya Nasrullah. Major General Zayyan Tureta sai da yayi kukan farinciki a daki kafin ya sauko faefajiyar gidan inda ake taron. Yau shine Allah Ya yiwa arzikin ganin wannan rana wadda da sai dai ayi babu shi. Kyauttuka kam an sha su. Ibrahim kamar ya lashe Zayyana don so shi kuwa Emzee da Rahima tsakaninsu sai satar kallon juna. Ta gama makaranta abinta tana jiran a fara karatu a school of nursing da ta sami gurbi. Emzee ya mamayeta yadda Awwab yace duk motsinta yana wurin amma babu yiwa juna magana. Ita ta sakawa ranta ta hakura dashi ne duk da tasan cewa yaudar zuciyarta take yi. Kullum sai ta jira text dinsa wanda babu kalmar soyayya sai nuna tarin kulawa. Sai dare su Radhiya suka koma gida Awwab ya jikata da salon soyayyarsa. Washegari ya damka mata mukullin hadaddiyar motar da ya saya mata a matsayin graduation gift. ********* SALLAMAR BANKWANA Wata hudu bayan gama karatun Radhiya suka je gidan Daada da Awwab gaishesu. Emzee ya tafi wani training a Warri yanzu mukaminsa ya koma Lieutenant. A falo su ka yada zango tana yiwa Nasrullah uban 'yan kyuya wasa ya hade rai abinsa yana neman Ummi da idanu ta ce, "Indai nice za ka zo ka sameni ne har gida kuma ba bari zanyi ka shigo ba" "Ba dole ya rinka gudunki ba kina zare masa idanu" cewar Awwab ya karbe shi. Kusa da Daada ta koma suna hira a hankali ta soma hade fuska tana sansana jikin kujera da su labule tana dagawa. "Lafiya dai kike min dage dage?" Cewar Ummi. Sake baza hanci tayi da kyau tace "Ummi warin magani ko dai maganin Nasr ne ya zube a wani wuri?" Daada na jin haka ya ajiye jaridar hannunsa yana kallonta "maganin kamar panadol yake Alheran?" Ta tafa hannu "eh wallahi Daada ka canka..." Ummi ya kalla ya soma dariya yana cewa "kina ji kamar ma ya rube ne?" Awwab ne ya bashi amsa "jiya sai da tasa na na juya gado da shirin falo gabadaya muna neman maganin da ya rube. Kuma ni bana jin komai wallahi ita kadai take ji" Dariya sosai Daada yake yi Ummi ta bar wurin da sauri don kunya tana ji yana cewa "wannan warin bazaka taba jinsa ba Awwab. Ke kuma sai hakuri yanzu kika fara ji amma ku je asibiti kiyi musu complain. Ina jin likita kika hadiya" Ta zaro ido "likita kuma Daada?" Ummi na jinsu ta dawo da sauri saboda ba karamin aikin Zayyan bane sakin baki a gaban suruki shiyasa tace yazo wayarsa na ringing. Ita kadai ta dawo daga baya suka yi sallama Awwab ya wuce asibiti da ita duk da tana cewa babu inda yake maga ciwo sai warin maganin. Gwajin ciki suka yi mata tana dashi har na sati tara. Murna a wurin Awwab ba sai an fada ba. Auren nasu shekara guda da watanni kadan ga Arifah tana nan da Nasrin dinta wadda sunan Tante taci aka juya mata shi. Tare suke kula da cikin yana ta girma har yayi wata bakwai. Laulayi gareta kamar Ummi shiyasa idan zai koma aiki sai dai Zayyana ta dawo gidan ko Rahima. Ranar wata asabar tafiya ta kama Daada zuwa Asaba aiki shi da wasu a karkashin jagorancinsa. Convoy din motoci biyar suka yi ciki Emzee da yake ta fushin kasa samun kan Rahima yace zai raka shi. Basu taba tafiya daga shi sai dan nasa ba saboda haka wannan ta basu damar yin hira sosai irin ta uba da da. Zayyan yasan komai game da lamarin Rahima ya rinka bashi shawarar yadda zaiyi ya shawo kanta su daidaita. Sun wuce wani kauye da kadan su ka kula motoci da yawa suna dawowa a guje wasu ma da ribas suke tafiya. Nan da nan yaransa su ka fara kiransa suna tambayarsa ko su ma su juya. "Are you crazy?" Ya dakawa mai tambayar tsawa "civilians su gudu muma mu gudu to waye zai kai taimako idan ana bukararsa" Kai tsaye ya bada umarnanin kada a tsaya. Kowa yana sanye da kayan sojoji tunda official tafiya ce banda Emzee dan rakiya. Suna karasowa motoci suka gani guda shida da 'yan fashi su ka kama sun kashe titin ta daya bangaren babu mai karasowa ga harbi suna yi kamar hauka sun kashe drebobi uku masu kokarin guduwa. Ganin motocin sojoji ga su suna dirowa da shirinsu yasa ogansu kiran wadansu ashe mugun yawa garesu. Tashin hankali ne muraran mutanen da suka biyo hanyar suka tsinci kawunansu a ciki. Baka jin komai sai tashin harsashi da kukan mutane. Abin ya wuce zatonsu dan karamin kauyen da yake gefen wurin shima sun yiwa mutanensa mummunar barna saboda rashin basu mafaka. Jikin Emzee a take ya fara rawa yau gashi a filin daga na gaske. Major General Zayyan tuni ya fito daga mota a sukwane babu wani tsoro ko fargaba yana bada umarnin duk wanda su ka kama zaiyi gardama su harbe shi a inda zai raunata shi sannan su tabbatar anyi saving mutanen wurin. Bindiga kirar AK47 ya dauko ya damki hannun Emzee ya bashi cikin rawar hannu ya saketa a kasa ga sautin harbi da kukan mata daga wannan kauye ya yawaita. Dauko bindigar Zayyan yayi ya ratayata a hannunsa kamar yadda ya rataya wadda zaiyi amfani da ita ya rike fuskar Emzee a tafukan hannunsa. "MUHAMMAD" ya kira shi da murya ta umarni babu wasa ko rangwame saboda dan cikinsa ne "this is why you became a soldier Lieutenant. You live and die for your country. Wancan kukan da akeyi da firgici aikinka ne ka tsayar dashi ka tseratar da mutanen nan" Jiki na rawa ya gyada kai yana jin kunnuwansa na neman toshewa saboda bala'i. Bindigar Zayyan ya sake mika masa yana jin wani karfin gwiwa su ka fara hawa dan tudun da zai karasa dasu kauyen Zayyan yana ta bada umarnin a kwashe tseratar da mutanen da aka kamawa motoci su bar wurin. Saboda wutar da aka bude 'yan fashin da yawansu sun buya ne a bayan gidaje suna harbin kan mai uwa da wabi. Sai da suka gama hawa tare da wasu sojojin Zayyan ya rike hannun Emzee idanunsa suka dan kada na dakika kadan "ka taimaka min na maidawa Mairama danta cikin aminci...Allah Ya tsare min kai" Bai jira komai ba ya kusa kai tsakanin katangar wani gida da na kusa dashi inda ya fi jin harbin ya soma sakarwa 'yan fashin nan harsashi. Emzee tuni ya nemi tsoro ya rasa sai aikin neman lada ya bautawa kasarsa. Harbi suke yi ba kakkautawa sai da suka tabbatar sun kora 'yan fashin suka soma dauko mutanen da suka jikkata a wurin suna dawo dasu bakin titi bayan kiran waya domin a kawo musu agaji. Duk sunyi futu futu dasu a tunaninsu sun gama Emzee ya jiyo kukan mace daga wani gida. Kutsa kai yayi ya hadu da mata mai tsohon ciki a durkushe tana murkususu. Fita yayi da sauri ya kira Zayyan dake rike da wani tsoho. Wani sojan ne ya karasa da tsohon shi kuma ya bi bayan Emzee. Suna shiga gidan aka rufe kofa 'yan fashin nan su hudu su ka sakawa matar bindiga sannan aka umarci Zayyan ya fadawa yaransa kowa ya bar wurin saboda tsaron rayukansu suka yi garkuwa da su. Tsananin tashin hankali sun shige shi domin matar gidan tana cikin mawuyacin hali. Zayyan bashi da zabi saboda rayuwar matar da dansa ya bada wannan umarni. Yaransa sun so yin gardama sai yayi musu bayani cikin lauya zance wanda su kadai sojoji ke ganewa akan cewa zasu iya hauro katangar gidan amma su bada lokaci. Cikin wadanda suka sami tserewa nan da nan labari ya bazu cewa 'yan fashi sun tare hanyar Asaba sunyi garkuwa da wasu sojoji. Yadda labari ke gudu a social media kafin a farga Ibrahim da ke Kano ya sami labarin. Hankalinsa a tashe saboda dazun nan suke chatting da Emzee sai ya ji shi shiru. Baba Hadir ya kira ya tambaya yace baiji labari ba. Shi da Daddy su ka shiga neman layukan Zayyan da Emzee shiru. Headquarter su ka je neman ba'asi amma aka so boye musu. Sau kuma ga 'yan jaridu da gidajen tv zancen kenan dai akeyi. Daddy da Baba Hadir basu bar wurin ba har dare sai da Baban Arifah ya zo sannan aka saki rahoto cewa lallai an sami distress call daga hanyar Asaba sojoji na neman taimako an kama shugabansu Major Gen. Tureta da dansa. Kan kace meye wannan zance ya zaha lumgu da sakon Nigeria ga masu mu'amala da social media ko sauraron labarai. Fadin tashin hankalin da Mairama ta shiga ma bazai yiwu ba. Tayi kuka har hawaye ya kafe a idanunta. Ga da ga miji ko shekara biyu baiyi da dawowa gareta ba. Duk wannan tashin hankalin kuma ga Radhiya can a labour room da ga jin zancen nakudar dole ta kama ta. Ga Nasr yana wani irin kuka na fitar hankali Mairama ta rasa inda zata tsoma ranta. Tana goye dashi suna asibiti tare da su Mami saboda an hanata zama ita kadai tana fama da tunani. A can kauyen da sojojin su ka haura gidan cikin dare basu ga kowa ba. Ashe karbe abin maganar Zayyan suka yi aka fasa sannan su ka tafi dasu cikin dajin wai bazasu barsu ba sai sun tabbatar cewa sun tsira. Ana wannan tafiya ga mai ciki ciwo yaci karfinta a wahale tace haihuwa ce suna tsare a wani kango. "Ku taimaka min" tace cikin tsananin azaba. "Daada taimaka mata ni zan rinka lekawa in shammacesu mu gudu" Emzee yace ko kallon matar baya son yi saboda tsoro. Duk da rashin wadatar haske Zayyan harararsa yayi "kai ya kamata ka taimaka mata saboda idonka yafi nawa gani girma ya kamani" "Laahhh Daada tun ina yaro aka ce na gado ciwon idon Ummi" yace yana matsawa baya. Zayyan bai ga abinda zai sa shi ganin haihuwa ba don gara a cigaba da fafatawa a wurinsa. Dakewa yayi yace "Lieutenant this is a command ka taimaka mata. Ba don chanjin zamani ba nasan cewa haihuwa a lokacinmu da naku da bambamci da ni zanyi komai" ya hadiyi yawu mai daci. "A BEG MAKE UNA HELP ME"(don Allah ku taimaka min) matar tace tana ciccije lebe ga 'yan fashin suna daka tsawar tayi musu shiru ko su harbe ta. Emzee na jin haka ya duka a gaban matar nan daga shi sai hasken farin wata yayi abinda bai taba zato ko tsammani ba. Ashe aikin soja ya wuce duk yadda ake tunaninsa. Yau shine da karbar haihuwa abinda ko a tv bai taba yarda ya kalla ba. Yana gabanta tana nishi tana fada masa ya duba ko kai ya fito. Muryar mahaifinsa yaji ya dafa kafadarsa "Make me proud my son." Ya tashi yayi waje batare da sauraron kiran da Emzee yake yi masa ba. Tashi yayi zai bi babansa matar tayi wani nishi iya karfinta sai ga da yana neman faduwa dole ya tare ya rike mata shi. Wuka ta dauko a gefen rigarta ta bashi ya yanke cibiya tace masa tun da mutanen suka fara harbi ta boye wukar domin tsaron kanta ashe zata yi musu amfani. Karar harbi suke ji daga waje ya tashi da jinjirin nan a jikinsa ta bashi wani mataccen dankwalinta ya zura yaron ya daure shi ta gabansa kamar wanda yayi daurin karaya. Yana fita ya sami maza uku a kwance ashe Zayyan ya shammacesu ne ya karbe bindigar daya. Harbi na hudu yaji ga hasken asubu ya fara ratsowa daidai da tahowar Zayyan daga bayan wasu bishiyu. Murmushi Emzee yayi ya taho gareshi da sauri ya mika hannu zai rungume shi kawai su ka ji sautin fitar bullet sai ga Emzee ya tafi gabadayansa ya fada jikin Zayyan tare da jaririn. Da hannu daya Zayyan ya riko shi suka kai kasa ya daidaici mutumin da yayi harbin ya sakar masa bullet a tsakar ka kafin ya fara kiran sunan Emzee a gigici yana kukan da ko fuskar Emzee din baya gani sosai. "Muhammad kada kayi min haka ban dawo domin in ga mutuwarka ba...Muhammad kada kasa na kasa fuskantar mahaifiyarku" kuka yake yana juya Emzee ga jaririn jikinsa ya na neman a ina aka harbe shi. Ba karamin tsorata yayi ba da ya ji a gefen cikinsa ne ya leka kangon matar ta tashi da dafa bango ya bata jaririnta sannan ya dawo ya goya Emzee su ka fara gudu saboda yana tsoron ko akwai wasu 'yan fashin a kusa. Sai da rana ta fito sosai wuraren karfe goma su ka bullo a bakin titi jikinsa jike da jinin Emzee. Motocin sojoji ne birjik a wurin an baza search party sai fito da 'yan fashi suke yi. Wani ne ya fara hango su da sauri ya soma ihun murna sauran su ka taho aka hadasu su ukun aka zuba a mota zuwa airport saboda a zatonsa Emzee ya riga ya cika. Ambulance ce tazo daukarsu daga airport din Abuja a guje aka tafi dasu National hospital. A daidai wannan lokacin kuma Allah Ya sauki Radhiya ta haifi 'yarta mace. Theatre aka shiga da Emzee emergency cikin sa'a bullet din bai taba muhimman organs ba aka cire. Zayyan yana tsaye a bakin kofar Daddy, Baba Hadir da Mairama suka iso. A guje ta rungume shi tana kuka sosai yana bata hakuri akan suyi masa addu'a. Suna kallo aka gangaro shi zuwa dakin hutu idanunsa a rufe. Radhiya ko awa batayi da haihuwa ba tace a kaita wurin Emzee da Daada. Yanayin da take ciki na tashin hankali Awwab ya daukota da Rahima da Mama aka bar babyn a asibiti da Mami. Jigum jigum ake zaune Radhiya ta fado dakin tana kuka a jikin Daada yace tayi hakuri. "Kai Adda ashe dai kina sona" su ka ji Emzee yace da gajiyayyar murya.. Ita da Ummi da Daada suka yi kansa Rahima tana gefe tana kuka. Sannu sannu suke yi masa ya kalli Radhiya "Adda ina cikin?" "Tana asibiti ta taho tarbar Baffanta da kanta" tace tana murmushi. Sai lokacin Daada ya kula "Taho kinji Innata mun saka ku a tashi hankali" ya rungumeta tare da Nasr da ya makale masa sai da ya ganshi ya dena wannan kukan. Da kyar Emzee ke magana ya yafito Baba Hadir ya ce "Baba don Allah ka aura min Rahima kafin na mutu." Kofar fita daga dakin Rahima ta nufa da sauri Daddy ya tsayar da ita "ko sannu baki tsaya kinyi masa ba zaki gudu" "Ba dole ba daga tashinsa zai matsawa 'yata" cewar Ummi tana harararsa. "Daddy kasa baki wallahi ni aure nake so" Daada yace "Anya yaron nan ba anasiziya bace bata sake shi ba?" Emzee yayi dariya a ransa ya kuma kafe Rahima da ido "idan bata amince ba ni dai ku aurar dani kada in sake zuwa wuri irin wannan ban dawo ba" Rahima na jin haka ta zaro ido Radhiya ta rike hannunta "ta amince don Allah ka dena yi mana sumbatu" Dariya aka saka baki daya sannan su ka fita domin barinsa ya huta ita kuma Radhiya ta koma wurin babynta. Bayan kwana hudu Emzee yaji sauki sosai an nemo 'yan uwan matar da ya karbi haihuwarta. 'Yan jarida har dakinsa matar tana yi musu godiya shi da mahaifinsa tace yaya sunansu. A tare su ka ce "ZAYYAN" Ta ce "duka ku biyun?" Su ka gyada kai. Jaririnta ta mikawa Daada ta cewa "ina fata wannan Zayyan din ma ya zama soja jajirtacce kamarku wanda zai iya sadaukar da rayuwarsa domin kasarsa. Nagode" Emzee ma sai da ya karbi yaron ya rungume shi saboda akwai wani bond kasancewar shi ya karbi zuwansa duniya. Bayan sun tafi ne Emzee yake fadawa su Daddy wayon da Daada yayi masa akayi ta dariya. A gefe guda soyayyarsa da aka sakawa comma (,) shi da Rahima ta sake daukar wani sabon salo mai shiga rai. Awwab da Radhiya suna tare da 'yarsu ya lalace wurin basu kulawa da soyayya. Ranar suna wanda aka yi gagarumin taro yarinya taci suna Zainab suna kiranta (Boubou). Mama bata taba zaton wannan karamci ba ai kuwa tayi rawar gani sosai. Boubou na ta wata takwas aka sake taruwa domin bikin da aka dade ba'ayi irinsa ba na Barr Ibrahim Hadir da Zayyana Mustapha wanda aka dauro aurensu a Katsina sai kuma Lt. Muhammad Zayyan Tureta da Rahima Idris Sumaila wanda aka dauro a Sumaila. Salame sai da tayi kuka ranar. Gida flat sama da kasa Daada ya kama musu babu nisa da su Radhiya saboda yace amaren da angwayen akwai danyen kai duka da kuruciya. Babu wanda ya rakasu gidajensu Emzee ya shiga nasa da yake kasa ya wuce daki kai tsaye inda Rahima ke zauna akan gado an rufe mata fuska da mayafi. Yana shigowa gadon ya hau ya tura kansa karkashin mayafin ya kwanta akan cinyarta. Kunya ta kamata ta soma ture shi. "Ya Emzee ka tashi don Allah" Sake gyara kwanciya ma yayi "saibkin gyara min suna zan tashi" "Me kake so nace?" Kamshin da take fitarwa da tsananin kyaun da tayi yasa shi lumshe ido yana budesu a hankali. "Kin fini sani" "Muhammadun Rahima ka tashi" tace tana murmushi gashi yaki bari ta budesu daga lullubin. "Rahiman Muhammadu ina sonki wallahi" Murmushi tayi tana cewa ya tashi tunda ta fada yace to. Dago kai yayi kamar zai tashi sai ji tayi ya birkitota gabadaya kansa ya rungumeta ya shiga kissing dinta. Da kyar ya tuna ya kamata suyi nafila ya dagota suka yi alwala da sallah. A baki ya rinka bata nama ita kadai take ci yana bin jikinta yana kissing dole ta hakura don ba iya ci zata yi ba. A daren ta tabbata Rahiman Muhammadu matar Muhammadun Rahima masoya daga Allah. BAYAN SHEKARA BIYAR Gidan Daada a hargitse yake da 'ya'ya da jikoki ana ta shirin zuwa Award Night da gwamnatin tarayya tare da hadin gwiwar kasashe da dama na Africa suka shiryawa Alheran Radhiya saboda services dinta to the military. Captain Muhammad Awwab da gis one and only Scharzi Alheran 'ya'yansu uku Boubou mai shekara biyar, Haidar takwaran tsoho mai ran karfe Malamijo mai uku da rabi sai Fatima (Islam) mai biyu ga karamin ciki. Zahra bayan Femi ta kara da Hassana da Hussaina (Taye da Kehinde) ana kiransu da duk wanda mutum yaso kira, sai Mu'az. Fauziyya bayan Jawad da Sahla ta kara da Mustapha (Ansar) da Iman. Arifah biyu gareta Nasrin da Nasir. Zayyana tayi biyu itama Zayyan (Junior) da Hassana (Mami), iyayen garke Rahima da Emzee suna da Hadir (Little), Idris (Abba), Ibrahim (Khaleel) sai Kauthar don haihuwa take duk shekara maigida kuma ya hana planning. So da kauna yake gwada mata kamar ya hadiyeta. Anyi taro lafiya an gama lafiya kowa ya koma gida cikin kewar juna. Tun dare Radhiya ta gama hadawa Boubou da Haidar kaya zasu tafi Katsina dasu Mami gidan zai huta na kwana biyu daga kiriniyarsu Awwab ya gama shirin sabon amarci. Gidan Daada su ka fara zuwa da yaran inda su Mami zasu zo daukarsu. Shigowar motarsu ke da wuya DK da yake wasa akan keke ya arta a guje ya shige cikin gida yana kwalawa Daada kira. "Menene DK?" Ya leko falon daga sama. "Su Boubou ne Daada" yace kamar zaiyi kuka. "Taho mu rufe kofa" ya dauke shi suka shige dakinsa ya kulle kofa Mairama tana musu dariyar wannan abu. Boubou na shigowa ta fara bude daki daki da bindigar wasanta a hannu tana kiran "Uncle DK". Yadda take matsanta masa da fitina idan yaji tazo baya iya zama. Nasr kuwa boss ne mai zaman kansa ba ta zuwa inda yake dama sai yaso wasa. Idan ka ga ya sake Ibrahim da Zayyana ne a gidan anzo da Mami. Gajiya Boubou tayi da nemansu ta fada jikin Ummi "Umminaaaa" "Boubou naaaa" Ummi tace tana jan hannunta zuwa dakin Daada, Radhiya da Awwab suna dariya don sun san sai anyi drama. Ai kuwa muryar Daada su ka ji yana cewa "Zainab ba fa zaki rinka zuwa kina takura kin yaro ba" sannan suka sauko su duka su Mami sun iso ga Baba Hadir da Mama. "Ummiiii" ta tabe baki tana kukan abinda Daada yace. "Rabu dasu idan kin zama soja babu ruwanki da kowa" cewar Mama Ta saki murmushi dimple dinta biyu suka lotsa. Fakar idonsu tayi ta dane bayan DK tana kai masa harbi hannu da kafa "zo muje muyi training Uncle DK kada a kaimu makarantar soja su koromu" Awwab ya tashi zai rabasu Baba Hadir ya hana sai zama da suka yi suna kallonsu ana dariya manya na fassara lamarin. Yana daga kwance ta danne shi yace "ni bazanyi soja ba don Allah ki dagani" Idanunta ta ware a kansa tana sukuwa a bayansa har ta soma tara masa gajiya "to waye zai kareka idan ana fa'a" Hantsilota yayi yana nishi "ba gaki ba idan kin zama sojan sai ki kareni" Tayi wani murmushin bada fadi ita ga soja sai kuma ta janyo kwalar rigarsa yana shirin guduwa "idan zan kareka ni me zaka rinka bani to?" "Boubou wuyana" ya ce ta sake shi da kyar "zan rinka siyo abinci ina kawo miki yadda Daada yake kawowa Ummi Baba kuma yake kaiwa Mama" "Ahh irin na Abbana da Mamma kenan fa...to na yarda amma wallahi ka goyani" ta haye bayan nasa Nasr ya janyota ta fado, Dama shima tara shi take yi ai kuwa ta juya ta ce "Haidar taron dangi" Barin kayan wasan yayi suka hadu shi da Boubou suka danne Nasr. Baba Hadir na ganin haka ya tashi ya raba fadan ya hadasu da sweet suka tafi yana jin DK yana Boubou ki kyaleni sai ta ce idan ta zama soja ta fasa kareshi. Awwab da Radhiya basu bi ta kan sauran yaran ba dama nan suka yi niyar barinsu suka wuce gida yana cewa yau zai kwana goge mata janbaki. Falon ya rage Zayyan da Mairama, Mustapha da Hassana sai Hadir da Zainab su ka zauna hira suna tunowa juna wasu lokuta da suka gabata da yadda rayuwa ta sauya musu. A kowane yanayi sai dai bawa yace ALHAMDULILLAH.